********************** ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** ************************* ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ************************** 💛 HAJAR 💛 by Nafeesah Yusuf Nagoda....✍️ A.K.A ~~(Feenerh_feeche)~~ BISMILLAH.. Dukkan godiya ga Allah ma ɗaukakin sarki da ya bani ikon fara rubuta wannan littafi, kuma ina roƙonsa ya bani ikon hattamashi lafiya, ɗumbin gaisuwa zuwa ga mahaifiyata Haj Anty, My sisto Hajiya kema ina miƙo gaisuwa, my little sister Mancy and my little brother Aliyu kuma na gaisheku da gudummuwar ku wajen disturbing ɗina idan ina update, my fans kuma bazan manta daku ba a duk inda kuke Feenerh_feeche na gaisheku. Let's connect.... _Facebook account @ Feenerh feeche _Facebook page @ Feenerh feeche Novels _Facebook group @ Feenerh feeche Novels _Arewabooks @Feenerhfeeche02 ~~~~~~ {1..} wane mahalukin ne da yake lungun ƙunshi a unguwar Dala bai san gidan gini ba, aiko unguwar ka shigo sai ka san gidan gini ballanta ƴan unguwa, gida ne wanda yayi fice yayi shura a fannin hargitsi da rashin zaman lafiya, hakan ya samo asaline daga iyalan gidan da suka kasance ƴan bala'i da jaraba, Magidancin gidan da ya kasance wani soloɓiyo matansa biyu suke juyasa tamkar waina a tanda yadda sukaga dama, Allah ya azurtasa da ƴaƴa mata har guda biyar da maza uku, matarsa ta farko ƴaƴanta biyar ta biyun kuma guda uku, kullum a gidan gini sai anyi hatsaniya tsakanin matan gidan domin tamkar suna ganin hajin junansu, kwata-kwata basa jituwa kullum cikin tashin hankali suke, ƴaƴansu mata ko wacce ta shigewa uwarta, wataran idan faɗa ya kacame har saita kai ga maƙota suna shigowa rabasu saboda wataran har dambe suke idan cacar baki tayi zafii, tin maƙota na shigowa rabasu har ta kai ga an watsar dasu ana barinsu suyi faɗansu iya iyawarsu su rabu dan kansu, kai wataran idan abu yayi tsamari har sai an raunata wasu, idan akai wannan gagarumin dambe haka gidan yake yin kaca kaca, filin tsakar gidan da ko daɓe babu sai burjin ƙasa ya koma tamkar gidan mahaukata da shirgin da akai jefe-jefe da doke-doke wajen dambe, haka Magidancin nan zai shiga tsakaninsu yana ƙoƙarin rabasu amma faɗa yaƙi ƙarewa daga matan har ƴaƴan nasa basa saduda sai ya yanke jiki ya faɗi wanda a sanadin haka ya haɗu da hawan jini, Malam Adamu mai gini shine magidancin wannan ɗan bala'in gida. da matansa biyu ta farko Rabi'atu wacca ake kira Maama saita biyu Fatima wacca ake kira Umma. ★Wani irin gyatsine take tana hura ɗan siririn hancinta ta fito tsakar gidan da yake duk cakwalkwali saboda ruwan da aka sheƙa daren jiya, hannuta riƙe da brush dinta da ta matso tooth paste akai, can wajen da suke tara ruwa cikin manyan tukanen ƙarfe irin wanda ake abincin gidan biki ta dosa, ta ajiye brush din hannunta akan wata murguɗaɗɗiyar kujera, ta ɗauki buta ta buɗe tukunya ɗaya ta kantami ruwa ta wuce hanyar banɗaki dake cikin wani lungu da wata siririyar kwata wacca ta ɓulla har cikin banɗakin tayi waje, ƙofar banɗakin ta langa-langa ta bubbuga, daga banɗakin aka yi mata gyaran murya, a hasale tace "koma waye aciki yayi sauri ya fito a matse nake!!!", wajen minti biyar tana jira amma ba a buɗe ƙofar banɗakin ba, ta sake bugawa da ƙarfi tace "wai wace shegiyar ce aciki ne??, dalla malama ki fito", daga cikin banɗakin aka ja wani dogon tsaki, a hasale ta banka ƙofar daman bata da sakata bare mukulli, turo ƙofar kawai ake sai a tokareta da wani mulmulen dutse da yake cikin banɗakin, Maimuna da take cikin banɗakin riƙe da buta a hannu ta kalli Hajar sama da ƙasa ta daka tsaki ta fito daga ciki, daman ta gama amfani da bayin amma da ta ji Hajar tana jiranta shine taƙi fitowa, Hajar ta karkaɗa kai ta dubeta tace "zaki sani ne??" ta shiga bayin tayi uzirinta ta fito, ta tsugunna gaban rariya tayi brush ta wanke fuskarta, ta miƙe ta shiga ɗakin umma wacca itace mahaifiyarta, umma da take zaune kan darduna tana irga cinikin kulelen da tayi jiya da yamma tace "makaranta zaki tafi Hajara?, toh wane zai auno min wake ya siyo min manja?", Hajar ta buɗe wardrobe ɗin da ta gama fatattakewa gata wata old modern gaba ɗaya ƙofofinta sun cire saidai a jingine su, ta zaro ironed uniform ɗinta tace "toh bari na shirya saina je na auno miki waken", umma tace "dama haƙura kikai da zuwa makarantar nan gashi kin makara kuma anyi ruwan sama nasan ajinku ma ya cika da ruwa", Hajar tace "A'a nidaii umma zani kinsan shirye-shiryen jarabawa muke, yau za ai mana thumb print wanda za muyi amfani dashi wajen rubuta NECO", Umma ta lalo kuɗi ta miƙa mata tace "wake kwano ɗaya sai manja rabin kwalba", Hajar ta karɓi kuɗin ta ajiye kan shirgin ƙullin kaya tace "ita Sabra ba zata makarantar ba??", Umma tace "Eh babu inda zata gaskiya, makarantarsu tafi taku lalacewa ko taje ma nasan dawowa zatai aii duk ranar da akai ruwa ba ayi", Hajar tace "tom", umma ta ƙulle ragowar kuɗinta a haɓar zani ta fita, Hajar ta janyo uniform ɗinta ta saka wanda sukay mata kyau duk da cewa ba wasu kayan ado bane, ta ɗauki kuɗin ta ɗakko slipers dinta a bayan ƙofa ta saka ta fita tsakar gida, umma ta gani tana wanke gwangwanayen kulele can bakin rariya, suka haɗa ido da Maimuna da take faman haska madubi a fuskarta tana mulka wani sabulu, Hajar tace "Banza mai bleeching", umma ta juya ta daka mata harara ta nuna mata ƙofa tace "akul zoki fita aiken da nayi miki", Maimuna ta ɗaga murya tace "uwar kice mai bleeching shiyasa ta haifeki fara", Maimuna ta cigaba da shafe fuskarta da take tamkar ta larabawa amma ƙafar nan da hannu baƙi ƙirin sai kace tayi dilke da gawayi, Sa'adatu ce ta fito daga ɗakin Maama itama dai fuskar nan taci bleeching daidai gwargwado tace "wai me naji mara kunyar yarinyar nan take faɗa miki ne??", Maimuna tace "aina gwaɓa mata maganar da ta dace da ita shegiya nunar rana", Nabila ma ta fito daga ɗaki tace "aii ni haushi kike bani Maimuna, ki zauna kina takun saƙa da waccan ƴar tatsitsiyar yarinyar har tana gwaɓa miki magana", Sa'adatu ta dungurewa Maimuna kai tace "shashasha kawai" ta koma ɗaki, umma duk tana jinsu bata ce musu komai ba kawai wankin gwangwanayenta take, Nabila ta ɗauki buta ta shiga bayi, Maimuna ta cigaba da ɗashe fuska da sabulu. Hajar tana fita daga gida ta kama hanyar shagon iliya mai awo, duk arean shine mai awon da yake fitowa da wuri, wani ɗan madaidaicin shago ne da ake siyar da kayan awo na masarufi da dai sauran ƴan tarkace, wasu maza ne a bakin shagon ɗaya yana kan benci ya kara rediyo a kunnensa ɗayan kuma yana ɗura manja a kwalba a kan wani tebur da yayi daƙal-ɗaƙal da mai da ƙura, Hajar ta tsaya a bakin shagon tace "salamu alaikum", mai ɗura manjan wanda shine mai shagon wato iliya yace "wa'alaikumus salam", Hajar tace "mal iliya a bani wake kwano ɗaya manja rabin kwalba", iliya ya shiga shago ya auno wake ya fito waje ya zuba manja a farar leda ya haɗesu a babbar leɗa ya miƙa mata, ta ciro kuɗinsa ta basa tace "Allah yasa dai manjan mai kyaune, ba irin na jiya mai warin mushe ba", iliya yace "idan an samu wata matsalar a dawomin da kayana saina baku kuɗinku", ƙasa ƙasa Hajar tace "uhmm sai kace gaske.." ta kama hanya zata bar bakin shagon mutumin da yake kan benci ya cire rediyon kunnensa yace "ke hajara akwai kulele??", ta juya tace "ka cire ke ɗin mana ka bar hajara, babu kulele sai anjima", ya kaɗa kai irin ai halinki ne yace "toh idan an gama ki kawomin ta ɗari biyu nan sai na baki kuɗin", ta yamutsa fuska tace "saidai ka tura yaro ya siyo maka" tayi gaba abunta, iliya ya koma kan benci ya zauna yace "ita da sauƙi fa", munkaila yace "inafa sauƙi, kasan maƙotanmu ne mun haɗa katanga dasu ta fuskar baya, wallahi shekaran jiya suna hatsaniyar nan tasu da suka saba iyalina ta shiga yi musu sulhu, wannan ja'irar yarinyar ce ta kwaɗa mata bokitin ƙarfe a hannu tazo kwaɗawa ƴar uwarta. harfa saida ta fitar mata da jini", iliya yace "aii mal Adamu bashi da iko da gidansa ace bazaka iya tsawatarwa matanka ba, abinda sukaga dama za suyi, ni ban taɓa ganin lusarin namiji kamarsa ba, sai kace wanda suka shanyesa", munkaila yace "ai a shanye yake, kai kana ganin wannan mutumin kasan shanyayye ne ainun, yanzu fa ƴaƴan nan nasa shafe-shafen nan na zamani suke, ni jiya da naga wata ma acikinsu ban ganeta ba saida naga tukubar hancin", iliya ya kyalkyale da dariya yace "ai jiya wata tazo nan siyan shinkafa wallahi data miƙomin kuɗi na ɗauka wani ne ya zuro hannu ta bayanta ya miƙomin kudin ba ita ba", munkaila yace "Allah dai ya kyauta ya shirya mana zuri'a". iliya ya tashi zai bawa wani yaro da yazo aunar masara, munkaila ya kara rediyonsa a kunne ya lumshe ido yana karkaɗa kai. Hajar na komawa gida ta tarar da umma tana tashin wuta a kurfotu, ta wuce ɗaki ta ajiye aiken ta fito ta kalli umma tace "ni zan tafi bazan daɗe ba inayin thumb print zan dawo", umma tace "bazaki jira na dama kunu ba??, haka zaki tafi makarantar ciki kwalam", Hajar ta kalli gawayin da umma take ƙoƙarin cinna masa wuta taga akwai lema ajikinsa tace "idan na dawo nasha, bari na gaida Baba". ta shiga ɗakin Baba da ƴar sallama, yana zaune gefen katifa yana jan wata doguwar cazbaha, ta tsugunna tace "barka da safiya Baba, an tashi lafiya??", Baba ya dubeta da wani irin yanayi, duk cikin ƴaƴansa mata yafi jinta a zuciyarsa, yace "lafiya lau Hajara, makaranta za a tafi?", tace "eh Baba, zanje ayi mana thumb print na jarabawar NECO da zamu zana", yace "Toh Allah ya bada sa'a" ya ciro ɗari biyu a aljihun wandonsa ya miƙa mata, ta sa hannu biyu ta ƙarba tace "nagode Allah ya saka da alkhairy". ta miƙe ta fita, a bakin ƙofa suka kusan yin karo da Mu'azzam wanda shine babban yayanta da suka haɗa uwa da uba ɗaya, Mu'azzam ya ɓalla mata harara ya haɗe rai yace "bani hanya..", da sauri ta matsa masa hanya ya shiga ita kuma ta kama hanyar soro. ★A hankali yake murza steering ɗin ɗumemiyar motar da yake driving, wayarsa da take gefensa ta hau tsuwwa, looking at the road ya kai hannu yayi picking ya kara a kunne yace "Salam Mami, har yanzu dai ban gane street ɗin ba, i thought Dala kika ce koh??", ya ɗanyi shiru sai kuma yace "ohk nagane, inajin nabi wrong way ne", wayar ya katse ya fara juya motar a ɗan tsukun layin da kwaltarsa ta gama ragargajewa, da yake expert ne wajen lailaya mota ya juyata cikin sauƙi ya koma ɗayan side ɗin kwarɓaɓɓen titin, yana fara tafiya wani mai mashin ya yanko gabansa tamkar an wurgosa, da sauri ya ɗauke kan motar yayi gefe da ita, motar ta faɗa cikin wani ruwan kwatami na ruwan sama da kwatocin gidajen mutane da suka ɓulla cikinsa, ruwan kwatar da jar ƙasa ya feshe Hajar da take tsaye a bakin wajen tana jiran napep, gaba ɗaya uniform ɗinta suka ɓaci da jar ƙasa, ga wani wari da ruwan yake na kwata, Hajar tabi jikinta da kallo ta hangame baki, a matuƙar zafafe ta dubi motar da tayi mata wannan aika aikar lokacin da mutumin ciki ya buɗe ƙofar driver......✍️ 💛 HAJAR💛 by Feenerh_feeche {2...} Fitowa yayi daga motar yana hangen mai mashin ɗin da ya shigo masa har ya bulale tsukun layin da hayaƙi ya fece, cikakken gashin kansa ya shafa yana ƙanƙance ido sai kuma ya kalli motar tasa da take cikin kwatami tsamo-tsamo, gefenta ya karkace wajen driver ne kawai bai shiga kwatamin ba, tsirarun mutanen da akai abun a kan idansu suka taso, Hajar da zuciyarta take tafasa tana kallon uniform ɗinta da bazasu taɓa tafiyuwa a wajenta a haka ba, wani ƙululu ne ya tsaya mata, what the heck isn't he going to apologise, a hankali ta taka tana tsantsamin kanta ta isa gabansa inda yake ƙoƙarin buɗe motar zai shiga, ya kai hannu kenan zai buɗe ƙofar motar ta riƙe handle ɗin tace "malam ba kaga abinda kayi bane??", da wani irin salo ta juya fararen idonta ta nuna masa uniform ɗin jikinta dasu, kallo ɗaya tak yayi mata yace "ohk sorry it was not my fault", up and down ta kallesa ta tsugunna ta kwarfo ruwan dattin a duka hannayenta ta shaɓune masa a farar Tshirt ɗin jikinsa, ta kama hanya fagam-fagam zata bar wajen, wani mutum ne ya kalleta yace "amma wallahi ke dai baki da kirki..", ta juya ta kallesa sai taga da ɗan girmansa zai iya kaiwa sa'an babanta hakan yasa ta mayar da asalin abin tayi niyyar fada tace "oh shi bakuga rashin kirkinsa da ya feshe ni da kwatami ba", mutumin yace "amma ai ba sa'an ki bane kuma ya baki hakuri yarinya", cike da tsiwa Hajar tace "banga zan iya hakura ba gaskiya" tayi gaba abunta, wani ne ya taso yace "au baka ganeta ba aii ƴar gidan gini ce zata iya aikata abinda yafi haka ma". kawai gaban Tshirt ɗin jikinsa yabi da kallo lokacin da kunnensa yaji (au baka ganeta ba, ai ƴar gidan gini ce zata aikata abinda yafi haka ma). Hajar na shiga gida tin daga soro ta rushe da kuka, ita duk wannan tsiwar ta ta kuka baya mata wuya, daga zarar zuciyarta ta ɓaci tom sai tayi kuka take jin daɗi, da Sa'adatu ta fara cin karo hannunta riƙe da bokitin ruwa da kwandon soso da sabulu zata shiga bayi, Sa'adatu ta daka wani uban tsaki tace "da murya sai kace ta gardawa an cikawa mutane gidan uba", Hajar ta sharce hawayen idonta tace "saiki nuna wanda ya diro daga sama jahila" ta ƙarasa shiga ciki, Sa'adatu ta mulmulo wata ashariya tace "ni yarinyar nan zata kira jahila" ta dire bokitin da kwandon ta biyota da gudu, kafin ma ta cimmata harta shige ɗakin umma, Mu'azzam da yake bakin ƙofa ya kalleta sama da ƙasa yace "ina makarantar??", Hajar tace "ba ina tsaye a bakin titi ina jiran napep ba wani mai mota ya fesa min cakwalkwali", ta cigaba da kukanta, Mu'azzam yace "A'a kinga malama ki rufewa mutane baki, ki canza wasu kayan ki tafi makaranta", Hajar na shessheƙar Kuka tace "toh aii banida wasu uniform ɗin kuma ance kowa da kayan makaranta za ai masa online registration", umma tace "Mu'azzam dan Allah daure ka rakata makarantar nan tinda kace yau bazaka aiki ba, ke kuma maza kije ki ɗauraye jikinki kizo ki canza kaya", Mu'azzam yace "karki ɓatamin lokaci ina ƙofar gida", ya fita daga ɗakin, Hajar ta wuce bakin rariya ta cire hijab ɗin jikinta ta ɗebi ruwa a buta ta fara ɗauraye inda cakwalkwali ya ɓata ta, cikin sanɗa Sa'adatu ta taho ta cakumo wuyanta tace "yanzu sai ki gayamin wace ce jahilar??", Hajar tace "dalla malama sake ni..", Sa'adatu tace "anƙi a sake kin, me zaki iya??", Maama ta yaye labule ta leƙo tace "naɗi ƴar iska, ki canza mata kamanni", Sa'adatu ta sake maƙure wuyan Hajar har saida idonta suka firfito amma baki nan bai mutu ba cewa take "Allah ya isa, muguwa azzaluma mai bleeching", mai bleeching ɗin nan shi yafi ƙonawa Sa'adatu rai don haka ta kamata da kokawa, Hajar da take ganin bazata ɓata lokacinta a nan wajen ba ta daddage ta danna mata wani mugun cizo a damtse, Sa'adatu da zafin cizo ya ratsa mata kwakwalwa da sauri ta saketa ta lailayo ashar tana kallon damtsenta da haƙoran Hajar suka fito ainun, cizon ya shigeta sosai domin ƙiris ya rage wajen bai fashe ba domin kuwa jeka huda yayi, Hajar ta manna aguje ta shige ɗakin umma tana waiwayen Sa'adatu. ★Sanye take cikin fararen kaya riga da wando sai wani ɗan ƙaramin hijab V-shape, ta ɗora kimono a saman kayan, hannunta riƙe da mug mai ɗauke da coffee, a hankali take tafiya har tazo ƙofar office ɗin tayi knocking a hankali, daga ciki akace "come in..", ta murɗa handle ta shiga ciki da ƴar sallama, secretary ta amsa tace "welcome Nurse Ruqayyah..", tace "yawwa Halima Doctor bai ƙaraso ba ne??", Halima tace "yes i think he is on his way", Ruqayyah tace "Ohk, bari na jirasa aciki", Halima tace "ohk then", Ruqayyah ta shiga babban office ɗin da ya gama ƙawatuwa, ga wani ƙamshi da sanyin Ac da yake tashi a cikinsa, Mug ɗin hannunta ta ajiye kan table ta ɗauki hoton da yake dirke a gefen table ɗin wanda ya haska fuskar wani mutum wanda yake sanye da lab coat ya rataya stethoscope a wuyansa, hannayensa zube a pocket ga kuma wani murmushi da yake shimfiɗe a fuskarsa, Ruqayyah ta zauna kan chair still looking at the picture, 20mins passed amma bata gaji da kallon picturen ba, ƙofa aka murɗa mutumin da yake cikin picturen ne ya shigo, hannunsa riƙe da briefcase, a hankali ya mayar da ƙofar ya ƙaraso ciki yana kallon Ruqayyah da take riƙe da hotonsa, briefcase ɗin ya ajiye akan table sannan ya cire lab coat din jikinsa ya ratayeta ajikin kujerar zamansa kana ya zauna, ajiyar zuciya ya sauke yana kallonta yace "good morning babe.. tinda yau ba za a gaishen ba", ta kallesa a fakaice ta zumɓuro baki tace "Dr yau mesa ka makara?, kuma nasan kanada surgery scheduled yau at 12pm", with a soft smile on his face yace "really akan surgery nan kika damu ko kuma mai yin surgeryn?", wani irin cuno baki tayi tace "of course not i care for the surgery not the surgeon", murmushin da ya bayyana fararen haƙoransa yayi yace "My coffee ko yau rowa za ai min?", ta mayar da hoton mazauninsa ta ɗauki Mug ɗin da ta ajiye ta miƙa masa tace "Here", ya amsa yace "thanks", one sip yayi ya ajiye yace "ya huce aii", tace "tinda ka makara yau mai sanyi zaka sha, now tell me, mene ya makarar da kai?", yace "ohh Mami ce ta turani na amso mata wani saƙo shine nabi wrong way, har car na ya samu matsala, you know yesterday anyi ruwa toh wani ruwa na faɗa a street ɗin, i wasted my time there looking for a solution", tace "ohk, Allah ya kiyaye", yace "Ameen, har yanzun ma coffee mai sanyi zan sha?", juya idanunta tayi ta miƙe ta duba wrist watch ɗinta tace "Byee, zan shiga surgery da Doctor Mansoor, see you later after the surgery.." ta fita ta rufe ƙofa. wasa ya farayi da yatsun hannunsa yana juyi a kan kujera idonsa a lumshe yana tunanin the girl he encounter with this morning, her face look so innocent but she's stubborn, ƴar gidan gini.........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {3...} Ƙarfe sha biyu na rana Dr Uthman ya shiga surgery with his well trained team, shi ƙwararren likita ne da ya karanci ɓangaren thorax da duk wani abu that is located in the chest region, alhmdllh surgeryn da Dr Uthman yayi was successful, yana dressing room yana cire kayan da yayi surgery dasu Dr Marwan ya shigo wanda shine yayi masa first assistance, Dr Marwan ya buɗe lockern kayansa yace "gaskiya Dr surgery nan yayi kyau, gashi patient ɗin ya daɗe da ciwon amma kuma komai yayi kyau", Dr Uthman yace "everything goes well saboda aikinku mai kyau my team members, idan babu ku ai komai bazai yi daɗi ba", Dr Marwan yayi murmushi yace "still dai kaine 70 percent na success ragowar percent ɗin aka raba mana", Dr Uthman yace "Marwan next week inada surgery amma bazan samu damar zuwa ba, kaine za kayi heading sai Khaleel yayi first assistance", Dr Marwan yace "sure Allah ya kaimu", Dr Uthman ya mayar da lab coat ɗinsa ya wuce office, Halima tace "welcome Dr akwai patient da yake jiranka, zan iya shigo dashi??", tsadadden wrist watch ɗinsa ya kalle yace "am off amma ki shigo dashi tinda ya riga yazo", tace "yes sir" ta ɗauki landline ta kira reception tace "hello patient ɗin da yake jiran Dr Uthman ya shigo yanzu" ta katse kiran. babu jimawa patient ɗin ya shigo office ɗin, Dr Uthman ya kallesa yace "referral ne??", patient din yace "Eh" ya miƙa masa wata takarda cikin envelope, glasses dinsa ya ɗauka ya kwamawa idanunsa kana ya karanta takardar tas yace "mal shu'aibu jeka ka kwanta a wancan gadon" yayi masa nuni da gadon da yake a can edge of the office, mal shu'aibu ya kwanta a gadon, Dr Uthman ya ɗauki stethoscope ya isa bakin gadon ya fara dubasa, bugun zuciyarsa ya fara ji sannan yace "mal shu'aibu kaja dogon numfashi", mal shu'aibu yayi yadda aka umarce sa, bayan Dr ya gama duk wani gwaje-gwaje ya koma mazauninsa yayi rubutu ya basa yace "tests ne guda biyu, ayi su kafin nan da sati mai zuwa sai a kawomin", mal shu'aibu yace "nagode likita" ya karɓi takardar ya fita. Dr Uthman ya ɗauki wayarsa yayi dialing numbern Nurse Ruqayyah wacca yayi saving da Love, ya jingina da kujera ya kara wayar a kunne. Nurse Ruqayyah tana zaune a nurse station taji wayarta na vibrating cikin aljihun rigarta, da sauri ta zarota ganin mai kiran tayi murmushi ta kara a kunne tace "my Dr badai harka fito ba??", daga ɗayan side din Dr Uthman yace "yeh na fito, yanzu ma zan wuce, yaushe zaki wuce gida?", tace "ohk, zan yiwa wata da za'a yiwa CS Anesthesia ne kafin na wuce gida", yace "ohk, byee Love", tayi murmushi tace "byee" ta katse kiran, Nurse Jidda da take kallonta tace "gaskiya Ruqayyah kin afka, yanzu fa shekara biyu kenan kuna tare da Dr Uthman, wai yaushe za muga cigaban wannan soyayyar ne??", Ruqayyah tayi ajiyar zuciya ta taɓe baki tace "kwana nan zamu girbi soyayyarmu inshallah, kinsan dai cewa iyayena sun san dashi tinda ya tura magabatansa sunje nema masa izinin zance, toh tin lokacin suka so su bada kuɗin aure, amma Daddy yaƙi amincewa yace sai mun fahimci juna tukun, toh dai tin daga lokacin ba a sake maganar kai kuɗi ba, daman bai gama shiryawa ba yana so ya ƙarasa gidansa kuma ya zama rigid a business ɗinsa, to alhmdllh komai dai ya zama settle gida ma har an saka masa padlock ya gama komai, and his business shima alhmdllh, last week yake gayamin cewa zai turo magabatansa a kawo kuɗi sannan asaka rana, though shi baya so asaka sama da three months, amma nasan Daddy bazai amince ba saboda he is not ready, toh kinji yadda muke ciki", Jidda ta jinjina kai tace "ohk mashallah, Allah ya tabbatar da Alkhairy", Ruqayyah tayi murmushi tace "Ameen". ★Umma na zaune akan kujera tana zuba ƙullun kulele cikin fafaffun gwangwanayen da aka shafesu da Manja, Sa'adatu ce ta fito daga ɗakin Maama taci kwalliya, wata riga da skirt ta saka na material mai rawa, kayan sun ɗameta sosai da kyar take tafiya ga takalmi mai uban tsini a ƙafarta, mayafin da ta saka dashi gara babu, fuskar nan ɗaɗau tasha hoda da mai, Baba ya fito daga ɗakinsa ya kalleta sama da ƙasa yace "ina za kije Sa'adatu?", Sa'adatu ta zumɓuri baki tace "Baba daman bikin wata ƙawarmu ake, yau ne ɗaurin aure", yace "toh wa kika tambaya da zaki fita a haka?", Sa'adatu ta yamutsa fuska tace "na gayawa Maama ai", Baba ya sake kallon shigar jikinta yace "koma ɗaki babu inda zaki", ta tsaya tana ƙunkuni da murguɗe-murguɗe, ya zabga mata carbin hannunsa a baya, ya sake ɗaga hannu zai zabga mata ta ruga da gudu tana gurɗewa ta afka ɗakin Maama, Nabilah da take laɓe a jikin labule ta tuntsure da dariya tace "Baba ya matsa lamba", Maama ta miƙe ta fita waje daman kaf tana jin abinda ya faru, Baba ya juya zai koma ɗaki Maama tace "haba mal ya za ai ka daddage ka daki yarinya budurwa haka, inaji dai ta gaya maka na bata izinin fita shine kake mata wannan dukan", ya juya ya kalleta yace "indai ni na haifi Sa'adatu to ban amince ta fita a haka ba", Maama ta ɗaga murya tace "Toh ai ba kai kaɗai ka haifeta ba malam, nice nan uwar Sa'adatu kuma ta samu amincewa ta", da karfi Maama tace "ke Sa'adatu maza fito ki kama gabanki, Allah ya tsare", Sa'adatu daga ƙuryar ɗaki tace "Tom Maama gani nan fitowa", Baba yace "Rabi ki cigaba da ɓata tarbiyyar ƴaƴanki, yaran nan ko makaranta sunƙi zuwa, ba arabi ba boko, wallahi muddun baki canza ba wataran zakiyi kuka da idanunki", Maama ta zabga uban salati tana tafa hannaye tace "Malam da sanyin safiyar nan kake ƙoƙarin yimin baki, kana kiramin kalmar kuka da idanuna, na shiga uku ni Rabi yau na gamu da jafa'i", Baba ya girgiza kai yace "ƴaƴanki bazasu taɓa koyi da ƴar uwarsu Hajara ba, yarinya mai son karatu", da gudu Nabilah ta antayo daga ɗaki tace "Baba Allah ya tsaremu muyi koyi da wannan tabbatacciyar shegiyar yarinyar", sai a lokacin Umma ta tanka tace "ke karki sake kiran ƴata tabbatacciyar shegiya na gaya miki", Maama ta rangaɗa wata shegiyar guɗa tace "ahayye, da Mu'azzam da Hajara duk shegu ne, da tsohon cikin Hajara da Mu'azzam yayayye kika zo gidan nan", Umma tace "ga ubansu nan, kuma shi yasan ƴaƴansa ne", Maama ta tafa hannaye tace "laha'ila ha illallahu, kuji fa wai Adamu ne uban Hajara da Mu'azzam, yau naga inda ake liƙawa mutum ɗan shege ta ƙarfin tsiya, wallahi ƙarya kike faɗima Sabra ce kaɗai ƴar Malam amma wallahi Hajara da Mu'azzam saidai ki nemo musu uba", Baba ya nuna Umma yace "faɗima karki sake cewa komai, koma ɗakinki", Umma ta rufe ƙullun kulelenta ta shiga ɗakinta, Sa'adatu kam tunda taji tsakar gida ya fara ɗaukar harami ta rungume cogen takalminta ta fita sum-sum tamkar munafuka tayi soro, Baba ya kalli Maama yace "Allah ya shiryeki Rabi idan kinada rabo" ya koma ɗakinsa, ai Maama saida ta gama kumfar bala'i ita kaɗai sannan ta koma ɗaki, Nabilah tace "Maama kinga har yanzu Maimuna bata dawo ba sai kace wacca aka aika wata duniyar", Maama ta zabga tsaki tace "inajin ta tafi sabgar gabanta". ★Washe gari da misalin ƙarfe biyu da Rabi na rana, Hajar ce ta fito tsakar gida sanye da uniform ɗinta na islamiyya, daga bakin rariya ta hango Naseer yana goge kaushi tace "yaya ina wuni", yace "lafiya Hajar makaranta za'a tafi", tace "Eh, Sabra nake jira", yace "toh Allah ya bada sa'a", sai kuma ya miƙe ya tsaya a bakin ƙofar ɗakin Maama ya kwalawa Maimuna kira, saida ya sake kiranta sau biyu sannan ta fito tace "yaya gani", yace "ke bazaki fito ki tafi makarantar ba", tace "yaya wace makaranta kuma??", ya daka mata tsawa har saida ta firgita yace "islamiyya mana", ta fara inda-inda tana mutsuttsuka hannaye tace "daman yau bazan je ba, Maama bata nan, Nabilah da Sa'adatu suma duk sun fita, wa zan barwa ɗakin Maaman??", yace "shiga ki sako kayan makaranta ki wuce ki tafi", tace "toh yaya wai wa zan barwa ɗakin..", kwalla mata mari yayi har saida ta bugu da bango yace "duk abinda kuke agidan nan kawai kallonku nake, yaushe rabon da kije makaranta, zaki wuce ko saina tattaka ki", a guje Maimuna ta afka ɗakin Maama tana gursheƙen kuka, ta buɗe Ghana most go ta ɗakko zumbulelen hijab ɗin islamiyya wanda rabonta dashi wajen wata huɗu, yaci uban squeezing yana warin ajiya, ta lalubi inda Maama take ajiye padlock ta ɗauka ta fito, Naseer yana tsaye a bakin ƙofar bai tafi ba ya kalleta ganin squeezing ɗin da hijab ɗinta yayi yace "ƙazama", Maimuna ta kulle ɗakin ta rufe fuskarta da hijab ta cigaba da kuka, Naseer yasa ƙafa ya kwarfeta ta baje a ƙasa yace "miƙe munafuka, ai Maama ce ta kyaleku kuke yin abinda kukaga dama, wallahi daga yau kika sake fashin makaranta saina tattaka ki mara kunya", da gudu tayi waje tana kuka, Hajar ta rufe fuskarta da hijab tana tiƙar dariya a zuciyarta tace (Allah shi ƙara), Sabra ta fito suka kama hanyar islamiyya. Hajar tana zuwa ajinsu Abubakar Siddiq wanda shine ajin sauka ta tarar har an fara bitar Al'qurani tinda sunyi sauka, saida aka gama bitar sannan Zainab ta taɓo Hajar tace "me yasa jiya bakizo ba?", Hajar tace "kinsan shirye-shiryen NECO muke, to jiya akai mana online registration", Zainab tace "nima ai naje registration ɗin kuma nazo islamiyya", Hajar tace "nida na kusa samun matsala, ai ina gaya miki saura ƙiris ayi NECOn bana ba ni", Zainab tace "A saboda me??", Hajar ta kwashe kaf abinda ya faru ta gaya mata, Zainab ta zabga mata harara tace "dalla malama gafara can, wai da kika ƙi haƙura kika shafa masa kwatamin mene ribarka?", Hajar tace "zuciyata tayi sanyi aii", Zainab tace "ki ringa haƙuri ƙawata dan Allah", Hajar tace "uhmm nidai akai min saina rama wallahi", Zainab tayi murmushi tace "mutuminki fa ya shigo ajin nan yafi sau ashirin jiya", Hajar ta yamutsa fuska tace "wa kenan??", Zainab tace "wa kika sani bayan ya sayyadi Nura..", Hajar ta juyar da fuskarta tana murmushi..........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {4...} Biyar da rabi na yamma ya sayyadi Nura ya shigo ajin yi musu kiran suna, idonsa akan Hajar ya fara sauka wacca ta sunkuyar da kanta tana duba abinda babu a jaka, Addu'a ya fara yi musu kana ya fara kiran suna, duk wanda aka kira sunansa sai ya tashi ya tafi gida idan kuma kasan kayi fashi sai ka jira ai maka hukuncii, ajin ya ɗaɗe ya rage daga Hajar sai ya sayyadi Nura, register ya rufe ya maida hankalinsa gareta, a hankali yace "Hajara mai yasa jiya kika yi fashi", Hajar ta haɗiyi wani yawu ba tare da ta kallesa ba tana wasa da hannunta cikin hijab tace "ya sayyadi online registration naje na NECO kuma ban dawo da wuri ba", ya sauke ajiyar zuciya yace "toh saiki dage da karatu kinji??", tace "Insha Allah", yace "har yanzu dai Nursing ɗin kike son karanta", a karo na farko da ta ɗago fararen idanunta sai kuma tayi sauri ta mayar dasu ƙasa tace "Eh", yace "toh shknn, indai kin ɓaro marks Insha Allah zaki tafi Nursing School", tace "insha Allah zanyi ƙoƙari", ya ringa kallonta sai kuma ya sauke sassanyar ajiyar zuciya yace "lokaci nake jira na nemi izini wajen Baba na ringa zuwa wajenki a gida, iya ganin da nake miki a makaranta yayimin kaɗan gaskiya, ace kullum idona baya ci ya ƙoshi", ta janyo hijab ɗinta ta rufe fuska murya can ƙasan maƙoshi tace "ni gida zan tafi", yayi murmushi mai sauti yace "toh taso ki tafi", a hankali ta tashi ta ɗauki jakarta ta fita a ajin ba tare da ta bari ta kalli wajen da yake ba. a gate ta tarar da zainab da take jiranta suka rankaya suka tafi gida. da daddare Hajar na zaune akan tabarma tana cin tuwo, umma ta fito daga ɗaki da mafici a hannunta itama ta samu guri ta zauna tace "kai gaskiya yau akwai zafi inajin hadari ne a garin", Hajar tace "ɗazu ma naga ana walƙiya, ina sabra ita bazata fito tasha iska ba sai sanƙarau ya kamata?", umma tace "tayi bacci kinsan daga anyi sallar isha'i take kwanciya". Maama tana daga can ƙofar ɗakinta tare da Maimuna wacca ta kawo mata ƙorafi akan Naseer. garin zafi ake shiyasa suka firfito tsakar gida shan iska, Hajar ta miƙe ta kai kwanon da ta gama cin abinci wajen wanke-wanke ta ɗebi ruwa tana wanke hannunta, Sallamar Baba ta janyo hankalin kowa garesa, Hajar tace "sannu da zuwa Baba", ya amsa yana miƙa mata ɗaya daga cikin ledar da ya shigo dasu, Maimuna tana ganin ya miƙawa Hajar leda ta miƙe zaune daga kan cinyar Maama tace "Baba sannu da zuwa", yace "yawwa zoki karɓar muku naku", Maimuna ta taso da sauri ya bata leda ɗaya ya wuce ɗakinsa da guda tinda ledojin uku ne. Hajar ta kaiwa umma ledar ta samu guri ta zauna ta tanƙwashe ƙafa, Umma ta buɗe leda, karfashe ne mai zafi ga kuma yaji a gefe, umma tace "kai Allah ya saka da alkhairy ya ƙara buɗi, sako hannu muce Hajara", a hankali Hajar take ƙurmushe karfashen saboda tana sonshi. Maimuna kam tana buɗe ledar ta kalli Maama tace "Chaɓ, daman tinda naji ƙarni nasan wannan abun ne", Maama ta warce ledar tace "idan bazaki ci ba ki barshi" ta ɗauki guda ɗaya ta luƙa a baki ta ƙurmushe, Nabilah ta fito daga ɗaki da fitilar wayarta rakani toilet ta haska kifin hannun Maama tace "me kuke ci ne naji ƙayau ƙayau ana tauna?", Maama tace "karfashe ne idan zaki ci, yanzu babanku ya shigo dashi", Nabilah ta taɓe baki tace "ni kam bazan ci ya farfasan baki ba, kina ganin abu sai kace ƙanzo, Sa'adatu nake jira nasan bazata shigo gidan nan hannu rabbana ba", Maimuna tace "wallahi nima ita nake jira", Maimuna tana rufe baki saiga sallamar Sa'adatu, hannunta riƙi-riƙi da ledoji, da sauri Maimuna ta tarota ta amso ledojin, Sa'adatu ta zauna kan tabarma ta fige ɗankwalin kanta tace "wash nagaji, Maama yau kam ai banyi dare ba ko??", Maama ta kawar da ledar karfashen da take ci ta suɗe hannu tace "Eh yau ba kiyi dare ba ƴar albarka", Sa'adatu ta warce ledojin hannun Maimuna tace "cewa nayi ki buɗe, ai kya bari na buɗe da kaina", Sa'adatu ta ciro takardar tsire da ƙatuwar robar ice cream tace "Maama ga naki", ta ciro wata takardar da kuma robar ice cream ta miƙawa Nabilah tace "keda Maimu". ta kwashi ragowar ledojin ta shiga ɗaki. hannu baka hannu kwarya sai kace mayatattu suke cin tsiren nan suna yaɓa ice cream a baki, Maama sai habaici take zubawa faɗi take "haihuwa tayi min rana, ina zaune akawomin tsire da ƙanƙara mai madara na more, wasu kam sunyi asara kullum saidai a kawo musu takarda ace anyi ƙoƙari a jarabawa", Nabilah ta danna tsire a baki tace "yo daman shege yanada wani amfani ne, ai amfanin shege bai wuce baƙin fenti ba". Hajar ta miƙe ta zazzagi omo ta wanke hannunta ta shiga ɗaki, muddin ta zauna a tsakar gidan nan to kwa tabbas za a iya tashin hankali domin kwa ba haƙuri ne da ita ba musamman ma aka taɓo mata uwa. Washe gari da wuri Hajar ta dawo daga school saboda ranar juma'a ce, umma ta tarar tayi shirin fita, Hajar ta ajiye jakarta tace "Umma fita zakiyi ne??", Umma tace "ta dole ce Hajara, gidan Jamila zanje na duba jikin Hafsa, kar abin ya zama shiririta na shiga wata sabgar ban dubata ba", Hajar tace "to bari nayi sauri na shirya saimu tafi tare", Umma ta girgiza kai tace "da ke nayi niyyar zuwa amma hakan bazai yiwu ba, inada ragowar kulele da ban siyar ba wajen ta dubu, daman ranar juma'a sai bayan masallaci akafi ciniki, ga Sabra nan ta tayaki zama bazan daɗe ba Insha Allah", Umma ta ɗauki ƴar purse ɗinta tace "Hajara karki biyewa kowa ayi tashin hankali dake kinji", Hajar ta jinjina kai tace "Allah ya tsare sai kin dawo..". Hajar tayi wanka ta shirya cikin riga da skirt na atamfa roba-roba, ta dasa kujera a tsagar gida tana yankewa Sabra farce, Sabra ta zille ƙafa tace "dan Allah Adda karki yanke ni", Hajar ta ɓalla mata harara ta fuzgo ƙafar tace "da can da nake yanke miki na taɓa yankar ki ne??". wani yaro ne yayi sallama siyar kulele, Sabra taje ta amso kuɗin Hajar ta zuba masa a kwanon da ya kawo, Hajar ta shiga ɗaki ta ɗakko canji ta bata ta kai masa tare da kulelen, saida yaron ya tafi ta tina cewa bata zuba masa yaji ba, tasan aiken iliya mai awo ne tinda taga kwanonsa ne, indai shine sai ya dawo yace a zuba masa yaji, ta zauna ta ƙarasawa Sabra yankar farcenta, tana gama mata ta fita wasa ita kuma ta shiga bayi, tana toilet ta jiyo yaron ya dawo yanata ɓurari wai a zuba yaji a kulele. Sa'adatu ta fito tsakar gida da kayanta haɗin bauta, zani jaka a tsaye sai wata tsohuwar riga Tshirt duk ta jeme, gyatsine tayi ta mulmulo ashar tace "kai me za a baka kake mana ihu??", yaron yace "yaji za'a zuba min a kulele", Sa'adatu taja wani dogon tsaki tamkar tsohuwar tsaka tace "kawo na zuba maka", ya miƙa mata kwanon, ta buɗe tana kallon kulelen da aka shanana masa manja gwanin sha'awa, ta taɓe baki ta tsugunna ta duntsi ƙasa cikin hannu ta barbaɗe kulelen da ita tas, ta rufe ta miƙa masa tace "jeka an zuba yajin", yaro yayi kasaƙe yana kallonta da mamaki, taja tsaki ta fara kwashe kayan shanyarta akan igiya, Hajar ta fito daga bayi taga yaro tsaye da kwano a hannunsa tace "yaji za'a zuba ko??", ya nuna Sa'adatu da hannu yace "waccan ce ta zuba ƙasa a ciki", Hajar ta zaro ido waje tace "ƙasa?" ta karɓi kwanon ta buɗe, ai kam dai kulelen nan bazata ciyu ba saboda tasha ƙasa harda tsakuwa, wani ƙululu ne ya tsaya mata a maƙoshi gashi umma ta mata gargaɗi, dole ta hakura ta zubo masa wata sabuwar kulelen ta juye waccan, ta koma kan kujera ta cigaba da yanke farce, gani tai bazata iya yin shiru ba kawai anyiwa baabarta asara ta ɗari biyu, ta kalli Sa'adatu da take kwashe kaya jikin igiya tana bigesu saita linke ta ɗora a kai tace "Sama fanta ƙasa coca cola, fuska fara ƙafa baƙa", Sa'adatu ta ƙyalƙyale da dariya amma a zuciyarta ji take kamar ana zuba mata dalma, Hajar kam kamar ta sani harma kamar waƙa take haka ta cigaba da cewa "Sama fanta ƙasa coca cola, fuska fara ƙafa baƙa", Sa'adatu da haushi ya gama turnuƙeta gashi Hajar ko kallonta ba tay ballantana tace da ita take ta shiga ɗaki tamkar zata tashi sama. ★Zaune take cikin wani jugunannen palour wanda ya ƙure lambar haɗuwa, hannunta riƙe da wani tsadadden bowl tana shan fruit salad, damɓasheshiyar Tvn palour sai aikinta take, wata ƴar budurwa ce ta sakko daga kan stairs ɗin da ya kewaye makeken palour, ta zauna kan sofa tace "Mami yaya Nurain bai dawo ba har yanzu??", Mami ta shanye fruit ɗin bakinta tace "Eh bai dawo ba", Noor ta taƙune fuska ta kalli agogo sai kuma ta jingina da kujera ta fara latsa tsaleliyar wayarta, Mami ta kalleta tace "is there any problem dear??", Noor ta ajiye wayar tace "No Mami", Mami tace "ohk" ta cigaba da shan fruit salad ɗinta tana kallon Tv, few Minutes after that wani sassanyar ƙamshi ya fara karaɗe palourn da yake ƙamshin breath taking freshner, Noor ta kalli door jin ƙamshin na yayanta ne, ai kam dai shi ɗin ne, yayi sallama ya tako a hankali hannunsa riƙe da briefcase, Mami ta ajiye bowl ɗin hannunta a hannun kujera bayan ta amsa sallamarsa, a kan soft carpet ɗin dake malale a palourn ya zauna yace "Mami barka da gida", Mami tayi murmushi tace "An dawo lafiya Nurain", yace "lafiya alhmdllh" ya koma kan kujera ya zauna. Noor tace "yaya sannu da dawowa", ya kalleta yace "yawwa Lil sis", Mami tace "a kawo maka abinci ko sai anjima", yace "amm yanzu zanci, Noor ta shirya min kafin na dawo", ya ɗauki briefcase ɗinsa yabi stairs, saida yayi wanka ya shirya cikin ƙananan kaya ƴan ubansu sannan ya sakko down stairs, already Noor ta gama shirya masa lunch, zama yayi yana ci peacefully, Mami tace "yauma kayi surgery ne Nurain??", ya ajiye spoon ɗin hannusa yace "yeah Mami, amma banje hospital da nufin yin surgery ba, wata patient aka kawo emergency tana buƙatar aiki in not less than 24hours, a rayuwar nan ta yanzu nothing goes without money, gashi asibiti sun buƙaci su kawo kuɗi mai yawa kuma basu da hali ga surgeon ɗin da zaiyi aikin yace sai an biya sa, ni kuma naga aikin is inside my field shine nayi surgeryn free", Mami ta jinjina kai tace "Allah ya saka maka da alkhairy, i know baka zama likita saboda neman kuɗi ba sai don temakon al'umma". yace "Mami akwai rashin temako a ƙasar mu sosai, masu temako basu da yawa". Mami tace "idan ka temaki wani Allah zai temake ka, Nurain Allah kaima ya dafa ma cikin lammuranka", yace "Ameen". glass cup ya ɗauka da lemon kwali, har zai buɗe lemon sai kuma ya fasa ya kalli Noor yace "plxx change it with chivita orange", ta miƙe ta amsa ta shiga kitchen ta buɗe damfareren fridge ta ɗakko masa chivita orange, ta dawo ta ajiye masa a gabansa sai kuma ta tsaya tana kallon rigar jikinsa fara tass, tsuke ido tayi tana nuna rigar tace "yaya wai rigar nan ta rannan da ka shafo taɓo ajiki yauma itace ka saka??", Nurain ya kalli rigar jikinsa yace "hey get out" ya saita mata hanya........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche { 5...} Noor ta koma kan kujera tana murmushi tace "Allah kam sai naga kamar rigar ce", shiru yayi mata ya buɗe lemonsa ya zuba a glass cup ya fara sipping, Noor ta tashi ta haye stairs ta kara wayarta a kunne tana murmushi. Mami ta kallesa tace "Nurain", ya ɗago yace "na'am Mami", Mami ta sauke ajiyar zuciya ta mayar da hankalinta kacokan akansa tace "you have to move on dear, me ake ciki ne maganarka da Ruqayyah??, ka riga da ka gama gini to mai kake jira, gaskiya ya kamata ka motsa kar iyayenta su ɗauka playing daughtern su kake", Nurain ya sauke sassanyar ajiyar zuciya ya dire cup ɗin hannunsa yace "yeah Mami daman ina so na gaya miki ki sanar da Abba, I'm ready a kai kuɗin, kuma..." sai yayi shiru yana shafa lallausar sumarsa, Mami tace "kuma me??", yace "kar a saka lokaci mai tsaho tinda dai mun gama fahimtar juna, kuma maganar lefe shima ba wata matsala Insha Allah", Mami tayi murmushi tace "idan kai a shirye kake toh iyayenta fa, nima kaina ban shirya ba", yace "Amma nasan kafin lokacin kin shirya aii", tace "maganar lefe mai za a ƙara nasan dai akwai wasu kayan wajen zulaiha, abinda ya rage bashi da yawa", yace "yeah munyi maganar da ita tace 2million sun isa a cike ragowar kayan", Mami tace "toh shknn zan sanar da Abbanku idan ya dawo", Nurain yace "ohk, bari na fita masallaci", ya miƙe ya fita daga palourn. Da daddare Mami ta tari Abba da maganar ta sanar dashi komai, Abba yana zaune a palournsa ya kalli Mami yace "ohk, kika ce yace he is ready??", tace "uhmm haka yace", yace "ohk then, bawai na rabu da Nurain yayi komai na aurensa yana nufin bana sonsa bane, abinda yasa ina son ya martaba matarsa ne kuma ya kula da ita, nafi so yayi aure da dukiyarsa yadda zaifi kula da matar da haƙƙoƙinta, though banida doubt akan Nurain amma i have to do this", tace "na fahimceka my prof". Abba ya ɗauki wayarsa yayi dialing numbern Nurain ya kara a kune, Nurain a lokacin yana balcony yana waya da Ruqayyah, ganin kiran da yake shigowa wayarsa yasa yace "ina zuwa bari na ɗauki kiran Abba zan kiraki if I'm done", Ruqayyah tace "ohk" ta katse kiran, yayi picking kiran Abba, ba tare da ɓata wani lokaci ba Abba yace masa ya samesa a palourn sa ya katse kiran, Nurain ya sakko down stairs ya wuce part ɗin Abba, ya murɗa tsadadden handle ɗin ƙofar palourn ya shiga da sallama, Mami ce ta amsa ya ƙaraso ciki ya zauna kan carpet yace "Abba gani", Abba ya nuna masa sofa yace "zauna", ba musu ya koma ya zauna inda Abba ya nuna masa, Abba yace "naji saƙonka wajen Maminku, naji daɗin hakan, kace kar a saka lokaci mai tsaho amma baka tunanin ɓangaren ita yarinyar zasu iya cewa lokacin ya musu ƙaranci, kamar month nawa kake so ayi fixing date??", Nurain yace "Amm kamar three months haka", Abba ya jinjina kai yace "ohk, kaine ai me aure shiyasa nake tambayarka, amma bazan yi assuring dinka three months ba idan sun nemi a ƙara musu lokaci za a mayar five months, idan kuma basu nema ba za a barshi a three months din da kake so, Insha Allah gobe zan samu uncles ɗinka next tommorow sai aje gidan nasu", Nurain yace "okay", Abba yace "ka iya tafiyarka". ★Umma na fita bakin titi ta tari napep ya kaita har ƙofar gidan Anty Jamila dake a unguwar Goron dutse, Umma ta shiga ɗan madaidaicin gidan mai ɗan ƙaramin gate da wajen parking mota ɗaya matsayin tsakar gida, Anty Jamila baki har kunne ta tarbi ƴar uwarta cike da murna, suka zauna a ɗan matsakaicin palourn Anty Jamila da yasha ado ba laifi, Hafsa ce ta shigo wacca itace second born ɗin Anty Jamila da jug mai ɗauke da zoɓo mai sanyi da ruwa ta ajiye a gaban umma, Umma tace "kai alhmdllh jiki yayi sauƙi, Allah ya ƙara afuwa", Hafsa tace "umma ina wuni, ya baki tahomin da Hajar ba?", Umma tace "lafiya lou, Hajar tana nan tafe zata zo aii", Hafsa tace "tom Allah ya kawota" ta fita ta basu waje. Anty Jamila tace "wllh Adda dama baki wahalar da kanki ba ai na gaya miki Hafsa taji sauƙi, amma naji daɗin zuwanki", Umma ta tsiyayi zoɓon a cup ta ajiye gefenta tace "akwai wani dalilin da ya kawoni bayan duba Hafsa aii", Anty Jamila ta gyara zamanta ta ɗauki remote ta kashe ƙarar Tv tace "ai da kin gaya min sai nazo can ɗin ma Adda ba sai kin wahalar da kanki ba", Umma ta sauke ajiyar zuciya tace "babu komai nan ɗin yafi", Anty Jamila tace "toh Adda Allah yasa dai lafiya", Umma tayi sipping zoɓo tace "Jamila babu abinda baki sani ba akan rayuwar gidan da nake, toh a da dai abin bai fiya damuna ba sai yanzu da Hajara ta fara mallakar hankalinta, yanzu fa gidan kullum cikin tashin hankali ake, ga Hajara ba zata taɓa gani ta kyale ba, in ƙarƙare miki zance har dambe ake yi dani", Anty Jamila ta riƙe baki ta zabga salati tace "Adda dambe..", Umma tace "da zarar sun tsokani Hajara saita rama, to sai su haɗu su lakaɗa mata duka, ni kuma idan naga zasu kassaramin ƴa saina shigar mata a haka abin yake zama dambe, babu irin faɗan da ban yiwa Hajara ba akan ta dena biye musu amma kuma taƙi ji saboda na lura da ita tanada zuciya kuma bata son wargi, toh yanzu gaba ɗaya lungun mu an riga da an canfa mana gida wai mu ƴan bala'i ne kullum cikin dambe muke, kinsan mutane wallahi harda nasu gishiri da magin suke ƙarawa, ni dai yanzu na yanke shawara zan mayar da Hajara wajen Iya ko a samu sauƙi, jira nake suyi sauka a islamiyya saita koma gaban Iya, ko ya kika gani??", Anty Jamila tace "Eh toh me zai hana ki kawomin ita nan saina haɗasu da Hafsa", Umma ta girgiza kai tace "gara dai na kaita wajen Iya kinga ta ringa taimaka mata da wasu abubuwan, amma kuma bansan ta yadda zan shawo kan Mal ba kinsan yadda yake jin Hajara duk cikin ƴaƴansa", Anty Jamila tace "indai kikai masa bayani ai zai gane". Umma bata baro gidan Anty Jamila ba sai bayan sallar la'asar. ★Wata numfasasshiyar Mota ce tayi parking a daidai lungun ƙunshi, saida motar tayi minti ashirin da tsayuwa sannan Sa'adatu ta buɗe ƙofar mai zaman banza ta fito, hannunta riƙe da ledoji ta fara tafiya tana rangwaɗa ta shiga lungunsu, Naseer na zaune akan benci gaban shagon Iliya kuma akan idonsa aka sauketa daga mota tazo ta wuce, iliya da Munkaila suka haɗa ido suka kasa cewa komai saboda kasancewar Naseer a wajen, ita kam Sa'adatu bata ma lura da yayan nata ba saboda duhun dare na damuna, saida Naseer ya bari tayi nisa sannan ya biyo bayanta, tana shiga soro shima ya shiga ya sakawa ƙofa sakata, ya saka ƙafa ya kwarfeta ta zube a ƙasa har saida bayanta ya amsa, beyi wata-wata ba ya zuge belt ɗin wandonsa ya fara zabga mata ta ko'ina, Sa'adatu ihu take tana neman ceto gashi ta kasa tashi ƙugunta ya riƙe, da iya ƙarfinsa yake sauke mata ruwan belt ajiki. Maama da Maimuna da kuma Nabilah da suke tsakar gida suka jiyo ihu a soro, Maama ta miƙe da sauri tana gyara zaninta da yake shirin kwancewa tace "ke Sa'adatu ce fa" tayi hanyar soro cikin sauri Maimuna ta bita a baya, Nabilah kuma ta rarumo wayarta keypad tana ƙoƙarin kunna fitila wayar ta suɓuce daga hannunta ta tawarwatse a ƙasa. soron duhu dunɗum Maama cewa take "Nasiru ka rabu da ita nace maka", Naseer kam dukan Sa'adatu yake da iya ƙarfinsa yana cewa "uban waye wancan da ya ajiyeki a mota??", Sa'adatu da azaba ta hanata magana sai gunji take, Maama ta kwalawa Nabilah kira tace "ki ɗakko min kyandir a ɗaki", kafin Nabila ta kawo kyandir ai Sa'adatu ta faɗawa ƴan garinsu, a matuƙar fusace Naseer ya wuce cikin gida Maimuna da take kan hanya itama saida ta samu rabonta, domin kuwa saida ya cije ya zabga mata belt ɗin hannunsa ta ɗaureta ya zuge mata ita ajiki tayi mata wankan jego, da mugun gudu Maimuna ta kyalla cikin gida tana soshe-soshe, batama san lokacin da ta bangaje Nabilah ba kyandir ɗin hannunta ya liƙe mata a wuya har saida fatar wajen ta kwaile, Nabilah da zafin wuta ya ratsata ta mulmulo ashar ta danƙara mata, a banza dan Maimuna batama san me ta aikata ba ji take tamkar an zuba mata tafasasshen ruwan zafi a fatar baya. Maama ta tallafi Sa'adatu ta shiga da ita cikin gida, gaba ɗaya jikinta yayi ruɗu-ruɗu da shatin belt, ga wani shaɗi da yayi mata a fuska wajen har ya kwaile, Nabilah ce ta tsaya ɗakko ledojin da Sa'adatu tayi wurgi dasu tin lokacin da Naseer ya kwarfeta, shawarma ce da pizza gaba ɗaya sun gama baɗewa da ƙasa babu ta yadda za ai su ciyu, ice cream kam kifewa yayi a ƙasa. Maama ta shiga ɗakinsu Naseer tace "Nasiru banyi maka gargaɗi akan dukar min ƴaƴa ba?", Naseer ya dafe kai yace "Maama dan Allah ki barni da yaran nan, wllh a wata ƙwatuwar mota aka sauketa, ki duba fa irin suturar jikinta sai kace ƴar arna", Maama tace "nima tashi ka dakeni Nasiru tinda har agaban idona kake kiran ƴata arniya", Naseer ya fice ya bar ɗakin yayi soro da sauri. Washe gari tinda Hajar tayi sallar asuba bata koma bacci ba, tana zaune tana tilawar Al'qurani har saida gari ya fara washewa sannan ta rufe karatun ta matsi toothpaste a brush ɗinta ta fita tsakar gida, saida ta kusan wurgi da brush din hannunta ganin Sa'adatu da take fitowa daga ɗakin Maama da ɗingishi, fuskarta ta kumbura idonta na hagu ya lume da taruwar jini a gefensa, gefen kumatunta ya kumbura suntum sai kace ta ajiye kwallon goruba a baki, duk da irin saɓanin da suke samu saida ta tausaya mata, jiya da daddare tana jin lokacin da Naseer ya lakaɗa mata na jaki, Hajar ta taɓe baki ta saka slipers dinta ta wuce gaban tukwanen ruwa, ta ɗebi ruwa a buta ta saka kujera ta zauna ta fara goge bakinta, kamar daga sama taji saukar wani mugun ɗaɗe a gadon bayanta, ta gantsare saboda azaba brush ɗinta ya suɓuce daga hannunta..........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {6...} Da sauri Hajar ta miƙe daga kan kujera ta juya taga wane ne yayi mata wannan azababben ɗaɗen na rashin imani, Maama ta gani tana mata wani kallo mai cike da tsantsar tsana, Hajar ta ja da baya idonta na kawo ruwa tace "me nayi miki??", Maama tace "uwarki kikay min, uban waye yace ki zauna min a kujera?, ko so kike ki shafamin baƙin fentin da ke tare dake", Hajar bata ce komai ba darajar Naseer da Huzaifa yasa take ragawa Maama, Sa'adatu ta ɗingiso tana ƙoƙarin buɗe idonta na hagu da ya kanne tace "chaɓ wannan ɗan dukan, ai da kin sani dundu kikay mata wanda shegiyar za tay aman wahala", Hajar ta tsotse kumfar bakinta ta tofar ta zabgawa Sa'adatu harara tace "ke dalla malama ja can da ruɓaɓɓen bakinki, wllh kika sake magana saina naushi ɗayan idon kinyi duka babu", umma daga cikin ɗaki ta jiyo muryar Hajar ai kam ta fito da sauri, tana ganin Hajar tsaye ta riƙe ƙugu ga Maama da Sa'adatu tasan ba lafiya, daga bakin ƙofa ta tsaya tace "Hajara zo nan yanzun nan", Hajar ta ɗauki buta ta kuskure bakinta ta ɓallawa Sa'adatu harara ta shiga ɗakin umma. Maama ta kalli fuskar Sa'adatu tace "keda nace karki fito, me za kiyi a wajen?", Sa'adatu tace "bayi zan shiga ne", Maama tace "toh ina Maimuna da nace ta taimaka miki kafin anjima a karɓo miki magani a chemist", Sa'adatu tace "uhmm Maimunan ce zata temaka min" ta ɗingisa ta ɗauki butar da Hajar ta ajiye mai ruwa ta shiga bayii. Maama ta bita da kallo sai kuma ta nufi ƙofar ɗakin su Naseer, bubbugawa ta shiga yi da ƙarfi, Mu'azzam ya buɗe, ta ɓalla masa harara tace "ban hanya", ba musu ya matsa mata ta tura kai ɗakin, Naseer da yake kwance a katifarsa ya rufa har ka ta tsaya tana kalla, ta yaye rufar tace "Nasiru tashi", ya buɗe idonsa da kyar ya miƙe zaune yace "Maama lafiya??", tace "ka gaida babanku kuwa?", ya juyar da kai yace "Tin asuba muka gaisa aii", tace "toh maza yanzu ka fito ka sameni a tsakar gida karka ɓata lokaci" ta fita a ɗakin. Umma ta kalli Hajar tace "waike Hajara mai yasa kike da kunnen ƙashi ne iyee, ba nace ki dena shiga sabgar su ba", Hajar tace "Allah umma ban shiga harkar su ba, kawai fa ina zaune ina goge baki shine Maama tayi min ɗaɗe a baya wai na zauna mata a kujera", ta kwashe rigarta tace "kinga wajen", Umma ta zabga wani uban salati ganin yatsu biyar cif raɗa-raɗa a bayan ƴarta, wajen yayi Jajur tamkar ka taɓa jini ya fito abinka da farar fata, Umma tace "wllh Allah ya isa ban yafe ba", Sabra da take shafa Vaseline a ƙafafuwanta ta miƙe da sauri tace "Adda nagani", Sabra ta zaro ido tace "lalala chaɓ", Hajar ta sauke rigarta ta kalli umma tace "Umma ki bani kuɗi na siyo brush nawa ya faɗi a gefen kwata", Umma tace "kije wajen babanku ki karɓa", Hajar tace "tom, daman yanzu zanje na gaishesa" ta fita waje, a ƙofar ɗakin Baba ta tsaya tayi sallama sannan ta yaye labule ta shiga, ta durƙusa tace "Baba barka da safiya, an tashi lafiya??", Baba yace "lafiya ƙalou Hajara Allah yayi albarka", tace "Ameen Baba", yace "yaushe zaku fara jarabawar??", tace "banda wannan satin wani mai zuwa zamu fara", yace "toh Allah yasa a fara a sa'a, saiki dage da karatu", tace "Tom Baba" sai kuma ta fara murza hannunta tace "Baba dan Allah ka tahomin da brush idan ka fita aiki nawa ya lalace", ya karkace ya ciro ɗari biyar daga aljihunsa yace "gashi ki sayi brush ɗin, ragowar canjin kuma kiyi kuɗin makaranta dasu na gobe", tasa hannu biyu ta karɓa tace "nagode" ta miƙe zata fita daga ɗakin, Naseer ne ya yaye labule ya shigo fuskarsa duk kumburin bacci, Maama ce ta kunno kai ta wani rirriƙo Sa'adatu, Hajar dai ta koma gefe tana kallon ikon Allah sai kuma tace "yaya ina kwana??", Naseer yana murje fuskarsa yace "lafiya" ya samu guri ya zauna, Maama ce ta tattagosa wai tana buƙatar ganinsa a ɗakin Baba, ita dai Hajar ta kama gabanta ta samfe a ɗakin, Maama ta zaunar da Sa'adatu itama ta zauna tana kallon Baba tace "barka da safiya mal, yaudai ga ɗanka nan na kawo maka shi kayi masa katangar ƙarfe da dukar min ƴaƴa, ni nayi masa magana yaƙi ji, kalli kaga yadda ya sauyawa Sa'adatu kamanni, Maimuna ma tana ɗaki ya kwaile mata baya, toh gashi nan dai kayi masa magana wataƙila kai yaji maganarka, nidai nan gaba idan ya sake dukar min ƴaƴa kamar haka to wllh saina kwashe masa albarka kaf ehee", Baba ya kalli Sa'adatu ya juya ya kalli Naseer yace "kai ka daketa ??", Maama ta ɗaga murya tace "yo ƙarya zan masa kake tambayarsa, kayi masa gargaɗi kawai mal", Baba yace "dakata Rabi ki bari na gama magana, Naseer ina jinka me ya faru", Naseer ya gyara zama yace "Baba yarinyar nan kullum akan hanyar fita take daga gidan nan da shigar da bata dace ba, da dare sai kaga an ajiyeta a wata ƙatuwar mota, kuma motar da take kawota daban-daban ce, nayi mata kashedi amma taƙi ji shine jiya na zaneta", Sa'adatu ta fashe da kuka tace "Baba wllh ƙarya yake min, ai Maama tasan inda nake zuwa wajen ƙawata kuma ni ba a taɓa sauke ni a mota ba a napep nake dawowa", Naseer yace "ni nake miki ƙarya?", Maama tace "yo yarinya da bakinta kana ƙoƙarin yi mata sharri ai dole ta ƙaryata ka, mal nidae daga yau sai yau kar Nasiru ya sake taɓa min ƴaƴa, tashi muje", Maama ta miƙar da Sa'adatu suka fice daga ɗakin, Naseer yace "Baba, Maama tana sakaci da tarbiyyar yaran nan, wllh yarinyar nan a mota ake ajiyeta kuma namiji ne ba mace ba, ai ko macen ce a zargeta duniya ta lalace", Baba yace "na yarda da kai Naseer, abinda nake so da kai duk wani hukunci da za kai ka fara sanar dani kafin ka wanzar dashi, tashi kayi tafiyarka Allah ya shiryesu". ★Nurain ya sakko down stairs yana gyara zaman rantsatten agogon hannunsa, bai samu kowa a main palour ba don haka ya wuce part din Mami, da sallama ya murɗa handle ɗin palourn Mami ya tarar bata nan sai ya nufi ƙofar bedroom ɗinta, a hankali yayi knocking, daga ciki Mami tace "come in", ya buɗe door ya shiga, Mami na zaune bisa prayer mat ta idar da sallar walha, ta kallesa tace "A'a fita za kai, yau ai ba aiki ko??", yace "yeah, wajen Anty Zulaiha zani, tace tana son gani na, and i have another appointment", tace "ohk, anjima Abba da su Salisu zasu je gidansu Ruqayyah aii", ya jinjina kai yace "ammm Mami kin yiwa Anty Zulaiha maganar ne??", tace "eh na sanar da ita jiya da daddare", yace "ohk i think that was the reason take nema na, Noor fa?", tace "ta fita Grocery shopping wai girki zata ma friends ɗinta zasu zo", yace "ohk, na wuce", Mami tace "wait" ta miƙe ta buɗe huge press ɗinta ta ɗakko wata paper bag ta miƙa masa tace "ka kaiwa zuhaiha", ya karɓa ya fice daga part ɗin, katafaren compound din gidan ya fito mai ɗauke da shuke-shuke masu kyau da parking lots na motoci ƴan ubansu, Garba ne ya taho da sauri ya russuna yace "barka da fitowa alhj ƙarami", Nurain yace "yawwa, an gama wanke motar", Garba na washe haƙora yace "Eh an gama alhj" ya ciro key daga aljihun rigarsa ya miƙa masa, Nurain ya karɓi key ɗin ya zura hannu a trouser pocket dinsa ya ciro wallet ya buɗe ya fello dubu goma ya miƙa masa, hannu bibbiyu Garba ya amsa yana washe haƙora yace "Alhj harda hidima haka, to nagode Allah ya saka da alkhairy yasa afi haka", Nurain ya nufi wajen wata dunƙulalliyar mota a parking lot ya buɗe ya shiga, yayi warming sannan ya mirgina ya fita daga gidan bayan mai gadi ya buɗe masa damfareren gate. Slowly yake driving yana waya da Ruqayyah, wani murmushi ya sake speaking calmly yace "why are you doing this babe?, mesa bazan zo yau ba?", from the other side Ruqayyah tace "haba dearest nidae kunya nakeji, ka bari sai gobe kazo", yace "naji cewa sai gobe amma mesa zakiji kunya bayan da kanki kika kaini gidanku kikace kina sona kuma zaki aureni...", ƙit yaji ta katse kiran yayi murmushi ya sake dialing amma taƙi picking, a hankali yace "shy girl". A daidai gate din wani gida Bungalow ya danna horn, Gate man ya buɗe masa ya shiga da Motar yayi parking ya buɗe ya ɗauki paper bag din da ya ajiye a kujerar mai zaman banza ya fito, direct Main building din gidan ya dosa, ya tsaya a ƙofar shiga ya ciro wayarsa daga pocket ya kira Antyn nasa, tana yin picking yace "I'm here Aunt", Anty Zulaiha tace "toh me kake jira come in mana", Nurain ya shiga palourn da ya ƙawatu ba ƙarya bayan yayi sallama ya zauna akan kujera ya ajiye bag din hannunsa a gefe, wata ƴar budurwa ce da bazata wuce 20yrs ba ta fito daga kitchen hannunta riƙe da serving spoon, zaro ido tayi ta ƙaraso cikin palourn tace "yaya Nurain sannu da zuwa", yace "yawwa Khausar, ina Anty?", tace "bari nayi mata magana" tabi wani corridor, tare suka fito da Anty Zulaiha, Khausar ta koma kitchen Anty Zulaiha ta zauna kan kujerar dake kusa da nashi tace "na taso Dr da sassafe", ya shafa sumar kansa yace "ai mun saba da fitar safe, ya gida Anty?", tace "lafiya, ya Noor ta dai ƙi zaman gidan nan", yace "ai Noor Mami's tail ce" ya ɗauki paper bag din ya miƙa mata yace "inji Mami", tace "toh me na samu haka wajen yayata haka" ta buɗe taga perfumes ne kala uku, Khausar ta fito daga kitchen da trayn mai ɗauke da drink da kuma snacks ta ajiye masa, ta buɗe lemon ta tsiyaya masa a glass cup sannan ta koma kitchen, ya ɗauki lemon yayi one sip ya ajiye, Anty Zulaiha tace "jiya Mami take gayamin abin arziƙi, ashe yau za a kai kuɗi da sa rana, toh Allah ya tabbatar da Alkhairy, Ruqayyahn ce dai koh??", yace "yeah", tace "tom, maganar lefe na gaya maka balance dai koh??", yace "yea, yanzu zan miki transfer ba 2m ba??", tace "Eh haka yake, Insha Allah zasu isa a gama harhaɗo abubuwan da suka rage..", yace "idan ma basu isa ba just Ping me". Khausar da take rakuɓe a ƙofar kitchen kaf hirarsu a kunnenta ta lumshe ido a hankali tace "what kuɗin Auren yaya Nurain za a kai".............✍️ 💛 HAJAR💛 by Feenerh_feeche {7...} A wannan rana aka kai kuɗin auren Nurain da Ruqayyah, tsakanin ɓangaren ango da na amarya aka taƙaice sa rana wata huɗu cif, hakan ba ƙaramin daɗi ya yiwa Nurain ba cause he is eager to have her as his wife, on Monday Ruqayyah na zaune a Nurse station, Nurse Jidda tace "an yiwa shuka bar ruwa tasha taki ranar girbi ya kusan ƙaratowa nanda 4months", Ruqayyah tayi murmushi a taƙaice tace "ni kam abin yayi min wuri, i thought Daddy zai saka 1year haka amma wai da suka ce wata uku shine ya ƙara wata ɗaya", Jidda tace "A'a shi Daddy da zai aurar dake ɗin ai ya shirya, toh ke mene dalilin ki da zaki ce yayi wuri??", keenly Ruqayyah tace "my own schedule, anyway nothing is going to change, i can deal with it", Jidda tace "hey i don't get you me kike cewa ne??", Ruqayyah tayi murmushi tace "zaki gane ne", Jidda ta ringa kallonta sai tace "think wise kafin kice za kiyi wani abun", Ruqayyah har ta buɗe baki sai kuma tayi shiru sakamakon wayarta da ta fara ringing, the ringing tone yasa tayi murmushi ta ciro wayar daga handbag ɗinta, ta haskawa Jiddah screen ɗin wayar tace "kin gani my Dr ne yake kira, he loves me so much duk abinda zanyi zai min uziri", har wayar ta katse wani kiran ya sake shigowa sannan Ruqayyah tayi picking ta kara a kunne tace "slm dearest, ka ƙaraso ne??", daga ɗayan ɓangaren Nurain yace "yeah", tace "ohk yanzu zan kawo maka coffeen nasan sai kasha zaka shiga surgery", wayar kare a kunnenta ta miƙe ta dubi Jidda tace "plxx ki kulamin da ward A kafin na dawo", Jidda ta galla mata harara tace "A nawa??", Ruqayyah tace "zan taya ki Night" ta wuce gaba. Nurain yana zaune a office ɗinsa yana duba tsirarun patients ɗin da zasu gansa a yau, Dr Marwan da Khaleel ne suka shigo a tare, Nurain ya ɗago ya kallesu ganin yanayin fuskokinsu yace "what??", Khaleel yace "Allah ya sanya Alkhairy Boss", Dr Marwan saida ya zauna kan kujera yace "fatan alkhairy", Nurain ya taɓe baki ya jingina da chair yana wasa da yatsunsa ya kallesu duka yace "tnx, ƙarfe 11am zamu shiga surgery, get ready", Khaleel yace "yes bari nayi gathering team ɗin", Nurain yace "good", Khaleel ya fita daga Office ɗin, Dr Marwan yace "who will anesthesetice the patient, our anesthesetic is absent", Nurain yace "that is not a problem i have one", Dr Marwan yace "ohk then", Ruqayyah ce ta shigo hannunta riƙe da Mug, Dr Marwan ya miƙe daga kujera yace "tom Dr sai mun haɗu a surgery room", saida yazo fita ya kalli Ruqayyah da take gefe yace "toh Allah ya sanya alkhairy A Nurse, naga tin yanzu ma ana kula mana da Dr ballanta an samu full license", Ruqayyah tayi murmushi tace "ya Amarya??", Dr Marwan yace "tana nan lafiya" ya buɗe door ya fita, ta taka a hankali ta zauna kan chair tana facing Nurain, gani tay ya wani haɗe rai yana latsa wayarsa, Mug ɗin da ta shigo dashi ta tura masa tace "dearest ga coffeen fa", ba tare da ya kalleta ba yace "take it with you", ajiyar zuciya ta sauke tace "sorry ai a faɗan laifina dai ko?", wayar ya ajiye ya zuba mata idanunsa da suke tamkar madara yace "daman kin iya murmushi haka??", dariya ce ta kusan kufce mata tace "jealousy sorry bazan sake ba", keenly yace "good". tace "happy tinda an saka lokaci kaɗan yadda kake so", yace "kefa ba kya farin ciki ne??", shiru tayi ta fara wasa da hannunta, yayi ajiyar zuciya yace "help me", ta ɗago da kanta tace "how?", yayi mata wani narkakken murmushi yace "zanyi surgery anjima zaki min anesthesia", ta juya idonta tace "sure my Dr". ★Maama daga bakin murhu tana kwashe abinci, kwanon Baba ta fara zubawa sai na sauran ƴaƴanta, bayan ta gama ta miƙe tana sharce gumin da ya tsattsafo mata a goshi saboda zafin wuta ta shiga ɗakinta, Sa'adatu tana kwance akan wani ruɓaɓɓen gado daga gani ba a rasa kuɗin cizo a cikinsa ba, Maimuna kuma tana shafa man bleeching ɗinta a fuska da ɗaurin ƙirji ajikinta sakamakon wankan da bata daɗe da fitowa ba, Maama ta kalli Maimuna tace "tin safe nake ce dake kiyi wanke-wanke amma kin ƙi, yanzu ga abinci can na gama amma babu kwanon da zan zuba muku", Sa'adatu tace "Maama mai aka dafa??", Maama tace "wake da shinkafa ne", Sa'adatu tace "dame kuma??", Maama tace "da manja da yaji", Sa'adatu tace "haka tsura ko ɗan salak babu" ta miƙe a hankali ta ɗingisa saboda har yanzu ƙugunta bai gama saki ba, ta ɗakko jakarta ta buɗe ta fello duba ɗaya, Maama ta zaro ido tace "Sa'adatu ina kika samu kuɗi haka", Sa'adatu ta yamutsa fuska ta miƙawa Maimuna kuɗin tace "ki siyo min kifi na ɗari biyar, balangu na ɗari uku saiki siyomin maltina ta gwangwani guda ɗaya", Maimuna tace "chaɓ gaskiya bazanje ba", Sa'adatu tace "ke dalla malama zan sammiki fa", Maimuna tayi gyatsine ta warce kuɗin, Maama tace "Sa'adatu magana fa nake miki", Sa'adatu tace "toh ai kece Maama wllh kin fiya maida hannun agogo baya, na gaya miki ƙawata ce fa take bani", Maama tace "Allah sarki, toh Allah ya biya ta". Maimuna ta zari hijab ta fita. Sa'adatu ta doka wani uban tsaki tace "Maama saida nace fa ki tuna min yau za a siyo piya-piya a yiwa ɗakin nan feshi ko ma samu sauƙin cizon kuɗin cizon nan, wallahi jiya kasa bacci nayi, ina kallon Maimuna da Nabilah ma sunata bige-bige cikin bacci", Maama tace "wai aikam na manta", Sa'adatu tace "shikenan nasan Maimuna ba sake fita za tay ba". Hajar ta fito daga ɗakin Umma da kwandon soso da sabulu a hannunta, bokiti ta ɗauka ta ɗebi ruwa ta shiga wanka, saida ta gama wanka ta fito ta shirya tsaf cikin uniform ɗin islamiyya, Sabra kam tayi gaba tinda ita da wuri ta dawo daga boko, Umma na linke kayan wanki tace "to Allah ya bada sa'a", Hajar ta ɗauki jakarta tace "Ameen". ★Kwanci tashi Hajar ta kammala rubuta jarabawar NECO, yanzu result kawai take jira saita fahimci wace alƙibla zata fuskanta, lokacin jarabawar kam tayi karatu ba ƙarya ga kuma wanda take yi tin fil azal, bayan sati biyu da kammala NECO a islamiyya ma aka fara yi musu screening ɗin sauka, daman sun shafe wata takwas da hattamawa suka tsaya ƙarasa littafai, yanzu kam satinsu uku da fara yin screening, A yammacin wannan rana Hajar ce zaune a kan kujera a bakin rariya tana wanke gwangwanayen kulele, Sabra na yi mata ɗauraya, takun takalma ƙwas ƙwas daga soro yana doso cikin gida yasa Hajar kallon ƙofa, Sa'adatu ce ta shigo cikin wata shiga half naked, ga wani uban kitson attachment da ta yarfa har mazaunai, fuskar nan ɗaɗau harda hujen hanci tayi tana taunar chewing gum ƙass ƙass tamkar cikakkiyar ƴar bariki, yanzu karenta take ci babu babbaka iskanci ya linka na da Maama na goya mata baya, dodon nata Naseer yanzu baya zama a gida tinda ya samu aikin direban tirelar Ɗangote dake jigila tsakanin kano da Lagos shikenan yayi wuyar gani, Hajar ta taɓe baki ta cigaba da sha'anin gabanta, sai kuma ta sake ɗagowa ganin wasu mata wanda suka amsa sunan cikakkun ƴan duniya su biyu a tare da Sa'adatun. Maama na rawar jiki ta shimfiɗa musu tabarma a tsakar gida, Sa'adatu ta nuna ɗaya daga ciki matan tace "Maama wannan itace zeenatu amma anfi kiranta da zeen" ta nuna ɗayar tace "wannan kuma mabaruka amma anfi kiranta da mabruk", Maama ta washe baki tace "Allah sarki, sannunku da ƙoƙari ƴaƴan nan, ai Sa'adatu tayi dacen samunku matsayin abokai", zeenatu tana taunar chewing gum tace "muma haka" cike da rashin ɗa'a da tarbiyya, Sa'adatu ta wage murya tace "ke Maimuna kina ji nazo bazaki fito ba", Maama tace "laaa ai bata nan", Sa'adatu tace "Nabilah fa?", Maama tace "tana ɗaki, ke Nabila ki fito ga ƴar uwarki nan tazo kina ji", Nabilah ta yaye labule ta ƙarewa su zeenatu da Mabaruka kallo tace "Sannunku" sai kuma ta kalli Sa'adatu tace "ɗan shigo daga ciki mana mu gaisa", Nabilah ta koma ɗaki Sa'adatu tabi bayanta, sama da ƙasa Nabilah ta ƙare mata kallo tace "kinga Sa'adatu ki dawo gida ki zauna, waɗannan kuma su waye haka kika kawosu marasa kyan ganii", Sa'adatu tace "nasan zaki zarge ni ai amma wllh kinji dai na rantse ko??, wllh bana kula maza bare takai da abinda kike tunani, rayuwa nake agidansu zeenatu da Mabaruka irin ta wayayyun mata masu ji da kansu", Nabilah tace "wayayyun mata??", Sa'adatu tace "Eh mana ko baki gani ba", Nabilah ta zabga uban tsaki tace "ni ban gani ba, kwata-kwata ma baku ɗauki hanyar zama wayayyun mata ba wllh, ai....", muryar Baba ce ta katse maganarta, a tare suka antayo waje, Baba ya kalli Maama yace "waɗannan su waye??", Maama tace "ƙawayen Sa'adatu ne fa", Baba ya nuna hanyar soro yace "ku tashi ku fitar min daga gida", Mabaruka ta kalli Sa'adatu tace "au daman Babanki bashi da mutunci Sa'adat", zeenatu ta figi jakarta tace "waini ake kora cikin wannan kuturun ruɓaɓɓen gidan sai kace kango, gidanda ko kiwon tumaki bazan yi ba, haba dattijo kai baka ji kunyar kiran wannan kangon da gida ba saboda tsiyar zuci". wani tuƙuƙin baƙin ciki ne ya takore maƙoshin Hajar da take zaune bakin rariya, da sauri ta ɗauraye kumfar hannunta ta gyara wuyan rigarta ta miƙe tsaye a fusace, Zeenatu da ta yo hanyar fita cikin sauri ta tsaya tana kallo, saida ta bari tazo gaf da ita zata wuce ta saka mata ƙafa, wani irin hantsilawa Zeenatu tayi ta kifa da ka, fuskarta ta faɗa cikin kwata, jikinta kuma ya afka kan gwangwanaye, warwas tayi a ƙasa cikin cakwalkwalin ruwan wanke-wanke mai datti da maiƙon manja, gaba ɗaya guiwoyinta da hannunta sun kwaile, da kyar zeenatu ta dafe hannunta ta miƙe bakinta da goshinta sun fashe, fuskarta dama-dama da kwata, Hajar ta gyara wuyan rigarta da wani irin rainin hankali tace "Baiwar Allah ki iya bakinki, kuma kisan a inda za kiyi zagi kici bulus, ke kin isa ki kalli mahaifina ki gaya masa magana akan idona, shiyasa na gurje bakin fitsarar da ruwan kwata, wllh kaɗan ma kika gani", waɗannan kalaman su suka dawo da Maama Sa'adatu Nabilah da Mabaruka daga duniyar daskarewa, zeenatu ta sharce kwatar da ta mamaye mata baki dake fitar da jini tana kallon Hajar cike da mamaki, Sa'adatu ta mulmulo wata ashariya tayo kan Hajar a fusace..........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {8...} Da sauri Hajar ta tuntsurar da ruwan ɗaurayar wanke-wanken, ta ɗauki bokitin ƙarfen ta nuna Sa'adatu da ta yo kanta tace "na rantse da girman Allah kika taɓani saina rotsa miki kai", Sabra tana ganin haka ta fita a guje kiran Umma da ta shiga makwabta barka, turus Sa'adatu tayi saboda tasan tsaf zata aikata, maimakon kan Hajar da tayi nufin yi saita juya akalarta zuwa ga zeenatu da take ta faman sharce kwatar fuskarta, Mabaruka ma ta taho da sauri ta kalli fuskar zeenatu tace "chab an tsokano sama da kara", Nabilah ta shiga tafa hannaye tana faɗin "mun shiga uku yau ga ƴar daba a gida tana dabanci", Maama tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un, mal kana ganin abinda shegiyar ƴar da kake iƙirarin takace ta aikata ko??, tafa fitarwa da ƴar mutane jini", Baba ya nuna Maama da hannunsa mai carbi yace "karki sake kiramin ƴa shegiya na gaya miki, Hajara ƴata ce", Maama ta tsaya tana kallon Baba galala tamkar wawuya sai kuma ta hura tukubar hancinta tace "wllh idan zaka shekara dubu kana kiran Hajara ƴarka saina ƙaryata", Hajar ta riƙe bokitin ƙarfen ta gam tana kallon kowa sama da ƙasa, Sa'adatu da Mabaruka suka temaki zeenatu ta wanke fuskarta da hannayenta, Mabaruka ta cire yalolon mayafin jikinta taci ɗammara ta kalli Nabilah tace "naji kin kirata da ƴar daba ko??, to ga wacca ta dameta ta shanyeta tas a iya dabanci", Baba ya ɗaga murya yace "Sa'adatu!!, ki kwashi ƙawayenki ki barmin gida", Mabaruka ta kaiwa Hajar wata damƙa, babu tausayi Hajar ta kwaɗa mata bokitin ƙarfe a hannu, azaba tasa Mabaruka durƙushewa tana yarfa hannu, da gudu Sa'adatu taje ta rarumo taɓarya zata jirga mata, Hajar ta kufce, da sauri Baba ya shiga tsakani hakan kuma yazo daidai da shigowar Umma gidan cikin sauri Sabra biye da ita, salati ta fara zabgawa ganin Hajar na huci hannunta riƙe da bokitin ƙarfe ga Sa'adatu itama da taɓarya, Maama tace "kin haifi bala'i da masifa wllh faɗima, ga shi nan shegiyar ƴarki ta kassara ƴaƴan mutane a gidan nan", Sa'adatu tsalle take tana hargowa tana ƙoƙarin bangaje Baba da ya shiga tsakaninta da Hajar faɗi take "kin san kwa su waye waɗannan, wllh yau sai kinyi nadamar zuwa gidan duniya", Hajar ta daka shewa tace "ahayye wllh sune za suyi nadamar zuwa gidan nan, dubeki dabba jahila daƙiƙiya kin tsaya kina hura hanci da ƙoƙarin bawa hammata iska akan jakunan da suka zagi mahaifinki, asararriya mara mafaɗi da tarbiyya....", Umma ta fizgi Hajar tana ƙoƙarin dannata a ɗaki, Sa'adatu ta yunƙuro tana ɓaɓɓarkawa Hajar zagi irin na cikakkun marasa tarbiyya, Hajar da Umma ta kusan cusata a ɗaki tace "tirr da halinki Sa'adatu, ki ɗauki tsummokaran jakunan ƙawayenki daga nan ku wuce chemist, gaba ɗayansu idan suka ji zugin shanshanbale na ratsasu suka ɗanɗana azaba zasu gane inda ya kamata su nuna rashin tarbiyyarsu", Sa'adatu tace "zaki gani ne ba dai zeen da Mabruk kika taɓa ba", Hajar tace "babu abinda zan gani sai alkhairy, sara da sassaƙa basa hana gamji tofo, jaka kawai". Umma tayi nasarar danna Hajar a ɗaki ta rufe ƙofa, wani irin huci Hajar takeyi tana sauke numfashi, Umma ta kalleta cike da takaici tace "ba kya jin magana Hajara, Insha Allah gobe goben nan zaki bar gidan nan", Hajar ta koma gefen gado ta zauna tana huci zuciyarta wasai. Washe gari Umma ta haɗawa Baba karin kumallo, ɗumamen tuwa da kunun tsamiya, zama tayi har saida ya gama cin abincin sannan tace "yawwa mal daman ina so Hajara ta koma wajen iya da zama tinda zamanta anan gidan ya ƙi daɗi, idan babu damuwa ta koma gaban iya", Baba ya zuba ruwa a kofin da ya gama shan kunu ya girgije yace "faɗima ina ne gidansu Hajara?", Umma tace "nan ne", yace "yawwa, to Hajara babu inda zata agidansu zata zauna", Umma tace "amma mal...", ya ɗaga mata hannu yace "ya isa haka, kirawo min Hajarar", tace "tom" ta fita a ɗakin ta shiga nata, Hajar da take gyara gado ta kalla tace "kije inji Babanku", Hajar ta ajiye bedsheet din hannunta ta fita, ɗakin Baba ta shiga da sallama ta tsugunna tace "Baba gani", ya kalleta yace "Hajara banji daɗi da kika biyewa fitsararrun nan ba jiya, kin saɓa alƙawarin da kikai min kwanaki cewa bazaki sake shiga sabgarsu ba, yanzu jiya me kika yi..", ta buɗe baki za tay magana ya ɗaga mata hannu yace "duk nasan abinda ya faru kuma nasan me yasa kika shiga sabgar su, da kinyi haƙuri saiki samu riba, karki sake aikata hakan kinji", tace "tom Baba", yace "tashi ki tafi Allah shiryeki". ta miƙe a sanyaye ta fita, gyaran gadon da take ta ƙarasa snn ta share ɗakin. ta fito tsakar gida tana kallon Umma da ke bakin rariya, kallo ɗaya umma tayi mata ta ɗauke kai ta cigaba da wanke waken kulele da za a kai markaɗe, Umma ta ɗauki zafi fishi take da Hajar ainun yau ko gaisuwarta bata amsa ba da asuba, Hajar ta tsugunna a gabanta tace "Umma dan Allah kiyi haƙuri, nadena bazan sake ba", ba tare da ta dubeta ba tace "ai daman kin iya tuban muzuru, ki matsa min a nan wajen", idon Hajar ya ciko tace "dan Allah Ummana ki yafemin nadena bazan sake ba", Umma ta ja tsaki tace "sau nawa akai hakan Hajara, tinda dai kinƙi jin maganata ai sai kiyi abinda kika ga dama, duk abinda haƙuri bai samar ba rashinsa bazai yi ba", Hajar tace "wllh Umma nifa bana shiga harkarsu tinda kikai min magana, sau nawa suna takalata bana kulasu, jiya ma fa ƙawayen Sa'adatu ne suka yiwa Baba rashin ɗa'a", Umma tace "uhmm ai kina ganinsu kinsan basu da tarbiyya dan me yasa zaki tanka masu", Hajar tace "bazan sake ba", Umma tace "da ya fi dai". Maimuna ce ta fito daga ɗakin Maama tana rangwaɗa, ta saka wasu matsattsun kaya riga da skirt na atamfa, saboda ɗamewar da skirt ɗin yayi mata har shatin panties ɗinta ana gani, itama ta tsiri fita yanzu kuma bata dawowa gida sai dare da ƴan ledojinta na kwaɗayi mabuɗin wahala, ko kallon inda take Umma da Hajar ba suyi ba tazo ta gama barbaɗesu da Harara kana ta fita. Hajar tace "umma dan Allah da yamma zanje gidansu zainab muyi karatu", Umma tace "toh shknn Allah ya kaimu". Bayan Sallahr la'asar Hajar tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga ta atamfa, ta kashe maiƙon fuskarta da farar huda ta murza lipstick a lips ɗinta, ta saka hijab da ya zarce mata guiwa, tayi kyau sosai sai kace wacca ta caɓa kwalliya, wani flat shoe ta ɗakko ta saka ta yiwa Umma sallama ta ƙara gaba, da yake gidansu Zainab ɗin akwai ƴar tazara daga gidansu, ta tsaya a bakin gate tana knocking a hankali, Zainab ce ta buɗe ƙofar ta haɗe rai tace "haba Hajar tin ɗazu fa nake jiranki amma sai yanzu zaki zo", Hajar tace "ke dalla malama Umma na taya aikin kulele", Zainab ta matsa gefe tace "Shigo mana", a ɗan matsakaicin compound ɗin gidan suka tsaya, Hajar ta kalleta da kyau tace "ke kuma ina zuwa??, naga kinyi shiga sai kace mai shirin fita", Zainab ta gyara yafen mayafinta tace "fita zanyi mana, tinda Allah ya kawoki saiki rakani Ummi ce ta aiken", Hajar tace "ban tambayi Umma ba iya nan kawai nace mata zanzo", Zainab tace "muje ki gaisa da Ummi saina kira Umma a waya mu tambayeta ko?", Hajar tace "Eh hakan dai yafi". cikin gidan suka shiga, Mamansu Zainab tana zaune a palour, Hajar ta tsugunna tace "Ummi ina wuni", Ummi tace "ina gajiya, ya Maman taku", Hajar tace "lafiya alhmdllh", Ummi tace "masha Allah", Zainab tace "Ummi ɗan aramin wayarki plxx", Ummi ta lalubi gefe da gefenta taji wayam tace "duba ɗakina", Zainab ta shiga ɗakin Ummi ta fito da wayar a hannunta ta kalli Hajar tace "taso muje", ɗakinsu Zainab suka shiga, Zainab ta miƙawa Hajar wayar tace "saka numbern Umma", bayan Hajar ta ɗura numbern tayi dialing, anayin picking Hajar taji muryar Sabra, Hajar tace "game kike mata ko?, maza ki kay mata wayarta", tana jiyo muryar Sabra tana cewa Adda ta bugo waya, Umma tayi sallama ta kara wayar a kunne, Hajar tace "Umma nice". da kyar Umma ta amince kuma tace mata kar ta kai magariba. bakin titi suka fito suka tari napep, unguwar da suka je ta masu hali ce haka ma gidan da suka amso saƙo wajen ƙawar Ummi, a clean and silent street ɗin suka tsaya suna jiran abin hawa. ★Noor na zaune a main palour tare da Khausar da yau kwananta biyu a gidan, wata spicy noodle mai shegen daɗi suke ci, gaba ɗaya hankalin Noor yana ga TV da ake haska wani Kdrama, Khausar ta ajiye fork ɗin hannunta tace "Noor what is the name of the drama??", ba tare da ta kalleta ba tace "Alchemy of souls", Khausar ta taɓe baki tace "ni kam nafi kallon Cdrama, ina yaya Nurain ne?", Noor bata amsata ba her mind was fully on screen, Khausar ta ɗala mata duka a cinya tace "hey I'm talking to you", Noor ta zabura tace "ouchh kadan ba saina rama ba" ta mayar da idonta Tv, Khausar tace "wai bazaki ci ba saita sandare", Noor idonta ƙur kan Tv tace "kashe AC", Khausar ta janyo wayarta tace "I'm not your servant". atmosphere ɗin living room ɗin ce ta fara canzawa zuwa wani breath taking scent mai daɗi, Khausar ta ɗago kanta suka haɗa ido da Nurain, murmushi yayi mata ya kalli Noor da bata ma san da shigowarsa ba yace "Noor.. Noor.. Noor.." ya kirata sau uku, saida Khausar ta zungureta sannan ta juya tace "what, wai mene??", da ido Khausar tayi mata nuni da Nurain tace "yaya na magana", yace "juicy fruit salad zaki hada min", Noor tace "ohk, amma babu fruit fa, apple and berries ne kawai ya rage", juyawa yayi ya fita daga palourn Khausar ta bisa da kallo, compound ya fita yana neman Garba ya bashi ya siyo masa fruits ɗin amma ya tarar baya nan, lallausar sumarsa ya shafa yace "shittt", ya shafa pocket ɗin wandonsa yaji key ɗin motarsa yace "good", motarsa ya dosa dake parking lot ya buɗe bayan ya gama warming ya mirgina ya bar compound ɗin, a hankali yake murza steering ɗin motar amma kuma ya take accelerator. Almost 20mis Hajar da Zainab na jiran napep, wasu yara su uku suna wasa da ball daga cikin wani ɗan fili, guda ɗaya ne ya buga ball ɗin da ƙarfi tayo kan road, da gudu yaron ya biyota a lokacin kuma wata dunƙulalliyar mota ta yanko cikin street ɗin with minimum speed, saura ƙiris motar ta bige yaron taci wani uban burki ƙiiii ta tsaya gaf da yaron da tsoro yasa ya ƙame, Hajar ta runtse idonta tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un", Zainab kam juya baya tayi ta toshe kunnuwanta da hannayenta, a hankali Hajar ta buɗe idonta ta dubi yaron da ya zama froze a gaban motar, da sauri ta isa gabansa ta fara shafa kansa a hankali tace "wake up kiddo babu abinda ya sameka", ajiyar zuciya yaron ya sauke. Tinda ya tabbatar bai bige yaron ba ya kifa kansa ga steering, calming kansa yake yana addu'a a zuci, ajiyar zuciya ya sauke ya ɗago kansa a hankali, ta front glass yake kallon yaron da kuma ƴar budurwar da take tare dashi wacca tayi backing dinsa bega face ɗinta ba. tamkar wacca aka umarta haka ta juya ta kalli glass ɗin motar da wani irin yanayi, in one sight ƙwaƙwalwarsa tayi booting on ya gane wannan fuskar, one thing came to his mind which is ƴar gidan gini.........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Nafeesah Yusuf Nagoda ~~(Feenerh_feeche)~~.........✍️ {9...} Da yake glass din motar tint ne yasa Hajar bata ga drivern ciki ba. hannun yaron ta riƙe still dai tana kallon glass din motar, kawai jira take drivern ciki ya fito, few seconds passed amma babu alamar wanda yaso aikata ta'asa zai fito, Zainab da ta toshe kunnuwanta har tayi jarumtar juyowa ta hango Hajar tsakiyar titi tare da yaron, Hajar taja hannun yaron ta tsaya bakin ƙofar driver ta shiga knocking glass, a hankali glass din yayi ƙasa ya zuge gaba ɗaya, wani sanyi da ƙamshi suka fara sirnanowa suna dukan fuskar Hajar da ta yaron. Hajar ta haɗe gira tana kallonsa tace "malam wai baka san darajar rai bane iyeee?, ya za ai ka kusan bige yaro amma ka wani hakimce a mota bazaka fito ka dubasa ba", Zainab ce ta tsallako kan titin itama tace "zo mu tafi ai Allah ya kiyaye tinda dai bai bigesa ba", Hajar tace "ke kinga mutumin nan fa ko a jikinsa, idan da ace ya bige yaron nan fa sai fa yadda Allah yayi", shi kam Nurain mamaki da firgicin da ya ziyarcesa ne ya hanasa magana, Hajar ta sake kallon cikin motar tace "Allah ya isan sa kuma a ringa sanin darajar ɗan Adam", Zainab ta zaro ido tace "Hajar mene haka", Hajar taja hannun yaron ta tsallar dashi titi tace "maza gida kaji", yaron ya kyalla da gudu ƴan uwansa suka take masa baya. wajen da suke jiran napep ta koma ta tsaya fuska a haɗe, mutanen yanzu basu da kirki ace ka kusan aika yaro lahira amma ka zauna ko a jikinka sai kace wanda ya kusan bige akuya yo ko akuyar ce aika fito ka duba idan kasan darajar rai, Zainab ta dawo gefenta ta tsaya tace "Hajar yanzu me kika aikata haka, Allah ya isa fa kikai masa, dubi fa har yanzu bai tafi ba", Hajar ta kalli motar da har yanzu take tsakiyar titi ta yamutsa fuska tace "me kwa na aikata, ya shekara a wajen kar ya tashi". a hankali ya juya kan motar ya gyara parking a gefen titi, Zainab ta damƙi hannun Hajar ta fara janta ganin ya fito daga motar ya tunkarosu, Zainab tana janta tace "Hajar kizo mu gudu kar yayi mana wani abun", Hajar ta fuzge hannunta tace "wllh bazan gudu ba", Zainab tayi tsam ganin har ya iso gabansu yayinda wani ƙamshi mai daɗi ya fara busowa a hancinsu, yana kallon Zainab speaking calmly yace "Assalamu alaikum young lady", a ɗarare ta amsa kana tace "bawan Allah kayi haƙuri dan Allah", Hajar da ta juyar da fuskarta ta juyo ta ɓalla mata harara jin abinda tace, girgiza kai yayi yace "ba komai, tell your friend itama tasan darajar ɗan Adam cause ba tayi hali ko kama da mutanen da suka san darajan mutum ba", da sauri Hajar ta juyo ta kallesa, and that look makes her brain to boot on, she see that calm and charming face familiar, but where and when??, walking fast ya koma ya shiga motarsa ya kunna ya fita daga street ɗin da reverse. gida ya koma sbd wannan incidence ɗin da ya faru yasa yama manta da wani batun fruit salad, yana parking motar Garba ya taho wajensa, ko kashe motar baiyi ba ya fito cikin sauri ya shiga cikin gida, Garba ne ya shiga motar ya kashe sannan ya zare key ya fito. har lokacin Noor da Khausar suna zaune a palour, Noor tana kallonsa tace "yaya ina fruit din ko basu ka fita nema ba", shiru yayi mata ya haye stairs, Khausar ta taɓota tace "he is weird", Noor ta sauke ajiyar zuciya tace "ina jin an ɓata masa rai ne", she knows her brother in and out kuma she is very sure rai aka ɓata masa. ★Hajar ta shiga gida sai gunguni take, Mu'azzam da yake alwala a bakin rariya yace "toh jarababbiya", ta zumɓuri baki tayi ɗakin umma, Maama da take talgen tuwo Nabila na mata tankaɗe tace "kin ji ba ɗan uwanta ma yasan jarababbiya ce", Nabila ta doka tsaki ta cigaba da tankaɗenta, Umma ta kalli Hajar da take ƙoƙarin cire hijab tace "ke kuma lafiya kike wani cin mur", Hajar tace "wai a duniyar nan Umma mutane basa son gaskiya, wai wani mutum ne ya kusan kaɗe wani yaro a titi amma ko a jikinsa, wllh ko fitowa ya duba yaron ƙi yayi", Umma tace "Allah ya kyauta bai dai bigesa ba ko??", Hajar tace "saura ƙiris fa, amma wllh mutumin nan yadda kika san gunki haka ya zauna a mota yaƙi fitowa ya duba yaron", Umma tace "ke kuma shine kike kumbura akan hakan", Hajar tayi shiru kawai tuno abinda yacewa Zainab take wai batayi hali ko kama da mutanen da suka san darajan ɗan Adam ba. kiran sallar magrib ne ya fitar da ita tsakar gida tayo alwala ta dawo ɗaki tayi sallah, bayan ta idar da Sallahr isha'i tana zaune akan darduma Sabra ta ajiye littafi a gabanta tace "Adda ki koyamin", Hajar ta janyo littafin ta duba kana ta fara gaya mata abinda zata rubuta. Umma ta shigo da wata warmer ta abincin da tayi tazarce ta ajiye a gefe guda, Hajar na kallon Sabra tace "yanzu ke Sabra mosquito din ne baki iya spelling ba, ƙwaƙwalwar dusa ne dake ko me??" ta zuba mata rankwashi aka, Sabra ta riƙe kai tace "ashhh Adda fa na iya", Hajar tace "to rubuta mana", Umma tace "kiyi mata a hankali dan Allah". washe gari Hajar taje islamiyya tayi screening dinta na ƙarshe, kuma a yau ne aka fayyace musu kuɗin sauka da walima, kwanaki uku bayan haka ranar Alhamis da yamma, Baba bai jima da dawowa daga wajen aiki ba yana zaune a ƙofar ɗakinsa yana cin abinci, wani yaro ne ya shigo gidan yace "wai ana sallama da mal Adamu", Hajar da take shanya kayan da ta gama wankewa tayi wuf ta shiga ɗaki, jikinta ne ya bata cewa ya sayyadi Nura ne yau yazo wajen Baba daman ya gaya mata zaizo, Baba ya ɗauki kofin ruwa ya sha sannan ya rufe ragowar abincin ya miƙe ya saka takalmi yayi soro, yana zuwa ya tarar da wasu mutane su uku, biyu zasu kai sa'anninsa ɗayan kuma matashi ne, matashin ne ya russuna yace "Baba barka da fitowa", Baba ya kallesa ya amsa, shi dai bai shaida su ba, Baba ya miƙa musu hannu su kay musabaha, ɗaya daga cikin manyan yace "daman munzo da wata magana ne", Baba yace "toh" ya koma cikin gida ya amso tabarma a wajen Umma, tinda Maama taga ya fita soro da tabarma taji hankalinta bai kwanta ba, ta kalli Maimuna da take zaune akan dokin ƙofa tana shan rake ita da Nabila tace "Maimuna leƙo mana su waye suka zo wajen Babanku", Maimuna ta ɗauki rakenta ta ɓalla sai kace sabuwar kamu ta wuce ƙofar soro ta laɓe, leƙawa ta farayi ta hango su a zazzaune, da sauri ta dawo da kanta tace "ya sayyadi Nura" sai kuma ta kasa kunne, kaf abinda suka zanta karaf a kunnuwanta tana naɗa, taɓe baki tayi ta dawo cikin gida tana zabga tsaki, Maama ta dakata da sharar da take tace "su waye??", Maimuna ta zauna dokin ƙofa ta ɓalli rage tace "wai neman izini suka zo yi a wajen Baba na neman waccan shegiyar", Maama ta saki tsintsiyar hannunta tace "neman izini kamar ya??", Maimuna ta hura buɗaɗɗen hancinta tace "ni dai a yadda na fahimta sunzo nemawa ɗansu auren shegiya ne", Maama ta zaro ido tace "aure??", Nabila ta zubar da tuƙar raken bakinta tace "Hajarar??", Maimuna ta kallesu duka tace "meye naga kun wani firgita ne??, bafa wani mai arziƙin ne yake nemanta ba, Nabila kin tuna ya sayyadi Nura??", Nabila tace "kwarai ma kuwa", Maimuna tace "toh shine fa yazo tare da iyayensa", Nabila ta daka wata shewa tace "waii tsiya ta ɗakko tsiya, da wannan ruɓaɓɓen shagon nasa zai riƙeta", Maama tace "kun sansa ne??", Nabila tace "farin sani ma kuwa, ya sayyadin islamiyyar mu da muka dena zuwa ne, wllh bashi da komai, matsolo ne ainun", Maama ta gasa mata harara tace "dalla gafara can, da bashi da komai ɗin ke kin taɓa kawo kamarsa ne eyee ko wanda bai kaishi matsolontaka ba?, wllh kun bani kunya duk irin samarin da kuka tara babu wanda ya taɓa zuwa gidan nan da maganar arziƙi, kuna zaune sai kace tsumammun kayan wanki waccan shegiyar zata cigaba", Maimuna tace "chaɓ, ina wani cigaba wajen Nura, wllh ci baya daii", Maama tace "ja can amma dai ta fi ku ko??", Maimuna tace "wllh bata fini ba nida nake da Alhaj, kuma yace aurena zaiyi, lokacin zuwa wajen Baba ne kawai bai samu ba". Baba ne ya dawo ciki ya naɗo tabarma a hannunsa, kan dardumarsa ya koma ya zauna ya kirawo Umma, Umma ta fito ta tsugunna tace "mal gani". Baba ya wassafa mata kaf abinda ya faru ya ƙarƙare da cewa "da har kuɗin aure suka ce zasu bayar na dakatar dasu sbd inaso na binciki yaron kuma a tabbatar da yarinya itama tana so", Umma tace "to mal Allah ya tabbatar da alkhairy". Maama da tayi karaf da kunnenta ta rangaɗa wata shegiyar guɗa ta cigaba da shararta. ★Nurain zaune a farar kujera a compound ɗin gidansu Ruqayyah yana jiran fitowarta, wayarsa yake latsawa a hankali, saida ya jingine 20mins amma bata fito ba abinda bai taɓa faruwa ba, dialing numbernta yayi, tana yin picking speaking keenly tace "ina zuwa dearest" ta katse kiran, after like 5mins ta fito sanye da hijab da riga da skirt na atamfa, taja kujera ta zauna tana facing ɗinsa tace "sorry na saka jira", wayarsa ya kashe ya saka a pocket yace "na ɗauka ma kwalliya aka tsaya tsara min", murmushin gefen baki tayi tace "ka jira lokaci, kwalliya har saika gaji da ita", ya ringa kallonta sai kuma yace "ehen ina jinki you said you want to talk to me", wasa ta farayi da fingers ɗinta tace "kana ji dearest", yace "all ears", ta sunkuyar da kanta tace "ina so a ɗaga lokacin bikin mu"............✍️ 💛 HAJAR 💛 by Nafeesah Yusuf Nagoda ~~(Feenerh_feeche)~~ {10...} with a weird facial expression Nurain ya kalli Ruqayyah, kallonta ya ringa yi ya kasa cewa komai, shirun da taji yayi ne yasa ta ɗago kanta sukay ido huɗu, tayi sauri ta sunkuyar da kanta tace "ina maka magana fa", keenly yace "naji ai, why Ruqayyah?, mesa kike so a ɗaga lokaci?", without looking at him tace "sai naga kamar za a matse maka hidima, dearest banaso ka matsawa kanka akan aurenmu, kabi komai a hankali, a maida lokacin nan da 10months kaga zaka fi balancing..", ido ya zaro yace "10 what?, Ruqayyah are you kidding me", tace "no dearest i am not kidding", ajiyar zuciya ya sauke yace "look Ruqayyah ba dai damuwanki karna takura kaina ba, babe just relax Inshallah komai zaizo cikin sauƙi, karki wani damu i planned for it", ajiyar zuciya ta sauke tace "alright", yace "good, yanzu wane shirye-shirye kika fara?", tace "ni ban fara shirin komai ba amma yanzu zan fara", yace "ohk, all the expenses on me", tace "Ohk". da haka kuma suka koma firarsu ta masoya mai daɗi. A kwana a tashi, bikin Nurain da Ruqayyah yau saura 3weeks cif kuma a yau ne aka shirya kai lefe, Anty Zulaiha da Sakeena step sis din Nurain da suke same father da Anty Mardiyya ƙanwar Abba sune jigajigai sai sauran ƴan uwa su biyar aka kai lefe. gaskiya an zuba bajinta, both sides sunyi ƙoƙari sosai, ammafa Ruqayyah ta samu lefe na gani na faɗa ba ƙarya. Nurain yana zaune a kan kujerar balconyn ɗakinsa dake up stairs yana jiran yaga motocin da aka tafi kai lefe dasu sun fara dawowa, ai kam yana ganin dawowar tasu ya sakko down stairs ya fita balcony, Anty Zulaiha da sauran suka wuce cikin gida, Nurain ya amshi baby boy ɗin hannun Sakeena yace "yawwa ƴar uwata fatan dai basu ƙara mana lokaci ba", Sakeena ta kallesa up and down tace "Nurain ni ka raina kenan ko?, nice baka jin kunya ba?, mesa baka tambayi anty Mardiyya ko Zuhaiha ba saini karkatacciya bishiyarka mai daɗin hawa ko?", yace "ohh wllh kin fiya son girma", handbag ɗinta ta ɗauka ta rufe motar tayi gaba tace "zaka ga son girma alhaji". yana kallonta ta shiga ciki ya shafa kansa shima ya shiga. A palour ya tarar dasu sun baje haja suna mayar da yadda akai, Mami ma na tare dasu suna wassafa mata yadda akai, Noor ta zazzaro ido tana dashare tooth a cikinsu, Allah kaɗai yasan yadda ta tamawa bikin nan, Nurain ya zaga ta bayan kujerar da Sakeena take ya ɗora mata Ayman a laps, ta juya ta kallesa tace "Au bazaka riƙemin shi ba, yanzu daga hidimarka na dawo kuma nagaji", yace "zan je Hospital ne akwai wani urgent patient da zan duba ne", tace "in this Noon?", yace "yeah, naso ma na makara fa na tsaya naga dawowarku ne", tace "Ohk saika dawo saika mayar dani gida banzo da Mota ba", yace "Ohk". ★Alhmdll acikin wannan taƙin result ɗin Hajar na NECO ya fito kuma taci sosai, Nura ne ya amshi takardun ya shiga fafutukar nema mata school of Nursing tinda shine burinta a karatu, Soyayya tsaftatacciyar mara algus Hajar da Nura suka yiwa junansu, a yanzu kam sun buɗe sabon shafi a soyayyarsu tinda sun samu lasisi mai kyau, Hajar na zaune a tsakar gida akan kujera tana buga game a sabuwar wayarta Android da Nura ya kawo mata shekaran jiya, Umma ta leƙo daga ɗaki tayi kiranta, tarar da ita tayi tana ƙoƙarin zura hijab tace "yanzu zaki tafi?", Umma tace "shirya mu tafi", Hajar tace "tom, amma Sabra fa idan ta dawo daga islamiyya", Umma tace "da wuri zamu dawo ai, wllh banyi niyyar zuwa dake ba amma ina tsoro na barki ke kaɗai a gidan nan ga Sa'adatu ma naga tazo", Hajar tace "Umma nifa na dena shiga sabgarsu, na miki alƙawari fa kuma Baba ma nayi masa", Umma tace "A'a shirya dai mu tafi, haƙurinki siƙewa yake". Hajar ta canza kayan jikinta na tsakar gida zuwa wata riga da skirt na atamfa Maroon da zanen manyan flowers pink wacca ta fito da hasken fatarta, mayafi mai ɗan girma pink ta yafa, Umma ta kalleta tace "sai kace zaki gidan biki, asibiti fa zamu", Hajar tace "Umma bafa kwalliya nayi ba, kaya kawai na canza, dan kuma zani asibiti sai nayi shiga hajaran majaran", Umma ta sake kallonta taga dai eh yanayin jikinta ne mai amsa. Hajar ta saka wayarta a handbag ɗin Umma ta ɗauki padlock a kan window, Huzaifa ne ya shigo wanda yazo hutun session daga FUD, cike da ladabi ya gaishe da Umma, Hajar tana gama rufe ɗaki da padlock ta gyara mayafinta ta gaishesa, Hajar da Umma suka wuce, Maama ta yaye labulen ɗakinta tace "uwarka ce ita kake gaisheta, nace Uwarka ce iyee, wllh kai da Nasiru da badan a gida na haifeku ba da na rantse na kuma rantsewa canje akaimin a asibiti", ya girgiza kai ya shiga ɗakinsu. Hajar da Umma suna isa Hospital suka bi dogon corridorn da zai kaisu ward A, Umma ta murɗa ƙofa ta shiga da sallama, masu jinyar patient dinda take gadon farko suka amsa mata, tayi musu ya me jiki kana ta fara duba gadon mara lafiyar da suka zo dubawa, Hajar da take biye da ita ta hango Anty Jamila daga can gefen gadon ƙarshe na ward din, Hajar tace "umma ga su can", bayan sun gaisa ne suka duba Wasila wacca take matsayin cousin ɗinsu Umma, Hajar dai gefe ta koma suka jone da Hafsa, Umma ta kalli Anty Jamila tace "waye a wajenta", Anty Jamila tace "Amina ce, tin ɗazu take sintiri zuwa wajen Nurse ɗinda tace ta ringa bibiyarta sbd likitan da zai dubata tin safe ake jiransa baizo ba", Umma ta kalli Wasila da take jin jiki tace "yanzu tin safe likitan baizo ba, wannan wane irin rashin tausayi ne, kai Allah ya gyara mana ƙasar mu", Anty Jamila tace "Ameen", Nurse Jidda ce ta shigo ta duba Wasila tace "ya ƙirjin har yanzu yana miki zafin", Wasila ta jinjina kai alamar eh, Nurse Jidda tace "Sorry, inshallah yanzu doctorn da zai dubaki zaizo" ta fita daga ward din, Hafsa ta kalli Hajar tace "wllh Nurse ɗin nan tanada kirki, a yadda Nurses suke zabga rashin mutunci ga patient ita dai banga tayi haka ba", Hajar tace "naji Anty ɗazu tana cewa wai likita baizo ya dubata tin safe ake jiransa?", Hafsa tace "eh muma wajen 1hour kenan da zuwan mu ana jiransa", Hajar ta taɓe baki tace "uhmm wannan rashin sanin darajar ɗan Adam ne...", wani ƙamshi wanda ba baƙonta bane ta shaƙa wanda ya katse sauran maganar bakinta daga fita, Nurse Jidda na leading dinsa har ya iso gaban gadon ya kalli Wasila with care, few minutes ya gama aikinsa, Hajar da ta gama fahimta shine likitan da ake jira tin safe ta juya idanunta akansa tana so ta tuno inda tasan wannan fuskar, coily hair dinsa da kuma ƙamshin da ta fuskanci nasa ne yasa kwanyarta ta amsa, a take ta ganesa a zuciyarta tace (no wonder, wllh an cuci doctors), kasa ɗauke idonta tayi daga kansa tana yamutsa fuska, Dr Uthman ya kalli Nurse Jidda yayi alama da hannu, tace "yess doctor". ya juya zai bar wajen sai kuma ya juyo ya kalli wajen da tin shigowarsa yaji kamar an zuba masa arwa, a take idanunsu suka sarƙe, ya ƙanƙance nasa, yayi wani slight smirk ya juya da tafiyarsa, Hajar taji cewa itama yanzu ne ya kamata ta rama abinda yace mata rannan, da sauri ta miƙe ta wurgawa Hafsa wayarta a cinya ta zura takalmi, Umma tace "ina zaki?", tana tafiya tace "yanzu zan dawo" ta fita daga ward din da sauri sbd karya ɓace mata, long corridorn ta tsaya tana kallo, ta kalli hagu taga bata hangosa ba, tana kallon right taga har ya kusan fita daga block din, ta daka tsaki tace "sauri sai kace lankarki" ta bisa da sauri-sauri gudu-gudu, ai kam har ya fita daga block ta cimmasa, railern stairs ta riƙe tace "ɗan dakata Doctor", the voice sound familiar and the name inkiyarsa ce a hospital, these two reason make him to turn around, kallon 1sec yayi mata ya zuba hannayensa a pocket ya juya zai cigaba da tafiyarsa tace "Fake doctor, i think the name fit you, wanda baisan darajan ɗan Adam ba bazai zama real doctor ba saidai Fake", tinda yake bai taɓa encounter da trouble maker irin wannan little girl din ba, kuma ko kaɗan baiji zafin maganar da ta gaya masa ba saima ya tsinci kansa da yin murmushin gefen baki sai kuma ya juya da nufin kallonta, amma tini har tayi nisa da barin wajen tana tafiyarta cikin nutsuwa. ★Biki bidiri bireɗeɗe, saura 1week cif aka fara gudanar da shagali, Ruqayyah dai ba tay wani event ba duk tace bata buƙata, Nurain kam ya sakar mata bakin aljihu duk abinda ta tambayesa sai yace gashi indai money ne, ranar juma'a ne ɗaurin aure, ranar Alhamis aka daki mother's Eve tare da kamun amarya, Ruqayyah ta fito daga toilet bayan tayi wanka ta wanke nude make-up din da aka mata ta mother's Eve, friends ɗinta su huɗu ne a ɗakin, Meema ce ta miƙo mata wayarta tace "it has been ringing for a while", Ruqayyah ta goge hannunta da yaji jan ƙunshi a jikin farin towel ɗin data ɗaura sannan ta karɓi wayar, wani kiran ne ya sake shigowa da ringing tone ɗinda tayi setting musamman sbd Nurain, murmushi tayi ta kara wayar a kunne, ajiyar zuciya taji ya sauke kana yace "ina kika shiga ne?", tayi wasa da kwayar idonta tace "ina kam zan shiga", yace "Ohk, sleep tight for today, tomorrow in my arms", ƙit ta kashe wayar ta harareta, ta dannata a silent sbd tasan definitely sai ya sake kira, kolacca mai sanyi ƙamshi ta ɗakko ta murza a jikinta sannan ta ɗela gado ta rufa da duvet, wayarta ta danna taga message from dearest, da sauri ta mayar masa da reply, few minutes saiga wani saƙon nan ya sake shigowa, ta mayar da reply, a haka dai sukay ta tura text message har basu san dare yayi sosai ba, text ɗinda ya shigo na ƙarshe hopping daga Nurain yake sai taga akasin haka. minti goma ta ɗauka tana karanta message din, a hankali ta tashi zaune ta kalli agogon wayarta, 3:00am passed, Meema da sauran friend ɗinta duk sun sheme. a hankali ta sakko daga kan gadon ta kunna fitilar wayarta sbd idan ta kunna ta ɗakin haske zai iya farkar da wani wanda a halin yanzu bata son kowa yasan abinda take shirin aikatawa sai zuwa gobe da safe tinda dole a sani. press din kayanta ta buɗe, gaba ɗaya kayanta masu kyau an riga an shirya mata su a box, waɗanda suka rage duk wanda bata buƙata ne na bayarwa, gashi box ɗin tana ɗakin Momy. sleeping gown din jikinta ta cire ta saka wata Abaya wacca ta Meema ce, cikin sanɗa ta fita a ɗakin ta wuce na Momy, a hankali ta murɗa handle ta shiga cikin sanɗa, ta haska fitilar wayarta ta buɗe box ɗin da kayanta suke, 5sets ta ɗiba ta zazzage jakar kayan Kulsum elder sister ɗinta ta zuba a ciki, ta ɗauki jakar ta fita, A palour ta ajiye jakar a kan kujera sai kuma ta juyo ta koma ɗakin Momy, bedside ta janyo a hankali ta ɗakko Jotter da biro tayi rubutu, ta yage papern ta soketa ajikin lamp sannan ta mayar da Jottern, Momy ta motsa tace "waye a nan?", Ruqayyah tayi tsam sai kuma tace "Momy nice, nazo neman paracetamol ne zan sha kaina ne yake ciwo", Momy ta fara ƙoƙarin miƙewa daman bata daɗe da kwanciya ba kuma tin shigowar Ruqayyah ta farko taji ɓuruntu, Ruqayyah tace "Momy ki koma ki kwanta na samu a jakar Kulsum" ta miƙe ta fita a ɗakin jikinta na rawa. ajiyar zuciya ta sauke ta ɗauki jakarta ta fita compound, iyakarta kenan domin daga nan bazata iya yin gaba ba sbd gate a garƙame yake, can bayan wani ƙaton drum da ake tara shara ta koma ta raɓe, she spent almost 2 and half hours there kafin abinda tayi fako ya wanzu, a kan idonta Daddy ya buɗe gate ya fita Masallaci Sallahr asuba, and she used that as an opportunity to fulfilled her mission...........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Nafeesah Yusuf Nagoda ~~(Feenerh_feeche)~~ {11...} ★Da misalin ƙarfe 7:40 na safe, Hajar ce zaune a gaban rariya tana rege waken kulele, a hankali take humming song tana aikinta, Naseer ne ya shigo hannunsa riƙe da damin doyar da ya siyo a Zaria, Hajar ta amsa sallamarsa tace "yaya sunnu da dawowa ya hanya?", yace "lafiya hajara" ya ƙarasa ciki, damin doyar ya ajiye a ƙofar ɗakin Baba kana ya shiga ciki, Naseer ya kalli Baba ganni yadda ya rame sosai, ya samu waje ya zauna suka gaisa, Baba yace "har kun juyo?", Naseer yace "Eh, sai gobe Inshallah zanyi lodin Lagos", Baba yace "to Allah ya taimaka", Naseer yace "ga doya nan na shigo da ita", Baba ya saka masa albarka tare da addu'ar Allah ya ruɓanya masa, Naseer yace "Ameen, bari na shiga na gaida Maama" ya miƙe ya fita daga ɗakin, a ƙofar ɗakin Maama ya tsaya yayi sallama, shiru yaji ba a amsa ba ya sake yin wata sallamar nanma dai shiru, ya ɗan yaye labule ya leƙa, Maama tana zaune ta miƙe ƙafa tana karkaɗata, Nabilah tana kwance a kan gado tana bacci kamar mushe don ko sallar asuba ba tay ba, Maimuna kuma tana shafa man bleeching a fuska ta dauɗe kunnuwanta da earpiece, ido huɗu Naseer sukay da Maama wacca take kallon ƙofar kuma tana jinsa tayi burus, takalminsa ya cire ya shigo ya samu waje ya zauna yace "Maama barka da safiya", ta kawar da kanta kamar bazata amsa ba tace "lafiya, ai da yake shi kaɗai ya haifeka dole ka fara zuwa wajensa", tin lokacin da ya shigo ta hangosa ta shatin labule, ya shafa kansa yace "ya gida Maama?", ta galla masa harara tace "saika tambayi gidan kaji ya yake, ni ka tambayeni wani gida, nice nan uwarka Nasiru, wato duk abinda ka shigo dashi saika nufi ɗakin mahaifinka ko, ni banida mutuncin da zaka fara zuwa wajena ko, kaida Huzaifa saidai nayi muku addu'ar Allah ya dawo muku da hankalinku da tunani, an riga an shanyemin ku wllh, ƴaƴana mata kam sai san barka ta ko'ina alheri nake samu dasu", shi dai ya sunkuyar da kai yace "ayi hakuri Maama", Maimuna kallo ɗaya tayi masa ta ɗauke kai ta cigaba da jin waƙarta tana sabgar gabanta, tashi yayi zai fita suka haɗa ido da Maimuna ta zumɓuri baki ta ɗauke kai, yana fita ta daka tsaki tace "masifa, jaraba ya dawo, Allah yasa dai yau zai koma", Maama ta kalleta tace "leƙa kiga akwai doya a tsakar gida", Maimuna ta leƙa ta dawo tace "Eh naga Baba yana rabawa", Maama ta miƙe ta gyara haɓar zaninta tace "rabawa kuma?" ta fita tsakar gida, Baba har ya gama kasafta doyar gida biyu dai-dai, ya ɗauki guda uku cikin kaso ɗaya ya ƙara a ɗaya, Maama dai ta bishi da kallo tana jiran taga abinda zai yi, ya dubi Maama ya nuna mata kason da yafi yawa yace "ɗauki wannan, Nasiru ne ya kawo mana", Maama ta harari kason doyar bata ce komai ba, Baba ya kira Umma ta fito daga ɗakinta itama ya nuna mata ƙaramin kason yace ta ɗauka Naseer ne ya kawo, Umma tace "toh mashallah, Allah yayi albarka an gode", Umma ta sunkuya ta fara ɗiban doyar, Maama ta daka wata tsawa tace "wllh ba a isa ba, idan na yadda kwarankwatsa dubu ta waɗo a kaina", Baba ya tsaya yana mata kallon mahaukaciya, Maama ta buga ƙafa har zaninta yana ƙoƙarin kuncewa ta nuna Umma tace "kaji matsiyaciya kwaɗayayyiya, yanzu ke baki ji kunyar ɗaukar doyar nan ba, ɗanki ne ya kawo ko ubanki, keda haihuwa ba tay miki rana ba shine zaki raɓo kice zakici arziƙina, wllh ki ajiye doyar nan tin kafin ranki yayi mugun ɓaci", Umma ta mayar da doyar da ta fara ɗiba ta ajiye ta juya zata koma ɗakinta, Baba ya dakatar da ita yace "Faɗima dawo ki ɗebi doyarki, ai ni Nasiru ya kawowa kuma inada iko akan wanda zan bawa", Maama ta rangaɗa Shewa tace "toh banda nan mal, iko ko?, to baka dashi anan, wllh wannan shegiyar da shegun ƴaƴanta bazasu ci doyar nan ba, haramiya ce a garesu", tana gama bambaminta ta kwalawa Maimuna kira, Maimuna bata ji ba sbd earpiece dake kunnenta, Maama ta leƙa ɗakin ta window ta ɗauki warin slipers ta jefa mata, Maimuna ta fizge earpiece ɗin kunnenta a hasale tace "wane ɗan iskan ne ya wurgomin takalmi", Maama tayi mata ɗaƙuwa tace "fito", kafin Maama ta ankara har Umma ta shiga da wata doyar ɗaki tinda Baba ya umarceta da ta ɗauka dole, Maama ta barƙa ashar tace "wllh saikin fito dasu" ta kalli Maimuna tace "shiga ɗakinta ki ɗakko min doyar da ɗana ya siyo, ni bazan shiga na ɗebo bala'i ba", Maimuna tace "chab kenan ni bala'in ya shafeni", Maama tace "tofe jikinki da addu'a ki shiga ki ɗakko min gumin ɗana", Baba ya nuna Maimuna da yatsa yace "karki kuskura ki shiga ɗakin nan", Maimuna tace "yo Baba kanafa gani Maama ce ta sakani" ta doshi ƙofar ɗakin, Hajar daman tana laɓe a jikin labule zuciyarta na tafasa, ai kam ta ɗauki doyar da Umma ta zube a bakin ƙofa, Maimuna tana kunno kai ta wurga mata ita a fuska, daman doyar guda huɗu ce kuma saida ta jefe Maimuna dasu tas a ƴan sakanni, Maimuna ta riƙe hancinta da doyar ƙarshe ta sauka akai tana jin kamar zai gutsire sbd azaba, Hajar tace "ga tsiyarku nan" ta banke ƙofa ta saka sakata, hannu biyu tasa ta rufe duka kunnuwanta tana bubbugasu sbd karma taji muryar Umma ko Baba. ★Da safiyar ranar ɗaurin aure, Meema friend ɗin Ruqayyah kuma cousin ɗinta ce ta fita palour neman amarya, gidansu Ruqayyah acike yake da ƴan uwa da abokan arziki, Kulsum ta hango akan kujera tana breakfast, Meema ta matsa kusa da ita tace "amm yaya ko kinga Ruqayyah", Kulsum ta ajiye mug ɗin hannunta a gefen kujera tace "A'a bata wajenku ne?, nima tin ɗazu nake nemanta ta ɗauki kayan da zata saka yanzu", Meema tace "Ohk, nima tinda na tashi ban ganta a room ɗin mu ba, to i thought tana wajen Momy ne", Kulsum tace "ping her on phone", Meema tace "switched off, tin ɗazu nake kira amma bari na sake kiran", Meema ta kunna wayarta dake hannunta tayi dialing numbern Ruqayyah ta saka a handsfree, switched off suka ji, Kulsum ta amshe wayar daga hannun Meema ta sake kira, same thing dai aka ce mata wato switched off, keenly Kulsum tace "where could she be?", ta miƙawa Meema mug ɗin hannunta da bata gama shan shayin ciki ba, direct ɗakin Momy ta wuce, ai kam dai tayi sa'a ba kowa a ɗakin sai Momy, kayanta tagani wargaje akan carpet a nannaɗe gefe ɗaya, ta kalli Momy tace "Momy wane ya fitomin da kaya daga cikin jaka??", Momy ta juya hannu tace "ni kam bansani ba, ai saida nace kisa a wardrobe", Kulsum ta fara mita ta tsugunna ta fara kwashe kayan sai kuma tace "to ina jakar kuma??", Momy tace "toh kodai ɓarawo ne ya shigo ɗakin nan, kinga yanzu ma naga box ɗin kayan Ruqayyah a buɗe", Kulsum tace "yawwa Ruqayyah ta gaya miki zata fita ne??", Momy ta buɗe wardrobe tace "A'a, me zai kaita fita yau", Kulsum tace "toh ina ta shiga, Meema ma tace bata wajensu", Momy ta dakata da abinda take cikin wardrobe ta juya tace "An kira wayarta", Kulsum tace "yess", Aisha ce ta shigo babbar ƴa agidan, ta wuce hanyar toilet tace "gwara nayi wankana da wuri kafin na shiga sabga, a matsayina na second mother", Kulsum tace "yaya ko kinga Ruqayyah", Aisha ta riƙe handle ɗin ƙofar toilet tace "A'a rabona da ita tin jiya wajen mother's Eve, me ya faru?", Kulsum tace "yo nemanta fa ake tazo ta shirya", Aisha tace "ko wajen make-up ta tafi?", Momy ta sauke ajiyar zuciya domin har hankalinta ya fara tashi, Kulsum tace "Eh kam haka ne, wajen make-up ta tafi, amma da wuri haka kuma bata gayawa kowa ba", Aisha tayi slight hiss tace "yaran yanzu rawar kaine dasu akan aure" ta shige toilet. Kulsum dai bataga jakar kayanta ba kawai ta saka kayan a press din Momy ta koma palour don ta ƙarasa shan shayinta, ta zauna a position ɗin data tashi ɗazu ta amshi shayin daga hannun Meema tace "toh ai Ruqayyahn wajen make-up ta tafi", Meema tace "wajen make-up, mai kwalliyar fa har gida zatazo tayi mata, kuma mafa kawai gyara mata fuska za tay da ɗauri ba wata kwalliya ta azo mugani za ay mata ba, kinsan Ruqayyah da maintaining natural beauty, aikam bari na kira makeup artist din". Meema ta takune gira bayan ta gama waya da mai kwalliya ta tabbatar mata Ruqayyah bata zo wajenta ba. secretly Meema da Kulsum suka fara neman Ruqayyah a gidan, ko ina saida suka duba kuma suka tambayi waɗanda suka dace, daga ƙarshe Kulsum ta koma ɗakin Momy, this time ƙannen Momy su biyu suna nan da ita kanta Momyn, Aisha kuma tana gefe tana rubbing lotion, Momy fuskar Kulsum kawai ta kalla tasan akwai damuwa don haka tace "mene ne??", Kulsum tace "Momy bafa a ga Ruqayyah ba?", Aisha ta dakata da shafa man da take tace "bata wajen make-up din", Kulsum tace "yess, mun duba ko ina a gidan nan, kuma mun tambayi waɗanda muke tunanin tana tare dasu amma bata nan, and her phone is switched off", hankalin kowa yayi kan Kulsum da ta gama magana, Momy ta zauna a kan bedside thinking of another thing, haj Safiyya tace "Kulsum ku nutsu dai ku dubata sosai, yo ina zata?", Kulsum tace "Aunt wllh bata nan, baki ga duban da mukai nida Meema ba", Momy tayi wani tunani tace "kun duba part din Daddy", Kulsum tace "nan ne kawai bamu shiga ba", Momy zata miƙe hook ɗin zip ɗin rigarta ya riƙo wani ɗan siririn plastic dake kewaye da bedside lamp, tana miƙewa lamp ɗin ta biyota, saura ƙiris ta faɗi, Momy ta mayar da ita sai kuma ta tsaya tana kallon papern data faɗi a kan tiles maimakon fitilar, bata san dalili ba amma tana kallon papern zuciyarta ta buga, ta sunkuya ta ɗauka a zatonta zata ga electricity bill da tayi misplacing jiya, saɓanin electricity bill sai taga rubutun ƴarta Ruqayyah wanda kalaman ciki suka sa ta koma ta zauna a kan bedside babu shiri, Sosai hankalin mutanen ɗakin yayo kanta, Aisha ce ta fara yo kanta tace "Momy lafiya" sai kuma ta zare takardar hannunta wacca ta lura itace ta jefata a wannan hali, Aisha ta zabga salati bayan ta gama karance takardar itama tace "jama'a Ruqayyah ta gudu". iya su da suke cikin ɗakin ne suka san abinda yake faruwa sai Meema wacca bata san cewa Ruqayyah gudawa tayi ba amma tasan ba a ganta ba. Kulsum ta sakawa ɗaki lock gudun kar wani ya shigo, bayan ƙura ta lafa na firgici da tsantsanin mamakin abinda Ruqayyah ta aikata ɗakin yayi tsit, Momy ta zabga uban tagumi tana kallon takardar, haj Safiyya tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un, ya kamata ki sanar da Daddy", Aisha tace "chab wannan wane irin abin kunya ne?", Momy ta sauke ajiyar zuciya, wato jiya da taga Ruqayyah da daddare wato ƙoƙarin guduwa take. ta ɗauki papern ta fita daga ɗakin, ƴan biki na gidan sai hada-hada suke wasu ma har sun fesa wanka sbd baifi saura awa ɗaya lokacin ɗaura aure yayi ba, haka Momy ta ringa ƙetaresu tana yaƙe harta wuce part ɗin Daddy, tin daga palour taji ƙamshin turarensa na tashi, Momy ta haɗiyi yawu tana son ƙwallon da ya tsaya mata a maƙoshi ya wuce, a hankali ta shiga bedroom ɗin Daddy da sallama, ta tarar dashi har ya shirya yana waya, ji tayi yace "Eh yau ne ɗaurin auren, ana idar da sallar Juma'a za a ɗaura Inshallah", ta koma gefen gado ta zauna tana jiran ya gama wayar, bai jima ba ya kammala ya juyo ya kalleta yace "me ya faru?" yana gyara hular kansa, bata basa amsa ba kawai ta miƙa masa takarda, karɓa yayi ya saka glasses a idonsa, ya buɗe takardar ya karanta yana ƙanƙance ido yace "meye wannan", Momy tace "Ruqayyah ce ta ajiye", ya cire hular kansa zanna bukar ya ajiye akan mirror, malum-malum ɗin jikinsa da ta sha ado na ɗinkin hannu da zare mai tsada itama ya cireta yayi hanging yace "Shikenan ta yiwa kanta". Daddy ya kira ƴan uwansa maza su huɗu ya sanar dasu abinda ake ciki kuma yace suje su sanar da dangin Ango. suma duk sun sha kwalliyar ɗaurin aure suka hau Mota suka nufi gidansu Ango. A Great room ɗin Abba aka saukesu, shima Abba he is ready duk da dai ya bawa ƙaninsa walicci. bayan sun gaisa babban cikinsu ya sanar da Abba komai, Abba ya sauke ajiyar zuciya bayan ya gama saurarensa yace "Allah ka shirya mana zuri'a", daga haka bai sake cewa komai ba. numbern Mami yayi dialing bayan sun tafi, after wayar tayi ringing sau huɗu Mami ta ɗauka, keenly Daddy yace mata yana bukatar ganinta yanzu a part ɗinsa, Mami ta shigo palour cikin wani dakakken lace ɗan ubansu wanda yasha stones da samfalwa mai rawa, fuskarta cike da walwala amma tana ganin fuskar Abba zuciyarta ta buga, kusa dashi ta zauna a kujera 2seater, yana kallon fuskarta sai yaga kamarta da Nurain ainun wanda zai samu karayar zuciya nanda wani lokaci mai ƙaratowa, Abba yace "Khadeeja", Mami tace "Na'am", ya ɗaga kansa ya kalli ceiling yana wasa da yatsun hannunsa yace "ki bawa Nurain haƙuri", ya gaya mata kaf abinda ƙannen Daddy suka gaya masa, tabbas Mami ta girgiza amma Nurain shi yafi tsaya mata a rai, ita uwace wacca tasan ciki da waje na ƴaƴanta, ta san ɗanta yana son Ruqayyah sosai ma kuwa, a hankali tace "shikenan, Allah ya basa wacca ta fita", Abba yana kallon ceiling yace "Ameen, kiyi azamar sanar dashi". Mami ta miƙe ta fita duk jikinta yayi sanyi, tana shiga main palour Noor da itama tasha lace irin nata tace "Mami na kai snacks ɗin ɗakinki, Anty Zulaiha kuma tana nemanki", Mami tace "Ohk, Nurain ya sakko?", Sakeena tace "No, ai duk nan shi muke jira ya sakko muga kwalliyar Ango". Mami ta kalli stairs ɗin da zai kaita ɗakin Nurain, a hankali ta fara hawa stairs ɗin harta kai ƙarshe, sau biyu tayi knocking ƙofar ɗakinsa ya buɗe, he is already dressed up, ta tsaya tana kallonsa da shigar da bata taɓa ganin yayi irinta ba, yayi kyau wanda bai taɓa irinsa ba, caramel skin ɗinsa tayi wani luf-luf, ga wani ƙamshi da yake tashi a jikinsa wanda bata taɓa jin irinsa a tare dashi ba, murmushin da yayi mata shima bata taɓa ganin irinsa ba, calmly tace "Son are you ready?", yace "almost", ta shiga ɗakin tace "i need to talk to you"..........✍️ (Aslm, ina mai bada haƙuri akan rashin samun update kullum da kuke yi, nasan dai kullum ya kamata ace ina muku posting amma bana yin hakan, plxx acigaba da amsar HAJAR a haka sbd ni Nafeesah marubuciyar I'm a student, school tana shan gabana shiyasa bana samun time da zanyi update, anyway inshallah idan na samu sarari zaku ga canji, tnx for your love to HAJAR 🥰 ). 💛 HAJAR💛 by Nafeesah Yusuf Nagoda ~~(Feenerh_feeche)~~ {12...} Nurain ya mayar da ƙofa ya rufe, Mami ta ruƙo hannunsa ta zaunar dashi a gefen bed kusa da gogaggiyar malum-malumsa da hula waɗanda yake shirin sakawa, da wani irin expressions yake kallonta, ta zaunar dashi sbd gudun kar ya faɗi idan yaji abinda zata faɗa duk da tasan shi mai tawakkali ne, a hankali tace "Uthman" tana shafa kansa, yace "na'am Mami na", tace "kasan duk wani abu da yake faruwa ko kuma zai faru nufi ne na Allah, kuma nasan cewa ka yadda da ƙaddara", ya lumshe idonsa yana jin yadda take shafa kansa kamar tana rarrashinsa, tinda yaji waɗannan kalaman yasan cewa something is odd, yace "Mami me kike so ki gayamin ne?", kusa dashi ta zauna kana ta fara magana a hankali tace "Ruqayyah yarinyar da zaka aura...", ta wassafa masa kaf abinda ya faru, wata irin aradu ce ta doka a zuciyarsa idonsa ya kaɗa yay jaa, ya kasa cewa komai sbd karayar zuci, ba ƙarya Ruqayyah broke his heart into million pieces, sama-sama yaji muryar Mami tana cewa "pray my Son, Addu'a itace maganin duk wata musiba, i know your in agony but plxx don't let it slaughter you", ya ɗago idanunsa da suke farare ƙal-ƙal amma a yanzu sun canja launi, ya buɗe baki kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru, ya miƙe da sauri ya zubar da links ɗin rigarsa da yake dunƙule a hannunsa, wayarsa da take kan mirror ya ɗauka, yayi dialing numbern Ruqayyah ya kara a kunne, bashi da shakku ko ɗigo akan maganar da Maminsa ta gaya masa, yana so ya tuhumi Ruqayyah ne ya tambayeta Why him?.., me yasa sai shi a duk faɗin mazan duniya zata yaudara?, me yasa ta zaɓi ta ragargaza masa zuciya?, wannan shine sakayyar da zata yiwa soyayyarsa agareta, All love dinda take nuna masa was it a pretence all those years, Mami tace "who are you calling?", ya sake dialing for the fifths times, Mami ta sake zaunar dashi a gefen gado tace "Uthman, plxx relax, ban sanka da haka ba", ya sauke ajiyar zuciya yace "Mami, I'm okay" sai ya dafe kansa, knocking door akay Noor ta shigo tace "Mami tin ɗazu Anty Zulaiha take jiranki", Mami tace "Ohk, muje", Noor ta kalli Nurain da ya dafe kansa sannan ta fita a ɗakin, Mami ta miƙe a hankali ta dubi Nurain sai kuma ta sunkuya ta kwashe links din da ya zubar ta ɗora akan mirror tabi bayan Noor, zuciyarsa tafasa take, akwai ciwo sosai ace wanda ka yarda dashi ya yaudareka, yaudarar ma me zafi irin wnn, wayarsa ce ta fara ringing, ko kallonta beyi ba at this time he don't want to talk to anybody, he don't want to see anybody, all what he want is an explanation from Ruqayyah, wayar ya fuzgo da niyyar dannata a jirgi wani kiran ya sake shigowa from Dr Marwan, ya haɗiyi wani abu yayi picking kana ya kara wayar a kunnensa, Dr Marwa yace "wai ina ka saka wayarka ne tin ɗazu nake kira baka picking, ka gama ne muzo mu ɗauke ka, everyone is there Ango kawai muke jira", Nurain yace "Marwan cancel everything", Marwa yace "Dr what do you mean", da kyar Nurain yace "yeah, plxx cancel the reception, ka bawa kowa haƙuri" ya katse kiran, ya janyo curtain ɗin wayar zai sakata a jirgi message ya shigo, saida ya saka wayar a jirgi sannan ya dawo ya fara karanta message din da ya shigo from Ruqayyah.. ( 😭 Sorry dearest, i want you to know that i madly love and i will be back to be with you, plxx wait for me.), yana gama karantawa yaji soyayyar Ruqayyah tana juyewa zuwa ƙiyayya, yayi wurgi da wayar ta daki bango sannan ta faɗi ƙasa ta tawarwatse. wnn text din babu abinda yayi masa saima ƙara masa raɗaɗi a zuciya, shi Ruqayyah zata yayyankawa zuciya da wuƙa mai kaifi kuma ta dawo ta bayan fage tana barbaɗa mata gishiri, dama bata turo masa wnn text ɗin ba da maybe some percent na son da yake mata zai ragu koda 3 ne, amma yanzu zero, zeron ma behind decimal point, ƙarƙat an yiwa mai dami ɗaya sata soyayyar Ruqayyah ta faɗi a ƙasa warwas, babu abinda yake ji sai tsanarta. Ruqayyah ta rushe da kuka bayan ta gama tura text message din, ta rungume wayar a ƙirjinta tana kuka sosai, few mutanen da suke kusa da ita a waiting chairs suka dubeta, saida taci kukanta ta more ta ciro barimar kunnenta, ta buɗe wajen sim card ta zare sims dinta ta zubasu a jaka, wayar ma ta wurgata a jaka, a lokacin aka fara announcing jirginsu zai loading, ta miƙe tabi queue akay checking dinta sannan ta shiga Flight, ta zauna a seat dake kusa da window ta jinginar da kanta ta lumshe ido, wata mata da take gefenta ce ta taɓota jin anata cewa kowa ya saka belt dinsa jirgi zai tashi amma bata motsa ba, Ruqayyah ta buɗe idonta da sukay jajur ta kalli matar, matar tayi mata murmushi tace "tight your belt lady", Ruqayyah tace "thank you" da dasasshiyar muryarta, ta janyo belt ɗin ta ɗaura, Jirginsu ya sharara gudu akan runway kana ya ɗaga zuwa sararin samaniya. ★Da wani irin expression Anty Zulaiha ta kalli Mami jin abinda ta gama faɗa tace "innalillahi wa'inna ilayhirraji'un, yanzu yarinyar da Nurain zai aura ce ta gudu", Mami tayi ajiyar zuciya tace "wai neman me kike min ne tin ɗazu", Anty Zulaiha tace "ai magana ma ta wuce, yanzu where is my Son", Mami tace "yana ɗakinsa, Allah yasa ma bai fita ba, he will be okay", Sakeena ta shigo tare da Noor, Noor ta kalli Mami tace "wai me yake damun yaya ne, kamar naga bashi da lfy lokacin da nazo kiranki", Mami ta kalli Sakeena tace "ina abincin Abba da nace ki ajiye", Sakeena tace "yana nan", Mami tace "toh ki kai masa yanzu", Sakeena tace "ai sun tafi wajen ɗaurin Aure", Mami tace "ai ba wani ɗaurin Aure da za ai an fasa" ta miƙe ta fita, Sakeena da Noor suka bi bayanta da kallo domin suna buƙatar concrete explanation ne akan maganarta, tana fita sai suka juya a tare suka kalli Anty Zulaiha da ta wayance da buɗe foil papern da aka rufe peppered chicken da ita, Na reception din Nurain ne wanda za a ƙara akan wanda akay order, Sakeena tace "Anty nifa bangane me Mami take nufi ba", Anty Zulaiha tace "Eh an fasa auren", Noor tace "but why?", Anty Zulaiha ta gaya musu komai. Sakeena taji zafi sosai, her only brother wanda take jinsa tamkar shaƙiƙinta, ita har mantawa take ba mahaifiyarsu ɗaya ba, indai Nurain zai kaiwa Ruqayyah wata kyauta kamar Ramadan basket da sallah gift ko kuma dai wani abin haka itace take shirya masa, ko jiya da ta ganshi da daddare a balcony yana waya da Ruqayyah saida ta tsokanesa, duk irin crush dinsa da ƴan mata suke amma ita ɗin dai yake so kuma bai haɗata da ko wace mace ba yana dating, shin her brother yayi deserving irin wnn yaudarar daga Ruqayyah. Biki dai ya mutu ƙurmus, ƴan biki da ɓaki kowa ya ɗaɗe gida ya koma sai ƴar cikinsa daga Anty Zulaiha sai Sakeena ne suka rage, Nurain all this while yana room ɗinsa bai sakko ba kuma Anty Zulaiha ta hana kowa yaje gunsa tace abarsa zuciyarsa ta huta, sai dare da misalin ƙarfe goma sannan Sakeena ta zuba abinci da drinks ta ɗora akan tray zata kai masa, Noor da Khausar ce kawai a main palour, Sakeena tazo zata wuce da abincin Noor tace "amm yaya Nurain zaki kaiwa", Sakeena tace "Eh", Noor ta miƙe tace "wait a minute" ta shiga kitchen, few minutes ta jona coffee maker ta haɗa wani yummy coffee ta tsiyaye a Mug, ta fito da Mug ɗin mai ɗauke da coffeen ta ɗora akan trayn hannun Sakeena tace "idan ma bai ci abincin ba I'm very sure zai sha coffeen ko yaya ne", Sakeena tabi stairs zuwa room ɗinsa, a hankali tayi knocking sai kuma ta kara bakinta jikin ƙofar tace "brother nice" ta murɗa handle ɗin ƙofar, half expected ta jita a ƙulle amma sai taji ta a buɗe, ɗakin dulum dunɗum duk an kashe light, ta wawaki bango ta danna switch ɗin fitilu, a take haske ya mamaye ɗakin, yana kwance akan gado yayi rigingine, farar T-shirt da brown trouser ne ajikinsa ya cire na ɗaurin Auren da basu gama daidaita ajikinsa ba, ga nan wayarsa a tarwatse ko sake bin takanta beyi ba, Sakeena ta kallesa kana ta ajiye trayn akan rest chair tace "brother ga abinci na kawo maka, plxx eat", ya ɗago ya kalleta yace "thank you", tace "ga coffee ma Noory ta haɗa maka", kalmar coffeen da ta ambata tasa yaji wata suya a zuciyarsa yace "sister off the lights", bata ce komai ba ta kashe fitilar sannan ta fita a ɗakin. Bayan kwanaki Biyu Momy da haj Safiyya da kuma Kulsum da Aysha suka zo gidansu Nurain, tamkar babu wani abu da ya faru Mami ta saukesu, bayan sun zazzauna ne saiga Garba nan ya fara shigo da akwatuna, Mami ta kalli akwatin na lefen Nurain ne, Momy ita dai duk kunya ta dameta, saida Garba ya gama shigo da akwatuna sannan Momy ta shigar da abinda ya kawosu, takanas suka zo bada haƙuri akan abinda ƴarsu tayi, Momy ta kalli akwatunan da suke tuli guda kuma shaƙure da kaya tace "ga kayan yaron nan, akwai waɗanda aka ɗinka Inshallah suma za'a ciko su, dan Allah hajiya a bawa yaron nan haƙuri", Mami tayi murmushin yaƙe tace "ba komai ba sai an ciko ba, anga ita Ruqayyahn kuwa", Momy tace "da kanta ta fita kuma dan kanta zata dawo, babu wani nemanta da zamu tsaya yi", Mami tace "Aa ai baza ai haka ba, hannunka baya taɓa ruɓewa ka gutsire ka yar, ya kamata a nemeta ai macace", Haj Safiyya ta ciro bunch of keys ta miƙawa Mami tace "mukullin gida ne da yake gurinmu, ai ba kaya ma muka zuba aciki ba ɗan albarkar yaron nan ya zuba komai a gidansa", Mami ta karɓi keys ɗin tana jin daɗi ɗanta ya samu shaida mai kyau, kuma ta godewa Allah da bashi bane ya kawo tangarɗa, basu wani jima ba suka yi sallama suka wuce. ★Da dare bayan Sallahr isha'i Hajar ta gyara fuskarta da oil control powder ta shafa colourless lipgloss a lips ɗinta, ta zauna a gefen gado tana jiran isowar Nura sbd yau ranar zuwansa ce, babu jimawa sai ga kiransa nan ya shigo wayarta ta ɗauka tace gata nan fitowa amma kuma tana zaune daram babu niyyar tashi, saida ta kwashi minti biyar sannan ta miƙe ta sake kallon kanta a mirror tana murza lips dinta ta saka hijab, darduma ta ɗauka guda biyu sannan ta fito tsakar gida, Umma da take bakin murhun ta kalla tace "Umma na fita soro", Umma tace "tom saikin dawo", Hajar ta nufi hanyar soro, tin kafin ta kai soron taji ƙamshin turarensa, ta isa da sallama ba tare da ta dubesa ba ta fara shimfiɗa dardumar, ya karɓi ɗayar yace "bari na taya ki" ya shimfiɗa ɗan nesa kaɗan da ta ta, ya zauna ya tanƙwashe ƙafarsa, itama ta zauna tana wasa da ƙasan hijab dinta suka gaisa, yace "kin taho da takardun naki kuwa?", tace "A'a zan shiga na ɗakko maka idan zaka wuce", ya ɗauki wayarsa da yake haska musu fitilarta, gallery ya shiga ya buɗo wani uncompleted building, ya haska mata screen ɗin wayar yace "kinga abinda ya wahalar miki dani", ta kalli hoton tace "har an zuba dakin?", yace "eh Allah ya bada iko" sai kuma yayi gaba ya buɗo wani hoton shi kuma na windows ne sliding da door irin na gida da ake ƙerasu da inganci, yace "kinga suma waɗan nan na gama da babinsu", ya sake buɗo wani hoton na kayan bathroom masu kyau har set biyu yace "kinga 2 bedroom toilets suma na gama dasu", Hajar sai murmushi take suna tsara yadda gidansu zai kasance tare da tanadi mai kyau na futuren su. da wata iriyar tafiya irinta mata ƴan duniya Sa'adatu ta shigo, har ta wucesu sai kuma ta dawo tana yamutsa fuska, Hajar da Nura ko ɗaga kansu su kalleta basuyi ba suka cigaba da kallonsu, Sa'adatu ta zuge handbag ɗinta ta ciro tsaleliyar wayarta da mabaruka ta siya mata, fitilar wayar mai haske ta kunna ta dallare su da ita tana jan dogon tsaki, Hajar ta ɗago kanta tana micincina ido sbd yadda hasken ya kashe mata ido, Sa'adatu ta hura kwai da chewing gum din bakinta sai kuma ta taunesa ya bada sautin ƙass, ta buga wani uban tsaki tace "ke ashe naki iskancin haka yake, wato ke ƴar iska shine kike kawo mana ƙattin banza har cikin gida ko?", Hajar ta ɗauke kanta sbd bata so ta tankawa Sa'adatu a wnn lokacin, Sa'adatu kuma already tayi noticing dinta dan haka ta sake ɗaura ɗammarar ci mata fuska a gaban Nura, ta sake dallare fuskokinsu tace "dalla malam tashi ka fitar mana daga gida, ka bari ta biyoka shago mana, amma bazaku yi mana sheɗanci a soron gida ba", Hajar is burning inside kuma she can't take it anymore, ta miƙe tamkar wacca aka tsikarawa allura tana huci..........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Nafeesah Yusuf Nagoda ~~(Feenerh_feeche)~~ {13...} Sa'adatu ta dallare Hajar da ta miƙe da fitilar wayarta, Hajar tayi mata wani irin kallo sai kuma ta wuce cikin gida ta shiga ɗaki, umma tana ganin yanayinta saita bita ɗakin, Hajar ta buɗe wardrobe inda take ajiye muhimman takardunta tana dube-dube, umma ta kalleta tace "lafiyarki kuwa hajara?, Nuran ya tafi ne?", Hajar ta cigaba da ɗaɗɗaga takardu hawaye ya cika mata ido tace "umma wnn wane irin masifa da bala'i ne, Maama da ƴaƴanta wllh annobane, ni kam nagaji da haƙuri dasu, na rantse da girman Allah daga yau duk wacca ta sake shiga harkata saina raunata ta, anƙi ayi haƙurin dasu, idan zaman lfy toh za'a zauna lfy ɗin, idan kuma zaman tashin hankali toh za'a tashi hankalin fiye da kima.....", umma ta katseta tace "toh maza ki ɗauki harama tinda ke kika haifi kanki, yanzu me ya faru?, naga dai zaune kike a soro da Nura", Hajar ta ɗauki envelop ɗin credentials ɗinta ta zauna a gefen gado ta share hawayen da ya zubo mata tace "Sa'adatu ce", umma tace "me Sa'adatun tayi?", Hajar ta gaya mata abinda tayi musu a soro, Umma tace "shknn, dafatan dai biki tanka mata ba?", Hajar ta girgiza kai tace "bance mata komai ba kawai tasowa nayi na dawo gida, wllh nasan idan na zauna za'a iya haifar ɗa mara ido", umma ta zabga mata harara tace "wato har wani cewa kike za'a haifi ɗa mara ido ko?, Hajara ki ringa sanyaya zuciyarki, ki dena ɗaukar komai da zafi, yanzu waɗan nan takardun su kuma me sukay miki da kika birkito su", Hajar tace "shine yace na kai masa", Umma tace "A'a naga ai kin basa takardun naki kwanaki?", Hajar tace "Eh, ai na secondary na basa, yanzu kuma primary certificate da testimonial zan basa", umma tace "toh, tashi ki kai masa saiki dawo gida gobe kwa ƙarasa". Hajar ta miƙe ta fita da envelope a hannunta, kasa kallonsa tayi tace "ga takardun", ya miƙe ya amsa sai kuma ya nannaɗe dardumar da ya tashi daga kai ya naɗe ta Hajar ɗinma, Hajar dai na wasa da fingers ɗinta tace "dama ka barshi zanyi ai", yace "na hutar dake", ya miƙa mata darduman tare da wayarta da ta ajiye a wajen yace "toh seda safe", ta karɓa kanta a ƙasa tace "seda safe", ya tsaya yana kallonta yace "toh shiga gida", ta juya a hankali ta shiga gida shi kuma yayi tafiyarsa, Hajar ta tsaya daga bakin rariya ta kunna wayarta tana murmushin mugunta tace "idan kince bulus shegiya nake", ta shiga contact ta lalubo numbern Naseer tayi dialing, bata daɗe da fara ringing ba ya ɗaga, Hajar ta sauke ajiyar zuciya tace "Yaya ina wuni", daga ɗayan ɓangaren Naseer yace "lafiya lou Hajar", tace "yaya daman Sa'adatu ce tazo, gata can sai rashin kunya takewa Maama sbd tace karta sake barin gida..", Naseer ya katse kiran ba tare da ya ce komai ba, Hajar ta kalli screen ɗin wayar tayi murmushi, tasan yanzu haka gida zai taho, daman tasan yana neman Sa'adatu tinda duk zuwan da yake takan ji yana tambayar Nabila ko Maama ina take wani sa'in. ta wuce tsakar gida ta tsaya tana kallon ɗakin Maama da ake jiyo muryoyinsu daga ciki suna hira da shewa, muryar Sa'adatu tafi ta kowa tashi, Hajar ta yamutsa fuska tace "zaki ɗanɗana ne jaka" tayi wucewarta ɗaki. Nabilah ta juya tsaleliyar wayar hannunta tace "yanzu Sa'adatu wnn wayar ta mazajen kuɗi itace a hannunki", Sa'adatu tace "rass ma kuwa ya son ranki, masoyiya Mabruk ce ta siya min", Maama ta karɓi wayar daga hannun Nabilah tace "gaskiya yaran nan suna sonki da arziƙi, nawa ma kika ce kuɗin ta?", Sa'adatu tayi kwai da chewing gum ɗin bakinta tace "dubu ɗari biyar", Maama tace "caɓɗijam", Maimuna da take kan gado ta sakko tace "yawwa Sa'adatu kince zaki faɗamin sunan man da kika koma shafawa wanda yasa kika koma fara gaba ɗayanki", Sa'adatu ta harareta tace "wane irin mai, yarinya wasa ma kike, ni na dena shafa mai sbd ɓata lokaci ne, allura ake min", Maimuna tace "Allura..??", Sa'adatu tace "rass, har fatar kaina da mazaunai na sun koma farare yanzu", Maimuna tace "chab gaskiya bazan iya allura ba", Sa'adatu tace "yo shknn kiyi ta shafa mai yana miki glass a fuska, yanzu ma kalli fuskarki kamar an watsa fitsari duk tayi wani jirwaye, ga wani map of Africa a kumatunki", Maimuna tace "naji, a haka Alhaj ɗina yake so", Sa'adatu ta warce wayarta da take hannun Maama ta duba lokaci, ta ɗauki handbag ɗinta ta ciro maƙudan kuɗi ta lalo dubu ashirin ta miƙawa Maama tace "toh da haka da haka baƙo zaiyi halinsa", Maama ta soke kuɗin a kirjinta tace "Au ƴar nan tafiya zaki yi baza ki kwana ba", Sa'adatu ta miƙe tsaye tana kakkaɓe jikinta sai kace wacca ta zauna a sahara tace "la la la bazan kwana ba wllh, kuɗin cizo da sauro suyi min illah", Nabilah tace "Sa'adatu naga kin mayar da kuɗin jaka, ni kuma fa ba ki ɗusheni ba", Sa'adatu ta yamutsa fuska tace "ai kece kinƙi ki waye, yanzu Maimu ba gashi nan ba kullum da ƴan canjinta a ƙugu, miƙomin jakar", Nabilah gaba take da Sa'adatu amma haka ta ɗauki jaka ta miƙa mata da hannu biyu, dubu biyar Sa'adatu ta lalo ta mannawa Nabilah a ƙirji tace "gashi dai mai kai a tukunya", Nabilah ta dafe kuɗin ta linkesu ta cusa a bra. Sa'adatu tace "toh na tafi Maama", Maama tace "karki daɗe baki zo ba kinji", Sa'adatu tace "toh zan duba na gani" ta fito tsakar gida ta saka takalmi ta fita. A soro sukay kaciɓus da Naseer wanda ya shigo a fusace, zuciyarta ta buga da ƙarfi ta juya zata koma ciki, wani gigitaccen marii ya sauke mata a fuska, tayi taga-taga tamkar zata waɗi ta bugu da bango, tsaleliyar wayarta saura ƙiris ta faɗi daga hannunta, tana dawowa hayyacinta ta ruga cikin gida ya biyota da sauri, takalmin da yake ƙafarta mai tsini ya gurɗeta aikam tayi mummunar faduwa a ƙasa daɓas, wayar hannunta kamar wacca aka fuzge haka tayi tsalle ta daki bango, Sa'adatu ta ɗora hannu a ka ta kurma ihu tace "wayyo wayata", Baba ya fito daga ɗakinsa da sauri yace "Nasiru zane min ita, zaneta nace", Maama ta fito jin abinda yake faruwa tana hura hanci tace "wllh karka kuskura ka taɓa ta", Baba zuciyarsa na masa zafi yace "Rabi idan kika sake magana anan wajen na rantse da girman Allah saina tsinke jemammiyar igiyar aurenki guda ɗaya da ta rage", Maama ta dafe ƙirji ta zaro ido amma ta kasa cewa komai, Saki kuma da girmanta da gemunta ace za'a saketa, dama igiyoyin auren saura ɗaya ce ta rage, Baba yace "Nasiru ka zane min ita", Sa'adatu ta wawaki ƙasa zata miƙe ta afka ɗakin Maama amma ina tini Naseer ya fuzgota. wani mabirki mai kauri na icce wanda ake kaɗa miyar yauƙi dashi ya ɗauka, Naseer ya ringa rankwala mata shi a jiki, saida ya kakkafe mata tsoka tass, ƴan yatsenta kam kamar zasu zube sbd yafi rankwala mata anan, Maama dai kawai kumbura take tana sacewa ita kaɗai, saida Sa'adatu ta faɗawa ƴan garinsu sannan Baba yace "ya isa haka, kullemin ita a can" yayi nuni da kitchen wanda basa amfani dashi sai tara shirgi, gaba ɗaya kitchen ɗin ya mutu, Naseer ya figi Sa'adatu ya dannata aciki ya banko mushiyar ƙofar langa-langar, Baba ya numfasa yace "ka gaji ko kuma da sauran ƙarfinka?", Naseer baice komai ba, Baba ya ɗaga murya da kanaji kasan a ɓace ransa yake yace "Maimuna!!, Maimuna!!", wani irin juyawa ƴan hanjin Maimuna da take laɓe jikin labule sukay, daga ita har Nabila sai suka fara neman gurin ɓuya, Baba yace "Shiga ka zanemin ita itama", wayyo daman Naseer dukkansu yanada cikinsu, ai Maimuna a ɗaki akay mata nata walmukalafatun, itama tasha mabirki daidai gwargwado, Baba yace itama a haɗata da Sa'adatu a rufe, Nabilah ma ta amshi rabonta saidai bai kai nasu ba, ita akai aka rarrankwala mata mabirkin sannan ta amshi maruka biyu zafafa, zuciyar Maama ta soyu iya soyuwa, tanaji tana gani aka zane mata ƴaƴa, Baba ya bawa Naseer padlock yace ya kulle kitchen ɗin anan zasu kwana. Hajar da take jikin window tana hangen duk abinda yake wakana tayi murmushi zuciyarta fess, ai ita dukan da akay wa Sa'adatu da kuma yadda wayarta ta daki bango shi yafi mata daɗi, wayar da aka wulaƙanta ta da ita a soro gashi nan fashe. washe gari da safe Hajar ta fito tsakar gida da kayanta da zata wanke, ta deɓi ruwa a bucket ta zazzaga omo ta sunkuya ta fara wankinta tana humming song, a fakaici ta kalli ƙofar langa-langar kitchen da take a garƙame da kwaɗo, har yanzu Sa'adatu da Maimuna suna ciki sunyi bugun sunyi kukan har sun gaji, muryar Maimuna taji tana kuka tana cewa "dan girman Allah Baba kayi haƙuri wllh bazan sake ba, wayyo Maamana na shiga uku na lalace, wllh kunama ta harɓeni dan Allah a buɗe mu, Sa'adatu ta yanke da ƙarfen langa-langa", Hajar ta kyalkyale da dariya tana wankinta, Maama ta fito daga ɗakinta zuciyarta busu-busu ta shiga ɗakin Baba, Baba ya gama shiryawa tass zai fita aiki, Maama tace "mal fita za kay?, yaran nan fa har yanzu ba a buɗesu ba", Baba ya gyara wuyan rigarsa yace "sai aka yi yaya da ba a buɗesu ba?", tace "daman naga ko sallar asuba basu yi ba gashi rana ta fito", yace "Au daman kina damuwa idan basuyi sallah ba?", ta fara ƙinƙina tace "dan girman Allah mal kayi haƙuri, a yi musu afuwa", Baba ya gyaɗa kai yace "za a yi musu, amma in tambayeki mana?", tace "toh mal", yace "waye uban Sa'adatu da Maimuna?", ta saki baki sai kuma tace "kaine mana mal", yace "ni mijinki ne ko A'a?", tace "kai mijina ne mana", yace "idan kina so igiyar aurenki ta cigaba da rayuwa to ki gyara tarbiyyar ƴaƴanki, idan kina son ƴaƴanki to ki gyara tarbiyyarsu, kar Sa'adatu ta sake barin gidan nan, Maimuna karta sake fita da daddare, Nabilah ta fito da miji na aurar da ita", Maama ta gyaɗa kai tamkar tsohuwar ƙadangaruwa tace "tom", ya ciro muƙulli daga aljihunsa ya bata yace "ki buɗesu idan na dawo ina son ganinsu", Maama ta karɓi muƙullin tana harararsa ƙasa-ƙasa tace "toh" ta fita a ɗakin, ruɓaɓɓen kichen ɗin ta buɗe Sa'adatu da Maimuna suka fito wujiga-wujiga, zafi ya dakasa ga kuma jikinsu da yayi tsami. ★Nurain ya fita masallaci sallar la'asar, bayan ya dawo ya tsaya suna gaisawa da Garba da yake bawa flowers ruwa, Nurain yace "wace motar ka wanke min?", Garba yace "farar na wanke maka", Nurain yace "Ohk, ka amso min takalmana daga wajen polish", Garba ya dukar da kai yace "toh alhaji ƙarami", Nurain ya wuce ciki, har zai zauna a balcony sai ya fasa dai ya shiga main palour ya zauna a kujera, remote ya ɗauka ya canza channel, bayan few minutes ya miƙe ya shiga kitchen ya buɗe fridge ya ɗauki Apple guda uku ya ɗora akan plate ya dawo palour ya zauna yana ci, Noor ta shigo palourn tace "Yaya Mami is calling", yace "Ohk", ya miƙe ya ɗauki plate ɗin Apple ɗinsa ya shiga part ɗin Mami, Mami ta ringa kallonsa har ya zauna a kujerar kusa da ita, ya ɗan rame kaɗan amma kuma fuskarsa babu wata damuwa, Mami tace "where is your phone?", ya shafa kansa yace "Ta fashe ne", tace "Ohk, toh dan ta fashe shine ba za ai amfani da ita ba, saika zauna haka ba waya", yace "zan siyo wata ne", tace "good do that fast", yace "yeah" tace "when are you resuming work?", yace "next week, daman na ɗauki leave na two weeks", ta gyaɗa kai tace "Son, why not go towards Khausar", yace "Khausar?", tace "yess Khausar"..........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Nafeesah Yusuf Nagoda ~~(Feenerh_feeche)~~ {14...} Nurain ya ajiye Apple ɗin hannunsa yace "Mami i don't get you", Mami ta ɗauki remote ta danna mute tace "Nurain, ga Khausar nan ƴar uwarka, me zai hana ka nemi aurenta, kasan yarinyar nan kuma kasan iyayenta, duk wani qualities da ake so a wajen mace Khausar na dashi, asali, ilimi, home training and what majority of men are after to, beauty right?, she's beautiful..", Nurain ya sauke ajiyar zuciya yace "but Mami I don't have such feeling for her, i only see her as my lil sister", Mami tace "Alright, tinda kace haka shknn, you may leave", ta ɗauki remote ta canza channel snn ta buɗe volume, Nurain dai bai sake cewa komai ba yana nan zaune ya cigaba da cin Apple ɗinsa, bayan 20minutes ya miƙe yana jan shirt ɗinsa ya nufi door, har ya murɗa handle Mami ta kira sunansa, ya juyo yace "Na'am", ta nuna masa plate ɗin da ya shigo dashi, ga apple nan guda daya da bai cinyeba akai, ya shafa kansa ya dawo ya ɗauki plate ɗin ya fita, Mami ta bisa da kallon gefen ido. room ɗinsa ya wuce yayi abinda zai yi snn ya sakko down stairs hannunsa riƙe da car key, compound ya fita ya wuce parking space, farar motarsa ya buɗe ya shiga, saida yayi warming snn ya gangara ya fita daga compound ɗin bayan mai gadi ya buɗe masa gate, a daidai wani katafaren wajen siyar da waya yayi parking, ya kashe motar ya buɗe door ya fita, ya shiga building din da akay molding ɗinsa da kirar waya, few minutes ya fito hannunsa riƙe da ƴar leda, yana komawa gida aka kira sallar magrib, yayi using tap din compound yayi alwala ya wuce mosque, bayan ya dawo daga masallaci ya bude car ya ɗauki ledar ya wuce ciki, direct a room ɗinsa yayi branching, ya ɗauki wayarsa da ta tashi daga aiki akan mirror, sim cards dinsa ya cire snn ya farke sabuwar wayar da ya siyo, ajiyar zuciya ya sauke yana kallon wayar tana booting bayan ya danne switch dinta, bai ɗaukesa wani lokaci ba ya gama setting wayar, kira ne ya shigo wayar, Nurain yayi murmushi ganin me kiran nasa video call ya ɗauka, Farooq ne cousin dinsa da yake Russia, Nurain yace "why the call dude", daga ɗayen ɓangaren Farooq da ya sha wata jibgegiyar sweeter yace "I can't reach you since last week, what was the problem?", Nurain ya jingina da allon gado yace "look, wnn wintern ta garin ku ai bazata bari kayi reaching mutane ba", Farooq ya ɗaga gira yace "decline, look for another way", Nurain yace "Ohk", Farooq yace "ya Mutan Niger?, ya su Mami", Nurain yace "All lafiya", Farooq yace "looks like you lost some weight Dr, ko dai Ruqayyah bata iya girki ba, i forgot to asked about her, how is she?", Nurain yace "she is great", Farooq yace "good", Nurain yace "when are you coming?", Farooq yace "nanda 2weeks insha Allah, kuma a gidanka zan fara sauka naci girkin Amarya Ruqayyah", calmly Nurain yace "Ruqayyah is not my wife and she will never be, i don't think ma zaka tarar dani a Nigeria", yadda Nurain yayi maganar without joke yasa Farooq fahimtar something has happened, Farooq yace "bro what...", Nurain ya katsesa yace "don't ask me, zan gaya maka later, after my heart is healed", Farooq yace "Ohk, amma ina zaka da kace bazan sameka a Nigeria ba?", Nurain yace "India", Farooq yace "Ohk, ynxu ka yarda zaka koma ka ƙaro karatun kenen", Nurain yace "yeah", Farooq yace "Ohk, i understand, i gotta go, good night", Nurain yace "Ohk, good night" ya katse kiran yana sauke ajiyar zuciya. ★Da daddare Baba yana zaune a ɗakinsa Maama tayi sallama ta shigo, tana daga bakin ƙofa tace "mal kace kana son ganin yaran nan?, toh su shigo yanzu ko sai anjima?", Baba yace "ki kirasu yanzu nan, kema kizo", Maama tace "tom" ta juya ta fita, ɗakinta ta shiga tana kallon ƴaƴan nata tace "kuzo inji Babanku", Maimuna ta tashi daga kan kayan wanki tace "na shiga uku na, Maama dan girman Allah kice nayi bacci, wllh har yanzu harbin kunamar nan bai bar jikina ba", Maama tace "A'a dole ki taso, ko baccin ma ki kai tashinki zanyi", ta kalli Sa'adatu da Nabilah tace "kunji dai me nace ko?, ku taso", Sa'adatu ta miƙe tana gunguni ta fita tsakar gida, Maama tabi bayanta, ɗakin Baba suka shiga suka zauna, suna zama Nabilah ma ta shigo, Maimuna ce ta shigo a ƙarshe, tana ƙoƙarin zama Baba yace "karki zauna Shiga wajen Umma ki kiramin ita da kuma Hajara", Maimuna ta kalli Maama, Maama ta ɗauke kanta, haka Maimuna ta fita ta tsaya a ƙofar ɗakin Umma tace "Baba yace kizo keda Hajara", Maimuna ta koma ɗakin Baba ta zauna kusa da Nabilah tace "na kirasu", Maama ta haɗe rai tace "mal naji kace a kira waccar matar da ƴarta, to mene dalili?, mene haɗinsu da zamanka da ƴaƴanka?", Baba yace "Toh haka dai nace a kirasu", Maama bata sake cewa komai ba, Umma ce tayi sallama ta shigo Hajar biye da ita, suka haɗa ido da Maama wacca take harararta ƙasa-ƙasa, Umma ta zauna tace "mal gani", Hajar ta zauna kusa da Umma, Baba ya ƙare musu kallo duka yace "Nabilah!!", Nabilah tace "Na'am", Baba yace "acikin samarinki ki fitar da wanda yayi miki kice masa ya fito, aurar dake zanyi, idan kuma baki da wanda kike so toh zaɓi yana wajena, na baki nanda sati biyu..", Nabilah ta marairaice fuska tace "Baba aure fa..", ya katseta yace "Ba cewa nayi kiyi magana ba, tashi ki ban waje", Nabilah ta miƙe ta fita zuciyarta na zafi, Baba ya juya kan Sa'adatu yace "Sa'adatu!!, Sa'adatu!!, Sa'adatu!!", Sa'adatu ta haɗe gira tace "Na'am", Baba yace "sau nawa na kiraki?", tace "Uku", ya gyaɗa kai yace "gargaɗi na ƙarshe kenan da zan miki, zunubin ki mai kauri ne, wllh wllh wllh tsattsauran mataki zan ɗauka akanki, tashi ki bani waje", Sa'adatu ta miƙe ta fita zuciyarta na tafarfasa, Baba yana gamawa da Sa'adatu ya juya kan Maimuna yace "ke kuma duk abinda Sa'adatu tayi shi kike yi ko?, kin ƙi makaranta kin zaɓi yawon dare ko?, toh ranar Litinin Mu'azzam zai mayar dake makaranta, ɓacemin daga gani", Maimuna ta miƙe ta fita ranta na soyewa, wai makaranta za'a mayar da ita. Baba ya dubi Hajar da take zaune kusa da Umma yace "saura ke Hajara, uwar rashin haƙuri, Nabilah, Sa'adatu duk yayyenki ne, Maimuna ce sakuwarki kuma itama ɗin gaba take dake, karki sake yi musu rashin kunya", Hajar tace "toh Baba", yace "toh tashi ki tafi, Allah yayi miki albarka". Maama ta hura tukubar hancinta tace "suma Allah yayi musu Albarka su da ba ƴaƴan so ba", ɗakin ya rage daga Baba sai Maama sai kuma Umma, Baba yace "Rabii", Maama ta miƙe tace "Allah ya tashemu lfy, ba sai kace komai ba mal, ai naji abinda kace da safe" ta fice a ɗakin tamkar zata tashi sama. Rayuwar gidan ce ta canza zuwa wani fannin daban, babu ruwan kowa da kowa, yau sati guda kenan ba ai hargitsi ba, sosai Maama tayi ladaf ta hana ƴaƴanta fita, daman suma sun tsorata da Baba shiyasa ko ƙoƙarin fitar ma basuyi ba. Sa'adatu ta leƙa kwanon ɗumamen tuwon da Maimuna ta shigo musu dashi matsayin breakfast tace "chab wllh bazan ci tuwo ba", Maimuna tace "ga koko nan", Sa'adatu ta zabga tsaki ta ɗauki jakarta ta ciro kuɗi ta saka hijab ta fita tsakar gida, Maama da take riƙe da kofin koko tace "ina zaki Sa'adatu", Sa'adatu tace "ba nisa zanyi ba, wajen mai shayi zanje na siyo biredi da shayi, ni bazan ci tuwo ba", Maama ta zaro ido tace "kin san dai Babanku ya hanaki fita ko?", Sa'adatu tace "ai ba ko wace fitar yake nufi ba, nifa nan nan wajen mai shayi zani ba wata uwa duniyar ba", Maama ta girgiza kai tace "A'a, kawo kuɗin na leƙa waje idan na samu yaro sai ya siyo miki", Sa'adatu ta miƙawa Maama duba ɗayar data rage mata, Maama ta bata kofin hannunta tace "shigarmin dashi ciki, bari na aika yaron", Sa'adatu ta amshi kofin ta koma ɗaki, Maama tayi hanyar soro kamar da gaske, tana zuwa soro ta laɓe a bayan ƙofa ta ɗaure kuɗin a haɓar zaninta ta koma ciki, Sa'adatu tace "Maama har an samu yaron", Maama tace "Eh yanzu zai kawo miki, ɗan gidan Munkaila ne", Sa'adatu tace "yawwa, ga kokon ki". Maama ta zauna tana kurɓar kokonta tana kallon Maimuna da Nabilah da suke kwarfa lomar tuwo. Shiru-shiru yaro zai kawo Shayi da biredi amma maƙatau ba labari, yunwa sai kartar ƴar hanjin Sa'adatu take, Sa'adatu ta leƙa soro a karo na bakwai ta dawo ciki tana gunguni ta kalli Maama dake bakin murhu tace "har yanzu fa yaron bai kawo ba, yunwa nake ji", Maama ta tura mata kwanon tuwon data rage tace "ki rage hanya da wnn kafin ya dawo", Sa'adatu tace "tuwon ne fa bazan ci ba", Maama ta gyaɗa kai tace "yo ba yunwar kike ji ba, shknn saiki jira shayin". ƙarfe sha biyu da rabi Sa'adatu ta fito ta wafci kwanon tuwon da Maama ta bata ɗazu tace bazata ci ba, loma huɗu tayi masa ta tashi dashi, ta ringa suɗe hannu tana muzurai don ko tsarga mata beyi ba. ★Momy ta Shiga palourn Daddy hannunta riƙe da tray, sallama tayi, Daddy dake zaune kan kujera shallow in thoughts ya amsa mata, Momy ta ajiye trayn akan center table kana ta shiga making tea, thick tea ta haɗa cikin Mug ta dire a gaban Daddy, ta buɗe warmer da ta shigo da ita mai ɗauke da chips, plate ta ɗauka ta zuba chips ɗin with omelette egg a gefe, ta matsa ketchup a wani ƙaramin bowl, ta jera in front of Daddy kana ta koma kusa dashi ta zauna, a hankali ya fara cakar chips din da fork yana dangwalar ketchup yana ci, kaɗan yaci ya ajiye fork ya ɗauki tean ya fara sipping, keenly yace "have you eaten?", Momy tace "I'm not hungry", yace "Tom", calmly tace "Alhaji yarinyar nanfa bamu san inda take ba har yanzu, yaufa kwana sha biyu babu ita babu dalilinta..", yace "so", tace "do something", yace "something like what?", Momy was speechless kawai kallon Daddy take, ya ajiye Mug din hannunsa yace "lokacin da Ruqayyah ta saka ƙafa ta fita na sani ne?, ajikin lettern da ta ajiye ma tace kar mu nemeta zata dawo, to kinga kuwa me zai sa na ɓata golden time ɗina wajen nemanta..", Momy tayi ajiyar zuciya tace "har yanzu fa ba a samun wayarta, ai dole hankalina ya tashi", yace "toh maza ki ɗauki haramar saka damuwa a ranki, wai yarinya nan ba da kanta ta fita ba, dan ba a sameta a waya ba ai ba wata matsalar bace, tana sane ta kashe wayar, what Ruqayyah did really hurts me, idan tanada wata damuwar why not ta sameki ta gaya miki, and she can talk to me if there is any problem, am i not a free Father?, plxx don't ruin my mood this morning akan maganar Ruqayyah", da haka Daddy ya miƙe ya shiga bedroom ɗinsa, Momy tabi bayansa da kallo sai kuma ta tashi ta fita a palourn, bedroom ɗinta ta shiga ta ɗauki wayarta tayi dialing numbern Kulsoom, saida ta kusan yankewa snn Kulsoom tayi picking, Momy tace "saiki ringa nesa da wayarki", Kulsoom tace "Momy ina kitchen ne", Momy tace "toh kina jina Daddy yaƙi saurarata, anjima da yamma sai muje police station mu shigar da report", Kulsoom tace "toh Momy, har yanzu babu wanda ta kira", Momy tace "Eh", Kulsoom tace "toh ina gama abinda nake zan shirya na taho", Momy tace "toh shknn saikin zo" ta datse kiran. ★Hajar ce zaune a ɗakin Umma tare da Zainab, Zainab tace "kefa ƴar rainin hankali ce wllh, yanzu saida kika tattagoni, ƙiri ƙiri kin ƙi hawa online", Hajar tace "kuma inada data isasshiya wllh, duk sati ya sayyadina sai ya sakomin credit da data", Zainab ta taɓe baki tace "toh ai kin kyauta da kike masa asara, idan baki yi amfani da ita ba ai tayi expire a wofi", Hajar tace "ya mutan gida?", Zainab tace "lfy wllh, kin san kwa me ya kawoni", Hajar tace "inafa zan sani, ai sai kin shaƙamin", Zainab tayi ƙasa da murya tace "kin tuna wnn katafaren gidan da kika rakani?", Hajar tace "katafaren gida?", Zainab tace "Eh mna, wanda muka je har kika yiwa wani mai mota rashin kunya..", Hajar tace "Au, wnn mutumin da bai san darajar ɗan Adam ba, kinsan kwa na sake ganinsa?", Zainab tace "A ina?", Hajar tace "A hospital, likitane", Zainab tace "okay, yanzu dai kina jina?, ɗan gidan ne yace na bashi digits ɗinki, wllh ya takuramin, ni kuma naƙi bashi nace saina sanar dake..", Hajar tace "yawwa gwara da baki basa ba..", Zainab tace "sbd me?", Hajar tace "toh meya haɗana dashi da zaki bashi digits ɗina?", Zainab ta harareta tace "malama karki raina min hankali, kinfa gane me nake nufi", Hajar ta langwaɓar da kai calmly tace "So, kinsan dai akwai wanda muke tare dashi, kuma har yazo gida", Zainab tace "yess nasani, toh ai ba baiko akai muku ba", Hajar ta juyar da kanta tace "kya yi kuma". can dai Zainab ta miƙe tace "toh zan tafi", suka fito tare da Hajar zata rakata ƙofar gida, Zainab ta yiwa Umma sallama suka wuce hanyar soro tare da Hajar, Sa'adatu ta fito daga bayi ta tsaya tana kallon Hajar da Zainab da suka nufo hanyar fita, Sa'adatu ta dire butar hannunta, daman yau ranta a ɓace yake neman wanda zata huce akansa take, Zainab ta marairaice tace "dan Allah Hajar ki sauraresa, zan bashi numbern..", Hajar tace "zanyi tunani.", Hajar ko kallon inda Sa'adatu take ba tay ba, Zainab tana zuwa wucewa Sa'adatu ta saka mata ƙafa. Zainab ta faɗi a ƙasa, Sa'adatu ta nuna Hajar da yatsa tace "kema baki isa ki kawo ƙawayenki gidan nan ba su fita lfy", Hajar da zuciyarta take tafarfasa ta durƙusa ta kamo Zainab ta taimaka mata ta miƙe tsaye, Hajar ta tsugunna kamar zata ɗakko jakar zainab dake ƙasa, ta saka iya ƙarfinta ta kwashi ƙafafuwan Sa'adatu ta nakata da ƙasa, a lokacin Baba yayi sallama ya shigo gidan, ya tsaya yana kallon Hajar.......✍️ 💛 HAJAR 💛 by ~Feenerh_feeche~ {15....} Wani ihu Sa'adatu ta kurma tace "Hajar kashe ne za kiyi?, nifa ƴar uwarki ce", Hajar ta kasa cewa komai sbd kallon da Baba yake mata, Sa'adatu ta miƙe tana dafe bayanta, Baba baice komai ba ya wuce cikin gida, Umma ce tayo hanyar soro sbd ihun da ta jiyo, kaciɓus sukay da Baba tace "sannu da zuwa Malam", Baba yace "yawwa", ya wuce ƙofar ɗakinsa, ya ciro keys a aljihunsa, ya buɗe padlock ɗin ya shiga, Sa'adatu ta cafki wuyar Hajar tana ƙunduma mata ashar, Hajar tace "wllh badai nawa ba, dalla malama sakeni niba jaka bace da zan haɗa ƙashi dake", Sa'adatu tace "keee anƙi a sake kin, kiyi abinda za kiyi", zainab dai sai raba idanu take tana cewa Hajar kyaleta dan Allah, Umma tana zuwa ta tarar da Sa'adatu ta cakumi Hajar, Umma ta fara ƙoƙarin ɓanɓare hannun Sa'adatu dake wuyan Hajar tace "meya haɗaku?", Sa'adatu ta cakumo Umma sannan ta danna ihu da ƙarfi tace "Maama ku fito, gasu nan sunyi min rubdugu zasu hallakani", Nabilah ce ta fito tana wuwwurga idanu sai kuma ta riƙe baki tace "Maama fito ki gani", Maama tana fitowa ta ɗauki takalmin roba ta rufe Umma da duka, Nabilah da Maimuna kuma suka taru akan Hajar, Sa'adatu kam har lokacin tana riƙe da Umma gam, Hajar ta kufce daga riƙon da Maimuna tayi mata ta gantsawara Sa'adatu cizo a hannun, Sa'adatu ta saki Umma tana lailayo ashar, Zainab dai jikinta sai rawa yake tana kallon ikon Allah, Sabra ta shigo da ɗan gudunta jikinta sanye da Kayan islamiyya, gefe ta koma ta rushe da kuka, hayaniyar da taƙi tsayawa ce tasa Baba ya fito, tsaye yayi yana kallonsu zuciyarsa na tafarfasa, Maimuna da Nabilah suna ganinsa suka saki Hajar suna huci, Baba ya rumgume hannu yana kallon yadda Maama ke laftawa Umma takalmi, Maama tana ankara da Baba ta wurgar da takalmin tace "mal baka ga yadda muka fito muka tarar da faɗima da ƴarta sun rufarwa Sa'adatu ba", Umma ta juya ta tsinkawa Hajar marii, Hajar ta riƙe kuncinta ta fashe da kuka, Umma ta daka mata tsawa tace "wuce ɗaki", da sauri Hajar ta shiga ɗaki tana shessheƙa, Sabra tabi bayanta itama tana kukan, Zainab dai ta ɗauki jakarta ta fita daga gidan. Umma ta shiga ɗakinta zuciyarta na tafarfasa, har lokacin Hajar bata dena kuka ba, Umma bata ce mata uffan ba sai haushinta da take ji. kiran sallar magrib akai Hajar ta miƙe da lulu eyes ɗinta da sukay jajur, ta fita tsakar gida tayi alwala ta dawo tayi sallah, bayan ta idar da sallar ta jingina da jikin wardrobe, Umma na zaune kan darduna bayan ta idar da sallah, Mu'azzam yayi sallama ya shigo, ya durƙusa a gaban Umma yace "Umma ina yini", Umma tace "lafiya, an taso lafiya", yace "eh lafiya alhmdllh", tace "toh Allah ya temaka", yace "Ameen", Hajar da dasasshiyar muryarta tace "yaya sannu da dawowa", ya ringa kallonta snn yace "yawwa", ya ciro biscuits daga pocket ɗinsa ya bawa Sabra da take homework, Umma ta kallesa tace "idan ka fita Sallahr isha'i ka tahomin da Gana most go", yace "tohm, wane size?", Umma tace "medium", yace "tom" ya tashi ya fita. ƙarfe takwas da rabi Mu'azzam ya dawo da Gana most go a hannunsa, ya miƙawa Umma yace "wnn tayi?", Umma ta karɓa tace "Eh, ga abincinka", ya ɗauki medium warmern abincinsa ya fita, Umma ta ɗauki Gana most go ɗin ta wurgawa Hajar tace "haɗa kayanki", Hajar ta ringa kallonta bata dai ɗauki Gana most gon ba, a hasale Umma tace "ba kiji me nace miki ba?", Hajar ta janyo Gana most gon tace "Umma kayan me zan haɗa?", Umma tace "kayan sawarki zaki haɗa", a sanyaye Hajar tace "tom", ta tashi ta buɗe wardrobe side ɗin da kayanta yake, ta ringa ciro kayan tana ɗorawa akan gado, sai kuma ta dawo ta zuba su a Gana most go, tana gama zubawa ta zuge zip ɗin, Umma ta taso ta kalli wardrobe din tace "waɗan nan kuma fa?", Hajar ta kwaso su ta zuge zip ta zuba, Umma duk tana kallonta, Sabra tace "Umma ina Adda zata?", Umma tace "ba kin gama homewark ɗinki ba, maza hau gado ki kwanta, karna sake jin bakinki", Sabra ta haye gado bata sake magana ba. Hajar dai tayi ta sa ran kiran Baba amma har bacci ɓarawo ya ɗauketa bai kirata ba. ƙarfe bakwai na safe Hajar ta fita tsakar gida tayi brush, tana so ta shiga ta gaishe da Baba amma kuma shakkar hakan take, ɗaki ta koma taga Umma tana shafawa Sabra Vaseline, tana gama shafa mata ta saka uniform ɗinta, Umma tace "ki shiga ki gaishe da Baba kafin ki tafi makarantar", Sabra ta goya jakarta tace "tom" ta fita, sai kuma gata ta dawo tace "Baban bacci yake", Umma dai tayi mamaki sbd da wuya ne kaga Baba yana baccin safe, Umma tace "toh maza ki tafi karki makara". Sabra tayi tafiyarta makaranta, Hajar tace "Umma ina wake yake zan tsince", Umma tace "A'a ba tsintar wake za kiyi ba, zoki shirya fita za muyi", Hajar dai zuciyarta bata yarda da fitar nan ba, haka ta shirya a sanyaye, Umma ta zauna gefen gado bayan ta saka Hijab dinta tace "kiyi sauri kar ki ɓatamin lokaci", Umma ta ɗauki wayarta tayi kira, wayar kare a kunnenta tace "Jamila insha Allah gani nan zuwa gidanki", bayan few seconds Umma ta katse kiran tana kallon Hajar da ta taƙune fuska, Umma ta miƙe ta ɗauki ƴar purse ɗinta tace "wuce muje", Hajar tace "tom" ta wuce zata fita, Umma ta dakatar da ita tace "zo ki ɗauki kayanki da kika haɗa", Hajar ta kalli Umma ganin babu sauƙi a fuskarta ta fara jan Gana most go ɗin data fi ƙarfinta, Umma ta rufe ɗakin da padlock, ruwa ya cicciko idanun Hajar, Umma na ankare da ita tace "muje mana", Hajar ta goge hawayen da ya zubo mata tace "Umma ban gaisa da Baba ba", Umma tace "bacci yake, ko baki ji abinda Sabra ta faɗa ba, ki ɗauki kayanki ki wuce malama, kina ɓatamin lokaci", Hajar ta fara kuka a hankali tace "bazan iya ɗauka ba", Umma ta haɗe rai tace "ƙoƙarta ki kaisu soro", Hajar ta fara jan kayan a hankali, Nabilah da ta fito bayi ta bita da harara tana taɓe baki. bayan Hajar ta kai kayan soro Umma ta saka almajiri ya ɗauka ya fitar musu dasu bakin titi, Umma ta tari Napep, ta kalli Hajar tace "shiga", bayan me napep ya saka Gana most gon a boot Umma ma ta shiga, few minutes suka isa gidan Anty Jamila, Hajar ta ɗan ji relief ganin inda suka zo, Bayan sun shiga gidan, Hajar ta ajiye kayanta a ƙofar palour, Umma ta zauna akan kujera suna gaisawa da Anty Jamila, Hajar ta zauna kan carpet tace "Anty ina kwana", Anty Jamila tace "lafiya lou Hajar", Umma tace "yara sun tafi makaranta ko?", Anty tace "Eh suna makaranta", Umma tace "Jamila dan Allah wata alfarma nake nema a wajenki", Anty tace "tom Adda", Umma tace "dan Allah ina son Hajara ta zauna a wajenki na ɗan lokaci", Anty tace "Adda wnn ai ba damuwa bace ni me riƙe Hajara ce", Hajar dai duk tana jinsu, Anty ta kalli Hajar tace "tashi ki shigo da kayanki ki kai ɗakinsu Hafsa", Hajar ta miƙe a sanyaye wani kuka yana taho mata, yanzu anan Umma zata barta knn, tasan dai Anty bata da wata damuwa, amma ita tanada kwakwar Uwa, ko kaɗan bata so tayi nesa da Umma shiyasa ma babu inda take zuwa. Anty tabi Hajar da kallo, Umma tace "tashin hankali akai jiya a gidan, kuma Hajar ce a gaba gaba wajen assasa hakan", Anty tace "garin yaya?", Umma ta taɓe baki ta gaya ma Anty iya abinda ta sani, Anty tace "Subhanallah, gaskiya Adda haƙurin ki yayi yawa, shine kika tsaya kishiya ta ringa dukanki da takalmi", Umma tayi ajiyar zuciya tace "duk Hajara ce ta jawo, nayi nayi da ita ta dena shiga harkar yaran can amma taƙi ji", Anty tace "toh ai baki san me ya haɗasu ba da har ta biye mata, kika sani cutar da ita tazo yi ita kuma tayi ƙoƙarin kare kanta", Umma ta miƙe tace "da tayi haƙuri ai da yafi, ba zama zanyi ba, daman cewa nai bari na kawota da kaina", Anty ta raka Umma har ƙofar gida, Hajar na fitowa daga ɗakinsu Hafsa taga babu kowa a palour, ai kam ta fita waje da Sauri, har Umma ta tsare nepep tana shirin shiga, Hajar ta riƙe ƙarfen Napep ɗin tace "Umma dan girman Allah kiyi haƙuri..", Umma ta harɗe rai sai kace bata jin zafin rabuwa da ƴar tata tace "ai bakya son zama dani Hajara", Umma na faɗin haka ta shige napep ɗin, mai nepep ya burgi babur ɗinsa, Hajar ta rufe fuskarta da hijab tana kuka ta koma gida, Anty da take bakin gate ta bata hanya ta wuce snn ta rufe ƙofa. Anty dai bata ce mata komai ba, Hajar taci kukanta ta more snn tayi shiru, Anty ta fito daga ɗakinta tace "kinci abinci ma kuwa?", Hajar ta girgiza kai tace "na ƙoshi", Anty tace "shknn" ta shiga kitchen. Umma tana komawa gida ta leƙa ɗakin Baba, a kwance ta ganshi har lokacin, ta tsaya tana kallonsa na 5second snn ta juya, keys ta ciro daga ƴar purse ɗinta ta buɗe ɗakinta, Hijab kawai ta cire ta fito tsakar gida ta fara aikace-aikace, da Hajar tana nan da tuni ta gama, Umma ta dasa kujera a tsakar gida ta zauna tana tsince wake, Maama ta fito da ɗaurin ƙirji da doya guda ɗaya hannunta, zama tayi ta fara yanka doyar, tana yankawa taga doyar gaba ɗayanta ta ruɓe, ta ja wani dogon tsaki ta tashi ta shiga ɗaki ta ɗakko wata, itama dai tana yankawa ta ganta ta ruɓe, Maama tayi wurgi da wuƙar hannunta ta miƙe ta shiga ɗaki, Umma dai tabi ruɓaɓɓiyar doyar da ke zube anan tsakar gida da kallo ta girgiza kai, Umma tana ta kallon ɗakin Baba taga ya fito amma shiru, a hankali tace "A'a wai yau malam lfy yake wnn baccin", ta janyo latsinetarta ta duba lokaci taga har tara da rabi ta gota, miƙewa tayi ta shiga ɗakin Baba, tayi sallama yafi sau uku amma shiru, ta ƙarasa inda yake kwance, sai taga nunfashinsa ya canza, ta taɓa goshin taji kamar tasa akan wuta sbd zafi, ta ɗan jijjigasa tace "malam!!, malam!, malam".............✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {16...} Umma ganin Baba bai amsa ba, ga kuma yadda numfashinsa yake fita sama sama yasa ta fita tsakar gida da sauri, salati da sallallami ta zabga snn tace "Rabi ku fito malam ba lafiya", Maama tana ɗaki tana jinta amma tayi mursisi, ita baƙin cikin doyarta da ta ruɓe ne ya turnuƙeta, ƴaƴanta kam suna kwance suna baccin asara, Nabilah ce kawai tayi sallar asuba itama da rana gatsal-gatsal, Umma ta matsa bakin ƙofar ɗakin Maama tace "ku fito mu kai malam asibiti, bashi da lfy", Maama ta gyara ɗaurin ƙirjinta ta fito ta yiwa Umma kallon hadarin kaji tace "Malama lfy kike mana ihu sai kace daga dawanau", Umma dai a rikice take tace "malam nefa ba lafiya", Maama ta tafa hannaye tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un, kika ce kin kashe malam", sai kuma ta rushe da kuka, Umma da take a rikice saida tayi sak jin abinda Maama ta faɗa, Maama ta koma ɗaki cikin sauri ta shiga ɗalawa ƴaƴanta duka a cinya, faɗi take "ƴaƴan nan ku tashi, faɗima ta kashe muku uba", Nabilah da ita baccin nata beyi nauyi ba ta miƙe tana zabga hamma, Maama tace "tashi ƴan uwanki, faɗima ta kashe malam", Nabilah ta zaro ido ta dafe ƙirji tace "Baba". Umma dai tinda taga haukan da Maama take shirin ƙullawa bata sake bi takanta ba, wayarta ta ɗauka ta kira Mu'azzam, tana fara ringing ya ɗauka, Umma tace "Mu'azzam kana ina?", yace "ina wajen mai shayi", tace "taho gida yanzun nan", yace "Tom", Umma ta katse wayar ta ɗauki hijab ɗinta ta fita, Umma ta dawo tare da Munkaila makwabcinsu, Umma ta nuna ɗakin Baba tace "Bismillah". Munkaila ya shiga ɗakin Umma tabi bayansa. Maama da ƴaƴanta sun rufa akan Baba sai kuka suke, Nabilah tace "wllh ai na gansu da sassafe da wata ƙatuwar bakko zasu gudu", Maama ta fyace majina tace "Ta kashe min miji", Umma ta harɗe rai tace "kiga mutuwa akanki, ni ba ce miki nayi ya mutu ba, dan Allah ku fita kun cika masa kunne da haushi, karku ƙara masa zafin ciwo", Maama ta wangale baki tace "haushi fa kika ce faɗi", Umma ta bawa shara ajiyarta ta dubi Munkaila tace "dan Allah Munkaila temaka min mu fita dashi", Munkaila da Umma suka fito da Baba tsakar gida, a lokacin kuma Mu'azzam ya shigo, Umma tace masa ya taro napep, Ta uwa ta uba Maama ta ringa zage Umma tamkar zogale, Umma dai bata biye mata ba, da taimakon Munkaila aka fita da Baba aka sakasa a Napep ɗinda Mu'azzam ya taro, Munkaila da Mu'azzam ne riƙe da Baba, Umma ta tari wani Napep din tabi bayansu zuwa asibiti, da yake ranar Monday ne akwai doctors, Emergency aka wuce da Baba, doctor yana dubasa ya rubuta allurai da za a masa a takarda, Mu'azzam ya amshi takardar yaje ya siyo da ƴan kuɗin da suke aljihunsa, Saida Baba ya zama stable snn aka basa gado sbd kwantar dashi akai, blood pressure dinsa ne yayi mugun high gashi kuma akwai slight heart attack da ake zargin ya samu, Umma dai bata kira kowa daga dangin Baba ba sbd ba ƴan Kano bane, ainahin garinsu Baba Yola, Umma tana zaune gefen gadon Baba da yake bacci sbd alluran da akay masa Mu'azzam ya matso kusa da ita da takarda a hannunsa, a hankali yace "Umma kinga likita ya rubuta tests da drugs da kuma allurai, kuɗin hannuna bazasu isa ba", Umma tace "tom, ka kira Naseer ka gaya masa", Mu'azzam yace "bari na kira saina baki wayar kiyi masa magana", Umma ta gyaɗa kai, Mu'azzam ya ciro wayarsa daga aljihu ya kira Naseer, Naseer na ɗagawa Mu'azzam yace "Yaya ga Umma za kuyi magana", Umma ta karɓi wayar ta kara a kunne, Naseer yace "ina kwana Umma", Umma tace "lafiya lou, ya aiki?", Naseer yace "alhmdllh", Umma tace "toh Allah ya temaka, Baba ne aka kawosa asibiti ba lfy, toh kuɗin hannun mu sun yanke, gashi kuma ba a gama siyan drugs ba", Naseer yace "me yake damunsa", Umma tace "jininsa ne ya hau", Naseer yace "toh Allah ya basa lafiya, Inshallah gobe zan dawo, yanzu dai Mu'azzam ya turomin da account number ɗinsa saina turo muku kuɗi", Umma tace "toh shknn". Mu'azzam ya turowa Naseer account number ɗinsa, babu jimawa saiga alert ya shigo wayar Mu'azzam na kudin da Naseer ya turo. Munkaila ne ya shigo ward ɗin ya yiwa Umma sallama, Umma tayi masa godiya Sosai. ★Through out the day Hajar was so Moody, har saida su Hafsa suka dawo daga schl snn ta ɗan sake, Hafsa ta fige hijab ɗin jikinta na uniform tana kallon Hajar tace "yau sai ga ki a gidan nan", Hajar tace "Eh mna", Hafsa tace "kice ƴan ziyarar sun motsa ta kanmu", Hajar ta nasa mata harara tace "kya ji dashi, naga kema ba zumuncin kike ba", Hafsa tace "Tahfeez", Hajar tace "Tahfeez ɗin ce ta hanaki fita knn?", Hafsa tace "yesso, bari na cire uniform" da haka ta shiga ɗakinsu, Hafsa saida tayi wanka snn ta fito, Hajar ta ɗaga kai ta kalleta, Hafsa tace "ina Anty ne?", Hajar tace "tana ɗakinta", Hafsa tace "kinci abinci?", Hajar ta girgiza mata kai, Hafsa ta wuce hanyar kitchen tace "bari na zubo mana", Hafsa ta zubo musu abincin a plate ɗaya, ta kawo ta ajiye akan carpet ta koma kitchen ta ɗakko musu pure water da gaseous drink, Hafsa ta zauna ta janyo plate ɗin abincin ta saka spoon tace "toh sakko hajiya ta", Hajar ta zamo daga kan kujerar da take ta ɗauki spoon ta fara cin abincin, Anty ce ta fito daga corridorn ɗakinta, zama tayi a palourn tace "yanzu kinga damar cin abincin knn?", Hajar tace "daman Hafsa nake jira". suna gama cin abincin Hajar ta ɗauki plate ɗin ta kai kitchen ta dawo ta zauna tana shan drink. da yamma Anty ta shiga room ɗinsu Hafsa, Hafsa na latsa wayarta, Hajar kuma na durƙushe gaban Gana most go ɗin kayanta, Anty tace "Hafsa ki bata space a press ɗinku ta jera kayanta", Hafsa tace "tom, wai daman da gaske kwana za tay", Anty tace "kun shigo ɗaki kunyi gurgumi sai kace wasu ƴan matan Amarya, wa zai girka muku abincin dare", Hafsa tace "wai da sai daren sai muyi jollof spaghetti", Anty tace "A'a tuwo zaku yi, Hajar tayi tuwo ke kiyi dry okra soup", Hafsa tace "tom, semovita ko?", Anty tace "Eh" ta fita ɗakin. Hajar ce ta haɗa duka tayi, da tuwan da miyar duk ita tayi su, kuma kafin a kira Sallahr magrib ta gama, Hafsa aikin fito mata da ingredients da jajjage kawai tayi, bayan sun idar da sallahr magrib sukay zamansu a palour, Abdallah ne ya shigo palourn first born ɗin Anty, ya kalli Hafsa da take bawa Hajar lbri yace "an gama dinner", Hafsa tace "Eh", ya shiga kitchen, sai kuma ya fito empty hand, ya haɗe rai yace "wai tuwo aka dafa?", Hafsa tace "Eh", yayi slight hiss ya ɗauki remote ya canza channel daga American zuwa channel ɗin da ake ball, ya zauna kan kujera, Hafsa ta kallesa tace "ka turo min 2GB, yanzu na tashi na dafa maka indomie sharp sharp", yace "toh sleep thief, saidai 1GB", Hafsa tace "Eh naji, turo min naga dahir", ya ciro wayarsa ya tura mata Data 1GB, Hafsa ta kalli wayarta da ke hannun kujera tace "yawwa sun shigo, Hajar ina zuwa", Hafsa ta miƙe ta shiga kitchen da wayarta a hannu, Abdallah yace "Hajar ki koyamin yadda ake dafa abar nan mna, waccan muguwar taƙi koyan kullum sai taci kuɗina kafin ta dafamin", Hajar tayi murmushi tace "tom shknn, karka damu, kafin nabar gidan nan saika zama expert wajen dahuwar indomie", yace "yawwa, ina autar Umma". Hajar tace "Sabra, tana nan lfy". Anty ta fito daga ɗakinta itama ta zauna tana kallon TV tace "meye wnn?, Abdallah idan za kayi kallon Ball dinka ka ringa tafiya can ɗakinka, kazo nan ta cika mu da hayaniya", Abdallah yace "toh" sai kuma ya miƙe ya shiga kitchen, Hafsa ta jingina da cabinet sai latsa waya take, ga tukunya nan akan gas wacca take dafa indomien, Abdallah yace "ai daman na sani, kiyi sauri malama, kin tsaya danna waya, I'm hungry", tace "tafa dahu, yanzu zan kawo maka", ya miƙa mata plate yace "juye min haka", ta amshi plate ɗin ta kashe gas, ta plastic handle ɗin tukunyar ta juye masa, wayarta ta ɗauka ta fita, saida ya ɗauki drink a fridge snn ya fita da plate ɗinsa na indomie, room ɗinsa ya wuce direct. Humaira ce ta rugo da gudu ta miƙawa Anty wayar hannunta tace "Ana kira", Anty tayi saurin ɗagawa ganin wacca take kiran nata, Hajar ta ringa kallonta sbd ta fahimci da wa take waya, Anty tace "toh Allah ya basa lfy, ya sa kaffara ne" ta katse kiran tana kallon Hajar da ta kura mata na mujiya, washe gari da misalin ƙarfe 11 na safe Hajar ta fito wanka, ta shafa man da ta gani kan mirror snn ta saka doguwar rigar atamfa, tana fita palour ta ga Anty ta fito daga kitchen da basket mai ɗauke da warmers, daman tin ɗazu suka gaisa, Hajar tace "Anty me za ai?", Anty tace "ba komai Hajar, ki ɗakko gyalenki fita za muyi, za muje asibiti mu duba Baba", zuciyar Hajar ta buga da ƙarfi tace "Baban ne bashi da lfy, dan Allah Anty me yake damunsa?", Anty tace "yafa ji sauƙi, kawai dai jininsa ne ya hau, kuma yanzu ma sallamarsa za aii", Hajar ta sauke ajiyar zuciya ta shiga ɗaki, Gana most go ɗinta ta buɗe ta ɗakko ironed Hijab maroon, tare da wayarta da tin jiya da bata bi takanta ba, hijab ɗin ta zumbula ta fito palour ta zauna tana jiran Anty, babu jimawa saiga Antyn nan ta fito daga room ɗinta. Hajar ta miƙe da sauri, Anty ta kalleta tace "toh ɗauki abincin muje", Hajar ta ɗauki basket ɗin ta fita compound, saida Anty ta rufe ko ina snn ta fito, Anty ta rufe ƙofar gate bayan sun fito ta zuba keys ɗin a hand bag, Hajar dai ta ƙagu kafin ma Anty ta gama rufe gida harta tsare Napep. Anty ta gayawa mai Napep asibitin da zai kaisu snn ta shiga, Hajar ma ta shiga. hankalin Hajar bai kwanta ba saida taga sun iso asibitin, Anty ta kira Umma a waya tayi mata kwatancen ward ɗin da aka kwantar da Baba, Anty ce ta fara shiga ward ɗin snn Hajar dake biye da ita, gadon da yake kusa da ƙofa anan Baba yake, Umma Maama sai Nabilah ne a asibitin, Anty ko kallon direction dinda Maama take ba tayi ba ta matsa kusa da Umma da take bawa Baba Youghurt, Hajar ta ajiye basket ɗin hannunta ta isa kusa da Baba da yake jingine da allon gado, a sanyaye tace "Baba sannu, Allah ya baka lafiya", Baba ya gyaɗa mata kai yace "Ameen Hajara", Hajar ta kalli Umma tace "Umma ina kwana, ya me jiki?", keenly Umma tace "lfy, jiki da sauqi", Anty ma suka gaisa da Baba da kuma Umma, saida Anty ta zauna snn tace "sannu Rabii, ya me jiki", Maama ta taɓe baki ta juyar da kai tana girgiza ƙafa, Anty a zuciyarta tace kinyi da ƴar halak, Umma ta kalli Hajar tace "Hajara idan kika fita ɗakin nan saiki bi hannun hagu, idan kika bi hagu saiki tambayi Nurse station, saiki tambayi Nurse ɗin wajen ya baki takardar test ki kawomin, tin ɗazu yace aje a ƙarba sbd dashi za mu ga likita anjima", Hajar ta miƙe tace "tom", walking slowly ta fita daga ward ɗin. perfectly tabi kwatance da Umma tay mata ta isa Nurse station, Sallama ta yiwa Nurse ɗin dake zaune kan white plastic chair tace "nazo amsar test ne", yace "name?", Hajar tace "Adam Muhd Gini", Nurse ɗin yace "Okay" ya buɗe wata drawer ya ciro paper ya miƙa mata, Hajar ta amshi paper snn ta juya tabar wajen da papern riƙe a hannunta. ★ƙarfe tara da rabi Nurain ya fito daga room ɗinsa, car key da briefcase ne riƙe a hannunsa, down stairs ya sauka, Noor ya tarar a kan dining tana breakfast, ta yi shirin fita schl shine ta tsaya yin breakfast, Noor ta kallesa tace "good morning", yace "morning lil sis", tace "ga breakfast", yace "enjoy it alone, idan kin gama help me with a cup of coffee", tace "Tom", yace "zan shiga wajen Abba, make it kafin na dawo", ya ajiye briefcase ɗin hannunsa a kan kujera snn ya wuce part ɗin Abbansa, da sallama Nurain ya murɗa tsadadden handle ɗin ƙofar palourn kana ya shiga, Nurain yaji daɗin ganin Mami itama a palourn tare da Abba, kan carpet ya zauna ya gaishesu, Abba ya amsa yana nuna masa kujara yace "sit", Nurain ya koma kan kujera ya zauna yana shafa kansa, a zuciyarsa addu'a yake Allah yasa parent ɗinsa su yarda da maganar da yazo musu da ita yanzu, Abba yace "is there any problem Uthman?, Nurain yace "yeah, but it is not a problem", Abba yace "then?", Mami ta ringa kallon Nurain tana jiran taji abinda zai ce, Calmly Nurain ya fara magana yace "Akan maganar course ɗin da 1yr back nace zanyi a India sai kuma na canza decision, yanzu kuma am ready to take it if i get your approval", Abba yace "for how long?", Nurain yace "six to eight months", da wani expression Mami ta kalli Nurain sai kuma ta girgiza kai tace "No", Abba ya kalleta yace "why ?", Mami tace "sai ya bar aikinsa da business ɗinsa da ya fara kafasa yanzu ya tafi wani karatu, gaskiya nidae bada yawuna ba", Abba yace "wnn ma ai zaiyi boosting qualifications ɗinsa snn kuma he need a rest, kinsan da hakan ko?", Mami ta kalli Nurain tace "tom shknn Allah ya bada sa'a", Nurain yace "Ameen, nagode Mami", Abba yace "saika fara shirye-shirye", Nurain yace "yeah, idan komai ya tafi normal ina jin ma ranar Friday zan tafi", Mami tace "this Friday?", Nurain yace "yeah", Abba yace "Ohk, Allah ya bada sa'a", Nurain yace "Ameen, yanzu ma zan wuce hospital nayi signing". Abba ya gyaɗa kai, Nurain yayi musu sallama ya fita. Main palour ya koma, a lokacin Noor ta fito da Mug ɗin coffeen da ta haɗa masa, Noor tace "in time?" ta miƙa masa, Nurain ya karɓa yace "thank you" ya zauna kan kujera kusa da briefcase ɗinsa ya fara sipping, Noor ta rataya jakarta zata fita dan already driver na jiranta, Nurain yace "muga wayarki", Noor tayi sak sai kuma ta zuge bag ɗinta ta ɗakko wayarta ta miƙa masa, jujjuyata kawai yayi bai kunna ba ya mayar mata da kayarta. saida ya gama shan coffeen snn ya ɗauki car key da briefcase ɗinsa ya fita compound, parking space ya nufa ya buɗe motarsa, bayan yayi warming ya fita daga compound ɗin ya hau kwaltar street ɗin gidansu dake a mulmule, with a minimum speed ya isa Hospital, wajen da aka tanada dominsa na parking anan ya paka motarsa, ya kashe motar ya fito hannunsa riƙe da briefcase, Majestically yake tafiya har yaje office ɗinsa, secretaryn sa Halima ta miƙe cike da girmamawa tace "welcome Dr, good morning", yace "Morning" ya wuce katafaren office ɗinsa, ajiyar zuciya ya sauke yana ƙarewa Office ɗin kallo sai kuma ya buɗe briefcase ɗin da ya shigo da ita ya ɗakko wani file, da file ɗin a hannunsa ya fito, Haleema ta miƙe da sauri tace "Sir aike ne?", yace "No, continue what you're doing", ya fita. wani corridor yabi yana shan kwana sukay karo da juna, kanta ya bugu da ƙirjinsa ta shaƙi ƙamshisa, hannunta kuma mai riƙe da papern da ta kwarɓo wajen Nurse ya bige file ɗin hannunsa, a take takardun file ɗin suka baje a ƙasa, itama takardar hannunta ta faɗa cikin takardun, Hajar ta ɗago da nufi basa haƙuri amma suna yin ido huɗu saita murtuke fuska taja da baya..........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {17..} Da wani irin expression Nurain ya kalli Hajar da ta wani murtuke fuska, ya kalli file ɗin da papers ɗin ciki suka baje a ƙasa, Hajar ta yamutsa fuska sbd scent ɗinsa da ya gama bulale corridorn, ta tsugunna ta fara laluben papern ta, tana ɗaukar papern ta miƙe ta zagayesa zata wuce, yayi mata side look yace "rashin sanin darajar mutanen naki har ya kai haka, ki bige mutum kuma bazaki basa haƙuri ba", Hajar tayi jim sai kuma ta juyo ta kallesa da lulu eyes ɗinta, ta nunasa da papern hannunta tace "mu bawa juna haƙuri daii", ta juya ta cigaba da tafiya, taku uku tayi taji anyi sama da papern hannunta, kafin ta waigo Nurain har ya sunkuya ya fara packing papers ɗinsa, ya zubasu a file ɗin ya miƙe, Hajar ta haɗe gira tace "ka bani takarda ta", ko dubanta beyi ba yayi wucewarsa bayan ya saka papern tata a pocket, galala Hajar tabi bayansa da kallo kafin ta fara tafiya da sauri following him, zumbulelen hijab ɗinta har taɗeta yake, tana zuwa kusa dashi ta rage speed amma duk da hka sauri take following him tace "ka bani paper na", idan corridorn da suke bi yayi magana to tabbas Nurain ya tanka, he is just walking Majestically like nobody is following him, Hajar ta naɗe hijab ɗinta tayi blocking front ɗinsa tace "bani paper na", wani kallo da yayi mata and how huge he is in front of her yasa tayi gefe tana juya lulu eyes ɗinta, yayi gaba abunsa, Hajar ta tsaya tana daidaita heart racing ɗinta kafin brain ɗinta tayi booting on, yanzu fa result ɗin gwajin Baba ya tafi dashi, toh taya Baba zaiga Doctor babu test ɗin, juyowa tayi taga har ya ɓace mata, yama fita daga block ɗin, a guje ta kwasa ta fito daga block ɗin itama, ta ringa kalle-kalle da waige-waige a compound ɗin asibitin sai kace mara gaskiya, a fili tace "wai nida lantarki", wani worker ta gani yana watering flowers ta isa gabansa tace "Assalamu alaikum, Malam barka dai", ya ajiye watering can ɗin yace "wa'alaykissam, yawwa barka", Hajar duk a daburce take tace "dan Allah kaga wani mutum da ya fito yanzun nan?", yace "ai mutane da yawa ke shige da fice ta ƙofar nan, gaskiya bazan iya tantancesa ba, amma ko zaki fasalta minshi wataƙila na ganesa", Hajar ba ta da wani option than to describe him, wani ƙulluto ne ya tsaya mata a wuya, how can she describe him?, toh tace me?, workern ganin ba tace komai ba yace "ko baki sansa bane?", Hajar ta gyaɗa kai tace "Eh bansan sa ba, amma dogo ne, shi ba fari ba kuma ba baƙi ba", worker ya ƙanƙance ido yace "topa", Hajar tace "gashin kansa me nannaɗewa kuma yana sanye da ƙananan kaya" ta runtse idonta sai kace wacca ta faɗi wani mugun abu, yace "Au Dakta wai?", Hajar tayi wani tunani tace "Eh shi", ya nuna mata wani direction yace "nan yayi", Hajar ta kalli direction ɗin tace "nagode", ta nufi direction ɗin da sauri, tsayawa tayi tane ƙarewa wajen kallo, ga wani entrance nan yana facing ɗinta, direct ta shiga entrance ɗin, wani sanyin AC ya daki fuskarta, gashi wajen so quiet and calm, few mutanen wajen ta tambaya, kuma amsa ɗaya suka bata wai bai shigo ba, Hajar ta fito duk guiwa babu ƙwari, ta ringa kallon makeken compound ɗin asibitin da mutanen da suke ta hada-hada, daga ƙarshe dai da ta gaji da dubansa ga rana sai kashe mata ido take kawai ta nufi hanyar ward ɗin da Baba yake, babu abinda zuciyarta take sai tafarfasa, sai kace wacca kwai ya fashewa a ciki haka ta shiga ward ɗin, sukay ido huɗu da Umma dake zaune kan darduma tana cin abincin da suka zo dashi, daga ita sai Anty Jamila, Maama da Nabilah sun tafi daman ba wani daɗewa sukay ba. Hajar ta ƙarasa gefen gado ta zaune kusa da ƙafar Baba da yake bacci, Umma tace "da baki gane wajen ba ai sai ki dawo, ba kije kiyi ta bulayi ba", Anty tace "yana ganki duk wani iri ne?", Hajar tace "takardar ce fa ta ɓata", Umma ta ajiye spoon ɗin hannunta tace "kamar ya ta ɓata?", Hajar ta fara jan fingers ɗinta tace "dana karɓo takardar a wajen Nurse kamar yadda kika gayamin shine a hanyar dawowa na kasa ganewa, shine na fita waje, a wajen ne iska ta ɗauke takardar ta shiga cikin silap ɗin kwata", Umma ta taɓe baki ta ɗauki spoon ta cigaba da cin abincinta ba tace komai ba, Anty tace "amma shine baki dawo da wuri kin sanar ba", Umma ta ɗago ta kalli Hajar tace "ƙarya take yi, da ita dai za a duba mahaifinki, idan kin salwantar da ita ke kika sani", wani takaici ya sake balbale Hajar kamar ta fashe da kuka haka take ji, Anty tace "Hajar da gaske kike ?", Hajar ta gyaɗa kai da sauri, wata matron ce ta shigo ta sanar da kowa ya fita za a bayar da magani, Anty tace "toh Adda Allah ya basa lfy, ni dai idan na fita wucewa zanyi", Umma tace "toh Jamila nagode, ku gaida gida", Anty tace "saina bar miki Hajar anan ko sbd wani temakon", Umma tace "A'a karki barmin ita, nima bazan daɗe ba zan koma gida, Naseer da Mu'azzam suna zuwa zan tafi", Anty tace "toh shknn, sune suke kwana dashi?", Umma tace "Eh", Anty ta ɗauki handbag ɗinta ta miƙe tana kallon Hajar tace "tashi mu tafi", Hajar ta tashi tace "Umma sai gobe, Allah ya basa lfy", Umma bata dubeta ba tace "Ameen". da suka fita farfajiyar asibitin Hajar ba abinda take sai faman baza idanu, ko kallon gabanta ma bayi take sosai ba, wani me motorbike ne ya kusan bigeta, Anty ta janyota gefe tace "ki kalli gabanki mana, kalle-kallen me kike haka?", sai a sannan Hajar ta maida hankalinta ga tafiyar da take. suna komawa gida Hajar ta shiga kichen ta fara preparing lunch, jollof rice ta dafa wacca taji attaruhu, a hankali Hajar take yanka cabbage ɗin gabanta a kan chopping board bayan ta gama goga carrots, time to time saita ja dogon tsaki tace "lallai ma mutumin nan", ƙarfe ɗaya da minti hamsin ta gama abinda za tay ta wuce ɗakinsu Hafsa, ta shiga toilet tayo alwala ta fito, darduma ta shimfiɗa tayi sallar azahar, tana idarwa ta miƙe ta linke darduman ta ajiye gefe, wayarta ta ɗauka taga missed call da two messages from Nura, karantawa tayi tana murmushi kafin ta shiga tura masa reply, tana tura masa message ɗin babu jimawa sai gashi yana kira, taɓe baki tayi ta kara wayar a kunne bayan ta ɗaga, Calmly tace "Salamu alayyykumm", Nura yayi slight voice smile yace "wa'alay kumussalam babe", tayi shiru ba tace komai ba, Nura yace "ina kika saka wayarki tin jiya ina nemanki", Hajar ta turo baki kamar tana gabansa tace "toh aii banida chaji", yace "toh yanzu kam anyi chajin ko?", tace "Eh", yace "gobe zanzo, kinga jiya ban samu nazo ba, gashi yauma inada appointment", tace "tom", yayi ƙasa da murya yace "saina tambaya ko?", Hajar tace "me?", yace "me yake damunki?, ki faɗa min?", Hajar taji kamar ta fashe da kuka daman tin ɗazu take cijewa, ga Umma na fishi da ita har yanzu bata huce ba, ga Baba ba lafiya, ga kuma baƙin cikin abinda wnn mutumin yayi mata, sosai ya ƙona mata rai, ko mene nashi na tafiya da papern oho, a hankali tace "Baba ne bashi da lafiya, an kwantar dashi a asibiti...", sai kuma ta fara kuka a hankali, Nura yayi ajiyar zuciya yace "me yake damunsa", tace "BP ɗinsa ne yayi high", yace "ki dena kuka kinji, zai samu lafiya Insha Allah", Hajar ta goge hawayen da ya zubo mata tace "tom", Hajar ta ɗago idanunta da suka fara canza launi ta kalli ƙofa, Hafsa ce ta shigo wacca ta dawo daga schl, Hafsa ta ajiye schl bag ɗin ta tana kallon Hajar, Hajar da waya kare a kunnenta tace "kun dawo?", Hafsa tace "yess, naga ana tsinkar flowers ai", Hajar ta harareta ta kwanta a gado tana sauraron abinda Nura yake faɗa mata. Hafsa tace "Eh lallai" ta fara cire uniform ɗinta ta ɗaura towel ta shiga toilet. harta fito daga wanka Hajar na maƙale da waya, ta buɗe press ta ɗauki kayan da zata saka tana satar kallon Hajar, Hafsa ta zauna akan stool tana rubbing lotion a fatarta. Hajar ta ajiye wayarta tana sauke ajiyar zuciya, ta miƙe zaune tana kallon Hafsa tace "wai har kin fito wanka", Hafsa tace "Eh mana", Hajar tace "nida jiƙa-jiƙa", Hafsa ta cigaba da rubbing lotion tace "ai dole kice haka sbd lokaci ya miki ƙaranci na tsinkar flowers". Hajar tace "ke kika sani, ina Humaira?", Hafsa tace "tayi wajen Anty", Hajar ta gyaɗa kai ba tace komai ba. Hafsa ta ɗauki kayanta ta saka, ta kalli Gana most gon kayan Hajar tace "Au baki shirya kayan a wardrobe ɗin ba", Hajar tace "nida ba daɗewa zanyi ba", Hafsa tace "oho miki, Anty ce dai tace na baki space, don haka muci abinci saina temaka miki ki shirya kayan a press". ★Nurain bai baro hospital ba saida ya gama komai da ya dace, ya ajiye aikinsa na good 8months, yayi submitting komai da ya dace, Office ɗinsa ya koma after that, ya tsaya wajen secretary Haleema yace ta kira masa Dr Marwan, Khaleel da sauran team members ɗinsa, with due respect tace "okay sir", Nurain ya wuce cikin Office ɗin, A kan kujera ya zauna wasu moments suna dawo masa a brain, ya kalli kujerar da Ruqayyah take zama, ya ɗauke idonsa daga wajen cause he don't want to think about her, lumshe idonsa yayi yana juyi kan kujerar da yake kai, a bazata yaji zuciyarsa ta sarƙe da tunaninta, a hankali yace "stubborn girl, ashe dai tana tsoro", ya zura hannunsa a pocket ya ciro papern, ya ringa kallon papern da take folded, yanayin papern ne yasa yayi unfolding ɗinta a hankali, kasancewar result ɗin dake rubuce a papern is inside his field ya fahimci komai, ya mayar da papern yadda take bayan ya linketa. Khaleel ne ya fara shigowa ya zauna kan soft sofas da suke hakimce gefe guda a Office ɗin, Khaleel yace "Gani Boss", Nurain na kallon wani makaken picturen heart dake office ɗin yace "Ohk, bari su Marwan su ƙaraso", Khaleel yace "Neh", few minutes kam Office ɗin ya cika da well trained team members of thoracic surgeon Dr Uthman, Nurain ya ringa kallonsu kafin yace "zanyi tafiya na 8 months, so i have to tell you this sbd we work together, kamar yadda idan wani uzirin ya kamani nake barin Dr Marwan incharge, to this time around ma shine, follow by Khaleel, i wish you people all the best", a hankali suka fara daɗewa bayan sunyi masa sallama da fatan Allah ya bada abinda akaje nema, Dr Marwan ne ƙarshen fita, har ya miƙe zai fita Nurain yace "Dr wait", Marwan ya dawo ya zauna kujerar dake facing ta Nurain, Nurain ya ɗauki papern gabansa ya miƙa masa yace "plxx, ka duba wnn patient ɗin", Marwan ya karɓa ya buɗe ya karanta, yana gama karantawa ya rufe yace "it is a cardiac arrest?", Nurain ya gyaɗa kai yace "yeah", Marwan yace "toh yana ina?", Nurain yace "yana cikin hospital ɗin nan, plxx kasa a nemo maka shi", Marwan yace "sure" ya miƙe ya fita da papern a hannunsa. ƙarfe uku da ƴan mintina Nurain ya koma gida, direct room ɗinsa ya wuce, after taking his bath ya shirya cikin ƙananan kaya ya fito sallar la'asar, bayan ya dawo salla ya wuce wajen Mami, saida ya dangana da bedroom snn ya tarar da ita tana sallah, palour ya dawo ya zauna yana latsa wayarsa, sai after 20minutes Mami ta fito sanye da hijab ɗin da tayi sallah ta zauna kan kujera three seater, Mami tace "ka dawo?", Nurain ya ajiye wayar da yake latsawa yace "Eh, tin ɗazu ma na shigo", Mami tace "Ohk, kaci abinci?", Nurain yace "A'a yanzu nake jiran Noor ta shigo saita kawo min", Mami tace "Noor bata dawo schl ba, saidai Laure ta kawo maka", Nurain ya shafa kansa yace "No, bari Noor ɗin dai ta dawo", Mami ta taɓe baki tace "toh ai shknn", ta gama rafko jirginsa, ya raina tsaftar Laure. Nurain yace "Mami daga yau bazan sake zuwa Hospital ba har saina dawo daga tafiya, na gama komai da zanyi a can, insha Allah ina sa ran ranar Friday zan tafi", Mood ɗin Mami ya canza, ta ƙurawa TV ido ba tace komai ba, Nurain ya ringa kallonta........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {18..} After the silence of about 5mins Mami tace "kuma kai hakan shi yafi yi maka?", Nurain ya kalleta yaga har lokacin idonta na kan TV, ya shafa kansa ya kwantar da voice yace "yeah Mami hakan shi yafi min", tace "Ohk shknn, Allah ya bada sa'a", yace "Ameen". Mami ta tashi ta fita ɗakin, bata daɗe ba ta dawo da tray a hannunta, akan carpet ta ajiye ta koma position ɗinta ta zauna, ta kalli Nurain tace "saika sauka kaci abincin", ya kalli trayn snn ya ajiye wayarsa akan hannun kujera ya sauka kan carpet, wamers ɗin ya fara buɗewa snn ya ɗauki plate ya zuba abincin, yana fara cin abinci akay knocking door, Mami tace "shigo" cause tasan waye, Laure ce ta shigo hannunta riƙe da tray mai ɗauke da bottle water sai lemon kwali da cup, Mami ta nuna mata Centre table tace "ajiye anan", a hankali ta ajiye kana ta juya ta fita, a hankali Nurain yake cin abincinsa har ya gama, ya ɗauki bottle water ya tsiyaya a cup ya sha, Mami tace "karka yi tafiyar nan ba tare da kaje kunyi sallama da Hajiya ba", yace "insha Allah Mami, zanje muyi sallama". tace "yawwa", ya tashi ya ɗauki wayarsa yace "zan ɗan fita", tace "wajen Hajiyar zaka?", yace "No", tace "Okay, ka taho min da counter", yace "tom" snn ya wuce ƙofa ya murɗa handle ya fita, room ɗinsa ya wuce ya ɗakko muƙullin Mota, daga nan ya fita compound ya shiga motarsa, slowly yake driving listing to the qira'a of Sheikh Husary, A wani annakakken wajen siyar da wayoyi yayi parking, same wajen da ya siyi sabuwar wayar hannunsa, bayan ya shiga building din da akay molding dinsa da pattern ɗin cell phone, tsayawa yayi yana tunanin wace wayar zai siyawa Noor, taɓe baki yayi ya nufi ɓangaren iPhone cause yasan sune ake yayi, ko wace ƴan mata tafi son iPhone, Shi kam waya indai ba Samsung bace ba toh a barta, iPhone mai kyau da tsada ya siya full series, credit card ɗinsa ya miƙawa cashier ta cire kuɗin snn ta miƙa masa with due respect, yana gamawa ya fito ya shiga motarsa, A junction yaga mai counter ya siyi guda uku mai haɗe da agogo, lokacin da ya koma gida har Magrib tayi, saida yayi sallah snn ya shiga ciki, Noor ta amsa sallamarsa, tayi wani dafa'an tana kallon stuff dinta na Kdrama, tace "yaya ina yini", yace "lfy lou", zama yayi akan kujera duk da ba hakan yaso ba, with stern Voice yace "zo nan", ta matsa gabansa ta zauna daga ƙasan carpet, ledar da ya shigo da ita ya ajiye mata akan cinya yace "your birthday presence", Noor tayi murmushi snn ta buɗe ledar, ai tana ganin abinda yake ciki ta daka tsalle ta rungumesa tace "thank you so much, nagode Allah ya saka da alkhairy yayana", yace "you know the rules right?, kuma kinsan warning ɗin da nayi miki ko?", ta gyaɗa kai da sauri all her white tooth out, ya shiga part din Mami ya kai mata counter, ya fito ya haura room ɗinsa cause yana so ya gama duk wani shirye-shirye kafin nanda Wednesday. ★Hajar na zaune a palour tare da Hafsa da Humaira suna kallon wani film a MBC 2 mai suna IT, Humaira duk ta ruɗe sbd film ɗin akwai abin tsoro, Hajar kam kwata kwata mind ɗinta was somewhere else, ita bata ma san me akeyi a film ɗinba, time to time kuma saita ja long hiss, Hafsa ta kalleta tace "wai me ya faru ne tin ɗazu kike mana tsaki?", Hajar ta sake yin wani tsakin tace "uhmm bazaki gane yadda nake jin haushi ba ne", Hafsa ta taɓe baki tace "toh ki gayamin mana, me ya baki haushin?", Hajar tace "wllh wani ɗan rainin hankali ne ya haɗamin zafi ɗazu a asibiti", Hafsa ta tare hammar da ta yanko mata tace "ni kam bangane wane rainin hankalin kike magana akai ba?", Hajar tace "ai shiyasa nace bazaki gane ba", Hafsa tace "taya za kice bazan gane ba bayan baki yimin yadda zan gane ɗin ba", Hajar tace "forget it kawai, Allah ya kaimu gobe, ai zan koma asibitin, wllh sai ya bani takardar test ɗin Babana", Hafsa ta koma tayi resting a jikin kujera tace "uhmm, ke kika sani dai", Anty ce ta fito daga ƙofar part ɗin mijinta, ta ƙare musu kallo snn tace "la'ila ƙarfe nawa har yanzu baki kwanta ba Humaira?", Humaira ta turo baki tace "ai su yaya ne sunƙi zuwa mu kwanta, kuma ni tsoro nake ji", Anty ta zauna ta kalli Hafsa da take ta faman hamma tace "toh kuje ku kwanta mana, sai zabga hamma kike, gobe da schl kinsan da hakan aii", Hafsa tace "Hajar nake jira", Anty tace "Ina ruwanki da ita, ita ba schl take zuwa ba don haka anytime zata iya kwanciya abinta", Hafsa tace "toh saina gama kallon film ɗin nan", Humaira tace "Anty ni tsoro nake ji, kuma bacci zanyi", Hafsa ta nasa mata harara tace "keee, wuce ki kwanta, tin ɗazu nayi miki shimfiɗa", Humaira ta noƙe kafaɗa ta koma cinyar Anty ta kwanta, Anty ta kalli Hajar tace "An sallami Baba", Hajar tace "yaushe?", Anty tace "ɗazu", Hajar ta gyaɗa kai tace "toh yaga likitan?", Anty tace "Eh, Adda tace har daƙi likita yazo ya dubasa, kuma likitan ne yazo da takardar test ɗin", Hajar was speechless sbd mamaki, how comes?, a ina doctorn ya samu test ɗin?, ko dai result ɗin biyu ne?, ganin bata da amsar waɗan nan questions ɗin saita ɓige da jinjina kai, sai kuma tace "gobe da safe zasu tafi gida knn?", Anty tace "Eh". Washe gari da wuri Hajar ta gama gyara gida, ta shiga toilet tayi wanka, ta fito ta ɗauki mai ta shafa, wardrobe ta buɗe ta ɗakko kaya ta saka, Hafsa dai saida ta jere mata kayan nan a press snn ranta yayi sanyi, wani material ta saka mai kyau, Anty ce ma ta bata shi ita da Sabra waccan sallar da ta wuce. gaban mirror ta tsaya tana kallon gashin kanta mai cika, yaushe rabon da ta taɓa sa, gashi nan kam duk ya cukurkuɗe alamar ba a untangling ɗinsa frequently amma kuma babu datti, cause tana wankesa akai akai amma fa tajewa ne yake mata wahala sbd cikarsa, most of the time ma Umma ce take taje mata, roban hair oil ta buɗe ta zauna akan stool, she spent almost 30mins making her black silky hair tide, a ƙeya tayi parking ta ɗaure da ribbon, ta tufke jelar wacca ta saukar mata har midback. ta mayar da comb ɗin cikin drawer snn ta rufe roban hair oil ɗin, ta ɗaura dan kwali ta fita palour, kitchen ta shiga ta tsiyayi ruwan Lipton a cup, ta haɗa tea snn ta ɗauki 4slice of bread to koma ɗakinsu Hafsa. tana cikin ci wayarta ta fara ringing, sosai tayi mamakin wane yake kiranta at this time, cup ɗin tean ta ajiye ta miƙe ta ɗakko wayar, kallon screen ɗin wayar ta tsaya yi ganin bata son numbern dake kiranta ba, har kiran ya yanke wani ya sake shigowa, slim finger ɗinta ta kai tayi picking snn ta kara wayar a right ear ɗinta haɗe da yin sallama with her cool voice, ɓoyayyen ajiyar zuciya taji an sauke snn aka amsa mata sallamar, ta yamutsa fuska jin muryar namiji, ta ciro wayar daga kunnen dama ta mayar da ita na hagu tace "Ahmm bangane mai magana ba?", yace "Eh, am Ahmad, na samu numbern ki a wajen friend ɗinki", ta taɓe baki sbd ta fahimci shine wanda Zainab tace zata basa digit dinta, tace "okay, but how can I help you?", yace "i want to talk to you", tace "Sorry, ba sai kayi magana ba ma, ina fatan dai Zainab tayi maka bayani", yace "wane bayanin?", tace "akwai baiko a kaina", daga haka ta katse kiran ta cigaba da shan shayinta, tana ajiye wayar saiga wani kiran nan yana shigowa, saida tayi ringing twice kafin ta ɗauka, yace "why did you hanged up?", ta juya lulu eyes ɗinta tace "ina aiki ne", yace "Okay, a gama lfy, zan kira later plxx pick up", tace "tom" ta katse. ★Ƙarfe goma da rabi na safe Naseer da Mu'azzam da kuma Huzaifa wanda ya baro lectures ɗinsa ya dawo gida suka shigo gida tare da mahaifinsu, Baba duk ya faɗa ya rame sosai, Umma ta fito ɗakinta tana musu barka da dawowa, ta wuce ƙofar ɗakin Baba ta buɗe padlock, Huzaifa ya tallafi Baba ya shiga ɗakinsa, ɗakin a gyara yake fes fes sai ƙamshin turaren tsinke yake, Umma ce ta gyara sa da sassafe tinda a gida take kwana. Mu'azzam ya shigo da ledar drugs ɗin Baba ya ajiye gefe, Umma ta fita tana kallon ɗakin Maama ta shiga nata, flask ɗin da ta dama kunun gyaɗa ta ɗauka da cup ta fita, ta kalli Mu'azzam da yake ƙoƙarin fitowa daga ɗakin tace "zaka sha kunu na zuba maka?", ya gyaɗa kai yace "Eh zan sha", ta ƙarasa shiga ɗakin Baba, ta ajiye flask din gefe, Huzaifa ya jingina pillow a bayan Baba snn yace "sannu Baba, Allah ya baka lfy", Baba yace "Ameen, Allah yayi muku albarka", Huzaifa da Umma suka ce Ameen, Umma tace "Huzaifa ina Naseer?", yace "ya shiga ɗaki", tace "ga kunu idan zaku sha na zuba muku?", Huzaifa yace "tom". cup guda uku Umma ta cika da groundnut pap, Huzaifa ya ɗauki nasa dana Naseer ya shigar musu dashi ɗakinsu, Umma ta rufewa Mu'azzam nasa da ya shiga toilet, Baba ya kalli Umma yace "ina Hajara?", tace "tana nan", yace "kirowamin Rabi", Umma ta waro ido amma ba tace komai ba ta tashi ta fito tsakar gida, A ƙofar ɗakinsu Naseer ta tsaya ta kira Huzaifa, ya fito hannunsa riƙe da kofin kununsa da har ya kusa shanyewa yace "na'am", tace "ka kira Maamanku tazo inji Malam", yace "tom" ya shiga ɗaki ya ajiye kofin kunun snn ya fito ya wuce ɗakin Maama, Umma tana ganin ya shiga wajen Maama ta koma ɗakin Baba tace masa gata nan zuwa. Huzaifa ya ringa kallon Maama wacca take zaune dafa'an akan ƙullin kayan wanki, ya durƙusa yace "Maama barka da safiya", tana karkaɗa ƙafa tace "ba yawwa ba, tinda kwanten gaisuwa zaka jefeni da ita, wai har waccar mayyar matar ta fini daraja a idanunku kai da Nasiru, ƙiri ƙiri bakwa kallona a matsayin mahaifiyarku, ace miƙiyyata itace wacca zaku fifita, koda yake ba laifin ku bane tinda an zuba a kunu an baku kun tanɗe..", Huzaifa dai ya shafa kai yace "Baba yana kiranki", ta taɓe baki tace "toh me zan masa da yake kirani, ince dai ga mayyar matarsa nan a tare dashi koh", shiru Huzaifa yayi baice komai ba. Maimuna da take kan gado rashe rashe itada Nabilah ce ta miƙe zaune tana hamma, wani irin wage baki tayi babu addu'ar neman tsari ga shaiɗan bare ta kai ga rufe wawakeken bakinta, buɗe idonta tayi tana soshe soshe snn ta zabga tsaki tace "Allah ya isa wllh, Sauro da kuɗin cizo sun suburbuɗe ni yasin, shiyasa Sa'adatu ta tsani gidan nan wllh, nima dai daf nake da barin kangon nan alkur'an...", dakatawa tayi da tijarar tana micincina idanu ganin Huzaifa, ta sakko daga gadon tace "Laa yaya ina kwana", tsaki yayi ya miƙe ya fita a ɗakin. Maimuna ta taɓe baki tace "ni kam Maama sai naga kamar yaya Huzaifa yana juyewa kamar yaya Naseer", Maama tayi kwafa tace "uhmm shima ai an shanyesa, har kunu fa ake damawa a basa, kinga kam bayan shanyewa har damesa akai". Maimuna ta cigaba da soshe soshe kafin tace "ni kam Maama wai ina ragowar piya-piyan nan yake yau na fesa a katifa?, kuɗin cizon nan yayi yawa", Maama ta ɗauke kanta tace "ya ƙare, daman Sa'adatu ce mai siya kuma kinga tin shekaran jiya rabonta da gidan nan, itace mai zuciyar siyar piya piya ayi feshi, ke kam tsimilmila da maƙo bazasu barki kiyi abin arziƙi ba, koni nan uwarki ba morarki nake ba, ko kuɗin kika samo saidai ki cinye ke kaɗai sbd rowar masifa, nasan yanzu haka kinada uban kuɗi a ƙugunki amma bazaki iya fitar da ɗari biyar a siyi piya piyan ba kin gwammace kuɗin cizon suyi ta cizonki....", Maimuna tace "kaiiii Maama", Maama ta harareta tace "gafara can za wani kicemin kaiiii, aa ba kaii ba hannu ko ƙafa, sakarya kawai, ki kira Sa'adatu yanzun nan kice mata ta dawo gida an sallamo malam, jiya naga kunyi waya da ita kuma nasan ƴan albarkar ƙawayenta har sun mayar mata da tsaleliyar wayar da ta rasa", Maimuna ta ringa ƙunƙuni snn ta ɗauki wayarta a ƙarƙashin pillow ta shiga dokawa Sa'adatu kira, sau uku ta kira wayar na ta ringing amma ba a ɗauka ba, ta zabga tsaki tace "Maama kinga dai bata ɗauka ba ko?, ni dai ba ruwana idan yaya Naseer ya sake lakaɗa mata na jaki", Maama ta harareta tace "sake kira", Maimuna tace "bafa ɗauka za tayi ba don nasan bacci ma take yanxu" ta shiga kiran Sa'adatu for the fourth time. daf kiran zai tsinke aka ɗaga, Maimuna tace "ke Sa'adatu toh ki taho gida inji Maama an sallamo Baba daga asibiti kuma yaya Naseer yana nan..". ƙit aka kashe wayar bayan wani dogon tsaki, Maimuna ta kalli screen ɗin wayar ta mulmulo ashar tace "Alfarmar Annabi da Alkur'ani sai Yaya Naseer ya lakaɗa miki duka"......✍️ Alhmdllh I'm back by Allah's grace. May be Daily update insha Allah... 💛 HAJAR💛 by Feenerh_feeche {19..} Maama ta hangame baki tana kallon Maimuna tace "A'a kaji mun muguwar yarinya, ya zaki ringa mata mugun fata kina wani cewa Naseer ya lakaɗa mata duka iyee?, akan me kike mata wnn fatan sbd ƙeta?", Maimuna ta hade gira tace "toh daga temako shine zata wulaƙantani?, kawai saita yimin tsaki ta kashemin waya daga temako", Maama tace "sake kiramin ita ki bani wayar nida kaina nayi mata magana", Maimuna tace "ba dai da katin wayata ba wllh" ta miƙe ta saka wayar a wardrobe. Maama tayi ƙwafa ta miƙe ta fita a ɗakin ta shiga na Baba, sallama tayi ta ƙarasa shiga ciki, Baba da yake jingine da pillow ya amsa mata, ta kalli Umma da take zuba kunu a cup ta taɓe baki snn ta koma gefe ta zauna tace "ya kufan jikin mal?", Baba na kallonta da kyau yace "da sauƙi alhmdllh, ina Sa'adatu da Maimuna sune ban gani ba a asibiti", Maama ta dubi Umma tace "Baiwar Allah saiki tashi ki fita ko, zanyi magana da uban ƴaƴana", Umma ta cigaba da abinda take ko dubanta ba tay ba, Maama tace "Keee magana nake miki fa, ko kurma ce?", Umma ta rufe flask din kunun ta ɗauki wanda ta zuba a cup ta kai gaban Baba tace "gashi, bari naje na ɗora faten accar", Maama ta buɗe ƙananan idanunta tamkar an kwantali ɗata tace "kai jama'a ki fita nace kike reto sai kace mai maula", Umma ta ɗauki flask ɗin snn ta fita ɗakin, da wata muguwar harara Maama ta bita sai kuma ta kalli Baba tace "ka gani ko?, ina mata magana tayi banza dani sbd wulaƙanci", Baba ya ɗauki kofin kunun ya kurɓa snn yace "wllh duk ranar da keda ƴaƴanki kuka kasheni kin shiga uku Rabii", tace "na shiga uku a ina?, sai kace wata mara madogara", wani tari ne ya sarƙe sa ya nunata da yatsa yace "fita Rabii", ya cigaba ta tarin a hankali, ta taɓe baki tace "Sannu, mura ce ta kamaka kenan?". da kyar Baba ya samu tarin ya lafa masa, ya lumshe idonsa ƙirjinsa na suya, Maama ta miƙe tana gyara haɓar zaninta tace "to bari na baka guri ka huta mal, tinda daga magana sai tarii kar ace ni na tayar maka da ciwo" da haka ta fice a ɗakin. Naseer da ya fito a ɗakinsu ta kalla tace "biyoni" ta shiga ɗakinta, Naseer ya shafa kai snn yabi bayanta, ya zauna kan ruɓaɓɓiyar ledar ɗakin, Maama dake gafen gado zaune kusa da Nabilah da take baccin asara ta dubesa tace "wai me yake damun mal ne?", yace "hawan jininsa ne ya tashi snn kuma ya kamu da ciwon zuciya", Maama ta gwalo micimicin idanunta waje ta dafe ƙirji tace "ciwon zuciya mal ɗin, Nasiru me kake cewa ne?". Nabilah ta zaburo ƙasa ashe ba bacci take ba tace "Baban ne ciwon zuciya ta kamasa" ta figi hijab tayi waje da sauri, Naseer da zuciyarsa duk ba daɗi ya dubi mahaifiyar tasa yace "Abinda Baba yake buƙata addu'a snn kuma kar a ringa ɓata masa rai, duk wani abu dai da zai daki zuciyarsa toh zai iya tayar masa da cutar, kuma daman ga hawan jini, ya kamata a kiyaye Maama". kallonsa Maama ta ringa yi kafin tace "A'a Nasiru ai ba ni zaka gayawa a kiyaye ba, waɗancan gayyar shegun zaka gayawa sbd nayi imani da Allah sune suka saka masa ciwon zuciya, ba kaga duk sunfi damuwa ba sbd sunsan abinda suka aikata, tsoro suke ji kar ya mutu ta sanadinsu, tin ranar da shegiyar yarinyar nan da uwarta suka yiwa Sa'adatu ƴar albarka rubdugu toh shknn mal ya kwanta rashin lfy, to Allah dai ya kyauta ai zama da shegu ba kanta sbd tsinannu ne....", Naseer ya katseta da cewa "ni zan shirya na koma wajen aiki, zan ringa zuwa duk bayan kwana uku tinda lodin Lagos zuwa kano nake yi", Maama ta gyaɗa kai tace "toh shknn, amma kuma gidan bamu da komai, mai fita ya kawo ya kwanta rashin lfy, kasan ba abincin ne a jibge ba kullum sai an auno wanda za a sa a bakin salati, ruwan amfani ma sai mun siya", yace "ba komai insha Allah zan ringa yo aike, snn kuma ga wnn" ya karkace ya ciro kuɗi masu ɗan kauri ya miƙa mata. wuff ta amshe snn ta shiga ɓaɓɓaka masa albarka da godiya, ya shafa kansa yace "ba komai Maama" snn ya miƙe ya fita. yana fita Nabilah ta shigo, Maama ta fara ƙoƙarin ɓoye kuɗin a ƙirjinta amma sbd suna da kauri sai suka fito, Nabila ta taɓe baki tace "A'a Maama dama kin dena ɓoyewa ai na gani kuma nasan ya Naseer ne ya baki", ta cire hijab ɗin jikinta snn ta zauna a ƙasa tana fifita dashi tace "Baba na shiga na duba kuma naga jikin da sauƙi, nawa yayan namu ya bayar ne?", Maama ta ciro kuɗin ta ƙulle a haɓar zaninta tace "na gida ne, ina Maimuna tazo ta kira Sa'adatu a waya", Nabilah tace "wanka take", Maama tace "wanka?, amma dai ba fita za tayi ba ko?", Nabilah tace "can ta matse mata, ni bansani ba". Bayan minti goma Maimuna ta shigo ɗakin da ɗaurin ƙirji, ta ajiye kwandon soso da sabulu akan window, wardrobe ta buɗe ta ɗakko kaya da jakar kayan kwalliya ta zauna ta fara shafa mai, tana gama shiryawa tass cikin wasu matsattsun kaya wanda rabin ƙirjinta a waje yake ta ɗauki hijab har ƙasa ta saka. Maama tace "Amma dai ba fita za kiyi ba dai ko?", Maimuna ta dakata da ɗaukar wayarta dake gefen gado tace "bangane ba, nafa gaya miki tin jiya", Maama tace "ehh kin gayamin amma yanzu kinga an sallamo babanku, kin manta dokar da ya kafa muku ne, toh babu inda zaki kuma ki kira Sa'adatu ta dawo.." tana gama faɗin haka ta miƙe ta fita tana cewa "ja'ira idan ma kin samo kuɗin ba alheri kike ba". ★Bayan sallar azahar Hajar ta shiga ɗakin Anty sbd kiranta da take, sallama tayi a hankali, Anty ta amsa mata snn ta shiga ɗakin. Hajar ta nemi guri zata zauna a kan carpet Anty ta nuni mata gefen gado tace "zauna anan", ba musu ta zauna a wajen da ta nuna mata, Anty ta ƙarasa abinda take jikin press ta zauna kan stool tana kallonta tace "kin cire kayanki daga Ghana most go dai ko?", Hajar tace "Eh Hafsa ta saka min a wardrobe", Anty ta gyaɗa kai tace "Okay, idan kina buƙatar wani abun saiki gaya min", Hajar tace "toh", Anty ta kalli fatar ƙafarta da dogon wuyanta tace "wane cream kike using?", Hajar tayi murmushi tace "duk wanda ya sawwaƙa ko petroleum jelly ko mai gurguwa ko kuma Habiba", Anty tace "Okay, kinci abinci?", Hajar ta girgiza kai tace "sai su Hafsa sun dawo", Anty ta kalli agogon da yake maƙale da bango tace "yanzu ma zaki gansu, ita Hafsan ce tace ki ringa jiranta?", Hajar ta girgiza kai tace "A'a Anty", Anty tace "toh shknn, je ki soyamin kajin dana sulala ɗazu", Hajar tace "tom" ta miƙe ta fita Anty ta bita da kallo. Anty dai tinda Hajar tazo gidan bata taɓa ganin wani aibunta ba or something bad akanta, kwata kwata ba ta da wata matsala, gata da tsafta kamar me, kafin ma ta tashi da safe ta gama gyara gidan tass, amma kuma ƴar uwarta na complain da ita. wai bata da haƙuri to gsky in rashin haƙurin ne ga dukkan alamu sai an taɓota. Hajar na fita ɗakin ta wuce kitchen ta ɗauki frying pan ta tuttuli vegetable oil ta ɗora akan gas, bayan oil ɗin yayi zafi ta fara soya naman. tana gama soyawa ta fita kitchen ɗin ta gayawa Anty snn ta wuce ɗakinsu Hafsa. wayarta ta ɗauka ta shiga kiran umma, Umma na ɗauka Hajar ta gaisheta tace "ya jikin Baba?", Umma tace "da sauƙi, mun dawo gida", Hajar tace "Allah ya ƙara afuwa", Umma tace "Ameen", Hajar tayi gathering courage tace "Umma yaushe to zan dawo gida?", Umma tace "wani abun ake miki anan ɗin ne?", Hajar ta girgiza kai tace "ni ba abinda ake min, nafi son gida wllh, dan Allah umma kiyi haƙuri", Umma tace "laifin me kika min da kike bani haƙuri, gwara ma ki saba da zama anan sbd gsky bazaki dawo gida yanzu ba", hawaye ya ciko idanun Hajar tace "dan Allah Ummana", Umma ta sauke wani ɓoyayyen ajiyar zuciya tace "kiyi haƙuri kinji, sai anjima", ta katse kiran. Hajar ta ringa kallon screen ɗin wayar tace "na shiga ukuna". palour ta fita ta zauna, tana zama Anty ta fito daga room ɗinta ta shiga kitchen ta fito da plate din abinci da soyayyen naman kaza a kai ta zauna a palourn tana ci, Anty tace "kee tashi ki zuba abinci ki ci ba wani sai Hafsa ta dawo", Hajar tace "Allah Anty bana jin yunwa", Anty ta cigaba da cin abinta bata sake cewa komai ba, few minutes kam saiga su Hafsa nan sun dawo. Bayan Hajar da Hafsa sun gama cin abinci Anty ta kalli Hafsa dake gyara wajen da suka ɓata tace "da yamma zan aike ku supermarket, idan kin kai plate din kitchen sai ki kawomin jotter da biro nayi list din abinda zaku siyo", Hafsa tace "toh" ta shiga kitchen. tana fitowa ta wuce ɗakinsu ta ɗakko jottern da pen ta kaiwa Anty. Bayan Sallahr la'asar rana tayi sanyi Hafsa da Hajar suka shirya zuwa supermarket. dukkansu dogon hijab suka saka. a tare suka fito palour, Anty dake palourn tace "yawwa karku kai magrib and go to the nearest", Hafsa tace "tom" ta amshi list ɗin da kuma Atm card ɗin da Anty take miƙa mata. Hajar tace "sai mun dawo". suka fita Anty na jadda musu cewa kar su kai magrib. suna fita road kam suka samu Napep, Hafsa tace "wellcare", mai Napep yace "Haɗeja Road?", Hafsa tace "Eh". ya faɗa musu bill. Hafsa ta shiga snn Hajar. saida suka hau saman titi snn Hajar tace "Anty fa tace muje na kusa shine zamu tafi Haɗeja Road". Hafsa tace "kinga supermarket ɗin da suke kusa ba komai ake samu a nan ba, kinga gwara muje wanda zamu samu komai mu dawo da wuri". Hajar dai ta gyaɗa kai ba tace komai ba. 20minutes of a ride suka isa supermarket ɗin. bayan sun sauka daga Napep ɗin Hafsa ta basa kuɗinsa snn suka nufi entrance. suna shiga ciki Hafsa ta ɗauki shopping basket ta miƙawa Hajar. ta ciro list ɗin ta fara ɗaukan abinda ke rubuce tana sakawa a basket ɗin hannun Hajar. bayan Hafsa ta gama ɗaukan komai dake rubuce a list ɗin tace "yawwa, saura man ki", Hajar tace "mai na kuma?", Hafsa tace "yess Anty tace a siya miki mai da turare, na ɗaukar miki turaren man ne dai bansan wanda zai miki ba", Hajar tace "ɗaukar min mai gurguwa", Hafsa tace "wane irin mai gurguwa?, bari na ɗaukar miki irin wanda nake shafawa", Hajar tace "A'a nifa man nan naki be min ba sai kace ka shafa ruwa gashi kuma kayi ta gumi kamar kuturu", Hafsa tayi murmushi tace "toh shknn bari na duba miki wani amma banda mai gurguwa", Hafsa ta juya wajen creams ɗin, a tsanake take dubawa cause Hajar is fair in complexion, haskenta irin me pink ɗin nan ne bata so ta ɗaukar mata wanda zai ɓata mata complexion. Tinda suka shigo harabar supermarket ɗin yake kallonta ta cikin tinted glass ɗin motarsa dake parking space, da sauri ya buɗe motar ya fito yabi bayansu, wani yadi ne ajikinsa sky blue mai mugun kyau, kai kana ganinsa kasan kuɗi sunyi kuka, tinda ya shiga wajen shopping ɗin yake nemansu sbd sun ɓace masa. ya ƙanƙance ido yana tuna fuskarta da ya taɓa gani sau ɗaya. tabbas itace. Hafsa ta ɗauki wani cream mai kyau ta saka a basket tace "yawwa mun gama mu tafi". Hajar na juyawa shi kuma ya iso wajen. kallon aisle ɗin da suke yayi. kallonta ya ringa yi ba ƙiftawa. a hankali Hajar da Hafsa suke fito daga aisle ɗin suka nufi counter. suna zuwa aka lissafa kayan aka zuba a ledoji biyu. Hafsa ta ciro card ta miƙawa cashiern wajen. cashier tace "ai ya biya kuɗin" ta faɗa tana miƙawa wani gentleman dake gefensu card ɗinsa......✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche { 20..} Idonsa akan Hajar ya karɓi card ɗin ya zura a aljihun gaban rigarsa yace "thanks", Hafsa ta kalli cashier tace "an biya kuma, waye ya biya?", cashier ta nuna mutumin da har lokacin yake tsaye a wajen tace "sir", a tare Hafsa da Hajar suka juyo suna dubansa, ido huɗu sukay da Hajar, Hafsah tace "but why?", baice komai ba ya ɗauki ledojin guda biyu yace "plxx let's talk outside" da haka ya nufi exit way. Hafsa ta dubi mutanen dake bayansu suna jiran su basu space suma a irga musu kayansu. hannun Hajar ta riƙe suka fita harabar supermarket ɗin. adaidai exist door ɗin suka gansa, Hafsa tace "bawan Allah bamu ledojin kayanmu", wani soft smile wanda ya sake feso da kyansa yayi yace "tom, gashi" ya miƙa mata ledojin. kin karɓa tayi ta miƙa masa Atm card tace "muje POS ka cire kuɗin ka", yace "No ba kyau mayar da hannun kyauta", Hafsa tace "toh sbd me zaka biya mana kuɗin shopping ba tare da sanin mu ba?", yace "plxx accept it, yanzu ai kun sani", Hafsa tace "malam kana ɓata mana lokaci, dan Allah ka bani account No ɗinka na dawo maka da kuɗin ka". murmushi yayi yace "A'a", Hajar da take jin duk abinda suke cewa ta yamutsa fuska tace "kinga bar masa kayan sai mu koma ciki mu ɗauki wasu" da haka ta riƙo hannun Hafsa suka nufi entrance, da sauri ya biyosu a baya with cool voice yace "Hajar". dakatawa Hajar tayi da tafiya a lokaci guda ta saki hannun Hafsa snn ta juyo ta zuba masa lulu eyes ɗinta. ya ciro ƴar ubansun wayarsa daga pocket ya danna kira. ƙarar waya ya fara fitowa daga jakar dake hannun Hafsa. Hafsa ta kalli Hajar snn ta ciro wayar ta miƙa mata. Hajar ta ringa kallon numbern dake kiranta wacca ɗazu da safe aka kirata da ita. a hankali ya katse kiran ya shafa kansa yana kallon fuskar Hajar yace "am Ahmad...", Hafsa ta kalli Hajar cike da mamaki tace "au daman kin san sa?", Hajar na kallon cikin idonsa tace "not at all, yanxu ma na fara ganinsa a rayuwa", jin zazzaƙar muryarta tayi beating eardrum ɗinsa ya lumshe ido, a zuciyarsa yace woww beautiful and tasty. Hajar ta juya ta cigaba da tafiya while her heart is palpitating rapidly. Hafsa ta juya zata bita, ya dakatar da ita da faɗin "alright muje a biya kudin kar na wahalar da ku, amma sure they will be next time". Hafsa ta dakatar da Hajar da take gaf da shiga wajen shopping ɗin tace "jirani anan bari ayi refunding kuɗinsa". Hajar ba tace komai ba ta cake a wajen ba tare da tayi kuskuren kallon inda take jin arwa akanta ba, tare dashi Hafsa ta koma ciki akai masa refunding kuɗinsa, ta amshi ledojin hannunsa tace "nagode". yace "is she your sister?", tace "sure, she's my maternal cousin", ya shafa kansa yace "ohk, amma dai ba baiko akanta ko?", Hafsa tayi shiru tana kallonsa kafin ta gyaɗa masa kai ta juya ta fita. bayanta yabi da kallo kafin shima ya fita, Hajar ta karɓi leda ɗaya a hannun Hafsa snn suka fita daga harabar supermarket ɗin. suna fita kam suka samu napep suka shiga. Ahmad ya shiga motarsa yana sauke ajiyar zuciya kafin ya zura key a ignition ya kunnata, bayan adaidaitan da ya ɗaukesu ya ringa bi har suka je inda zasu. a gaban idonsa suka sauka daga Napep, Hafsa ta biya kuɗin napep snn suka shiga gida. wani murmushi yayi ya daki steering motar snn ya lailayasa gami da juya kan motar. ya gammace ya haƙura da appointment ɗinsa da yayi loosing wnn babban opportunityn, he won't let go of this hot cake again. su Hajar suna shiga gida aka kira sallar magrib, Anty da take kitchen tana kwashe tuwo ta fito tace "saida dai ku kai magrib ko?", Hajar tace "abin hawa ne suke wahala Anty?", Hafsa ta ƙarasa cikin palour ta ajiye ledar hannunta. Hajar ma ta ajiye ledar hannunta snn ta shige ɗaki domin yin alwala. tana fitowa daga toilet ta shimfiɗa darduma ta kabbara sallah, Hafsa ce ta shigo itama ta shiga toilet tayo alwala ta fito. a gefen gado ta zauna tana kallon Hajar har ta idar da sallah. Hafsa tace "kin sansa ko?", Hajar ta cigaba da azkar ɗinta bata tanka ta ba, Hafsa tace "gashi nan yanada numbern ki". Hajar ta shafa addu'ar da ta gama snn ta kalli Hafsa tace "yaushe kika zama journalist ne?", Hafsa tace "dan Allah ki bani amsa". Hajar tace "alright, Eh na sansa amma ban taɓa ganinsa ba sai yau, Zainab ce ta bashi numbern ta, ɗazu da safe ya kirani ni kuma na saita masa hanya sbd nasan bazai taɓa samun abinda yake so daga gareni ba" Hafsa ta gyara zama tace "toh sbd me?", Hajar tace "inada wanda nake so", Hafsa tayi tsaki tace "au sbd kinada wanda kike so shine kike ƙoƙarin rejecting dinsa, wllh kinada matsala Hajar, ai ni dai a shawarce ba a riƙon saurayi ɗaya sbd may be ba shine zai zama mijinka ba, kuma suma samarin ba sa zama da girlfriend ɗaya wllh", Hajar ta miƙe daga kan dardumar tace "i won't double date gsky", Hafsa ta buɗe baki za tay magana Hajar ta katseta da faɗin "ki tsaya zance lokacin sallah ya wuce ki". da misalin karfe tara da ƴar mintina na dare kowa na gidan na zaune a palour, wayar Hajar ta fara ringing. ignoring call ɗin ta ringa yi sbd ta sha Ahmad ne, Anty tace "wai wayar waye wnn?", sai a lokacin Hajar ta kalli wayarta ta, ganin mai kiran yasa tayi saurin ɗaukar wayar a hannunta amma kuma ba tay picking ba. kiran na yankewa ta miƙe daga palourn ta nufi ɗakinsu Hafsa, Anty da Hafsa suka bi bayanta da kallo. Hafsa ta kalli Abdallah da yake jujjuya abincin gabansa, wato yau maƙiyinsa akai wato tuwo, ga Anty ta hana a dafa wata indomie, a hankali Hafsa ta fara dariya, Abdallah ya juyo ya kalleta ya haɗe jira yace "kee, meye haka?", ai kam ta sake tuntsurewa da dariya tace "ba komai yaya gani nai miyar taji busasshen kifi", tsaki yayi snn ya miƙe ya ɗauki kwanon abincin da bai ci ba ya wuce kitchen, Anty tace "ina zaka da abinci Abdallah?", yace "na ƙoshi", Anty ta ɗaga kafaɗa tace "shknn, wllh ka fiya tsirfa, naga da kana cin tuwon ai, Hafsa dafa masa indomien, sai yayi ta tsaho kamar wani zalɓe tinda haka ya zaɓa, amma mutum zai kwanta ba zai ci abu mai nauyi ba sai wata shegiyar indomie", Hafsa tace "tom" ta tashi ta nufi hanyar kitchen, tana zuwa kusa da Abdallah ta rage murya tace "ka turo 2GB ko nai maka mai uban yaji kuma na dafe ta", harara ya galla mata ya miƙa mata plate ɗin tuwon yace "ƙarasa dashi, zan turo miki 500MB in yayi miki, idan kuma bakya so shknn", Hafsa tace "Eh, turo amma zan gumbuɗa yaji" ta shige kitchen. Hajar na shiga ɗaki da sauri ta amsa kiran Nura da ya sake shigowa. tace "Assalamu alaikum" fuskarta ƙunshe da murmushi, yace "wa'alaykissam salam gimbiyata", tayi murmushi tace "ina yini", yace "lfy alhmdllh, ykk?", tayi twinking lulu eyes ɗinta gami da sukuwa kan gado tana rungume pillow a ƙirjinta tace "ina lfy alhmdllh, kaima ykk, ya aiki?", yace "alhmdllh, mun gode Allah", shiru tay bata ce komai ba, yace "ya jikin Baba?", tace "da sauƙi", yace "to masha Allah, Allah ya ƙara afuwa, insha Allah gobe zan shigo na dubasa", tace "tom, Allah ya kaimu goben", yace "Ameen, snn bayan isha'i kema zanzo", tace "ai yanzu bana gida", yace "kamarya bakya gida?, to ina kika je?", tace "ina gidan Anty Jamilah zan zaune a wajenta for the mean time", yace "okay, dole kam na biyo ki nan". tayi murmushi ba tace komai ba. ★Sa'adatu ce rakuɓe a soro ta ɓuya a bayan ƙofa, a hankali ta cire takalmanta ta rungumesu a ƙirji ta leƙa cikin gida, zaro ido tay waje ganin Huzaifa a bakin tukwanen ruwa yana ɗiba, ƙirji ta dafe tace "na shiga duba daman ya Naseer bai tafi ba", ta sake leƙawa sukay ido huɗu, Huzaifa yace "waye a nan?", wani relief taji da ta fahimci ba dodonta bane, tayi sauri ta ajiye takalmanta snn ta saka ta shiga ciki, karo suka kusa yi da shi. ya kalleta sama da ƙasa yace "ke daga ina kike?", tace "Maama ce ta aiken", ya kalli cikin idonta yace "nace daga ina kike?", ta murguɗa baki tace "to nace maka Maama ce ta aikeni gidan Balaraba..", gwaɓe mata bakin yayi har saida yayi jini yace "tin muna shaida juna ki gayamin daga gidan uban wa kike kafin na sumar dake", daddagewa tayi ta buɗe murya ta fara kiran Maama, afujajan Maama ta fito daga ɗakinta jin muryar shalelen ƴarta, Maama tace "Sa'adatun Maama kin dawo?", Sa'adatu ta ruga gabanta tace "Huzaifa ne", Maama ta kalli Huzaifa snn ta kalli Sa'adatu tace "me yayi miki?", Sa'adatu ta buga ƙafa a ƙasa tace "dukana yayi a baki, kuma Allah ya isana", Maama tace "duka kuma?, Akul Huzaifa karka sake taɓata", yace "ke ni kikewa Allah ya isa?, wllh saina kifar dake", Sa'adatu ta rakuɓe bayan Maama tace "Eh, mugu kawai". Maama tace "A'a Sa'adatun Maama yayanki ne fa banda rashin kunya", Sa'adatu ta cokalo baki snn ta shige ɗaki. Huzaifa ya sauke numfashi a hankali zuciyarsa na zafii. Maama tace "karka ɗauki halin Nasiru, ku ringa ririta ƴan ƙannenku, amma indai kuka haɗu dasu sai duka, haba don Allah..." ta juya ta koma ɗakinta. Washe gari tin ƙarfe takwas Huzaifa ya shirya komawa schl. ɗakin Baba ya shiga da ƴar jakarsa goye a baya yayi masa sallama, Baba yace "toh Allah ya kiyaye hanya, Allah yayi maka albarka", Huzaifa yace "Ameen Baba", Huzaifa ya fito daga ɗakin ya doshi na mahaifiyarsa, yana ƙoƙarin shiga ɗakin sai gata nan ta fito, ya durƙusa ya gaisheta yace "Maama ni zan koma", tace "Au kaima tafiya za kayi, jiya fa Naseer ya tafi", yace "lecture ta kankama ne", tace "toh, wai saura shekara nawa ne ka gama wnn jarababbiyar makarantar?", yace "saura shekara ɗaya insha Allah", tace "toh Allah ya bada Sa'a", yace "Ameen". Umma ta fito ɗakinsa hannunta riƙe da tsintsiya da abin kwashe shara da ta share ɗaki, Huzaifa ya russunar da kai yace "Umma zan wuce", Umma tayi murmushi tace "Allah ya kiyaye hanya", yace "Ameen". Maama ta ƙunduma masa wani zagi tace "dalla malam fita". Huzaifa ya gyara zaman jakar bayansa snn ya fita. da yamma Umma ta fito ɗakinta tana zubawa wata yarinya da tazo siyan kulele, ta gama zuba kulelen a leda ta bawa yarinyar ta shiga ɗaki ɗakko mata canji, tana fitowa ta bawa yarinyar canji saiga dan Munkaila makwabcinsu nan ya shigo yace wai ana sallama a waje, Nabilah da take zaune tsakar gida tayi caraf tace "inji wa?", yaron yace "bari na tambayo" ya fita da gudu, ba jimawa sai gashi ya dawo yace "wai Nura ne". Nabilah tace "kace masa me za a basa", yaron ya juya kenan zai fita Mu'azzam ya fito daga ɗakinsu yace "tafi wasanka kaji", da sauri yaron ya fita Mu'azzam kuma yayi hanyar soro, Umma dai ta koma ɗaki. tare da Nura Mu'azzam ya dawo gidan, ɗakin Baba suka nufa. Nabilah ta taɓe baki tana kallon Nura sama da ƙasa. a hankali Nura ya cire takalmansa ya shiga ɗakin Baba da Mu'azzam ya yaye masa labule. ya durƙusa cike da ladabi kansa a ƙasa yace "Baba barka da yamma", Baba yace "barka dai samari", Nura yace "ya kufan jiki?", Baba yace "Alhmdllh", Nura yace "Allah ya ƙara afuwa", Baba yace "Ameen", Nura bai jima ba ya yiwa Baba sallama. wasu manyan ledoji da ya shigo dasu ya ajiye snn ya fita. tare da Mu'azzam suka fito. a soro suka tsaya Nura yace "Mu'azzam ka ƙi juyowa hadda ko?", Mu'azzam ya shafa kansa yace "A'a ya sayyadi haddar nan fa bazata shiga ba", Nura yayi murmushi yace "Allah ya ƙarawa Baba lfy", Mu'azzam yace "Ameen Ameen", Nura yace "toh sai anjima", Mu'azzam yace "A sauka lfy ya sayyadi". Nura ya wuce Mu'azzam kuma ya dawo gida. Maama da take rakuɓe jikin labulen ɗaki ta fito ta kalli Nabilah tace "wane wnn da naga ya shigo da manyan ledoji?", Nabilah tace "matsolon Hajara ne", Maama tace "ban gane ba?, wnn shine malamin naku?", Nabilah tace "malaminsu daii", Maama tace "Amma ku ka ce min faƙiri ne?, ji fa manyan ledojin da ya shigo dasu snn kuma ji suturar jikinsa", Nabilah tace "wllh faƙiri ne wani kuturun shagon chajin waya ne dashi fa, tsabar ƙanƙantar shagon mutum ɗaya yake ci, gashi kuma na katako, katakon ma duk ya ruɓe gara ta cinyesa tasss, gidansu ma ba kanta wllh, Babarsa ma ɗan wake take siyarwa", Maama ta sauke ajiyar zuciya har cikin ranta taji daɗi tace "Eh lallai uwarsa me siyar da ɗan wake ga uwar wacca zai aura me siyar da alalar gwangwani abincin yan wahala". Nabilah ta sheƙe da dariya tace "kai Maama", Maama ta gyaɗa kai tace "Allah kuwa". Sa'adatu ce ta fito tana latsa wayarta tace "Maama wai baki san Opay ba?", Maama tace "meye kuma Opay?", Sa'adatu tace "kayan haya mana, wnn kayan fa da kika ga ya saka ba nasa bane na aro ne, zuwa yayi aka ara masa don yazo yayi fafa, tin daga kan agogo takalmi hula da tsadaddiyar shaddar jikinsa wllh duk na aro ne", Maama ta sake sauke ajiyar zuciyar daɗi tace "nifa ince, ai daga gani ma kasan kayan na aro ne, ke har turaren ma da ya tsayamin a maƙogaro na aro ne koh?", Sa'adatu tace "kwarai ma kuwa". Maama tayi hanyar ɗakin Baba tace "bari naga wace tsiyar aka lafto a manyan ledojin", Sa'adatu tace "yawwa gano mana tsiyar". ba ko sallama Maama ta afka ɗakin, kallo ɗaya Baba yayi mata ya kauda kai. tamkar shege a rabon gado haka ta ringa kwalala ido har ta hango ledojin a gefe guda, a wulaƙance ta waftosu ta bankaɗa ta fara duba abinda yake ciki, saida numfashinta ya ɗauke ganin uban kayan, leda ɗaya fruits ne aciki harda Apple da pear, ɗayar ledar kuma kayan shayi. Baba baice mata komai ba ta gama bincika kayan snn ta miƙe ta fita zuciyarta na tafarfasa. Nabilah tace "Maama wace tsiyar ce aciki?", Maama tayi mata wani mugun kallo ta shige ɗakinta. ★A yammacin wannan rana Nurain ya fito daga room ɗinsa ya sakko down stairs zuwa part ɗin Mami, wata jumfa ya sanya coffee mai shegen kyau sai zuba ƙamshi yake, murɗa door handle yayi snn yayi sallama ya shiga, Mami na zaune tana shan red watermelon ita da Noor, Nurain yace "Mami zan je wajen Hajiya", Mami tace "Ohk, ka gaidamin ita da sauran mutan gidan", yace "tomm", Noor tace "yaya ka gaida Iron Lady", yace "Ohk". ya fita palour. katafaren compound ɗin gidansu ya fita, ya doshi parking space ya shiga motarsa, few minutes ya gama warming ya fita daga gidan bayan mai gadi ya buɗe masa gate yana ɗaga masa hannu. Slowly yake driving as usual yana sauraron qira'ar Sheikh Abdul Baseet. A ride of 15minutes ya isa gidan uncle ɗinsa Salisu, a bakin gate ya danna horn, parking motarsa yayi a harabar gidan snn ya nufi main building ɗin kansa tsaye. hannu ya kai ya danna bell ɗin door, babu jimawa mai aikin gidan ta buɗe masa, har ƙasa ta tsugunna ta gaishe sa, ya amsa ba tare da ya dubeta ba. da sauri ta shiga wata ƙofa dake palourn don sanar da ƴan gida. palourn ba kowa sai sanyin Ac da ƙamshin freshner mai daɗi. Nurain ya zauna a kan kujera ya ciro wayarsa a aljihu yana latsawa. few minutes kam saiga wata kyakkyawar mace nan ta fito sanye ta hijab har ƙasa, murmushi ne shimfiɗe a fuskarta tace "Nurain", Nurain ya mayar da wayarsa pocket ya russuna yace "ina yini Ummi", Ummi tace "lfy lou, yasu Maami da Noory?", yace "suna nan lfy", tace "toh madallah", yace "daman zuwa nayi na muku sallama jibi zan tafi India", tace "Au kuma ɗan uwanka na shirin dawowa next week kai kuma zaka tafi, toh Allah ya temaka ya bada abinda akaje nema", yace "Ameen, Hajiya fa?", Ummi tace "tana part ɗinta", yace "Ohk bari na shiga wajenta". ya tashi ya nufi ɗakin Hajiya........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche { 21..} A hankali Nurain yayi knocking ƙofar ɗakin Hajiya, da ga cike akace "waye ne?". Nurain ya haɗe gira snn ya murɗa ya shiga. tinda ya shigo Hajiya da ke zaune bisa lallausar rug ɗin ɗakin take kallonsa har ya zauna a ɗaya daga cikin kujerun ɗakin. Hajiya ta gwalo ido cikin ƙwamemen glasses ɗinta tace "O oho ashe Usuman ne, ai daman tinda naga abu kamar fel waya nasan kaine, angona ba sangameme bane irinka, ni ko yaushe ma zai dawo daga ƙasar can mai ƙanƙanra karfa ya daskare na shiga uku....", Nurain yace "su duk mutanen da suke rayuwa a ƙasar basu daskare ba sai shi", tace "A'a bar wannan zance ai su daman can ƙanƙarar ta gama musu illa sun saba", yace "shima ya saba aii", tace "inafa zai saba, shi da ba jinsin su ba, mutane kamar an bursuna musu garin filawa, angona da yake baƙi ai sam ba gami tsakaninsu, da zan samu jirgin da zai kai masa saƙo ai da na bada maganin sanyi an kai masa..", Nurain yace "toh ki kwantar da hankalin ki next week zai dawo", ta kallesa ta saman glasses ɗinta tace "Au shi Umarun ne zai dawo?, eh ai gara ya dawo kar ya daskare gsky, to kai wa ya gaya maka zai dawo?", Nurain yace "A waya mu kay magana", tace "Oh ni, babu yadda banyi da yarinyar nan Shatu akan ta kira min shi ba amma ta ƙi, yaufa wajen wata guda kenan ina fama da ja'irar yarinyar nan, yanzu kam tinda kazo maza kamo min shi na gansa..", yace "ki bari nan da mako mai zuwa zaki gansa a zahiri yanzu dare ne a can", kafa masa dattijan idanunta tayi ta saman glasses tace "Auu, kaima ja'irin ne kenan?", hade gira yayi yana pointing kansa yace "nine ja'iri Hajiya?", tace "yo ba gashi na gani ba, nace ka kiramin mijina kace min wai dare yayi sbd ka iya lafto ƙarya, ga rana gatsal-gatsal amma kana kiran dare..", gyada kai yayi yace "toh shknn, ni daman zuwa nayi muyi sallama jibi zan bar ƙasar", zaro ido tayi tace "zaka bar ƙasar kamar ya?, kaima garin arnan zaka koma?", yace "Eh", tace "amma dai ban taɓa sanin notin kan Muntari ya kunce ba sai yanzu, shine ya barka ka koma ƙasar arnan, har itama Khadijan notin kanta ya kwance wllh. kamar abin arziƙi ka doshi hanyar zama cikakken mutum sai kuma ka koma baya, da tini kaima da iyalinka dan ma yarinyar ta kasa ka, au koda yake ba jikana ta kasa ba wllh kanta ta kasa, eh shegiya ita taga duhu wllh dan har abada ta rasa nagartacce kamar jikana....", Nurain ya haɗiyi wani yawu cause his wound is still fresh yace "bari na kira miki angon naki", wayarsa ya ciro daga pocket ya kunna data ya shiga kiran Farooq video call. ba ta daɗe tana ringing ba Farooq ya ɗaga. Nurain yayi waving hannunsa a screen ɗin wayar yace "ba fa na ganinka, ka kunna haske Iron Lady ke son magana da kai", Farooq yace "Ohh really, seee yaah My bride" ya miƙe daga kan table ɗin karatunsa ya kunna Light, fuskarsa ta bayyana raɗau sbd haske, yau ma dai jibgegiyar sweater ce ajikinsa, Farooq yace "tana ina?", Nurain ya haska masa fuskar Hajiya, Hajiya na ganin Farooq tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un me ya kumbura ka haka sai kace wanda aka buga masa iska?", Farooq yayi murmushi sbd ba abinda yake gani sai fuskarta da kantamemen glasses ɗinta sun cika screen ɗin wayar. Hajiya tace "ka yiwa Allah da manzon sa ka dawo gida", Farooq yace "next week zan dawo amaryata", tace "Atoh ya dai kamata wnn kumburi haka..", Farooq yace "ba fa kumbura nayi ba rigar sanyi ce, bari na cire ki ga", da sauri ta katsesa tace "A'a karka cire ka daskare, tinda dai baka kumbura ba shknn", Farooq yace "toh shknn". tace "kaga wnn fel wayar wai shima ƙasar arnan zai koma sbd shegiyar yarinyar da zai aura ta gudu ta barsa shine ba zai nemi wata ba", Farooq was shocked da abinda ta faɗa amma yace "ni kam ina dawowa zan miki kishiya", tace "Eh maza ka dawo kayi min ai kishiya alheri ce indai ta gari ce..", yace "Au ba kya kishi na kenan?", tace "kaji wani zance yo wnn ai shine kishin", Farooq ya murtuke fuska kamar gaske yace "ni bani ɗan uwana", Nurain ya karɓi wayar don yanajin komai da suke faɗa. Farooq yace "so that's why you said until your heart healed?", Nurain ya gyaɗa kai yace "sure, and now it's healing..", Farooq yace "wish you all the best bro", Nurain yace "thank you i will call you tomorrow" ya katse kiran. ganin magrib na dosowa yasa Nurain ya yiwa grandmother ɗin tasa sallama, Hajiya tace "toh yanzu sai yaushe Usuman?, kaima shekarun zaka ɗauka kamar Umaru ko?", yace "A'a Hajiya, wata takwas zan yi insha Allah na dawo gida", tace "O oho har wata takwas ɗan nan, Allah ya tsare...", ta miƙe tana dogara sandarta ta shiga bedroom ɗinta, bayan wani lokaci ta fito da ƴar leda tace "ungo na kane kai kaɗai, karka tsamma kowa", ya karbi ledar yana leƙa cikinta yace "wai har takwarar taki?", tace "A'a ni ba takwarata bace, ni ba sunana Noor ba", yace "ai ɓoyewa akai, to Hajiyarmu khairan", Hajiya ta fara matsar kwalla tace "to Usuman ka kula da addininka don Allah", yace "insha Allah" da haka ya nufi door ya fita, saida sukay sallama da Ummi snn ya wuce. ★Tin safe Hajar take neman hanyar da zata sanar da Anty zuwan Nura, sau biyu tana attempting amma saita kasa, a zaune take akan stairs ɗin varendern palour, wayarta ce ta fara ringing, yamutsa fuska tayi ganin numbern dake kiranta, a fili tace "na shiga uku wai wnn wane irin naci ne", tana kallon wayar har kiran ya katse wani ya sake shigowa, 20+ missed call yayi mata daga safe zuwa yanxu, da kyar ta ɗauka ta wani sha kunu, daga ɗaya ɓangaren Ahmad yace "Assalamu alaikum", a wani daƙile tace "wslm", yace "how are you?", tace "fine", yace "alhmdllh, Hajar plxx just give me a chance to show my feelings", tayi gathering courage tace "don't you have anything else better to do?, I'll pretend that I didn't hear that", ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace "you heard everything, you can't pretend that you didn't", ta ciji lower lip ɗinta painlessly dan sosai maganarsa ta shigeta, tace "i have to hang up....", pleadingly yace "plxx answer me before you hang up", kasa cewa komai tayi, shiru ne ya dauka har hakan yasa su ke jin breathing din juna, tayi twinking lulu eyes dinta tace "aiki nake yi", after few seconds yace "alright...", da sauri ta katse kiran ba ta jira sauran cewarsa ba. blocking numbernsa tayi snn ta goge call log ɗinsa gaba ɗaya, murya can ciki tace "Allah ya baka gaba Ahmad". bata da wani space a zuciyarta, Nura has already filled everywhere. knocking gate aka yi ta miƙe ta buɗe, su Hafsa ne suka dawo daga school, Hajar ta matsa musu hanya tace "barka da dawowa yan bokoko", Hafsa tace "na dai kusa gamawa", ƴar autar Anty kam tini ta wuce ciki tana fige hijab ɗinta. bayan Sallahr la'asar Hafsa ta shiga ɗakinsu tana dafe kai, Hajar da ke nannaɗe darduman da tayi sallah tace "lafiya?", Hafsa ta yamutsa fuska tace "kaina ke ciwo", Hajar tace "sannu kinsha magani?", Hafsa tace "A'a yanzu dai zan je wajen Anty na amso paracetamol", Hajar tace "okay, zauna na kama miki kan sai kuma kisha magana za kiji sauƙi sosai", Hafsa tace "tom" ta zaune gefen gado, gefenta Hajar ta tsaya snn ta fara kama mata kan tana hura mata addu'a, tana gamawa ta matsa thick vein ɗin goshin ta yarfe tace "toh ya kika ji?", Hafsa tace "wllh har ya lafa sosai" ta mike zata fita a ɗakin, Hajar tace "wajen Antyn zaki amso magani?", Hafsa ta gyaɗa mata kai, Hajar tace "dan Allah kice mata anjima zanyi baƙo", Hafsa tace "Au haba mutumin jiya ne zai zo?", Hajar tace "kinji ki da wani zance wai mutumin jiya toh bashi bane", Hafsa tace "toh waye?", twinking eyes Hajar tayi tace "Ya sayyadi na ne zai zo", Hafsa ta tace "wai daman har yanzu kuna tare da Nura?", Hajar tace "Eh, ai iyayensa ma sunje wajen Baba", Hafsa tace "kaiii amma shine baki fadamin ba, da yaushe zai zo?", Hajar tace "da yamma", Hafsa ta fita daga ɗakin ta shiga kitchen ta ɗauki pure water snn ta shiga room ɗin Anty, motsin ruwa taji a toilet, bedside drawer ta janyo ta fara neman Panadol tinda anan suke ajiye first aid drugs, ta dauke panadol ta ɓalli two tablets ta mayar da sachet ɗin. da kyar ta haɗiye maganin tana yamutsa fuska, Anty ta fito daga toilet tana gyara hular kanta tace "ku shirya ke da Hajar muje barkar Fauziyya", Hafsa tace "yanzu zamu?", Anty tace "Eh", Hafsa ta ɗaga ragowar pure watern da ta sha drug tace "Anty wllh kaina ke ciwo yanzu ma nasha magani, ko na bari ranar suna naje da yamma", Anty "tom shknn, kyaje ranar suna dama ba zuwa zanyi ba", Hafsa tace "tom, Hajar tace anjima za tay baƙo", Anty ta ciro kayan da zata saka daga wardrobe tace "ke ta aiko knn?", Hafsa tace "A'a wai bazata iya gaya miki ba", Anty tace "toh shknn, sai ta saukesa a sitting room, akwai semosa a fridge", Hafsa tace "tom" ta miƙe ta fita. Anty tana gama shiryawa ta ɗauki handbag dinta ta fita, ɗakinsu Hafsa ta shiga tace "toh sai Allah ya dawo dani", Hajar tace "Allah ya tsare", Hafsa tace "sai kin dawo". Biyar da rabi na yamma Hajar ta fito daga wanka, ta shafe jikinta da sabon cream ɗinta mai daɗin ƙamshi, riga da skirt ta saka na atamfa ta tsaya gaban mirror tana cakare ɗauri, Hafsa ta shigo tace "uhmm kinyi kyau, na gama soya semosan", Hajar na zizara kwalli a fatar manyan idanunta farare ƙal tamkar madara tace "nagode". wayarta dake tsuwwa ta ɗauka ganin me kira tayi murmushi tace "ina jin ma ya iso", kara wayar tayi a kunne tace "okay, gani nan fitowa", mayafin da ta fitar ta ɗauka ta yafa, Hafsa tace "laa ya naga kinsa mayafi ba Hijab ba, ko ba ustaz bane?", Hajar ta zabga mata harara tace "chab wai dan yana malamin islamiyya shine zai zama ustaz, wllh ba ruwansa indai zaki saka abinda zai rufe miki jiki to shi bashi da damuwa", Hafsa ta kalleta sama da ƙasa taga dai ruf mayafin da ta saka ya rufe mata jiki kuma ba shara shara bane, Hafsa tace "Eh, kinsan mazan ma kowa da ra'ayinsa, wani yafi son Hijab wani kuma mayafi wani kuma duka, wani kuma babu ruwansa indai za kiyi decent dressing is okay", Hajar tace "that's my Man shima decent kawai yake so", Hafsa tace "yana fa jira", Hajar tayi wasa da kwayar idonta tace "ai ya saba" ta ɗauki turare ta fesa sama sama. slowly Hajar ta fito compound ta nufi gate, ta bude ƙofa ta fita, yana tsaye jikin fillelen sabon motorbike dinsa yana danna wayarsa, yana ganinta yayi murmushi ya mayar da wayar aljihu, kallonta ya ringa yi ba ƙiftawa har ta ƙaraso, sosai silent kwalliyar da tayi da kuma decent dressing ɗinta ya tafi da imaninsa, sunkuyar da kanta tayi tace "sannu da zuwa", baice komai ba kawai kallonta yake, shirun da taji ne yasa ta ɗago kanta ai kam sukay ido huɗu, tayi sauri ta sunkuyar da nata tace "Bismillah ka shigo", yace "A'a nidae bazan shiga gidan mutane ba", tace "toh nan fa kan hanya ne", ya dubi street ɗin yaga akwai mutane yace "toh amma dai ansan da zuwa na dai ko?", childishly ta hararasa tace "Bismillah" ta juya ta koma ciki ba tare da ta jira cewarsa ba. bayanta yabi har suka shiga gidan tayi leading ɗinsa har sitting room. a kujera one seater ya zauna ita kuma ta zauna a two seater dake gefensa, Calmly tace "ina yini", ya ringa kallonta, ɗago kanta tayi jin bai amsa ba sukay ido huɗu, tayi pouting lips ta rufe fuskarta da palms ɗinta tace "dan Allah ka barii", murmushi mai sauti yayi yace "me fa?", tace "why are you staring at me?", yace "because i missed you so much and you look beautiful", murmushi tayi tana wasa da yatsun ƙafarta, yace "ba ki rubuta Jamb ba ko?", ta gyaɗa masa kai tace "Eh neco kawai na zana", yace "Ohk, suma yanxu school of Nursing suna amfani da jamb, gashi baki rubuta ba amma ba damuwa saiki rubuta next year ko?", tace "Admission din bazai samu ba saida Jamb result knn?", yace "Eh, ai da nasan sun canja tsari da sai kin zana jamb, kamar yanxu ne zaki ji an fara registration, and you're still young kinada enough time", tace "Ahh I'm not young", yace "ohk sai ki gayawa wanda bai sanki ba to me you're a little girl kuma you know akwai certificate of birth ɗinki a wajena", sallama akai a bakin ƙofa Hajar ta amsa, Hafsa ce ta shigo tana sanye da hijab hannunta riƙe da tray mai dauke da bottle water da drinks sai kuma plate ɗin semosa, a hankali ta ajiye trayn akan Centre table ta zauna kusa da Hajar, Hafsa tace "sannu da zuwa, ina yini", Nura yace "mun yini lfy?", tace "alhmdllh", yace "masha Allah, ya karatu?", Hafsa tace "alhmdllh", a hankali Hafsa ta miƙe ta basu waje tana fita ɗakin akay knocking gate, bakin gate ɗin ta wuce ta buɗe ƙofa, ita tasha ma Humaira ce ta dawo daga islamiyya amma me sai taga wani yaro, tace "ya akai?", yaron yace "wane mutum ne yace wai ana sallama da Hajar", Hafsa tace "yana ina?", yaron yayi nuni da wata jugunanniyar mota dake gefen titi a parke, Hafsa ta kalli mutum da ya fito daga cikin motar, zaro ido tayi sbd ta ganesa, shine mutumin da suka hadu jiya a supermarket, Ahmad ya ƙaraso bakin gate ɗin yana kallon Hafsa da itama take kallonsa cike da mamaki.......✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche { 22..} Ahmad ya shafa kansa yana kallon Hafsa yace "Assalamu alaikum", har lokacin mamaki bai bar face dinta ba tace "wslm, ina yini", yace "lfy lou, kinyi mamakin gani na ko?", tace "dole, ince dai lfy bawan Allah?", numfashi ya sauke a sauƙaƙe yace "Ammm lfy", tace "Ohk" ta juya zata koma gida, da sauri yace "amm Hajar fa?" ya fada yana shafa kwantaccen beard ɗinsa, ta juyo tace "what about her?", yace "i came for her, help me by informing her", hannuta na riƙe da ƙofa tace "ohh, amma Hajar ba ta nan", mood ɗinsa ne ya canza lokaci guda yace "bata nan?", Hafsa ta gyaɗa masa kai cause that was the only way, yace "I'm sorry to invade her privacy, tana ina?", ta saukar da kanta ƙasa tana tunanin abinda za ta faɗa, few seconds passed amma ba tace komai ba, ya ringa kallon fuskarta with his cool voice yace "girl.., where is your sister?", ta ɗago ta kallesa sbd yadda yayi pronouncing girl ɗin tace "amm sunje unguwa da Babarmu", yace "Okay thank you, ai naga yamma ma tayi sosai, bari kawai na jirata...", ta katsesa tace "A'a karka jirata, ba yanxu zasu dawo ba", yace "toh sai yaushe?" yana kallon cikin idonta da rashin gaskiya ya bayyana ainun, hade gira tayi tace "A'a, nace fa ba yanxu zasu dawo ba, may be ma acan zasu kwana", Humaira ce ta ɓullo ta layin dake gefen gidan ta dawo daga islamiyya, sosai gaban Hafsa ya faɗi ganinta da tayi, Humaira ta tsaya tana kallonsu ko ƙiftawa babu sai kuma ta ƙaraso ta shiga gida, Hafsa ta sauke ajiyar zuciya tabi bayanta da kallo, rediyo me jini knn, tasan tabbas saita zayyanawa Anty abinda ta gani, Hafsa tace "sai dai ka dawo gobe", yace "No zan dawo anjima dai", tace "toh idan kuma basu dawo ba fa sun kwana acan", yace "No problem sai na dawo gobe, she worth it", tace "alright" ta juya zata shiga gida yace "wait", ta tsaya ba tare da ta juyo ba, yace "kinga kwa Cousin dinki tana bani wahala kema kina tayata ko?", tace "kamar ya?", yayi slight smirk yace "kin ƙi faɗamin whereabout ɗinta, and my heart keep saying that my Hajar is inside the house", Hafsa can't help it dole tayi slight smile ta juyo tace "really", ya gyaɗa kai yace "sure, young lady do you believe in fate?", sosai tambayarsa ta bata mamaki tace "Yess Noo", yace "hmmm, toh yess ne or No?", ta karyar da kai gefe tace "toh nidae a nawa view ɗin is No, a view din wasu kuma zance yess", yace "toh a ajiye naki view din a gefe a dauki na wasun, kema nasan bazaki so ki zama silar datse fate ba", kallonsa tay tace "sure bazan so hakan ba, abu guda ɗaya i promise you ni da kaina zan fito maka da Hajar amma not today, zanyi hakan ne dan na nuna maka cewa bazan datse fate ba..", kallonta ya ringa yi kafin yace "then when?", tace "sooner or later", ya gyaɗa kai yace "amma taya zan san lokacin?", tace "where is your phone?", wayarsa ya ciro a aljihu, a hankali ta fara karanto masa number yana lodawa, tana gama gaya masa tace "sau ɗaya zaka kira, idan lokacin yayi zan kiraka..." da haka ta shige gida ta rufe ba ta jira cewarsa ba. Ahmad yayi murmushi yana sauke ajiyar zuciya ya shiga motarsa, saida ya kira layin Hajar wajen sau uku amma bata shiga, tin ɗazu abinda ake ce masa knn. ƙarfe shida da minti sha biyar Nura ya miƙe daga kan kujera, ya ciro bandir ɗin ƴan 200 ya ajiye a hannun kujera, Hajar na ganin haka tace "kaga ka ɗauki kuɗinka", yace "toh ai ba ke na bawa ba, na Hafsa ne", ya fita a ɗakin tabi bayansa, a bakin gate ya tsaya yana kallonta yace "toh sai munyi waya", ta gyaɗa kai tace "toh", yace "toh shiga gida", ta juya ta shiga gida a hankali ta rufe ƙofa, sitting room ta shiga ta ɗauki kuɗin da tray ta fita, kitchen ta fara shiga ta ajiye trayn ta ɗauki glass cup mai ɗauke da ragowar lemon da ya rage tana murmushi, a hankali ta kafa kai ta moɗe lemon snn ta fito ta shiga ɗakinsu Hafsa, rafar kuɗin ta ajiye akan cinyar Hafsa dake gefen gado tana operating wayarta, ga Humaira a gefenta sai zaro idanu take tamkar ɓera a buta, Hafsa ta dube Hajar da mamaki tace "meye wnn?", Hajar na warware ɗaurin dankwali tace "cewa yayi na baki", Hafsa ta zaro ido tace "na shiga uku Hajar shine kuma kika amsa", Hajar tace "tinda yayi niyya wllh ba yadda na iya", Hafsa ta ɗauki kuɗin tana juyasu tace "amma sunyi yawa wllh, ni ya zanyi dasu?", Hajar tace "nima ban sani ba", Hafsa ta kalli Humaira ta galla mata harara tace "na dai gaya miki, wllh kika kuskura kikai wata magana a gaban Anty sai na kira miki IT, yadda ya cinye wnn yaron acikin kwata kema haka zai miki", a rikice Humaira tace "dan Allah kiyi haƙuri wllh bazan ce komai ba", Hafsa ta hade gira tace "yawwa kin temakin kanki, tashi ki tafi palour ki kunna cartoon", a hankali Humaira ta miƙe tana murza ido ta fita, Hajar tace "ji muguwa, me yasa kike threatening dinta?", Hafsa tace "guess what?", Hajar "what?", Hafsa tace "wnn mutumin da muka hadu a supermarket ne yazo", Hajar tace "ban gane ba", Hafsa tace "ɗazu ne kina tare da Nura, bayan na fito daga wajenku naji ana knocking gate, ina buɗe gate na tarar dashi a ƙofar gida, ke ba kiga dagar da mukay dashi ba kafin ya tafi, toh shine Humaira ta ganni dashi a ƙofar gida, kinsan rediyo me jini ce yanxu saita rattaɓawa Anty a yimin wata fassarar ta daban", Hajar ta taɓe baki tace "toh taya ya san gidan nan?", Hafsa tace "ke zan tambaya", Hajar ba tace komai ba ta canza kayan jikinta ta fita ɗakin zuwa kitchen ta ɗora dinner. ★Washe gari da safe Umma ta hadawa Baba breakfast ɗinsa, tana zaune gefensa yana cin abincin a hankali tana masa fifita, ledar drugs ɗinsa ta janyo ta ɓalli wanda zai sha ta basa, Baba yace "Allah yayi albarka", tayi murmushi tace "Ameen", ya jinginar da kansa ga bango yace "wai ina Hajara ne?", Umma ta ajiye maficin hannunta tace "tana gidan Jamila", ya gyaɗa kai yace "toh ta dawo gida haka nan", Umma ta gyara zama tace "malam na fi son ta cigaba da zama a can, wllh yanxu gidan nan kunnenmu ƙanƙanra ba hatsaniya, Hajara ba hakuri gareta ba, kamar dage take indai aka taɓata saita rama, zamanta acan shine zaman lfy", Baba ya ajiye numfashi a hankali yace "a wnn marrar bazaka ɗauki nauyinka ka rataya a wuyan wani ba, ai a rayuwar nan zama inda Allah ya ajiyeka da kuma ƙarƙashin wnda Allah ya ɗaurawa nauyinka shine daidai, idan kana so ka zauna lfy da mutane to ka guji abin hannunsu. Hajar ta dawo gida yau ɗin nan", Umma tace "amma malam...", katseta yayi yace "kiyi abinda nace", a hankali tace "toh, insha Allah zata dawo", Maama ce ta bankaɗo labule da ƙarfi ba ko sallama ta antayo ɗakin, hannunta riƙe da wani kantamemen kofi da cokali, daga tsayen da take tace "malam ya kufan jiki?", ba tare da ya dubeta ba yace "alhmdllh", ta gallawa Umma harara tace "madara zan ɗiba zamu karya kumallo nida yara", Baba yace "toh ina kika ga madarar?", Maama ta geɓare baki tace "Auu malam jiya fa naga an kawo maka manya manyan gwangwanaye na madara da milo, kayan marmarin ma sai sun ruɓe ba za a kasafta ba, ya kamata a raba a bawa kowa rabonsa", Baba yace "anƙi a raba", hangame baki Maama tayi tace "toh ai shknn, toh a bamu madarar mu karya kumallo", yace "suma an hana, mai neman auren Hajara ne ya kawo, ita kuma da kike kira da shegiya toh wnn arziƙinta ne....", Maama ta gyara hular kanta da ta wani waskace gefe tace "toh shknn.." ta fita fuuu a ɗakin sai kace wata kububuwa. ɗakinta ta shiga tana hucii, Maimuna da take tsefe kitson attachment tace "Maama ina madarar?", Maama ta wurga mata ƙaton kofin hannunta a fusace tace "madarar gidanku, malama ki cire kuɗi a ƙugunki ki siya, uwar tsimilmila kawai", Maimuna ta taɓe baki ta cigaba da tsefe kitsonta, Nabilah dake haɗa kayanta masu datti da zata wanke tace "toh Maama ina kuɗin da yaya Naseer ya baki ne?, ki bayar a siyo mana ƙosai da gasara", Maama tace "baki da hankali, toh ƙosan ɗari biyar ma yayi mana kaɗan", Nabilah tace "toh wainar gero fa?", Maama tace "wllh an wulaƙanta ni, ina Sa'adatu na", Maimuna tace "ta fita", Nabilah tace "wane ɗan abu kazan kasan ne ya wulaƙantaki Maama?", Maama ta sauke ajiyar zuciya tace "wai akan wata mushiyar madara ake min gori", Nabilah ta yamutsa fuska tace "daman ai saida nace miki kar kije amma kika biyewa Maimuna ƴar san banza, ai ga irinta nan", Maama tace "ke Maimuna wai ina Alhaj ɗin naki ne shi bazai kawowa mahaifin naki kayan dubiya ba?, ko baki gaya masa ba?", Maimuna tace "chab na gaya masa mana amma bana son yazo ruɓaɓɓen gidan nan gaskiya, da ace ma har yanxu Baban na asibiti da sai yazo, ko da yake baya nan ma ya tafi Abuja", Maama ta wangale baki tace "Allah, wato har Habuja yana zuwa?", Maimuna na taje figaggen gashinta wanda ya gama tsiyacewa tass sbd yawan saka attachment tace "uhmm ai yace idan ya aureni acan zamu zauna", Nabilah ta kwashi kayan wankinta tayi waje tana cewa "bamu gani a ƙasa ba". Maimuna ta ɗaga murya tace "oho miki dai, ƴar ciki baƙi kawai", Maama tace "muna fatan Allah ya mayar da ƙoƙo masaki". Maimuna ta miƙe ta tattara gashin attach ɗin da ta gama tsefewa tace "Ameen". Umma na fitowa ɗakin Baba ta shiga nata, wayarta ta ɗauka ta fara kiran ƴar uwarta, bayan sun gaisa Umma tace "ya yaran ya ɗawainiya?", Anty tace "alhmdllh Adda", Umma tace "Hajara ta shirya ta taho gida..", Anty tace "to sbd me Adda?", Umma ta sauke ajiyar zuciya tace "wllh malam ne yace lallai lallai yau ta dawo gida, ba yadda banyi ba akan ya haƙura amma ya kasa fahimta, kuma wllh ni wani abun ma sbd shi nake, yanzu fa ba isasshiyar lfy garesa ba, idan Hajara ta dawo gidan nan sai anyi hatsaniya, ita fa ba a mata ta kyale, ga muƙarrabanta nan suma duk suna nan", Anty tace "toh shknn Adda, nida kaina zan dawo da ita, kuma zan ja mata kunne, amma dai nidae tinda tazo gidan da nake banga wata matsalar ba", Umma tace "uhmm ai hakuri ne yayi mata ƙaranci", Anty tace "ba damuwa zan mata nasiha, insha Allah da yamma zan kawota tinda mahaifinta yace ta dawo gida", Umma tace "toh sai kinzo Allah yayi albarka, a yiwa Kabiru godiya da ɗawainiya", Anty tace "laa ba komai Adda muma fa masu riƙe Hajar ne, sai anjima" ta katse kiran. ★Da misalin sha biyu da minti uku Anty na zaune palour Hajar ta fito daga ɗakinsu Hafsa ta shiga kitchen, fridge ta buɗe ta ɗauki ruwa ta sha snn ta fito, har zata koma ɗaki Anty ta kirata, dawowa tay ta zaune kan carpet tace "Anty gani", Anty ta ɗakko sababbin ƴan ɗari biyu dake gefenta ta miƙa mata tace "toh kema ga naki", Hajar ta ɗaga kai ta kalli kuɗin ta girgiza kai tace "A'a na Hafsa ne", Anty tace "ba zaki amsa ba", Hajar ta sunkuyar da kanta tace "ai Hafsa ya bawa", Anty tace "Eh naji Hafsa ya bawa, ita kuma Hafsa ta baki, ki amsa tin kafin rai na ya ɓaci", a hankali Hajar ta sa hannu ta amshi kuɗin ta ajiye kan cinyarta tana ganin aukinsu, kamarma gida biyu aka raba su aka bata rabi, Anty ta gyara zama tana kallonta da kyau tace "Hajar", Hajar ta ɗago kai tace "Na'am", Anty tayi softening voice tace "Haƙuri shine babbar ribar zama da mutane, duk wani mai haƙuri yana tare da waraka da kuma wadata shiyasa hausawa suka ce mahaƙurci mawadaci, akwai laifin da za ai maka ka rama akwai kuma wanda za ai maka ka haƙura, ammafa wanda za kayi haƙurin ya fi riba, Hajar ki zama mai haƙuri daidai mitsali ba wai wanda zaki zauna a cutar dake ba, kinsan me yasa nace ki zama mai haƙuri", a hankali Hajar ta girgiza kai, Anty tace "yawwa, nasan kinada haƙuri daidai naki amma ina so ki ƙara akai, ɗazu mukay waya da Adda tace Babanki yace ki koma gida yau ɗin nan, toh anjima da yamma zan mayar dake, kinsan dalilin da yasa mahaifiyarki ta haƙura da zama dake ta kawo ki nan dai ko?, ki ringa jin duk abinda mahaifiyarki ta gaya miki, tin kina ƴar tatsitsiya take haƙuri da kishiyarta a haka dai rayuwa take gara mata cikin zaman doya da manja, babu abinda ya cita dan tayi haƙuri, amma ke kin ƙi haƙuri ki zauna lfy, kimin alƙawarin cewa bazaki shiga gonar ƴan uwanki ba, kuma bazaki biye musu ayi tashin hankali dake ba..", da kyar Hajar tace "toh Anty, wllh abinda suke min ne yayi yawa nida Umma...." nan ta shiga gayawa Anty irin abubuwan da siblings ɗinta suke mata. Anty ta sauke wani ɓoyayyen ajiyar zuciya tace "Allah ya kyauta, haƙurin dai da nace shi zaki yi, ba abinda yake dawamamme wata rana sai labari, Wataqila ma ba zaki ƙara shekara ba a gidan zaki tafi naki tinda Allah ya baki manema sai dai fatan zaɓi na gari", Hajar tace "Toh Anty, nagode", Anty tace "yawwa, Allah ya yi miki albarka, tashi ki haɗa kayanki". Hajar ta kwashi kuɗin da suke kan cinyarta ta miƙe ta wuce ɗakinsu Hafsa, bata wani daɗe ba ta gama shirya kayanta tass, komai da komai ta haɗa, a ƙasan zuciyarta kam wani irin daɗi take ji zata koma gidansu wajen Ummanta. Da yamma kam suka shirya duk kansu harda Hafsa da Humaira, Hafsa dai bata ji daɗin wnn lamari ba, tinda mai Napep ya saukesu a daidai lungun ƙunshi Hajar take murmushi, Hafsa ce ta fara shiga gidan snn Humaira da Anty sai Hajar tare da almajirin da ya ɗakko jakar kayanta, da sauri Umma ta fito daga ɗaki tana musu brka da zuwa, Anty ta tsaya a tsakar gida suka gaisa da Baba dake zaune bisa darduma a ƙofar ɗakinsa, su Hafsa ma suka gaisa snn suka shiga wajen Umma. Hajar ta sunkuya gaban mahaifin nata tace "Baba barka da yamma", yace "ywwa Hajara", tace "ya kufan jiki?" yace "alhmdllh", tace "Allah ya ƙara afuwa" tayi zamanta nan kusa dashi. Sa'adatu ta leƙo ta ruɓaɓɓiyar windown ɗakin Maama tana yamutsa fuska tace "gayyar tsiya knn". Su Anty basu wani jima ba suka wuce gida, har bakin Titi Hajar da Sabra suka rakasu, Hajar ta kamo hannun Humaira ta damƙa mata rabin kuɗin da Antyn ta bata ɗazu tace karta gayawa kowa, bayan su Anty sun hau Napep sun wuce Hajar da Sabra suka koma gida. ★Washe gari Friday, a hankali Nurain yake sakkowa daga stairs, hannunsa riƙe da ƴar ƙaramar trolley da ya zuba kayansa, yayi matuƙar kyau cikin shigar ƙananan kayan da yayi all back, hakan sai ya sake haska caramel skin ɗinsa sosai, wata shegiyar Pcap black ya ɗora akan cikakkiyar sumarsa and that makes him to look younger than his age, Mami Noor sai Khausar da ta zo jiya ne zaune a main palourn, daman Noor da Khausar ƴan rakiyar airport ne, duk kansu Abaya suka saka ta Noor black ta khausar kuma maroon, Mami ta dubi ɗan nata tace "har ka fito Uthman?", a hankali ya ƙaraso kusa da ita yace "yeah Mami", Mami tace "toh ka yiwa Abba sallama naga time ya ja tinda jirgin 9am ne, yanxu gashi eight har ta gota". Majestically Nurain ya wuce palourn Abba, Abba ya fito daga bedroom ɗinsa yace "za ka wuce knn?", Nurain ya durƙusa yace "Eh Abba", Abba yace "wane zai kaika airport?", Nurain yace "Driver", Abba yace "toh Allah ya kiyaye, you call me right away after landing..", Nurain yace "insha Allah Abba" ya miƙe ya fita dan already takwas da minti goma ta gota, yana fitowa daga palourn Mami ta miƙe ta nufi part ɗinta, Nurain yace "Mami" sai kuma ya cire Pcap ɗin kansa ya ƙarasa gabanta, murmushi tayi ta shafa kansa tace "Allah ya tsare Son", baice komai ba ya rungumeta yana lumshe ido. har compound Mami ta raka sa, Noor da Khausar suka shiga back seats, Nurain ya kalli drivern da zai tuƙasu yace "bani key", ba musu drivern ya miƙa masa, ya san drivern baya gudu tinda dokar Abba yake bi, shi kuma yanxu sauri yake kar yayi missing flight, driver seat Nurain ya shiga drivern kuma ya shiga kujerar mai zaman banza, Garba da sauran ma'aikatan gidan na ɗaga masa hannu ya fita daga gidan, suna hawa saman titi Nurain ya take accelerator, ai kam few minutes of a ride suka isa airport, 9:05 dot jirginsu Nurain yayi take off, driver ne ya mayar da su Noor gida. Bayan minti goma da take off ɗin jirgin da zai tafi India jirgin da yazo daga Egypt yayi landing. a hankali passengers ɗin suke sakkowa daga matattakalar jirgin. wani murmushi Ruqayyah tayi bayan ta shaƙi iskar 9ja, a hankali ta ƙarasa fitowa daga airport ɗin bayan ta gama bin duk wasu procedures, wayarta ta ciro da handbag ta kira bolt dake within her location. after 15minutes bolt ɗin ta ƙaraso, a boot drivern bolt din ya saka mata jakarta snn ya buɗe mata back seat ta shiga. location ɗin da ta gaya masa nan ya ringa bi, wani irin bugawa zuciyar Ruqayyah tayi da taga sun shiga street ɗin gidansu. a ƙofar gidansu tace ma mai bolt ɗin yayi parking, a hankali ta sakko daga motar, tayi masa transfer ɗin kuɗinsa, ya ciro mata jakarta daga boot snn ya shiga motarsa ya juya ya fita daga street ɗin. Ruqayyah ta sauke ajiyar zuciya tana kallon gate ɗin gidansu, har lokacin wani irin bugu zuciyarta take tamkar zata bulluƙo, da kyar ta kai hannu tayi knocking a hankali.........✍️ More likes nd comments..... ehmmm update akai akai...😀 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche { 23..} Har biyar tana knocking amma ba wani respond, da ɗan karfi ta buga tana karanto duk addu'ar da tazo mata baki, mai gadi ne ya buɗe, idonsa duk a kumbure alamar bacci, bake bake yayi a hanya yace "wai waye ne?", Ruqayyah da bugun zuciyarta ya ƙaru tace "sallau bani hanya na wuce", zaro kumburarrun idanunsa yayi ya saki baki yana kallonta, lokacin guda kuma ya saki kabbara yace "alhmdllh, Allah mun gode maka da ka bayyana Hajiya ƙarama....", Ruqayyah ta yamutsa fuska tace "ba ɓata nayi ba sallau ƙasar waje naje", yace "barka da dawowa hajiya", da sauri ya matsa mata hanya, sai kace wacca take taka rurutaccen garwashin wuta haka take tafiya a ɗan madaidaicin compound ɗin gidan nasu, mai gadi biye da ita da jakar kayanta, ajiyar zuciya ta shiga jerawa da idonta ya kyallaro motar Daddy dake parking space, knn bai fita work ba, a bakin ƙofar shiga main building ɗin ta tsaya, mai gadi ya ajiye mata jakarta ya ƙara gaba. a hankali ta kai hannu ta murɗa handle ɗin ƙofar snn ta shiga ciki sai kace wata ɓarauniya, palourn ta tsaya ƙarewa kallo sai kace wani baƙonta, babu kowa sai motsin da take jiyowa daga kitchen. murya na rawa tace "Assalamu alaikum..." tana raba idanu. Momy ce ta fito daga kitchen hannunta riƙe da Mug, wani irin kamewa tayi tana kallon ƴarta ta da wani weird expression, Ruqayyah tace "Mommyy.." sai kuma ta nufi Mahaifiyar ta ta da sauri da nufin rungumeta, Momy tana ganin haka ta juya ta koma kitchen fuskarta ba yabo ba fallasa, a take Ruqayyah ta fara shan jinin jikinta, kitchen ɗin ta bita ta tarar da ita tana kaɗa kwai, hawaye har ya ciko idonta ta ƙarasa gaban Momy tace "Momy... Please let me explain", banza Momy tayi da ita ta kunna gas ta ɗora kasko ta fara frying omelette, kusa da ita Ruqayyah ta matsa tana ƙoƙarin riƙo hannunta, da wani irin zafin nama Momy ta hankaɗa ta, Ruqayyah ta afka can jikin cabinet ragowar tafarfasasshen ruwan zafi a kettle ya kwararo mata a hannu, ƙara ta fasa sbd zafin ruwan ta shiga sosa wajen a gigice. Momy ko a jikinta ta cigaba da juya kwan da take soyawa a kasko. sink Ruqayyah ta nufa da sauri ta buɗe famfo ta shiga zuba ruwan sanyi a wajen da ta ƙone, ai kam ta ƙone sosai domin kwa wajen yayi jajur har fatar ma ta tattare. Ruqayyah ba ta sake gigin zuwa kusa da Momy ba, sai yanxu take ganin girman laifin da tayi, ita ta sha abun ba zai kai haka ba, wai Momyn ta ce ta ƙonata da ruwan zafi amma ko a jikinta, lallai akwai lukutar masifa, Momy ta gama haɗa komai na breakfast ta jera a tray snn ta fita kitchen ɗin. Bayanta Ruqayyah tabi ta zube a gabanta lokacin da ta ƙarasa palour, duk ka ƙafafuwan Momy Ruqayyah ta riƙe ta fara kuka tace "dan girman Allah Momy ki saurareni, wllh ban aikata hakan wai don bana son auren ba, ina son auren wllh, ki tsaya nayi miki bayani dan Allah...", Momy ta ajiye trayn hannunta akan kujerar da ke kusa da ita. Ruqayyah na ɗago kai ta ɗauketa da wani gigitaccen marii a kuncin dama, bata gama dawowa hayyacinta ba ta sauke mata wani a kuncin hagu har saida ta kifa, Ruqayyah da ke ganin wasu white stars na haskawa a idonta ta rushe da matsanancin kuka tace "na shiga uku Momyyy kin tsiyayar min da ruwan ido", Momy na huci tace "shut up Ruqayyah, dabba ma ya fiki tunani, are you mad da zaki zo kina cemin na tsaya kimin bayani?, bayanin uban me zaki min nonsense, wllh kika sake magana saina sumar dake Coward..." da haka Momy ta ɗauki trayn ta wuce part ɗin Daddy, Ruqayyah kuka take kamar ranta zai fita, ba ta taɓa tunanin abin zai dagule haka ba, ta ɗauka faɗa kawai za ai mata amma shine harda mugayen maruka, toh Momy ma knn inaga Daddy, da sallama Momy ta shiga palourn Daddy, Daddy da ke kallon news ya amsa sallamar yana nazarin expression ɗin fuskarta, Momy daurewa kawai take har ta gama serving ɗinsa abinci, Daddy yayi sipping tea yana kallon fuskarta yace "what happened?", remote control ta ɗauka ta ƙara volume tace "A'a, ba komai", yace "alright indai akan Ruqayyah ne ai jiya naje police station na shigar da report, yau ma zan koma naji ya ake ciki", Momy ta sauke ajiyar zuciya tace "Ohk idan ka koma sai kasa ayi closing case ɗin cause Ruqayyah tana gidan nan yanzu haka..", bread ɗin hannunsa ya ajiye yace "Ruqayyah na gidan nan?", Momy tayi resting a jikin kujera tace "Eh, ba ta daɗe da shigowa ba, she's perfectly fine..", gyaɗa kai Daddy yayi ya cigaba da cin abincinsa yace "daman na gaya miki don't stress yourself about Ruqayyah's missing, gashi nan ta dawo aii..", Momy ta sauke numfashi a hankali har lokacin zuciyarta zafii take. saida Ruqayyah taci kukanta ta ƙoshi snn ta ja jiki ta shiga room ɗinta, toilet ta shiga ta wanke fuskarta ta fito ta tsaya a gaban mirror tana kallon fuskar, a hankali ta kai hannu ta shafa kuncinta inda ya kumbura da shatin yatsun Momy biyar ciff. fita tayi daga ɗakin ta kama hanyar part ɗin Daddy, da sallama ta murɗa handle ta shiga kanta a ƙasa, kallo ɗaya Daddy yayi mata ya kawar da kai, Ruqayyah ta zube nan kan carpet kusa da ƙafarsa tace "Daddy ina kwana..", without looking at her yace "lfy Ruqayyah, kinga dama kin dawo knn", shiru tai ba tace komai ba, Momy dake karkaɗa legs tace "fita malama, ban san ganinki...", Daddy ya ɗaga mata hannu yace "No leave her, Ruqayyah kin dawo ko?, toh shknn sannu da zuwa", hawaye ne ya zubo idon Ruqayyah ta ɗago kai tace "Daddy I'm very sorry...", yace "No Ruqayyah sorry for yourself, ke kikai loosing.." da haka ya miƙe ya shiga bedroom ɗinsa, Momy tabi bayansa da kallo snn ta miƙe ta fita palourn, da kyar Ruqayyah ta miƙe itama ta fita daga palourn, duk wani hope da karsashinta ya tsiyaye, sosai reaction ɗin Daddy ya dagargaza mata zuciya, toh da wnn action ɗin ai gara shima ya falla mata mari kamar Momy, jakar kayanta ta ɗauka ta shiga room ɗinta sai kace wacca kwai ya fashewa a ciki. ★Hajar ce tsaye gaban wardrobe tana jera kayanta, tana gama jera kayan ta linke Ghana most gon ta ɗaga katifar gado ta saka, tsintsiyar laushi ta ɗauka a bayan ƙofa ta fara share ledar ɗakin, tass ta share ta gyara ko ina, ta kunna turaren tsinke, zanin wanka ta ɗaura a ƙirji snn ta cire kayan jikinta, ta saka dogon hijab ta ɗauki kwandon soso da sabulu ta fita. Umma na yanka albasa cikin ƙullun alale, Hajar tace "Umma nazo na shafa miki manja a gwanayen?, tin ɗazu na wanke yanxu nasan sun bushe", Umma ta kalleta tace "ba wanka za kiyi ba?", Hajar tace "Eh wanka zanyi", Umma tace "toh jeki kiyi wankanki na karasa", Hajar tace "tom" ta wuce gaban tukwanen ruwa, bokiti ta ɗauka ta fara kanfatar ruwan tana zubawa. tana gama cika bokitin ta ɗauka ta wuce hanyar toilet, da gudu Nabilah da ta fito daga ɗaki tazo ta bangajeta ta shige banɗakin, Hajar tayi ƴar ƙara sbd bokitin ruwan da ya saukar mata a ƙafa, a fusace Hajar ta buɗe baki za tay magana sai kuma tayi shiru ta tsaya tana kallon ƙofar banɗakin, juyawa tayi ta dawo tsakar gida ta ɗauki kwandon da ta kife gwangwanaye ta ajiye kusa da Umma, ta koma ta ɗakko tasar manja da audiga suma ta kai gaban Umma ta ajiye, durƙusawa tayi ta fara shafa Manjan jikin tin, Umma tace "yawwa Hajara haka nake so, ko sun takaleki dan Allah karki kulasu", Hajar tayi murmushi tace "insha Allah Umma..", Umma tace "yawwa Allah ya yi miki albarka". sai bayan minti ashirin snn Nabilah ta fito daga toilet tana yatsine, ta kalli Umma da Hajar ta buga uban tsaki tace "annoba" ta shige ɗaki. Hajar ta miƙe ta sake ɗiban wani ruwan ta shiga wanka. Nabilah da ta shiga ɗaki ta dubi Sa'adatu tace "banza, wai ke Sa'adatu wane irin gigin bacci kike ne?, sai ki ringa tattaɓa jikin mutum sai kace wata ƴar yaye, wllh jiya da kyar nayi bacci duk kin ƙadabaibaiye ni sai kace wata ƙadandoniya, mtswww", wani shu'umin kallo Sa'adatu tayi mata tace "ina Maama?", Nabilah tace "ta tafi gidan Balaraba ita da Maimuna", Sa'adatu tayi wani murmushi mai ma'ana daban daban tace "Nabilah kina so ki samu mazajen kuɗi?", Nabilah ta zaro ido tace "so kai", Sa'adatu ta dafa kafaɗarta tace "wllh kizo na haɗaki da zeenatu da Mabaruka, zaki samu kuɗin a wajensu wllh tallahi..", Nabilah tace "Allah, aikatau zan musu?", Sa'adatu tace "lah lah lah ko ɗaya babu aikin da za ki musu, rayuwa irin ta wayayyun mata kawai zaku ringa yi, kiji daɗi ina gaya miki malam, kici mai kyau ki sha mai, ki kwanta a lafiyayyen gado fatarki ta sha raɓa, ga kuma uban kuɗi a aljihunki", Nabilah tace "toh wai mene rayuwar wayayyun matan?", Sa'adatu tace "rayuwar ƴanci knn ba ruwan mu da maza mu kaɗai mun ishi kan mu", Nabilah ta taɓe baki tace "mtswww, dalla malama ni ban fahimta ba", Sa'adatu ta hura hanci tace "idan kin yarda gobe zani gidansu saiki rakani kiga irin rayuwar da nake nufii", Nabilah ta gyaɗa kai tace "zanyi tunani". Bayan an sakko daga masallaci sallar juma'a Baba ya shigo gida tare da Mu'azzam, nan tsakar gida Baba ya zauna daga jikin inuwa. Mu'azzam ya durƙusa gabansa yace "Baba zan wuce aiki", Baba yace "har yanzu baku gama sakawa gidan tiles ba?", Mu'azzam yace "mun gama tarazo mukewa farfajiyar gidan", Baba yace "toh Allah ya temaka, ka kai Maimuna makarantar da nace ka mayar da ita?", Mu'azzam ya shafa kai yace "A'a Baba, ai ranar Litinin ɗin muna asibiti", Baba ya gyaɗa kai yace "toh jibi saika kaita", Mu'azzam yace "tom" ya miƙe ya leƙa ɗakin Umma yayi mata sallama snn ya fita. Baba ya ringa kwalawa Maimuna kira amma shiru, Nabilah ce ta fito tace "Bata nan sun fita da Maama", yace "ina Sa'adatu?", Nabilah tace "tana ɗaki", yace "kira min ita", Nabilah tace "tom" ta koma ɗaki, Sa'adatu sai gyatsine take tinda taji komai, Nabilah tace "Eh ai kinji dai ko?, saiki je". Sa'adatu ta fice fuu ta sha kunu, can gefen Baba ta koma ta rakuɓe tana zumɓuro baki, Baba yace "toh kema ki shirya jibi Mu'azzam zai mayar dake makaranta ke da Maimuna..", zaro ido tayi tace "Baba makaranta fa kace", yace "Eh, idan kuma ba kya son karatun saiki fito da miji na aurar da ke, itama Nabilah na bata lokacii..", Sa'adatu ta girgiza kai tace "wllh ni bana son aure, gwara na koma makaranta", Baba ya ringa kallonta kafin yace "tashi ki ban waje, saiki shirya ranar litinin...", bazar bazar ta koma ɗaki tana taɓe baki wai ita shagwaɓaɓɓiya. ★Raqayyah ta sake dialing numbern da tayi saving da dearest a wajen karo na ashirin tin dawowarta gida, abu ɗaya dai ake ta nanata mata wato the number you dial is switched off, wurgi tayi da wayar akan gado tana jin wani zafi a zuciyarta, she madly missed his stern voice, sound of his deep breathe out, komai nashi tayi missing sosai. lumshe ido tayi tana jin tsantsar kewarsa a duka sassan jikinta, maganarsa ta ƙarshe da tayi hitting eardrums ɗinta wacca she'll never forget ( sleep tight for today tomorrow in my arms), a fili tace "Soon dearest". towel ta ɗora a jikinta ta shiga wanka, ɗaure da towel ta fito tana tsane fresh fair skin ɗinta da hand towel, ta buɗe press ɗinta, ganin babu kaya aciki ta mayar ta rufe, ta tina ashe fa kayanta na ɗakin Momy acikin ɗaya daga cikin boxes ɗin lefenta, Abayar da ta cire ta mayar snn ta fita zuwa ɗakin Momy, a hankali tayi knocking ta shiga, ta tarar Momy ba ta nan don haka ta fara surveying ɗakin da idonta tana neman boxes ɗin lefenta. har press ta buɗe amma ba taga alamar akwatunan lefe ba, tana rufe press Momy ta shigo, Momy ta kalleta sama da ƙasa tace "kee me kike yimin a ɗaki?", Ruqayyah tayi gathering courage tace "amm Boxes ɗin lefe nake nema zan ɗauki kaya", wata muguwar harara Momy ta galla mata ta nuna mata wata box dake kusa da shoe shelf tace "ga kayan ki can, ba ki ma da hankali da kike neman wasu akwatunan lefe, toh kwananki biyu da guduwa muka mayarwa da Nurain kayansa..", da ƙarfi zuciyar Ruqayyah ta buga, ji tayi kamar ta fita daga ƙirjinta ta koma ciki sbd anan take jin bugunta, a lokacin idan akace mata ta haɗiyi zuciyarta ne to fa ba za tayi musu ba. lips ɗinta na zikiri tace "Momyy... wllh banji me kika ce ba, me aka mayar?".......✍️ i know it's short, just manage..., Busy and lazy lol 😉 🥴 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {24..} Momy ta ringa kallonta kafin tace "Au maimaita miki zanyi knn, kada Allah yasa kiji, take your belongings and leave my room idiot", Ruqayyah da har lokacin bata gama recover ba tace "Momy call me anything amma dan Allah ba a mayar da lefena ba ko?", tsaki Momy tayi ta janyo box ɗin kayan ta dire mata tace "hmmm, ƙarya zan miki, ko na taɓa miki ƙarya ne?", wani kuka ne ya kwace mata tace "A'a Momy, wllh biki taɓa min ƙarya ba", Momy ta haɗe girar sama da ƙasa tace "toh sai kuma me?, ba dai auren ne bakya so ba har da su guduwa?, toh everything was cancelled, ba wata maganar aure, tinda kin fi son ki zauna a gida nida ke muna haɗa kafaɗa toh shknn ai ga fili ga mai doki, waccan ɗakin dai kwalli ɗaya tak da shi kaɗai zaki tsira...", Ruqayyah ta sake rushewa da kuka tace "na shiga uku na lalace, Momy kun karanta lettern da na bari kuwa?", Momy tace "ai lettern taki ce tasa akay cancelling komai, ki ɗauki kayanki ki fita, mu dosa zama nida ke a gidan nan tinda haka kike so", da gudu Ruqayyah ta fice a ɗakin tana kuka sosai, Momy tace "Au kayan fa.", Ruqayyah na shiga ɗakinta ta zube a kan gado, kuka ta ringa yi kamar ranta zai fita, wai an mayar da kayan lefenta kuma anyi cancelling aurenta da dearest, sharce hawayen da ya jiƙa mata cheeks tayi ta janyo wayarta, dialing numbernsa ta sake yi, ai tasan dearest ɗinta bazai fasa aurenta ba, Momy da Daddy ne kawai suke zancensu, tinda tayi masa message tace ya jirata tana nan dawowa garesa ai end of discussion, kuma she's very sure ya yarda da ita, wasu twin tears ne suka zubo a cheeks ɗinta jin wanda take da hope a kansa har yanzu wayarsa switched off, sister ɗinta Kulsoom ta shiga kira, Kulsoom na ɗagawa Ruqayyah ta fashe mata da kuka tace "na mutu na lalace sister..", a rikice Kulsoom tace "Ruqayyah kina ina?", Ruqayyah tace "am home sister, ina gida, ina cikin lukutar masifa da bala'i", Kulsoom ta sauke ajiyar zuciya don ba ƙaramar firgita tayi ba tace "toh wace masifa kuma?, tinda kinga dama kin dawo gida ai shknn", da muryar kuka Ruqayyah tace "mayarmin fa da kayan lefena sukai kuma wai anyi cancelling aurena da dearest..", tsaki Kulsoom tayi tace "ke dalla malama kin cika min kunne, uban wa yace kice ba kya son auren, ai abinda kike so akai miki", Ruqayyah ta zaro ido tace "billahillazi la'ilaha illa huwa ni bance bana san auren ba, wllh bance haka ba..", katseta Kulsoom tayi tace "dakata malama, kinsan irin baƙin fenti da kikai mana kuwa?, kin san irin kunyar da kika bamu kuwa, har yanzu tabon abinda kika aikata bai goge ba, dan wulaƙanci kuma kika kashe wayarki, da farko ma dai ina kika je?", Ruqayyah ta haɗiyi wani ɗaci tace "Egypt naje", Kulsoom tace "au ƙasar ma kika bari, toh me ya kaiki Egypt?", Ruqayyah tace "later zan miki bayani sister, ni yanzu so nake ki tayani bawa Momy da Daddy haƙuri don Allah su bar maganar cancelling auren nan", ta rushe da matsanancin kuka tace "wllh i can't imagine me loosing Nurain, na shiga uku na lalace, help me sister..", Kulsoom tayi tsaki tace "lallai Ruqayyah surely you need a Psychiatrist don kwakwalwarki ta taɓu..", Ruqayyah tace "naji ko ma me zaki ce kice nidai ki temakamin", Kulsoom tace "ehmm toh ki kira ya Aysha wataqila ta taimaka miki nikam I can't face our parent da maganarki, sai anjima girki nakewa mijina..", ƙif ta kashe wayarta, Ruqayyah ta ringa kallon screen ɗin wayar baki buɗe. kamar wata marainiya haka ta koma ta kwanta tana hawaye, saida akay Sallahr magrib snn ta tashi tayo alwala tayi sallah, zaune tayi kan prayer mat ta rasa abinda ke mata daɗi, ƙarfe tara da rabi na dare ta tashi ta fito palour, kitchen ta shiga sbd ta samu wani abun ta zuba a cikinta, tin abincin jirgi babu abinda ta sake ci ko ruwa ba ta sha ba, kwata kwata ma bata da wani appetite, fridge ta buɗe tana neman koda fruit ne, ai kam dai babu fruit, glass cup ta ɗauka ta bude fresh milk, rabin cup ta zuba snn ta mayar da bottle din madarar fridge, sai kace mai shan maganin haka ta ɗaga ta kwankwaɗe tana yamutsa fuska, har wani amai ne ke taho mata. room ɗinta ta koma ta kwanta tana jin kanta na juya mata, har dare ya raba babu alamar bacci a idonta, kawai tunanin moment ɗinta da Nurain take, idan ta tuna cewa wai an mayar da lefe kuma an fasa aure sai hankalinta ya ɗugunzuma. sai wajajen Asuba snn bacci ɓarawo ya figeta. ★Washe gari Sa'adatu ta cakare kwalliya cikin matsattsun kayan da ta saba snn ta zumbula hijab har ƙasa, ta dubi Nabilah dake saka riga tace "wllh kin fiya nawa Nabilah, tin ɗazu baki shirya ba", Nabilah tace "ke Malama sauri fa nake yi", Maimuna tace "Sa'adatu nima na shirya mu tafi tare.." haɗe gira Sa'adatu tayi tace "A'a yi zamanki ban gayyace ki ba", Maimuna ta taɓe baki tace "ku kuka ga duhu da kunje dani da ni zan biya kuɗin Napep zuwa da dawowa", Sa'adatu ta yatsine fuska tana mata kallon hadarin kaji tace "ji faƙiriyar talaka, ni za kice zaki biyawa kuɗin Napep, mtsww dalla can riƙe tsiyarki, ke daman ba cin arziƙinki ake ba uwar mammaƙo kawai...", Maimuna tace "A'a kinga malama karki gayan ba daɗi mana, tinda kince dai ba zaki dani ba ai shknn magana ta ƙare". Sa'adatu tace "kin samawa kanki salama kuwa". Maama ce ta shigo da kwanon abinci tace "kai jama'a har sai rana tayi zafi baku tafi ba", Sa'adatu taja dogon tsaki tace "wllh Nabilah ce, sai kace ba ƙaruwarta ba, tayi abu da jiki sai wani salalo-salalo take kamar dodon koɗi", Nabilah tace "kai jaraba nagama mu tafi" ta zaro takalminta daga karshin gado tana kwamawa, Maama tace "ke Nabilah dan Allah ki tsaya ki musu abinda suke so kema ai kya fito gari, ɗan kuɗin nan ki ringa samu muma ki tsammana, karki musu kauyanci da gidahumanci da sakarci", Nabilah tace "idan abin baifi ƙarfina ba zanyi", Maama tace "yawwa ku salallaɓa ku fita karku bari malam yaji motsinku". tamkar munafukai haka suka fita ɗakin suna tafiya a hankali. Hajar da ke tsakar gida tayi musu kallo ɗaya ta ɗauke kai ta cigaba da abinda take. bakin titi suka fita suka tsarar da Napep, Sa'adatu ta faɗi unguwar da zai kaisu, mai Napep yana cewa zashi ba wani ciniki Sa'adatu ta shiga, Nabilah tabi bayanta tace "ba kuyi ciniki ba", mai Napep yace "kuɗin ku dubu ɗaya ne", Nabilah ta zaro ido za tay magana Sa'adatu tace "Allah ya kaimu lfy", suna hawa saman titi Sa'adatu tace "sai munje zaki fahimci me nake nufi..", Nabilah dai tace "uhmm". tafiya mai nisa sukay suka isa unguwar da zasu, a bakin wani annakakken gida suka sauka, Sa'adatu ta fello duba ɗayar mai Napep ta basa. wani lafiyayyen gida suka shiga, Nabilah sai kalle kalle take, Sa'adatu ta riƙe hannunta har suka shiga cikin gidan. direct wata ƙofa Sa'adatu ta murɗa sai gasu a wani katafaren palour. Zeenatu da ke zaune kan sofa tana cin cake ta juyo jin ƙarar ƙofa, zaro ido tayi ganin Sa'adatu, ta taso da sauri ta rumgumeta tace "nayi masifar kewarki baby", Sa'adatu tace "nima haka, ina baby Mabruk?", Zeenatu tace "tana ɗaki tare da Teema", Sa'adatu tace "hegiyar kati yaushe tazo?", Zeenatu tace "jiya, wace wnn?" ta nuna Nabilah, Sa'adatu tace "mu shiga daga ciki nayi miki bayani". Zeenatu ta nunawa Nabilah kujera tace "zauna ga guri", Nabilah ta zauna tana kallon damfareriyar TVn dake palourn, kitchen Sa'adatu ta shiga ta jibgo kayan ciye ciye tray guda, a gaban Nabilah ta girke tana mata wani shegen murmushi. Nabilah ta ringa kallon kayan ciye ciye yawunta na tsinkewa. kusa da Zeenatu Sa'adatu ta zauna ta ɗauki cake ɗin da take ci ta kai baki, Zeenatu ta rage murya tace "itama ƴar hannu ce?", Sa'adatu tace "ke ƴar uwata ce fa, sabuwa ce fil a leda", Zeenatu tace "Allah itama ta amince ta shiga ƙungiyar tamu?..", Sa'adatu ta dubi Nabilah tace "Eh, ta amince", Zeenatu tayi wani makirin murmushi tace "gaskiya ni zan buɗeta daga kwali, bari na jarabata", Sa'adatu tace "toh", Zeenatu ta miƙe tana gyara kwalar rigar da ta bayyana rabi da kwatan ƙirjinta tace "baiwar Allah ya sunanki?", Nabilah da ke yagar naman kaza tace "Nabilah", Zeenatu tace "wow sunanki yayi min daɗi, taso muje", Nabilah ta ajiye naman hannunta tace "ina?", Sa'adatu tace "wai me Maama ta gaya miki ne, bafa cinyeki za tayi ba aikinki zata nuna miki". Nabilah ta miƙe tabi bayan Zeenatu suka shiga wani ɗaki. ko minti goma ba suyi da shiga ba Nabilah ta fito a fusace hannunta riƙe da gyalenta, Sa'adatu ta saki cake ɗin da take ci ta miƙe tsaye ganin Zeenatu ta fito itama a fusace, a hasale Zeenatu tace "ki fita da wnn bagidajiyar daga gidan nan Sa'adat idan ba haka ba nasa karnuka na su yagalgala namanta", Sa'adatu ta dubi Nabilah da ke huci jikinta na kyarma a hankali tace "mene haka Nabilah?", a hasale Nabilah ta ɓarka mata ashar snn ta wuce fuu ta fita daga palourn. da sauri Sa'adatu tabi bayanta, wani uban sauri Nabilah take zabgawa har ta doshi gate, tana fita waje tabi layin tana tafiya zuwa bakin titi, Sa'adatu biye da ita har suka ƙarasa main road. babu wanda yace da wani uffan har aka saukesu a bakin lungunsu, Nabilah na fita ta shiga lungunsu da sauri, Sa'adatu ta biya kuɗi snn ta biyota, adaidai ƙofar gida Sa'adatu tace "kin san bazaki iya ba shine kika zubar min da mutunci da kima", a karo na farko Nabilah tace "mutuncinki da kimarki duk sunci abu ta kaza kazan su, da ke da ƙawayen naki duk mahaukata ne ƴan iska tsinannu, dabba kawai, jaka mara ilimin addini bare na boko..", Sa'adatu ta mulmulo ashar tace "jar bala'i daga temako shine kike zagina", Nabilah tace "an zage kin kiyi abinda zaki.." ta wuce cikin gida a fusace. da gudu Sa'adatu ta bita ta cakumota a tsakar gida, Nabilah ta juyo ta wanka mata wani mari na bazata, habawa ai hannun Nabilah bai gama leveling ba Sa'adatu ta ɗaga nata itama ta wanke ta da mari, lokaci guda suka kaure da dambe, Umma da tin shigowarsu take kallonsu tana daga tsaye inda take kwashe kaya akan igiya tace "kai ku bari mana..", Maama ta fito da sauri tana tafa hannaye ta shiga raba su, dambe kawai suke ba ji ba gani, Hajar dai na tsaye daga bakin ƙofar ɗakin Umma tana kallon ikon Allah, saida zanin Maama ya kwance garin raba faɗa amma basu saduda ba, Maama faɗi take "ba zaku bari ba, ke Sa'adatu bari mana, Nabilah ba magana nake miki ba, ku bari nace, ku wuce ɗaki kuyi acan cikin sirri...", Maimuna ma dai ƴar kallon ta zama tana dariya ƙasa ƙasa, ba wai su ƴan uwa ba aka wareta aka ƙi tafiya da ita ai gashi ba aje ko ina ba ta jagwale musu. da kyar Maama ta ɓamɓaresu tace "hauka kuke, mene haka?", sai huci suka suna kallo juna sai kace wasu maƙiya ba waɗanda suka fito ciki ɗaya ba, Sa'adatu ta goge bakinta da ke fitar da jini tace "wllh saina rama", Nabilah tace "idan kin fasa baki haifu ba", bangaje Maama Sa'adatu tayi ta cakumo Nabilah, damben da yaci uwar na farko suka ɓarke dashi, har ƙasa Nabilah ta yaga zumbulelen hijab ɗin Sa'adatu, takaici yasa Sa'adatu ta kama doguwar rigar Nabilah ta dire mata ita har ƙasa, cikin bacci Baba ya jiyo hanyani, fitowa yayi ya tsaya yana kallonsu. ɗakinsa ya koma ya ɗakko carbi, yana fitowa ya nufesu ya shiga tsula musu a jiki, ai dole suka rabu sbd zafin carbin, da hannu Baba ya nuna su yana so yayi magana amma wani tari ya sarƙesa, tamkar zai fitar da ruhinsa haka yake tarii, Umma tazo ta janyesa ta shiga dashi ɗaki. Maama da takaicin ƴaƴan nata ya turnuƙeta tace "abinda ku ka tarka knn?, ciwon zuciya za ku samin iyee?, dambe sai kace karnuka, me ya haɗa ku?", Nabilah da ta cukuikuiyo rigarta da ta ɓarke tace "wai wnn mahaukaciyar yarinyar shine ta kaini wajen tumakan ƙawayenta har suna ƙoƙarin taɓamin jiki...", Sa'adatu tace "ƙarya take munafuka, mai kai a tukunya kawai, wai fa aikinta za a nuna mata shine ta fara hauka da ballagazanci", Maama ta riƙe haɓa tace "mu shiga ɗaki karku tonawa kanku asiri a bainan nazi a tambara min ku, ku wuce ɗaki", Maama ta haɗa kawunansu ta turasu ɗaki. ★A hankali Hajar take cin abincin da ke gabanta, yamutsa fuska take cike da rashin jin daɗi sbd lower abdominal cramp da ke damunta, tin safe ta tashi da ciwon gashi har dare bai dena ba saidai yana lafa mata time to time, abincin ta ture ta sha ruwa ta haye gado ta kwanta gefen Sabra, Umma ce ta shigo ɗakin, ganin Hajar ta kwanta ga ragowar abincinta nan bata cinye ba ta kira sunanta, Hajar ta miƙe zaune tinda ba bacci take ba tace "Na'am..", Umma tace "ya baki cinye abincin ba?", Hajar na yamutsa fuska tace "na ƙoshi", Umma tace "ya ciwon yayi sauƙi?", girgiza kai Hajar tayi tace "A'a", Umma tace "toh taso muje chemist tinda yaƙi lafawa gwara ayi miki allura kawai", zaro ido Hajar tayi tace "Allah bana son allura, magani zan sha", Umma ta ringa kallonta kafin tace "toh bari na kira Mu'azzam sai ya taho miki da magani" ta ɗauki wayarta ta kira Mu'azzam, yana ɗagawa tace "kafin ka shigo gida ka biya ta chemist ka siyowa Hajara magani", yace "wane iri?", Umma ta kalli Hajar snn ta mika mata wayar tace "fada masa sunan maganin da kike sha ɗin", Hajar ta amshi wayar ta gaya masa. bayan kamar minti sha bakwai sai gashi nan ya shigo da maganin, tinda Hajar tasha magani ta samu relief, daman duk month sai ta samu cramp though ba ta flowing heavily amma dai abin na wahalar da ita. washe gari kam sumul ta miƙe ta fara harkokinta, yau dai kam Baba ya fita aiki, Umma kuma ta shirya zuwa Wajen Iya don haka Hajar ta bari a gida, Hajar na zaune tsakar gida akan kujera tana cin gyaɗa, Sabra ta shigo tace "Adda zan ci abinci", Hajar ta tashi ta zuba mata taliyar hausa da manja da yaji tinda ita ta dafa, Sabra ta amshi abincin ta wanko hannunta ta zauna tana ci. Hajar tace "ki yi sauri lokacin islamiyya ya kusa", Sabra tace "toh" ta cigaba da zuƙar taliyarta cike da yarinta. Maimuna ce ta fito daga ɗaki da ɗaurin ƙirji sai kace wata tsohuwar guzuma, kan Sabra da ke cin abinci ta tsaya tace "ke je ki wajen Iliya mai awo ki aunomin shinkafa ƴar hausa gwangwani huɗu" ta faɗa tana miƙa mata kuɗin hannunta, Sabra tace "toh bari na ƙarasa cin abinci", fatali Maimuna tayi da kwanon abincin tace "kee ni sa'ar kice ko sa'ar uwarki da zan aikeki kice sai kin gama cin abinci", Sabra ta sunkuyar da kai tana hawaye ta ƙi amsar kuɗin, damƙota Maimuna tayi ta miƙar da ita tsaye ta kifa mata mari tace "ba magana nake miki ba", ɗaure fuska Hajar tayi tamkar wacca bata taɓa murmushi ba tayi wurgi da gyaɗar da take ci. gam ta riƙe hannun Maimuna da ta ɗaga zata sake saukesa akan fuskar little sister ɗinta......✍️ Likes comment and share my beautiful fans.😍 🤗 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {25..} Maimuna ta wancakalar da hannunta tace "dalla malama cikani", Hajar bata tanka mata ba ta fizge ƙanwarta da ke kuka sosai, hawaye ta share mata tace "je ki wanke fuskarki, zan zuba miki wata taliyar, yi sauri kinji yarinyar kirki kar ayi miki dukan makara a islamiyya", a hankali Sabra ta wuce bakin rariya, Hajar ta ɗauki ledar gyaɗarta ta zauna ta cigaba da ci, baki buɗe Maimuna ke kallonta kafin ta mulmulo ashar tace "kut melesi, ke shegiya Hajara ina ruwanki dani, ina yiwa ƙanwata hukunci za ki shiga, ke asu wa iyee?, shegiya da ke kawai ƴar gaba da fatiha..", Hajar da zuciyarta ke tafarfasa hundred degree celsius ta mike tana kallon Maimuna, ji take kamar ta fizge tsumman zanin da tayi ɗaurin ƙirji dashi saita nuna mata aikin shegantaka da hujja, da sauri ta shige ɗaki zuciyarta na zafi don tabbas in ta tsaya zata iya waskatarwa da Maimuna mummuƙe. Maimuna ta koma bakin ƙofar ɗakin tace "ashe dai tsoro ne, da ki tsaya mana ki ga yadda zan yagalgala ki, da saina waskace miki ƙugun nan mai zubin na ƴar duniya, shegiyar nunar rana...", Hajar kam zama tayi kan leda ta dafe kanta, calming kanta kawai take cause tana so tayi keeping promise ɗin da tayi, wllh ba daban promise din ba da sai ta gayawa Maimuna maganar da har ta mutu bazata manta da ita ba. wai itace shegiya nunar rana mai ƙugun ƴan duniya duk ita kaɗai, shiyasa bahaushe yace muni tudu ne ka taka naka ka hango na wani, wai har Maimuna ce za tace mata nunar rana ita ba taga kanta bane ai tafi kama da nunar rana tinda itace me bleeching irin na ƴan tasha iya fuska, kuma ƙugu ta godewa Allah yafi nata da yake flat sai kace an ɗaurawa muciya zani, gsky ita fa an mata katsalandan a al'amura, itafa haƙurinta bai kai nan ba wllh, bai kai gejin da za ayi mata rashin mutunci ko a gaya mata magana ta haƙura ba, amma dai yau Maimuna taci darajar masu daraja, ita kaɗai ta ringa sauke ajiyar zuciya tana huci, har Sabra ta shigo tayi shirin islamiyya tace "Adda zan tafi", Hajar ta ciro 20naira a bayan wayarta ta miƙa mata tace "toh ga kuɗin makaranta", Sabra ta amsa tace "na tafi" ta ɗau jakarta ta fita. Hajar ba ta sake fita tsakar gida ba, wayarta ta janyo ta buɗe data ta shiga whatsapp, yaushe rabon da ta shiga ita chatting bai dameta ba, saida tayi upgrading Whatsapp ɗin sbd ya zama outdated, ai kam ga unread messages nan rututu daga friends ɗinta na islamiyya da boko, message ɗin Zainab ta gani a sama ƙasansa kuma na Hafsa, tana gama karanta message ɗin Zainab ta taɓe baki ta shiga mayar mata da reply tinda online take, Zainab tayi mata reply da "Hajar kiji tsoron Allah daga tambayarki mutum sai kice kin saita masa hanya", Hajar ta yamutsa fuska bayan ta karanta ta rubuta mata "uhmm ke nifa ban ma basa fuska ba, na gaya miki ya sayyadi ya maye ko ina". Zainab ta turo da steaker ta duka. murmushi Hajar tayi ta rubuta "ban jin duka, malama ki canza topic, bana son wnn zancen", Zainab ta turo "Allah ya bawa mai sonki haƙuri", Hajar ta tura mata "Ameeennnn.." sosai chatting ɗinta da Zainab ya sanyaya mata zuciya, sai bayan sallar la'asar Umma ta dawo gida, Hajar ta mata sannu da zuwa tace "ya hajiya Iyalluwa", Umma ta mata daƙuwa tace "in kinje kya kirata da Iyalluwa, me kika dafa da rana", Hajar tace "taliyar hausa da manja", Umma ta cire hijab ɗinta tace "waii wnn ba cimar da malam bace, tashi ki tankaɗen gari na ɗora tuwo", mikewa Hajar tayi tace "maƙiyin Abdallah knn, ya tsani tuwo, duk ranar da akay tuwo bazai ci ba saidai a dafa masa indomie", garin tuwo dake cikin buhu ta ɗauka ta fita, saida ta hura mangal ta ɗora ruwa snn ta zauna tankaɗen, tana gama tankaɗen already ruwan ya tafasa tayi talge. Maama ta fito toilet ta ajiye butar hannunta bakin rariya, har zata shiga ɗaki sai kuma ta fasa ta tsaya akan Hajar tace "kee sbd baki da kunya da mutunci har ni zan aiki Sabra ki hanata zuwa", Hajar ta cigaba da gyara kayan miyar da za tay miya tace "ni ba hanata nayi ba", Maama ta lafto ashar ta danƙara mata tace "za kimin shiru ko saina kifa kanki a talgen tuwan nan", Hajar ta turo baki ta miƙe zata bar wajen, fuzgota Maama tayi ta daki bakin tace "nace rashin kunya zaki min kike turomin baki sai kace an mari kare", Hajar ta kalli ƙasa tana jin kamar ta kurma ihu sbd takaici, rankwashi Maama ta zuba mata a kai snn ta hankaɗeta, saura ƙiris ta faɗa kan tukunyar dake kan wuta tana zaɓalɓala da talgen tuwa, Maama tace "saina miki ƙafa ɗaya idan kika sake shiga gonata", da sauri Hajar ta shiga ɗaki sbd kukan da ya cicciyota, a ƙasa ta zube ta rushe da kuka, Umma ta kashe rediyon da take ji jikin waya tace "lfy Hajara?", Hajar dai ta kasa cewa komai kawai kuka take zuciyarta na tafarfasa, ita babban takaicinta da aka hanata ramawa, sosai hankalin Umma ya tashi tace "ciwon marar ne?", Hajar na shessheƙar kuka tace "ba waccar matar bace da ƴaƴanta", Umma ta kunna rediyonta tace "ai kam aiki ya sameki, ruwan idonki daf yake da tsiyayewa, kin gama haɗa miyar", Hajar ta girgiza kai tace "A'a, kayan miyar fa nake gyarawa waccar matar ta takura min", Umma ta miƙe tace "bari kiga na ƙarasa kar magariba tayi ba a gama abincin dare ba" ta fita. washe gari Monday Mu'azzam ya fito tsakar gida da kuftarsa hartin da wando, agogon wayarsa ya duba yaga ƙarfe takwas harta gota, tsaki yayi ya jingina da bango, shi kam yaga ta kansa Baba ya haɗasa da ƴaƴan Maama marasa ta ido, shi ko kallo ma basu ishesa ba, ba ruwansa da su tinda ya lura ba mutunci suka cika ba, tasa ƙanwarma da suke uwa ɗaya da yaga tana shiga sabgarsu magana ya dena mata, har takwas da rabi yana tsaye wajen, ɗakin Baba ya leƙa yace "Baba har yanzu fa basu fito ba", Baba yace "har yanzu" ya tashi ya fito, ƙofar ɗakin Maama ya buga, Maama ta fito tace "A'a malam lfy?", yace "Sa'adatu da Maimuna su fito a mayar dasu makaranta", Maama ta gwalo micimicin idanunta tace "makaranta mal, wace irin makaranta ana zaune ƙalau?", yace "su fito su wuce lokacin na ƙurewa gashi kuma suna ɓatawa wnda zai kaisu lokaci", Maama ta riƙe baki tace "Eh ba shakka, toh waye wanda zai kai sun?, naga duk yayyen nasu basa gari", kai tsaye yace "Mu'azzam ne zai kaisu su fito yanzu", taɓe baki tayi tace "ai kwa dai bacci suke", Baba yace "tashe su, nan da minti biyar na gansu a waje" ya juya ya koma ɗakinsa, Maama ta hura hanci tace "toh idan ma na tashen su haka zasu tafi makarantar ciki kwalam, sai dai shi mai kaisun ya tsaya su karya kumallo nanda awa biyu ehe", da gayya ta faɗi hakan tana yiwa Mu'azzam mugun kallo ta shige ɗaki, da kyar Maama ta tashi Sa'adatu da Maimuna da suke bacci tamkar mushe, saida suka daɗe suna diminiya snn suka fito, lokacin kam har tara tayi, fuskar Mu'azzam kamar ta bujumin sa yayi hanyar soro, suka bi bayansa. ƙarfe sha ɗaya da rabi suka dawo gida, Mu'azzam ya yiwa Baba bayanin komai, Maimuna jss 3 aka kaita, Sa'adatu kam dilhu dankali da makani knn daman ƙwaƙwalwar fanko ce da kyar aka barta a jss 2. ★Ƙarfe takwas da rabi na safe Ruqayyah ta fito daga wanka, box ɗin kayanta da ta ɗakko jiya daga room ɗin Momy ta buɗe, daman ta kwafe a ranta bazata mayar da kayanta wardrobe ba har sai an ɗaura mata aure da dearest snn zata jera a press ɗinta ta gidan Nurain, ga kayanta ga nasa, sassanyan ƙamshinsa ya ratsa nata kayan, uniform ɗinta na Nurses ta saka, ta ɗora black Abaya a saman uniform ɗin, gaban mirror ta tsaya tana kallon fuskarta, sai kace wata taɓaɓɓiya haka ta ringa gwada yadda zata bawa Nurain haƙuri da irin kalaman da zata gaya masa, chappette mai strawberry ta shafa a pink lips ɗinta, tasa pinky finger ta kwantar da eyebrows ɗinta, ta sake gyara zaman V-shapped hijab ɗinta da kyau, perfume mai sanyin ƙamshi ta fesa sama sama, takalmi black ta sanya sandals ta ɗauki jaka ta fita palour, direct kitchen ta wuce dan ta jiyo motsin Momy a nan, ganin Momy ta kunna gas tana girki Ruqayyah tace "Momy na fa dafa breakfast, na ajiye muku a warmer...", Momy ta ajiye serving ɗin da take juya sauce tace "So, ai bance zanci ba, kinsan bana son high carbohydrate da zaki dafa doya da kwai tsura ba vegetables", Ruqayyah tace "nayi tomato sauce aii", yamutsa fuska Momy tayi tace "too much Acid knn". Ruqayyah dai ta fahimci cewa har yanxu Momyn ta bata gama hucewa ba, a ƙasan ranta tayi alƙawarin sai ta goge stain ɗin da tayi musu a zuciya, daga ta rarrashi dearest mgana ta ƙare. tace "Momy zan wuce aiki", Momy ta cigaba da aikinta tace "Ohk, kin sanar da Baban ki?", Ruqayyah tace "No, kafin na fita zan gaya masa", Momy ta taɓe baki ba tace komai ba, bayan Ruqayyah tabi da kallo tana girgiza kai tace "Allah ya baki dama kinsa ƙafa kinyi fatali da ita". Da sallama Ruqayyah ta murɗa door handle ɗin palourn Daddy, durƙusawa tayi ta gaishesa, Daddy ya amsa ba yabo ba fallasa yana duban dress ɗin jikinta, tace "Daddy zan fita aiki", his piercing eyes fixed on her yace "Okay, sai ki rubuta resignation letter ki submitting kafin ki dawo gida", a razane ta gwalo ido waje, gashi with seriousness on his voice ya fadi hakan, har ruwa ya ciko idonta tace "resignation letter?", yace "are you questioning me?", yarfe hannu tayi tace "No Daddy, i won't dare", ya daka mata tsawa yace "get lost my friend". da sauri ta miƙe ta zabga tuntuɓe da jikin kujera, saida tayi karo da bango har kanta ya sara snn ta lalubi ƙofa ta fita, tana zuwa palour ta sulale ƙasa tana yarfe hannu ta fashe da matsanancin kuka, Momy ta fito kitchen ta ringa kallonta cike da mamaki, har ƙoƙarin birgima Ruqayyah take sbd raɗaɗin da zuciyarta ke mata, Momy ta haɗe gira tace "meye haka?", Ruqayyah ta taso da gudu ta rumgumeta ta cigaba da kuka, Momy tace "ba tambayarki nake ba", Ruqayyah ta ɗago kanta daga shoulder ɗin Momy tace "Daddy ne yace nayi resigning from work..", Momy ta buɗe baki tace "ban gane ki bar aikinki ba", Ruqayyah na shessheƙar kuka tace "haka yace idan naje aiki yau sai na rubuta resignation letter na kai, na shiga uku Momyyy, wllh i love my job", Momy ta zameta daga jikinta ta shiga wajen Daddy, malamala Ruqayyah tayi a ƙasa tana hawaye, after 10mins Momy ta fito fuskarta a haɗe, Ruqayyah ta ɗago idanunta da suka rine tana kallonta, Momy tace "tashi ki tafi, ki rubuta resignation lettern ki dawo gida da ita", Ruqayyah ta sauke ajiyar zuciya tace "tom, kar nayi submitting?", Momy tayi tsaki tace "ai kinji me nace" ta nufi room ɗinta. saida Ruqayyy ta koma ɗakinta ta wanke fuska snn ta fita daga gidan, har ta isa Hospital tunani kawai take, ai abun sai yayi mata yawa ga rashin dearest ga kuma rashin aiki, tsaf zuciyarta za tayi bombing idan ta rasa these two valuable things. a hankali take tafiya cikin babban compound din, wajen da ake parking motoci ta tsaya tana kallo, idonta ya sauka a parking space din thoracic surgeon Dr Uthman, babu mota a parking space din nasa, tayi murmushin ƙarfin hali tace "dearest bai ƙaraso ba". Nurse station ta wuce, gaisawa sukay da colleague ɗin nata su biyu dake zaune wajen, Ruqayyah tace "ina Jiddah?", ɗaya daga cikin Nurses din tace "ai kam ina jin ta tafi gida da yake jiya night tayi", Ruqayyah tace "Ohk". wani room da suke ajiye ƴan kayansu na Nurses ta shiga, kettle ɗin ruwan zafi ta nufa ta kunna, ta buɗe locker dinta ta ɗakko mug da coffee powder, coffee mai rai da lafiya ta haɗa snn ta fito daga room ɗin. barin Nurse station ɗin tayi ta wuce Office ɗin Dr Uthman zuciyarta na harbawa, a garƙame ta tarar da office ɗin, kan silver chair da ke wajen Office ɗin inda patient ke jira ta zauna, almost 1hour babu alamar wnda take jira zai zo, har secretarynsa ma bata zo ba, Ruqayyah ta sauke ajiyar zuciya deeply in thoughts ta dubi Mug ɗin hannunta da coffeen ciki ya gama hucewa, ta duba agogon dake wrist dinta taga har 11am ta wuce, murya can ƙasan maƙoshi tace "Dearest". ta ciro wayarta daga pocket ta shiga kiran layinsa, saida ta kira sau goma amma switched off, hankalinta ne ya kuma tashi, Sha daya da rabi na cika ta tashi ta nufi Office din Dr Marwan, patient ta tarar yana dubawa don haka ta samu space ta zauna, Dr Marwan ya gyara zaman glasses dinsa yana rubutu jikin card, patient din ya miƙawa card ɗin yace "sai next week", patient ta amshi card ɗinta snn ta fita, Ruqayyah da hankalinta ba a jikinta yake ba tace "barka da safiya Dr", Dr Marwan da ke mata wani weird look yace "yawwa A Nurse", tace "ya aikin?", yace "Alhmdllh, wai ina kika shiga ne A Nurse?, har mun fara samun matsala wajen anesthesia", murmushin yaƙe Ruqayyah tayi tace "Egypt naje, yanxu kam ba ku da matsala tinda na dawo", yace "great, Khaleel ma ya gama complain ɗinsa", tace "yau ba ku da surgery ne naga Dr baizo ba har yanzu?", file ɗin dake kan table ya shiga buɗewa like he don't care yace "Boss yana India, this Friday ya tafi". tamkar wata statue in human form haka ta ringa kallonsa, shirun da yaji tayi ne yasa ya ɗago idanunsa ya kalleta, kallonsa yaga tana yi yace "A Nurse, kinyi shiru?".......✍️ Toh a cigaba dai da haquri da yanayin post en, ba nida enough time wollah, schl woah..🥴 More likes and comments snn a tayani sharing lol, tnx 🤗 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {26..} Wannan time ɗin ma dai Ruqayyah a ciki ta ji bugun zuciyarta, har wani darkness ne ya rufe mata sight, sama sama taji muryar Dr Marwan, a firgice tace "Dr, kamar dai banji me kace ba..", yace "i said kinyi shiru..." da sauri ta katsesa tace "No ba wnn ba", kallonta ya ringa yi ganin she isn't herself yace "ohk, which one?", tace "you said something like Boss yana India, this Friday ya tafi", he can't help it dole yayi blushing yace "Ohh you heard it, am jet serious baya nan, sai nanda 8months insha Allah zamu gansa", ƙirjinta ta dafe tace "8months..", katseta yayi yace "A Nurse i thought you are here for something serious, but i have patients waiting outside", tamkar wacca aka zarewa spine haka ta miƙe tace "Alright, thank you for the little time" da haka ta nufi door ta buɗe ta fita, da kyar ta isa Nurse station cause har yanzu darkness ɗin da yayi mending sight ɗinta bai gama fading ba. room ɗin dake station ɗin ta shiga, tsaye tayi tamkar wata statue, a tare ƙafafuwanta da hannayenta suka fara karkarwa sai kace wnda aka jona musu shocking machine, ta dubi Mug ɗin hannunta mai ɗauke da coffeen da ya zama tap water tsabar hucewar da yayi, tasss Cup din ya faɗi ya tawarwatse, two seconds da faɗuwarsa itama ta bisa ƙasan. kuka take son yi amma ta kasa, tears sun ƙafe a idanunta, kawai mgnar Dr Marwan ce take amsa ƙuwwa a kwanyarta, she spent 15 good minutes durƙushe tana kukan zuci, ta lumshe idonta da ƙarfi, she wish this is nothing but a nightmare, ita kanta tasan she was just fooling herself babu wani nightmare. wata colleague ɗinta ce ta shigo, kallonta ta tsaya yi kafin ta dubi broken cup ɗin dake ƙasa tace "Ruqayyah are you okay", Ruqayyah ta miƙe tana murje idonta wanda take fatan hawaye ya cikosa tace "partially, kai na ke ciwo Amina", Amina tace "ohh sorry bari na kawo miki drug", tsugunnawa Ruqayyah tayi ta fara packing pieces ɗin broken cup ɗin tace "don't burder I'm going home", Amina tace "Okay lemmi help you", Ruqayyah ta tashi ta dafe kanta tace "thank you", tarkacenta ta ɗauka ta bar asibitin da ya zame mata one living hell, a wani book shop ta tsaya ta siyi plain sheet da envelope snn ta fito ta tari Napep ta wuce gida, kafin taje gida ciwon kan da ta kirawa kanta ya lulluɓeta, a ɗan madaidaicin compound ɗin gidan nasu ta tsaya, ta zauna akan dakalin shiga main building ɗin, jakarta ta buɗe ta ɗakko pen da plain sheet ɗin da ta siya ta ɗora akan jotter, tana ɗora pen kan papern hannunta ya ringa rawa, da kyar ta gama rubuta umarnin da Daddy ya bata, tayi folding papern ta saka cikin envelope amma bata liƙe ba, tashi tayi ta shiga ciki da sallama, Momy dake zaune palour ta amsa, Ruqayyah da kanta ya fara juya mata tace "Momy barka da gida, na dawo", Momy ta kalli agogon dake palourn tace "da wuri haka", Ruqayyah ba tace komai ba, Momy ta taɓe baki tace "ina resignation lettern?", Ruqayyah ta miƙe mata white envelope dake hannunta, amsa Momy tayi ta ajiye hannun kujera, Ruqayyah tace "Momy na shiga ciki" ta wuce room ɗinta, da ido Momy ta bita ganin yadda ta dawo odd, she looks disturb and weak. wunin yau Ruqayyah bata ji daɗinsa ba, tama rasa meke damunta, gaba ɗaya ta kasa figuring out what is happening to her, abinci ma saida Momy ta kirata tace mata taci snn taci kaɗan, that was bayan sallar la'asar, tinda taci ta koma ɗakinta har akay sallar magrib da isha bata fito ba, tana kwance kan tiles tana juye juye Momy ta shigo, kallonta ta ringa yi kafin tace "ke me yake damunki ne waii?", zaune Ruqayyah ta miƙe tace "ba komai Momy", ai ko karen hauka ne ya cijeta bazata iya faɗin damuwarta ba, daman Momy ba haƙura ta gama yi ba tasan tsaf za tace mata Allah shi ƙara or something that will add salt to her fresh wound. Momy tace "ki sameni a palourn Daddy yanxun nan, kuma in kinje karki ce komai haquri kawai zaki basa", Ruqayyah ta gyaɗa kai, Momy ta juya ta fita. Ruqayyah ta ɗauki hijab ɗin da tayi sallah ta saka ta fita, zuciyarta na lugude ta shiga palourn Daddy, rakuɓewa tayi gefe saman carpet ta zauna, Daddy ya ɗauki envelope da ke gefensa ya wurga mata yace "ni zaki kawowa ko ni na baki aikin", Ruqayyah dai kanta a ƙasa tace "sorry Daddy, dan girman Allah kayi haƙuri, wllh i learn my mistakes", keenly yace "wane mistake?", kuka ta ringa yi kamar ranta zai fita tace "kayi haƙuri dan Allah..", wani ɓoyayyen ajiyar zuciya yayi baice komai ba, sai a lokacin Momy dake zaune palour itama tace "ayi mata afuwa Alhaji, wnn shine first time da tayi wronging namu amma kuma she won't go free ayi mata wani hukuncin dan Allah", shiru Daddy yayi na wani lokaci kafin yace "da farko ma dai ina yarinyar taje?", Momy ta kalli Ruqayyah tace "talk", Ruqayyah ta sharce hawayen idonta tace "Egypt naje", baki buɗe Momy tace "Ruqayyah me ya kaiki Egypt?", Ruqayyah tace "kuyi haƙuri dan Allah..", wani tsawa Momy ta daka mata tace "wnn ba zancen haƙuri bane magana za kiyi malama", Ruqayyah ta kwantar da murya tana shessheƙa tace "wani aiki naje nema amma ban samu ba...", Momy tace "karki bari na sake tambayarki Ruqayyah, I'm giving you this last warning, ki gaya min komai", Ruqayyah ta share zufar dake keto mata tace "few months kafin a kawo kuɗin aurena na cike wani form online na wani aiki da ƙasar Egypt take bayarwa na waɗan da suke da karatu a fannin lafiya, aikine na shekara ɗaya mai kyau, bayan na tura musu form ɗin suka turomin da saƙon cewa zasu nemeni domin yin interview, ban sake samun wani message ba har sai ranar wata alhamis ranar mother's eve ɗina, tsakar dare na ga message cewa anyi hiring ɗina don haka kafin ranar Monday na kasance a garin Cairo, ban tafi haka ba saida na ajiye muku latter ai kuma shima Nurain na tura masa saƙon cewa ya jirani zan dawo, ranar juma'a na hau jirgi zuwa Abuja kamar yadda suka ce nan ne meeting point ɗin da zamu taru kafin mu wuce Egypt, A Cairo Monday ta riskeni, akay mana interview amma ni banci ba, don haka suka ce na ƙara gaba baza a ɗaukeni ba, da kyar na samu aikin da nayi na samu kuɗin ticket din jirgi na dawo Nigeria, Momy Daddy wnn shine gaskiyar dan Allah kuyi haƙuri na ɓoye muku da nayi, ina tsoron ku hanani shiyasa ban gaya muku ba...", Daddy ya jinjina kai ya kalli Momy yace "barin aikin shine hukuncin da ya dace da ita...", Momy dai tayi tagumi takaicin ƴarta ta ya gama cikata, ajiyar zuciya tayi tace "get out Ruqayyah", Ruqayyah na sharɓe hawaye ta miƙe ta fita, Momy tace "Alhaji karka yanke hukunci cikin fishi, ka tsaya kayi nazari dan Allah, yaran yanxu sai a hankali idan ka biye musu sai ka bata musu rayuwa da baki ko kuma ka tagayyara su da wani action ɗin, Allah ya huci zuciyarka, plxx think twice kafin ka zartar da hukunci...". ajiyar zuciya yayi yace "toh aurar da ita zanyi daman har yanzu Dauda na ciki", Momy tace "Eh ba damuwa gara ayi mata auren" da haka ta tashi ta fita. ★Tinda aka mayar da Sa'adatu da Maimuna makaranta shegun suka samu babban lasisin tsula tsiyarsu, yau sati uku kenan sau ɗaya suka taɓa zuwa, a kullum zasu shirya cikin uniform harda jaka snn su fita, daga sun fita sai ko wacca ta kama hanyarta, Maimuna ta wuce yawonta daga wnn hotel ɗin zuwa wani, Sa'adatu kam gidansu Mabaruka take wucewarta su sheƙa ayarsu san ransu, daga lokacin tashi daga makaranta yayi sai su dawo gida, hakan ba ƙaramin daɗi yake musu ba, su a ganinsu da baƙi ƙirin gwara baƙi baƙi. A fanin Hajar kam babu abinda ya shalleta dasu, a kwandon shara ta wurga su, ita gani take ma kamar babu su a gidan, koda sun takaleta saidai ta yamutsa fuska tayi banza dasu ko kuma ta shige ɗaki. ta kwantar da hankalinta ta zubawa idonta toka bama ta gani ba bare ta tanka, ta tushe kunnenta bama ta ji ba bare ta tanka, ranar Alhamis da daddare Hajar na zaune a soro tare da Nura, firar su suke cike da shauƙi da kaunar juna, rufe fuskarta tayi da hijab tana tiƙar dariya sbd abin dariyar da ya fada, shima dariyar yake yace "insha Allah gobe zasu kawo min kuɗina wajen Baba..", ta bude fuskarta tace "kuɗin me?", yace "kuɗin da zan ɗauki hanyar mallakarki..", turo baki tayi tace "kaji ka ko, toh wai haka ake yi, nifa har yanzu ba sanka nake ba, kuma ni ƴar yarinya ce ban isa aure ba" ta murguɗa masa baki childishly, murmushi mai sauti yayi yace "Ohh really, ai naga alama shiyasa yau kika takura sai naxo kin ganni hakan ma ai duk cikin rashin so ne, snn kuma very soon zaki zama mother kinga ba maganar yarinta..", ta juya manyan idanunta tace "Au nice ma nace maka kaxo ko?", kafaɗa ya ɗaga yace "Eh mana, kin ga you inform your parent kinji", wani gwalo ido waje tayi tace "chabb ai kwa ba za a kawo kuɗin ba indai ni zan gaya musu", dariya ta basa sosai na expression dinta yace "toh meye aciki?", yana kwaikwayon muryarta yace "haka fa kawai zaki ce, Umma Baba gobe za a kawo kuɗin", turo baki tayi tace "ni gida zan shiga", ya kalli agogon wayarsa yace "Okay, sai munyi waya don ban gaji da jin muryarki ba", ledar da yazo da ita ya miƙa mata, ƙin amsa tayi tace "A'a nagode", haɗe gira yayi yace "amshi mana ko so kike mu ɓata", a hankali ta amsa tace "nagode", ya tashi ya nannaɗe darduman da ya zauna ya naɗe wacca Hajar ta zauna ma, amsar darduman tayi tace "nace maka fa ka ringa bar min zan naɗe fa", yace "naƙi ɗin..", ya ringa kallonta har saida ta gaji ta juya masa baya tana turo baki tace "Allah nace maka fa banaso", yace "toh me nayi miki", tace "saida safe" ta shige gida. tinda ta shigo Maama da Sa'adatu dake zaune bakin ƙofar ɗaki suke binta dana mujiya, Maama tayi tsaki tana kallon ledar hannunta, Sa'adatu tace "kullum sai a shigo da wata mitsiyaciyar leda, uhmm Maama za kiji zuwan da dawowar wllh, a banza ake zaman soro harda su leda, ai nasha ganin blue film na zahiri a soron nan...", Maama tace "barewa tayi gudu ɗanta yayi rarrafe, ai muna ganin jalala a wnn gidan...", Hajar dai ta wuce ɗaki abinta. washe gari Juma'a, bayan Sallahr la'asar aka kawo kuɗin Hajar, Baba ya shigo gida da uban kuɗin a hannunsa yana kabbara yace "alhmdllh", yaye labule Maama tayi tace "wnn kabbara haka malam sai kace wanda akay wa bushara da gidan aljanna..", yace "ki fito ki saka albarka kuɗin auren Hajara aka kawo", Maama ta buga wata shegiyar guɗa ta fito tace "Au haba, ƙwandala nawa aka kawo?", ƙanƙance ido yayi yace "wace irin ƙwandala kuma Rabii?, ke me yasa ba a abin arziƙi ne dake", tace "ai gani nai ƙwandalar ce ta dace da ita", Baba ya girgiza kai yace "kiyi fatan Allah ya bawa ƴaƴanki ko da rabin nata ne..", da sauri Sa'adatu da Maimuna suka matso jikin window suka kasa kunne suji nawa aka kawo, Nabilah kam taɓe baki tayi, Maama tace "nawa ne", Baba baice komai ba ya kunce ledar uwar kuɗin ya fito dasu, zaro ido Maama tayi ganin yawansu, tinda take bata taɓa ganin kuɗi masu kaurin haka ba, Baba ya mayar da kuɗin yace "ƙwandala goma ne" ya wuce ɗakinsa ya barta nan tsaye da sakakken baki, wani tuƙuƙin baƙin ciki da hassada ne ya turnuƙeta, tamkar kububu haka ta afka ɗakinta, ta dubi Maimuna da ke jikin window tace "wai mahaukaciya kuka mayar dani ko me?", Maimuna ta turɓune fuska cike da rashin ɗa'a tace "toh wai ke Maama me mukay miki ne?", wata muguwar ashariya Maama ta lafta mata tace "uban ki kikai min, ji nake cemin kukai faƙiri ne ke neman auren Hajara, toh ba kuga uban kuɗin da aka kawo ba na aure", Sa'adatu tace "wai uban kuɗi naji fa Baba yace ƙwandala goma", Maama da zuciyarta ke tafarfasa tace "toh wasu dunƙulallun kuɗi ne ƴan dubu dubu, kaurinsu da aukinsu inajin sun doshi miliyan...", baki suka haɗa sukace "Aaaaaa Maama haba dai", cike da takaici ta shiga kutuntuma musu ashar tace "ƙarya nake knn?", Nabilah ta fashe da dariya tace "A haba dai Maama ya zai kiyi ƙarya ai saidai ki faɗa ba daidai ba ko Maimu", Maimuna tace "kwarai kuwa, Maama na rasa me yasa kika ɗaga hankalinki a kan wanda waccar matsiyaciyar zata aura", Maama ta gasa mata harara tace "yo ba dole hankalina ya tashi ba, ha kurum sai taci gaba kuna zaune jaɓar kuna kallonta..", Sa'adatu tace "Maama nifa kinsan ba aure zanyi ba, indai cigaba na aure kike magana toh na yarda Hajara ta fini a wnn fannin", Maama ta saki baki tana kallonta tace "Au haka zaki zauna a gidan ba xaki gidan mijinki ba...", Nabilah ta taɓe baki tace "Ayyah Maama ai ki saka Sa'adatu a addu'ar ki ta koda yaushe, dan na gaya miki irin alfashar da nake tunanin suna aikatawa da tumakan ƙawayenta amma kin ƙi yarda", Sa'adatu tace "dalla malama ban kasafta dake ba bare ki dauka..", Nabilah tace "kinyi kaɗan bari kiji in gaya miki, toh baki kai nan....", Maama tace "ya ishesku, zaku fara raba halin naku knn", Maimuna tace "dama kin rabu dasu yauma nasha kallo, ai sun iya bawa hammata iska" ta fashe dariya. Da misalin tara da rabi na dare wayar Hajar tay ringing, yamutsa fuska tayi snn ta sakata a silent, yau dai baza tay picking ba, gado ta hau tayi kwanciyarta zuciyarta wasai, an kawo kuɗin aurenta da ya sayyadi, washe gari ta tashi ta gama komai na gyaran gida da ta saba, har waken kulele saida ta wanke, bayan ta gama komai ta shiga wanka, tana shafa mai Umma ta shigo ɗakin, gaban wardrobe ta tsaya ta ciro kuɗi snn ta koma gefen gado ta zauna tace "idan kin shirya zan aikeki gidan Jamila", Hajar tace "tom" ta cigaba da rubbing cream a fatarta, doguwar rigar atamfa ta saka, ta sanya hijab da ya tsaya mata a guiwa tace "Umma na gama", Umma ta miƙa mata kuɗin hannunta tace "ki kai mata wnn, za muyi waya da ita", Hajar ta amshi kuɗin ta saka a jakarta tace "na tafi", Umma tace "karki kai yamma", tace "tom" ta ɗauki flat shoe a ƙarƙashin gado ta fita, a soro ta tarar da Naseer da yazo jiya, ta sunkuya tace "yaya ina yini", yana kallonta yace "lfy lou, ina zaki haka?", tace "Umma ce ta aiken gidan Anty Jamilah", gyaɗa kai yayi yace "Okay" ya wuce ciki ita kuma ta fita, cike da nutsuwa take tafiya har ta isa bakin titi, cikin sa'a kam ta samu Napep da wuri, tana zuwa gidan ta tsaya bakin gate tayi knocking, Hafsa ce ta buɗe tana ganinta ta zaro ido tace "the bride to be wnn bazata hka", Hajar ta shiga gidan tace "ina Tahfeez din, yau naga asaba..", Hafsa tace "ba nida lafiya". da haka suka shiga ciki, Hajar ta durƙusa ta gaida Anty, Anty tace "lfy lou, ya mutan gidan", Hajar tace "suna lfy", Anty tace "madallah", Hajar ta zuge jakarta ta ciro aiken ta mikawa Anty tace "gashi inji Umma".......✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {27..} Da mamaki a fuskar Anty ta amshi kuɗin tace "toh, na mene?", Hajar ta girgiza kai tace "bansani ba amma tace za kuyi waya", Anty ta gyaɗa kai tace "Okay". Hafsa ta tashi ta nufi ɗakinsu, wayarta da ke kan mirror ta ɗauka, call log ta shigo ta nemo wata number ta shiga dialing, tana fara ringing akay rejecting few seconds kira ya shiga daga same numbern, ta kara a kunne tace "Assalamu alaikum", from the other side Ahmad yace "Wa'alaykissam salam, young lady", tace "yawwa, nace ba, yau idan babu damuwa zaka iya zuwa na cika alkawarin da nayi maka", keenly yace "Okay, na ɗauka ma kin manta ashe ba haka bane", tace "yap, sai kazo immediately after Asr prayer", yace "insha Allah", kashe wayar tayi tace "kar alƙawari ya zarbaɗo ƙafata ranar lahira ya hanani gudun famfalaƙi..", palour ta fito ta zauna, Anty ta kwashe kuɗin da ta ajiye hannun kujera ta shiga room ɗinta, wayarta ta dauka, missed call ta gani daga ƴar uwarta, zama tayi gefen gado ta shiga kiranta, Umma na dauka suka gaisa, Anty tace "Hajar taxo da saƙo, Adda kuɗin na mene?", Umma tace "kinsan jiya aka kawo kuɗin auren Hajara, Jamila ba a fafe gora ranar tafiya, wnn kuɗin wnda nake ɗan tarawa ne tin tini, shine nace bari na turo miki su sai a fara mata ƴan tsince tsince sha'anin aure da yawa..", Anty tace "gaskiya haka ne ba a fafe gora ranar tafiya, toh mai za a tsinto da wadan nan kuɗin?", Umma tace "abinda kika ga ya dace Jamila, koma mene asiya a ajiye", Anty tace "wata shida suka sa ko?", Umma tace "Eh, kinga kwa ba lokaci, yanxu sai kiga abin yaxo kusa, idan na sake tara wasu saina turo miki kafin lokacin muga abinda za muyi", Anty tace "gsky kam, toh wnn kuɗin dai saidai na siya mata decorants, kayan kitchen nawa ne ni zan mata", Umma tace "Kaii Jamila abun fa da yawa", Anty tace "she's my daughter fa, insha Allah zan mata duk wani abu da ya danganci kitchen, cikin rufin asiri zamu kaita insha Allah babu me rainata a dangin miji ko kuma a goranta mata". Umma ta ajiye numfashi tace "toh Ameen, Allah ya tabbatar mana da alkhairy", Anty tace "Ameen". Hafsa ta kalli Hajar tace "gsky fa zanyi amarancin a bikinki, daman nice ƙirjin biki kuma babbar aminiyar amarya", Hajar tayi murmushi tace "yayi kyau..", Hafsa tace "anko kala uku zan fitar mana na ƙawayen amarya snn kuma zan shiga na ƴan gida, ga wanda zanyi iri ɗaya da amarya ranar yini, kai abinfa ba a cewa komai gsky zan zuba amaranci", Hajar dai ta ringa binta da ido tana murmushi, wai itace wacca ake maganar bikinta, bikin ma da rabin zuciyarta Nura. Hafsa tace "amma dai ba yau zaki tafi ba ko?", harararta Hajar tayi tace "chab ana yin sallar la'asar zan samfe..", Hafsa tace "kaiii dan Allah ki kwana", Hajar tace "yau naga jalala daga zuwa kuma sai kwana, A'a wllh tafiya zanyi", Hafsa ta haɗe gira ta tashi tace "sai ki ta tafiya" ta wuce kitchen, Hajar tace "ai daman tafiyar zan". Abinci ta zubo musu ta kawo ta ajiye, ta koma kitchen ta ɗakko gaseous drink da pure water ta kawo ta ajiye, tana hararar Hajar ƙasa ƙasa tace "saiki matso muci", salon ta sake bata haushi tace "na ƙoshi", Hafsa ta ajiye spoon ɗin hannunta tace "ke kin isa, kadan ba sai kinci ba", Hajar ta tashi ta cire hijab ɗinta snn ta zauna ta ɗauki spoon, Hafsa ta kai spoon baki tace "toh ki bari ƙarfe biyar da rabi ko shida saiki tafi", Hajar ta noƙe kafaɗa ta cigaba da cin abincinta, suna gama ci Hafsa ta tattare plate da empty bottle na drink ɗin ta wuce kitchen dasu, ganin ta daɗe bata fito ba Hajar ta bi bayanta, tarar da ita tayi tana wanke wanke bakin sink, Hajar tace "Au wanke wanke kika tsaya", Hafsa tace "harda left over na safe da banyi ba". Hajar ta tattare hannun rigarta ta matsa gaban sink ɗin ta fara temaka mata da ɗauraya, Hafsa tace "kina fa da kirki amma kaɗan" Hajar tace "point of correction bani dashi". wata small pot Hafsa ta ringa gurzawa soson ƙarfe tace "Abdallah ne ya babbaka indomie da safe", Hajar ta leƙa cikin tukunyar ganin yadda tayi baƙi ta fashe da dariya tace "amma dai Indomien ba tada maraba da gawayi", Hafsa tace "uhmm gobara ya kusan tayarwa fa, ba kiga faɗan da yasha ba kuwa wajen Abba, har suka fita kasuwa Abba na faɗa", Hajar tace "wai Allah ya kiyaye". Ana yin sallar la'asar Hajar ta fara shirin tafiya, ta tsaya gaban mirror tana gyara ɗaurin dankwali, hijab ɗinta ta janyo zata saka Hafsa tayi wuf ta amshe tace "ki bari ba yanzu ba", Hajar ta riƙe ƙugu tace "ka jimu da mata, toh wai me zan miki?", Hafsa tayi serious face ta nuna mata kusa da ita tace "dan Allah zauna kiji", Hajar ta zauna tana kallonta tace "what..?", Hafsa ta marairaice fuska tace "tin kina nan gidan nayi masa alƙawari", Hajar da ta ƙosa taji mene tace "wa knn?", Hafsa tace "wnn mutumin da muka haɗu a supermarket", Hajar ta ƙanƙance ido tana nazari, lokaci guda ta gwalo ido waje tace "alƙawarin me kikai masa", kaf Hafsa ta gaya mata abinda ya faru, Hajar tace "toh yanxu ya kike so ayi?", Hafsa tace "so nake idan yazo ki fita, ni ko biki masa magana ba hakan ya wadatar", Hajar tace "da baikon a kaina zan tsaya da wni namijin", Hafsa tace "ai manufar abin zaki duba, bawai zaki tsaya dashi bane a matsayin saurayi, dan Allah don't turn me down just say Hi shknn", Hajar ta dafe kanta tace "wllh kin tafka wauta, idan ya wuce huɗu da arba'in tafiya zanyi wllh", Hafsa tace "bazai ma kai haka ba..." ko gama rufe baki ba tayi ba saiga kira nan yana shigowa wayarta, numbern kawai ta gani tayi ajiyar zuciya ta ɗauka, kara wayar tayi a kunne, yace "nazo", tace "Alright, wait a minute". ta kashe wayar ta kalli Hajar dake kallonta tace "yazo", gyaɗa kai Hajar tayi tace "toh sai muje ko", Hafsa ta gwalo ido waje tace "wai tare zamu, kefa kaɗai zaki", Hajar ta gyara zama tace "kince kar naje knn", Hafsa tace "toh sai ki yiwa Anty sallama daga nan ki wuce kinga na samu hanya sai nace rakaki zanyi", Hafsa ta saka hijab dinta, dakin Anty Hajar ta shiga tayi mata sallama, Anty ta bata 1k kuɗin mota, Hafsa tace "Anty na fita rakata", tare suka fita gate, Hajar ta matsa gefe tace "fara fita", buɗe ƙofar gate ɗin Hafsa tayi snn ta fita, yau ma dai a wata jugunanniyar motar yazo saɓanin ta ranan, yana hangota ta tint glass ɗin ya buɗe motar ya fito, mayar da door yayi ya rufe snn ya ƙaraso wajenta yayi sallama, tace "wslm, ina yini", yace "lfy lou, ykk?", tace "alhmdllh am great", juyawa tayi da nufi mgana da Hajar ai kam taga wayam, tace "lemme get her" ta shiga gida, a tsaye ta ganta da wani expression bisa fuskarta, Hafsa tace "toh muje", Hajar tace "wllh ban san me zance masa ba", Hafsa ta ja hannunta tace "anything" saida ta kaita har gabansa snn ta cikata, Hajar ta ja baya making some distance between them, Hafsa tace "As promised", waje ta basu ta shiga maƙotansu, gefe Hajar ta kalla tace "ina yini", bai amsa ba ya jefa mata tambaya "you blocked my number right?", kanta a ƙasa tace "yess", kallon fuskarta kawai yake yace "why?", tace "sorry you ask for a chance da bazan iya baka ba, kayi haƙuri dan Allah, wllh a lokacin inada manemi wnda yaje wajen iyayena, bana so na ɓata maka lokaci shiyasa", wani iri ya ji har cikin zuciyarsa yace "Alright, ynxu fa?", tace "ynxu kam an riga an min baiko, kayi haƙuri..", wani deep breathe ya sauke yace "ba damuwa Hajar, loosing you is one of my destiny, may Allah choose the best for us", a karo na farko da ta ɗago ta dubesa, ta mayar da kanta da sauri tace "Ameen, nagode", gidan da Hafsa ta shiga ta nufa ta fara knocking, Hafsa ce ta buɗe ganinta ta fito tace "har ya tafi..." shiru tayi ganinsa a tsaye yana kallonsu, ta ƙarasa inda yake tace "then ynxu dai na fita daga jerin masu yanke fate, na cika alkawari", yace "thank you", tace "don't mention, sai anjima", yayi waving ɗinta slightly snn ya juya ya shiga motarsa zuciyarsa a dagargaje, wani irin cin taya yayi ya juya kan motar, da gudu yabar unguwar tamkar zai tashi sama, Hajar tabi ƙurar da ya tayar da kallo snn ta matsa kusa da Hafsa suka sauka kan titi, Hajar tace "ya bani tausayi wllh", Hafsa tace "Allah ya basa wata". da haka Hajar ta tsari Napep ta wuce gida. ★A kwana a tashi lokaci bashi da wuya wajen shuɗewa a wajen Ubangijin talikai, mu shagalallun bayi mu muke ganin jimawarsa harda ɗokin cika burikan rayuwa ( yau HAJAR ya ɗakko wani daga cikin scene na littafina SOHANA), A wannan rana ta laraba saura wata ɗaya bikin Hajar, kuma a wnn rana aka kawo lefe, manya manyan tabarmi har guda biyu aka baje a tsakar gida da yamma ana jiran ƴan kawo lefe, Maama da ƴaƴanta sai shige da fice suke suna yaɓa baƙaƙen maganganu, tin Anty Jamilah na sharesu har ta fara mayar musu da wacca tafi tasu zafi da ciwo. an zuba bajinta gsky, lefen Hajar san kowa ƙin wanda ya rasa, dangin Ango suna gama sauke kayan lefe suka ce suna buƙatar a ƙara musu wata ɗaya domin ango ya gama shirye-shiryen sa, kai tsaye aka amsa musu dan Anty da Umma suma suna son su gwangwaje ƴarsu, tray tray su Anty da wasila da sauran ƴan uwan Umma suka ringa fitarwa na kayan motsa baki da kaji da kuma steak suka bawa ƴan kawo lefe, ga kuma kuɗin tukuici mai tsoka da aka basu, sunji daɗin karamcin da iyayen Hajar sukay musu, nan fa aka baje kaya ana musu ɗaɗɗai kowa na sanya albarka, maƙwabta da abokar arziƙi kowa shigowa yake yana kashe kwarkwatar idonsa, a duk wnn zazzafar wainar da ake toyawa Maama da ƴaƴanta sun ƙule ɗaki saidai fa komai akan micimicin idanunsu tinda laɓewa sukay jikin labule da window suna leƙe. baƙin ciki da hassada ainun suke nunawa, Anty sai ɗaɗɗaga kaya take tana saka albarka, wasila kuma na rangaɗa guɗa, da baƙin ciki ya ishi Maama da sauri ta bar bakin labule ta zauna ƙasa daɓas ta dafe kai, Sa'adatu kam tsaki tayi ta koma gado tayi kwanciyarta tace "ko sha'awa", Maama tace "ƙarya kike munafuka, wane mai zuciyar ne zaiga uban kayan nan yace basu birgesa ba..", Nabilah ta rage murya tace "haba Maama kiyi magana a hankali kar ace baƙin ciki muke", da ƙarfi Maama tace "Eh aji ɗin mna" sai kuma ta miƙe ta gyara ɗaurin zaninta ta saɓi hijab tayi waje, da sauri Maama ta fice daga gidan zuciyarta na tafarfasa ta saɓi hanya........✍️ 🔔*WEDDING BELL*🔔 Ehen it's ringing...... ƙalalannnn comments Likes nd share 🤗 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche. {28..} Can cikin lungunsu ta shiga, bayan tayi tafiya ba mai nisa ba tazo ƙarshen lungun, ta gangara can ciki, wani tsukun layi ta shiga mai wawakekiyar kwata, ƙudaje da ƙwari sai shawagi suke, wari kam ba a cewa komai sbd kwatar ta Engine markaɗe ce kuma mara gudana, wani kuturun gida na laka Maama ta shiga ta zabga sallama daga soro, ta kutsa kai ciki, wata mata ce ta fito wacca za su kai shekaru ɗaya da Maaman daga wani ɗaki, ganin Maama ta riƙe baki tace "lale lale maraba da baƙuwar yamma", Maama tace "bani ruwa na sha maƙoshina a bushe yake", wata randa dake can gefe matar ta buɗe ta kantamo ruwa a cup ta kawo mata, daga tsaye Maama ta moɗe ruwan, tayi ajiyar zuciya tana hura tukubar hanci ta miƙawa matar kofin tace "yawwa Balaraba, da zance nazo", Balaraba tace "Atoh mu shiga ɗaki ko mu zauna nan waje tinda ba kowa, duk basa gidan", Maama tace "mu zauna nan tsakar gida yafi iska", Balaraba ta shiga ɗaki ta ɗakko wata yagulamun tabarma duk ta zare ta shimfiɗa musu, suka zauna, Balaraba tace "lfy dai Aminiya", Maama ta sharce zufar da ta tsattsafo mata da ƙasan hijab tace "Balaraba ƴaƴana gaba ɗayansu sun wurgar da zuciyoyinsu a ƙasa kare ya lashe". Balaraba tace "me ya faru?, shaƙamin mana", Maama tace "kinsan dai ina zaune bazan bari ƴaƴan faɗima sufi nawa ba, wai wnn shegiyar ƴar Hajara itace yau aka kawowa lefe", tayi shiru ta riƙe baki tace "ke baki ga uwar dukiyar da aka lafto ba", Balaraba tace "babbar magana, toh su kuma yara meye haɗin su da wnn lamari kika ce kare ya lashe musu zuciya?", Maama tace "kwanwar su ce fa duka, gaba ɗayansu gaba suke da ita, ni bama wnn ba wnda shegiyar zata aura ne matsalata", Balaraba ta taɓe baki tace "ɗan gidan waye?", Maama ta juya hannu tace "oho ni bansani ba, amma dai wai malamin makarantarsu ne, yaran nan da yake sun sansa shine suka ce min wai faƙiri ne bashi da komai, wai ƙaramin shagon chajin waya yake dashi, uwarsa ɗan wake take jefawa a ruwa, kin san me?", Balaraba tace "yo ina zan sani ai sai kin gayamin", da wani irin takaici Maama tace "hmmm arziƙi da rashinsa ai basa ɓuya, wllh in gaya miki lokacin da malam ya kwanta a asibiti ke baki ga uban kayan da ya kawo masa ba na dubiya, tin daga lokacin zuciyata ta fara wasiwasi akansa, wai sai Sa'adatu tace min kayan haya ne, wai shi Opay, in gaya miki aka zo aka kawo kuɗin aure, nidai tinda nake ban taɓa ganin kuɗi masu aukinsu ba, to sai wnn kayan na lefe da aka kawo, shknn fa akasa muƙeƙiyar sanda aka bajar dani a ƙasa, kinji fa lukutar masifar da nake ciki..", Balaraba ta jinjina kai ta riƙe haɓa tace "amma baki taɓa sanar dani ba Rabi", Maama tace "ai yaran nan ne sukai ta juyar min da kai da tunani, suka ringa cewa matsolo ne kuma faƙiri shiyasa ban damu ba, nidai yanxu ki bani shawara me zanyi?", Balaraba tace "ai kwa dai bazaki zauna ba kina ji kina gani ƴar faɗima tafi naki ƴaƴan, yanxu dai yaushe ne bikin?", Maama tace "naji ɗaxu dangin mijin suna cewa saura wata biyu", Balaraba ta washe haƙoranta da suka gama dafewa sbd cin goro tace "yo wnn ai me sauƙi ne, munada lokaci isasshe, wata biyu ai da yawa", Maama tace "kar dai muyi sake, ta ina zamu fara?", Balaraba tace "toh wai me kike so ayi ne?", Maama tace "A'a haba ke kuwa Balaraba ai kinsan me nake bake so", Balaraba ta ɓarke da dariya tace "Azzaluma Rabii", Maama tace "har na kaiki", Balaraba tace "gidansu yaron zamu fara nemowa, ai bazai wuce unguwar Dala ba tinda kince malamin islamiyya ne", Maama tace "to wa zai nemo gidan nasu?", Balaraba tace "haba Rabii sai kace baki san ko ni wace ce ba, nice larabe uwar kwakkwafi da bin diddiƙi", Maama tayi ajiyar zuciya tace "yawwa, na bar komai a hannunki, sai zuwa yaushe zan ji ki?", Balaraba tace "har gida zanzo na sameki ai wnn abu nima ya shafeni, bazan bari kiji kunya ba Rabii", sai ynxu zuciyar Maama ta sake, taji daɗi har cikin ranta tace "to bari na saɓa, wai ƴar tafiyar nan da nayi ba kiji yadda ƙirjina ya riƙe ba sai kace wata wacca ta tara kitse, yo Allah na tuba ina naga maiƙon", Balaraba tace "ai da anci maiƙon, yanzu ne dai babu, amma da gidan Malam Adamu ai baya rabo da maiƙo, ke kanki maiƙon kika gani kika liƙe masa..", Maama tace "gsky dai sai bayan da aka haifi autar gidan arziƙi ya yanke mana, malam yana riƙon gida sosai, yanxun ma yana bamu daidai ƙarfinsa, kin san ni ba ruwana in mutum yayi abin arziƙi bazan kushesa ba, shiyasa nima nayi masa halacci na zauna dashi a babu", da haka Maama ta miƙe, soro Balaraba ta rakata, sukay sallama Maama ta wuce, har ta koma gida jama'a basu baje ba, ynxu ne suka fara shigowa, abinka da unguwar tsuku wato gheto, wnn gayawa wnn haka suka cika gida suna kallon abin arziƙi, sai bayan Sallahr magrib aka samu masaka tsinke, Anty ta riƙe haɓa tana kallon Umma tace "Adda mutane akwai gulma", Umma tace "uhmm bare ƴan lungun nan", Anty ta kalli boxes ɗin da Mu'azzam ke jigilar shigowa dasu tace "Alhmdllh gsky kaya sunyi kyau sai san barka Allah yaci da ƴan baya", Umma tace "Ameen, zan tambayi mal nanda kwana biyu sai a kai kayan gidan ki", Anty tace "toh shknn, wnn tururuwar jama'a haka ai ba a rasa mai dogon hannu ba, yanxu sai ki ga kaya na ɓata, haka kurum su cuci yarinya mutanen yanxu ba imani", sai takwas da ƴan mintina Anty ta tafi gida. ★Washe gari Umma ta saka Mu'azzam ya kai lefen ɗakin Baba don ya gani, ko gama buɗe box ɗin atamfofi Umma ba tay ba ya dakatar da ita yace Allah ya saka albarka yasa rabonta ne, Umma tace "Ameen" ta rufe kayan, bayan Sallahr la'asar Hajar ta dawo gida, daman gidan Iya taje ta kwana abinta don haka bata san wainar da aka toya jiya ba, tasan dai za a kawo lefe, koda ta shiga ɗaki taga boxes ɗin lefen murmushi kawai tayi ta kawar da kai, ammafa sun burgeta, nace uhmm hajiya Hajar don ma ba kiga abin arziƙin dake ciki ba da sai bakinki ya yage. da yammacin ranar Naseer yazo sbd kiransa da Baba yayi, ya durƙusa ya gaida mahaifin nasa, Baba ya amsa yace "Naseer akan filina dake unguwar Ring road, kasan na sakasa a kasuwa?", Naseer ya shafa kai yace "Eh Baba na sani", Baba yace "toh yawwa, an samu mai siya, anyi ciniki anyi komai, kuma an samu riba sosai, kasan filin yanada girma kuma na daɗe da siyarsa", Naseer yace "Eh", Baba ya gaya masa adadin kuɗin, mazajen kuɗi Baba ya ambata, Naseer ya jinjina kai, Baba yace "yawwa, gida huɗu za'a raba kuɗin, kaso ɗaya na Hajara ne dashi za ai mata kayan ɗaki, ragowar kaso ukun kuma na Nabilah da Sa'adatu da Maimuna ne, suma duk ranar da Allah ya kawo musu mazaje sai ayi musu kayan ɗaki", Naseer ya gyaɗa kai yace "hakan yayi Baba, Allah ya ƙara girma", Baba yace "A Bank account ɗinka za a tura kuɗin", Naseer yace "toh Baba", Baba yace "idan aka ɗauki na Hajara sai kuma a nemi wani filin can wajen gari a siya da kuɗin su Nabilah", Naseer yace "nima ai akwai tawa gudummawar da zan bayar, zan siya mata katifu", Baba ya jinjina kai yace "Masha Allah, Allah yayi abarka ya yauƙaƙa maka hanyar samu, Allah ya baka ikon kula da ƙannenka ko bayan raina", Naseer yace "Ameen", Baba ya ciro wata paper daga aljihu ya miƙa masa yace "gashi lambar mai siyan filin ce, ka kirasa sai ka tura masa da account numbern", Naseer yace "tom" yasa hannu biyu ya amshi papern, tashi yayi ya fita, har karo suka kusa yi da Maama dake musu laɓe, zuciyarsa ce ta buga ganinta tsaye a ƙofar ɗakin, tayi masa wani mugun kallo tayi ƙasa da murya tace "biyoni Nasiru" ta shiga ɗakinta, dole ya bita ɗakin, ta inda ta shiga ba tanan take fita ba, wani huci tayi tace "sbd kai sakarai ne wai zaka mata katifu, A'a ba katifu ba kamfanin Royal foam zaka siyar mata, toh wllh bada yawuna ba karka kuskura ko ficika ka bayar a bikin Hajara, idan kuma ka bayar to ban yafe ba wllh, kaji dai na gaya maka", murtuke fuska yayi yace "kiyi haƙuri Maama na riga na siya ai", hangame baki tayi tace "saika mayar kamfanin a baka kuɗinka, ai ba a ciniki dole, idan kuma bazaka mayar ba ni ka kawomin daman tawa ta ruɓe, kannenka duk sun lotse ta", baice komai ba ya miƙe ya fita zuciyarsa duk a dagule. Bayan sati biyu Umma na bakin rariya tana alwala, Balaraba ta zabga sallama a gidan, Umma ta amsa bayan tayi mata kallo ɗaya, Balaraba ta yatsine fuska tace "wai ina mutan gidan ne inata sallama bare na amsawa", da jin muryarta Maama ta fito tace "ai gamu nan, muna miki lale maraba", Balaraba tace "toh daga sallama sai bare su amsa", Maama tace "kedai mu shiga daga ciki", Maama ta yaye mata labule ta shiga snn itama ta shiga, Nabilah ce kawai a ɗakin, sauran kam sun tafi makarantar gogi, Maama tace "Nabilatuwa bamu waje kinji", Nabilah ta yatsine fuska tace "toh ni kuma inje ina?", Maama tace "tsakar gida zaki fita", sakkowa tayi daga ruɓaɓɓen gadon tace "tsakar gida akwai rana wllh", Maama tace "ki zauna can kusa da banɗaki ba rana anan", tace "Maama warin kwata fa?", fuskar Shanu Maama tayi tace "ke dalla malama fitarmin daga ɗaki don ma kinga ana lallaɓaki, fita malama", Nabilah ta zumɓuri baki ta zumbula hijab ta fita, Balaraba dake kallonsu tace "gsky Rabii kin sangarta ƴaƴan nan naki", Maama tace "nasan akwai magana tinda naga kin fito rana gatsal-gatsal", Balaraba tace "uhmm, ai bazan iya bari rana tayi sanyi ba maganar cina take", Maama ta samu waje ta zauna tace "toh ya muke ciki ƴar uwa?", Balaraba ta riƙe haɓa tace "uhmm, ai ƴaƴanki basu miki ƙarya ba Rabii, Nura ai shagon chaji ne dashi ammafa a da, dan yanxu a babbar kasuwar saida wayoyi ya mallaki babban shago, uwarsa ma tayi sana'ar sayar da ɗan wake ammafa banda yanzu, tashi ɗaya Allah ya azurtashi daman ance akwai shi da ƙoƙari da neman na kai, yanxu dai babu maganar matsolontaka ko faƙiranci a tattare dashi, Mahaifinsa ya mutu shine yake kula da ƙannensa mata biyu da mahaifiyarsa cikin yalwa da wadata", Maama ta sharce zufar da ta keto mata ta tashin hankali tace "na shiga uku, ynxu ya za ai Balaraba?".........✍️ Likes comments and shares widely..👏 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {29..} Wani mugun murmushi Balaraba tayi tace "wnn ai bai kai abinda zaki shiga uku ba ƙawata, karki damu..", Maama ta katseta da faɗin "ya za kice kar na damu.., nace miki fa bana son yarinyar da uwarta su cigaba", Balaraba tayi tsaki tace "ai bazasu cigaban ba, me kike so ayi?", Maama tace "kar ayi auren nan ko ta halin ƙaƙa ne", Balaraba tace "kinxo ta gidan sauƙi, malamin tsamiya shi zai zartar miki da aiki kina zaune hankali kwance, wllh aikinsa kamar yankan wuƙa", Maama tace "yo ai idan ana neman ruwan kashe gobara har na kwata ɗiba ake, sai muje wajen nasa", Balaraba tace "hmm matsalarsa kuɗi, baya aiki sai yaji dumuss", Maama tace "wnn ba matsala bane, kamar nawa zan tanada?", Balaraba tace "Aƙalla ki riƙe dubu hamsin a hannunki", Maama ta gwalo ido tace "dubu hamsin, jar bala'i ina naga dubu hamsin", Balaraba tace "dole kam kiyo kashinsu in kina son burinki ya cika", Maama ta zabga tagumi tana tinanin a ina zata samo waɗannan kuɗi, Balaraba tace "uhmm idan so samu ne ma ace yanxu haka kinada kuɗin, in ban manta ba dududu saura wata ɗaya da sati biyu bikin ko?", Maama tace "haka yake", Balaraba tace "gsky dai ya kamata ki farga, ki nemo kuɗin nan fa", Maama tace "bani kwana uku zan nemosu kuwa", Balaraba tace "A toh kika tsaya bacci dai kwaɗo ne zai miki ƙafa", Maama tace "ke an ma samu fa an gama waɗannan kuɗi", Balaraba ta miƙe tace "to nidai nabi ta nan, daman cewa nayi bari nayi maza na ankarar dake", Maama tace "sai kin jini", Balaraba ta fito tsakar gida Maama biye da ita, a lokacin Hajar ta fito daga bayi knn, ta gefen ido Balaraba ke kallonta snn tayi soro, ta juya ta dubi Maama tace "itace ko?", Maama tace "itace shegiyar..", Balaraba ta jinjina kai sukay sallama da Maama ta tafi. Washe gari Hajar ta haɗa ƴan kayanta a Jaka zata wuce gidan Anty Jamila, tin ranar da aka kawo lefe Anty taso ta bita gidan amma Umma tace malam bazai bari ba, yanxun ma dai da kyar Baban ya amince, da yamma ta tafi bayan ta gama shirinta, murna wajen Hafsa ba'a cewa komai tace "yanzu fa shknn, ba zuwa gidan nan zaki ringa yi kina kwana ba", Hajar ta juya idonta tace "kin san me?", Hafsa tace "A'a saikin faɗa", Hajar tace "nifa banga lefen ba, ranar da aka kawo bana nan ina gidan Iya, kuma dana dawo ban bi takansu ba kar Umma tace min mara kunya", Hafsa tace "toh yanxu ya za ai?, gani za kiyi ne?, sai Anty tace miki mara kunyar", Hajar tace "A'a ke ni ba gani zanyi ba, ki gayamin mene ne aciki", Hafsa tace "chabbbb ai ki gani da idonki yafi, gsky fa ya sayyadinki ya zuba miki kaya", murmushi Hajar tayi tace "Allah..", Hafsa tace "Anty ta kira wacca za ta ringa yi miki gyaran jiki, ina jin ma jibi zata fara zuwa", Hajar ta gwalo lulu eyes ɗinta tana kallon jikinta tace "Me za a gyara", harararta Hafsa tayi tace "zaki gani ne aii". Humaira ce ta shigo tace "yaya Hajar wai kixo inji Anty", Hajar ta tashi tace "toh", suka fita tare da Humaira, room ɗin Anty suka shiga, Anty na zaune gefen gado ga boxes nan sun cika sararin ɗakin, Anty ta kalli Hajar tace "ki ma kwa ga kayan?", gyaɗa kai Hajar tayi tace "Eh", Anty tace "toh daman kiran da nay miki knn, tinda kin gani shknn", Hajar ta juya ta fita ta koma wajen Hafsa, tace "kiran da tay min tambayata tai naga kaya, ni kuma nace mata Eh", Hafsa tace "kinga kwantar da hankalinki, nasan Anty a wnn week ɗin ma saita fita, tinda bana zuwa schl an mana hutu mu bari idan ta fita sai muje kiga lefenki a tsanake". ★Da daddare Maama ta tarfa Sa'adatu da Maimuna a ɗaki, Sa'adatu tace "wllh Maama ni ba nida kuɗi, ina naga wata dubu talatin, ina ma laifin dubu goma amma shine za kice na baki dubu talatin, wllh ban dasu ba nida dalilinsu...", Maimuna da ta tamke fuska tamkar tsohon baƙin hadari tace "yo kema knn, bare ni, wai dubu ashirin", Maama tayi kwafa tace "duk za kuci gidan ku, dani kuke zancen, toh wllh ko kunƙi ko kun so sai kun bani kuɗin nan, yanxun nan ma kuwa", Maimuna tace "nidai Maama saidai ki yanka ni amma ban dasu eheee", Nabilah dake sauraron su tace "anayi ina cin indomie, ni kam ko ta kaina ba a bi sbd ansan babu, Hajjajai maza ku buɗe lalita hajiya Maama na jiran dumuss", Sa'adatu tace "ai kam dai baxa ta ji wani dumuss ba, Maama nidai kin san in ina dashi zan baki", Maimuna tace "nima dai in ina dashi zan.....", katseta Maama tayi da faɗin "ƙarya kike uwar mammaƙo, a gidan ubanwa kike ban iyee?, toh bari kuji in gaya muku karku zata ban sani ba, sarai nasan cewa ba makaranta kuke zuwa ba daga zarar kun fita sai ko waccen ku ta wuce shu'uninta, ko ku bani kuɗi ko na gayawa Babanku, kuma kun san cewa Nasiru na gida, babu abinda ya shalleni haka zan bada fuska ya zane muku jiki, kai wllh har ziga mal zan ringa yi dan jikinku ya gaya muku, ni zaku mayar yarinya kucemin wai baku da kuɗi..", Sa'adatu tace "to ki faɗa mana ai nace miki banda su...", Maama tace "haka kika ce ko?", Maimuna tace "Maama ai gaskiyar knn", gyaɗa kai Maama tayi ta isa bakin ƙofa ta ɗaga murya tace "Malammm", da wani mugun zafin nama Sa'adatu ta rufe mata baki, Maimuna kuma ta kama zaninta sai muzurai take, habawa ai Nabilah kifowa tayi daga kan gado sbd dariya, Maama ta kwace bakinta tace "zaku bayar ko a'a?", haɗa baki sukay su kace "zamu bayar", Maama ta hura tukubar hanci tace "jikinku ya huta" ta fizge zaninta daga hannun Maimuna. daga waje Baba ke neman ba'asin kiransa da akay, Maama ta sake ɗaga murya tace "daman cewa nayi barka da hutawa". A take Maimuna ta buɗe jakarta ta lalo duba ashiri ta miƙa mata a wulaƙance, Sa'adatu kuma ta kira Zeenatu tana mata wata maganar ƙirsa tace ta turo mata mutsabbai, da kyar Sa'adatu ta lusar da Maama cewa gobe da safe zata fita Pos ta ciro mata kuɗin. Da sassafe kam Maama ta tayar mata da mandiran zuciya, haka ta fita tasha wahala harta nemo pos ta ciro kuɗin ta kawo mata, tinda Maama taga dubu hamsin dumuss a hannunta ta fara shirin zuwa gidan Balaraba, ƙarfe goma na safe ta fice don saida ta bari Baba ya fita, tana isa gidan abokiyar cin mushen nata ta azalzale ta, sharp sharp Balaraba ta shirya suka saɓi hanya, tin ƙarfe sha ɗaya suka fita amma basu dawo ba sai yamma liƙis, gidan Balaraba Maama ta tsaya ta huta snn kuma ta amsa mata tambayoyin da take ta riƙonsu tin bayan fitowarsu daga wajen malamin tsamiya, ruwa kawai tasha ta hau surfa mata tambaya, Balaraba tace "kai Jama'a tinda fa yace aiki ya kammala to mgana ta ƙare", Maama da idanunta sukay jajur tsabar wahala ta tafiyar mota da ƙafa tace "da farko fa cewa yayi tabbas yaga ana biki, kuma aure sai an ɗaurasa", Balaraba tace "ai kece kika ringa cewa ga abinda kike so ayi, kinga kin ce masa a sawa yaron tsanar yarinyar kuma da ya duba allon bokancinsa yace miki hakan bazai yiwu ba sbd yaron akwai addini, ba za a iya samun galaba dashi cikin sauƙi ba, idan kwa aka matsa to lokaci zai ƙure har ranar auren tazo ba a samu galabar ba, shine yace ya sami lagon yaron wanda dashi zaiyi amfani, kuma ma yace aiki ya kammala kawai ki jira lokaci", Maama ta sauke wata gauruwar ajiyar zuciya tace "yanzu dai ba matsala knn?", Balaraba tace "kwarai kuwa, ki saki jikinki ki shiga bidirin biki, daga gefe kuma ki zubawa sarautar Allah ido kiga ta inda ɓaraka zata ɓullo", tin daga wnn moment Maama ta samu peace of mind, daga gefe guda kuma tana jiran ranar da faɗima da shegiyar ƴarta za suji kunya. ★Wani irin fresh Hajar tayi, fatarta tayi luwai luwai har wani sheƙi take sbd gyaran jikin da akai mata na sati biyar, ga wani sassanyar kamshi da yake tashi ajikinta, duk inda ta gifta sai ƙamshi, ko a waje ta zauna sai ya ɗauki lokaci ƙamshin bai baje ba, ilahirin jikinta kamshi yake, gashinta kam tamkar gonar furanni masu ƙamshi, babu inda take zuwa, ba ta shiga rana shiyasa gyaran yayi armashi, ko kitchen Anty ta hanata shiga, idan ma aikin za tayi iyakacinta palour da ɗakuna amma banda gaban wuta da rana, Nura kam kullum yana kan hanyar zuwa, ɗaiɗaikun ranaku ne kawai baya zuwa, ji yake tamkar ya janyo lokacin akay masa ita kawai, wata shaƙuwa ce ta shiga tsakaninsu a wnn taƙin, Yau ma dai mai gyaran jiki tazo tayi mata ta gama ta tafi, toilet ta shiga tayi wanka, ta fito tana wani ƙamshi na daban wadan ya gauraya da wanda take zubawa kafin shigarta wankan, zama tayi kan stool ta janyo sabon man da take shafawa na gyara fata da saka glowing, a tsanake take tattale fatarta da tayi wani laushi da santsi, ita kanta yaba kyan da tayi take a zuciya, Hafsa ce ta shigo hannunta riƙe da cup, ajiye cup ɗin tayi kan mirror tace "ki shanye yanxu ki bani kofin na mayar mata", Hajar ta ɗauki kofin ta kwankwaɗe ta miƙa mata empty, ( Ehen ba fa maganin mata bane, it's not good a bawa budurwa, maganin infection ne da cire dattin golden organs of a woman). doguwar riga ta material ta saka snn ta fita palour, zama tayi kan kujera tana latsa wayarta, tanan suke magana da zainab akan bikin musamman ma walimar da zatay, Anty ta fito da shirin fita da jaka a hannunta tace "ina Hafsa?", Hajar tace "tana kitchen", kitchen ɗin Anty ta shiga, bayan few seconds ta fito tace "na tafi", Hajar tace "A dawo lfy", tace "Ameen", snn ta fita, su Anty an shiga ruruma don yanxu bikin saura 1week, sha'anin jera gidan amarya suka karkata. A hankali Hajar ta dafe kanta tace "subhanallah innalillah wa'inna ilayhirraji'un" sakamakon gabanta da ya yanke ya faɗi ba gaira ba dalili, sau huɗu yana mata haka bayan zamanta a palourn, wayar ta ajiye ta miƙe ta tafi kitchen wajen Hafsa, Hafsa tace "Abu zaki ɗauka ne?", girgiza kai Hajar tayi tace "nope nagaji da zama ni kaɗai", Hafsa tace "kinga ki fita ynxu zan fito bari na gama zuba seasoning a miyar", Hajar tace "kawo na ɓare miki maggin", Hafsa tace "A'a zanyi da kaina, Anty fa tace ki dena shiga kitchen", turo baki tayi ta buɗe fridge ta ɗauki ruwa ta fita, tana ƙoƙarin zama gaban nata ya sake faɗuwa, nan ma dai Addu'ar tayi, har bayan Sallahr isha'i abinda take fama dashi knn, a hankali ta tashi daga kan dardumar da tayi sallah ta nannaɗe, wayar tace tayi ƙara wanda ya razanata tsabar rashin sukunin da ya risketa a bazata, ta ɗauki wayar tana kallon mai kiranta, ( ya sayyadi na) haka tayi saving, picking tayi ta kara wayar a kunne, ajiyar zuciya taji ya sauke snn yace "Hajar", tace "Na'am", yace "dan Allah fito na ganki, gani nan a ƙofar gida".......✍️ sorry 4d late update. likes comments and share my novel widely. 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {30..} Shiru tayi na some seconds kafin tace "tom" ta katse kiran, da dogon hijab din da tayi sallah ta fita, Humaira da Hafsa ne zaune palour, Abdallah ya fita masallaci salla, Hajar tace "Hafsa zan fita ƙofar gida", Hafsa tace "okay zuwa yayi knn?", gyaɗa mata kai kawai tayi ta nufi ƙofa, ta ƙetare small compound ɗin gidan ta buɗe ƙofar gate ta fita, jingine ta gansa da jikin gate ɗin, street light ta haska masa fuskarta, yayi ajiyar zuciya yana kallonta sosai, jinginar da kanta tayi jikin gate ɗin itama tace "ina yini", tini hancinsa ya cika da scent ɗinta, da cool voice ɗinsa yace "lfy alhmdllh, ykk?", tace "am fine", ya juyo sosai yana kallon yace "Hajar", kanta a ƙasa tace "Na'am", yace "karki bari azkar ya fita a bakinki, kinga dai ynxu zaki shiga ruruma, ki dage da Addu'a kinji", gyaɗa masa kai tace "insha Allah", ta ɗago ta kallesa tace "amma dai lafiya ko?", yayi ajiyar zuciya yace "alhmdllh", tace "ni kuma sai naga kamar you're not okay", keenly yace "partially", tace "me yake damunka?", murmushi yayi yace "ai tinda na ganki komai ya wuce, na dawo normal", tace "da gaske?", yace "uhmm", shiru ne ya ɗauka na wasu ƴan sakanni, ya katse shirun da faɗin "toh me kika shirya a bikin?", ta girgiza kai tace "ba komai", yace "ba komai, babu abinda za kiyi?", ta gyaɗa kai, murmushi yayi ya zaro envelope daga pocket ɗinsa, miƙa mata yayi yace "take", tace "meye wnn ɗin?", hade gira yayi yace "i said take", tasa hannu ta amsa tace "nagode", yace "good girl, toh shiga gida saida safe", tace "Allah ya tashemu lfy", har ta juya zata shiga sai kuma ta fasa ta juyo ta tsaya tana kallonsa kamar yadda shima yake kallonta, murmushi yay mata ta mayar masa snn ta shige. Ranar talata da yamma Hafsa ta rakata wajen salon, Anty tace tayi amfani da kuɗin da ya bata, wankin kai na musamman akay mata, natural aka bar mata gashin, steaming kawai aka ƙara mata bayan wash and set, sai kyalli gashin yake da sheƙi, daman baƙi ne siɗik shiyasa sheƙin yay yawa, Hafsa ma aka wanke mata nata, kafin magrib suka dawo gida, da wuri Hajar ta kwanta sbd ciwon kan da ya dameta uwa uba faɗuwar gaban da take fama da ita, washe gari da sassafe wacca za tay mata lalle tazo, saida tayi breakfast wanda kawai turawa take snn ta zauna aka fara shaɗana mata lallen, jan lalle kawai akay mata banda baƙi, inda za ai baƙin akay mata shi da ja, waoh lalle ya samu inda yake so wato farar fata ga kuma jiki yaji gyara, duk da yadda kanta ke ciwo haka ta jure aka rangaɗa mata kunshinta, mai lallen ce ta yarfa mata kitso sirara mai kyau two steps, sha biyu na rana angama mata komai, tayi kyau harta gaji kamar a sace ta, kaf suka shirya suka wuce ainahin gidan biki sbd a ranar akwai ƴar gaɗa da ƙawayenta suka shirya. lfy ƙalau aka gudanar da shagalin gaɗa a wani kango da aka gyara tsaf dake bayan gidansu, washe gari Alhamis saura kwana ɗaya ɗaurin aure wato ranar Juma'a, a ranar akay walima wacca ta ƙawatu matuƙa daidai gwargwado, Hajar tasha kyau har ta gaji. Maama kam bata tsoma hannunta aka komai ba haka ƴan ci ku bamunta, saidai fa zuciyar nan baƙi ƙirin tamkar ta iblus. ★Baba ne zaune bisa bencin mai siyar da dankali da doya a bakin titi, mai dankali dake cin banɗashen gurasa yace "mal Adamu gobe ne ko?", Baba yace "insha Allah, bayan Sallahr Juma'a za'a ɗaura", mai dankali yace "anan ƙofar gidan naka?", Baba yace "Eh", mai dankali ya luƙa wata ƙatuwar yankan gurasa baki yace "so samu ayi a masallacin juma'a na unguwar nan, yafi sarari kuma ga albarkar mutane", Baba yace "Eh saidai nafi son a ɗaura a ƙofar gidana, ƙofar gidansu yarinya", mai dankali ya jinjina kai yace "hakan ma yafi wllh, Allah ya kaimu goben", Baba yace "Ameen". wata shimfiɗeɗiyar mota mai numfashi ce tazo ta wuce, har tayi nisa sai kuma ta dakata kafin ta dawo da reverse, adaidai saitin benci da Baba da mai dankali ke zaune ta tsaya, tsayuwar motar a wajen ya katse musu firarsu, mai dankali ya suɗe hannu ya miƙe ya isa gaban motar sbd a zatonsa siyar dankalinsa ko doya za ai, tsaye yayi bakin motar yana gwalo ido yana jiran a buɗe ayi masa ciniki, da yake glass din motar tint ne don haka ba'a ganin wnda ke cikinta, back seat aka buɗe a hankali, wani mutum ne ya fito wnda yake sanye cikin wata shegiyar shadda, kawai kallon Baba yake kamar yadda Baban ma ya ƙura masa ido, mutumin ya saɓa babbar rigar jikinsa yana micincina idanu, miƙewa Baba yayi daga kan bencin, mutumin ya tako har kusa da Baba yace "Adam", Baba da shima ya ganesa ainun yace "Muktar", Alhj Muktar ya miƙawa Baba hannu sukay musabaha yace "duniya mai yalwa, Adam daman kana garin nan?", Baba yayi murmushin manya yace "Muktar ai kai zan tambaya daman kana garin nan, tinda nidae a sanina ai kana Abuja", Alhj Muktar yace "shekara ta sha biyar da baro Abuja na dawo Kano", Baba yace "ba masaniya", Alhj Muktar ya gyara babbar rigarsa ya samu waje ya zauna kan benci, Baba ma ya koma ya zauna, Alhj Muktar da yake jin wani daɗi na ganin aminin nasa da ya jima yana nema yace "ya bayan saduwa, ya iyali?", Baba yace "bayan saduwa sai alkhairy, iyali lfy alhmdllh an gode Allah, ya naka iyalin Muktar?", Alhj Muktar yace "Alhmdllh, amma dai ba'a kano kake zaune ba?", Baba yace "kano nake zaune Muktar", Alhj Muktar yace "baka koma Yola ba knn?", Baba yace "Eh, nan nake rayuwa da iyalina saidai dangina na can Yola", Alhj Muktar yace "masha Allah" ya faɗi hakan yana duba tsadadden wrist watch ɗin hannunsa, Baba yace "shekara da yawa Muktar, ban taɓa tunanin zan sake ganinka ba", Alhj Muktar yace "ikon Allah....", bai ƙarasa maganar ba drivern sa ya fito hannunsa riƙe da waya dake tsuwwa, russuna yayi ya miƙa masa hannu bibbiyu cike da girmamawa yace "ranka shi daɗe ana kira", Alhaj Muktar ya amshi wayar snn ya ɗaga kiran, maganar da bata wuce ta minti ɗaya ba yayi ya katse yana kallon Baba yace "Adam, zan sameka gobe a nan wajen", Baba yace "Eh to, ba damuwa zaka samen", Alhj Muktar yace "ko dai anan unguwar kake da zama?", Baba ya gyaɗa kai yace "a nan nake", Alhj Muktar ya jinjina kai yace "to ko bayan nan akwai wani wajen da zan iya samunka, insha Allah gobe fa zan dawo Adam", Baba yace "idan ma baka sameni anan ba, kana tambayar gidan gini shknn", Alhj Muktar yayi ajiyar zuciya ya miƙe, ya bawa Baba hannu sukay sallama snn ya doshi motarsa da driver ya buɗe masa ƙofa, mai dankali da ke daskare tin ɗaxu yaja baya gudun kar a markaɗe masa ƙafa, saida motar ta ɓace snn ya juyo ya kalli Baba, ya ƙaraso ya zauna yace "mal Adamu, wnn mutumin fa?", Baba yace "mutumin arziƙi wanda ya gaji ainihin arziƙi ba ƴan tashi firgigit ba, Muktar knn", mai dankali ya kasa kunne yace "yo Mal Adamu aini a duhu ka sake dulmiyani, ai ban gane me kake nufi ba", Baba ya dubesa yace "hmmmm, Idi knn" daga haka bai sake cewa komai ba. ★Ranar ta yau itace fa Juma'a, ranar ɗaurin auren Hajar, tin bayan sallar asuba ƴan uwan Umma suka ɗora sanwa, tuwo suka mulluƙa aka ɗaɗɗaura shi a leda aka zuba a ƙatuwar warmer, dabgen miyar taushe da taji tantakwashi itama aka juye ta a warmer, bayan nan aka shiga tuyar wainar shinkafa da sinasir, ga kuma gurasa da Mu'azzam ya kawo buhu guda. kai Hajar dai mai ƙashin arziƙi ce, tinda aka fara shagalin bikinta ba ai abu na ƙaranta ba duba da cewa gidansu ba masu hannu da shuni bane, komai an yisa cikin wadata, wnn magana ake ta masu arziki da yalwar zuci bata masu kuɗin banza da basu ciyuwa ba saidai a fito daga gida ana ƙombo, yo wasu masu kudin ma ai gidan su living hell ne. da gyatsine Balaraba ta shigo tsakar gida, duk wanda ke tsakar gidan nan kallon hadarin kaji tayi masa kafin ta faɗa ɗakin Maama, a karo na farko da Maama ta washe haƙora tin wayewar gari, Balaraba tace "wai haka aka mayar miki da gida sai kace na mahaukata Rabii", Maama ta taɓe baki tace "uhmm, baƙin cikin da nake shaƙa yafi ƙarfin kwatance", Balaraba ta ƙarewa Sa'adatu da Maimuna dake bacci kallo tace "su kuma basu tashi ba", Maama tace "ai jiya ba a barmu munyi baccin kirki ba a gidan nan", Nabilah da ke malelewa ƙasan siminti tace "Anty Balaraba ina kwana", Balaraba tace "yawwa". Maama ta matso kusa da Balaraba ta rage murya can ƙasa tace "kinga dai babu wani cigaba, anya kwa aikin malamin nan yayi?", Balaraba tayi yadda Maama tayi tace "hmm ai zuwa nayi na tayaki farin ciki, snn nima nasha kallo, don tinda malamin tsamiya yace ba aure to magana ta ƙare, kedai kawai mu zuba ido", Maama tayi ajiyar zuciya ta gyaɗa kai tamkar tsohuwar ƙadangaruwa. Tin daga soro har zuwa ƙarshen lungun ƙunshi aciki yake taf da jama'a, maza wanda suka zo halartar ɗaurin aure, ƴan uwan Baba na Yola da abokan arziki, ga dangin umma. daga soro kuma waliyyin Amarya da sauransu ne zaune suna jiran dangin Ango, lokacin ɗaura aure harya gota amma har yanzu dangin Ango basu hallara ba. Naseer da ke zaune soron ya dubi agogon hannunsa, yayi kyau sosai cikin farar shaddar da ya saka ta ankon da sukay shi da Huzaifa da Mu'azzam da kuma mahaifinsu, Naseer yace "lfy kuwa, ya har yanxu basu iso ba", Bappa ƙanin Baba wanda shi ne waliyyi yace "Baka da lambar wani daga cikin dangin Angon?", Naseer yace "ba nida ita Bappa", Mu'azzam ya shafa aljihun wandonsa yace "bari ni na kira Bappa", Bappa yace "yawwa, marmaza kira su, jama'a na jira", Mu'azzam ya ciro wayarsa daga pocket ya shiga kiran Nura Ango tinda lambarsa yake da ita, sau uku ya kira tanata ringing amma ba'a ɗaga ba. tsayawa yayi yana kallon uncle din nasa, Bappa yace "ya akay?", Mu'azzam yace "ba'a ɗauka ba"..........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {31..} A tare Baba da Bappa suka dubi Mu'azzam, Naseer yace "ka sake kira", Mu'azzam yace "tom" snn ya sake dialing numbern Nura, respond din dai daya ne, Baba da hankalinsa ya fara tashi yace "A ɗan jinkirta zuwa nan da minti goma sha biyar, ko wani uzirin ne ya riƙesu..", Bappa ya gyaɗa kai yace "ai ba jiran bane damuwa, jama'ar da suka taru kuma ba a rasa masu wani appointment din bayan wnn ba", Naseer yace "insha Allah yanxu zasu ƙaraso". Bappa yace "toh Allah yasa kar abar mutane a tsaye", kai har minti sha biyar da Baba ya ambata babu alamar dangin ango, tuni mutane suka fara canza fuska harda masu cewa su sauri suke, a yanxu kam hankalin Baba ya kai maƙura wajen tashi, Mu'azzam kam tinda ya koma gefe yake kiran lambar Nura. Naseer yanata duba agogon wayarsa, Bappa ya sharce zufar da ta wanke masa fuska sbd zafi, soron a cike yake da mutane gashi kuma ba a aiwatar da abinda ya tara jama'ar ba. kai abu fa ya fara wuce jira domin har an fara sidetalks, Huzaifa ne ya fito daga cikin gida ya durƙusa gaban Bappa yace "ko muje gidan nasu a jiyo lfy tinda nan gangare ne bamu da nisa", Bappa ya karkaɗa ɗan yatsansa yace "samm, ba zamu zubarwa da kanmu mutunci ba, a cigaba da jiran nasu, ai idan matsala ce waya zasu bugo", Huzaifa ya tashi ya koma kusa da Mu'azzam yana tambayarsa ko ya samu lambar. Daga ta cikin gida kam gidan biki ya ɗau harami, Umma sai warkajaminta take cikin riga da zani na atamfa mai shegen kyau, ta kashe ɗaurinta ture kaga tsiya, Hajar kam tana ɗakin Baba tare da ƙawayenta, kai kana kallonta kasan itace Amarya, tayi kyau harta gaji, abinda yafi birgeni da kwalliyarta shine yadda tayi maintaining natural beautyn ta, ba wata make-up da akay mata, Hafsa ce ta gyara mata fuska, powder mai tsane gumi kawai ta shafa mata sai zizaren kwalli da kuma colourless lip gloss wanda yasa pink lips ɗinta shining matuƙa, sassanyar kyau tayi kam ba ƙarya, ko nanda shekara ashirin ba a kalli hoton bikinta ayi dariya ba, dan wnn make-up ɗin ta zamani canja kamanni take ainun. Zainab ta kalli agogon wayarta tace "uhmm yaci ace an ɗaura fa, Hajar ta kusa zama matar ya sayyadi Nura", murmushi Hajar tayi tana jin wani daɗi har cikin ranta, hannunta da yaji zanen ƙunshi ta saka ta janyo wayarta, mesaage din da ya turo mata yau da safe ta binciko, ta karanta fuskarta ƙunshe da murmushi sai kuma ta sauke ajiyar zuciya tana juya lulu eyes ɗinta da yayi wani fari sol tamkar madara sbd kwallin da aka zizara masa, Hafsa tace "ko na zubo mana abinci ne?", Zainab tace "Eh kam gwara muci yanxu don nasan bayan ɗaurin aure sha'anin yini zamu shiga", Hafsa ta fita tsakar gida ta fara neman Anty tinda itace incharge of abinci, a ɗakin Umma ta sameta tana zuba tuwo sinasir wainar shinkafa da gurasa a mabanbantan warmers, Hafsa tace "Anty zan zuba mana abinci", Anty tace "tom ga plates can, idan kin gama zuba muku ki fita ki kiramin Mu'azzam ko Abdallah su fitar da na ƴan daurin aure gashi nan na fitar musu da nasu", Hafsa tace "tom", ta dauki plate ta zuba musu waina da sinasir, wani plate ɗin ta ɗauka ta zuba miyar taushe da isasshen tantakwashi, saida ta kai abincin ɗakin da suke snn ta fito ta doshi soro, leƙawa tayi waiko zata hango Mu'azzam amma bata ganshi ba, juyawa tayi kawai zata koma gida sai kuma ta tsaya tana sauraron wasu maganganu, cikin gida ta koma ta tarar da Anty ta fito tsakar gida, wajenta ta isa ta rage murya tace "Anty, kinji wai har yanxu dangin Angon basu zo ba", Anty tace "kamarya basu zo ba ai na ɗauka ma an gama ɗaura aure shiyasa nace ki fita kira Mu'azzam", Hafsa tace "A'a wllh ba a ɗaura ba", Anty tace "ikon Allah ko mene ya makarar dasu". Hafsa tace "bari naje muci abinci" da haka ta shige wajensu Hajar. wata shegiyar dariya Maama ta ɓarke da ita ta miƙawa Balaraba hannu suka kashe, Maama tace "ga dukkan alamu aiki yayi kyau, kinga har yanzu mirsisi banji maroƙi ya ambaci cewa an ɗaura aure ba", Balaraba tace "hmm ke dai bari, yanxu kawai tashi mu fita tsakar gida yadda zamu sha kallo muga ƴan bori", Maama ta tuntsure da dariya zuciyarta wasai tace "wllh kam ƴan bori, dan wllh tllh idan aka fasa auren nan tsaf faɗima za tayi bori", su Nabilah dai kawai binsu suke da kallo don basu rafko jirgin ba, miƙewa Maama tayi ta fita tsakar gida Balaraba biye da ita, kawai kallon Umma take tana yamutsa fuska cike da tsantsar tsana. A hankali yake shigowa cikin lungun yana ratsa mutane da suke basa hanya da kansu sbd shigarsa ta kamala, hehehe akace kuɗi ƙumbar susa, yana zuwa ƙofar gidan nan ma aka bashi hanya, ido huɗu sukay da Baba da ya kafe ƙofa da ido yana fatan dangin ango su shigo, Baba ya goge fuskarsa da handkerchief ya miƙe tsaye yace "Muktar, barka da isowa", Alhj Muktar yace "Amma Adam jiya fa muka haɗu da kai amma baka sanar min da abin arziƙin nan ba", Baba dai baice komai ba sbd hankalinsa baya jikinsa, Alhj Muktar ya gaggaisa da mutanen soron snn ya samu waje ya zauna. ★Wata zufa ce mai shegen yawa take tsattsafowa Nura, tamkar ƙaramin yaro haka yayi dafa'an gaban Hajiyarsa, fuskarta a murtuke tamkar baƙin hadari, Nura da zuciyarsa ke wani irin tafarfasa gami da dagargajewa yace "dan girman Allah Hajiyarmu kar ki min haka, kiyi haƙuri dan Allah", Hajiya dake zaune bisa kujera ta wani harɗe ƙafa tace "Nuraddeen", yace "na'am Hajiyarmu", with seriousness in her tone tace "matuƙar ni na kawoka duniya, matuƙar ni na ɗauki cikinka na wata tara, matuƙar ni na shayar da kai, matuƙar ni na raineka, matuƙar ina da daraja da kima a idonta to nace bana son auren nan, nace a fasa yin sa bazaka auri yarinyar ba", wata gudumar tashin hankali ce ta doka a kwanyarsa, kansa ya ɗau zafin da ya saka jinin jikinsa tafarfasa wanda ya linka tsiyayar gumi a sassan jikinsa, tamkar wanda aka sharawa ruwa haka gumi ya jiƙasa, farar Sabuwa shaddar jikinsa mai kyalli ta jiƙe sharkaf, idonsa da ya rine yayi jajur ya ɗago yace "Hajiyata, karki min haka dan Allah, me yasa.....", tsawa ta daka masa tace "tambayata kake Nuraddeen, akan wata zaka zo ka titsiyeni kana min tambaya sai kace sa'arka, wllh tllh indai baka tashi daga gabana ba yanzun nan saina tsine maka, kaji mu da mara kunyar yaro, daman an haifi wata yarinya a duniyar nan da zaka zauna a gabana ina fada kana fada akanta, to wllh kar a kuskura a ɗaura auren nan na gaya maka", shi dai kawai kallonta yake sbd canzawar da tayi, kamar ba Hajiyarsa ba, wacca bata masa tsawa, wacca kullum cikin saka masa albarka take, sai kace wacca aljanu suka shafa, sai ranar ɗaurin aure za tace a fasa, to me yake faruwa ne, kamar ba ita bace ta daɗe tana jiran wnn rana, guiwa a sace ya miƙe ya fita daga palourn nata, Babban palourn gidan ya shiga inda Uncles da kuma Aunties ɗinsa ke jiransa, tin ɗazu da Hajiya ta tubure aka kasa shawo kanta shine yace zaije da kansa ya bata haƙuri, shimfiɗar fuskarsa ma kaɗai amsa ce, kallonsa suka ringa yi kafin Uncle ɗinsa Saminu yace "ta haƙura Nuraddeen", Nura ya haɗiyi wani yawu wanda ya gagara wuce maƙogoronsa yace "A'a, tace tsine min za tayi", baki buɗe Saminu yace "A haba dai, ina zuwa", ya miƙe ya shiga palourn Hajiyar, haj Yahanasu ƙanwar Hajiya ta miƙe itama ta shiga palourn Hajiyar, Nura da kansa ke juya masa ya koma da baya ya tsaya a bakin palourn, duk abinda suke cewa yana ji a inda yake tsaye daga bakin ƙofa, Hajiya har ƙwarewa tayi tana kumfar bala'i ita Nura ba zaiyi aure ba, haj Yahanasu ta sauke wata ɓoyayyar ajiyar zuciya tace "Haba dan Allah yaya ki yiwa yaron nan adalci mana, mene dalilinki da zaki ce ba zai yi aure ba?, ki dubi Allah kuma kiji tsoronsa karki ɗauki haƙƙin yaron nan dan kina matsayin mahaifiyarsa", Hajiya tace "dakata Yahanasu karki min wata maganar banza a nan, cewa nayi kar yayi aure, ni ban hana Nuraddeen aure ba, abinda nace shine ba zai auri yarinyar can ba", haj Yahanasu tace "Yaya karki datse soyayyar dake tsakanin yaran nan dan girman Allah...", a matukar hasale Hajiya tace "Yahanasu karki kaini bango, dan wllh tllh zan iya zazzabga miki marii, kuma zan tsinewa Nuraddeen Albarka", sai a yanxu Saminu ya tanka yace "Hajiya ayi haƙuri, Nura fa ba yaro bane, tinda har yace aure zaiyi to ayi masa...", hannu Hajiya ta ɗaga masa tana karkaɗa ƙafa tace "wai ku me yasa baku da hankali ne, nifa ban hana Nuraddeen aure ba, amma tinda har kun ɗauki haramar fassarani baibai, bari na kashe bakin tsanya, ka aura masa ƴar wajenka Maryam yanzun nan, ai yarinyar na sonsa shine ya ƙi yace wai ƴar gidan gini yake so, ai aure dai aure ne ko wane iri ne, na yarda a aura masa Maryam a maimakon ƴar gidan gini", Nura ya jinginar da kansa a bango ya lumshe idanunsa da suke masa zugi, a zuciyarsa ya furta "innalillah wa'inna ilayhirraji'un", wai shine zai rasa Hajar ɗinsa, wnn wace irin mummunar ƙaddara ce, shekara sama da goma ya rayu da soyayyar Hajar ɗinsa, tin tana ƴar yarinya yake sonta har lokacin da ta mallaki hankalinta ta gane kuma Allah ya haɗa zuciyoyinsu, ya sake furta kalmar "innalillah wa'inna ilayhirraji'un" a fili. Saminu ya shafa tsigaggen gemunsa yace "anyi haka kuwa Hajiya, karfa ayi abinda zai ɓata zumunci", Hajiya tace "wnn abu ai saidai ya gyara zumunci Saminu, idan ka amince ka bayar da Maryam magana ta ƙare, na gaya maka Maryam tana sonsa, tin tini nasan da hakan har maganarta nayi masa kwanaki", Saminu ya sauke ajiyar zuciya don sosai ya aminta da hakan, barin ma da yaga Nura ya fara tara abin duniya. cikin mintinan da basu wuce ashirin ba aka ɗaura auren Nura da Maryam a babban palourn gidan, Nura da already ya fara ganin baƙi baƙi ya tashi yana haɗa hanya ya shige ɗakinsa. daga nan kuma wani ƙanin Hajiya ya bada shawarar cewa aje gidansu Hajar a sanar musu cewa an fasa auren, su uku ne suka shirya suka nufi gidan. wajen da aka bubbuɗa musu a soron suka zauna, wani sanyi Baba yaji a zuciyarsa, Bappa kam kallonsu yake ganin hannunsu siƙam babu goron ɗaurin aure, ƙanin Hajiya wanda shine Babba a cikinsu ya fara koro bayani, rufa rufa yayi ya musu bayani mai cike da nutsuwa ta hanyar da bai bayyana ainahin abinda ya faru ba, sarawa kan Baba yayi ya miƙe yace "ku dai ba mutanen kwarai bane wllh, baku san darajar alƙawari ba, kunsan baku shirya aurar da dan naku ba kuka nemi da a basa auren yarinya....", sarƙewa maganar tayi ya fara tari, da sauri Naseer ya miƙe ya riƙosa yana ƙoƙarin zaunar dashi, Bappa ya gyaɗa kai cike da takaici yace "Allah ubangijj ya musanya mata da wanda yafi ɗan ku Alkhairy a gareta, muma mun fasa aura muku ƴar mu", Saminu yace "Ayi haƙuri, dan Allah idan an nutsu kuje ku kwashe kayanku da ku ka zuba a gidan yaron mu, muma wanda muka kawo muku ku dawo mana da abin mu, ai da sulhu muka zo", Bappa yace "karku damu za a dawo muku da komai tsinke ba za a bari ba". Saminu yace "Allah ya haɗa kowa da rabonsa", da haka suka bar soron, ƴan ɗaurin aure suka fara tashi da nufin tafiya, wasu na jajantawa yayinda wasu suka samu abin gulma, tamkar saukar wahayi daga zama haka soron ya amsa ƙuwwa da kalmomi shida da suka fita daga bakinsa "ina nemawa ɗana auren wnn yarinya", Bappa ya dubi Alhj Muktar da yayi wnn furuci, Baba ma da yake cikin tashin hankali ya dubesa, mutanen da suka fara tashi da sauri suka koma suka zauna, Alhj Muktar ya miƙe ya isa gaban Baba yace "Adam ina nemawa ɗana auren ƴar wajenka da aka fasa aura yanxu", wani ɗaci ne ya kauraye bakin Baba wanda yake jin tamkar an musanya masa miyau da ruwan maɗaci, expression ɗin fuskarsa bazai misaltu ba, kasa cewa komai yayi, Bappa ya girgiza kai yace "A'a, ba zan iya aura mata wanda bansan koshi waye ba, ban san komai a kansa da ya kamata na sani kafin aure ba...", Alhj Muktar yace "nine mahaifinsa, amma nasan bana daga cikin jerin mutanen da za a tambaya shaida a kansa, koda ba za a tambayeni ba amma zan faɗa cewa ɗana nagartacce ne, halayensa masu kyau ne saidai kuma ko wane ɗan Adam tara yake bai cika goma ba, a matsayina na uba kuma mahaifi wanda bazan so abinda zai cutar da ƴaƴana ba toh haka zalika bazan cutar da ƴaƴan wasu ba, ba nida wata manufa na nemawa ɗana auren wnn yarinya face manufar alkhairy". Bappa ya sake girgiza kai, Naseer ma dai girgiza kan yayi kuma har cikin ransa bai aminta ba, Baba ya dubi fuskar aminin nasa Alhj Muktar snn ya dubi ta ƙaninsa Bappa, ajiyar zuciya yayi yace "Muktar na amince maka, Bappa a ɗaurawa Hajara aure da ɗan gidan Muktar".........✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {32..} Bappa ya ringa kallon Baba kafin yace "kace na daurawa Hajara aure da yaron da ba musan waye shiba?", Alhj Muktar yayi murmushin manya yace "naji daɗin wnn furuci naka, tabbas kanada gsky sosai, nima hkan zanyi idan na samu kaina a matsayinka na yanzu, kuma nima na taɓa shiga irin wnn yanayin da Adam ya shiga yanzu, na sake faɗa cewa ɗana nagartacce ne, amma idan zuciyarka ba ta aminta ba shknn ba damuwa", Baba ya dubi Bappa yace "A ɗaura mata aure da ɗan gidan Muktar, ba nida shakku ko kaɗan a kalamansa, na yarda dashi...", Bappa yayi ajiyar zuciya yace "tom, Allah ubangiji ya tabbatar da Alkairi" sai kuma ya dubi Alhj Muktar yace "fatan dai akwai sadaki a kusa", Alhj Muktar da walwala ta bayyana ƙarara a fuskarsa yace "akwai, bani minti uku", wayarsa ya ciro daga aljihu ya kira drivernsa, da sauri driver ya ɗauka, Alhj Muktar ya umarcesa da ya ɗakko masa kuɗi a mota, bayan minti bakwai driver ya bayyana a soron, ya durƙusa gaban Boss dinsa ya ciro wasu maƙudan kuɗi daga pocket ya ajiye, Alhj Muktar yace "zauna ka zama shaida", ba musu ya zauna ya tankwashe ƙafa, Alhj Muktar ya ɗauki uwar kuɗin ya ajiye gaban Bappa, Bappa ya dubi kuɗin ya girgiza kai yace "wnn kuɗin sunyi yawa", Alhj Muktar yace "ba suyi yawa ba, sadaki ai baya yawa saidai yayi kaɗan", ( Ehennnn a zamanin nan sai kaji mutane suna cewa wai ba a tsawwala sadaki ai ba siyar da yarinya za ai ba, to ga point of correction ba wani siyar da yarinya, shi fa sadakin aure baya yawa a musulunce, matuƙar kanada ikon bawa matarka zunzurutun dukiya mai yawa matsayin sadaki toh ba matsala, tauye sa shine matsala, wllh idan ma kanada arziƙin raba kano gida biyu ka bata rabi matsayin sadaki hakan daidai ne). An ɗaura auren Hajar da ɗan gidan Alhj Muktar bisa sadaki mai tsoka, ɗaurin auren ya samu shaidu masu yawa, Baba ya lumshe idonsa ya furta "alhmdllh", maroƙi ya ɗaga murya yana sanar da jama'a cewa ɗaurin aure ya kammala, muryarsa har cikin gida ta ratsa, wani mugun bugu zuciyar Maama tayi jin muryar maroƙi ta daki dodon kunnenta, ta juya ta kalli Balaraba da ta hangame baki har ƙuda na ƙoƙarin afkawa ciki, Wasila ta ɗaga zureren hancinta sama ta rangaɗa guɗa, murmushi mai kyau Umma tayi. Maama da idonta ya kisfe tsabar takaici tace "wllh sai malamin nan ya biya ni kuɗi na, kadan ba sai ya biya ba", Balaraba tace "abin fa da mamaki, tinda nake dashi bai taɓamin aiki baici ba, wllh a tarihin aikinsa ma baya faɗuwa, gaskiya akai abinda ya faru Rabii", Maama tace "Eh ai kam ga aiki nan na gani", Balaraba ta dafe kai tace "Rabii akwai lauje cikin naɗi, mu tsaya dai muyi kallo". Mu'azzam ne da Huzaifa suka ringa firfita da abinci, walima aka baje a soro ana kwasar dabge. Alhj Muktar da Baba suka fita daga soron zuwa can inda babu taron jama'a, godiya Alhj Muktar ya ringa yiwa Baba, shima Baban godiya yake masa domin kwa ya fitar dashi kunya, Alhj Muktar yace "insha Allah da yamma zasu zo", Baba yace "bana ganin ɗaukar yarinyar nan zai yiwu a yau, a bari zuwa gobe, kaga dai yadda lamarin ya jirkita, shima yaro ai sai an sanar dashi...", Alhj Muktar yace "toh ba damuwa da yau da gobe ai duk ɗaya ne, karka damu yaro a shirye yake", Baba yace "nagode fa, kaxo domin mu gana sai kuma wnn batu ya gifta bamu samu lokacin ganawarba", Alhj Muktar yace "daman nazo ne domin naga inda kake Adam", Baba yace "Allah sarki", Alhj Muktar ya miƙa masa hannu sukay sallama snn ya tafi. saida rurumar ƴar ɗaurin aure ta tsagaita snn Baba ya samu shiga gidan nasa, nan fa akay masa caa da gaisuwa da kuma fatan alkhairy, da sakakkiyar fuska ya ringa amsawa yana neman Umma da idanu, daga ɗakinta ta fito fuskarta ƙunshe da walwala, Baba ya dubeta yace "ɗakinsu Nasiru a buɗe yake?", tace "bari na duba", ta wuce ƙofar ɗakin ta tura taga a buɗe take, tace "Eh a buɗe take", ya ƙarasa ƙofar ɗakin yace "ina son ganinki" ya shiga ciki. afujajan Maama ta fito daga ɗakinta jin muryar Baba, wuwwurga idanu ta fara yi duk ta jiƙe da gumi, hangosa tayi lokacin da ya shiga ɗakinsu Huzaifa, da sauri ta wuce har tana ƙoƙarin bangaje Umma ta shiga ɗakin, kallonta Baba da yake shirin zama yayi, Umma dai ta shigo ta samu waje ta zauna, daga tsaye Maama tace "tin safe ka hana mu kudin abinci a gidan nan mal", yace "kuɗin abinci kuma Rabii?, ga abinci nan ku zuba kuci", tace "a ina yake abincin?, ni bangani ba", ya ciro 1k daga aljihun gaban rigarsa ya miƙa mata yace "gashi", amshewa tayi tace "yo da an barni da yunwa nida ƴaƴana", ta juya zata fita sai kuma ta dubi Umma tana yamutsa fuska, dawowa tayi ta zauna ta wani sha kunu, Baba yace "ba na baki kuɗin abincin ba", gefe ta kalla tace "Eh anan zan zauna", Baba yayi ajiyar zuciya baice komai ba, shiru ɗakin ya ɗauka babu wanda ya sake magana, bayan wani lokaci Umma tace "mal ko na tafi ne akwai baƙi da suke jirana", Baba ya girgiza kai yana kallonta yace "Faɗima", tace "na'am". kaf ya wassafa mata abinda ya faru akan auren ƴarta. wata katafariyar shewa Maama ta daka, ta miƙe da sauri ta fice tana gyara haɓar zaninta, saida ta shiga tsakiyar ƴan biki tace "ahayye riiiiiii, an yanka ta tashi, kowa ya baje an gama biki", ta afka ɗakinta domin ta sheƙawa Balaraba nasarar da suka samu, murna suka shiga ɓarkawa a ɗaki tamkar waɗanda akay wa bushara da gidan aljanna, sosai suka saki baki suna zance sbd su Nabilah sun fice daga gidan. Umma ta tuge ture kaga tsiyar kanta ta share zufar da ta tsattsafo mata tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un, mal dama baka ɗaura mata aure da wani ba...", katseta yayi yace "karki ɗaga hankalinki Faɗima, kiyi mata addu'a Allah yasa hakan shine alkhairy a gareta", tace "amma mal...", yace "idan kika ɗaga hankalinki waye zai kwantarwa da Hajara nata, itace wacca ya kamata a duba, idan kika samu nutsuwa itama hankalinta ba zai tashi sosaii ba, ƙaddararta ce, ko wane dan Adam da irin tasa, Allah ya rubuta ba Nura ne mijinta ba, ni kuma na gaya miki mutumin da na bawa auren Hajara bashi da matsala", Umma ta ajiye deep breathe tace "Allah yasa hakan shine alkhairy, amma taya ya zan sanar da ita?", Baba yace "she's your daughter fa, ki kiramin ita", ta gyara daurin dankwalinta ta miƙe ta fita da wani facial expression a fuskarta. ɗakin Baba ta nufa inda Hajar da muƙarrabanta ke zauna, a bakin ƙofa ta tsaya tana kallonsu, Umma ta dubi Hajar da tayi wani kyau wanda bata taɓa irinsa ba a rayuwa tace "kije inji Babanku yana ɗakinsu Mu'azzam", Hajar tace "tom", ta saka wayarta acikin handbag dinta, gyara yafen mayafinta da yake fitar da ainahin ƙamshin kabbasa tayi, ta saka takalminta flat mai kyau snn ta fita. Umma kam ɗakinta ta shige, ta matsar da kayan dake gefen gado ta zauna ta dafe kanta, a haka Anty ta shigo ta sameta tace "Adda, lfy kuwa?, ya da tagumi haka a lokacin farin ciki", Umma ta ajiye numfashi a hankali tace "Jamila", Anty ta samu guri ta zauna sbd yanayin ƴar uwarta ta, Umma tace "kin san kwa bada Nura aka ɗaurawa Hajara aure ba", Anty ta gwalo ido tace "ban fahimce ki ba Adda", Umma tace "uhmmm" ta labarta mata abinda Baba ya sanar da ita, shiru Anty tayi tana kallonta, kasa cewa komai tay kawai juya lamarin take a kwanyarta, can tace "kiyi haƙuri Adda amma sai naga kamar kun yiwa Hajar gaggawa, wai har nawa take har yanxu fa bata cike shekara 18 ba, dan ma tanada garun jiki amma wllh bata isa aure ba...", Umma tace "ba haka bane Jamila, muma ai bamu kaita ba aka kaimu gidan miji, kuma muka zauna", Anty tace "haka ne Adda, duk yadda zamani ya juya haka za a tafi dashi, a wnn zamanin aure yafi kyau idan yarinya ta kai shekaru 20, ta mallaki hankalinta...", Umma dai tayi shiru, Anty tace "Hajar ɗin ta sani?", Umma tace "Eh nasan yanzu ta sani, Mal ya sanar da ita". Hajar ta fito daga ɗakinsu Mu'azzam ƙafarta na harɗewa, da gudu ta shige ɗakin Umma ta zube a ƙasa snn ta fashe da wani matsanancin kuka mai ban tausayi, runtse ido Umma tayi tana jin itama kamar tayi kukan, Anty ta taso ta ɗagota ta rufe mata baki tace "shhhh, kiyi haƙuri kinji", kuka take kamar ranta zai fita. ★Mami ta murɗa handle ɗin ƙofar part ɗin Abba, da sallama ta shiga, Abba dake zaune kan kujera two sitter ya amsa mata, a gefensa ta zauna, ta ɗauke hularsa dake hannun kujerar ta ajiye bisa huge Centre table dake palourn, tace "gani yallabai, amma dai ba'a masallacin sarki kayi juma'a ba?", Abba ya sosa forehead dinsa yace "Eh, a can Masallacin Abubakar Siddiq nayi", tace "Ohk", yace "yau ce ranar da Uthman zai dawo ko?", tace "insha Allah, ɗazu na gama waya dashi sun ma taso, 9pm za suyi landing", ya gyaɗa kai yace "Alright, a yau da na fita ban dawo gida ba saida na ɗaurawa Nurain aure", cike da mamaki Mami ta dubesa har tana haɗe gira tace "aure kuma yallaɓai?", yace "yess, so start all the necessary preparations tommorow insha Allah za aje a ɗakko masa matarsa", Mami was speechless na kusan 1minute kafin tace "but without his consent aka ɗaura", yace "Do i need his consent, he is my son, he most respect my decision", Mami tace "this is a different case...", yace "i know, a da fa haka ake daura maka aure ba tare da kasan waye ka aura ba, iyaye ne kawai suke haɗinsu", Maami exhale heavily tace "wa ka aura masa?", yace "sunanta Hajar, ƴar wajen abokina ce", tace "Allah ya basu zaman lfy", yace "Ameen, key din gidansa na wajenki ko?", tace "Eh suna wajena", yace "ohk, sai a duba gidan nasa kafin Allah ya kaimu gobe", tace "sure, za ai komai". Mami na fitowa daga wajen Abba ta shiga kiran ƴar uwarta Zulaiha, tana picking Mami tace "idan ba damuwa ina son ganinki Zulaiha", Anty Zulaiha tace "ohk, when?", Mami tace "idan ma zaki taho yanxu to nafi son haka", Anty Zulaiha tace "is everything ok?", Mami tace "sure, komai lfy urgent abu ne ya taso", Anty Zulaiha tace "Shknn I'll be there right away", da haka Mami ta katse kiran thinking of another thing to do, After 40mins Anty Zulaiha ta iso tare da Khausar, direct palourn Mami suka wuce, Khausar ta sunkuya ta gaida Mami, amsawa Mami tayi tana tambayarta school, Noor ce ta fito daga bedroom din Mami sanye da english wears, gaisawa sukay da Anty Zulaiha snn taja hannun Khausar suka fita daga part din zuwa huge room ɗinta, Anty Zulaiha ta cire gyalenta ta gyara zama sosai bisa executive sofar palourn tace "wai mene ne abinda ya taso urgent?", Mami tace "ɗaxu Abba da ya dawo daga masallaci yake gayamin cewa wai ya ɗaurawa Nurain aure da ƴar abokinsa", Anty Zulaiha tace "ikon Allah, daman har yanzu ana irin wnn haɗin", Mami tace "nima dai haka nagani, saidai fatan alkhairy, wai sai gobe za a kawo amaryar, yanzu dai gidan Nurain din nake so aje a duba, an riga anyi furnishing dinsa amma kuma almost 8months ba shigesa ba, kinga za aje a dudduba abinda yayi damage, komai dai ya zama intact", Anty Zulaiha tace "toh ai wnn ba aikin mu bane, na dangin Amarya ne", Mami tace "yess nasu ne, Abba ne yace a buɗe gidan a gyara", Anty Zulaiha tace "toh shknn, ai sai a tura ma'aikata su gyara, su firfito da abinda yayi damage, mu kuma in Allah ya kaimu goben sai muje mu gani", Mami tace "nima haka nake tunani, kawai a tura masu aiki", Anty Zulaiha tace "toh kuma haka za a ajiye yarinyar a gidan babu mijinta", Mami tace "No, ai yau Nurain ɗin zai dawo", Anty Zulaiha tace "toh masha Allah abu yayi kyau kinga yana dawowa sai yayi Settling down, Allah yasa ta zame masa babban tukuici na abinda Ruqayyah tayi masa", Mami tace "Ameen". labourer aka tura katafaren gidan Nurain, tin daga sama har ƙasa aka shiga tsaftacesa, babu wani datti sai dust da dry falling leaves. ★Da misalin ƙarfe takwas da minti hamsin na dare ya parker luntsumemiyar motarsa a parking space da ke babban international airport na garin kano, waiting area ya nufa ya zauna yana kallon wajen da matafiya suke ɓullowa, yana jin announcement na saukar jirgin da ya iso daga India ya miƙe tsaye, few minutes kam suka fara fitowa, shine na biyar, sanye yake cikin ƙananan kaya da Pcap saman kansa kamar yadda ya bar 9ja, hannunsa daya na riƙe da trolley da yake ja yayinda ɗaya yake maƙale cikin sweet black pant nasa, Farooq na hango brother din nasa ya fara tafiya towards him, Nurain ya ciro hannunsa daga pocket ya dunƙulesa, shima Farooq dunƙule hannun nasa yayi, suna haɗewa suka haɗa hannayen nasu, Nurain yayi murmushi yace "hey dude", Farooq yayi masa side hug yace "barka da zuwa punk". saida aka gama checking luggage ɗin Nurain snn suka baro airport din, Farooq dake driving da mininum speed yace "ko dai wajen amaryata zamu wuce", Nurain yace "No, iron lady ban shirya facing dinta ba", slight smirk Farooq yayi yace "tsohuwa mai ran ƙarfe", Nurain yace "oh God look at how you're driving, ka take accelerator", Farooq yace "as in how na take accelerator, wai naga fa Doctors suna lallaɓa lafiyarsa amma look at you kana so ayi risking taka", Nurain yayi resting jikin kujera can ƙasan maƙoshi yace "hurry up". Farooq ya ƙara gudun motar kaɗan, slow down yayi kafin ya juya kan motar ya shiga street din gidan uncle ɗinsa, a bakin huge gate ɗin gidan ya danna horn, da sauri mai gadi ya zuge gate, ya danna motar ciki, parking lots ya isa yayi parking snn ya kashe motar, yana ciro key daga Ignition yace "did you just take a nap?", Nurain ya buɗe idonsa yana kallon environment ɗin ya yake ciki, buɗe motar yayi ya fita, yayi ajiyar zuciya yana stretching kansa yace "home sweet slum".......✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {33..} Farooq ya buɗe back seat ya ciro bag da trolley, ya kalli Nurain da ya gama stretching kansa yace "wai ka gaji ne?", Nurain yayi ƙass ƙass da fingers ɗinsa yace "yeah, am exhausted". da sauri Garba ya taho wajen, har ƙasa ya durƙusa yace "sannu da zuwa Alhj ƙarami, an dawo lfy", Nurain yace "yauwa Garba, ya ƙasa?", Garba yace "ƙasa tana nan yadda ka barta", tashi yayi ya gaida Farooq ma snn ya amshi bag da trolley. huge luxury main building ɗin gidan suka nufa, suna isa balcony Nurain ya danna bell, few seconds Noor ta buɗe, ta daka tsalle tace "oyoyo Yaya" sai kuma ta koma cikin palourn tana cewa "the groom is here Mami", sosai abinda ta faɗa yayi hitting eardrums dinsa, wai the groom, ya juya ya dubi Farooq yace "you", Farooq ya girgiza kai yace "nope", ai tini Noor ta shige part din Mami, Farooq ya zauna a daya daga cikin executive sofar dake babban palourn, Garba ya ajiye kayan da ya shigo dasu yayi waje, Nurain kam part din Mamin sa ya nufa, Mami ta fito daga bedroom ɗinta knn ya shigo, Pcap ɗin kansa ya cire ya zo ya rungumeta yace "i missed you Mami", Mami tace "Nurain...", Noor da ke murmushi all her white tooth out tace "Yaya sannu da zuwa", yace "lil iron lady, how are you doing", tace "am great alhmdllh", Mami tace "ina Umar ɗin?", yace "yana palour", tace "Ohk, muje can", main palourn suka fito, Mami ta zauna tace "mijin Hajiya", Farooq yayi murmushi yana shafa kansa ya zamo ƙasa ya gaidata, Mami ta amsa tace "ka ɗakko brother ɗinka knn?", Nurain ya zauna bisa lallausar rug din palourn ya gaisheta shima, ta amsa tana saka masa albarka, Kitchen Noor ta shiga ta ɗakko ruwa da drinks with glass goblet ta fito, kusa da Farooq ta ajiye tace "ina yina ya Farooq", yace "lfy lou Noory", tace "yasu Ummi da Aysha?", yace "suna nan lfy". Nurain yace "Abba fa?", Mami tace "yana ciki", yace "ohk bari naje wajensa", ya dubi Farooq yace "muje dude", a tare suka shiga part din Abba, Mami ta dubi Noor dake operating waya tace "ohh kin fara jarabar danna wayar ko?", tace "No Mami, course mate ɗita ce ta turomin da question na assignment", Mami tace "toh tashi ki shirya musu dining kafin su fito", tace "tom", ta ajiye wayar ta gyara hular kanta ta shiga kitchen. Abba ya kawar da system da yake operating ya daga kai yana kallon zaratan samarinsa, da Farooq suka fara gaisawa kana Nurain, Abba yace "ya aiki Engineer?", Farooq ya shafa kansa yace "alhmdllh Abba", Abba yace "toh madallah Allah ya temaka", Farooq yace "Ameen", Abba yace "Uthman..", Nurain yace "na'am", Abba yace "ya karatun, an gama lfy?", Nurain yace "Eh alhmdllh, an samu abinda aka je nema", Abba yayi ajiyar zuciya yace "masha Allah, Allah yasa ya amfana", tare suka amsa da Ameen snn suka fito. already Noor ta gama setting table, Mami tace "ga abinci kan dining", Farooq ya dubi tsadadden agogon wrist dinsa yace "wllh Alhmdllh, am full, zan wuce yanxu", yayi musu sallama ya tafi, har compound Nurain ya rakasa snn ya dawo, Noor ya saka ta kawo masa abincin nan palour ya ci don shi he don't like it eating on table, ba laifi yaci abincin cause yaji taste en abincin na Mami ne, ya ture plate din daga gabansa ya buɗe bottle water ya zuba a cup ya sha, stretching kansa yayi yana lumshe ido, duk gajiya ce ajikinsa, duk lokacin da yayi tafiya a jirgi sai yaji kamar nerves ɗinsa sunyi freezing, shiyasa yake yawan yin miƙa, Mami tace "ka je ka huta Nurain", yayi ajiyar zuciya yace "yeah", ya tashi yana massaging neck dinsa, trolleynsa ya janyo yace "ga stuff na India", Noor tace "Yaya a New Delhi ka zauna?", yace "yap, that's where my school is", da haka ya ɗauki bag ɗinsa ya haye stairs still massaging his thick neck, ya tarar da room ɗinsa a gyare tsaf tsaf komai tide, ƙamshin freshner da traditional scent mai dadi ne yake tashi, ga sanyin Ac, huge Chinese comfortable bed ɗinsa malale da white bedding. wayarsa ya ɗakko daga bag yayi powering dinta, ya cire Sim card ɗin ciki ya musanya da ainahin nasa na Nigeria, ya ajiye wayar akan mirror ya shiga bathroom domin ya sakarwa kansa warm water, ko 1min beyi ba da shiga wayarsa ta fara tsuwwa, kiran na yankewa wani ya sake shigowa, shima yana katsewa wani ya biyo baya, haka kiran yayi ta shigowa ba ƙaƙƙautawa, da sauri ya gama abinda zai ya fito, yayi wrapping kansa da bathrobe, gefen kunnensa duk kumfa sbd saurin da yayi ya fito don yaga wane yake masa wnn mummunar kiran daga kunna waya, ɗaukar wayar yayi wacca take ringing har lokacin, ya tattare gira gami da tsuke piercing eyes ɗinsa yana kallon screen ɗin wayar, sunan da yake jiki da kuma numbern ba baƙinsa bane, tabbas beyi blocking numbern ta ba amma kuma bai sake kira ba, wani ɗaci yaji a throat ensa, ya dangwarar da wayar yace "Damn it.." ★Kaf waɗanda suka zo biki sun daɗe, mutanen Yola kam ana gama ɗaurin aure suka saɓi hanya, Anty Jamila sai Hafsa wacca aka bari domin ta ɗebeba Hajar kewa ne kawai suke rage a gidan, Wasila kuma ta tafi da zummar insha Allah gobe da sassafe zata dawo. da hijab ɗin da tayi sallar isha'i ta ƙudunduna ta takure waje ɗaya, a kwance take kan dardumar da ta idar da sallah, hawaye na zuba daga manyan lulu eyes ɗinta waɗanda suka ƙanƙance tsabar kukan da ta sha, ƙirjinta da maƙoranta har zafi suke sbd shessheƙar kuka, Anty ta tsaya a kanta tace "hasbunallah, Hajar ba zaki dena kukan nan ba ko?", da dasasshiyar murya tace "ba kuka nake ba", Anty tace "toh tashi zaune", a hankali Hajar ta miƙe zaune ta jingina da bango, sosai ta bawa Anty tausayi tace "za kici abinci?", ta girgiza kai tana goge kumatunta tace "na ƙoshi, bazan iya ci ba ƙirjina ciwo yake", Anty tace "sannu, ai baza ki kwanta da yunwa ba bari a siyo miki yoghurt" da haka ta fita daga ɗakin. Hafsa ta matsa kusa da Hajar tace "sannu sister", Hajar tace "wllh ji nake kamar zuciyata zata fashe, wai ba ya sayyadina na aura ba, na shiga uku Hafsa", ta rufe fuskarta da hijab ta sake rushewa da kuka, Hafsa tace "Allah ya ƙaddara ba shine mijinki ba, kiyi addu'a Allah yasa hakan alkhairy ne a gareki", Hajar na shessheƙar kuka tace "ban san fa wanda aka aura min ba, ban san wane irin mutum bane". Hafsa tace "koma waye insha Allah alkhairy ne", jinginar da kanta tayi a bango ta lumshe idonta, hawayen da suka taru suka fara zarya a kuncinta. Sallama aka rangaɗa daga soro, Anty dake tsakar gida tana waya da Mu'azzam da take basa saƙon siyo yoghurt, kashe wayar tayi ta amsa sallamar da akay, Umma ta fito daga ɗakin Baba tace "waye?", matar da tayi sallama ce ta shigo tace "Larai ce", Umma ta tsaya tana kallonta da taimakon hasken kwan lantarki sbd akwai nepa, Umma ta shimfiɗa tabarma tace "Bismillah" duk da dai bata shaida wace ce ba, dattijuwar da ta kira kanta da Larai ta zauna akan tabarmar da Umma ta shimfiɗa, gaisawa sukay, Anty ma ta gaisheta, ta dubi Umma tace "baiwar Allah kece mahaifiyar Hajara", Umma tace "Eh nice", tace "Alhmdllh, wllh tllh nice nayi muku laifi, dan girman Allah kuyi haƙuri", Umma tace "Allah sarki, laifin me kika min baiwar Allah?, ai ni ban ma shaida ki ba", tace "mahaifiyar Nuraddeen ce wanda za a ɗaura masa aure da ƴarku", tini Umma ta canza fuska, Anty da ke zaune kan ƙaramar kujera ta ɗaure fuska, Umma tace "oho, to ince dai lfy?, ai an mayar muku da kayanku", Hajiya tace "ba wnn bace ta kawoni, dan girman Allah kuyi haƙuri akan abinda mu kayi muku, wllh laifina ne shiyasa na taso takanas nazo domin na baku haƙuri", Umma tayi murmushin yaƙe tace "ba komai mun haƙura, muma Allah ya yafe mana", Hajiya tayi ajiyar zuciya tace "Alhmdllh, Allah yayi albarka, auren da aka fasa ɗaurawa da rana sai a ɗaurasa yanxu da daddare", Umma ta ajiye numfashi tace "bari nayi miki magana da baban yarinyar" da haka ta miƙe ta shiga ɗakin Baba, kaf yaji abinda ya faru don haka bai bata damar magana ba ya fito tsakar gidan, Anty ta tashi ta shiga ɗaki. Baba ya gaisa da Hajiya wacca ta shiga basa haƙuri, yace "Allah sarki, ai komai muƙaddari ne..", Hajiya tace "haka ne, amma wllh nice nan silar wnn babbar ɓarna, dan girman Allah ku yafe min, a ɗaurawa ɗana Auren da yarinyar ku", Baba yayi ajiyar zuciya yana jujjuya wnn lamari, Maama ta fito da ɗauri ƙirji da mafici a hannunta tace "haba don Allah, wllh kun fiya gutsittsira zance, kawai ku gaya mata cewa an ɗaurawa Hajara aure da wani a maimakon ɗanta", da matuƙar mamaki Hajiya ta dubeta sai kuma ta kalli Baba tace "wai haka ne?", Maami tace "Yo ya faɗa miki da bakinsa kiji, shi ya aura mata wani da ɗanki yace ya fasa", Hajiya ta fara matsar kwalla tace "wllh babu ruwan Nuraddeen, nice me laifi, ni nace a fasa auren, wllh lokacin da nake faɗa ma ban san inda kaina yake ba, dan Allah dan darajar alƙur'ani mai girma karku hana ɗana auren ƴarku", Baba yayi ajiyar zuciya gami da yin gyaran murya yace "Hajiya ai bakin alƙalami ya bushe sai dai ɗanki ya nemi wata, yanzu maganar da nake miki na aurar da Hajara", Maama na fifita da mafici tace "Atoh ai yafi dai ka gaya mata gaskiya", Hajiya ta zabga wani uban salati sai kuma ta ɗaga murya tace "Nuraddeen...", Nura ne ya shigo da sallama, daman yana soro a tsaye shine ma ya rako Hajiyar. wata iriyar zabura Hajar tayi ta miƙe tsaye jin muryarsa, ta tsaya a jikin window tana leƙen tsakar gida, wani shauƙin kuka ne taho mata da taga fuskarsa, Hajiya tace "Nuraddeen, basu haƙuri da kanka, ni kam sun ƙi amsar nawa", Nura da har fuskarsa ta faɗa na wuni ɗaya ya durƙusa, ya gaishe da Baba kana Umma da hankalinta ya fara tashi, fuska babu yabo ba fallasa Baba yace "ba ƙin haƙura mukay ba, ai haƙurin ne ma yasa na saurare ki, kuma haƙurin za kuyi Hajara matar wani ce", Nura ya zuba guiwoyinsa a ƙasa yace "Baba, dan Allah kar a rabani da Hajar, ku yafe min...", Umma ta tashi ta shiga ɗaki, Baba ya girgiza kai yace "kayi haƙuri Nura wllh an riga an ɗaurawa Hajara aure...", Hajiya ta ɓarke da kuka tace "wllh nice sila, Nuraddeen ka yafe min, ban kyauta maka ba, ban yi maka adalci ba, duk abinda nake so shi kake min, ni kuma na datse maka farin ciki, wllh ban san na aikata maka hakan ba, na ɗauka mafarki nake ashe a zahiri na aikata...", Nura kam ko fahimta me take cewa beyi ba sbd juyawar da kansa yake masa, ga wani raɗaɗi da zuciyarsa ke masa, Baba ya kawar da kai yana jujjuya wnn lamari a kwanyarsa, abu sai kace a film. Nura ya tashi yana layi ya taimaki mahaifiyarsa ta tashi itama yace "Allahumma ajirni fi musibati wa aklufuli khairan nimha", shi wnn babbar musiba ce a wajensa, ya juya yay hanyar soro, Hajar ta sulale ƙasa ta cigaba da rusa kuka da dashasshiyar murya, a ƙofar gida Nura ya haɗu da Mu'azzam da yake shirin shiga gida, cike da mamaki Mu'azzam ya dubesa yace "ya sayyadi..", Nura ya kallesa da jan ido yace "Mu'azzam" da haka yayi gaba ya fara tafiya da sauri tamkar zai tashi sama, gida Mu'azzam ya shiga, yabi Hajiya da ido wacca take ƙoƙarin fita tana matsar kwalla. yayi sallama a bakin ƙofar ɗakin Umma ya bawa Anty saƙon yoghurt da ya siyo. da kyar Hajar ta sha quartern yoghurt din, ta sha panadol sbd kanta da yake mugun ciwo. wnn night shine worst night a rayuwarta, she couldn't sleep at all even a nap. ★Washe gari da safe, Nurain na zaune a balcony perceiving the morning blessings, wayarsa yake latsawa time to tima kuma yana sipping black coffee, last night da kira aka addabesa har saida yayi silencing wayar ya samu yay bacci, da safe kam missed calls da ya shallake expectation nasa ya gani, sai kuma ta ɗora da text message, a ƙalla daga asuba zuwa yanzu da ake maganar ƙarfe bakwai da rabi ta turo masa da messages sama da goma, kuma ko ɗaya bai karanta ba, daga message ɗinta ya shigo yake wipping notifications ɗin wayar, shifa indai ya bar abu to ya barshi kenan no going back, yanada zuciya sosai saidai kuma kafin yayi zuciyar sai ransa ya ɓaci. wayarsa tay vibrating, yana dubawa yaga Abba ke kiransa, picking yayi ya kara a kunne, Abba yace "ka sameni a great room now", Nurain yace "yeah", da haka Abba ya katse kiran, ya ɗaga coffeen sa ya shanye snn ya tashi ya shiga ciki da cup ɗin a hannunsa, kitchen ya wuce ya ajiye cup din snn ya fito ya nufi great room din Abban sa. ya cire soft slippers dake clean legs ɗinsa ya shiga great room din, yana shiga Abba yayi pointing kujera yace "sit", Nurain ya zauna looking at his Father. Abba yace "Uthman, tin jiya naso nayi informing ɗinka amma na bari sai yau", Nurain dai baice komai ba kawai kallon Abban nasa yake, Abba exhale heavily yace "na ɗaura maka aure da ƴar wajen abokina...", with a weird facial expression Nurain ya dubesa, peach lips dinsa ya motsa a hankali yace "marriage..", direct Abba yace "yess, jiya aka ɗaura auren, and insha Allah today za a kai maka matarka gidanka, get ready to settle down Son".....✍️ ☺️☺️idan na waiga naga comments dinku na jiran littafin Hajar sai naji wani iri, cause nasan kuna jiran update, duk da dai nasan bxn iya update kullum ba amma i will try my best na ringa posting duk bayan kwana biyu. plxx be patient with me. just manage 🤗 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {34..} Nurain was speechless at that moment, he was shocked and confused, marriage shine plan dinsa na ƙarshe a yanzu, Abba ya katse silence din da faɗin "don't you have anything to say?", Nurain ya shafa cikakkiyar sumarsa yace "Abba, kawai i don't expect this, beside ma i think am not ready..", Abba yace "wane ready kuma Nurain?, ai komai an gama, shirin da ya rage maka shine settling down, kanada gida, kanada Sana'ar da zaka riƙe even four wives, you're rigid enough, sai dai in auren da nayi maka ne baka so", Nurain yayi ajiyar zuciya yace "No Abba, i like it, sai dai akwai consequences..", Abba yace "no matter what the consequences might be you most settle down, kamar duk wani abu mai merit to definitely yanada demerit, abinda nake so da kai shine, ka amshi auren nan ka zauna da matarka lfy, Allah ya bka ladan biyyar da kay min...", Nurain yace "ba komai Abba, nagode sosai..", Abba yace "madallah, Allah yay albarka..", Nurain yace "Ameen, if you excuse me?", Abba yace "fine, you may leave", tashi Nurain yayi ya fita, shi dai bashi da wni feeling akan mattern, shi ba mai farin ciki ba kuma ba mai baƙin ciki ba, Mami ta fito kitchen hannunta rike da wani royal tea flask, ganin Nurain na fitowa daga great din Abba ta tsaya kallon expression en fuskarsa, tasan Abba ya gaya masa maganar auren, ya zuba hannayensa a pocket walking towards her yace "i just talk with Abba", tace "ka sani knn?", yace "sure, are you happy with the marriage..", Mami tace "Eh mna, am very happy, Allah ya sanya alkhairy.." da hka ta wucesa ta shiga great room din Abba. ƙarfe sha ɗaya Sakeena ta iso gidan da kids dinta guda biyu, Aymana da kuma Ayman wanda take goyo, a part din Mami tayi branching, Mami ta dauki Ayman tana masa wasa, Sakeena ta cire veil dinta ta zauna tace "ina kwana Mami..", Mami tace "lfy lou, ya kids", Sakeena tace "suna lfy, ai Abba ma ya kusa zuwa yaye..", Mami ta shafa kan Ayman dake cinyarta tace "A'a Sakeena, wnn ɗan ne ya isa yaye?..", Sakeena tace "laa ya isa, watansa 11 fa", Mami ta haɗe gira tace "A'a gsky bai isa ba..", Sakeena tayi ƴar dariya tace "kamar haka na yaye Aymana ma..", Mami tace "ai dan an gansu ƴan lukutaye shi yasa ake ɗaukar alhakinsu..", Sakeena ta gyara zama tace "kuma a yau za a ɗakko amaryar?", Mami tayi ajiyar zuciya tace "Eh, yau da yamma ba", Sakeena tace "ƴar Abokin Abba ce ko?", Mami tace "Eh, but I don't know which one...", Sakeena tace "Alright, Allah yasa dai mai kirki ce", Mami tace "Ameen". Anty Zulaiha ma ta hallara da misalin ƙarfe ɗaya da ƴan mintina, ba ta jima ba saiga Mama Mardiyya ƙanwar Abba da kuma Umminsu Farooq, Mami tasa aka firfito da lefen Nurain na bikinsa da Ruqayyah, tace "yawwa da cewa nayi kawai sai a basu lefen idan an kawo amaryar...", Mama Mardiyya tace "Shknn kam, kinga an wuce wajen", Mami tace "to ku duba ko akwai abinda za a ƙara...", Ummi tace "wai lefen Nurain ne, ai a yadda nasan lefen nan baya buƙatar ƙari..", ai kam dai boxes ɗin nan basu da masaka tsinke acike suke ɗam ɗam, Sakeena tace "Ai da aka kaiwa Ruqayyah sun taɓasa..", Mami tace "Atampa da lace kawai suka ɗauka, kuma nayi replacing da wasu..", Anty Zulaiha tace "A wnn abu yayi, kawai miƙa musu za ai", Mama Mardiyya tace "Nurain ya bani tausayi a lokacin da aka fasa aurensa na farko, Allah yasa wnn shine mafi alkhairy", kowa ya amsa da Ameen, Ummi tace "Hajiya ma da cewa tayi zata biyoni sai kuma ciwon ƙafa ya hanata, ba mamaki idan taji dama dama tazo anjima, dan cewa tay ita zata riƙo matar Nurain", Anty Zulaiha tace "Allah sarki, ai Hajiya na ji da jikokinta..", Sakeena tace "Iron Ladyn mu akwai rigima...", Mama Mardiyya tace "gidanku, bazaku dena ce mata iron lady ba ko?", Sakeena tace "Allah ba ruwana Mama, Noory da Aysha ne suke ce mata iron lady...", Anty Zulaiha tace "toh yanzu dai da kayan lefen zamu tafi ɗakko ta knn?", Mami tace "wai da cewa nayi akai lefen can gidan Nurain, idan aka kaita can ɗin sai a basu lefen a can..", Ummi tace "Eh, hakan yayi, ba nan za a kawota ba knn?", Mami tace "gwara ta fara shiga gidanta in yaso Nurain ya kawota mu gaisa daga baya..". Haka kuwa akay ana idar da Sallar la'asar Ummi Anty Zulaiha da Mama Mardiyya suka tafi ɗakko Amarya, mota uku sukay, drivern Abba da yasan gidan shine yake musu jagoranci. Abba ya kira Baba ya sanar dashi don daman sunyi exchanging phone number. Sakeena Noory Aysha da kuma Khausar kuma aka haɗasu da kayan lefe suka wuce gidan Nurain. ★Taci kuka harta gaji ta zubawa sarautar Allah ido, tin ɗan yoghurt din da ta sha daren jiya bata sake cin komai ba sai bayan Sallahr azahar taci awara kaɗan, Baba yana dawowa daga masallaci sallar la'asar ya sami Umma ya sanar da ita cewa su shirya yanxu za a zo ɗaukar Hajara, wani yanayi Umma ta shiga amma haka ta jure ta sanar da Anty, Anty tasa Hajar tayi wanka, babu musu ta tashi tayi, ita ta riga da ta saddaƙar tana jiran sakamakonta, asalin kayan da aka tanadar mata na zuwa gidan miji ta saka, atampa black mai manyan flowers red, da mayafi red mai stone na shuwariski mai walwali, sai handbag da flat shoe black colour, Hajar tayi kyau sosai duk da dai babu walwala a fuskarta, aihanin ƙamshinta na gyaran jiki da kuma na kayan da akay musu kabbasa ga kuma perfume sai tashi yake daga jikinta, a gefen gado ta zauna tana wasa da slim fingera dinta da suka sha zanen jan ƙunshi wanda a yanxu ya koma maroon, Hafsa ce a kusa da ita itama ta shirya abinda, Sabra na tsaye daga jikin wardrobe ta zubawa yayarta ido, Hajar ta dubi little sister ɗinta tace "zo Sabra", da sauri ta matsa kusa da ita, Hajar ta riƙo hannunta, Sabra tace "Adda me yasa ki kai ta kuka jiya?", Hajar tace "kuka nake yi sbd zan rabu da ku, ke da Umma da Baba da yaya..", Sabra ta zaro ido tace "tafiya zaki ki barmu", Hajar ta gyaɗa kai tace "Eh, zaki bini?", ta gyaɗa kai da sauri tace "Eh zan biki..", Sallama ce ta ratsa tsakar gida tare da ƴar ruruma, Hajar ta runtse idonta snn ta damƙe hannun Sabra dake cikin nata, tabbas tasan cewa masu ɗaukarta ne suka hallara. Hafsa ta miƙe ta janyo mayafin Hajar ta rufe mata fuska. Shimfiɗar fuska da ta tabarma su Anty sukay wa baƙinsu, su Mama Mardiyya suka zazzauna, aka fara exchanging greetings ga juna, bayan nan Wasila ta kawo drinks da snacks da aka tanadar ta ajiye musu. Maama ta fito daga ɗaki tana ƙarewa baƙin kallo, sosai gabanta ya faɗi sbd yanayinsu, sam ba suyi kama da ƴan wahala ko yaku bayi ba, hutu ne kawai yake haskawa a jikinsu, ta shiga muhawara da zuciyarta, shin wane ne wnn abokin na Baba da aka ɗaurawa Hajara aure da ɗansa, tin safe take jiran taga su waye zasu zo ɗaukar Hajar, ta yamutsa fuska ta koma ɗaki ta hau canza kayan jikinta zuwa masu ɗan dama dama, Nabilah tace "Maama fita za kiyi?", Maama tace "zuwa zanyi naga kangon da za a kai Hajara". Mama Mardiyya ta ɗaga kai tana kallon Maimuna da ta fito daga wanka, ɗaurin ƙirji ne ajikinta, ga fuskarta ɗaɗau tasha man bleeching jiki kuma baƙi ƙirin, ko kallon inda suke Maimuna ba tay ba ta tsugunna gaban rariya ta fara goge baki. Mama Mardiyya suka haɗa ido da Anty Zulaiha. Ummi tayi ajiyar zuciya don itama taga Maimuna tace "ba zama za muyi ba ina ƴar tamu?", Anty tace "tana ciki, wai yau zaku tafi da ƴar taku?, sai kuma naga ba a gyara mata ɗaki ba", Anty Zulaiha tace "ai ɗakinta a gyare yake, jiranta kawai yake", Anty tayi murmushi ta tashi ta shiga ɗakin Umma, ta tsaya tana kallon Hajar tace "to taso Hajar", hannunta riƙe da na Sabra ta tashi tana jin bugun zuciyarta a maƙoshi, kawai dagewa take amma jikinta duk yayi sanyi, Hafsa ma ta miƙe, Anty tace "toh cikata mana, kin riƙe yarinya", da cracking voice tace "da ita zan tafi..", baki buɗe Anty tace "Au da ita zaki tafi..", ta gyaɗa kai don da gaske take. Anty ta riƙe ɗayan hannunta wanda ta saƙalo small handbag dinta ta fito da ita tsakar gida, Mama Mardiyya tace "masha Allah" sai kuma ta miƙe tace "toh mu tashi ko", ta shatin veil dinta da ya rufe mata fuska take kallon Umma, ta saki hannun Sabra taje ta rumgumeta, sai alokacin ta saki kukan da take ta dannewa, idon Umma yayi rau rau don itama yaƙe kawai take, da kyar ta yaficeta daga jikinta ta shige ɗaki, Hajar ta kuma rushewa da kuka tamkar zata shiɗe, Ummi ta riƙota tace "yi haquri ko wace mace yar haka ce". Maama ta kirma wani uban hijab tana kallon Nabilah tace "ki taso muje muga kangon da za a kai Hajara", Nabilah tace "A'a nidae ba inda zani", Maimuna tace "ni bari na saka kaya mu tafi", Maama ta leƙa window tace "yi da jiki naga sun tashi..", shap shap Maimuna ta gama saka kaya, suna fita already anyi soro da Hajar dake gursheken kuka. da yake mota uku suka zo da ita akwai space sosai, Amarya Mama Mardiyya da Anty suka shiga mota guda, sai Hafsa a front seat, Ummi da Anty Zulaiha da wasila suka shiga mota daya, Maama da taga an barta a waje ta shiga buga windown motar Amarya, Mama Mardiyya ta buɗe glass tace "lfy?", Maama tace "ban gane lfy ba, ai harda ni za a kai amaryar", Mama Mardiyya tace "Ohk, ga wani motar can ai saiki shiga.." da haka ta zuge glass dinta, wani takaici ne ya turnuƙe Anty, idon baƙi ne zai hana ta tatawa Maama rashin mutunci, ɗayar Motar da ta rage Maama ta shiga tana zare ido, jikinta har rawa yake tana fatan waɗan nan motocin duk na haya ne wato Opay, Maimuna tayi kwam a gaban Mota, tafiyar minti talatin ce ta kaisu unguwar da zasu, motarsu Maama ce a front don haka itace ta fara shan kwanar street din gida, Maimuna sai cizon lips take tana kallon tsala tsalan gidajen da ke layin, a bakin gate din gidan da yafi ko wanne gida ƙawatuwa a layin motar ta tsaya, Maama ta ɗaga murya tana kallon driver tace "kai malam ya zaka ajiyemu a ƙofar gidan ƴan yankan kai, ba wancan ne gidan ba?..." ta nuna wani gida da duk yafi ƙanƙanta da rashin kyau a layin, driver ya danna horn yace "A'a ba nan bane, wnn wanda zamu shiga shine gidan", wani irin sakin baki Maama tayi har yawu na zuba. lokacin da suka shiga harabar gidan kam suman zaune tayi, motar Amarya da tasu Ummi ma ta shigo, Hajar Amarya ta fito a hankali tamkar wacca kwai ya fashewa aciki, idonta sai zugi yake tana shessheƙa a hankali. Mama Mardiyya da Ummi sukay main building da ita, Ummi tace "toh shiga da ƙafar dama da Bismillah"......✍️ 💛 HAJAR💛 by Feenerh_feeche {35..} A hankali Hajar ta saka ƙafarta ta dama ta shiga gidanta bayan tayi Bismillah a zuciya, wani irin sanyi ne ya tsarga mata a jijiyoyin jiki, su Sakeena dake zaune a katafaren palourn suka fara musu sannu da zuwa, upstairs aka wuce da Hajar domin kaita ainahin ɗakinta, the room was in woah ba a cewa komai, it's very huge and luxury, aka ajiyeta a makeken italian bed dake ɗakin wanda a halin yanxu ya zama nata. Anty dake biye dasu tanata zabga murmushi tace "masha Allah", Hafsa ta shigo tana jan box din kayan Hajar, ta zauna gefenta tana ƙarewa ɗakin kallo, wnn ai daula aka kawo ƴar uwarta, wani hanin ga Allah baiwa ne, Allah ya bata zaman lfy da mijinta shine fatanta agareta, Anty ta fita tana bin ɗakunan dake saman ɗaya bayan ɗaya, bedroom biyu ne extra bayan wanda aka kai Hajar, saidai basu kai nata girma ba, wata sliding glass door ta hango wacca ko ba a gaya mata ba tasan turakar mai gidan ce, don haka ba tay hanyar ba kuma daman ma a rufe yake. da kyar Maama ta iya fitowa daga mota sbd jin ƙafafuwanta take tamkar ba zasu ɗauketa ba, Maimuna kam tini ta shige tana kashe kwarkwatar idonta, tamkar an wurgota haka ta shiga palourn tana zazzare ido, duk da sanyin Ac amma zufa take, Noor ta yamutsa fuska tace "wnn kuma daga ina?..", Aysha tace "who knows..", babu inda Maama bata shiga ba a ɗakunan ƙasa, kuma duk wanda ta shiga sai numfashinta ya ɗauke, nadama kam tayi yafi cikin kwando, duk ɗakin da ta shiga saita fito a gigice, tuntuɓe kam tayi wajen sau ashirin sbd kallon fitilu na jikin roof, tin jama'a basu lura ba har suka fara fahimta, a sama suka haɗu da Maimuna wacca ta maƙale a bedroom ɗaya tana fatan dama nata ne, Maama tace "kinga abinda Babanku ya aikata ko, ya siyar da Hajara, wnn ai gidan yankan kai ne", "ki ga yankan kai a kanki, wnn gidan auren Hajar ne..", Anty ce ta furta hakan tana shigowa dakin, Maama tace "ke Jamila ki shiga taitayinki..", Anty ta taɓe baki tace "dalla malamai ku fita karka saka mata ƙazanta a ɗaki, sa'a ma ku ka ci da akazo da ku..", Maama ta buɗe baki za tay magana Anty ta turata waje tace "ki fita nace Rabii", Maimuna ta buɗe baki za tay mgana Anty ta daka mata tsawa itama ta hankaɗata waje ta rufe ɗakin tace "da so samu ne ma ku fita, ko mala'ikun rahama sun shigo" da haka ta bar wajen ta sauka ƙasa. Maimuna ta mulmulo ashar tace "ni za'a wulaƙanta akan wnn kuturun gidan, wllh gidan da Alhaj ɗina zai sakani yafi wnn sau dubu", Maama ta gasa mata wata shegiyar harara tace "zan ɗuɗɗura miki ashar wllh, Alhaj ɗin banza Alhaj ɗin wofi, yana ina shi Alhaj ɗin", Maimuna ta tsuke ido tace "Maama fa zaginsa kikai?", Maama da take neman gurin huce takaici tace "na zaga ɗin", Maimuna tayi kwafa tace "kin dena cin ƙwandala daga kudinsa wllh, ni na tafi gida bazan zauna ana min gori ba", Maama tace "tsayani mu tafi kar zuciyata ta fashe..", a hankali Maimuna take sauka daga kan stairs din da yasha mable, Maama na biye da ita, fitilun da ke jikin bangon stairs din da kuma na sama suka ja hankalin Maama, ai kam baifi saura stairs shida ba bayan Maimuna ta kai ƙasa ji kake timm Maama ta faɗo, goshinta ya daki tsinin tiles na ƙarshen stairs din, a take jini ya ɓalle, hankalin Jama'ar dake palour suna gabatar da kayan lefe yayo kanta, a gigice ta miƙe ta saka duƙunƙunannen hijab dinta ta dafe goshin, Mama Mardiyya tace "ya salam, taji ciwo ko?", Aysha da ta fito daga guest room da ƙaramar kit ta jewelry na lefe tace "taji ciwo, ga stain din jini a floor", Anty ta taɓe baki ta kawar da kai, kowa na palourn saida yayi mata sannu banda Anty da wasila, Maama ta kyallaro idonta ɗaya wanda yake a buɗe tana kallon akwatunan da suke baje a tsakiyar hamshaƙin palourn, Anty Zulaiha tace "ya kamata a kaita Hospital, naga kamar she's bleeding, Noor yi ma driver magana", Noor da takewa Maama kallon wata psycho tace "ohk" ta tashi ta fita. Mama Mardiyya tace "ga lefen yarinya", Maama ta zaro ido jin an ambaci kalmar lefe, chab wnn ne lefe sai kace na budurwa uku, ya linka wanda aka kawo mata na Nura, Maimuna da ta tsaya gulma ta hura hanci tace "Maama ni kam na tafi sai kiyi ta tsayuwa", Maama bata san lokacin da ta ɓarke da kuka ba, hannunta dafe da goshinta ido ɗaya a rufe ta wuce Maimuna ta fita, Maimuna tabi bayanta da sauri, Mama Mardiyya da daman bata taking shit tace "who is this woman?", Anty tace "kishiyar Babar Hajar ce", Mama Mardiyya tace "Allah ya kyauta, sai kace mai junnu..", Noor ta shigo tace "Ammi (Anty Zulaiha) na gaya masa yace ta fito", Anty Zulaiha tace "ai sun tafi ma..", Noor ta tsaya kusa da Aysha da Khausar tace "mu tafi wajen Amarya..". suka wuce upstairs. bayan su Anty sun gama ganin lefe Mama Mardiyya tace "Alhmdllh, mu dai fatan mu Allah ya basu zaman lafiya", Anty tace "Ameen". da haka suka miƙe domin tafiya don basa son sukay magrib, a lokacin ne kam suka hau sama domin suga fuskar amarya, tinda su Noor suka shigo suka bude mata fuska, Hajar tayi sauri zata rufe fuska ganin su Ummi na shigowa, Anty Zulaiha tayi murmushi tace "ƴar fillo", Mama Mardiyya tace "to ai shknn wataran ma gani" da haka suka fice daga ɗakin. Anty ta keɓe ta sanar da Umma abinda ya faru a waya, ta tambayeta ya za ai da lefen, Umma tace a barsu anan kar a taho dasu. Anty ta shiga wajen Hajar domin mata sallama, Hajar ta riƙe mayafinta ta ringa kuka kamar zata shiɗe, da kyar Anty ta rarrasheta ta samu tayi shiru, Hafsa tayi mata sallama da cewar gobe zata dawo, kowa ya tafi aka bar su Noor da ita, Sakeena ma tabi su Ummi. ★Through out the day Nurain na room ɗinsa, bacci ma yayi abunsa, lokacin sallah ne kawai yake fito dashi, yana dawowa daga sallar magrib ya tarar da su sun dawo kenan, wajen motocin ya dosa yana musu barka da zuwa, suka ringa sa masa albarka tare da fatan Allah ya bada zaman lfy, shi dai baice komai ba saidai ya shafa kai. bayan sun shiga ciki Sakeena tace "So.. ashe kai a angonce ka dawo 9ja, Abba ya kyauta", ya zura hannayensa a pocket yana kallonta da kyau yace "And shknn.. nima na huta da surutun ku, that bla bla bla Nurain kayi aure you're not getting younger..", tace "Sure kuma fa ka huta, am telling you wllh tafi Ruqayyah kyau nesa ba kusa ba, she's beautiful and young bana jin ma ta kai sa'ar Noory", ya ja pointed nose ɗinsa yace "really.. toh yayi kyau", tace "brother harna tausaya maka wllh zaka sha shagwaɓa don shagwaɓaɓɓiya ce, tin fa da aka kawota take kuka har muka taho bata dena ba, ya kamata ka tafi da wuri kaje kayi aikin rarrashi kar ƴar mutane ta haɗiyi zuciya..", yayi ajiyar zuciya yace "wai ke baki san ba auren soyayya bane wnn", tayi hitting ɗinsa lightly tace "that doesn't change the fact that she's your wife, arranged marriage ko kuma auren soyayya ai duk ɗaya ne tinda dai an zama miji da mata, and kar kayi using that bullshit think of you kayi maltreating yarinya..", ya zaro ido yayi pointing kansa yace "Nah?", tace "Yess you", yace "ai kinsan ba halina bane", tace "yeah, i know brother, naji kana wani zance ne daga nace kayi consoling yarinya..", murmushi yayi yace "uhmm ai ba sai kin koya min yadda zan kula da baby wife dina ba", wucewarta tayi ta barsa a wajen tana cewa "shine ka tsaya kana ɓatan lokaci.." ta shiga ciki. ƙarfe takwas da rabi na dare Nurain na tsaye gaban Mirror, buttoning rigar dake jikinsa yake, dakakkiyar shadda ce mai tsadar gaske, sabuwa fil wacca ya ɗinka a lokacin bikinsa da Ruqayyah kuma ya tanade ta ne sbd shiga gidansa na farko wajen matarsa, ashe dai ba Ruqayyah bace, wata ce daban, sai a yanxu ma ya fara tambayar kansa shin ya wacca aka aura masa take, yana gama bottoning ya kafa hula samar cikakkiyar baƙar sumarsa, ya fito a well dressed gentleman, wata ƙaramar trolley da ya haɗa few belongings nasa ya ja ya fito daga room ɗin nasa, ya rufe ya saka key din a pocket, down stairs ya sauka yana zuba ƙamshi, Farooq da ke zaune main palour yana latsa wayarsa ya ɗaga kai ya dubesa, Nurain ya ajiye trolleyn ya wuce part din Mami sukay sallama, tare suka fito da Sakeena, ya shiga part din Abba ita kuma ta ƙarasa wajen Farooq, ta miƙa masa key din motarta tace "plxx brother ka taho min da car na tana can gidan..", yace "what about mine?", tace "ai yanxu a ta Nurain zaku tafi, idan ku ka je sai ka taho da tawa ka bar masa tasa, idan ka dawo saika dauki taka", yace "Ohk, you wet my work fa, banyi niyyar dawowa ba..", tace "sorry, ai daman ma saika dawo tinda zaka ɗakko su Noory..", ya amshi key ɗin ya zura a pocket. Nurain yay sallama da Abbansa snn yace "amm naga alert daga wajenka, what about the money?", Abba yace "ka yi amfani dasu ko wajen siyan foodstuffs ne", Nurain yace "ngd Allah ya saka da alkhairy" da haka ya bar room din, yana fita main palour Farooq ya miƙe yace "let's go..", Nurain ya tsaya yana kallonsa yace "muje zuwa ina?..", Farooq yace "zuwa gidanka mna, amarya na jira", trolleyn kayansa ya ɗauka ya fita compound, parking space ya dosa ya buɗe black ride dinsa, ya bude back seat ya ajiye trolleyn snn ya shiga driver seat, Farooq ya shiga front seat yana cewa "wai rakiyar ce baka so?", direct yace "yap" ya kunna motar yana warming, Farooq yace "i guess right, Mami ce tace nazo ai, you know I can't say no to her", Nurain yace "that's right..", ya fita daga parking lot din da reverse snn ya juya suka bar gidan. A wani babban supermarket yayi parking, yace "zanyi shopping, do you mind going in?", Farooq yace "nope saika fito", Nurain bai kashe motar ba ya barta a kunne sbd AC tinda Farooq na ciki, wajen shopping din ya shiga, after 20min ya gama, shopping yayi sosai da kudin da Abba yay masa transfer kuma a hakan ma ko quarter bai taɓa ba, saida back seat ya cika da ledoji, bayan ya gama ya shiga mota suka bar harabar supermarket din, Nurain yace "i never thought arranged marriage za a min, my wish is to marry someone that I love and she loves me too...", Farooq yace "Allah planned the best for us, wish kuma wani abu ne na rayuwa wasu nasu fulfill wasu kuma unfulfill, in your case ba zamu ce naka unfulfill bane cause you have another three chances", Nurain yace "kuma ba nida niyyar auren mace sama da ɗaya", Farooq yace "Ohk, saika ajiye niyyar kayi fulfilling wish dinka", Nurain yayi ajiyar zuciya baice komai ba, ganin sun wuce wani wajen suya da gashin kaji Farooq yace "kayi mantuwa fa punk", Nurain na murza steering his eye fixed on the road yace "mantuwar me?", Farooq yace "baka siyi roasted chicken ba", yayi slowing down yace "damn it, yanxu kuma naga mun wuce suya..", Farooq yace "sai ka koma ka siyo..", Allah yaso ba suyi nisa sosai ba tinda yau baya gudu, da reverse ya koma wajen Suyar, Kaji guda uku da tsinken tsire shida akay masa wrapping, ya biya bill ya bude back seat ya ajiye, saida suka hau saman titi yace "Allah bashi ka ɗauka dude, wai kana ganin inata wahala bazaka temaka ba ko..", Farooq yayi wani murmushi mai sauti yace "hmmm, toh ai naga kamar u don't need a help, rakiyar ma baka so ba..", Nurain yayi ajiyar zuciya baice komai ba, After 15mins yay parking a gaban gidansa da fitilunsa suka ƙara hasken layin, ya miƙawa Farooq muƙulli yace "buɗe gate", ya amsa ya fita daga motar ya buɗe gidan snn ya shiga ya zuge gate ɗin that's soft in sliding, Nurain ya shigar da motar ciki yay parking. Farooq ya rufe gate en snn ya ƙarasa ciki. Ta jikin window Aysha taga shigowarsu ta dubi su Noor tace "Yaya ya ƙaraso, tare suke da ya Farooq", wani irin nervousness ne ya lulluɓe Hajar, shin da wane irin mutum za tay tozali matsayin mijinta, Khausar tace "gashi can suna knocking", da sauri Aysha ta fita ta sauka ƙasa ta buɗe ƙofa, Farooq yace "ina sauran suke, fetch them now karku ɓata min lokaci", tace "tom", da sauri ta haura sama ta sanar dasu Noor, ai kam da sauri suka haɗa kayansu sbd sun san halin Farooq, yanxu sai ransu ya ɓaci, sukay wa Hajar sallama suka fita, a hankali ta gyara zamanta a gefen gado, ta janyo mayafinta ta ɗora a kai har yana rufe mata goshi, wani irin feeling take ji, zuciyarta na lugude. suna sauka down Farooq da ya shigo da ledoji a hannunsa yace "ku jirani a waje", ba musu sum sum suka fita, Nurain ne ya shiga da ledojin ƙarshe wanda sune na kaji ya ajiye a palour, Farooq ya miƙa masa hannu yace "toh brother, wish you Happy marriage life..", sukay shaking hands Nurain yace "thank you", compound suka fita tare, Farooq ya shiga driver seat na motar Sakeena, Noor a front seat Khausar da Aysha suka shiga back seat. saida suka fita daga gidan snn Nurain ya rufe gate da padlock, ya duba ko ina a compound din yaga dai ba matsala snn ya shiga ciki, ya sakawa ƙofar lock yana sauke ajiyar zuciya, trolleyn kayansa ya ɗauka ya haura sama, ya kalli doors ɗin ɗakunan yana jin wani irin feeling, definitely his wedded wife tana ɗaya daga ciki. part dinsa ya wuce ya ciro key ya buɗe ya shiga, ya lalubi bango ya danna switch, a take haske ya gauraye makaken palourn nasa, kai palourn nan fa ya naɗi pulus, ya wuce master bedroom wanda yafi ko wane ɗaki girma a gidan, tsabar girman dakin daga can nesa zaka hango makeken bed din ɗakin, ya ajiye trolleyn a kusa da closet ya juya ya fita daga part din, a long corridor dake ɗauke da three bedrooms din ya tsaya, ya saki ajiyar zuciya mai karfi kafin ya buɗe room na farko, da sallama ya shiga ya tarar ba anan aka ajiye masa matarsa ba, room na biyu ma haka, yana taɓa door handle na room na uku yaji iced shock, ya murɗa handle din gami ta tura ƙofar ya shiga, ya mayar da ƙofar ya rufe a hankali yace "Assalamu alaikum...", da cracking voice wacca ta dashe ta amsa ciki ciki, ta sunkuyar da kanta tana kallon slim fingers ɗinta da take wasa dasu, his piercing eyes land on her slim fingers da suka ji zanen ƙunshi, a hankali ta ajiye numfashi ta lumshe idonta perceiving his pure men scent da rairayin sanyin Ac ya kwaso, takowa ya farayi towards her, yayinda ita kuma taji tamkar an ɗago fuskarta, idonta ya faɗa cikin nasa, ya dakata da tafiyar yana kallon innocent face ɗinta wacca tasa brain ɗinsa ta amsa, sosai idanunsu suka sarƙe, he automatically get froze bayan ya gane wnn fuskar, tamkar robot da aka kunna da remote control haka ta miƙe zumbur, ta zaro lulu eyes ɗinta waje, mayafinta ya zamo daga kanta zuwa shoulders ɗinta kafin ya zame ƙasa gaba ɗaya, ta kurma wani uban ihu kafin ta sulale ƙasa tabi mayafinta.....✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh _feeche {36..} At first tsayawa yayi yana kallonta kafin ya ƙara one step, tsananin shock da abinda bata fatan haka ne yasa ta sulale ƙasa, Hajar ta yayibi mayafinta ta miƙe nan ma sai kace robot, ta lulluɓe jikinta gami da kallon mutumin front dinta wanda shima yake analysis me ya kawo wnn yarinyar nan, Hajar da take shivering as a result of shock din da tayi ta nunasa da yatsa tace "me kake yi anan?", da wani irin expression yake kallonta cause he will never accept what his mind is thinking, ta zuba masa lulu eyes ɗinta kawai amsa take jira ya bata, After few seconds of silence ta sake cewa "nace me kake yi anan...", da stern voice yace "that question goes to you young lady, what are you doing in my house...?", shivering da jikinta yake har saida ya ratsa zuwa lips dinta snn yayi birki a muryarta tace "your house..?" kafin ta sake sulalewa ƙasa a karo na biyu, maimakon ƙara da ta fasa wancan karon yanxu kuma saita rushe da kuka, what wnn mutumin da ta ƙi jini, mutumin da bai san darajar ɗan Adam ba, ko 10sec bai ƙara a tsaye ba ya juya ya bar ɗakin, gaba ɗaya brain ɗinsa ta kulle, he can't think otherwise, downstairs ya sauka ya nufi main door, har ya fara murza key sai kuma ya kalli agogon wrist ensa wanda yake nuni da sha ɗaya na dare saura few minutes, fasa buɗe ƙofar yayi ya koma ya zauna akan ɗaya daga cikin exclusive sofa dake palourn, yayi resting jikin kujerar gami da lumshe ido, bayan minti goma ya buɗe idonsa, ya ciro wayarsa daga pocket snn ya tashi ya koma upstairs, part dinsa ya shiga ya zauna a palour, kunna wayar yayi ya fara ƙoƙarin dialing numbern Abbansa, kiran ko shiga beyi ba saiga kiran wacca ta takura masa nan yana shigowa, ya tsaya yana jiran kiran ya katse, yana katsewa wani ya sake shigowa, sau biyar yana attempting kiran Abba amma kiranta ya hana nasa shiga, shi kam bashi da lokacin blocking numberta cause she didn't worth it, idan ma yayi blocking layinta ai ta samu matsayi, daga dawowarsa jiya zuwa yau gaba ɗaya ta hanasa operating wayarsa lfy, daga text messages sai uban kira, fasa kiran Abban yayi ya ajiye wayar gefe guda, yana jin sai vibrating take, yayi ajiyar zuciya ya cire hular kansa ya ajiye kan huge center table dake palourn, shafa cikakkiyar sumarsa yayi yana nazarin demon din dake gabansa. The girl... ya tuna encounter dinsa da ita.. na farko lokacin da ta shafa masa cakwalkwali, cike da tsiwa take magana "malam ba kaga abinda kayi bane??, oh shi bakuga rashin kirkinsa da ya feshe ni da kwatami ba, banga zan iya hakura ba gaskiya". na biyu lokacin da ya kusan bige wani yaro da mota... "malam wai baka san darajar rai bane iyeee?, ya za ai ka kusan bige yaro amma ka wani hakimce a mota bazaka fito ka dubasa ba, ke kinga mutumin nan fa ko a jikinsa, idan da ace ya bige yaron nan fa sai yadda Allah yayi, to Allah ya isan sa kuma a ringa sanin darajar ɗan Adam". encounter na uku... "Fake doctor, i think the name fit you, wanda baisan darajan ɗan Adam ba bazai zama real doctor ba saidai Fake", sai kuma na ƙarshe... "mu bawa juna haƙuri daii". not her gaskiya, da dai ace wata ce daban da zai haqura yayi accepting marriage din nan amma wnn yarinyar mara ta ido, bama ta ido ba bata da manners. tunani kawai yake yana nemawa kansa solution, idan ya saƙa wancan sai ya kwance wancan, after 40mins dai ya samu solution ɗaya, ya tashi ya shiga huge bedroom nasa ya wuce bathroom, alwala yay ya fito yana jan hannun rigarsa da ya tattare, nafila ya shiga jerowa, nap na few hours ya samu kafin sallar asuba, ya sake wata alwala yay sallah, ƙarfe shida da minti hamsin na safe ya fito hannunsa riƙe da car key, ko kallon ƙofar room din da take beyi ba ya gangara downstairs, ya dubi ledojin da ke palourn wanda bai sake bi takansu ba, compound ya fita bayan ya rufe main door din da key, ya wuce wajen motarsa ya bude ya shiga ya kunnata, a kunne ya bar motar tana warming ya fito ya nufi gate ya bude, dawowa yayi ya shiga motar snn ya fito daga gidan, ya sauka ya rufe gate din shima da mukulli snn ya koma mota ya fara driving, ƙarfe bakwai da minti sha biyar ya danna horn a ƙofar gidansu, mai gadi ya bude masa, ya shiga wawakeken compound din gida yayi parking ya kashe motar ya fito, ya danna door bell, babu jimawa Laure mai aiki ta buɗe masa, bai saurari gaisuwar da take masa ba ya wuce great room din Abba, Noor ta fito daga kitchen da Apron a jikinta tace "wane yake knocking?", Laura tace "Alhj ƙarami ne..", Noor ta zaro ido tace "Yaya na?", Laure tace "Eh hajiya..", Noor tabi palourn da kallo tace "ina ya shiga?..", Laure tace "ɓangaren Alhj", Noor ba tace komai ba ta koma kitchen ta cigaba da suyar plantain da take. Nurain na shiga great din Abba ya ciro wayarsa daga pocket ya fara kiran Abban, tana daf da katsewa Abba ya ɗaga yayi sallama yace "Uthman..", Nurain yace "na'am, am so sorry for disturbing you, barka da safiya Abba..", Abba yace "lfy lou..", Nurain yace "dan Allah i need to talk to you Abba, gani nan a palourn ka..", Abba yace "Alright" da haka ya katse kiran, bayan minti biyu ya bayyana a great room din da coffee color jallabiya a jikinsa, Nurain ya sauka kan carpet ya sake gaishesa, Abba yace "me ya faru Son?, what's the matter?", Nurain yayi gathering courage yace "am sorry Abba, wllh i can't accept this marriage, zan datse sa", Abba ya ringa kallonsa kafin yace "what happened all of a sudden Nurain?", Nurain ya shafa kansa yayi ajiyar zuciya yace "bazan iya zaman aure da yarinyar ba Abba", Abba exhale heavily yace "why?, musaka ce, ko akwai tawaya ajikinta ko wani abun?", Nurain ya kasa cewa komai, Abba yace "answer me..", ɗago kansa yayi yace "no one, kawai dai i will never accept her as my wife", Abba yayi shiru na some seconds kafin yace "toh ya kake so ayi Nurain, an riga an ɗaura auren?..", Nurain yace "plxx father ina neman yardar ka dan sakinta zanyi..", Abba yace "toh me yasa zaka nemi yarda ta Nurain, ai wuƙa da nama na hannunka, na gama role dina, ra'ayin ka ne ka zauna da ita snn kuma ra'ayin ka ne ka rabu da ita, kai ne mai saki a hannu...", Nurain yace "am very sorry to turn you down father..", Abba ya gyaɗa kai yace "ba komai, bazan tilasta maka ba Nurain, amma ka tabbatar bka son auren?", Nurain yace "yeah", Abba yace "i will find another way, ka rubuta takardar sakin ka kawomin...", buɗe ƙofa akay, suka juya suna kallon mai shigowa, Hajjaju Hajiya ta shigo tana dogara sandarta, ta kalli Abba ta cikin kantamemen glasses dinta tace "Muntari, ya naji kana cewa yaro ya kawo takardar saki, takardar saki kamar ya?, karfa ina ganin kayi abin arziƙi ka ɓige da tsiya Muntari...", Abba yace "sannu da zuwa Hajiya", ba ta amsa ba kawai dai ta kafesa da idanu ta cikin glasses tana lasar wawulon bakinta, Nurain ya miƙe yace "sannu da zuwa", ta ɗaga kai tana kallonsa tace "wai Usuman, ince dai kai ma garin ƙanƙara kaje don naga ka ƙara haske", yace "babu ƙanƙara a ƙasar da naje" ya riƙo hannunta ya ƙarasa shigowa da ita palourn, Nurain ya koma position dinsa ya zauna, saida ta zauna akan kujera ta kalli Abba da ke shirin gaisheta tace "tin jiya naso zuwa naje na rungumo matar Usuman na kai masa ɗaki, to ciwon ƙafa ya hanani, ai dole tayi ciwo na azabtar da ita lokacin ƙuruciya, tinda aka idar da Sallar asuba nake neman wanda zai kai ni gidan Usuman, shi Umaru bacci yake kuma gsky bazan tashi mai gida ba, ita kuma Shatu ba a maganarta maƙiwaciya ce..", Abba yace "Allah sarki", ya russuna yace "Hajiya barka da safiya..", tace "A'a bar barka da safiyar nan tukunna, wace takardar saki za a kawo?, wa za a saki?, waye zai yi saki?, kasan na tsani kalmar saki Muntari...", Abba ya kalli Nurain yace "Nurain ne zai saki matarsa..", Hajiya ta buɗe bakinta mai wawulo tace "wai Usuman, wace matar zai saka kuma?", Abba ya dubi Nurain yace "talk my friend..", Nurain ya sha kunu baice komai ba, Hajiya tace "Usuman a sbd wani dalilin za ka saki matar da aka aura ma jiya?, notin kanka ya kunce", Nurain yace "ba dalili, kawai bazan zauna da ita ba", Hajiya ta buga sandarta a kan carpet tace "haka fa, wato sbd ka mayar da mu ƙananan mutane a idon duniya ko, sbd ka zubarwa da Muntari kima ko, sbd ka zubar mana da mutunci ko, zaɓin mahaifin naka ne bai maka ba ko me?, naga hakan ne ya dace da kai tinda zaɓin naka da ka kawo guduwa tayi ta barka, shine daga aura maka yarinya jiya jiyan nan kace zaka saketa, toh ai ba akuya ko tinkiyar turke bace da za a saketa sakaka, sam ban amince da hakan ba, ai wnn ƙaranta ce...", Abba yayi ajiyar zuciya yace "Hajiya ayi haƙuri, nima Uthman ya bani mamaki wllh ban taɓa tunanin hakan daga garesa ba, tinda dai yace baya so ina ganin kawai ya saketan..", Hajiya ta fara matsar kwalla tace "Au Muntari isa zaka nuna min akan ɗanka, wato abinda yake so za muyi sbd gashi uban mu, toh wllh bai isa yayi sakin nan ba, wnn ai mugunta ce da cin zali an auro yarinya jiya jiyan nan sai a saketa yau sbd rashin imani..", Abba ya rage murya yace "an janye maganar sakin, dan Allah Hajiya kiyi haƙuri..", ta janyo lulluɓin da ke kanta na atamfa ta cire glasses ta goge hawayen tace "Muntari na tsani kalmar saki", Abba yace "na sani Hajiya", ta mayar da glasses din ta dubi Nurain tace "Usuman na tsani kalmar saki", Nurain da zuciyarsa ke ƙoƙarin bombing ya shafa fuskarsa snn ya miƙe ya fita. ★Maama ce a tsakar gida sai zance take mara kan gado, goshi a kumbure yayi lemon tsami, ta gyara haɓar zaninta tace "tin jiya nake magana a gidan nan amma anƙi saurara ta, kawai an ɗau yarinya an kaita gidan yankan kai sai kace mara galihu iyee, naga dai da gatanta a duniya..", Baba ya fito daga ɗakinsa da shirin fita wajen aiki, yana zura takalmi Maama ta matsa kusa dashi tace "mal kana ji ina magana fa, wllh abinda kayi bai dace ba, ya zaka ɗauki ƴarka ka miƙata ga halaka ka kaita gidan yankan kai..", Baba ya kalleta yace "Au haba, ashe kin san Hajara ƴata ce ko Rabi?", Maama tace "yo ai ana ganin Hajara an san kaika haifeta mal, ni dai ina baka shawara wllh kaje ka ɗakko ƴarka daga wnn gidan tin kafin ayi layya da ita, toh ni dae na faɗa gidan yankan kai aka kaita..", Baba yayi wani murmushi na manya yace "tinda dai ba Nabilah ko Sa'adatu ko Maimuna na siyar ba ai shknn, ki zuba ruwa a ƙasa ki sha", da haka ya kira Umma da ke ɗakinta, fitowa tayi tace "gani mal", yace "na fita", tace "Allah ya tsare mal", yace "Ameen" ya saka kai ya fita daga gidan, Umma ta juya zata shiga ɗaki Maama tace "faɗima..", Umma ta haɗe gira ta juyo ta kalleta tace "dani kike?", Maama da ta koma wata psycho tace "akwai wata faɗimar ne bayan ke, dake nake..", Umma tace "Au", Maama har dasu gyara tsayuwa tace "idan mal baiji ba ina fatan ke kiji, wllh shawara nake baki, karki bari ayi layya da ƴarki, marmaza ki rugungunta kije ki ɗakko ƴarki..", Umma tayi wani murmushi tana kallon Maama sama da ƙasa tace "kashh baiwar Allah aini bana ɗaukan shawara dama dai basir ne wataƙila na ɗauka.." da haka ta bankaɗa labule ta shige ɗakinta ta bar Maama da sakakken baki, Maama ta ɗaga murya tace "in Allah ya yarda sai kunyi nadama keda mal, tinda kunnen ƙashi ne daku, a kwali za a kawo muku gunduguilar kan Hajara anyi layya da ita..", Sa'adatu ta fito tace "haba Maama ya zaki tashi da safiyar Allah ki ringa mana ihu a gida", Maama tace "Sa'adatu wai Maimuna ba ta gaya miki cewa mal ya siyar da Hajara ba, ai ita taga gidan, wllh na ƴan yankan kai ne", Sa'adatu ta yamutsa fuska tace "toh wai ina ruwanki Maama, ko gidan yankan kai aka kaita meye naki aciki..", Maama tace "wllh kuwa ba nawa a ciki, kawai dai shawara nake bawa mal yaje ya ɗakko ƴarsa a raba auren..", Sa'adatu tayi tsaki ta koma ɗaki. Maama tabi bayanta tana cewa "kamo min Balaraba a wayarki", Sa'adatu tace "ni bani da lambarta, Nabilah ce mai ita..", Maama ta ɗauki wayar Nabilah ta lalubo lambar Balaraba, tayi dialing saidai kuma babu kuɗi a wayar, da kyar Sa'adatu ta kira mata ita a tata wayar, tsabar rashin nutsuwa a waskace Maama ta riƙe wayar ta kara a kunne, Balaraba na ɗauka Maama tace "an yanka ta tashi, sai an biyani kuɗina", Balaraba tace "lfy ƙawata?", Maama tace "ina fa lfy, ai ko ƙamshin lfy babu a tare dani, gani nan zuwa gidan ki..", ba ta ƙarasa magana ba Sa'adatu ta warce wayar ta kashe tace "daman minti ɗaya nace", Maama ta bita da kallo. ★Noor ta shiga part din Mami ta sanar da ita cewar ta gama haɗa breakfast da za a kai gidan Nurain, Mami tace "good, an shirya a basket ko?", Noor tace "na bar Laure na shiryawa", Mami tace "Ohk, to kiyi sauri ki shirya a kai musu", Noor tace "tom, ai Yaya ma yazo", Mami tace "Nurain din, tin yaushe?", Noor tace "almost 20minutes, Hajiya ma is here tana part din Abba", Mami tace "okay, je ki shirya". Noor ta fita zuwa room dinta, Mami kuma ta fita zuwa part din Abba, Mami na shiga Hajiya ta miƙe kenan tayi support da sandarta, Mami ta gaisheta cike da ladabi, Hajiya ta amsa tace "ina Usuman din yazo ya kaini gidansa", Abba yace "call him for her", Mami tace "yana nan ne", Yace "yanxu ya fita daga nan", Mami tace "tom" da haka ta juya ta fita, upstairs ta haura zuwa room ɗinsa, ta ringa knocking amma no respond, murɗa handle din ƙofar tayi don taji a rufe yake ko a buɗe, ai kam tana murɗawa ta buɗe, Mami ta shiga, yana kwance kan bed yayi rigingine, kallon 5sec Mami tayi masa trying to figure out me yake damunsa, ta kirasa bai amsa ba, ta sake kiransa nan ma bai amsa ba, da alama ya lume cikin tunanin da yake, gefen bed din tayi taping tace "Nurain are you Okay?", ya tashi yana goge fuskarsa da palm yace "Sure, am okay", ta ringa kallonsa kafin tace "Alright, ka taso ka kai Hajiya gidanka", shiru yayi baice komai ba, Mami tace "kaji me nace?", yace "yeah", tace "toh yi da jiki gata can tana jiranka a palour", ta fita a ɗakin, saida yayi wanka ya canza kayan jikinsa zuwa ƙanana snn ya fito, a hankali yake sakkowa daga stairs, thick eyebrows dinsa a haɗe, tini Hajiya da ke zaune main palour ta dogara sandarta tayi hanyar fita, Mami tace "tare da Noor za ku tafi zata kai breakfast", yace "tom" yabi bayan Hajiya, Noor ta fito daga kitchen da basket a hannunta Laure biye da ita itama da wani basket din a hannunta, Hajiya ta hakimce a gaban mota rungume da sandarta, Noor ta saka basket din abincin a boot snn ta shiga back seat, shi dai Nurain baice komai ba kawai ya kunna qira'ar Sheikh Abdul Baseet yana sauraro, har suka je gidan ba wanda yayi magana, ya sauka ya buɗe gate snn ya dawo ya shigar da motar compound, yana parking ya fita yaje ya buɗe ƙofar shiga main building, Hajiya ta dashare tooth tana kallon flower tace "kaii gida zakwai", Hajiya na zuwa balcony Nurain ya buɗe mata ƙofar ta shiga shi kuma ya bar wajen, Noor na gama sauke basket yaja motarsa ya bar gidan daman bai rufe gate ba da suka shigo, saida ya zuge gate din amma bai sa masa key ba snn ya bar unguwar, da ɗaɗɗaya Noor ta shiga da kayan Abincin, Hajiya na tsaye ƙiƙam a palour tana ƙarewa ko ina kallo, Hajiya tace "kinga sai sallama nake ba amsa", Noor ta dubi tulin ledojin dake yashe a palourn tace "tana sama Hajiya, bari na kirata", Hajiya tace "A'a ina ke ina hawa sama, mijinta yazo ya kirata", Noor tace "ai ya fita", Hajiya ta hangame baki tace "ban san me yasa Usuman ya zama mai baƙar zuciya ba, kina gani fa zaman kurame mukay dashi a mota", Noor tace "mood ne ironlady..", Hajiya tace "meye kuma mood?", Noor tace "ina zuwa", ta haye stairs, ta kwankwasa ɗakin da Hajar take, bayan kamar minti uku tana knocking kawai ta murɗa ta shiga, surveying ɗakin ta ringa yi da idonta, daga can gefen gado ƙasan tiles ta hangota a kwance, ta ƙarasa kusa da ita ta tsugunna tace "Hajar.. Hajar.. Hajar..", ko motsi Hajar ba tay ba, Noor tayi taping ɗinta nan ma dai bata motsa ba, saida Noor ta nutsu snn taga yadda take breathing a hankali kamar zai ɗauke, ta taɓa goshinta taji zafi ɗau tamkar tasa akan wuta......✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {37..} Noor ta sake taping dinta a hankali gami da kiran sunanta, da kyar Hajar ta buɗe idonta da sukay mata nauyi, tana buɗewa ta mayar ta rufe, Noor ta taɓa wuyanta taji shima yayi zafi ɗau amma bai kai kanta ba, Noor tace "Hajar are you Okay?", Hajar ta sake buɗe idonta da kyar tana jin yadda kanta ke sarawa kamar zai tsage, dishi dishi take ganin Noor, tace "Umma.. Umma.." kafin ta kuma lumshe idon, Noor dai ta fara firgita cause Hajar was so weak, ta tashi da sauri ta fita a ɗakin, downstairs ta sauka ta nufi inda ta ajiye handbag dinta, Hajiya da ke zaune kan sofa tace "ina matar gidan take?", Noor na ƙoƙarin ciro wayarta daga jaka tace "ina jin ba tada lfy ne, bari na kira yaya", tayi dialing numbern Nurain, no respond, ta kuma kira nan ma same thing, Hajiya tace "kai jama'a, ƴar nan kiyi min magana yadda zan gane mana waye kuma ba lfy?", Noor tace "Amaryar ce, jikinta zafi, ko motsi bata yi", Hajiya tace "ba kanta, sbd Usuman ya zama mai baƙin hali daga nace kar ya saki yarinya shine ya ƙullaceni, ya kawoni gidansa ya yasar sai kace bola, da badan ni na haifi mahaifinsa ba da yau sai ya iya kwakkwalla min mari, don yadda ya fusata ɗin nan ƙiris ya rage ya zargeni ɗaxu a palourn Muntari..", Noor dai bata tanka ba kawai kiran layin yayan ta take, sau wajen goma tana kira, ta sauke wayar daga kunnenta tace "Hajiya kinga bai ɗauka ba yanxu ya zanyi?, ba fa ta motsi", Hajiya ta gwalo ido tace "mun shiga uku, tana numfashi?", Noor ta haura sama da sauri da wayarta a hannunta, Hajiya dai ta bita da ido don ba ƙafar hawa bene, yadda Noor ta barta haka ta sake tarar da ita, ta ajiye wayarta gefen gado ta durƙusa gabanta ta kira sunanta don taga dai is she concious, yess she is concious amma daf take da zama unconscious, Noor ta fara ƙoƙarin ɗagata daga kan tiles, Hajar ta saka last strength dinta tayi ƙoƙarin miƙewa amma ta kasa, ƙafarta ta lankwashe za tayi collapsing a ƙasa Noor tayi saurin tarota ta turata kan gado, sosai hankalin Noor ya tashi ta ɗauki waya ta kira Mami, Mami na ɗaga Noor tace "Mami, Hajar ce ba tada lfy, I don't think she is concious..", Mami tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un mai ya sameta?", Noor tace "i don't know wllh a haka na sameta", Mami tace "ina Nurain din?", Noor tace "he is not around tinda ya sauke mu ya fita, na kira wayarsa beyi picking ba..", Mami tace "seak for help outside, gani nan zuwa.." da haka ta katse kiran, Noor ta ringa kallon fuskar Hajar da pity eyes sai kuma ta juya ta fita, compound ta fita tana jin Hajiya na watso mata tambaya, ta buɗe gate ta fita, ta ringa bin layin da kallo wai ko zata ga wani, tsit har bayan minti goma da fitowarta ba taga wani ba, tayi deciding ko ta shiga wajen neighbors, gidan dake very close to the house ta fara knocking da dutse, almost 5mins amma ba a buɗe ba, wani tunani ne yazo mata don haka ta koma gida, ta maƙale jamlock ta yadda ƙofar ba zata garƙame ba, tana shiga palourn taga Hajiya sai jinjina take tana ƙoƙarin hawa stairs, ta riƙe railer gam da hannun dama hannu hagu kuma sandarta, Noor tace "Hajiya ki koma ki zauna bafa zaki iya hawa ba", Hajiya ta koma gefe tana haki tace "hankalina yaƙi ya kwanta wllh, naji kince batada lfy kuma naga kin fita kin barta ita kaɗai shine nace bari naje na zauna da ita ba a barin mara lfy shi kaɗai", Noor tace "ga Mami nan zuwa ai", taimako gaggawa Noor ta bawa Hajar ta hanyar jiƙa towel ta ɗora mata a forehead sbd zazzaɓin ya sauka. Babu daɗewa Mami da iso gidan tare da driver, Hajiya tace "Dije, a tsakani ga Allah mai Usuman yake shirin zama ne, tinda ya kawomu ya yasar ya saka kai ya fita, ga yarinya can a ƙololuwar samaniya sai suma teke tana farfaɗowa, mijinta likita amma bashi da wani amfani..", Mami tace "Noor na sama da ita knn?", Hajiya ta gyaɗa kai tace "takwarata keta wahala wllh", Mami ta haura saman, ƙofar da ta gani a buɗe ta shiga, Noor ta miƙe daga gefen bed tace "Mami you're here already..", Mami tana kallon innocent face din Hajat tace "how is she?", Noor taji ajiyar zuciya tace "A bit okay", Mami ta matsa kusa da gadon tana kallon kyakkyawar fuskar Hajar, indeed she is beautiful and young, Mami tace "Bacci take?", Noor tace "A'a ta zama very weak ne", Mami tace "gyara mata ɗankwali sai mu wuce hospital en Dr Mansoor", Noor tace "tin ɗazu nake gyara mata sai ya kuma zamewa, bari nasa mata hula kawai" ta cire hular kanta ta rufewa Hajar black silky hair dinta da aka yarfawa siraran kitso. Babban private hospital aka kai Hajar, tini doctors suka amsheta, a Amenity room aka kwantar da ita aka saka mata drip, cikin mintinan da basu wuce uku ba ta zama stable, fever din ta sauka, akai mata allurar bacci sbd ta huta, Mami ta fita reception ta cigaba da kiran Nurain da tin ɗazu take kira baya picking, wajen Hajiya da ke zaune kan silver chair ta nufa tace "Hajiya, driver zai mayar dake gida...", Hajiya tace "ina fa zan koma gida ga ƴar mutane rai a hannun Allah, yanxu wnn kyakkyawar yarinya ɗanya shagaf Usuman zaice baya so, kyan fuska dai ya samu Allah yasa zuciyar ma me kyau ce, ni babu inda zani sai ƴar mutane ta farfaɗo", Mami tace "ai ta samu lfy, bacci take zata huta daga ta farka shkn. zata tashi sumul", da kyar Mami tayi convincing Hajiya ta yarda zata koma gida, Hajiya na tafiya tare da driver Mami ta kira Anty Zulaiha ta gaya mata abinda ya faru, bayan ta gama waya da Anty Zulaiha ta sake kiran Nurain, ba ƙaramin ɓaci ranta yayi ba da baya picking. ★Nurain kam daman kai tsaye gidansu Farooq ya wuce, yana parking motarsa ya zagaya ta bayan gidan inda zai shiga part ɗin Hajiya direct ba sai yabi ta main door ba, anan kusa da part din Hajiya ɗakin Farooq yake, Nurain yayi knocking ƙofar ɗakin Farooq, Farooq ya buɗe ƙofa ya kallesa da sleepy eyes ɗinsa sai kuma ya ƙanƙance ido yace "brother, me ya fito da sabon ango this early morning?..", Nurain da yake moody yace "move", Farooq ya basa hanya ya wuce, yana shiga Farooq ya rufe ƙofar ya bisa da kallo, Nurain ya zaune kan executive coach dake ɗakin gami da lumshe ido, Farooq ya zaune gefen gado yana facing dinsa yace "what's up..?", Nurain bai tanka masa ba saima ya kwanta kan coach din yayi pillow da hannunsa, Farooq yayi kwanciyarsa don bacci bai ishesa ba, weekends ne kawai yake samun hutu ba fitar sassafe zuwa work, Nurain kam gaba ɗaya mind dinsa a cunkushe take, meyasa bashi da sa'a ne wajen aure, Ruqayyah betrayed him and now an aura masa mara manners, tashi yayi ya zauna ya dafe kansa, Farooq ya miƙe ya zuro ƙafafuwansa ƙasa yana kallon brother din nasa yace "wai me yake damunka ne Nurain?, aren't you here to tell me..", Nurain yace "auren da akay min ne banaso wllh, am not happy with it..", Farooq yace "why?, naga dai jiya lfy na maka rakiya, and it seems like you were happy that time..", Nurain yayi ajiyar zuciya yace "damn it, ko a lokacin bana farin ciki kawai dai i was calm to accept it as my destiny, but now bazan hakura ba gsky, ban taɓa tunanin akwai ranar da zan turning Abba down ba sai wnn karon, turning din kwa shine wllh sakinta zanyi, waccar rigimammiyar tsohuwar ce ta mayarmin da agogo anticlockwise, wllh da tini na wuce wajen..", Farooq da bai fahimci brother din nasa sosai ba yace "wai kana nufin kace sakin matar da aka aura maka jiya za kayi?", Nurain ya shafa fuska yace "yeah, sakinta zanyi sbd bazan zauna da ita a matsayin mata ta ba...", Farooq yace "ban san mene dalilinka ba amma kana ganin sakinta shine solution, what about Abba..", Nurain ya katsesa da fadin "Abba babu abinda yace infact ma cewa yayi ai ya gama role dinsa ynxu option ya rage nawa, ruwana ne na zauna da ita ruwana ne na saketa, so na gama yanke decision zan rubuta takardar sakin na kaiwa Abba tinda ya amince..", Farooq yayi murmushi yace "shi Abban ne ya baka damar ka saketa?", Nurain yace "Sure", Farooq ya sake yin wani murmushin yana jujjuya kai, Nurain ya hade gira yace "meye haka..", Farooq yace "uhmm, are you a kid?, toh wllh Abba testing naka yake, am telling you gwada ka yake punk, taya ya zai baka go ahead direct ka saki ƴar mutane", Nurain yace "Allah ko, toh kwa zanyi failing don bazan ci test dinsa ba..", Farooq ya tashi yace "nidai ga piece of Advice zan baka, indai dalilinka bai kai wanda zaka saki ƴar mutane ba toh ka janye batun nan, ko don reputation din Abba ya ɗaure a idon iyayen yarinyar..", Nurain ya wani galla masa harara yace "oh really, i don't want your Advice ka rike abinka", Farooq ya ɗaga kafaɗa ya buɗe huge wardrobe ensa ya ɗauki button down shirt and dark blue jeans trouser ya shiga bathroom, bayan minti goma ya fito da kayan da ya shiga dasu ajikinsa, Farooq ya tsaya jikin mirror yana goge kansa da hand towel, yayi combing hair din da brush snn ya shafa mai a palm da legs, Farooq ya dubi Nurain yace "am coming" da haka ya buɗe door ya fita, after like 5mins ya dawo dakin da rufaffen plate a hannunsa, ya ajiye plate din akan bedside, mini fridge dinsa dake ɗakin ya buɗe ya ɗakko lemon kwali na raspberry, gefen gado ya zauna ya ɗauki plate en da ya shigo dashi ya buɗe, chips ne da kwai sai satchet ketchup, Farooq yace "ga breakfast", Nurain yace "No, thanks..", Farooq yaci abinci yayi nak abinsa, ya zuba juice yasha daman shi baya shan tea da safe sai dare, Nurain ya tsiyayi lemon yana sipping, wayar Farooq ce tayi ringing, Farooq yayi unplugging dinta daga charge da take, ganin mai kiransa ya dubi Nurain kafin yayi picking ya kara a kunne yace "Na'am Mami..", yay shiru na second uku sai kuma yace "eh yana nan", yana kallon Nurain da shima yake kallonsa yace "okay" ya sauke wayar daga kunnensa, Farooq yace "Mami ce take tambayarka, tin ɗazu take kiran wayarka baka picking", Nurain ya ajiye cup din lemon da yake sha ya tashi ya fita, compound ya fita wajen motarsa, ya buɗe ya ɗauki wayarsa da ya manta kan dashboard, 40 missed calls ya gani daga different people, na Mami duk yafi yawa sai na Noor ga kuma na Abba ma guda uku, sai kuma na wacca tasa ya tsani wayar, ya kare hasken rana dake haske masa ido da hannu, numbern Mami yayi dialing, tana shiga tayi picking, ya lumshe ido yana jin yadda muryarta ta canza tana masa faɗa, Calmly yace "am sorry Mami". ★Anty Zulaiha na kallon Hajar dake bacci tace "wai me yake damunta Mami, lafiya lou fa jiya muka barta tare dasu Khausar..?", Mami tayi ajiyar zuciya tace "sai doctor yazo zai faɗi abinda suka gani, ba kiga a yadda muka kawota nan ba, Noor kam cewa tayi lokacin da ta ganta ko numfashi ba ta yi sosai..?", Anty Zulaiha tace "innalillah, Allah ya rufa asiri, shi kuma Nurain ina ya shiga har yarinyar mutane ta shiga wani hali", Mami tace "wa ya sanar masa, da sassafe dai yazo gida wajen Abba, daman Hajiya ta zabga sammako tazo tace a kaita taga Amarya shine ya ɗauketa ita da Noor zata kai musu breakfast zuwa gidan nasa, wai ashe yana ajiyesu ya juya yabar gidan, Noor ta kirani take gayamin wai Hajar en ba lfy, saida naje gidan snn muka ɗakkota muka taho nan, tin ina gida nake kiran Nurain amma bai ɗauki kirana ba, saida na kira Farooq na tambayesa, shine yake gayamin wai yana gidansu, Nurain bai taɓa ɓatamin rai kamar na yau ba, zaizo ya sameni aii", knocking ƙofa akay Dr ya shigo tare da Nurse biye dashi, ya gaisa dasu Mami snn ya wuce gadon patient yana magana da Nurse din, yace "for now kar ay mata amfani da normal saline..", Nurse tace "yess dr", ya duba ruwan da ake ƙara mata snn yayi feeling temperaturen ta, discharging Nurse en yayi ta fita, ya juya yana kallon su Mami yace "me ya faru da ita haka har bp nata yayi high?", Anty Zulaiha ta kalli Mami da weird expression, Mami tace "Bp doctor?", Dr ya gyaɗa kai yace "yess, jininta ne ya hau sosai, Allah yaso kunyi rushing zuwa hospital da ba haka ba zuciyarta zata iya exploding cause jinin ya hau sosai..", Mami ta miƙe tace "what's her condition now?", yace "Alhmdllh everything has been taken care of, ba matsala insha Allah she is stable", Mami tace "Alhmdllh", yace "i will send a prescription right away, a siyo drugs en a bata idan ta farka taci abinci" da haka ya fita daga ɗakin, Mami ta dubi Noor tace "bisa ki amso prescription din", Noor tace "tom" ta tashi tabi bayan doctor, Anty Zulaiha tace "an kwa sanar da iyayenta?", Mami ta girgiza kai tace "A'a, bamu da contact dinsu..", Anty Zulaiha tace "ya kamata a gaya musu kwa, kinga ma a tambayesu akan Bpn nata ko tuntuni tana dashi", Mami tayi ajiyar zuciya ba tace komai ba, knocking akay kafin aka buɗe ƙofar aka shigo, Nurain ne ya shigo shi da Farooq, Mami ta ɗauke kanta ta haɗe gira, tini Nurain ya sha jinin jikinsa, suka gaisa da Anty Zulaiha, Farooq ma haka snn ya juya ya gaida Mami ta amsa masa, Farooq yace "ya me jiki?", Mami tace "alhmdllh da sauƙi", yace "Allah ya ƙara lfy ya mayar kaffara" da haka ya matsa kusa da gadon da Hajar ke kwance, Nurain ya shafa kai yace "Mami how is...", Mami ta dakatar dashi ta hanyar ɗaga masa hannu, Anty Zulaiha tace "kiyi haƙuri don Allah..", Mami tace "meye dalilinsa da har yarinya ta zama unconscious amma be sani ba, da safiyar Allah ya kama ƙafa ya fita ya barta ita kaɗai duk bance masa komai ba, snn ma da ya kaisu Noor gidan me yasa ya tafi ya barsu haka nan, gashi wayarsa ba tada amfani ko emergency ya taso ba za'a sami taimako daga wajensa ba..", ta kalli Nurain da kansa ke ƙasa zuciyarsa na tafarfasa tace "Uthman, wllh Allah idan wani abun ya samu yarinyar nan you are going to see the other side of me, ai Abba ya gaya min abinda ka tarka mara tushe da kan gado" da serious note ta faɗi hakan, Noor ta shigo da prescription paper a hannunta ta miƙawa Mami, without looking at him Mami tace "bashi ya siyo drugs en", Noor ta miƙa masa takardar, ya warce kafin ya fita daga ɗakin da speed, Farooq ya ja kujera ya zauna, a hankali Hajar ta fara motsi da hannunta kafin ta kaisa ta dafe goshinta, ta buɗe idonta tana ƙarewa environment ɗin da take ciki kallo, Farooq da yayi noticing yace "ta farka". Mami ta taso ta zauna gefen gadon tace "sorry dear", Hajar ta haɗiyi wani yawu wanda da kyar ta samesa sbd bakinta a ƙafe yake, support tayi da hannunta ta miƙe zaune, ta kalli hannunta mai canular da ake mata ƙarin ruwa, sai kuma ta ɗaga kai tana kallon drip stand din da akay connecting da hannunta, tass ta fahimci a inda take amma bata san mutanen da ke wajen ba, Noor kawai ta shaida, ta lumshe idanunta ta kuma buɗesu murya a dashe tace "Umma.. Umma.. Ummata".....✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {38..} Kawai Ummata Hajar take kira, Mami tace "Umman ki za'a kira miki?", ta gyaɗa kai a hankali, Mami tace "alright, insha Allah za'a kira miki ita, how are you feeling now?", Hajar tace "alhmdllh", Anty Zulaiha ta taso ta tsaya gaban gadon tace "sannu ko", a hankali ta jinjina kai sai kuma ta koma ta kwanta ta lumshe ido, few seconds bacci mai nauyi ya sake figarta cause allurar baccin bata gama sakinta ba... Nurain na fita ya buɗe prescription paper en ya karanta content en ciki, he was totally confused bayan yayi realizing drugs en dake rubuce, murya can ciki yace "too young, may be inheritable..", wani near by pharmacy ya shiga ya siyo drug en, ya dawo asibitin da ledar magungunan a hannunsa, duk iya ƙoƙarin sa na ganin ya saki fuskarsa kafin ya shiga Amenity room en kasawa yayi, cause da gasken gaske zuciyarsa ba dadi, ya murɗa ƙofa ya shiga kafin yay sallama ciki ciki, Anty Zulaiha ta amsa, nan kan kujera ya ajiye ledan yace "gashi", without looking at him Mami tace "saura abinda za taci idan ta tashi", still yay na few seconds kafin yace "i thought daga gida za'a kawo abincin..", tace "right, amma ita bashi zata ci ba, so ka samo mata nata kafin ta farka", yace "yeah" zuciyarsa kamar zata fashe, ya juya ya fita, Farooq dake zaune kan plastic chair ya tashi yabi bayansa, Anty Zulaiha tace "Mami that was too tough", Mami tace "No Zulaiha, abinda ba halinsa bane yake so ya tarka, ba zai yiwu ba wllh, bazan bari yayi abinda bai dace ba gsky, ko baki lura da reaction ensa bane, bayan ya kulle yarinya a gida harta shiga wani halin, nifa I'm not in support Nurain ya bagarar da yarinya in the name of aura masa ita akay, bazan so ayi ma nawa yayan haka ba don haka nima bazan bari ayima yayan wasu ba..", Anty Zulaiha tace "kin san arranged marriage akan samu irin haka Mami..", Mami tace "ai irin hakan ne banaso..", Anty Zulaiha ba ta sake cewa komai ba. bayan 40mins Farooq ya shigo with bags a hannunsa, ya ajiye snn ya juya ya fita, Mami tace "check.. kiga nemi aciki", Anty Zulaiha ta janyo ledojin gabanta ta duba, grilled fish ne na manyan tilaphia with potatoes, sai ƙatuwar bottle of fresh milk da kuma leda guda ta fruits, Mami dai combination na abincin bai mata ba, kifi da madara, kawai dai tayi shiru tinda dai ya siyo. Farooq ya ringa kallo kujerar da ya bar Nurain akay nan reception ganin empty baya nan, toh ina yaje, cewa fa yayi zai jira shi anan ya fito sai su wuce Chinese restaurant suci seafood. Nurain yayi knocking consultation room kafin ya murɗa ya shiga, ya zauna ɗaya daga kujeru biyu da suka gaban huge table da ke ɗauke da nameplate da sauran tarkace na doctor, gaisawa sukay da Doctorn, Dr yace "Dr Uthman right?", Nurain yace "yeah", Dr yace "ya aiki..?", Nurain yace "Alhmdllh ya naku?..", Dr yace "same alhmdllh", Nurain yace "Dr Mansoor bai ƙaraso ba knn?", Dr yace "Eh, sai qarfe biyar zai shigo", Nurain yace "Ohk, amm akwai wata patient da aka kawo.." sai kuma yayi shiru cause bai san sunan da zaice ba, tunawa yayi da numbern room din yace "wacca take Amenity room 2", Dr yace "Ohh, what about he?", Nurain ya sauke numfashi yace "how's her condition, za'a iya dischaging nata kafin dare..", Dr yace "No, her condition is totally not enough for discharge, za'a ɗan riƙeta na some days sbd kula da yanayin Bpn..", Nurain ya jinjina kai yace "Alright, ba damuwa kawai ayi dischaging nata akwai family doctor da zai kula da ita a gida", Dr yayi shiru yana kallonsa sai kuma yace "is she part of your family?", Nurain yace "No", Dr yay jim jin yadda ya basa amsa with repartee, Nurain yace "look, she's the daughter of my father's friend, rashin zuwan family doctor en ne yasa aka kawota nan toh yanzu doctor yazo, he will take over insha Allah...", Dr yace "Ohk", nan ya shiga yiwa Nurain bayanin komai, treatment en da aka fara mata ta yadda kawai Dr ɗorawa zaiyi, da yake shine ya duba Hajar din a take ya rubuta referral letter ya bada amma sai yamma za sallameta under cewar wani dr zai taking over, Nurain ya basa hannu sukay sallama kafin ya ɗauki referral papern ya fita a office en, wnn shine kawai option ensa to get rid of Mami's anger, yasan mene a zaman asibiti ai, ganin dr da gwaje gwaje, All Bp stuffs yana dasu a gida. sai ƙarfe biyu na rana Hajar ta farka, ba kamar ɗazu ba yanxu jikin yafi kwari, sai kace wata qaramar yarinya ta fara kiran ummata, Anty Zulaiha ce kawai a dakin Mami bata dade da fita ba wajen Dr, Noor kuma ta wuce gida Mami ce tace ta tafi sbd Hajiya na can kar tayi zugum ita kaɗai, Anty Zulaiha tace "toh fadi numbern umman taki sai a kirata", ai kam da sauri ta fara karanto numbern Umma dake haddace akanta, Anty Zulaiha ta rubuta snn tayi dialing, har ta katse ba a dauka ba ka sake kira, tana daf da katsewa aka daga, cikin dabara kuma a nutse Anty Zulaiha ta fara yiwa Umma bayani, don haka Umma bata wani firgita sosai ba, daga ƙarshe Anty Zulaiha ta kwatanta mata asibitin tace idan zata zo amma dai ba wata matsala Hajar ta samu lfy, sai a lokacin Hajar ta dan ji relief, ta fara ƙoƙarin sakkowa daga gado, Anty Zulaiha tace "mene ne, akwai inda ke miki ciwo ne?", ta girgiza kai tace "A'a sallah zanyi" tana kallon wall clock dake ɗakin, Anty Zulaiha "Ohk, zaki iya tafiya da kanki", ta gyaɗa kai tace "zan iya", a hankali Hajar ta sakko daga gado ta ɗane hannun da aka saka mata canular, ruwa leda biyu aka saka mata, tana bacci aka cire na biyun ba a saka wani ba sai kuma dare sbd kar tayi swelling tinda ba tada rashin ruwa a jiki kawai na kwarin jiki ne, Anty Zulaiha ta nuna mata door din toilet dake dakin, Hajar ta shiga toilet en tana bin bango tayo alwala ta fito, hannu a ɗane ta fito tana riritasa sai kace wani babban ciwo, Anty Zulaiha ta bata prayer mat da Nursa ta ara musu ita babu jimawa za suyi sallah, mayafinta da ɗauka ta yafa tinda babba ne snn kuma kayan jikinta is more than decent, ta hau kan prayer mat din ta tayar da sallah, kafin ta idar Mami ta shigo, ba ƙaramin daɗi taji ba ganin Hajar harta samu kwarin sallah, Anty Zulaiha tace "na kira Mamanta na gaya mata..", Mami tace "Ohk, Dr ma yace insha Allah zuwa yamma zai iya dischaging enta, toh kinga kwa Alhmdllh jiki da sauƙi", Hajar na idar da sallah ta koma ta jingina da wall, Mami ta dubeta da sakakkiyar fuska tace "ya jikin naki?", Hajar tace "da sauƙi" tana kallon hannunta da ta ɗane sa, Mami tace "toh koma kan bed ki kwanta", ba musu ta miƙe ta koma kan gadon ta zauna, Anty Zulaiha ta ɗakko robar grilled fish ta bata, da rubber fork Hajar ta ringa cakar dankalin tana ci, kaɗan taci kifin tace ta ƙoshi, tasha ruwa da already shima Anty Zulaiha ta ajiye mata, Mami ta buɗe ledar drug dinta ta duba dose kafin ta ɓalla ta bata, wani irin yamutsa fuska Hajar tayi don idan akwai abinda ta tsana bayan allura to magani ne, da ɗaɗɗaya da ɗaɗɗaya ta haɗiye three tablets din. da misalin uku da minti hamsin Umma ta iso asibitin ita da Anty Jamilah, wata staff ce mai shara ta rakosu room din da suka gaya mata sunansa da Anty Zulaiha ta sanar musu ta waya, Hajar na ganin Ummanta ta sakko daga kan gadon tabi bango taje ta rumgumeta hawaye na zuba idonta, Umma tayi yaƙe ta shafa bayanta, Anty Jamilah ta zauna sukay exchanging gaisuwa dasu Mami, Anty Zulaiha ce ta sanar da Mami wace ce Anty Jamilah, Umma kan ba sai an gaya mata ba cause Hajar ta sanar da ita, Umma ta janyeta daga jikinta ta ƙarasa kusa da Anty Jamilah ta zauna, suka gaisa da su Mami, Hajar ta rakuɓe nan gafe guda hannu a ɗane tama faman riritasa, Anty Zulaiha tace "dan dai ta damu da sai an kira mata Ummanta ai da sai mun koma gida za a gaya muku, tinda da yammar nan za a sallameta", Anty Jamilah tayi murmushi tace "gashi dai kam ai lafiya ta samu, ai ƴar uwarta ma taje gidan tanata tsaye a waje ashe ba kowa ana asibiti", Anty Zulaiha tace "Allah sarki, ai tin safe muke nan da yake ciwon da safe ya tasar mata..", Umma ta ɗan tattare fuska, ciwon ya tasar mata, idan fa akace ciwo ya tashi to ana nufin daman tin tini mutum na ɗauke dashi, toh me yake damun ƴarta don ita dai tasan batada wani ciwo. Dr ne ya shigo wanda yayi taking over tinda wanda ta gani da safe ya tafi, kallon gado yayi ganin wayam yace "where is the patient", Hajar ta turo baki ta tashi tana layi kaɗan ta koma kan gadon, few questions yayi mata kafin ya fita yace zai dawo nan da 1 hour, su Umma basu wani jima ba suka tashi tafiya, nan hankalin Hajar ya kuma ɗagawa, Anty Jamilah na kallon fuskarta da hawaye ya cika tam a idonta tasan kuka za tay, ta isa gefen gadon ta zauna kusa da ita ta fara mata magana a hankali, Hajar ta gyaɗa kai tana controlling kukan da yke shirin kwace mata, da kyar tace "tom, na dena wllh kuma zan kwantar da hankalina", Anty tace "good, to sai nazo" da haka ta miƙe ta sake yiwa su Mami sallama, Umma ta dubi Hajar da take daf da rushewa da kuka tayi mata murmushi snn ta buɗe ƙofa ta fita Anty Zulaiha tabi bayanta. Hajar tayi sauri ta kwanta ta tsiyayar da ruwan hawayen da ya cika mata idanu, After 1 hour din kam Doctorn ya dawo a lokacin biyar saura, kai tsaye sallama ya basu daman sunyi magana da waccan Drn. ƙofa akay knocking kafin aka shigo, Nurain ne, ido huɗu sukay da Hajar, yay saurin ɗauke kansa ya hade gira, Mami na kallon Dr tace "A cire mata canular", with a repartee Nurain yace "No, kar a cire", Mami ta dubesa ba tace komai ba, Dr yay musu sallama kafin ya fita. Anty Zulaiha na riƙe da hannun Hajar suka fita harabar Hospital en, Farooq dake zaune a under tree ya taso, Nurain ya shiga front seat ya bawa Farooq key din Mota don haka ya shiga driver seat, Mami Anty Zulaiha da Hajar kuma suka shiga baya, Farooq ya kunna motar ya fara driving suka fita daga asibitin, direct daman hanyar gidan Abba ya ɗauka. ★Maama ta rantse ta kuma rantsewa ta buga cinya tace "billahillazi la'ilaha illa huwa sai malamin tsamiya ya biyani kudina dubu arba'in, tinda aikinsa bai ci ba wllh sai ya biyani kuɗina", Balaraba da ke kallonta baki a hangame tace "ai kwa kya yi kya gama Rabii, wane cin kike magana a kai, naga dai auren da ba kya so a ɗaura naga dai ba a ɗaura ba, bata auri malamin makarantar ba ehee, kinga kwa malamin tsamiya yaci kuɗinsa wllh", Maama ta fige ɗan kwalin kanta da ya rufawa kanta asiri, don wani irin tsohon kitso ne a kanta wanda zai kai wata huɗu, ta sosa kan wanda nasan babu shakka kwarkwata ce ta mintsileta, tace "Balaraba malamin nan dan abu kaza kaza ne, me yasa bai hango wanda zata aura ba iyee, wllh da nasan haka zata faru wllh tllh bazan yi asarar kudina ba, ai gwara ta auri malamin makarantar....", Balaraba tace "Wai a sbd me kike faɗin haka?", Maama ta dafe goshinta mai lemon tsami tace "dana sanin da nayi yafi cikin kwando Balaraba, wato ina gaya miki, malamin makarantar nan ba komai bane akan wanda Hajara ta aura...", Balaraba ta kuma hangame baki har ƙudaje suka fara shawagi, Maama ta sharce zufar dake keto mata tace "ke kinga gidan da aka kaita kuwa gari guda, lefen da aka bata kam ya linka na malamin makaranta sau shida..", Balaraba ta kore ƙudajen da suke shawagi kusa da bakinta tace "an shiga ƙuryar ɗaka ba'a tsira ba, Rabi kimin bayani yadda zan gane..", nan Maama ta gyara zama ta shiga fesawa Balaraba zance, ta ƙarashe tana sharce zufa tace "kinga lukutar masifar dana jibgowa kaina", Balaraba ta gyaɗai kai cike mamaki ta kasa cewa komai, Maama ta hauta da masifa tace "dalla malama ya zaki min shiru na zo ki bani hanyar ɓullewa, kin wani hangame baki wari duk ya cikamin hanci ciki ya kumbura, kiyi magana na shaƙi warin da hujja tinda dai na rage zafi amma kinyi shiru inata shaƙar ɗoyi a banza", Balaraba tace "Au haka fa, kinsan gwano baya jin warin kansa, ni da kika buɗe wnn tsumman kan naki sai kace hammatar ɗan iskan sabon gari mai ɗoyin tsiya bance komai ba sai ke, toh kafin cikin ki ya kumbura nawa ya gama cika dammm da samamin kanki..", Maama tayi kwafa tace "haka kika ce ko?", Balaraba tayi tsaki tace "Ahap ai kinji mai nace", Maama ta ɗaura ɗan kwalinta tace "biyani dubu biyar ɗita..", Baraba tace "wace dubu biyar?", Maama ta miƙe tsaye a fusace tace "wacca kika ce sai na baki zaki rakani wajen malami..", Balaraba ta miƙe itama tace "bazan biya ba, akan me zan biya bayan na miki aiki kin samu", Maama ta yayibi duƙunnanen hijab dinta mai warin dauɗa ta saka ta fice fuuu daga gidan kamar zata tashi sama, Balaraba ta buga cinya tace "Allah raka taki gona, ni nan da kike ganina ɗuwaiwai ce ko dan zama a nemeni". daf da magrib Maama ta koma gida a fusace, Baba da ke alwala nan bakin rariya ya ringa kallonta kafin yace "daga ina kike?", ta hura hanci tace "nan nan maƙota na shiga an yiwa ɗan gidan shayi", Baba bai sake ce mata komai ba ya cigaba da alwalarsa, Umma ta fito daga ɗakinta itama za tay alwalar, ta ɗau buta ta buɗe tukunya ta ɗebi ruwa, Baba da ke wanke ƙafa yace "ya jikin Hajaran?", Umma tace "Ahh da sauƙi sosai..", Maama da bata ƙarasa shigewa ɗakinta ba ta juyo tana tafa hannaye tace "za kiga sauƙi, wato har an fara tsotse jininta, wllh duk wanda ya hau motar kwaɗayi babu inda zata ajiyesa sai a tashar wulaƙanci, kuɗi ƙumbar susa sun hanaku amso ƴarku ko, toh wllh ku ka bari aka tsotse mata jini har ta mutu ranar gobe qiyama sai an muku hisabi da ita, wnn ai cin zali ne da tauye haƙƙi, ƙiri ƙiri kuɗi sun ruɗeku kun wurga yarinya a halaka, kun kaita gidan yankan kai za ai layya da ita..." Baba ya tashi yayi ficewarsa cause har an kira sallah, Umma tayi shigewar ta bayi, Maama ta gyaɗa kai tace "hmmm, a banza an yakushi kakkausa, wllh kanku kuka wulaƙanta" da haka ta afka ɗakinta, ta kalli Nabilah tace "Su Sa'adatu basu dawo ba ko?", Nabilah tace "Eh, dan Allah Maama wai ina ruwanki da auren Hajara ne", Maama ta zabga wani uban tsaki tace "shknn, tinda nace kar su kai dare amma saida suka kai wllh ba ruwana idan mal ya gansu, kar ma shegiyar da ta ambaci suna na". ★Wani extra room dake part din Mami aka gyarawa Hajar, Noor ta kawo mata kaya set biyu da kuma sleeping gown, bayan tayi wanka ta ɗauki guda ɗaya ta saka, Hajiya har nan tazo ta dubata tana rafsa salati da godiya, ai gwara da ta warke kar ace a gidan jikanta ne, Hajar ta durƙusa har ƙasa ta gaida Hajiya, bata amsa ba ta tsaya tana kallon hannun Hajar din take maƙalesa tsabar san jiki, Hajiya tace "meye wnn en kuma ya sandarar mata da hannu?", Noor da itama ke ɗakin tace "Canular ce iron lady, abin ƙarin ruwa..", Hajiya tace "toh me yasa basu cire mata ba a can asibitin suka barta da wahala?", Noor tace "nima ban sani ba", Hajiya ta kalleta ta saman kantamemen glasses dinta tace "tafi kira Usuman yazo ya cire mata, ji fa yadda hannu ya sandare", Noor tace "ya fita masallaci", Hajiya ta danne sandarta ta mike daga gefen gado da ta zauna tace "nima bari naje nayi sallar" da haka ta dogara sandarta ta fita, Noor tayi ajiyar zuciya tace "Ohh, Hajiya iron lady", Hajar tayi murmushi, Noor tace "kiyi sallah, yanxu zan kawo miki abinci", ta fita, Hajar tayi sallah, tana idarwa ba jimawa saiga mai aiki da tray na abinci, ta ajiye kan couch kafin ta fita, Hajar na idar da sallah ta jingina da jikin gado ta lumshe ido, jiri ne yake ɗan ɗibanta kaɗan, Mami ta shigo, ganinta a haka tace "are you okay dear?, idan akwai inda ke miki ciwo say it out", Hajar tace "bana jin komai", Mami tace "Alhmdllh, ga abinci ki ci sai ki sha drugs ki kwanta ki huta ko", tace "tom nagode", saida tayi sallar isha'i wacca da kyar ta iya yinta a tsaye sbd jiri snn ta buɗe abincin, aroma na abincin ne ya ɗebeta har ta ɗan ci kaɗan, ta sha ruwa, daga haka ta malale kan carpet, (that question goes to you young lady, what are you doing in my house) shine abinda ya amsa a brain dinta, ta lumshe idanunta hawaye na zubowa a cheeks dinta... Nurain ya shigo palourn Mami da leda a hannunsa, Mami na shan fruits Salad while watching news, kujerar da ke facing ɗinta ya samu ya zauna, ya ringa kallonta ganin ko kallon inda yake ba tay ba her eyes fixed on TV, calmly yace "Mami zan dubata", tace "ohk" tana shan fruits Salad dinta, yayi ajiyar zuciya yace "zan sa mata drip ne, na mata injection..", tace "toh..", shiru palourn ya ɗauka sai ƙarar TV, shi bai sake cewa komai ba kuma bai tashi yayi abinda yace zaiyi ɗin ba, Noor ta shigo tana dariya tace "wnn aboniki naki iron lady ina zan kai yajinsa, dole Aysha ta gudu idan kika ce ta shafa miki..", hanyar room din da Hajar take ta wuce, Nurain yace "Noor", ta juyo tana kallonsa tace "Na'am", yace "tana ina?", tace "waa?", ya tsuke piercing eyes ɗinsa, Mami dai ba tace komai ba, Noor tayi tsaye tana jiran yace wani abun, a dan hasale yace "ina patient din?", tace "tana ciki" tayi masa nuni da ƙofar ɗakin da Hajar take, miƙewa yayi da ledar a hannunsa ya shiga ɗakin, Mami ta bisa da kallo, Noor ta shiga ɗakin itama, a bakin door ta gansa ta wucesa ta durƙusa gaban Hajar dake kwance kan carpet, taping dinta tayi a hankali tace "Hajar are you okay?", Hajar ta miƙe a hankali tana kallon ɗakin sbd scent din da tayi perceiving, jajayen idanunta suka faɗa cikin nasa, da sauri ta sauke kanta ƙasa tana yamutsa fuska, yace "Noor help her to bed", Noor ta tashi ta riƙe hannunta ta temaka mata ta koma kan bed, Nurain ya ajiye ledar hannunsa kan chest of drawers ya fara haɗa ruwan injection, ya fito da ruwan da zai ƙara mata ya ciro empty syringe ya zuƙi ruwan kafin ya isa gefen gadon, koda wasa bai dubeta ba, hannun da take maƙewa yake kallo don tanan zai mata allurar ya sa mata ruwa, Noor ta tashi zata basa waje yace "no, ɗago min hannun", Noor ta dauki pillow ta ɗora hannun Hajar mai canular a kai ta matsa gefe, ya kwance Canularn making sure bai taɓata ba, ruwan da ya zuƙa cikin syringe ya fara ɗura mata sbd yayi flushing vein en kafin ya zuba ainahin ruwan allurar, wani zafi Hajar taji a hannun da take riritawa, a zabure ta janye hannunta ta kwala ihu.....✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {39..} Still Nurain yayi yana kallon syring en da ta bar masa a hannu, Hajar ta zaro ido tana yarfe hannunta da already jini ya gama wankesa cause Canularn a buɗe take, da sauri Noor ta isa gaban mirror ta dakko kwalin tissue, ta zauna gefen gadon ta kamo hannun Hajar tana goge mata jinin, Mami ce ta shigo da sauri cause taji ihun Hajar tinda door a buɗe take, Mami tana kallon Nurain tace "what is happening here?", Noor tace "amm flushing vein en ake mata za'a mata allura", Mami ta ƙaraso gefen gadon tana kallon Nurain da ke riƙe da syringe tace "ka mata a hankali mna, you know it's hurting...", baice komai ba ya bar wajen ya ajiye syringe en cikin ledar dake kan chest of drawers snn ya nufi door, Mami tace "Nurain...", ya juyo yace "na'am Mami", tace "ina kuma zaka?, ka gama mata injection din ne?", yace "No, kawai tasha drugs.." da haka ya fice mai gaba ɗaya, Mami ta dubi Hajar da hawaye ya ciko idanunta tace "Sorry" sai kuma ta dubi Noor tace "take that thing off her vein kawai" ta fita a ɗakin, a hankali Noor ta zare mata canularn daga hannun, ta bata tissue ta danne wajen, wani sakayau Hajar taji hannun yayi mata, bayan kamar 2minutes Mami ta dawo ɗakin da ledar drugs da bottle water an rufa mata disposable cup, da kyar Hajar ta iya haɗiyar maganin tana yamutsa fuska, Noor ta gyara mata pillow ta kwanta, Mami tace "Noor saiki kwana anan ko?", Noor tace "tom, bari naje room dina na dawo". ko minti biyar ba ai da fitar Mami da Noor ba bacci ya kwashe Hajar, luntsum tayi cikin duvet tana baccin da ba daban rashin lfy ba bazata iya yinsa ba, Noor na gama uzirinta a room ɗinta ta dawo ɗakin da Hajar take ta kwanta. tsakar dare Hajar ta farka sbd kanta da take jin tamkar zai tsage, ga wani azababben jiri da take jin tamkar ana hajijiya da ita daga kwance, sideways take jujjuya kanta ba tare da tasan tana aikata hakan ba, slight movement da take yi ne ya farkar da Noor wacca sam sam ba tada nauyin bacci, Noor ta kunna bedside lamp kafin ta yaye duvet da ta rufa ta miƙe zaune, saida vision dinta ya daidaita ta lura da yadda Hajar take motsi involuntarily, da sauri ta sakko daga gadon ta kunna lights sosai, with compassion Noor ta taɓa forehead dinta, her temperature was very high at that moment, direct Noor ta fita a ɗakin, after like 5minutes ta dawo tare da Mami, sosai hankalin Mami ya tashi, amma kuma da ta fahimci cewa Hajar na cikin hayyacinta sai damuwar ta ragu, complain ɗin da Hajar tay kawai shine kaii sbd shi yafi takura mata, har Mami zata bata panadol sai kuma ta fasa, Noor da idonta ke cike da bacci tace "kamar ma anyi dischaging enta da wuri fa", Mami tayi ajiyar zuciya tace "nima dai haka na gani, what says the time?", Noor ta duba lokaci a wayarta tace "biyu da minti sha uku..", Mami ba tace komai ba ta tashi ta fita, Hajar dai na jingine da allon gado idonta a lumshe. Mami na fita kai tsaye room din Nurain ta wuce, knocking door tayi, ko 1minute ba tay da fara knocking ba ya bude, ya zaro sleepy eyes dinsa yace "Mami..", tace "kazo ka duba Hajar jikin ya tashi", yace "tom ina zuwa" ya koma cikin ɗakin nasa domin ɗaukar wasu abubuwan, definitely yasan haka saita faru tinda taƙi bari yay mata allura, yana gama ɗaukar abinda zai ɗauka ya fito, yabi bayan Mami suka wuce part enta, yana shiga ɗakin ya ɗauki ledar da ya bari kan chest of drawers, ya zuƙi injection dose en da zai mata a syringe, ya isa inda take jingine da gado yana kallon hannunta da yaji zanen ƙunshi, Mami ta ringa kallonsa ganin yayi tsaye bashi da niyyar yi mata allurar, har ya kai hannu zai riƙe hannunta sai kuma ya fasa, ya farke ledar hands gloves da ya shigo da ita ya saka gloves en a hannunsa, Mami da Noor dai suka bisa da ido, ita kam baiwar Allah Hajar ko iya buɗe idonta ba tayi sbd haske linka mata ciwon kan yake, a damtse yayi mata allurar, ta motsa kaɗan lokacin da ya zare empty syringe en daga muscle enta, ya saka mata drip da bai sa mata ɗazu ba, deeply in his mind saida yayi dana sanin da yasa akay dischaging enta, wai shi gudun liability na asibiti yayi, sai gashi bai tsira ba, yana gama mata duk wani abin da ya dace yace "Mami you should get back to sleep, itama bacci za tay", Mami na kallon Hajar tace "gobe da sassafe sai mu koma asibiti gsky", yace "No, insha Allah she'll be fine", Mami tace "toh Allah yasa, Allah yay albarka", yace "Ameen" kafin ya fita, bayan minti goma da fitarsa Mami taga jikin nata har yay sauqi, ta koma baccinta kuma babu zazzaɓi a jikinta, Mami ta kashe musu fitila kafin ta bar room din, washe gari kam jikin Hajar saidai nace alhmdllh cause kamar ba ita bace ta cikin dare jiya, har ɗaki aka kawo mata breakfast, daga wayewar gari zuwa yanxu da ake maganar 10 na safe Mami ta shigo dubata sau uku, Noor kuma ta wuce school tinda ranar Monday ne. ★Hakima Ruqayyah ta ajiye wayarta a kan mirror bayan ta gama tura text message, ta gyara wuyan rigar kayan baccin jikinta wando da riga kafin ta fita daga ɗakin nata, kitchen ta shiga ta fara preparing breakfast, omelette roll da toasted bread saita tafasa black tea mai kayan ƙamshi, tana gama haɗa breakfast din ta ɗakko Oat meal ta damawa kanta, ta zuba isasshen powdered milk da sugar kaɗan, ta zuba 4pieces na omelette roll ta ɗauki oat meal din ta fita, a palour ta zauna ta ci abincin, tana gama ci ta kai plate da cup en kitchen ta wanke, ta koma room enta ta shiga wanka, ta fito ta tsaya gaban mirror ta gama shafe shafenta tana humming song da tayi setting enta matsayin ringtone na dearest, well ironed uniform ɗinta ta ɗakko ta saka, as usual ta ɗora black Abaya saman uniform en, tsaf ta shirya snn ta ɗauki wayarta ta zura a jaka ta fita ta rufo ɗakin, room din Momy ta shiga don ta sanar da ita ta fita, Momy ta amsa gaisuwar da ta mata tace "kuma kika ce yau night ne dake?", Ruqayyah tace "Eh, exchanging nayi da wata collegue dita ita tamada abinda za tay da safe", Momy tace "ohk, toh sai kin dawo", Ruqayyah tace "uhmm, nayi breakfast na ajiye muku a kitchen", Momy tace "Okay", Ruqayyah ta miƙe zata fita, har ta kai ƙofa Momy ta kirata, dawowa tayi ta zauna, Momy tace "kinsan dai lokacin da Daddy ya ɗebar miki ya kusa ƙarewa ko, ya maganar Dr tinda kince kun sasanta idan ya dawo daga tafiyar komai zai daidaita, ya ake ciki ya dawo en ko bai dawo ba, don na gaji da kareki a wajen Daddy zanyi shiru na zuba idanu ya aura miki Daudan tinda dai bashi da wata matsala...", Ruqayyah ta sauke wata ɓoyayyar ajiyar zuciya tace "Momy, har yanzu bai dawo bane, daga ya dawo shknn, dan Allah ki cigaba da bawa Daddy haƙuri, wllh bana son Dauda bayan mata biyu da yake dasu gashi gajere kamar a kife da kwando, kuma fa ɗingishi yake wllh sai a zata gurgune..", tini idonta ya kawo ruwa, Momy ta taɓe baki tace "Au lallai Ruqayyah har kinada bakin kushe wani ko, toh ke da kike ba nakasasshiya ba ai ba finsa kikai wajen Allah ba, toh kwa ki san inda dare yayi miki wllh, haba kin bi kin nace sai Dr, Doctorn da kika tozarta kika gudu kika barsa ranar ɗaurin aure, daman ni jinki kawai nake da kike cewa ai kun sasanta, ai ba zuciyar kare ne dashi ba da zai yarda dake bayan cin amanar da kikai masa, wani chance en sau ɗaya yke zuwa a rayuwa, ki tsaida hankalinki ki fuskanci reality, ki na dai da manema ba babu ba...", Ruqayyah dai gaba ɗaya guiwarta ta saki, ta goge kwallar da ta zubo mata, Momy tace "you may leave na gama dake", Ruqayyah ta tashi tana goge idonta tace "zan biya gidan ya Kulsoom", Momy tace "kar kiyi dare", tace "tom" kafin ta buɗe ƙofa ta fita, slowly take tafiya a street en gidansu tana saƙa da warwara a zuciyarta har ta fita babban titi, ta tsayar da Napep ta gaya masa inda zai kaita, har cikin asibitin ya shigar da ita, ta sauka ta buɗe jaka ta bawa mai napep kuɗinsa, a hankali take tafiya tana kallon parking spaces, wani irin harbawa zuciyarta tayi, hope din da take dashi ya zagwanye gami da tsiyayewa ta guiwarta ganin babu motar Dr Uthman a wajen parking ensa, direct hanyar office ensa ta nufa, tayi zaman jira kan silver chair dake ƙofar office en nasa, nace wasa farin girki hakima Rukky, almost one hour tana jira amma babu alamarsa, ta shiga aikin da ta saba na kiransa da tura masa text message, ta ciro handkerchief ta fara share hawayen dake sauka idonta, ji tayi ance "A Nurse are you okay?", ta ɗago kanta sukay ido huɗu da Khaleel, tayi fake smile tace "Oh Dr am fine..", ya tsuke ido yace "are you sure?", tace "sure", ya kalli ƙofar office en Dr Uthman yace "but what are you doing here all alone?, aren't you suppose to be in nurse station?", ta sake yin wani fake murmushin tace "yeah, yanzu nake shirin tafiya can en", yace "ohk see you later.." da haka ya bar wajen ya barta zaune, ta dafe kanta a hankali tana tunanin what next, ga dukkan alamu dai wanda tazo Hospital en dominsa bazai zo ba, daman yau sai dare take da duty amma sbd shi ta ƙuma uban sammako, gashi kuma bai zo ba, tamkar wacca aka zarewa spine haka ta tashi ta bar bakin office en, wani irin nauyi zuciyarta tayi mata, haka ta sake saɓa ta fito daga asibitin, ta tsari napep zuwa gidan Kulsoom. ★Sosai Hajar ta ware, she really appreciate yadda mutanen gidan suke they were so humble and caring, duk abinda take buƙata an mata shi, lunch ma har ɗaki mai aiki ta kawo mata, ga Mami wacca take dubata akai akai, da daddare Hajar ta idar da sallahr magrib knn tana wrapping prayer mat Noor ta shigo, tace "Alhmdllh jiki yay sauqi, ai zaki iya fitowa ko?..", Hajar ta ajiye darduman kan stool ta girgiza kai a hankali, Noor ta jingina da jikin ƙofa tace "na shi gangaɗe...", da farko kamar Hajar ba zata tambaya ba sai kuma tace "me ya faru?", Noor ta shafa forehead dinta tace "wllh iron lady ce, nace mata kin samu lfy amma duk bayan minti talatin saita ce nazo naga ya kike, wai ƙafarta ke ciwo bazata iya tafiya sosai ba, ta hanani ma kallon stuff ena gashi i hate watching it on phone or computer, i prepare watching it on TV...", Hajar dai ba tace komai ba, Noor tace "dan Allah kizo muje ta ganki in yaso saiki dawo, Allah bazata barni na huta ba", Hajar dai tayi shiru ba ta san me za tace ba, ita kam bata son ma ta ɗara ko ina, kawai dai dagewa take tana so ta zama comfortable which was very hard on her, ta kalli expression en fuskar Noor wacca take kallonta da pleading eyes tana jiran amsa, da kyar ta iya cewa "tomm", Noor tayi clapping hands enta wanda hkan ya bada sound kaɗan tace "thank you, muje ko, tana ganin dai you are fine saiki dawo abinki, rigimar tsufa ne..." da haka ta buɗe ƙofa, Hajar ta gyara wuyan dogon hijab din da ta idar da sallah kafin tabi bayanta, ba kowa a huge palourn Mami, itama Mamin ta shiga bedroom enta daman idan ta shiga sallar magrib bata fitowa sai after isha'i, Hajar tayi surveying palourn da idanunta tana biye da Noor, Noor ta buɗe ƙofar fita daga part en kafin suka wuce long corridor suka fita main palour, nan ma dai saida Hajar tayi surveying ensa, wani nervousness ne ya rufe ta, ta fara tambayar kanta to wane ne wnn abokin na Baba ita dai bata sansa ba, tinda take bata taɓa ganin palour mai girma da ƙawatu kamarsa ba, ita bata tsaya ƙarewa gidan kallo ba jiya da aka kawota, ko lokacin sallah da agogon room enda take ciki take amfani cause bata gane dare da rana sbd komai na gidan equal yake, safe rana dare duk akwai wuta, Noor ta wuce hanyar da zai leading zuwa part en Hajiya, Hajar dai was following her like one living statue, buɗe ƙofan part en Hajiya Noor tayi da sallama, Hajiya dake zauna kan lallausan carpet ta miƙe ƙafafuwa ta kalli door tace "waye anan?", Noor ta matsa gefe Hajar ta shigo da sallama, Hajiya ta sake cewa "nace waye anan...", Noor ta tsugunna gabanta ta ɗauki glasses enta ta saka mata tace "da me yasa kika cire glasses dinki..?", Hajiya tace "yo idon ne yake min ƙaiƙaiyi shine na cire zan sosa, ban kai ga sosawar ba naga inuwa akaina", Noor ta dubi Hajar tace "ƙaraso mana", Hajar ta ƙarasa shiga cikin palourn ta zauna can ƙarshe carpet, Hajiya ta bita da ido, Hajar tace "ina yini..", Hajiya tace "wace ce wnn?", Noor tace "Au keda glasses din ma idon naki sai a slow, wacca fa kika takura naje na dubo miki ce fa", Hajiya tace "O oho matar Usuman din ce?", Noor tace "daman nace miki taji sauqi, toh gashi dai yanxu idonki ya gani", Hajiya tace "matso kusa mana ƴar nan saiki raɓe can ƙarshen buzu sai kace wata bare ba ƴar gida ba", Hajar ta matso a hankali ta shigo kan carpet en sosai ta sake tisa gaisuwar da tayi mata, Hajiya ta amsa tana dashare wawulon bakinta tace "tubarkallah masha Allah, yarinya ta saɓe jiki yayi kyau alhmdllh", Noor tace "ai na gaya miki", Hajiya tace "ita ta zaunar dani a gidan nan, yo inba larura ba mai zaisa na baro mijina na zo nan na zauna, hankalina ne yaƙi ya kwanta wllh tin jiya da naga yadda muka kaita asibiti, ace ana kawo mna yarinya sai kawai ta kwanta ciwo sai kace an kawota wajen mayu, kinga kwa gobe in Allah ya kaimu saina kira Umaru yazo ya ɗaukeni na koma gidan tsamiya..", Noor ta haɗe gira tace "nan ma ai gidan tsamiya ne", Hajiya tace "nan fa ɗaya, ba miji a gida ta ina ya zama gidan tsamiya", Noor ta miƙe tana kallon Hajar tace "bari nayi leading enki ki koma ko..?", Hajar ta gyaɗa kai, Hajiya tace "ta koma ina kuma, rabu da ita anan tayi zamanta tinda ba tace ta gaji ba, haka kurum ki ƙugata a ɗaki", Noor ta koma kan kujera two sitter ta zauna, remote ta janyo ta canza channel, tayi murmushi don yanxu ne ake taken next Cdrama da take so, ta fara cin coconut macaroons da ta ajiye nan tare da popcorn, Hajiya ta micincina idanu tana kallon Tvn tace "ji mutane sai kace aljanu, fuska kamar anyi ɓarin filawa, anya ma kwa akwai ji a jikinsu?", Noor dai an riga da an bada amanna ba ta ji ma sosai, a hankali Hajar dake wasa da laushin carpet ta ɗaga kai ta kalli TV, ko minti goma ba ai da fara film en ba ta ji ya ɗan birgeta sbd margic da ake zubawa, Hajiya sai mita take a mayar mata da makka, Noor kam tayi mata shiru tinda ita ta nace saita zauna a wajenta don haka sai ta gama kallonta kuwa, Hajiya ta saƙa hannunta ƙarƙashin kujerar da ta jingina da ita ta ciro kwalbar man zafi (Aboniki), ta buɗe kwalbar ta shiga lakuta tana laftawa a sangalale, tini Noor ta toshe hanci sbd har yaji ya bulale palourn, saida ta lafce ƙafufuwanta tasss da Aboniki, sai shining suke da sheƙi, can wajen yatsun ƙafar ne kawai bata shafawa ba sbd hannunta bazai kai ba kuma bata iya tankwashe ƙafar, ta lakuto wani lafcece kafin ta dubi Hajar da already idonta ya kawo ruwa sbd yaji tinda tafi kusa da ita tace "shafa min daga nan saman makyangyamar..", ba musu Hajar ta miƙa hannu Hajiya ta lakuce mata uban man Aboniki a tafin hannu, a hankali Hajar tayi rubbing dinsa a palm kafin ta fara shafesa a toes en Hajiya da suke a yamushe kuma a tattare sbd tsufa. juyowar da Noor za tay kenan taga Hajar na aikin da ita da Aysha ke gudu, Noor tayi murmushi ta kuma toshe hancinta ta cigaba da kallonta, door aka buɗe aka shigo, scent ensa ne ya mamaye palourn, yay sallama yana ƙarasa shigowa sai kuma ya tsaya cak, Hajar ta ɗauke hannunta daga legs en Hajiya gami da mayar dashi cikin hijab ta juya ta cigaba da kallonta, and that gives him the full access to saw her face completely, and he realized her, automatically ya juya ya fita a palourn tare da banging door......✍️ _Dear HAJAR fans, sai fa kun yiwa Feenerh feeche uxuri, a tsakani ga Allah wllh ni kadai nasan irin stressing kaina da nake wajen typing, 3 to 4 hours nake ɗauka kafin na gama one chapter banda editing, ku kuma a minti biyar zuwa goma kuke karanta shi. you know ni sabuwar writer ce speed en typing dina ba mai yawa bane, plxx be patient with me, insha Allah together we'll see the end of this book. my pleasure. ina yinku wujiga wujiga mutane na. 😍 🥰 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_ feeche {40..} Hajiya tabi ƙofar da Nurain yayi banging da kallo tace "ikon mai duka, cewa nayi fa zanyi magana da kai shine zaka zo ka nunamin wata fuskarka da na rasa dalilin sauyawarta ka fita", Hajar ta runtse idonta tana haɗiyar wani kwallo da ya tsaya mata a throat, ta wutsiyar ido ta gansa shine ta maze, gaba ɗaya taji ta tsani zaman nan en so take ta koma inda ta fito, a hankali ta miƙe tana jan fingers, Hajiya ta dena sababin da take ta ɗaga kai tana kallon Hajar tace "lafiya kika miƙe sai kace wacca aka zubawa mugun mintsili?..", Hajar tayi kasa da idonta tace "zanyi sallah ne..", Hajiya ta nuna mata qibla tace "buzun tsaftatacce ne, kiyi sallar ki", Hajar dai tayi shiru don ba haka taso ba, ita so take ta bar nan din kawai, Hajiya tayi kasaƙe tana kallonta ganin bata kalli qiblar ba kuma ba tada niyyar kabbara sallar da tace za tay, Hajiya ta dubi Noor tace "ƴar nan, kee", ina Noor sai blushing take tana tura coconut macaroons a baki, gaba ɗaya mind dinta na kan TV, Hajiya ta ɗauki trow pillow ta wurga mata, sai a snn Noor ta juyo tana wuri wuri da ido tace "mene ne iron lady?", Hajiya ta mata daƙuwa tace "wnn wane irin masifar kallo kike ne, nayi ta miki magana amma kin saki baki da hanci kin zubawa wasu ƙodaddu idanuwa a talabijin", Noor ta ajiye coconut macaroons da take ci tayi folding hands tace "Allah ya baki haƙuri, banji bane", Hajiya tayi tsaki tace "kinga ƴar nan matar Usuman tace zatay sallah nace tayi anan tinda buzun tsaftatacce ne amma taƙi yi, toh inajin dai tsaftarsa ba tay mata ba, ki tashi ki ɗakko mata wani acikin ɗaka sai ta ɗora akan wnn tayi sallar", Hajar tayi ƙasa da murya kanta a ƙasa tace "A'a zan koma can din ne sai nayi sallar a can", Noor ta tashi tace "alright muje na rakaki..", da haka Noor ta nufi door Hajar tabi bayanta walking slowly, Hajiya ta bisu da kallo tana taɓe baki tace "Au wnn aka aurawa Usuman, da gani bata son mutane, ta zauna a cikin mutane amma taƙi ta gwammace ta ƙursuma a ɗaki, Allah dai ya kyauta...". har sun kama hanyar part din Mami sai kuma Noor ta dakata, ta juyo tana ƙarewa main palourn kallo, taji scent dinsa amma kuma bata gansa ba, yana zaune a edge of executive two seater yana operating Mac phone, Noor ta buɗewa Hajar ƙofar shiga part en Mami tace "go ahead am coming", Hajar ta shige ciki, Noor ta koma main palourn ta isa kusa dashi ta tsaya daga gefen kujerar tace "Yaya ina yini?", ciki ciki ya amsa mata ba tare da ya kalleta ba kawai danne dannesa yake jikin Mac phone, tace "Yaya don Allah zan turo maka da project dina ka duba min kafin nayi submitting na gama..", sai a lokacin ya ɗaga kai ya kalleta kafin ya mayar da idonsa kan abinda yake yace "Ohk, Allah yasa ba shirme kike rubuta ba, don naga yanzu ba kya karatu sai kallon shirme kika iya, keep this in front of your mind idan shirme kika rubuta am going to punish you", ta sosa forehead dinta tace "shknn ma, yaya Farooq zan turawa ma kar nayi stressing dinka", yace "kafin 9pm naga mail dinki in my inbox Noory", ta gyaɗa kai a hankali tace "Sure Yaya" ta bar wajen ƙirjinta na bugawa, tasan dai bata rubuta shirme ba cause saida tayi research kafin ta rubuta komai, amma dai dole sai an mata gyara, ta shiga part en Mami, a tsaye ta tarar da Hajar a corridor ta jigina da bango, Hajar tayi saurin juyar da kanta gefe tana goge cheeks dinta, Noor taso ta fahimci cewa kuka take amma kuma demon en gabanta shine ya kwashe mata tunani, har ɗaki ta raka Hajar kafin ta fito, direct kuma room dinta ta wuce tayi plugging Lap top dinta a charge. Hajar ta idar da sallah, kwanciya tayi kan carpet ta lulluɓe da babban hijab din da tayi sallar, tara da rabi Mami ta shigo dubata, Mami ta dafa forehead dinta to feel her temperature, Hajar ta buɗe idonta don ba bacci take ba, tunani ne iri iri ya cunkushe mata a brain, Mami tace "ki dena kwanciya kan carpet ga bed nan, ko headache en ne?", Hajar ta tashi zaune tana girgiza kai tace "A'a ya dena ciwo", Mami tace "toh alhmdllh, ya baki ci abincin da aka kawo miki ba, ko ba kya son sa?", Hajar tace "na ƙoshi, naci da yamma", Mami tace "Okay, toh kisha drugs enki sai ki kwanta ko, if you need anything just let me know kinji", Hajar ta gyaɗa kai a hankali, Mami na fita Hajar ta shiga bathroom, tayi wanka ta fito ta saka kayan baccin da Noor ta bata, like yesterday night wnn ma ba tayi bacci ba, saidai wnn daren lafiyar ta lou kawai dai ta kasa rintsawa. ★Hajiya ce zaune bisa 3 sitter a great room din Abba, tayi shirinta tsaf da shigar asun da asun na atamfa, ga ɗaurin kallabi irin na tsofaffin nan mai santi, ta zubawa Abba dattijon idanunta da suka sha farin kwalli tace "Muntari nidai ban fahimci zaman Usuman a gidan nan ba, ya ɗauki matarsa su koma gidansu tinda ta warke sumul abinta, tinda dai waraka ta sauka to banga amfanin zama a nan ba, su koma gidan su kar aje a ƙuma musu sata, don wnn uwar dukiyar da aka laftawa gidan ɓarayi sai su shigar musu tinda banga alamar mai gadi ba, amma kuma dai naga wayar shokin zagaye da gidan, ɓarayi ba zasu iya shiga ba gsky..", Abba yace "insha Allah this week zasu koma..", Hajiya ta katsesa da fadin "toh mai zai hana yau su tattara su tafi, nifa yau zan rugungunta na tafi, kamata yayi ma mu fita gidan nan tare dasu, nasan yanzu ma Umaru yana kan hanyar zuwa ɗaukata", da taushin murya Abba yace "Hajiya ku dan sake zama mana zuwa wani lokaci ko sati fa ba kiyi ba..", Hajiya ta girgiza kai tace "A'a A'a Muntari kasan dai ni adala ce, shekarata biyu a gidan nan banje gidan Salisusu ba ina nan, shima saina jingine masa shekaru biyu kafin na juyo nan idan Allah ya ara min lokacin". knocking door akay kafin aka buɗe aka shigo, Mami ta shigo da sallama, ta sanar da Hajiya cewa breakfast dinta is ready, Hajiya tace a kawo mata abincin nan anan zata ci, Mami ta juya ta fita, babu jimawa ta dawo da tray a hannunta, tayi serving Hajiya creamy groundnut pap with yummy beans cake. Mami na gama serving dinta ta tashi zata fita, Hajiya ta ajiye cup en pap tace "Khadijah...", Mami ta juyo tace "Na'am Hajiya", Hajiya tace "naga jikin ƴar taki da sauƙi toh shine nace me zai hana yau su tattara su koma gidansu..", Mami tace "Eh Alhmdllh ta samu sauqi sosai, amma dai bata gama shan drugs dinta ba, da sai nan da sati mai zuwa sai a mayar da ita ɗakinta lokacin insha Allah ta gama shan drugs en, amma yadda kika ce ai haka za ai Hajiya", Hajiya ta rausayar da kai tana cin ƙosai tace "ai shknn tinda kin kawo batun magani, shima mijin naki haka yace sai sati mai zuwa da yake bakinku ɗaya". kwanan Hajar hudu a gidansu Nurain, tin ranar da suka je wajen Hajiya bata sake fita daga part en Mami ba, everytime tana ɗakin da aka ajiyeta, tana dai fita palourn Mami ta gaisheta sai kuma ta koma ɗaki, Sosai suka saba da Noor sbd tare suke kwana, da rana kuma ta zauna ita kadai idan Noor ta tafi schl, ƙarfe biyar da minti huɗu Noor ta shiga ɗakin da Hajar take, dawowarta daga schl knn, wanka kawai tayi ta canza kaya, Noor tayi murmushi tace "masha Allah, waoh gsky kayan nan sun miki kyau", Hajar ta dubi kanta, straight skirt ne na english wears da shirt dinsa masu kyau, Noor din ce ta kawo mata su tinda daman kayanta take sawa, duk yawancin kayan da ta bata ƙanana ne amma decent, don Noor ta fi son su sbd tafi zama comfortable dasu, Noor ta ringa yaba kyan Hajar da kayan, sun fi yiwa Hajar din ma kyau don ita data saka sau ɗaya basu mata kyan haka ba, Hajar tayi murmushi tace "an dawo schl lfy?", Noor tace "lfy alhmdllh, za kici Noodles?'', Hajar ta gyaɗa kai tace "Eh zan ci", daman kaɗan taci lunch da aka kawo mata, Noor tace "Ohk, let's prepare it together", Hajar tace "together?", Noor tace "yhap", ƙin yarda Hajar tayi wai ita bazata fita ba, daga ƙarshe ma tace ta ƙoshi, da kyar Noor tayi convincing dinta ta yarda, zumbulelan Hijab din da take sallah ta kirma, Noor ta bita da kallo tace "keda zaki kitchen meye kuma na saka hijab", Hajar tace "in ba dashi ba na fasa zuwa", tare suka fito main palour suka shiga huge luxury kitchen din gidan mai shegen kyau, kitchen island ma wani irin makeke, ga cupboards da drawers suma manya wanda suka zagaye girman kitchen din, Noor ta ɗakko pot kafin ta fara harhaɗo ingredients, Hajar daga gefe ta tsaya tana kallonta, within 15mins Noor ta gama dafa wata shaɗananniyar Noodles, ga fried egg with sausage, A babban plate ta juyo musu, Noor ta buɗe fridge ta ɗakko lemon kwali da ruwa ta bawa Hajar ta riƙe musu ita kuma ta ɗakko plate en Noodles en, a Main palour suka zauna wanda Hajar ba taso hakan ba, Still Hajar tayi tana kallon Noor ganin abinda ta ajiye musu a maimakon fork, Hajar ta ringa kallon tsinkayen tace "meye kuma wnn?", Noor ta ɗauki chopsticks din ta fara ci dashi, sosai ta iya amfani da Chopsticks, saida Noor taci loma uku amma Hajar ko attempting ɗaukar sticks en ma ba tay ba, Noor tace "ya naga ba kya ci?", Hajar ta ɗauki Chopsticks en gabanta ta fara ƙoƙarin ɗebo Noodles din, daga ta ɗiba sai ta zame, Noor ta ringa mata dariya kafin ta tashi ta shiga kitchen ta ɗakko mata fork, Hajar tace "tayi daɗi sosai", Noor tace "really, da fatan dai kin riƙe recipe din cause it's one of yaya Nurain's favorite", suna gama ci Hajar ta ɗauki plate din ta shiga kitchen dashi, Noor ta juya tana kallon stairs jin footsteps, tini ta ajiye cup din lemon da take sha ta tashi da sauri ta ruga ɗakinta, tsoron haɗuwarsu take sbd wata red cancel ya turo mata akan project dinta da ta tura masa hakan yana nufin shirme tayi kenan, gashi yace sai yayi punishing dinta idan shirme tayi, shiyasa take avoiding dinsa kar ya kamata, Nurain ya ƙarasa sakkowa downstairs yana kallon ƙofar part din Mami, kitchen ya nufa da cup din Coffee da ya gama sha, yana shirin murɗa handle kawai yaji an murɗa ta ciki kafin aka buɗe ƙofar, kanta a ƙasa tana tattare ƙasan hijab dinta da yake sharar floor, ji tay tayi karo da abu, ta ja baya da sauri ta ɗago kanta, girarsa a matuƙar haɗe yake kallonta, Hajar ta zuba masa lulu eyes dinta zuciyarta na bugawa, ita tsorata ma tayi shiyasa take masa wnn kallon, da sauri ta janye idonta tabi ta gefensa zata wuce tinda akwai space sosai da yake ƙofar babba ce, ( mu bawa juna haƙuri daii ) shine abinda ya amsa a brain din Nurain within 1sec, this time around din ma junan zasu bawa haƙuri ko kuma ita zata basa, hannu yasa ya fixgota baya ya mayar da ita kitchen din, yace "kee are you mad?, dutse kika bige ne?..", Hajar ta yamutsa fuska tace "wa ya sani ko dutsen ne".......✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {41..} Nurain was more than shocked jin abinda ta faɗa, wnn ƴar kucular yarinyar ce zata gaya masa haka, nawa take a wajensa, with hatred yake kallonta, itama Hajar da hatred din take kallonsa har wani zugii take ji a zuciyarta, da mugun sauri ta sake kewayesa zata wuce, hijab dinta ya taɗeta saura ƙiris ta baje a ƙasa tayi saurin dafa handle, a fusace Nurain ya juyo da nufi koya mata hankali, a ransa ya ji dama faɗuwar tayi ta dauje guiwa, Mami da ta fito daga part din Abba a daidai lokacin da Hajar ta taɗe snn kuma lokacin da Nurain ya juyo a fusace sai taga kamar Nurain din ne ya hankaɗota, Hajar da bata lura da presence din Mami a palour ba tayi sauri ta zagaya ta bayan kujeru ta shiga part din Mami, Mami ta bita da kallo kafin ta fara tafiya towards Nurain daya daskare a tsaye, tace "daman ka na gidan nan Nurain..?", don gaba ɗaya ya ƙauracewa part dinta, kwana biyar knn bai shiga part en ba, saidai ya gaisheta a main palour ko kuma part en Abba idan sun haɗu a can, Nurain yace "yeah, shirye shiryen kowama work nake so am busy in my room.." da haka ya shige kitchen, Mami ta bisa cikin kitchen din, ya ajiye cup din dake hannunsa a sink yana sauke ajiyar zuciya, Mami tace "i saw what you did Nurain", ya juyo ya zuba mata idanunsa da kana gani kasan ransa a ɓace yake ba tare da yace komai ba don bai fahimci me take nufi ba, tace "why did you pushed her..?", Nurain was confused don brain dinsa ma ta kasa basa hadin kai yayi thinking, bai ma san me zai ce ba sbd bai gane me take cewa ba, da kyar ya samu kansa da cewa "Mami i don't get you", sosai ran Mami ya fara ɓaci kawai ta juya tabar kitchen din. Hajar na shiga ɗakin da take ta kafa goshinta a bango tana jin suya a ƙahon zuciyarta, hawaye ne suka fara bin cheeks dinta kafin ta fashe da kuka gaba ɗaya, a haka Mami ta shigo ɗakin ta tarar da ita, har harɗewa ƙafafuwan Mami suke ta iso wajenta ta riƙe both shoulders dinta tana tambayarta me ya faru, Hajar ta girgiza kai alamar ba komai tana ƙoƙarin danne kukan, Mami da hankalin ta ya tashi sosai tace "talk to me my dear what happened..?", kawai girgiza kai Hajar take taƙi tace komai, gashi kuma ta kasa haɗiye kukan sbd zuciyarta a raunane take, da kyar Mami tayi consoling dinta duk da taƙi gaya mata damuwarta. Hajar ta shiga toilet ta wanke fuska ta fito, wani irin fige hijab ɗin jikinta tayi sbd ƙamshin Nurain da ta fahimci akwai ajiki, kodai hancinta ne ke jin hakan, tayi wurgi da hijab ɗin a tsakar ɗakin, ta juyar da kanta gefe tana kallon damtsenta inda ya rutsa ya fuzgota baya, cike da takaici tayi kwafa tace "Allah ya saka min da ka taɓa ni..." ★Maama ta saki tsintsiya da abin kwasar sharar da ta sharo uban dattin dakinta wanda ke ɗauke da mushen kuɗin cizo da aka zubawa piya piya daren jiya tana kallon ƙattin da suke shigowa da buhunhunan shinkafa, da catoon na spaghetti Macaroni da Indomie, ga kuma manya mayan jarkokin Mai biyu, Baba ne ya shigo yana nuna musu inda zasu ajiye kayan, har suka gama shigar da kayan ɗakin Baba Maama bata dena kallonsu ba, Nabilah ma dake zaune gaban murhu tana jefa ɗan wake sakin baki tay tana bin kayan abincin da ido, har kumfar ɗan waken da ta zuba a tukunya ta fara zuba bata sani ba, Baba ya sallami yaran da suka shigo da kayan kafin ya ja ƙofar ɗakin nasa ya saka mata kwaɗo, Maama ta washe yalayen haƙoranta tace "sannu da ƙoƙari mal, wnn irin uban kayan abinci haka, ai ma shekara muna ci wllh, Allah ya biya buƙatu ya bunƙasa hanyar nema, shine nace dama ba ɗakinka aka kai ba ga kitchen nan da ba a amfani dashi sai a ciro shirgin ciki a kai bola a zuba kayan abincin anan, kaga ba a ringa takura maka ba idan zamu ɗiba, wllh tllh dama a kitchen aka ajiye...", Baba dai kawai jinta yake, ta sake cewa "idan ka yarda yanzu sai na ci ɗammara na fara fiddo shirgin kitchen din, ina da ma piya piya saina feshe sa da shi gudun ƙananan ƙwari..", direct Baba yace "Ai ba namu bane garar Hajara ce", Maama ta zaro mici micin idanunta tamkar an kwantali ɗata tace "kam bala'i da masifa, me kake nufi mal, wai kanaso kace min wnn uban kayan Hajara za a kaiwa da sunan gara?", yace "Eh Rabii, kayan garar Hajara ne", Maama tayi wani murmushin takaici tace "wasa ma knn, nan da kake gani na ba karen hauka ne ya cijeni da zan zauna inaji ina gani a ɗebi kayan nan akaiwa Hajara ba, idan kai da matarka kun makance to ni garau nake, muna fama da yar Hausa Mai da yaji da tuwan dawa shine za a kwaso yar gwamnati da abincin kwali a kaiwa yar so ko, ni ban taɓa ganin inda ake haka ba wllh, ai wnn ƙarawa mai kuɗi ƙarfi ne, ce muku akay babu abinci a gidan nata ne, koda yake ashe baku je kunga gidan ƴan yankan kan ba..", Baba yace "sai kuma kiyi, gara dai sai an kai mata, babu ruwana da cewar masu kuɗi ne, mutuncin ƴata zan kare..", Maama ta fara fyace majina tana sharar kwalla don sosai maganar tayi mata ciwo tace "wllh Allah sai ya saka min nida ƴaƴana yadda ake mana cin kashi a gidan nan...", Baba ya haɗe rai yace "Da Hajara da su Maimuna duk ɗaya suke a wajena, idan kina ganin rashin adalci nake yi akan su to kwa kin yaudari kanki, dukka abinda na yiwa Hajara insha Allah irinsa zan maimaita idan Allah ya kawo lokacin auren su Maimuna" da haka ya barta a wajen ya matsa kusa da ɗakin Umma ya kirata, Umma ta amsa ta fito tace "gani mal", duk tana jin abinda ya faru daga ɗaki, Baba yace "Jamilah ce zata amso kayan zaƙin ko?", Umma tace "Eh, in Allah ya yarda ranar juma'a za a kawo", yace "yawwa gobe knn, zuwa ranar asabar ko lahadi sai a kai mata garar ta", Umma tace "toh Allah ya nuna mana da rai da lfy, Allah ya saka da alkhairy", yace "Ameen" ya fita daga gidan, Nabilah da take jefa ɗan wake ta ɗago kai ta dubi Maama tace "dan Allah Maama ki ringa ragawa Babanmu, nifa yanzu na zama ƴar ba ruwana wllh, idan ma bai mana irin na Hajara ba ai Allah na gani..", Maama ta rausayar da kai tace "idan bai muku ba ni zan muku da yardar Allah, kuma sai Allah ya kawo muku mazaje wanda suka kere dan yankan kan da waccar shegiyar ta aura, ai tin yanzu ma na fara gani tinda Alhaj ɗin Maimuna a Habuja yake, kinga kuwa ai yanada kuɗi". Umma na komawa ɗaki tayi dialing numbern Anty Jamilah, tana ɗagawa bayan sun gaisa Umma tace "Jamilah ya maganar mai dubulan da alkakin nan ne..?, da ƙarfe nawa zata bayar goben..?", Anty Jamilah tace "da safe tace wajen ƙarfe goma", Umma tace "tom, ga su shinkafa da taliyar har an kawo, kin san mal da karfin hali tinda yaji cewa ba a jerawa Hajara kayan ɗaki ba ya dage akan sai an mata gara, yace bazai bari mutumcin ƴarsa ya zube ba ace ba a kaita da ko tsinke ba, kuɗin kayan ɗakinta da aka siyar dasu yayi amfani wajen siyayyar garar snn kuma yace ragowar nata ne", Anty Jamilah tace "Alhmdllh, Allah ya saka da alkhairy, ai hakan shine dai dai wllh", Umma tace "wai ya ƴar taki kuwa? ni kam bana samun wayarta...", Anty Jamilah tace "nima haka Adda, ashe ma tana gidan su mijin, da naji bana samunta a waya shine na kira numbern wacca nake zaton kwanwar mother in law dinta ce wacca na amsa a wajenki ranar da muka dubota a hospital, shine fa take gayamin cewa ai Hajar na gidan surkanta", Umma tace "tofa ashe haka akay", daga haka sukay sallama. ★Da daddare da misalin tara da rabi, da ɗan sauri Nurain yake sakkowa daga stairs ya zura right hand dinsa a pocket na dark brown sweat pant dake jikinsa, left hand din kuma yana shafa tsakiyar cikakkiyar sumar kansa, hanyar part din Abba ya nufa, ya murɗa door handle na great room din kafin ya shiga da sallama, ya cire soft room slippers dinsa ya ƙarasa ciki, har zai zauna kan carpet Abba ya nuna masa sofa don haka ya zauna a sofar, Mami ta gama zubawa Abba Moringa tea ta miƙa masa, ya amsa yana murmushi yace "thank you..", tace "ur welcome dear..", Mami ta ɗago sukay ido huɗu da Nurain, ɗauke kanta tayi ta tashi ta shiga bedroom din Abba, Abba ya ɗauki tean yayi sipping, sip uku yayi snn ya ajiye Mug din, ya rage volume din TV, Abba ya dubi Nurain da yake jiran kiran da ake masa yace "ya project din Mamana tace ta turo maka zaka duba mata...?", Nurain yace "Yeah she try", Abba ya gyaɗa kai yace "good", after like 5secs Abba ya nisa yace "Uthmaan kasan me yasa na kiraka nan..?", Nurain dai kawai kallon Abba yake ya girgiza kai yace "A'a..", Abba yace "lokacin da Allah ya yiwa first wife dina rasuwa the mother of Sakeena, Sakeena was just 3months old lokacin da mamanta ta rasu, duk wanda yaga Sakeena sai yaji tausayinta sosai, dangin mahaifiyarta sun so su amsheta su riƙeta ni kuma nace bazan basu ba sbd tana ɗebemin kewar mahaifiyarta, a koda yaushe Sakeena na wajena sai idan zan fita aiki ne nake kaita wajen Hajiya idan na taso kuma na ɗakkota mu koma gida, Hajiya tayi min mgna akan na ƙara aure amma ni kuma sam aure ya fita a raina, a haka har Sakeena ta cika wata bakwai a lokacin ne kuma na tafi Abuja wani aiki", Abba yayi murmushin manya snn ya cigaba da magana yace "ai sai dawowa nayi daga Abuja na tarar da gidana a buɗe an kawo min mata, aikin Hajiya ne, itace ta shiga ta fita ta haɗa aurena da Maminku tinda ƴar Aminiyarta ce, Hajiya tayi kicin kicin ta ɗaure fuska da ta ganni kawai warkajaminta take, ban kai ga mata magana ba tace min ai Uwa ta yiwa Sakeena, ai kam dai Hajiya gave Sakeena the best Mother ever domin kuwa hannu bibbiyu Mami ta riƙeta tamkar ƴar cikinta, ni kuma Allah ya musanya min ita da Marigayiyar mata ta, sosai na samu peace of mind wllh, your Mother is a good woman..", Abba ya dakata yana sauke ajiyar zuciya yace "kaga biyayyar da nayi ma Hajiya a tashar da ta ajiyeni, nine na kasance a farin ciki da kwanciyar hankali, don good wife ita ke riƙon gida ba kuɗi da kyale kyale ba, kasan me yasa na baka brief storyn nan??", Nurain yace "No Father", Abba yace "sbd kaima ka shiga irin halin da na shiga Son, saidai nawa da naka akwai bambancin amma kuma suna kamanceceniya, hankalinka da nutsuwarka da sanin kai din waye da kuma iko yasa na aura maka yarinyar nan", nan Abba ya shiga labarta masa yadda komai ya wanzu har ya aura masa Hajar, Abba yayi sipping tea yace "ina da babban hope akanka Son shiyasa na tafi kai tsaye na amso maka auren yarinyar nan, amma look at what happened you are trying to do something da ban taɓa tsammani ba, Uthmaan wllh da nasan za kace sakin yarinyar nan za kai bazan aura maka ita ba, wai ni nan gata na gwada maka snn kuma na haɗa da taimako, ranar nan da Hajiya tace a bar maganar saki kawai shiru nayi sbd bana so ranta ya ɓaci , amma yanxu mu ɗora daga inda muka tsaya Uthman, ka amince zaka zauna da yarinyar ko kuma kana kan bakarka na sakinta...?", Nurain ya ɗago kansa yana kallon Abba ya kasa cewa komai, ya shafa kansa har yanzu baice komai ba, Abba ya ƙura masa ido yana jiran amsa, Nurain ya kalli fuskar Abba kafin ya runtse idonsa ya buɗesu, a lokaci ƙanƙani suka rune, da kyar ya motsa peach lips dinsa maganar ma bata fita sosai yace "Abba na amince zan zauna da ita..", Abba yayi ajiyar zuciya yace "Allah yayi maka albarka, zaka iya aurar wacca kake so a ko wani lokaci, zaka girbi iri mai kyau for your obedient", Nurain dai ya dena fahimta sakamako tsittsinkewar da zuciyarsa take, Abba yace "toh yaushe zaka ɗauki matarka ku koma gida...?", Nurain da throat dinsa ya bushe yace "i think on Saturday insha Allah...", Abba yace "jibi knn?", Nurain yace "Yeah", Abba ya gyaɗa kai ya cigaba da sipping tea, Nurain ya miƙe yana jan farar T-shirt dake jikinsa yace "can i excuse myself", Abba yace "sure", Nurain ya masa saida safe ya nufi ƙofa, room slippers dinsa ya zura zai fita Abba yace "gobe in Allah ya kaimu zamu fita bayan sallar Juma'a", Nurain yace "Ohk" da haka ya buɗe ƙofar ya fita Abba ya bisa da kallo, Mami ta fito daga bedroom din Abba ta zauna side dinsa ta dafa hannunsa tace "hakan ai yafi gwara musan road din da zasu bi kafin abu ya tabarbare...", yace "haka ne, All thanks to you Mami". ★Washe gari da ta kasance juma'a, ƙarfe sha biyu Nurain ya fito huge compound din gidansu ya isa parking spaces, ya buɗe motarsa da ya fita da ita jiya da yamma ya shiga, wayarsa dake kan dashboard ya ƙurawa ido, gaba ɗaya ya dena amfani da ita saidai yayi using Mac phone, haka yake baya son takura, ya kwantar da hand brake ya tada motar, after warming for few minutes yaja motar ya fita daga gidan, tunani iri iri ke kawowa brain dinsa amma sai ya kawar dasu ta hanyar bin karatun Alkur'ani dake tashi a motar, wayarsa ce ta fara ringing, da kamar bazai ɗauka ba sai kuma yabi gefen titi ya ɗauki wayar ya duba wake kiransa, Farooq ne, Nurain ya saka wayar a handsfree ya cigaba da driving slowly, complain Farooq ya fara masa akan baya ɗaga wayarsa, Nurain yace "Hey punk nafa gaya maka ka dena kira idan zaka ajiye mail da yafi maka", Farooq yace "i won't, kira naga dama", Nurain ya ɗaga kafaɗa yace "Alright..", Farooq yace "ni idan ba ma iron lady da ta takura na kiraka ba me zaisa na kira unavailable person", Nurain yayi murmushi yace "kai har kayi mgana anan punk..", Farooq yace "are you coming daman iron lady ce take son ganinka..?", a hankali Nurain yace "yeah, idan na dawo daga mosque zan shigo", Farooq yace "fine" da hka ya katse wayarsa, saida Nurain yaje masallacin da ya saba zuwa sallar Juma'a snn ya wuce gidansu Farooq, suka gaisa da Ummi kafin ya wuce part din Hajiya, bai jima da zama ba saiga drink da ruwa Aysha ta shigo masa dasu harda abinci, Aysha ta tashi zata fita Hajiya tace "tin ɗazu nake fama dake Shatu akan ki shafamin man zafi a saman makyangyama amma kinyi burus dani, jifa yadda ƙafafuwan suka sussuntuma sai kace an buga musu iska, da kyar na iya yin sallah fa", Aysha tayi fuskar mage tace "iron lady, ina zuwa yanzu zan dawo, kinga abinci nake kawowa yaya ai bai kamata na taɓa man zafi ba", Hajiya ta ɗaga kai sama tana kallon Nurain ta ƙasan glasses tace "ke da Allah rabu dashi kizo ki shafamin mai na, yo ina ruwanki dashi shi da yake da aure, zukumin cikinsa na wajen matarsa, kai matar Usuman yar aljanna ce yarinyar nan, wllh ta iya shafa man zafi, tinda nake ba a taɓa shafamin wanda naji daɗinsa kamar nata ba, ni idan ma naga ina ƙoƙarin rasa ƙafafuwan babu abinda zai hanani tarewa gidan Usuman..", Nurain dai kawai latsa wayarsa yake like he was not existed there, sai a lokacin yace "toh taso mu tafi", Hajiya tace "mu tafi ina kuma, ai cewa nayi sai naga ina ƙoƙarin rasa ƙafafuwan...", Nurain ya miƙe tsaye yana kallon hajiya yace "na tafi, idan Farooq ya dawo masallaci kuce masa na tafi", Aysha tace "Yaya what about the food", ko amsa bai bata ba ya nufi door, Hajiya kam kasa magana tai sbd abinda ma ta kirasa ta gaya masa bata kai ga fada ba, da sauri Nurain ya shiga motarsa ya bar gidan, shaf ya manta cewa Abba yace zasu fita yau, hold off ne ya riƙesa a wani round about, almost 20mins hold off din bai ware ba, Nurain ya daki steering motar murya ƙasan throat yace "damn it", kiran Abba ne ya shigo wayarsa, yayi picking, Abba ya tambayesa whereabouts dinsa, yace hold off ne ya tsaresa bayan ya fito daga masallaci, Abba yace "Okay, ni na riga na wuca ma amma zan turo maka inda zaka sameni sai ka tafi can din", Nurain yace "Aha". Nurain ya buɗe google map a wayarsa yana bin direction din da zai kaisa unguwar da Abba ke jiransa bayan ya samu ya fito daga hold off din, ya ringa kallon screen ɗin wayar ganin inda arrorn map din ke masa pointing, ya ɗago kansa yana kallon street din a zahiri wanda ya karya kwanarsa yanxu, street din ba baƙonsa bane kuma zamm ya ganesa tinda ya ajiye memory a nan din, Slowly yake driving a street din sbd ruɓewar kwalta da kuma shagiɗaɗɗun jakin baban gida, opposite inda Incidence din memoryn sa ya faru yaga motar Abba, drivern Abba ya fito yana ɗaga masa hannu, Nurain ya samu gefe yayi parking motar ya buɗe ya fito, koda ya fito sai ya tsaya yana kallon daidai wajen da motarsa ta taɓa ruftawa, anan ne kuma first encounter dinsa da mara kunyar yarinyar nan wacca a yanxu ta amsa sunan matarsa....✍️ As promised, ga Hajar nan na muku.. 🤙🤙 share as widely as possible, more likes and comments don na samu kwarin guiwar yi muku update tomorrow 🤗 🌝.... Masu tambayar novel din HAJAR complete ina muku Albishir akwai a arewa book tin daga farko, just search @feenerhfeeche02 and follow my profile. daga nayi update zaku ringa samu 🤗 💛 HAJAR 💛 by Feenerh_feeche {42..} Tsallaka titin Nurain yayi ya isa wajen Motar Abba, driver ya buɗewa Abba motar ya fito, Abba ya ringa kallon Nurain da ya ƙurawa street din ido yace "wajen mahaifin Hajar na kawoka ka gaishesa, ya kamata ya sanka..", Nurain ya kare hasken rana da yake haske masa ido yana tunanin wace ce kuma Hajar, sunan ya ringa yawo a brain dinsa amma ya kasa gane wace, ganin bai fahimta ba Abba yace "your wife, ko baka san sunanta ba..?", Calmly Nurain yace "Ohk, amm nan ne unguwar...?", Abba yace "yess, ga layin gidan can" ya nuna kwarɓaɓɓen lungun gidansu Hajar, with disgusting look Nurain ya kalli layin, how mutane suka rayuwa a nan wajen, Abba ya ciro wayarsa daga pocket yayi making call na minti biyu, yana gama wayar yace "muje" da haka ya fara tafiya ya shiga layin, Nurain yabi bayansa, Nurain dai kawai bin Abba yake suna surƙumawa cikin lungun, wani irin nisa yaga tafiyar ta masa duk da cewa gidan bashi da nisa da titi, Abba ya tsaya a daidai ƙofar gidan, Baba da already yana soro ya fito waje sukay musabaha da Abba, Baba yace "Bismillah", Abba ya bisa suka shiga soron gidan ya zauna kan tabarma da ke shimfiɗe a soron, saida Nurain ya rage tsaho snn ya shiga, ya zauna daga gefe yana kallon Baba yace "barka da rana", da fara'a Baba ya amsa, Abba yayi murmushi yace "he is my second born Uthman, dashi aka ɗaura auren...", Baba yayi ajiyar zuciya yana kallon Nurain yace "masha Allah..", Nurain ya ɗaga kansa yana kallon roof din soron wanda spider web ta cikasa har tana zazzagowa, Abba da Baba sai taɗinsu suke, past dinsu suke tunawa suna mgana akai, after 5mins Nurain ya duba agogon wrist dinsa, Abba ya dubesa ta gefen ido kafin yace "Nurain you can go idan Kanada wani appointment din", cike da girmamawa Nurain ya yiwa Baba sallama kafin ya tashi ya bar soron, Nurain na fita daga lungun ya ciro handkerchief ya goge fuskarsa, titi ya tsallaka ya shiga motarsa, zaune yayi cikin motar bayan ya kunna ya ware Ac, So a nan Abba ya masa aure, Ghetto area, shi ba wnn ne damuwarsa ba ma, bayan ƴar Ghetto da aka aura masa kuma mara manners, da reverse ya fita daga street din, yana hawa main road ya take accelerator, hanyar gidansa ya ɗiba, few minutes ya isa unguwar duk da cewa akwai nisa cause ya take motar ba ƙarya, a ƙofar gida yayi parking ya fito, Garba dake tsaye bakin gate tare da wani mutumi ya taso yana yiwa Nurain barka da zuwa, Nurain ya amsa yana kallon mutumin dake tare da Garba, Garba ya dubi mutumin yace "ga uban gidan nawa fa..", da sauri mutumin ya russuna yace "barka da zuwa Alhj..", Nurain yace "an yini lfy...?", mutumin yace "lfy alhmdllh an gode Allah...", Nurain na kallon Garba yace "shine ko?", Garba ya shafa kai yana ɗan russunawa yace "Eh alhj ƙarami, shine wllh, ɗan uwa na ne na jini, da Babansa da mahaifina uwarsu ɗaya ubansu ɗaya..", Nurain ya jinjina kai yace "Ohk, hakan yayi" da haka ya ƙarasa bakin gate din ya buɗe, ya koma cikin motar Garba ya zuge masa gate ya shigar da ita huge parking space dake gidan nasa, saida Garba ya bari mutumin da suke tare ya shigo snn ya mayar da gate din ya rufe, Nurain ya fito daga mota bayan ya gama parking, ya ringa kallon compound din, kiran Garba yayi wanda ya taho da sauri, Nurain yace "ka gaya masa aikinsa ko?", Garba yace "Eh na gaya masa komai, gadi da bar ruwan shuka sai share tsakar gida", Nurain yace "Yawwa, kira min shi", Garba ya tafi ya kira mutumin suka taho tare, Nurain yace "Garba ya maka bayani ai", mutumin kansa a ƙasa yace "Eh alhj..", Nurain yace "yawwa, bar ruwan shuka da share tsakar gida na wani lokacin ne kafin a samu me yi naka dai shine gadi", mutumin yace "insha Allah komai bazai gagara ba..", Nurain ya gyaɗa kai yace "suna fa..?", mutumin yace "Inuwa..", Nurain ya jinjina kai kafin ya wuce ya bar wajen ya nufi main entrance din shiga gidan. Garba ya dashe haƙora yace "Allah kuwa Inuwa ka kwashi dami a akala don wllh tllh kirki dai a wajen bawan Allahn nan har ya masa yawa, ni dai na gaya maka ka zama mai gsky da amana, idan ka riƙesa da kyau tabbas zaka samu alkhairy bana wasa ba, wllh don ma dai kai ne amma in ba haka ba wani huhulahun zan nemawa wnn gangariyar aiki...", Inuwa yayi murmushi har cikin ransa yaji daɗi yace "ai Allah ne zai biyaka Garbati da wnn taimako da ka min", Garba yace "wnn fa aikin nawa ne na sadaukar maka..", Inuwa yace "ai shiyasa nake ta gode maka...", bayan minti sha biyu Nurain ya fito bayan ya rufe ko ina, keys guda biyu ya bawa Inuwa yace "key din ɗakinka ne da kuma gate, gobe da safe saika zo kayi abinda za kai ka buɗe ɗakinka, amma yau dai ka tsaya tare da Garba", hannu biyu Inuwa yasa ya amshi keys din, Garba ne ya masa nuni da ɗakin nasa wanda ke kusa da gate, Nurain ya ciro kuɗi daga pocket ya bawa Garba yace "saiku koma can gidan..", godiya Garba yayi masa sosai. sai bayan Sallahr la'asar wajen ƙarfe biyar snn Nurain ya koma gida, don sai yau ne ya samu yaje wuraren da yake son zuwa tin dawowarsa 9ja. ★Hajar ta saka Hijab dinta tabi bayan Noor data isar mata da saƙon kiran da Mami ke mata, Mami na zaune palourn ta tare da Tailor wacca ta saba musu ɗinki, Noor ta koma inda ta tashi ta cigaba da latsa wayarta, Hajar ta zauna kan carpet tace "gani", Mami ta dubi Tailorn tace "ga mai kayan nan", Tailorn tace "Okay tom bari na aunata..", bai ɗauketa wani lokaci ba ta gama auna Hajar tass, Mami tace "gobe fa nake son kayan nan Salmah", Salmah tayi murmushi tace "Mami kar kiji komai insha Allah gobe sha biyu na rana a gidan nan zata yiwa kayan nan..", Mami tace "toh Allah yasa", Salmah ta yafa mayafin Abayarta, ta ɗauki wata Babban leda dake kusa da ita tace "toh Mami na wuce, Noor sai anjima..", Noor ta ɗago kanta daga kallon waya tace "da wuri haka...", Salmah tace "gwara na tafi yanzu na fara aiki, bana so naƙi cikawa Mami alƙawari", Mami tace "dan kwa faɗa zanyi wllh idan kayan nan basu samu gobe da wuri ba", Salmah tace "insha Allah baza aji kanmu ba Mami.." da haka ta musu sallama ta tafi, Hajar bata koma ɗaki ba tayi zamanta anan, buɗe ƙofa akay Nurain ya shigo, hannunsa riƙe da handle ya ƙarewa ɗakin kallo, har yayi wanka ya canza kayan jikinsa daga manya zuwa ƙanana da yke zaman gida dasu, wani irin zaro ido Noor tayi ganinsa unexpected, da sauri ta kara wayarta a kunne ta fara wayar ƙarya, ta tashi zata shige bedroom din Mami, ƙarasa shigowa palourn yayi yace "idan kika shiga har nan zan biyoki na zaneki", Noor ta yarfe hannunta tace "yaya ka tsaya kaji don Allah...", yatsansa ya ɗora a lips yace "shhhh na tambayeki ne...?" ya samu Sofa ya zauna, yana zama Hajar ta miƙe ta nufi hayar ɗakin da take, Mami ta kirata tace "ina zaki...?", Hajar ta juyo a hankali tace "ciki zan koma..", Mami tace "dawo ki zauna nifa na kiraki kuma bance ki tafi ba..", ba yadda Hajar ta iya haka ta dawo ta zauna, koda wasa bata dubi position din da Nurain yake ba, shima tinda ya kalli inda tke sau ɗaya bai sake kallon wajen ba, Nurain ya dubi Noor da tay tsaye sai wurwurga idanu take, murya ƙasan maƙoshi yace "je ki kawomin abinci, surely we will meet later..", a ɗarare Noor tace "tom", har ta kai bakin ƙofa Mami ta kirata, ta dawo da baya tana kallon Mami, Mami tace "je ki kunna burners ki zuba turaren wuta..", Noor ta dubi Nurain kafin tace "tom" ta dawo ta shiga bedroom din Mami, Mami ta kalli Hajar da ta zubawa Tv ido, kawai Tv take kallo duk da ba wani abun arziƙi ake haskawa ba amma ta gwammace ta kalli Tv sbd kar idonta yaje inda zuciyarta zata sosu, Mami tace "Hajar..", Hajar ta kalli Mami tace "Na'am", Mami tace "tashi kije kitchen za kiga wasu silver warmers guda uku akan cabinet ki ɗakko min su, idan kin kawo sai ki koma ki ɗakko min ruwa da drink a fridge", Hajar tace "tom" ta tashi ta fita daga palourn, Nurain yayi kamar baiji me Mami ta faɗa ba ya fara duba Mac phone, Mami dake kallonsa tace "misplacing phone dinka kayi ne..?", yace "A'a, a ɗaki na barta", Mami tace "alright then", Hajar ta shigo da tray a hannunta mai ɗauke da warmers, ta ajiye nan kan carpet kafin ta juya ta sake fita, babu jiwa ta dawo da wani tray din na ruwa da lemo da Cup da kuma plate with spoon, ta ajiye kusa da warmers din, a hankali tace "zan koma ciki", ba ta bari ta kalli Mami ba ta faɗi hakan, Mami tace "toh", Hajar ta tafi a hankali tana zuwa ƙofar ɗakin ta buɗe ta shige da sauri har dasu tuntuɓe, jingina tay da jikin ƙofar ta lumshe idanunta. Ganin har wajen minti talatin da ajiye masa abincin amma bai taɓa ba yasa Mami tace "Nurain ba Abincin zaka ci ba kasa aka kawo maka..?", ya ajiye Mac phone din a gefensa yace "A'a ni ba ci zanyi ba, i thought ke zaki ci ma", da mamaki Mami ta ringa kallonsa, after looking at him for few seconds tace "zuba abinci kaci malam", ya shafa kansa yace "nifa am full bance zanci ba", Mami ta haɗe gira tace "nace ka zuba abinci", bai sake mata musu ba ya ɗebi abincin kaɗan wanda bai wuce loma biyar ba, duk da irin yunwar da yake ji amma samm yaji baya sha'awar abincin, gaba ɗaya ya fitar masa a raii, ya ringa juya spoon ɗin hannunsa, Mami dai ta ringa kallonsa ta gefen ido har ya gama caccakar abincin wanda ko kusa da baki be kai ba ya ajiye, ruwa da lemon ma bai sha ba haka ya tashi ya fita, Mami ta bisa da kallo, girgiza kai tayi a ranta tana addu'ar Allah yasa dai wnn abu mai ɗorewa ne kar ya zama fitina. washe gari wani irin odd Hajar ta ringa jin kanta, tinda aka kawota gidan yau ne ta wayi gari taji hakan, ita ba mai rashin lfy ba kuma bazata kira kanta da mai lfy kai tsaye ba, breakfast da aka kawo mata ma kaɗan taci, Noor ma saida ta tambayeta lafiyar ta kuwa sbd sauyin nata, Hajar tace "bacci ne bai isheni ba inajin", Noor tace "toh ki koma ki kwanta kawai..", Kwanciyar da Hajar tayi sam bata samu bacci ko na 1sec ba, kawai juye juye ta ringa yi sai kace ƙadondoniya, wajen ɗaya saura ta tashi ta shiga bathroom ta ɗora alwala ta fito, bayan ta idar da sallah ta sake kwanciya, kamar wasa sai bacci ya ɗauketa, ba ita ta farka ba sai daf da sallahr la'asar, Noor ce ta shigo ganin ta farka ta fita a ɗakin, babu jimawa sai gata ta dawo tare da Mami, Noor ta ajiye kayan da suke hannunta a gefen bed kafin ta juya ta fita, Mami tace "har kin tashi dear..?", Hajar ta gyaɗa, Mami tace "Sallah za kiyi ne..", Hajar tace "Eh", Mami tace "idan kinyi Sallahr sai kiyi wanka ki saka waɗan nan kayan kinji", Hajar tayi shiru tana kallon kayan dake gefen gado kafin ta gyaɗa kai tace "tom", saida tayi sallah taci Lunch da Noor ta kawo mata snn ta shiga wanka kamar yadda Mami tace tayi, ta fito ɗaure da towel ta zumbula hijab, mai ta shafa kafin ta dawo gefen gadon ta zauna ta fara warware gogaggun kayan, wani sassanyan ƙamshi ne yake tashi daga jikinsu, Atampa ce mai laushin gaske kai kana ganinta kasan mai tsada ce, Hajar ta ringa shafa kayan kafin dai ta warware ta saka a jikinta, sosai sukay mata kyau dass dass, riga da skirt sosai yake fito da ainahin shafe dinta, ɗan kwali da mayafi sai pendant necklace da ear rings ne kawai bata saka ba, da sauri ta fara ƙoƙarin rufe kanta ganin Mami ta shigo, ɗan kwalin ta yafa a kanta ta rufe gashinta, Mami ta zauna gefen gadon itama ta riƙo hannunta tace "Yau kuma sai gidanki insha Allah", wani darammm Hajar taji a ƙirjinta, Mami tace "Allah yayi miki albarka tare da zaman lafiya madauwami, maza ki ƙarasa shiriyawa...", hawayen da suka cika idanunta suka fara zarya bisa kuncinta wanda bata shiryawa hakan ba, Mami that was very surprised da ganin tears ɗinta tace "what happened Hajar...?, akwai abinda yake damunki..?", Hajar tasa bayan hannu ta goge hawayen ta girgiza kai a hankali tace "A'a, kawai dai ni bansan waye wanda aka aura min ba, ni dai nasan Baba na yace yamin aure amma ban san waye ya aura min ba..", ta fara kuka a hankali, Mami tayi ajiyar zuciya ta tausasa murya tace "dear he is my son wanda aka aura miki, yayan Noor ai kin ganesa ko", Hajar na kallon Mami da jajayen eyes ɗinta ta gyaɗa kai, knn dai shi ɗin ne ko, Mami tace "Stop crying kinji, he will not harm you i promise..", Hajar dai ta rasa a wani position zata ajiye zuciyarta don ji take tamkar an tsireta da tsinken tsire ana gasawa a tukuba, Noor ce ta shigo, ganin yadda idanun Hajar suka kumbura tace "subhanallah kuka kike..", Mami ta tashi tace "she is not, gyara mata fuskarta ina zuwa" da haka ta buɗe ƙofa ta fita, Noor ta saka mata ear rings da necklace snn ta mata ɗauri mai kyau, saida ta ɗauki kwalbar turare dake kan mirror ta sake baƙaƙa mata ajiki duk da irin ƙamshin da kayan suke, biyar da ƴan mintina Hajar na zaune main palourn tare da Noor, Mami ta fito daga part din Abba ta kama hannun Hajar suka shiga part din, 5minutes da shigarsu suka fito bayan Hajar ta gaida Abba, don daman bai taɓa ganinta ba sai yau. Mami na kallon Noor dake zaune main palour tace "Nurain din bai fito ba har yanzu..?", Noor tace "Eh bai sakko ba", Mami ta kalli stairs kafin ta wuce ta fara hawa, knocking door ɗin ɗakinsa tayi, ya buɗe ƙofar yana kallonta, tace "baka gama bane..?", yace "yanzu zan sauko" da haka ya mayar da ƙofarsa ya rufe, yayi ajiyar zuciya, ya ƙarasa buttoning rigarsa ya saka links, shi kaɗai yasan abinda yake ji a zuciyarsa kawai jurewa yake, down stairs ya sauka bayan ya kulle ɗakin nasa, part din Abba ya shiga ya masa sallama, ya yiwa Mami ma dake zaune main palour daga haka ya fita compound, packing space ya isa ga buɗe motarsa ya shiga, Noor riƙe da tagomishin kayan arziƙin da Mami ta haɗawa Hajar na turaruka ta fita compound, Noor ta saka turarukan a back seat, ta dawo ta riƙe hannun Hajar zuwa wajen motar, front seat ta buɗe mata, a hankali Hajar ta shiga motar, Noor tace "sai nazo sister" da haka ta rufe motar taja baya, Nurain ya ƙurawa steering ido bai bari ya kalli inda take ba, saida ya gama warming motar snn ya fara driving a hankali ya fita daga gidan, tinda suka hau babban titi Hajar ta juyar da kanta side glass din ƙofa kawai kallon waje take, sanyin Ac ya ringa shigarta ga kuma abinda yafi tsaya mata a maƙogoro scent dinsa, ita dai bata san ma ina suka bi ba kawai gani tai sun tsaya a bakin gate ɗin wani katafaren gida, Nurain ya danna horn, mai gadi ya buɗe gate da sauri, Nurain ya parker motar a parking space kafin ya kashe ya zare key daga Ignition, buɗe murfin motar yayi ya fita, a hankali Hajar ta buɗe motar ta fito, ya buɗe back seat ya ciro ledar da Noor ta ajiye ya rufe motarsa, dire ledar yayi nan bakin motar yayi wucewarsa ciki, a karo na farko data ɗaga kai ta kallesa, ta taɓe baki ta sunkuya ta ɗauki ledar tayi hanyar da ta ga yabi, tsaye tayi bayan ta shiga palour, ta ajiye ledar hannunta, ta ƙarewa palourn kallo tass, direct Nurain upstairs ya haura ya shiga ɗakinsa bayan ya kunna Solar, trolleyn kayansa tin wacca ya kawo last week ya buɗe, arranging kayan ciki ya fara yi awajen da yake so, duk yawanci ma kayan aikinsa ne aciki ba sutura ba don on Monday yake da shirin rusuming work, yana gama arranging kayan yaji ana kiran sallah, huge bathroom dinsa ya shiga yayo alwala, da sauri ya gama ya fito, fita yayi ya sauka down stairs, Hajar na rakuɓe daga bayan kujera har ta gaji da tsayuwa ta samu guri ta zauna, kallo ɗaya yayi mata ya fita zuwa masallaci wanda akwai tazara kaɗan tsakaninsa da gidan, Hajar ta miƙe tsaye tana tunanin ina ne alqibla don da alwalarta sallah kawai za tay, kallon stairs tai wani tunani yazo mata, bayan ta gane gabas tayi sallar ta, har sallar isha'i Nurain yayi kafin ya dawo gida wajen takwas da ƴan mintina, muƙullin motarsa ya ɗauka ya fita, eatery ya fita ya siyo abinci ya dawo, wai yau shine da siyar abinci a waje, abinda bai taɓa sha'awa ba knn, kan Centre table ya ajiye ledojin da ya shigo dasu kafin ya haura sama, Hajar da bacci ya fara kwasarta ba tama san ya shigo ba, Sha ɗaya da rabi ya sakko with Pajamas mai sweat pant, ledojin dake kan Centre table ya ɗauka ya bar guda ɗaya, har ya fara hawa stairs sai kuma ya dawo baya, tsayawa yayi yana kallonta, jingine take da kujera bacci yayi awan gaba da ita, maganar Abba ce tayi hitting brain dinsa, kallonta ma da yake wani maƙaƙi ya ringa ji a zuciyarsa, ya taka a hankali ya tsaya gaban kujerar da ta jingina da ita, kujerar ya bubbuga yace "hey"......✍️ Masu tmbyr cmplt kuje arewa book ku karanta, just search HAJAR and follow my account @ feenerhfeeche02 💛 HAJAR 💛 by Feenerh feeche {43..} Saida ya sake buga kujerar snn ta motsa, daman ba wani daɗin baccin take ji ba, buɗe idanunta tayi, yana ganin haka ya bada distance a tsakaninsu yace "hey, you better find a place to sleep, nan ba wajen bacci bane", ta buɗe idanunta tarwal ta mutsuttsukasu da hannu, taɓe baki tayi tace "what concern you da wajen dana kwanta..", ta mayar da kanta jikin kujerar ta lumshe ido, sake bubbuga kujerar yayi this time around da ƙarfi yace "you are not serious, ki tafi wani wajen malama amma banda nan", miƙewa tayi tsaye ta gyara yafen mayafinta, ledar data rage akan Centre table ya ɗauka yace "follow me...", ɗauke kanta tayi kamar ba taji me yace ba, yayi controlling tempern dake taso masa yace "i said follow me", ta sake juyar da kanta tayi folding both hands dinta tace "kayi mgana da yaren da zan gane..", yace "haka ne fa, ohk, duba da irin localityn da kika taso bai kamata a miki magana ta masu ilimi ba, cewa nayi ki biyo ni", bai jira cewarta ba ya fara hawa stairs, bin bayansa tay da kallo kafin ta haura saman, a daidai ƙofar ɗakin dake matsayin nata ya dakata, ya murɗa door handle ya buɗe, ajiye mata ledar yayi a gefenta ya koma ƙasa, ta yiwa ledar wani kallon hadarin kaji ta shiga ɗakin ta barta a nan, Nurain ya kashe duk bulbs dake kunne palourn, ya haura sama da ledar abincinsa a hannu, tsayawa yayi yana kallon ledar da ta bari inda ya ajiye, ya ɗaga kafaɗa ya wuce part ɗinsa, a palour ya zauna ya buɗe ledar, abinci ne mai rai da lafiya jollof rice da taji kayan lambu sai quartern kaza da soyayyen plaintain, spoon ya ɗauka ya ɗebi rice din ya kai baki, ajiye spoon din yayi yana kallon abincin, ya koma yayi resting da kujera don taste din bai masa ba, kwata kwata baya son abincin waje, rufe abincin yayi ya buɗe bottle water ya sha, daga ƙarshe dai ya tashi daga palourn ya shiga bedroom, ya rage hasken fitulu ya bar dim ta bedside, ya ɗauki Mac phone dinsa dake kan bedside ya kunna. Hajar ta gama ƙarewa ɗakin kallo kafin ta taɓe baki, da sauri ta isa gaban gado ganin handbag dinta, ta ɗauki handbag din ta buɗe, wayarta ta fara cirowa tana jujjuyata, kunnawa za tay taga ta mutu, acikin hand bag din ta zaro charge tayi plugging wayar a socket da ta gani a room din, zama tayi kusa da wayar har saida tayi 10% ta kunnata, bayan wayar ta gama booting taga missed call da yawa wanda sune ma suka sa wayar ta mutu tinda ba wani charge ne da ita ba lokacin da aka kawota gidan, call log ta shiga ta kira Ummanta, ba tama damu da dare yayi ba, don a lokacin sha biyu na dare ake magana, har kiran ya katse Umma bata ɗaga ba, Sake kira Hajar tayi, daf da kiran zai katse aka ɗaga, wani ajiyar zuciya Hajar ta saki tace "Umma na..", Umma ta tashi zaune don bacci take kiran wayar ya farkar da ita, Umma tace "Hajara..", tini hawaye ya ciko idanun Hajar tace "Na'am Umma", Umma tace "ina kika saka wayarki anata kira ba a samu..?", Hajar tace "a gida na barta kuma babu chaji..", Umma tace "Okay, toh ykk ya zaman sabon waje?", Hajar da already hawayen idonta sun fara tsiyaya tace "Ya Baba da Sabra da Yaya...?", Umma tace "kowa lfy alhmdllh..", Shiru Hajar tayi ba tace komai ba don wata ball ce ta tsaya mata a throat, jin tayi shiru Umma tace "ya jikin naki..?", da kyar tace "naji sauƙi sosai..", tayi shiru kafin tace "Umma..." sai kuma ta kasa cewa komai don ta rasa me zata ce, daga ƙarshe dai tace "Umma seda safe nasan ma kin fara bacci na tashe ki" da haka ta kashe wayar ta fashe da kuka, har cikin ƙasan zuciyarta bata san auren nan, saida taci kukan mai isarta har kanta ya fara ciwo, ta goge hawayen da ya jiƙa mata cheeks kafin ta tashi daga tiles da ta zauna, bathroom ta shiga ta wanke fuskarta ta fito, pillow ta ɗakko daga kan gado ta wurgar kan lallausan carpet dake room din, ta kware duvet din gado shima, tayi kwanciyarta kan carpet ta rufa har ka da duvet din don wani irin sanyi ne yake ratsata na Ac, har uku na dare idonta biyu ta kasa bacci sai juye juye take, babu kalar tunanin da ba tay ba a zuciyarta, sai wajen huɗu da ƴan mintina bacci ɓarawo ya kwasheta, alarm din wayarta ne ya tasheta wanda tintini take dashi wanda yake tashinta da asuba sbd ɓatan rana, kafin ma ya tasheta take tashi, da kyar ta yunƙura ta miƙe zaune ta dafe kanta sbd faskarawar da yayi, ta tashi ta kashe alarm din, a hankali ta fara jiyo kiraye kiaryen sallar asuba, ta dai samu ta daddafa ta shiga toilet tayo alwala tayi sallah, tana idar da sallah ta koma ta kwanta don da gaske kanta ciwo yake. Washe gari ƙarfe takwas da rabi na safe Nurain ya sauko down stairs da key din motarsa a hannunsa, saida ya rufe main door din shiga gidan kafin ya wuce parking spaces, Inuwa mai gadi da ke goge motar da soft duster ya gaishesa da ladabi, Nurain ya amsa yace "zan fita amma ba jimawa zanyi ba..", Inuwa yace "toh Alhj Allah ya tsare", Nurain yace "Ameen" ya buɗe motar ya shiga, da sauri Inuwa yaje ya buɗe gate, da reverse ya fitar da motar daga parking space kafin ya juyata ya fita daga gidan, Inuwa ya mayar da gate din ya rufe ya ɗauki watering can yana bawa flowers ruwa, Supermarket Nurain ya tafi, duk wani kayan abinci saida ya siya na tsaba da kuma masarufi, ruwa da lemo ma bai barsu ba saida ya siyo, har da perishable food ya siyo, sai 11 ya gama siyayyan ya wuce gida, yana parker motar ya zaga backyard ya buɗe wata glass door wacca zata kaika kitchen, ya shiga kitchen din, ya buɗe store dake cikin kitchen din, gas ya kunna wanda cylinder dinsa ke can bayan gidan anyi connecting pipes zuwa kitchen, ranar Thursday da yazo giran yasa aka masa refilling babar cylindern, daga haka kuma ya sake fita compound wajen motarsa ya buɗe booth, Inuwa ya saka ya ringa jigilar kai kayan da ya siyo yana libgewa a store, wanda za a ajiye a freezer kamar meat da chicken suma aka zuba a freezer, lemo da ruwa kuma a store aka ajiyesu bayan an zuba wasu a babban fridge dake kitchen din, a section na biyu na fridge din kuma aka zuba kayan miya, kitchen dai ya cika tsaf, bayan an gama shigar da komai Nurain ya buɗe cupboard ya ajiye Coffee powder da ya siyo ma kansa, daga haka ya buɗe ƙofar palour ya shiga, upstairs ya haura zuwa part dinsa, after like 10mins ya fito ya bar gidan mai gaba ɗaya a motarsa. ★Anty Jamilah ta yafa gyalenta tana kallon Umma tace "toh bari mu wuce kar muyi yamma tinda an gama fita da kayan", Umma tace "Amma kina ganin abin nan bazai zama gulma ba bafa wanda aka gayyata kai garar", Anty tace "babu gulmar da za ai wllh, toh Allah na tuba wanda ma yayi gulmar ai shi yaga zai iya yawunsa ne zai ƙafe a banza, yaushe aka gama bikin da zamu sake jajiɓowa kanmu jama'a wani kai gara, yarinya fa za a yiwa ba wani abun kallo bane, ai na ɗebar miki dubulan da Alkaki da gireba da chin chin saiki ƙuƙƙulla a leda a rabawa maƙota da abokan arziki", Umma tace "toh ai shknn, ince dai dangin mijin sun sani..?", Anty tace "mu dai namu kaiwa, ita Hajarar ta gaya musu da kanta..", Umma tace "hakan ma yayi", Anty ta miƙawa Hafsah dake zaune ɗakin hand bag dinta tace "tashi muje..", Hafsah ta amshi jakar ta tashi ta fita ta tsaya bakin ƙofa, Anty ta fito tana kwalawa Mu'azzam kira don dashi za a tafi, ya fito daga ɗakinsu yace "Anty gani", tace "ko ka fasa zuwa kaga ƙanwar taka ne..?", ya girgiza kai yace "A'a zani", Shi dai so yake yaje yaga halin da ƙanwarsa take duba da irin auren da akay mata, gaba ɗaya ya kasa nutsuwa tin bayan auren, gashi kuma lokaci da dama ya kira wayarta switched off, Anty tace "toh muje ko" da haka tayi soro Hafsah tabi bayanta, Mu'azzam ya saka takalmansa ya fita shima, a soro suka kusa yin karo da Maimuna dake ƙoƙarin shigowa ta ɓoye wani abu a hijab, ko kallonta beyi ba ya wuceta ya cigaba da tafiya, Maimuna ta taɓe baki ta zabga masa harara ta shiga cikin gida da gudu, ɗakin Maama ta shiga tana zazzare ido ta fito da abinda take ɓoyewa cikin hijab, Maama dake tsaye da ɗaurin ƙirji tace "amma Maimuna Ala wadaran nawarki, daga siyo shinkafar ɓera shine kika je kikai zamanki sai kace an aiki bawa garinsu, wllh kin cuce ni, har an gama fita da kayan..", gwalo ido Maimuna tayi tace "mun shiga uku, har an gama fita dasu..", Umma tace "tin ɗazu ma, ai bakya abu da jiki daman baki so aiken ba..", cikin ɗaga murya Maimuna ta dakawa Maama tsawa tace "wai ke dalla Maama kin san da ya akai na samo bom din ɓeran nan kuwa, saida na fita daga unguwar nan sannan na samo sa fa", Maama ta saki baki jin yadda ƴar cikinta ke mata magana na rashin ɗa'a, Maimuna ta zabga tsaki tace "kuma wllh bazan yi asarar ɗari shida ta ba sai kin biya ni..", Maama tace "toh ai saiki bisu can gidan ki zazzaga bomm din da kanki don ni babu yadda zanyi tinda har sun fita", Maimuna tace "A jarkar mai zan zuba ko?", Maama tace "Eh shine yafi sauƙi tinda dai ba zaki iya farke buhun shinkafa ba amma idan kika ɓalle jarkar mai kika zazzaga saiki rufe kawai", Maimuna tace "bari na bisu kuwa don wllh sai Hajara tayi nadamar cin abincin nan", Maama tace "maza ƴar albarka ki tafi kar su ɓace miki", da gudu Maimuna ta fita daga gidan, Maama ta rafsa wata shegiyar guɗa ta buga cinya tace "sai a koma asibiti kuma bayan an take tumbi da abinci", Maimuna na fita bakin titi ta tarar har an gama saka kayan a ƴar ƙurƙura, Mu'azzam ya shiga gaban ƙurƙurar Anty da Hafsah kuma sun tari napep suna ciniki, Maimuna ta matsa kusa da napep din ta wani haɗe rai, Anty ta kalleta ba tace mata komai ba ta cigaba da kwatantawa mai napep unguwar da zai kaisu, Hafsah tace "Anty muje kawai zan gane gidan", Anty ta shiga napep din Hafsah ma ta shiga, ba kunya ba tsoron Allah Maimuna ta riƙe ƙarfen napep ta fara shirin hawa, Hafsah ta leƙo tace "ke malama ina zaki...?", Maimuna tace "kin fini kusanci ne da gidan wacca zaki..?, dalla malama dakatamin ki tsaya iya matsayinki, ke asuwa banza karan kaɗa miya a jefa bayan gida", Hafsah ta jefa hand bag din Anty dake hannunta a booth din napep, tasa hannu biyu ta hankaɗa Maimuna da ta turo buttocks zata zauna, saura ƙiris Maimuna ta baje a ƙasa, ta kasa yiwa Hafsah komai sbd bomb din ɓeran da take ƙunshewa a hijab, Maimuna tasa hannu ɗaya ta riƙe karfen napep din tana ɓarkawa Hafsah zagi, Hafsah ta taɓe baki tace "ban iya ba wllh, zagi ko toh ni ban iya ba, mai daidaita sahu kawai bi takanta muje", Kawai Maimuna ganin Mu'azzam tayi a gabanta, yace "ke dan uwarki ban nan wajen kafin na ɓarar dake...", Maimuna ta saki ƙarfen napep din ta matsa baya, Mu'azzam yayi kwafa ya koma ya shiga ƴar ƙurƙurar, mai napep yaja napep dinsa suka hau saman titi, bayansu su Mu'azzam suka bi tinda su za su musu jagora, Maimuna ta kalli kuɗin dake hannunta ɗari tara, tsayar da mai napep din da yazo wucewa tayi, da sauri ta shiga ta nuna masa motar su Mu'azzam wacca tayi nisa tace "yi sauri malam ƴar ƙurƙurar can zaka bi karsu ɓacemin", mai napep yace "tom" ya bawa babur ɗinsa wuta daman kuma sabo ne, Maimuna ta ringa azalzalal mai napep kar ya bari su ɓace masa don idan suka ɓace babu yadda zatay, gashi dai ta taɓa zuwa gidan amma kuma bazata gane ba sbd dulhu dankali ce, daga farkon layin Maimuna tasa mai napep ya ajiyeta tinda zata iya gane gidan daga nan, bill dinsa ta tambayesa, direct yace "dubu ɗaya zaki bayar hajiya", zaro ido tayi tace "duba ɗaya kuma, gsky ɗari biyu da hamsin zan baka..", yace "ɗari biyu da hamsin taɓɗi", Maimuna tace "nidae haka zan baka..", yace "haba malama duk wnn tafiyar, Shata fa kika ɗauka don baki bari na ɗauki wani pasinjan ba..", mai napep da yaga tana ƙoƙarin ɓata masa lokaci tini ya kashe babur din ya fito, yace "ko ki bani kuɗina ko na haɗa miki jini da majina, ce miki akay ruwa na zubawa babur din, ko baki san yadda fetur yayi tsada ba..", tini jikin Maimuna ya hau zikiri don kwa layin tsit babu kowa, hannunta na rawa ta fito da ɗari tarar data rage mata tace "dan girman Allah yi haƙuri ka amshi wnn, wllh su kenan a hannuna", da magiya da komai ya haƙura ya amshi ɗari tarar bayan ya mata Allah ya isan ɗarinsa ya burga mashin dinsa ya tafi. mai gadi ya buɗe gate da ake knocking ya tsaya yana kallon su Anty, gaisheta yayi ya bata hanya ta wuce, Hafsah tabi bayan Anty zuwa cikin gidan, mai gadi da mai ƴar ƙurƙura sai Mu'azzam ne suka sauke kayan suka shigar dasu ciki, Mu'azzam yayi mamakin ganin gidan da aka kawo ƙanwarsa, Inuwa sai duban kayan yake yana gyaɗa kai, da ake cewa babu kuɗi a gari ashe dai kuɗi suna nan inda suke, Hafsah ta danna bell ɗin main door ta shiga gidan bayan knocking da tayi, Anty ta ciro wayarta ta shiga kiran layin Hajar, tana dai ringing amma no respond, Anty tace "ikon Allah, ko basa nan ne, munyi waya fa da ita ɗazu tace min tana nan", Hafsah tace "toh bari a tambayi mutumin da ya buɗe mana ƙofa", Hafsah ta ƙarasa wajen da Inuwa ya koma kan white plastic chair ya zauna, tace "mutanen gidan basa nan ne...?", mai gadi yace "Alhj ne kawai ya fita", Hafsah tace "mu gashi nan sai bubbuga ƙofa muke amma shiru", mai gadi ya tashi yace "bari na nuna muku ta baya sai ku shiga" ya wuce gaba Hafsah tabi bayansa, har ƙofar kitchen dake backyard ya rakasu kafin ya koma bakin aikinsa, Anty ta murɗa ƙofar tashiga taga ashe kitchen ne, ta kalli Mu'azzam tace "a shigo dasu nan kawai, ba a barsu yashe a tsakar gida ba", har sukay minti goma da shiga palourn basu ga alamar Hajar ba, daga karshe dai Hafsah ta tashi ta haura sama, a hankali tayi knocking ƙofar ɗakin da tasan an kai Hajar, murɗa ƙofar tayi ta shiga, ba taga kowa ba saidai taji ƙarar ruwa daga toilet, tsaye Hafsah tayi tana jiran fitowarta, few minutes kam sai gata nan ta fito tana tafiya a hankali......✍️ 💛 HAJAR 💛 by Feenerh feeche {44..} Tamkar wata munafuka haka Mainuna ta ƙarasa bakin gate din gidan ta bubbuga, mai gadi ya buɗe ƙofar, tsayawa yayi yana kallonta, Maimuna tace "zan wuce ko", mai gadi yace "hajiya daga ina...?", tace "tare muke da mutanen da suka shigo yanzu, na tsaya ne akan hanya na amshi saƙo..", mai gadi ya sake kallonta sama da ƙasa don sam ba tayi kama da mutanen ba, fuskarta sai kace horror duk ta ɗashe sbd azabar shafa mai, ga kuma uban ƙuraje da barni da mugu, kayan jikinta ma ba kanta don wani yagulamun hijab ne sanye ajikinta duk ya ƙoƙƙone ya farke, matsa mata yayi ta shiga ya rufe gidan, wani kallon baƙin ciki Maimuna take bin compound din dashi, tsaye tayi ta rasa ina ma zata dosa, Inuwa da har ya koma ya zauna ya sake tashi ganinta a tsaye, yace "bari na nuna miki ta baya tinda naga tanan a rufe take..", gyaɗa masa kai kawai tayi don tsoro ya fara shigarta, wai ta yaya ma zata iya zuba shinkafar ɓeran, haka tabi mai gadi har ya nuna mata hanyar baya, kasa shiga tayi don tsoro ya kamata fa ainun, shi dai mai gadi tinda ya gwada mata ƙofar ya koma bakin aikinsa, shahada kawai tayi ta tura ƙofar a hankali, tinda dai ta riga da tazo babu yadda za suyi da ita, saɗaf saɗaf ta shiga da wani suɗaɗɗen takalminta, cak ta tsaya tana kallon kitchen din ganin kayan garar zube a nan, wani daɗi ne ya tsarga mata a zuciya, da sauri ta fito da ledar da take ƙunshewa a hijab. Tare da Hafsah Hajar suka sauko ƙasa, Hafsah ce ma ta riƙota don da kyar take tafiya sbd ciwon kan, ga kuma yunwa da ta mata illa don rabonta da abinci tin jiya da yamma, sosai Hajar taji daɗin ganin Anty da Mu'azzam, saida suka gaisa gaba ɗaya snn ta samu waje ta zauna ta jingina da kujera, Mu'azzam na kallonta yace "ke lafiyar ki kuwa..?", Hafsah tace "kanta ne yake ciwo..", yace "Sannu, Allah ya sauwaƙe", Anty tace "Ayya sannu kinsha magani..?", Hajar ta girgiza kai tace "babu maganin ai", Anty tace "tin yaushe kan naki ke ciwon..?", Hajar tace "tin safe", Anty tace "akwai panadol a jakata, Hafsah buɗe ki ɗakko mata", Mu'azzam ya tashi yana ciro wayarsa da tay vibrate daga aljihu, ƙofar kitchen ya murɗa ya shiga, a gigice Maimuna dake tsugunne gaban jarkar mai ta ɓalle murfin tana shirin zazzaga shinkafar ɓeran data buɗe ta ɗago kanta, wani irin juyawa ƴan hanjinta sukay ganin Mu'azzam, tsabar gigicewa sai ta saki ledar shinkafar ɓeran a ƙasa, daɓas ta zube a ƙasa tana raba ido tamkar ɓera a buta, da mamaki Mu'azzam yake kallonta, mayar da wayar yayi aljihu ya fasa ɗaga kiran, ledar da ta wurgar ya ɗauka, ƙurawa ledar ido yayi, ya dubi Maimuna da tayi tsilli tsilli, wata mummunar zuciya ce ta ɗebesa ya haɗa kanta da cooking gas, wata razananniyar ƙara ta fasa sbd ji tai kamar raba mata kan gida biyu yayi, tini zufa ta fara tsattsafo masa a goshi, Anty ce ta shigo kitchen din, still tay tana kallon Maimuna da goshinta ya wanke da jini, Mu'azzam ya goge zufar goshinsa yana kallon Anty yace "Why, ƙoƙarin kashe min ƙanwa take Anty" ya juya yana nuna Maimuna da yatsa yace "so take ta kashe min ƙanwa...", Anty ta ringa kallon Maimuna sai kuma ta dubi Mu'azzam, bata kai ga cewa komai ba ya nuna mata ledar bomb din ɓeran hannunsa har rawa yake yace "kamata nayi tana ƙoƙarin zubawa a cikin mai", Anty da mamakin ganin Maimuna a nan ya gama cikata tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un, mun shiga uku, yanzu Shayin ɓera ka kamata zata zuba a mai", Anty ta sakawa ƙofar kitchen ɗin lock sbd bata son Hajar ko Hafsah su shigo ta juya tana kallon Mu'azzam tace "dan girman Allah fitar mana da ita daga nan, marmaza ka fita da ita wnn ai gara annoba da ita, yanxu ke har zuciyarki tayi baƙin da zaki cutar da mutum da bomb din ɓera", Mu'azzam ya iza ƙeyar Maimuna suka fita daga kitchen din, Anty tabi bayansa tace "ka tabbatar bata zuba ba...?", yace "Eh bata kai ga zubawar ba na kamata..", Anty ta koma cikin gidan hankalinta duk a tashe, banzatar da Hafsah dake tambayarta me ya faru tayi, bayan ta nunawa Hajar kayan ta shirya tace tafiya za tay, don gaba ɗaya hankalinta ya ɗugunzuma gwara taje ta zauna da ƴar uwarta, wnn abu ai ba na wasa bane, a nan ta bar Hafsah zata tafi gida daga baya bayan tace mata karta kai dare, sosai Hajar taji daɗin bar mata Hafsah da akai, Hafsah ta shiga kitchen ta dafa mata Noodles, ta ringa mita bayan ta kawo mata Noodles din tace "ga abinci ba zaki dafa kici ba saiki ta zama da yunwa", Hajar na tura Noodles din tace "bana jin daɗi ne", Hafsah tace "yunwa ce fa..", Hajar na gama cin Noodles din da zata iya tasha panadol da Anty ta bari, sosai taji dama dama kan ya dena ciwo, Hafsah taje kitchen ta ɗakko ledar da suka zo da ita wacca ke ɗauke da turaren wuta da sauran tarkace da Anty ta haɗawa Hajar, Hafsah tace "bari na rage miki aiki", upstairs suka haura again zuwa ɗakin Hajar, Hafsah ta buɗe box din kayan Hajar ta jera mata su a wardrobe, kayan lefenta ma saida Hafsah ta buɗe ta mata tsince tsince, kayan bacci da mayuka da perfumes, mirror kam saida ya cika damm da kayan shafe shafe don Hafsah bata barsa haka nan ba, ita dai Hajar kawai kallonta take tana yamutsa fuska, ita sam babu abinda ya birgeta na daga gidan ko kuma kayan cikinsa, garar da Baban ta yayi mata ya fiye mata komai na gidan, daga ƙarshe Hafsah ta shiga bathroom tayi masa jerensa shima, Shower gel Shampoo da conditioner duk ta jera su a cupboard dake toilet din, saida Hafsah ta gajiyar da kanta don har shara tayi ta goge ko ina ta bisa da turaren wuta a burners, da joke Hafsah tace "da fatan dai kin ɗauki course, haka zaki ringa yi kullum", Hajar ta taɓe baki tace "uhmm", Hafsah tayi ajiyar zuciya ta saka serious face tace "Sister i understand your feelings, nasan yadda kike ji, amma ki ajiye komai ki riƙe hakan as one out of your destiny, ke naki ƙaddarar knn, Allah ya rubuta wnn da aka aura miki shine mijinki, nothing can change that, don Allah ki kwantar da hankalinki ki amshi ƙaddarar ki hannu biyu, forget about the past and face the future ehmmm", Hajar tace "idan da ban haƙura na amshi ƙaddarar ba ai bazan zauna ba Hafsah, wllh tllh Baba nake dubawa shiyasa na zauna amma baya ga haka babu abinda zai zaunar dani", Hafsah tace "Eh hkan ma yayi, komai na rayuwa ai sila ne, in Allah ya yarda wnn auren sai ya zame miki jin daɗi da kwanciyar hankali...", Hajar ta rausayar da kai ba tace komai ba, ƙarfe biyar Hafsah ta fara shirin tafiya, tini mood din Hajar yana canza, Hafsah tayi kamar bata fahimta ba ta cigaba da shirinta, tana gama shiryawa ta ɗauki jakarta, har bakin gate Hajar ta rakata, bayan ta tafi ta koma ciki. Hafsah tsaye bakin road tana jiran napep bayan tayi ƴar tafiya ta fito daga layin gidan, napep biyar ta tare kuma duk basu ɗauketa ba wai ba za suyi hanyar ba, har ta fara gajiya da tsayuwa, wata lafiyayyiyar Mota ce taci taya a gabanta, ganin motar ta kare mata titi ta matsa daga wajen, driver seat aka buɗe, wani gentleman ya fito his eyes covered with shade, ta cikin shade din ya ringa kallonta kafin ya rufe murfin motar ya isa inda take, Calmly yace "Assalamu alaikum...", Hafsah ta juyo tana kallonsa ba tare da ta amsa sallamar ba, sake matsawa tayi ta haɗe gira, cire shade din yayi yana kallon side view din face ɗinta yace "Young Lady", juyowa tayi ta ƙura masa ido, tsuke ido tayi bata kai ga magana ba ya rigata yace "it is me Ahmad..", ta zaro ido tace "ohh Sannu ai ban gane ba da farko", yayi murmushi yana shafa kwantaccen beard dinsa yace "how are you...?", tace "am fine alhmdllh", yace "masha Allah..", ya kalli road din da yake tamkar an sharesa babu motoci sosai ma bare kuma napep yace "where are you heading to...?", tace "Gida zani", yace "toh bari na ajiyeki ko", a fakaice ta dubesa sai kuma ta girgiza kai tace "No thank you...", yace "me yasa ba zakizo na ajiye ki ba..?, zafa ki iya kai Magrib anan tricycle basu wucewa sosai tanan", ta sake girgiza kai tace "i can wait....", da kyar yayi convincing dinta ta yarda bayan dai taga tabbas zata iya kai magrib don tin zuwansa wajen babu napep din da ya sake wucewa, da kansa ya buɗe mata front seat ta shiga a hankali ya mayar da ƙofar ya rufe kafin ya zaga ya buɗe driver seat ya shiga, ita dai ta maƙale daga jin window, gaba ɗaya she isn't comfortable ta takure waje ɗaya, Ahmad ya kunna motar ya fara driving da minimum speed, Silence ne ya ɗauka a motar, bayan sun fita daga unguwar Ahmad yayi breaking silence ɗin da faɗin "ya school...?", tana kallon handbag dinta dake kan laps ɗinta tace "alhmdllh ai mun kusa gamawa..", yace "University fa", tace "No secondary ne..", ya jinjina kai yace "as expected you are a teenager", zaro ido tayi tace "A'a fah", his eyes fixed on the road a hankali yace "how is she..?", ɗaga kanta tayi ta kallesa, a lokaci guda ya juyo sukay ido huɗu, da sauri ta ɗauke kanta ta kalli window tace "tana lfy alhmdllh...", yayi ajiyar zuciya yace "Ohk" da haka bai sake cewa komai ba, ita dai tana jiran taji ya tambayeta hanyar unguwar tasu don sai take ganin kamar ya manta, amma sai taga beyi hakan ba kuma tiryan tiryan hanyar unguwar yake bi, Hafsah tana ganin sun shigo unguwarsu zuciyarta ta buga, basu ƙarasa gidansu ba tayi saurin cewa "amm drop me here zan ƙarasa", slowing down yayi yabi gefen titi ya tsaya, tace "nagode" ta fara ƙoƙarin buɗe motar taji a ƙulle don bai buɗe lock ba, ta juya za tace masa ya buɗe taga ashe kallonta yake, da wani irin expression bisa fuskarsa yace "Sorry, one minute please", ta sauke hannunta dake riƙe da handle din ƙofar tace "Okay", yayi ajiyar zuciya still looking at her yace "the last time i met her ta gayamin cewa she is getting marry soon, at that time na yarda amma bayan wani lokaci sai mind dina taƙi yarda..", yayi shiru na 3secs kafin ya ɗora "i want you to tell me the truth..", ta ɗago kanta ta kallesa kafin ta mayar ƙasa tana wasa da ƙasan mayafinta tace "me yasa kake tambayata wnn...?", yace "bcox i need to confirm it ko na samu rest of mind..", kai tsaye tace "Alright, the truth is since last week Friday akay bikinta, yanxu ma daga gidanta nake...", Ahmad was very shocked and dump founded, yama kasa cewa komai, zuciyarsa ce ta ringa confusing nasa tana ce masa ai Hajar kawai tace masa haka ne to get rid of him amma ba hakan bane, Hafsah dai ganin baice komai ba tace "please open the door one minute has passed..", buɗe lock din yayi da kyar yace "sai anjima..", tace "thank you..", ya gyaɗa kai yace "you're welcome", ta buɗe motar ta fita ta rufe masa ƙofar, ta ƙarewa street din nasu kallo wai ko za taga wani wanda yaga fitowarta daga motar kuma wanda ta sani, Sosai taji daɗi da ta lura babu kowa, tana ƙarasawa ƙofar gida ta juyo, sosai tayi mamakin ganin motarsa bai tafi ba har lokacin, ita dai ta ɗakko keys daga jaka ta buɗe gida ta shiga. ★Umma ta ɗora hannu bibbiyu aka ta zabga wani uban salati tana kallon Anty tace "Jamilah na shiga uku na lalace shayin ɓera fa kika ce", Anty tace "ai ba ɗora hannu a ka za kiyi ba, kuma biki shiga uku ba Adda, wllh tllh zama bai kamace ki ba, idan haƙuri yayi yawa toh cutarwa ma yawa take, abu ne wanda ba yanxu aka fara ba an ɗebi shekaru anayi, ace har an fara farautar raii, gsky ya kamata ki farga cutar tayi yawa, idan da ace Mu'azzam bai ganta ba da shknn sai yadda Allah yayi, wa yasan halin da Hajar da Mijinta zasu shiga idan sukaci oil din nan, gani nai bazan iya shiru ba shine nace bari na dawo na tasheki daga barcin da kike..", Umma da kuka ya kwace mata tace "Jamilah yanzu ya zanyi dan Allah wnn wane irin masifa da bala'i ne, ace yarinyar nan tayi aure ta bar maku gida amma ku bita har gidanta da bita da ƙulli, da tana gida ma baku barta zaman lfy ba ita da gidan ubanta gashi gidan mijin ma an bita, wnn wace irin rayuwa ce..", Anty tace "Ahapp ki dena ɓaɓatu kina ƙarar da yawun bakin ki Adda, tashi tsaye za kiyi ki nemawa kanki salama, ki buga ƴan iska ga hukuma, wnn lamari ai ba na wasa bane, ƙoƙarin kisa fa..", Umma ta sharce hawayenta tace "bari mal ya dawo..", Anty tace "A'a Adda mal ai ba hukuma bane, idan nice ke yanzu ba sai anjima ba zan wanke ƙafa na tafi inda za a nemamin haƙƙina", tini Umma ta zari hijab ta saka ta ɗauki ƴar purse ɗinta tace "a ina zan buga matsiyatan..?", Anty ta tashi tace "muje", da sauri Umma ta fita tsakar gida Anty na biye da ita, banke ƙofar ɗakin nata kawai tayi babu wani batun padlock, tin daga soro kake jin muryar Baba yana kwalawa Maimuna kira, da iya volume din muryarsa yake kiranta har yana ƙoƙarin ƙwarewa, da mugun gudu Maama ta fito daga toilet, har tana fyarɗe hannu da ƙarfen langa langar ƙofar banɗakin, banga banga tayi a ƙofar ɗakinta tana zaro ido, a matuƙar fusace Baba da ya shigo gidan shi da Mu'azzam yace "ina Maimuna..?", Maama da hannunta yake azabar raɗaɗi da zugi tace "wace Maimuna kuma mal, yarinyar dake kwance tin shekaran jiya tana fama da masassara, yau kuma ta tashi cikinta ya tsuru wuni tayi tana fatattaka gudawa, gaba ɗaya ta fita daga hayyacinta ido ya zuzzurma...", Umma dake tsaye tsakar gidan ta daka mata wata gagarumar tsawa tace "wllh ko kashin ƴan hanjinta take saita ɗanɗana kuɗarta a yau, na gaji da abinda ake min a gidan nan yau an kaini bango, billahillazi la'ilaha illa huwa bazan haƙura ba..", galala Maama take kallon Umma ta hura tukubar hanci tace "toh ai sai kizo kisa ta ɗanɗana kuɗarata ta, ke kin isa ma ki ɗora hannunki akan ƴata", Baba da tari yake ƙoƙarin sarƙe masa numfashi yace "Rabii ki faɗamin inda Maimuna take ko na sake ki..", Maama ta dafe ƙirjinta ta gwalo idanu waje tace "da girmana da gemuna mal kake cewa zaka sakeni a bainan nasi, toh Maimuna dai ƴarka ce kuma gata can kwance tana makyarkyata...", Baba yace "So nake ta fito nan yanzu yanzun nan..", kasaƙe Maama tayi sai kuma ta rausayar da kai ta shiga ɗakinta, Maimuna da ke rakuɓe can ƙarshen gado ta haɗa hannayenta waje guda tace "Maama dan girman Allah ki rufa min asiri, na shiga uku na lalace..", Maama tace "A'a Maimuna a gaskiya tashi za kiyi ki fita, kina jifa sakina yace zaiyi idan ya sakeni ina na dosa..", Nabilah dake ɗakin itama tace "wanda baiji bari ba ai yaji hoho, saida nace ki bari Maimuna amma saida kika biyewa Maama, tinda dai baku rasa ci da sha ba ina ruwanku da garar Hajara, ga dai irin ƙarangiyar da kika jajiɓowa kanki...", Maimuna ta rushe da kuka ga goshi yayi suntumm, tini Maama ta figi ƙafar Maimuna ta fara janta ƙiyyy jin Baba na sake jaddada mata zai saketa, Maimuna ta riƙe gado ta daƙile tana kurma ihu, ta ƙarfi da yaji Maama ta fitar da ita, daga ita har Maimunan haki suka ringa yi, Maama tace "ƴarka ce daii", Anty dai tinda ta jingina da bango tana kallon ikon Allah ba tace komai ba, Baba kawai kallon Maimuna yake da wani irin takaici, shi ba ya mata baki rayuwarta taɓarɓarce ba. Maimuna ta faɗawa ƴan garinsu da shaɗin carbi, daga tazo guduwa Mu'azzam zai tarota ya dawo da ita don ji yake kamar ya taya Baba dukan ƴar banza, Maimuna da taji azaba iya azaba tace "na rantse da Allah Maama ce ta sani, itace tace na zuba wllh" tana soshe soshe, saura ƙiris Baba yayi collapsing Mu'azzam ya riƙosa ya kaisa ɗakinsa, wnn dalilin ne yasa Umma ta fasa fita, maganin Baban dake wajenta ta ɗakko da ruwa ta shiga ta kai masa, Wani irin tari mai ƙarfin gaske Baba yake, idanunsu sun firfito waje, da kyar aka sami kansa, Maimuna dai ta samu ta arce ɗaki tana soshe soshe, Maama ta bita ɗakin tana sababi tace "Shine kika fita bainan nasi kikai yama ɗiɗi dani..", a gigice Maimuna tace "Allah ya isa na bazan taɓa yafewa ba, munafiki azzalumi mugu..", Nabilah tace "kan bala'i Maimuna wa kikewa Allah ya isa...?", Maimuna tace "waccan Shegen Mu'azzam ai shine yazo ya ƙalamin sharri, kuma na rantse da izu sittin sai yasan ni aka daka ta dalilinsa, wllh tllh saina biya ƴan daba kuɗi sun sassara shi, idan yaci buluss shegiya nake, shi ya isa yasa a dakeni kuma ya fasamin goshi a banza, wllh Allah sai nasa ƴan daba sun sassara shi...". ★Nurain ne zaune main palourn gidansu, plate din abinci da Noor ta zubo masa ne a gabansa yana ci, Mami ta fito daga part dinta, shigowa palourn tayi tana kallonsa sai kuma ta kalli plate din abincin tace "har yanzu baka tafi gida ba Nurain...?", ya ajiye spoon din hannunsa yace "yeah na tsaya yin dinner ne", tace "Ohk hurry up ka gama dare yayi fa 9 ya wuce tin ɗazu..", yace "Ohk", Mami ta zauna kan kujera, kaɗan ya rage abincin ya tashi ya shiga da plate din kitchen, ya fito da bottle water a hannunsa, Mami ta tashi tace "toh good night zan sawa door lock", kallonta ya ringa yi da mamaki sai kuma yace "am spending the night here", with facial expression take kallonsa tace "baka isa ba kuma wnn", ya girgiza kansa don yana sane ya faɗi hakan don yaji view ɗinta, upstairs ya haura zuwa room ɗinsa, bayan few minutes ya sakko da wata medium bag a hannunsa wacca ya zubo kayan sawa, ya yiwa Mami sallama wacca har lokacin bata bar palourn ba ya fita, yana fita Mami ta sakawa door lock, Nurain ya girgiza kansa don yaji lokacin da ta saka lock din, wato dai Mami harda kora, motarsa ya shiga ya bar gidan, yana zuwa gida bayan yayi parking ya fito daga motar, Inuwa mai gadi ya masa sannu da zuwa, Nurain ya wuce hanyar shiga gidan, keys ya ciro ya buɗe ƙofar ya shiga, tsayawa yayi yana kallon palourn da yake tsaf tsaf sai ƙamshi ke tashi, tsaki yayi ya taɓe baki ya haura sama with his bag, bayan yayi wanka ya shirya cikin Pajamas ya ɗauki jakar Laptop dinsa ya sake sakkowa downstairs, ajiye bag din Laptop din yayi kan kujera ya shiga kitchen, shima dai kitchen din tass yake komai a mazauninsa, daga can gefe yaga foodstuffs, still yayi yana kallon foodstuffs din, ga kuma bucket guda huɗu kusa da foodstuffs din, ya buɗe bucket ɗaya wanda yake cike damm da dubulan, ya sake buɗe wani shi kuma yaga Alkaki shima acike damm, bai buɗe ragowar ba sbd ya gane na mene, Coffee maker ya jona jikin socket kafin ya buɗe cupboard da ya ajiye Coffee powder ciki, within few minutes ya gama haɗa black coffee ya bar kitchen din, saida ya kashe dukka fitulun palourn snn ya zauna a kujera ya kunna Laptop dinsa, operating system din yake at same time kuma yana sipping Coffee, ɗago kansa yayi ya kalli stairs jin footsteps, a hankali Hajar take sakkowa daga benen, harta fara bacci wata azababbiyar yunwa ta farkar da ita, tamkar an yashe mata kayan ciki haka take ji tsabar yunwa, tunawa da kayan garar da aka kawo mata ne yasa ta fito domin ta ɗiba taci kar yunwa ta halaka ta, kafin ma ta ƙarasa sakkowa ƙasa ta hango duhun palourn, Allah yaso da wayarta a hannu, tana gama sakkowa ta kunna fitilar wayar, rays ɗin hasken fitilar wayar da ta kunna ya dallare masa ido......✍️ Feenerhfeeche02 @ Arewa book Chapter 45 is available on 👉 Arewa book... Arewa book suna rigaku samun update da wuri, follow my account to stay connected @ feenerhfeeche02 💛 HAJAR 💛 by Feenerh feeche {45..} Da sauri Nurain ya lumshe idonsa tsabar yadda hasken ya kashe masa su, Hajar da tsoro ya sandarar da ita ta kasa wani cikakken motsi, sosai ta razana don ba tayi tunanin akwai mutum a wajen ba, Nurain ya ajiye cup din Coffeen ya kaucewa hasken yace "kee mene haka kuma are you mad...?", da sauri ta janye hasken daga kansa, furiously ya tashi ya kunna bulbs haske ya gauraye palourn, wani irin shan kunu Hajar tayi ta shige kitchen da sigar ko in kula, sarai tasan haske masa ido tayi amma she don't care tinda dai ba intentionally ta aikata hakan ba, wani tuƙuƙi ne ma ya mamaye mata zuciya da taga fuskar tasa, plate ta ɗauka ta zuba dubulan da Alkaki sai chin chin, cup ta ɗauka ta buɗe tap din sink ta cika da ruwa, daga haka ta fita daga kitchen din, direct stairs ta dosa, Nurain ya miƙe daga hannun kujerar da ya zauna ya zuba both hands dinsa a pocket fuskarsa a murtuke yace "hey you stay there", tamke fuskarta tayi ta cigaba da tafiya a hankali sbd kar cup din da ta ciko da ruwa yayi tambal tambal ya zube, yayi blocking front dinta yana binta da wani kallon tsana yace "wnn shine karo na ƙarshe da zaki sake fitowa palourn nan idan ina zaune, daga ƙarfe shida na yamma bana son ko silhouette naki ya gifta ta palourn nan, ko me za kiyi ki yisa kafin wnn time din that is weekdays knn, a weekend kuma you just have 3 hours daga shida na safe zuwa tara, daga nan kuma sai gobe, am i clear...?", ta juya lulu eyes ɗinta ta yamutsa fuska sbd yadda tayi perceiving pure men scent dinsa, ta taɓe baki tace "sorry you can't tell me what to do...", yace "ko, toh ki jini da kyau as far as you are living in my house you must follow my rules, bad attitudes din kike ji dashi toh ki tattarasa ki ajiye gefe, ba dai a nan ba saiki bari lokacin da kika gaji da zama kika sallami kanki ki ɗauki abinki ki ƙara gaba, this is my last warning...", da haka ya barta tsaye ya ɗauki Laptop dinsa da cup of coffeen zai haura sama, wata nannayar ajiyar zuciya Hajar ta sauke, har wani huci take masifar ta motsa, idonta ya kawo ruwa, tana ganin yayi rabin stairs din tace "ji mana malam, karka tsaya wahalar da kanka, ka damƙa min shaida kaga idan ban ƙara gaban ba", ya juyo ya wurga mata wani mugun kallo yace "save the time that you are free to roam in my house..." da haka ya juya ya haura stairs, har wajen 50seconds tana tsaye inda ya barta, gyaɗa kai tayi ta numfasa tace "lallai wnn mutumin bai sanni ba, sanin da yayi min na taɓin gishiri ne, mu zuba ni da kai wanda ya fasa bai haifu ba", ɗakinta ta wuce abinta, akan mirror ta ajiye plate da cup din da ta shigo dasu, ta zauna akan stool dake gaban mirror din tana kallon kanta, kwafa tayi ta girgiza kai ta ja plate din gabanta ta fara cin tarkacen da ta ɗeba, tana gama cin iya yadda zai mata ta sha ruwa, tayi kwanciyarta kan carpet kamar yadda tayi jiya, ta lulluɓe da duvet don wani azabar sanyi ɗakin yake mata sbd Ac gashi bata san ta inda zata kashe ba. Nurain ya gama abinda zai yi jikin Laptop kafin ya kashe ya mayar da ita bag, ya fita da cup din daya gama shan Coffee zuwa Kitchen yana dawowa kuma ya kwanta, da Asuba bayan ya shiga toilet ya dauro alwala ya fita daga room din nasa, a corridor ya tsaya yana kallon ƙofar ɗakinta, after looking at the for few seconds kawai ya sauka downstairs, bayan ya dawo daga masallaci ya zauna yayi recitation of the holy book, sai wajen 8 na safe ya rufe karatun, daman already yau Monday yake son komawa work, bathroom ya shiga bayan yayi wanka ya fito da towel a hannunsa yana goge cikakkiyar sumarsa, 9 ya gama shirinsa tsaf ya ɗauki briefcase da ya saka Laptop dinsa ya sauko ƙasa bayan ya rufe part din nasa, bai ga dai alamar ta sakko ba har ya shiga kitchen, ya haɗa tea ya dawo palour yana sha, tsaki yayi don ya saba yin full breakfast kafin ya fita aiki, daga karshe dai ya gama shanye tean ya kai cup din kitchen, daga haka ya fita compound bayan ya rufe main door ya zuba keys din a pocket, da sauri Inuwa dake zaune kan white plastic chair a bakin gate ya taso, ya russuna da kyau ya gaida Nurain, a takaice ya amsa yace "akwai wanda suka zo jiya ne bayan fita ta..?", Inuwa yace "Eh alhj anyi baƙi sunxo nan da kayan abinci..", Nurain ya gyaɗa kai bai ce komai ba ya buɗe motarsa da Inuwa ya gogeta tass ya wanke wheels ɗin kuma, bayan ya gama warming ya ja motar ya bar parking space din ya fita daga gidan dan already mai gadi ya buɗe gate, after a ride of 20mins ya isa hospital, yayi parking motar, kallon yawarsa dake kan dashboard yayi kafin yasa hannu ya ɗauka ya zurata a pocket, ya fito walking majestically ya nufi hanyar office dinsa, securities da sauran ma'aikata suka ringa gaishesa da welcoming dinsa, briefly yake amsa gaisuwar yana tafiya, yana ƙarasawa office din ya buɗe ya shiga, secretaryn sa Haleema da ya turawa saƙo ta email cewa zai shigo on Monday, shiyasa tin ranar friday tasa aka kyara office din, Haleema ta tashi with respect tace "good morning sir", da sakakkiyar fuska ya amsa mata yace "morning, ykk..", tace "alhmdllh sir an dawo lfy..?", yace "fine alhmdllh" da haka ya shige cikin office din, ƙarewa office din kallo yayi kafin ya ajiye briefcase din hannunsa kan huge table dake office din, after surveying the huge office ya zauna kan kujera yana sauke ajiyar zuciya, ya kalli glass nameplate dake gaban table din mai ɗauke da sunansa (Dr Uthman). wayarsa ya ciro ya kunna, saida ta gama booting uban messages da suke pending suka gama shigowa, call log ya shiga yayi dialing numbern Khaleel, tana fara ringing Khaleel yayi picking, Khaleel yace "ba dai ka dawo ba boss..", Nurain yace "gani ma a office", Khaleel ya katse kiran, after like 5minutes ya shigo office din, Khaleel ya zauna kan ɗaya daga biyun kujeru da suke gaban table din, bayan sunyi exchanging greetings Khaleel yace "An dawo lfy..?", Nurain yace "alhmdllh, Dr Marwan ya shigo..?", Khaleel yace "yeah amma ya shiga surgery not too long ago", Nurain yace "Ohk", Khaleel ya ciro wayarsa da tayi ringing daga pocket din labcoat dinsa, few seconds ya katse kiran ya tashi yace "i have to go now ana kirana a E.R". Khaleel na fita office din Nurain ya kira Haleema ta landline, tayi picking tace "yess sir", yace "Patients zasu iya fara shigowa", tace "Okay sir". Nurain ya fara attending first patient da ya shigo, yana yiwa patient din ƴan tambayoyi aka buɗe ƙofa aka shigo, kallo ɗaya ya mata ya ɗauke kansa ya cigaba da attending patient dinsa, jingina Ruqayyah tayi jikin ƙofar tana mayar da numfashi, ta lumshe idonta tana sauke ajiyar zuciya sai kuma ta buɗe idanun, kamar a yanzu ta fara ganinsa haka ta zuba masa na mujiya, kawai kallonsa take babu ƙiftawa ta jingina da jikin ƙofar, Nurain yayi prescribing patient din with drugs da cewar zai dawo nan da 2weeks follow up, Ruqayyah ta matsa gefe ta bawa patient din hanya ya fita, tamkar wacca kawai ya fashewa acikin haka ta isa gaban table din nasa kanta a ƙasa tana wasa with her fingers, tinda ya mata kallo ɗayan nan bai sake ba, kwata kwata bai nuna yasan ma da shigowarta ba, ya cigaba da rubutu jikin record book, muryarta na rawa kanta a ƙasa tace "Dearest...", next patient ce ta shigo ƴar dattijuwa, ganin haka yasa Ruqayyah ta bata space, sai a lokacin Nurain ya ɗago yayi attending patient dinsa, a haka dai saida yayi attending 5 Patients kuma har lokacin Ruqayyah na tsaye bata fita ba, na biyar din patient na fita, da sauri Ruqayyah taje ta rufe ƙofa, Nurain ya kira landline yace "i need security now", kasaƙe Ruqayyah tayi tana kallonsa sai kuma ta haɗa hannayenta waje ɗaya tace "plxx talk to me, dan Allah kayi haƙuri ka saurareni Dearest...", rubuce rubucen sa ya cigaba da yi, Security man ya buɗe ƙofa ya shigo with respect yace "sir you call", ba tare da ya ɗago kansa ba yace "get her out of my office", security man yace "yess", ya kalli Ruqayyah da Mamaki ya gama daskarar da ita yace "Muje hajiya..", wani kwallo mai uban tauri Ruqayyah ta haɗiya lokaci guda ta fita daga office din with speed hawaye na zuba idonta. Nurse station ta wuce, tana zuwa ta zauna kan kujera ta hade kanta da table din station din ta fashe da kuka, Nurse Jidda da ita kaɗai ce a station din duk sauran sun shiga ward ta ajiye kidney dish din hannunta tace "Ruqayyah lfy...?", Kuka kawai Ruqayyah take taƙi tace komai, da damuwa Jiddah tace "subhanallah dan Allah ki gayamin mene ya faru..?", Ruqayyah ta ɗago kanta tana kallon Jiddah da jajayen idanunta tace "Jiddah ni yanxu ya zanyi, Dr yaƙi saurarata...", Jiddah ta jinjina kai ba tace komai ba, ita ganin ƙarfin halin Ruqayyah take, yo ko itace Dr ai bazata saurareta ba, Ruqayyah ta goge cheeks dinta tace "wai fa security ya kira yace yayi waje dani sai kace wata ɓarauniya..", ta sake fashewa da kuka, Jidda tace "bari na duba patient a ward A" da haka ta saka kidney dish din da ta ajiye a cikin tray ta ɗauka tabar station din. ★Sai goma da rabi Hajar ta farka daga baccin da ta koma bayan ta idar da sallar asuba, bathroom ta shiga tayi brush ta wanke bakinta da mouth wash, tayi wanka, saida ta wanke bathroom din snn ta fito, tsaye tayi bakin mirror tana kallon uban kayan shafe shafen da Hafsah ta jera mata jiya, wani body lotion ta ɗauka tana duba sunansa sbd da shower gel dinsa tayi wanka, ta zauna kan stool ta fara rubbing lotion din, ta ringa kallon gashin kanta da duk kitson ya fara warwarewa da kansa, bai ɗauketa wani minti 20 ba ta gama tsefe ƙananan kitson kanta tass, daga ta kama jelar zugeta kawai take cause gashinta mai laushi da santsi ne na fulani, combing hair din tayi ta shafa masa oil shima da ta gani, tayi parking dinsa a ƙeya ta tufke jelar, daga haka ta tashi daga gaban mirrorn, ta buɗe huge wardrobe tana taɓe baki, ita dama a box Hafsah ta bar mata kayanta, wata doguwar riga ta atamfa ta saka, ta zumbula hijab ta fita a ɗakin ta sauka ƙasa da cup da plate din jiya da taci kayan gara, kayan garar ta sake ɗiba taci a kitchen din tasha ruwanta a famfo kafin ta fito ta koma room dinta, tanata zaune a ɗakin saidai tayi game a wayarta inta gaji ta ajiye har akay sallar Azahar, tana idar da sallah taji wata yunwa ta bijiro mata, kayan garar dai ta kuma ɗurawa cikinta, samm taƙi yin girki sbd gani take knn ma rayuwa mai tsayi zata yi, palour ta fito ta ringa kallon ƙofa kafin ta matsa kusa da ita ta kama handle ta murɗa, a rufe taji ƙofar, ta koma kitchen ta buɗe ƙofar da zata sadaka da backyard din gidan, luckily ta jita a buɗe, ta ringa kallon backyard din tana ɗan zagawa, ta zauna kan wani dakali da ta gani wanda shine chamber na ruwa, sosai zaman wajen yayi mata daɗi don ji tayi kamar an cirota daga maƙabarta, ba tasan iya awannin da ta ɗauka zaune a wajen ba tana tunani iri iri, motsin zubar ruwa ta jiyo daga front din gidan, tashi tayi ta ringa bin inda motsin yake, mai gadi ne ya kunna famfon compound din yana alwala, ɗan russunawa yayi ganinta ya kashe famfon yace "ina wuni Hajiya..", Hajar ta mayar masa da gaisuwar don ta ganesa ranar da suka dawo gidan shi suka tarar, Inuwa ya duƙar da kai yace "wani abin za a amso miki hajiya...?", Hajar ta girgiza kai ta juya ta koma backyard din, ciki ta koma don yin sallah, tana idar da sallah wayarta ta fara ringing, ta ringa kallon screen ɗin wayar ganin number ke kiranta kuma bata san numbern ba har kiran ya katse wani ya sake shigowa, picking tayi ta kara a kunne ba tace komai ba, wani murmushi tayi bayan ta ɗau murya tace "Noor...", Noor tayi dariya tace "ta ya akay kika gane...?", Hajar tayi ƴar dariya tace "your voice mna", Noor tace "toh ykk ya gida...", Hajar tace "lfy lou and you..?", Noor tace "am great wllh..", Hajar tace "good, toh yaushe zaki zo..?", zaro ido Noor tayi tace "not soon..", Hajar ta marairaice murya tace "kefa kika ce zaki zo..", Noor tace "yeah zan zo amma ba yanzu ba..", Hajar tace "toh shknn sai kinxo", sun ɗan jima suna hira da Noor kafin daga karshe Noor tayi mata sallama, Hajar ta tashi ta naɗe darduman da tayi sallah, sai kace wata ƴar kurkuku haka take jin rayuwar gidan, daga ƙarshe dai ta fara gyara ɗakinta wanda babu wani datti ta masa turaren wuta wai dan duk ta ɗan ware, taje kitchen ta ciko plate da kayan garar da ta mayar abinci, da kyar ta iya hawa stairs bayan ta fito daga kitchen sbd ƙullewar da cikinta yayi, ta samu dai ta shiga ɗakinta ta zaune gefen gado ta danne cikin da yake kan murɗa mata, bayan wani lokaci cikin na murɗawa sai ta fara yin ƙalas, maiƙon Alkaki yazo ya tsaya mata a wuya har tana jin kamar za tayi amai. ★ƙarfe biyu da ƴan mintina Nurain ya fito daga office dinsa holding his briefcase, saida yayi attending kaf patient da suka zo shiyasa ya kai wnn time din, acikin doctors da suke aiki a hospital din shine me wnn halin, indai kaga kazo ganinsa bai duba ka ba toh akwai babban dalili amma duk yawan patient yana squeezing ya duba su, Ruqayyah dake zaune bakin office din over three hours tana jiran fitowarsa ta tashi da sauri tabi bayansa, tana zuwa gaf dashi tace "Dr..", dakatawa yayi da tafiyar ya jiyo yana kallonta ba tare da yace komai ba, kallon da yayi nata sai taji gaba ɗaya ɗan guntun courage dinta ya narke gami da tsiyayewa ta guiwarta, ta kasa cewa komai amma lips dinta sai ɓari suke, shi kam da yasan ma itace wllh bazai dakata ba, shi Allah ya masa wani hali na bagarar da lamari indai ya bar abu topa shknn, don yanzu idan nace muku ya manta muryarta ne shiyasa ma har ya juyo data kirasa kar kuyi mamaki, ya haɗe thick eyebrows dinsa ya juya ya cigaba da tafiyarsa, Ruqayyah tayi ajiyar zuciya ta lumshe idanunta da suke mata zugi tsabar kukan da ta sha, da sauri ta kuma binsa sai kace mayya tace "dan girman Allah Dearest kayi haƙuri, make time for us so that we can discuss about it, i will tell you all what happened...", har suka fito harabar hospital din tana biye dashi tana masa magiya, ganin ba sauraronta zaiyi ba ta tsaya a ƙofar department din gudun kar ta dizga kanta a public, Nurain yana isa parking space ya shiga motarsa, keys ya zura a ignition ya kunna motar, har lokacin girarsa a haɗe take don ba ƙaramin fama masa zuciya waccar psycho din tayi ba, he dislike the sight of her, direct gidansu ya dosa don bazai koma gidansa yaga wani abun da zai sake ɓata masa rai ba, bayan yayi parking motarsa ya shiga ciki. Mami na zaune a main palourn da wasu close friends dinta guda biyu, ya ƙarasa shiga palourn ya gaishesu duka da ladabi, Mami dai tayi mamakin ganinsa a wnn lokacin it seems like daga wajen aiki yake shine ya zarto nan a maimakon gidansa, shidai yana gama gaidasu ya wuce upstairs, Mami ta bisa da kallo, Haj Sadeeya tace "Aaa aha ashe duk munyi furfura don Allah kalli yadda yaron nan ya koma Nurainin Mami, kinga ma ban tambayesa iyalin ba don ina Canada kika gayamin zancen aurensa...", Mami tayi yaƙe tace "matarsa na nan lfy baifi kwana goma da yin auren ba..", Haj Sadeeya tace "kwana goma kuma nifa mganar almost one year nake miki..", Haj Fati tace "ni dai nasan wancan an fasa yinsa, bayan nan ma Nurain din ya koma India, toh dai wnn na kwana goman ne bansan dashi ba.." ta fadi hakan tana kallon Mami, Mami ta kallesu duka tace "wllh auren ne yazo unexpected, nima kaina saida aka ɗaurasa na sani, prof ne ya haɗasa da ƴar abokinsa, shima yaron ba sani yayi ba don lokacin ma bai dawo ƙasar ba..", Haj Sadeeya tace "duk ba labari da fasa wancan din da kuma sabon, toh in banda abinki Mami aiko baza mu zo ba ai kya gaya mana", Mami tayi ajiyar zuciya tace "duk kuyi haƙuri abin ne yazo unexpected shiyasa, ba a nitse nake ba wllh". uku da minti goma Nurain ya sakko har yayi wanka ya sauya kayan jikinsa, yana kallon Mami yace "Noory fa..", Mami tace "bata dawo schl ba..", yace "Okay" yana kallon hanyar kitchen kafin ya wuce can din, kitchen din ya shiga bayan few minutes ya fito da plate din Abinci, dining ya wuce ya zauna ya fara cin abincin, saida ya cinye tass don yunwa yake ji ba kaɗan ba tin tea da yasha da safe bai sake cin komai ba banda water, Nurain bai baro gidansu ba sai ƙarfe takwas na dare, a hakan ma sbd Mami ne dan ya lura da irin kallon da take masa ga dukkan alamu tana so ta fadi wani abun ne amma bata fada ba, yana zuwa gida daman a palourn ƙasa yayi branching, yayi powering TV kafin ya zauna kan exclusive sofa dake palourn, almost 30mins da zamansa aka buɗe ƙofar kitchen, da sauri ya kalli direction din, a hankali ta fito daga kitchen din da cup ta ciko da ruwa, ta juya ta rufe ƙofar, ƙishi ruwa ne yasata fitowa tin ɗazu, shine da tazo kitchen ɗiba ciwon cikin ya murɗa mata ta durƙushe a ƙasan kitchen din tana murƙususu har saida taji dama dama snn ta iya tashi ta ɗebi ruwan ta samu ta fito, wani irin haɗe rai Nurain yayi, wato bata ji warning din da ya mata ba knn, how dare her zata ringa masa taurin kai, who born her with her bad attitudes, dole tayi abinda yace indai tana son cigaba da zama a gidan, furiously ya tashi yace "ke ba kiji warning din da na miki ba knn..", hannunta ɗaya riƙe da cup dayan kuma ta dafe cikinta, da kyar ta iya cewa "daman nace maka naji ne.., na riga na gaya maka you can't tell me what to do malam" tana gama fadin haka ta nufi stairs, bata ankara ba taji an fixgota baya ta bige da hannun kujera.....✍️ Chapter 46.... on Arewabooks.... 💛 HAJAR 💛 na Nafeesah Yusuf Nagoda A.K.A Feenerh feeche {46..} Nurain was extremely angry at that moment, yana mata wani kallon barazana yace "maimaita abinda kika ce..", ta ja da baya zuciyarta na lugude tace "bazan maimaita din ba, idan baka ji ba kai ka sani...", da sauri ta durƙushe ƙasa ta ajiye cup din ruwan ta damƙe cikinta tana murƙususu, fashewa tayi da kuka tana yarfe hannu tace "na shiga uku cikina", tsuke idanunsa yayi ya matsa daga kusa da ita yana kallonta, after looking at her for few seconds yace "hey get up..", banza tayi dashi ta cigaba da kukanta a hankali, folding hands dinsa yayi yace "ke tashi daga nan...", duk da irin azabar da take ji hakan bai hanata ɗaga kai ta zabga masa harara ba, ya koma kan kujera ya zauna gami da ɗaukan remove ya ƙure volume din Tv don baya son ya cigaba da jin sautin kukanta, saida cikin ya lafa mata bayan kamar minti goma ta tashi tana goge fuskarta, ta ɗauki kofin ruwan ta haura sama tana tafiya a hankali, bayanta yabi da kallo bai san lokacin da wani tsaki ya kufce masa ba, ya tashi ya kashe Tvn gaba ɗaya, kitchen ya shiga yana ƙare masa kallo, ya buɗe store ya duba ko ina, yadda ya ajiye foodstuffs haka ya gansu ba a taɓa ba, carton din Noodles kawai ya gani a bude kuma shima pack ɗaya aka ɗauka, ya fito daga storen ya buɗe fridge shima dai babu abinda aka taɓa, ganin bottle water shima ko ɗaya ba'a taɓa ba murya ƙasan maƙoshi yace "what.. toh wane ruwa take sha..", bottle water ya ɗauka ya rufe fridge din snn ya bar kitchen din, upstairs ya haura zuwa part dinsa, direct bedroom ya shiga ya kunna lights, yayi drawing bedside drawer ya ɗauki wani satchet na drug, tashi yayi ya fito daga bedroom din snn ya fita daga part din, tsaye yayi a corridor yana kallon ƙofar ɗakinta, after standing for few seconds ya haɗe gira ya murɗa handle din ƙofar ya shiga, ƙasa ƙasa yayi sallama wanda ta tsaya iya lips, kwance ya ganta kan carpet ta rufa da duvet har ka, ya ƙarasa cikin ɗakin bayan yabar door a wangale, controlling ɓacin ran dake taso masa yayi, chest of drawers ya bubbuga yace "hey", ta yaye rufar da tayi ta tashi zaune, kallo ɗaya ta masa ta ɗauke kanta, fuskarsa a haɗe ya ƙara four steps towards her, dungurar da bottle water din yayi a gabanta, ta juyo ta kalli ruwan ta ɗaga kai ta kallesa, ya ajiye satchet din drug din yace "take it..", ta haɗe gira tace "bazan sha ba...", one step ya kara getting even more closer to her, tayi sauri ta muskuta ta bada space a tsakaninsu, taɓe baki yayi yace "an gaya miki nayi hakan ne sbd ke, hmm you don't worth it ba dan ke nayi ba, darajar Abba kika ci, tinda an riga an liƙa min ke babu yadda zan iya and now we are living in the same roof, so listen tinda kema kin nace kina son auren nan toh ga fili ga mai doki, zaki zauna anan amma kuma bazaki jamin matsala ba, na fita haƙƙina na ajiye miki foodstuffs, you are free ki shiga kitchen ki dafa abinda za kice idan kinga dama, don babu wanda zai miki gage, secondly you see this room da downstairs palour and kitchen are the only places da kike da damar shiga daga su kar kiyi gigin shiga wani wajen, and if you need anything bance kimin magana ba, ki nemi pen da jotter ki ajiye duk sanda kike buƙatar wani abu ki rubuta ki ajiye kan center table a palour, i will give that idan baki da shi, am done with you...." da haka ya isa gaban mirror ya ɗauki cup din da ta ajiye, girgiza kai yayi yana kallon ruwan kafin ya juyo ya dubeta yace "for your own heath tap water ba shine ruwan sha a nan ba...", ƙofa ya nufa zai fita yaji tace "malam ka gama, dawo ka ɗauki tarkacen da ka zube min a nan who are you to give me drug, kai tinda aka kawoni wnn ƙaddararran gidan na taɓa mka magana ne da farko da kake cewa wani kar na maka mgana, kaga malam nifa ba mara galihu bace da zaka ringa giggilamin sharuɗa sai kace wata ƴarka, ni nan na fika tsanar wnn jarababben auren wllh, da zaka sauwaƙe mna da ka huta..." ta ƙarashe tana murguɗa baki gami da hura siririn hancinta, bai motsa daga inda yake tsaye yana kallonta ba, tana lura da reaction din fuskarsa zuciyarta ta buga da ƙarfi, tayi sauri ta yaye duvet din da ta lulluɓe jikinta ta miƙe tsaye fuskarta a haɗe, lokaci guda ta dubi kanta, kayan bacci ne a jikinta riga da wando, ai kam da sauri ta durƙusa ta yayibi duvet din ta rufe jikinta, kamar me ƙirga takunsa haka ya fara walking towards her, ganin haka yasa ta fara tafiya da baya tana banka masa harara, da gudu ta shige bathroom tana taɗewa da duvet din, tayi sauri ta saka lock tana sauke numfashi, Nurain ya sauke ajiyar zuciya yana bin ƙofar bathroom din da kallo kafin ya juya ya fita daga ɗakin, jingina Hajar tayi da jikin ƙofa, ta hura hanci tace "Wllh ka gayamin ajali sai na gaya mka mutuwa, haka kurum ba zaka danƙaramin magana nayi shiru na kyaleka ba zuciyata ta buga, kai da kanka zaka koma wajen wnda ya ƙulla wnn jarababben auren ya kunce sa ehe, dan billahillazi la'ilaha illa huwa yanxu na fara musguna maka a gidan nan, kai ka isa ka aureni kai asuwa...", ita kaɗai ta ringa huci sai kace wata kububuwa, bayan kamar minti goma ta buɗe ƙofar a hankali, ta gama surveying ɗakin da idanunta kafin ta fito, tsaki tayi taje ta rufe ƙofarta, tasa ƙafa tayi fatali da bottle water da satchet din maganin dake kan carpet, ta sake yin wani tsakin tayi kwanciyarta, tsakar dare ciki yace ba sai kiyi baccin na gani ba, duk da sanyin AC gumi ne ya ringa tsattsafo mata a goshi, ganin alamar dai cikin nan ba lafa mata zaiyi ba ta tashi zaune, a gigice ta fara laluben maganin tana rarrafe, taci sa'a kam ta hango sa a karkashin mirror, ta ƙarasa bakin ƙofa ta ɗauki ruwan da ta wurga can, da sauri ta buɗe bottle din ta ɓalli 2tablets ta afa a baki ta bisa da ruwa, within minutes Allah ya taimaketa cikin ya lafa, ta ringa kallon satchet din maganin kafin ta tashi ta ajiye bisa mirror ta koma ta kwanta. washe gari wajen ƙarfe takwas da rabi Hajar ta fito daga ɗakinta bayan tayi wanka ta shirya, downstairs ta sauka zuwa kitchen, tana buɗe ƙofar kitchen sukay ido huɗu da Nurain da ke making coffee, da sauri ta rufe ƙofar ta haura sama, Nurain ya kashe coffee makern bayan ya gama haɗawa, zai ɗau cup din Coffeen knn wayarsa ta fara vibrate, da asuba ya dakkota daga mota bayan ya dawo masallaci, ya duba yaga babu wani missed call kuma luckily wacca tasa ya tsani wayar bata kira ba kuma bata turo message ba, ya ciro wayar daga pocket yayi picking ganin Dr Marwan, fita yayi daga kitchen din still yana wayar, Nurain yace "alright send it now..", Dr Marwan yace "Okay", Nurain yace "when is it going to start..?", Dr Marwan yace "12noon insha Allah...", Nurain yace "Neh, i will be there before then..", Dr Marwan yace "thank you Dr..", Nurain ya katse wayar ya haura sama ya shiga part dinsa, Laptop dinsa dake jone a charge ya ciro ya zauna yayi switching dinta on, tana gama booting ya buɗe WiFi, it connected automatically with the house router, ai kam sai ga mail daga Dr Marwan, Nurain ya bude mail din yana duba hoton jiki, almost 30mins yana examining picturen, it is a human chest diagram, a zuciyarsa wondering yake who is this patient with a damage lungs. Hajar ta sake sakkowa ƙasa don yunwa take ji sosai, plain Noodles ta dafa ta juye a plate, tinda ta shigo kitchen din take kallon Cup din dake cike da Coffee, bayan ta gama tafasa tea ta juye a cup ta zuba sugar da lipton, har zata fita da shayi da Noodles dinta a hannu sai kuma ta dawo da baya, ta ajiyesu kan kitchen island, store ta shiga ta ɗakko ledar gishiri ta fito, farke ledar tayi ta ɗauki spoon ta matsa wajen Coffeen, ta zuba cokali biyar cikakku na gishiri a Coffeen tana murmushi, ta mayar da gishirin store ta fito tana kakkaɓe hannunta tace "Asha shayii lfy.. counting from today..." kafin ta ɗauki plate din Noodles da kofin shayinta ta fita. Nurain ya shigo kitchen din bayan fitar Hajar da minti biyu, direct Coffeen sa ya ɗauka, ya ringa kallon coffeen ganin kamar ya ƙara yawa, gashi kuma it is not hot but warm, tinda it is warm he can take it, Sipping yayi domin yaji temp din dai a bakinsa, guntse wanda ya kurɓa yayi ya yamutsa fuska, lokaci guda ya isa gaban sink ya zubar ya kunna tap ya wanke bakinsa, har lokacin wani irin taste yake ji a bakinsa wanda ya kasa gane masa, ya ringa kallon Coffeen kafin ya sheƙar dashi ya bar kitchen din, yana zuwa ɗakinsa ya wuce bathroom ya shiga wanke bakinsa da mouth wash har saida yaji taste din ya ragu sosai. ★Tin daga soro Sa'adatu ta fara zabga sallama harta shiga cikin gida, wani kallon hadarin kaji ta watsawa Umma dake zaune kan ƙaramar kujera tana shafa manja jikin gwangwanaye, ɗakin Maama ta shiga, Maimuna dake zaune kan gado ta bita da kallo tace "kin dawo..?", Sa'adatu ta saki baki tana kallon Maimuna kafin ta yakice hijab din da ta zumbula a jikinta, wasu irin matsattsun kaya ne jikinta wanda ya bayyana shape din bom bom dinta da ƙirjinta, ta zauna kusa da Maimuna ta sake ƙare mata kallo tace "ke kuma wa ya mayar dake wnn mummunar halittar, babur ne ya bigeki...?", Maimuna ta shafa goshinta tace "idan na gaya miki Allah yasa ki yarda.., wai fa Mu'azzam ne yamin haka..", Sa'adatu ta hangame baki tace "Mu'azzam din ne ya miki haka...?", Maimuna da takaici ya kuma maƙureta tace "shifa..", Sa'adatu tace "chaɓɗi jamm, wato har dasu kaza acin danƙo, ke me ya haɗani da wnn jakin har yayi miki haka...?", Maimuna ta kwashe kaf abinda ya faru ta gaya mata, Sa'adatu ta ringa jinjina kai tana hura bubble da chewing gum din bakinta, Maimuna ta kwashe cinya tace "kinga walmukalafatun da Baba yayi min..", Sa'adatu tace "karki yarda wllh tllh, toh aiko shinkafar ɓeran kika zuba iya abinda za a miki knn, karki haƙura wllh..", Maimuna tace "ke ko ce miki akai zan haƙuri zaki yarda ne, dan na rantse da zabbatin Ubangiji bazan yarda ba..", Sa'adatu ta karyar da kai tace "wllh karki haƙura wannan halittar da ya mayar dake ai ya cuce ki, fuska duk ta suntuma, ji fa yadda idanunki suka koma ciki sai kace fuskar biri bukka, kibi dare idan ya kwanta ki rusa masa taɓarya a ka..", Maimuna tace "A'a ni bazan taɓasa da hannuna ba, dafa kuɗina a ƙugu, ƴan daba zan biya su lakaɗa masa duka su sassara banza su jefar a layii", Sa'adatu ta sheƙe da dariya tace "hakan yayi... wai ina Maama da waccan mai kai a tukunyar...?", Maimuna tace "Maama ta fita bansan inda taje ba, Nabilah kuma ta fita auno shinkafa...". babu jimawa Maama ta shigo gidan bayan ta dawo daga gidan Balaraba, ganin Sa'adatu Maama ta yaƙe haƙora tace "Sa'adatun Maama kin dawo...?", Sa'adatu tace "nadawo Maama..", Maama tace "ai kinga haka yafi kin cika alƙawari, kinga gobe ma sai nasan ƙaryar da zan shiryawa malam idan ya tambayeki, ina ƴan albarkar ƙawayen naki kuwa...?", Sa'adatu tace "suna nan kalau Maama sunce ma na gaisheki..", Maama ta washe haƙora tace "Ahh ina amsawa kuwa..", Nabilah ta shigo hannunta riƙe da baƙar leda, kallo daya ta yiwa Sa'adatu ta ɗauke kanta, hijab dinta ta cire zata fita Maama tace "haba Annabilatuwa biki ga ƴar uwarki ba", Nabilah ta juyo tace "Au sannunta toh" da haka ta fice a ɗakin, gawayi ta zuba a kurfotu ta tashi wuta, tana fifita wutar Naseer ya shigo, ta masa sannu da zuwa ya amsa a taƙaice, Maama ta leƙo tace "A'a Nasiru sannu da zuwa..", Naseer ya ajiye doyar da ya shigo da ita ya russuna ya gaisheta, Maama tace "lfy lou, ya wajen aikin..?", yace "Alhmdllh an gode Allah..", bai tambayi Baba ba sbd yasan dai a wnn lokacin Baba ya fita aiki, ganin haka yasa Nabilah tace "Yaya Baba yana nan fa..", yace "toh" ya shiga ɗakin Baban da Sallama, Maama ta zabgawa Nabilah wata harara tace "naga ranar da wnn munafikin canjin naki zai ɗore..", bayan Naseer sun gaisa da Baba yace "Baba ko dai jikin ne..?", Baba ya numfasa yace "Nasiru duk ranar da kuka wayi gari bani toh mahaifiyarku ce sila..", Naseer ya kasa cewa komai tsabar ydda mgnar Baba ta dakesa, can dai yace "Ayi haƙuri Baba, Allah ya huci zuciyarku..", Baba yace "haƙuri ai ya zama dole tinda ta gama zubamin virus ta haifeku...", Naseer dai kawai haƙuri ya ringa basa duk da cewa bai san me ya faru ba. ★Kamar yadda Nurain yace kafin 12noon zai iso hospital, 11:40 ya isa hospital din, yana shiga office dinsa yasa Haleema ta kira masa his team members, har zai wuce sai kuma ya dawo yace "exclude A Nurse, call Nurse Amina instead..", Haleema tace "yess sir", ta ɗauki landline ta shiga kiran members din, babu jimawa kam All of them suka hallara a office din, Nurse Amina ce kawai ba tazo ba, briefing dinsu Nurain yayi akan surgeryn da zasu shiga, daga nan suka fita to get ready, Nurain na wanke hannunsa kafin ya shiga surgery room din Khaleel ya da already dressed up in surgeon gown da nose mask a fuskarsa amma bai rufe hancin ba ya iso wajen yace "Boss everyone is here banda Nurse Amina, kuma i informed her tace tana zuwa..", Nurain na cigaba da wanke hannunsa yace "lets wait for her since the surgery is not yet started...", Khaleel yace "sure..", Nurain na gama wanke hands daman already ya sanya surgical Scrub. Surgery room din ya shiga, wani Nurse dake riƙe da surgeon gown ya ƙaraso kusa da shi helping him to wear the gown, Nurain ya saka nose mask da hand gloves kafin ya isa position dinsa na head of the surgery ya tsaya, patient din daman tintini aka masa anesthesia. Ruqayyah na zaune Nurse station duk abin duniya ya isheta, tinda tazo babu wani aikin arziƙi da tayi kawai safa da marwa take tsakanin Nurse station da Office din Nurain, taje office din yafi sau biyar saita tarar baizo ba, Nurse Amina ce ta shigo station din in a hurry tace "please Ruqayyah ki kulamin da ward C ina dawowa..", Ruqayyah tace "ina zaki haka..?", Nurse Amina ta dafe goshinta tace "Dr Uthman ne yake nemana a surgery room..", miƙewa Ruqayyah tayi tace "surgery zaiyi knn..?", Nurse Amina tace "eh..", wani irin ɗaci Ruqayyah taji ya taso mata daga zuciya, she is part of the team toh me yasa ake neman wata Nurse din bayan gata, Nurse Amina tace "Please Rukky..", Ruqayyah ta girgiza kai tace "A'a gaskiya bazan kula miki da ward ba saidai ke ki zauna in shiga surgeryn", Nurse Amina tace "ai kwa da na fi son hakan ma, nagode sosai..", Ruqayyah tace "don't mention" da haka ta bar station din walking fast, surgery gown ta ɗora kan uniform dinta ta saka nose mask da gloves kafin ta shiga surgery room din kanta a ƙasa, with respect ta ɗan russuna tace "sorry Dr..", Khaleel yace "come closer..", ta ƙarasa ciki tana satan kallon Nurain, surgery tray ta dauka ta tsaya position dinta, ta ɗauki Scalpel ta miƙawa Nurain, da haka aka fara surgeryn, kawai aikinsa yake cike da nutsuwa yayinda Ruqayyah ta kafa masa idanu tamkar zata cinyesa, wani sa'in ma sai yace ta basa instrument snn take basa sbd rashin nutsuwa, a haka dai har suka gama surgeryn, bayan an fita da patient din sauran doctors din ma sun fita Nurain ya cire hands gloves yayi disposing, sauke nose mask din fuskarsa yayi ya wuce zai bar room din, Ruqayyah tace "Dr...", ya juyo yace "yess Nurse Amina...", idonta yayi rau rau ta kai hannu ta zame nose mask dinta....✍️ Chapter 47.... Arewabooks @ feenerhfeeche02 💛 HAJAR 💛 Feenerh feeche ce {47..} Da mamaki Nurain ya ringa kallonta dan bai taɓa tunanin da ita akay surgeryn ba Nurse Amina ba, Ruqayyah ta sauke idonta ƙasa a hankali tace "the surgery was a success, alhmdllh..", baice mata ƙala ba ya juya ya fita daga surgery room din ya barta tsaye, tabi bayansa da kallo hawayen da suka taru idonta suka fara bin kuncinta, fita tayi daga room din bayan ta gama matsewa, ta cire surgeon gown kafin ta wuce Nurse station, bag dinta ta buɗe ta ɗauki black Abaya ta ɗora saman uniform dinta, daga haka ta saƙala jakarta a shoulder ta yiwa colleagues dinta sallama ta bar hospital din, tana fita titi ta tari napep ta gaya masa unguwar da zai kaita, shiga napep din tayi bayan sun gama ciniki, tafiyar minti ashirin ce ta kaisu unguwar, ya shiga da ita har layin da ta masa kwatance, sauka tayi daga napep din ta buɗe handbag dinta ta ciro kuɗinsa ta basa, ya miƙa mata chanjinta yaja machine dinsa, wani gida mai brown paint da black gate ta dosa ta fara knocking, almajirin gidan ne ya buɗe mata, bayan ta shiga ya gaisheta ta amsa a takaice kafin ta nufi entrance din gidan, ta buɗe ƙofa ta shiga palour da sallama, ƙarewa palourn dake tashi da ƙamshin turaren wuta gauraye da na freshner kallo take sai kace wani baƙonta, ta sake yin wata sallamar kafin ta zauna kan kujera, ƙofar wani room dake palourn aka buɗe, Kulsoom ta fito da 2months old babyn ta goye a baya tana jijjigasa, ganin Ruqayyah tace "Ruqayyatu kece kika ta sallama sai kace wata baƙuwa..", Ruqayyah ta cire ƙaramin hijab dinta tayi resting da kujera tace "ina wuni sister..", Kulsoom ta ƙaraso cikin palourn tana jijjiga babyn dake ƙishi ƙishin kuka tace "mun yini lfy...", Ruqayyah tace "alhmdllh..", Kulsoom na kallon fuskar ƴar uwarta ta da ta lura tayi duhu tace "kin kwaso rana..", Ruqayyah tayi ajiyar zuciya tace "kawosa naga kamar kuka zaiyi..", Kulsoom ta kwanto babyn ta miƙa mata tace "rigimamme ne wllh.." da haka ta wuce kitchen, Ruqayyah ta ringa kallon Babyn kafin ta lakuce masa hanci tace "shine kake wa sister na kukan banza ko, tubarkallah ga ka dai narkeke sai kace ba watanka biyu ba bare ace yunwa kake ji", ta ringa patting soft cheeks dinsa, deeply in her mind taji dama babyn ta ne, da anyi aurenta da Dearest da tini itama ta kusa haifar baby, Kulsoom ta fito kitchen da tray a hannunta, ajiye trayn tayi kan Centre table tace "toh ga ruwa kisha kafin na gama girki na ga kinyi wani wujiga wujiga...", Ruqayyah tace "na gaji ne, kuma gashi na shiga surgery yau na 3hours", Kulsoom dai ta gyaɗa kai tace "Okay", a ƙasan ranta tasan bayan gajiya akwai damuwa a tattare da Ruqayyah, Ruqayyah ta zuba ruwa tasha tana jin yadda sanyin ruwan ya sanyaya mata maƙoshi, bayan kamar 15mins Kulsoom ta tashi ta shiga kitchen, babu jimawa ta fito da plate da bowl a hannunta, Ruqayyah ta ringa kallon abincin tana jin appetite dinta na dawowa, lafiyayyen dambun shinkafa ne wanda yaji attaruhu da albasa da gyaɗa yana bayar da wani ƙayataccen aroma, sai kuma coleslaw a bowl, Ruqayyah ta janyo abincin tana ci a hankali, kallonta Kulsoom ta ringa yi tana feeding babyn ta, saida taga ta ture plate din alamar ta ƙoshi tace "kin gama....?", Ruqayyah tayi gyatsa tace "alhmdllh, godiya dubu..", Kulsoom na shafa kan babyn ta looking at Ruqayyah tace "now tell me, me yake damunki sister...?", Ruqayyah ta zaro ido tace "Ni.. me kika gani..?", Kulsoom ta saka serious face tace "haba Ruqayyah nifa ƴar uwarki ce na sanki ciki da bai, wllh there most be something troubling you, ji fa yadda kika rame kuma kinyi duhu ai ba haka hasken ki yake ba..", Ruqayyah bata san lokacin da hawaye ya fara zuba cheeks dinta ba, Kulsoom ba tace komai ba kawai kallonta take, Ruqayyah ta share hawayen tace "tin lokacin da na dawo Daddy ya yankamin warning cewa na fito da miji shi aurar dani zaiyi idan kuma banyi hakan ba zai aura min Dauda, Dauda fa wnn mai bacogalar ƙafar, da kyar da maƙyarƙyata na shawo kan Momy ta shigemin a wajen Daddy bayan na shirga mata ƙarya nace ai mun sasanta da Dr, idan ya dawo daga tafiya za a ɗaura mna aure, da haka na samu abubuwa suka lafamin a wajen Daddy, sister wllh na gama sakankancewa ina tutiya da irin son da Dr yake min kawai jira nake ya dawo na basa haƙuri, and now he is back almost 2weeks da dawowarsa, nayi kiran a waya na tura text message amma duk a banza, babu kalar haƙurin da ban rubuta a message na tura masa ba amma he didn't respond to any of it, ke na ƙarƙare miki mgana jiya har office dinsa naje ina basa haƙuri amma yaƙi saurarata, daga ƙarshe ya kiramin security, yau kam he kick me out of the surgery team..", Ruqayyah ta fashe da kuka tace "wllh Allah ina sonsa, i can't live without him Allah kuwa..", Kulsoom ta jinjina kai ta kwantar da Babyn da ta gama feeding tace "gsky kinyi babban kuskure da kika yiwa Momy ƙarya Ruqayyah..", Ruqayyah tace "toh ya zanyi sister dole ce tasa na mata ƙaryar nan, da banyi haka ba da tini an wuce wajen an auramin Dauda bacogala..", Kulsoom tace "ke kika fusata Daddy shiyasa ya kafe sai ya aurar dake, Ruqayyah yau inda ace baki aikata abinda kika yi ba wllh kinji dai har na rantse babu abinda zai sa Daddy ya miki auren dole, zai dauka cewa Allah ne bai kawo lokacin aurenki ba, amma akazo akay komai da komai ranar ɗaurin aure kika kwashi ƙafa kika gudu...", Ruqayyah ta kastseta da faɗin "wllh ba guduwa nayi ba..", Kulsoom ta haɗe gira tace "let me land malama, idan ba guduwar ki kay ba toh uban me ki kai, yanzu dai ina baki shawara kije ki gayawa Momy cewa ƙarya kika shirga mata snn kuma ki haƙura da wani Dr, yo Allah na tuba mazan yanzu har wasu abin so ne, an gaya miki in this era ana yiwa namiji makahon so ne, namiji ya soka ma yaka ƙare da wulaƙancin sa ballantana wanda ya fito ra'ayil aini ya nuna baya sonka, idan Dr ya soki a baya toh yanzu ba hakan bane, ai kin masa narkakken wulaƙanci ba ƙarya duk abinda ya miki ke kika siya da kuɗinki, so wake up malama ki san inda yake miki ciwo, kin zauna kina wani ɓare baki kina kuka shaɓa shaɓe akan wani namiji.... ehen ki ajiyesa a gefe ko shine autan maza", tinda ta fara magana Ruqayyah ta saki baki hanci kunne tana kallonta tamkar wata psycho, idonta har wani wulƙilewa yayi tsabar yadda take kallon Kulsoom cike da ruɗin abinda ta gaya mata, Dearest din zata ajiye a gefe, da kyar ta iya cewa "wai doctorn zan ajiye a gefe..?", Kulsoom tace "yhap shi din mna tinda kinyi loosing opportunity tin farko...", Ruqayyah ba ta sake cewa komai ba ta fara haɗa kayanta, ta saka wayarta a jaka, hijab dinta ta sanya kafin ta miƙe ta fara zura Abaya, Kulsoom ta bita da ido, Ruqayyah na gama saka Abayar ta ɗauki handbag dinta tace "sai anjima", Kulsoom ta taɓe baki tace "mu jima da yawa..", ficewa Ruqayyah tayi daga gidan fuskarta a haɗe, da badan Kulsoom ƴar uwarta bace da babu abinda zai hanata danƙara mata baƙar magana, kuma taci sa'a elder sister dinta ce yau da ace itace gaba da Kulsoom to babu abinda zai dakatar da ita daga kwalla mata marii, wai ta ajiye Dearest a gefe wato ta rabu da shi, never ever babu abinda zai sa ta rabu da shi sai mutuwa, tana isa bakin titi ta tari napep zuwa gida. ★Hajar ta gyara ɗakinta fes bayan ta gama cin Noodles da ta dafa, ta rufe ɗakin ta sauka downstairs zata kai plate da cup din da tayi amfani dasu kitchen, gaban sink ta tsaya tana kallon liquid soap dake wajen, ta kunna pampo ta matsa liquid soap din a plate ta tashi foam, sponge ta dauka ta fara wanke utensils din da ta ɓata, tass ta wankesu ta kife a inda ta ɗauka, duk da kitchen din babu datti amma saida ta sake gyarasa, tayi drying hannunta da towel kafin ta fita daga kitchen din, room dinta ta koma tayi zugum sai kace wata prisoner, can dai ta gaji da zaman daƙin ta tashi ta fita, ta kitchen tabi ta fita daga gidan zuwa backyard, through out the day anan tayi zamanta kamar dai jiya sai idan za tayi sallah ne take komawa ciki, bayan ta idar da sallar la'asar ta birkito kayan da ta saka set biyu sai nities da hijab biyu, toilet ta shiga da kayan ta zazzaga detergent a bucket ta shiga wankesu duk da cewa ba suyi wani datti ba, tana gama wankewa ta ɗauraye toilet din ta fito da kayan cikin bucket, can backyard din ta wuce ta shanya kayan jikin flowers, tana cikin shanyar saiga mai gadi da watering can a hannunsa zai bawa flowers ruwan yamma, dan russunawa yayi ya gaisheta ta amsa kafin ta ɗauki bucket din tabar wajen dan ta gama shanyar, tana shiga palour taji kamar ana buɗe main door din gidan, ta ringa kallon ƙofar har aka buɗeta, Nurain ne ya shigo Farooq biye dashi, suna yin ido huɗu tayi sauri ta ɗauke kanta ta wuce zata haura sama taji ance "Amarya..", dakatawa tayi amma bata juya ba, Nurain ya wurgawa Farooq wani kallo kafin ya wuce ya haye sama, Farooq ya ɗaga shoulder ya ƙarasa cikin palourn, a hankali Hajar tace "ina yini..", Farooq yayi murmushi yace "lfy lou amarya.. how are you..", tace "am fine thank you.." da haka ta nufi stairs ta haura sama, Farooq ya zaune kan kujera ya ciro wayarsa daga pocket yana latsawa, after 20mins yana zaune palourn ya daga kai yana kallon stairs, contact ya shiga yayi dialing numbern Nurain har ta gama ringing bai ɗauka ba, babu jimawa saiga shi nan yana sakkowa, Farooq ya ringa kallonsa har ya ƙaraso palourn yace "muje..", Farooq bai motsa ba yace "daga ɗakko paper saika tsaya wanka kuma..", Nurain ya nufi door yace "c^mon let go..", Farooq na fitowa Nurain ya rufe ƙofar da mukulli, shidai Farooq yana so yace wani abun amma dai ya fasa, a tare suka nufi gate, Inuwa dake zaune nan bakin gate din yayi saurin miƙewa har suka ƙaraso, russunawa yayi ya gaidasu duka, shidai bai san lokacin da suka shigo ba sbd a lokacin ya tafi can backyard, Nurain yace "ba wanda yazo..?", Inuwa yace "Eh Alhj..", Nurain yace "Okay, zan sake fita sai na dawo..", Inuwa yace "Allah ya tsare..", Nurain yace "Ameen" ya buɗe ƙofa suka fita gidan da Farooq, motarsa da ya parker nan waje ya bude ya shiga, Farooq ya shiga front seat, tada Motar Nurain yayi ya fara driving out of the street, suna hawa main road Farooq yace "Allah yasa dai ba rufe yar mutane kake a gida ba..", banza Nurain yayi dashi kamar baiji ba, Farooq ya sake cewa "kaga idan ma rufeta kake to ka dena dan naji Mami tayi complain akan hakan a asibiti..", still Nurain bai tanka masa ba kawai driving dinsa yake, Farooq ya gyara zama yace "if i were you banza zanyi da rayuwa wllh, tini zan saki jikina with my cutie wifey, the girl is so cute...", Nurain ya ƙara speed din motar kafin ya juyo ya dubi Farooq yace "really, tinda she is cute idan kana sonta sai in saketa kawai ka aureta punk...", Farooq ya haɗe gira yace "you're not serious...", Nurain yace "am jet serious..", da wani irin expression Farooq ya ringa kallonsa ya kasa cewa komai, Nurain ya juyo sukay ido huɗu, ganin reaction din fuskarsa Nurain yayi murmushi, Farooq ya fara latsa wayarsa bai sake cewa komai ba har suka je inda zasu, 40mins suka ɗauka a wajen kafin suka gama abinda za suyi suka fito, bayan sun shiga Mota Farooq yace "dude you have to make this thing serious, container nawa ce zata sauka..?", Nurain yace "three.. next month", Farooq yace "Ohk..", Nurain yace "lokacin da nake India naje China nayi order dinsu, you know shipping zasu jima basu zo ba..", suna zuwa wani junction Farooq yace "drop me here..", Nurain yace "bari nayi dropping dinka gida mna..", Farooq yace "i have another appointment..", Nurain yace "Ohk", Farooq ya buɗe motar ya sauka. Nurain na zaune main palourn gidansu bayan ya dawo daga masallaci sallar isha'i, Noor ta shigo palourn da Laptop dinta a hannu, ta zauna a gefensa tace "Yaya please duba min..", keenly yace "Ohk..", kunna Laptop din tayi ta shiga slide din, duba mata ya fara yi inda akwai gyara sai ya nuna mata ta goge ta gyara, resting yayi jikin kujera ya lumshe idonsa, Noor ta gama typing mistake din da ya gyara mata tace "Ya am done..", yace "get me something to eat first..", tace "tom" ta tashi ta shiga kitchen, abincin da aka dafa na dinner ta zubo masa, ta haɗo da ruwa da lemo ta kawo masa a tray, saida ya gama cin abincin snn suka cigaba, Mami ce ta shigo, tayi still tana kallonsa kafin ta dubi wall clock dake palourn da ya nuna 9:20 dot, Mami ta kalli Plate din abincin da ya gama ci, tini taji wani iri a ranta, sau uku knn, Mami ta ƙaraso kusa dasu tace "Nurain me yasa kake dare ne baka tafi gida ba, i thought ka tafi ma since..", ya shafa kansa a hankali yace "ina dubawa Noor project dinta ne...", Noor tayi saurin cewa "we will continue tomorrow then Yaya, thank you..", Nurain ya miƙe yace "Mami saida safe..", without looking at him Mami tace "Ohh Allah ya tashe mu lfy..", Noor tace "Yaya ka gaida Hajar Please..", ya gyaɗa kai kawai da haka ya fita, Mami na kallon Noor tace "wane yaci abinci..?", Noor tace "Yaya ne", Mami ta wuce part din Abba dan daman nan ta fito shiga, Noor ta kwala kiran mai aiki, Laure ta fito daga kitchen tace "gani hajiya ƙarama..", Noor tace "Please gyara nan wajen", Laure ta dauke trayn ta shiga kitchen. ƙarfe tara da minti arba'in a gida ta yiwa Nurain cause gudunsa ya falfala a mota, kuma yana shiga gidan daman Kitchen ya wuce, yaufa gaba ɗaya bai sha coffee ba shiyasa yake jinsa moody, kuma bazai iya bacci bai sha ba, ya buɗe Cupboard ya ɗakko Coffee powder yana sake duba expire date, coffeen da ya sha da safe was the worst coffee ever da ya taɓa sha, shine yake duba expire date wai ko powdern tayi expire shiyasa yaji na safe da ya hada rotten, still dai wani sabon pack din ya buɗe cause bai yarda ba kar yaje daga powdern ne, da sauri ya dubi window ganin kamar mutum ya gifta, ya ƙurawa windown ido yana mamakin abinda ya gani, ƙofar kitchen wacca ta fita ta backyard aka buɗe, rumgume da kayanta da ta wanke ta shigo, ta ɗan firgita ganinsa a kitchen din sai kuma ta haɗe rai ta wuce, ta buɗe ƙofar shiga cikin gidan ta shiga palour, Nurain ya ringa kallon ƙofar backyard din, jinjina kansa yayi ya fita kitchen din, ya haura sama ya shiga part dinsa, drawer da ya ajiye kaff spare keys din gidan ya buɗe ya ɗauki guda ɗaya kafin ya fito ya koma kitchen din, ya gama making coffee ya juye a cup, ya matsa gaban ƙofar backyard din ya zura key din ya kulle, saida ya tabbatar ta rufe gamm snn ya cire key din, ya ɗauki Cup of Coffee dinsa ya bar kitchen din bayan ya kashe lights....✍️ yan Arewa ku rungumi sorry yau 😅🌝 💛 HAJAR 💛 by Feenerh feeche {48..} Washe gari tinda Hajar ta idar da sallar asuba bata koma bacci ba sbd da wuri ta kwanta jiya, tana kwance kan carpet ta rufa da duvet da wayarta ta buɗe Alqur'anin tana karantawa, sai ƙarfe bakwai da rabi ta ajiye karatun, linke duvet din tayi ta maida kan bed, shima pillow da ta tada kai ta mayar dashi gado, bathroom ta shiga dan yin wanka, minti ashirin ta ɗauka tana wankan kafin ta fito ɗaure da towel da yazo mata har guiwa, sai ƙamshin tsadadden showel gel da tayi wanka ne ke tashi a ɗakin, gaban mirror ta tsaya kafin taja stool ta zauna, body lotion ta janyo ta fara rubbing a jikinta, a hankali take shafa man tunani iri iri na amsawa a brain dinta, da sauri ta dubi ƙofa jin alamar za a shigo, ido huɗu sukay da Nurain, yana riƙe da handle din ƙofar, Hajar ta zaro ido kafin ta fasa ƙara ta fara kare jikinta, ya ɗauke kansa fuskarsa a murtuke, da wani irin zafin nama ta tashi daga kan stool din ta wafci hijab dinta ta saka, ƙarasa shigowa ɗakin yayi ya ajiye pen da jotter din hannunsa, da haka ya doshi ƙofa zai fita, Hajar da jikinta yake mugun rawa sbd tinda take babu wani namiji da ya taɓa ganinta a haka, har ruwa idonta ya kawo, da kyar tace "malam ka dena shigo min haka nan without notice...", fita yayi daga ɗakin, ta bisa da sauri ta tsaya bakin ƙofa tace "kai da Allah da ka shigo min babu sallama...", tana kallonsa ya shiga part dinsa, ta juya ta koma ɗakinta zuciyarta na tafasa, wani irin yamutsa fuska tayi sbd kawai ƙamshinsa da ya bari ne ke tashi a ɗakin, ƙamshin da sam baya mata daɗi, ta ɗauki freshner ta hau feshe room din amma duk da haka pure men scent dinsa bai disashe ba, Shafa man da bata ƙarasa ba knn ta buɗe wardrobe ta ɗauki kaya ta saka, har ta gama shiryawa zuciyarta ba ta dena tafasa ba, knn yaga bati, a fili tace "shi ya isa yaga bati, wllh Allah ban yafe ba..", gaban mirror ta koma ta ringa kallon jotter da pen din da ya ajiye, ta taɓe baki kafin ta ɗauki biron, rubutun da bai wuce 5lines tayi ba ta yage papern tayi folding dinta, da papern a hannunta ta sauka downstairs, ta wurga takardar kan Centre table tace "wnn kaɗai nake buƙata a wajen ka malam..", kitchen ta shiga dan samawa kanta abinda zata ci, ta buɗe fridge tana kallon fresh vegetables dake ciki, ta rufe fridge din kafin ta buɗe freezer wacca take cike da nama da chicken ga kuma fish duk frozen, shawara ta yanke akan cewa anjima za tayi stew saita ajiye a fridge ta ringa amfani da abarta na ƴan kwanaki, ruwan shayi ta tafasa ta soya kwai guda biyu da haka tabar kitchen din, bata haura sama ba ta zauna nan palour, Centre table da Tv stand da kujerun duk sunyi ƙura, tin ranar da Hafsah ta gyara palourn rabonsa da ganin tsintsiya, taɓe baki Hajar tayi tace "uhmm tinda ba ubana ne ya zuba ba babu abinda ya shalleni..", ta ɗauki kofin shayinta ta fara sha tana gutsirar kwai, tana gama cin abincin ta tashi ta shiga kitchen, ta wanke kwanukan da ta ɓata ta mayar dasu position dinsu, tin kafin ta gama wanke wanken ma take kallon ƙofar backyard, Alla alla take ta gama ta fita can ta ɗan sarara, bakin door din ta isa ta murɗa handle, sake murɗa handle din tayi da ɗan ƙarfi jin ƙofar taƙi buɗewa, lokaci guda ta saki handle din ta kafawa ƙofar ido, shiknn a kulle take, sosai ranta ya ɓaci dan zaman backyard din nan sosai yake rage mata kaɗaici, ranta duk ba daɗi ta bar kitchen din, main door ta ringa attempting buɗewa itama dai a rufe. tinda aka kawota gidan duk wnn ranar tafi mata zafi, baccin rana ma kasawa tayi, babban abinda yafi tsaya mata a rai bai wuce na safe da ya shigo mata ba, bayan tayi sallar la'asar ta kira Umma, gaisawa sukay Umma ta tambayeta ya take, Hajar dai tace lfy amma dai a ƙasan ranta ba haka bane, har Sabra ta tambaya tana cewa yaushe za a kawo mata ita, Umma tace mata ba yanzu ba, da haka suka kashe wayar. ★Nurain na zaune bisa executive kujera dake office dinsa bayan ya gama attending last patient, ƙofar office din aka buɗe aka shigo, ya ajiye plastic heart like da yake wasa da ita ya ɗaga kai ya dubi wanda ya shigo, lokaci guda ya haɗe thick eyebrows dinsa, da sauri Haleema ta shigo office din itama gaba ɗaya a ruɗe take, ta kalli Ruqayyah tace "Maam please get out..", ko kallonta Ruqayyah ba tayi ba ta isa gaban table tana kallon Nurain tace "i can stand any humiliation as far as zaka saurareni Dearest....", Nurain ya maida dubansa ga Haleema yace "amm me na gaya miki ne...?", with due respect Haleema tace "don't let her in..", Calmly as if speaking to himself yace "bayan nan..?", Haleema tace "call security..", ya gyaɗa kai yace "good.." kafin ya ɗauki heart din da ya ajiye ya cigaba da wasa da ita, Haleema ta fita daga office din da sauri, Ruqayyah ta zauna kan ɗaya daga kujeru biyu dake gaban table din, kallonsa ta ringa yi babu ko ƙiftawa, kifa kanta tayi da table din ta fashe da kuka tana girgiza kai tace "na haɗaka da Allah, na haɗaka da manzon Allah, please talk to me Dearest, ko scolding dina kayi that will be better amma...", ta kasa cigaba da maganar tana kuka sosaii, a hankali yayi baya da kujerarsa ya tashi salum alum ya nufi door ya buɗe ya fita, Ruqayyah ta ɗago kanta ta bisa da kallo da jajayen idanunta, Office din Dr Marwan ya wuce, Dr Marwan na kallonsa yace "is there any problem Dr..?", Nurain yace "not at all, how is the patient..?", Dr Marwan yace "alhmdllh he is recovering gradually..", Nurain ya gyaɗa kai yace "how about his vital..?", Dr Marwan yace "great, Khaleel ya duba not too long ago", Nurain bai sake cewa komai ba yayi resting jikin kujerar, after few minutes of silence Dr Marwan yace "naji ana maganar Seminar wacca za aje Abuja nan da 1month, all thoracic surgeon must be there..", Nurain yace "am not going..", Dr Marwan yace "why..?", Nurain ya ɗaga shoulder yace "kawai.." da haka ya dubi wrist watch dinsa, tashi yayi ya yiwa Dr Marwan sallama, yana fita daga department din ya ciro wayarsa yayi dialing numbern Haleema, tana picking yace ta kawo masa briefcase dinsa yana parking lot, da haka ya kashe kiran ya cigaba da tafiya zuwa inda ya parker motarsa, buɗe motar yayi ya shiga, babu jimawa saiga Haleema da briefcase din tasa, ya amsa ba yabo ba fallasa yace "thank you..", tace "am so sorry sir about what happened, i tried to stopped her...", ya ɗaga mata hannu yace "it's okay..", tace "thank you sir", murmushi kawai ya mata ya sauke handbrake yaja motar yabar harabar hospital din, driving kawai yake saman titi amma bai san inda ya nufa ba, lokaci guda yayi murmushi yace "ironlady..", yana zuwa wani roundabout ya juya kan motar, yana zuwa gidan ya danna horn, mai gadi ya buɗe masa gate ya shigar da motar, fitowa yayi daga motar bayan ya gama parking, ta baya yabi inda direct nan ne zai kaika part din Hajiya, da sallama ya shiga palourn Hajiya, Hajiya na zaune kan darduma ƴar dattijuwar mai aikinta tana yanka mata papaya, Hajiya ta kalli Nurain ta saman kantamemen glasses dinta tace "ywwa ga likita ma Allah jefomin daga sama, Usuman cikina ne ya ɗaure kwana biyu ban kewaya ba, toh duk ya dameni ji nake kamar anyi min jeren marmaroni a kyuiɓi ko isasshen bacci bana samu, dana gaji da azaba shine nasa Umaru ya kwaso min gwanda kwallo uku, na sha kwallo guda da safe yanzu ma gashi ana yankan wata zan shanye, da daddare in Allah ya kaimu a yanke min gudar da ta rage itama na shanye, ai idan nayi hakan na huta da jarabar basir din nan, ba kaga da yaya na shanye wacca aka yankan da safe ba, cikina har baya kamar zanyi amai amma kuma ai lfy nake nema, yanzu haka har na fara tararrbin yadda zan shanye wnn..", Nurain yayi still yana sauraronta kafin ya samu waje ya zauna yace "karki sake shan wata ta safen is Okay..", Hajiya tace "Allah ko idan na sake sha zan iya tsurewa knn...?", ta dubi mai aikin tace "ke Asabe maza fita da ita duk warinta ya cikan hanci, kije can ki shanye rabonki ce", mai aikin ta ɗauki plate din papayan tayi waje da ita. Hajiya tace "na ganawa kaina azaba har yanxu gyatsar wnn aba nake, kai ina jin ma harna koma ga mahalicca na bazan sake shan gwanda ba duk ta gundureni", Nurain yace "ba kya jin komai daga wnn...?", tace "A'a ƙalau nake Usuman, haka kurum nace maka wani waje na min ciwo ka samu hanyar da zaka fara zuba min allurai..", yace "toh shknn tinda lafiyar ki ƙalau..", Hajiya tace "toh madallah ya gyatumar taka.." sai kuma ta tsuke baki tace "ji wani sakarci nida zan fara tambayarka matarka kuma na tafi wani wajen, Mami ai ba gida ɗaya kuke kwana ba yanzu..", shi dai baice mata komai ba, bayan ƴan mintina yace "bari na gaida Ummi.." da haka ya tashi ya buɗe wata ƙofa ya shiga, luckily ya tarar da Ummi na palour, ya gaisheta with respect, amsawa tayi tana tambayarsa aiki da iyali, shi dai ya shafa kansa ya amsa a takaice kafin ya mata sallama ya bar palourn ya koma na Hajiya, babu jimawa da zamansa saiga Abinci Ummi tasa an kawo masa, sosai Nurain yaji daɗin hakan, plate ya ɗauka zai zuba abincin Hajiya tace "wai ci za kayi kai Usuman na matarka fa..?", yace "shima zanci", ya faɗi hakan ne dan ya huta da surutunta ta barsa lfy yaci abincin kar ya dawo masa ta hanci. tin ɗaya da rabi sai uku da arba'in Nurain ya bar gidan, bai jira Farooq ba sbd baya dawowa aikin da wuri cause na Company ne. gidansu ya wuce, yana gama parking motarsa yaji ana kiran sallah, yayi amfani da tap dake compound yayi alwala ya wuce mosque, bayan ya dawo masallaci ya shiga ciki, part din Mami ya shiga ya gaisheta kafin ya fito ya haura room dinsa. bashi ya sakko ba sai biyar saura shima sbd Noor ne wacca ta takura masa akan project dinsa, saida sukay chapter biyu snn ranta yayi fari tinda saura ɗaya ya rage su gama. ƙarfe bakwai da arba'in Nurain ya shiga wajen Mami, attention dinta ta mayar kansa, Nurain yace "Mami saida safe ni zan wuce..", Mami ta dubi agogo ganin lokaci tace "yawwa toh Allah ya tashemu lfy, ka ringa tafiya gida da wuri ai yafi son..", ya shafa kansa yace "tom Mami", Compound ya fita ya shiga motarsa, ya ciro wayarsa yayi dialing numbern Noor, tana picking yace "yi sauri malama", tace "Yaya gani nan..", few minutes saiga tanan ta ɓillo ta can baya da basket a hannunta, ta buɗe front seat ta ajiye basket din ta rufe door, Nurain ya gyara zama ya tada motar. saida ya tsaya wajen suya ya siyi kaza snn ya wuce gida, fitowa yayi daga motar yana amsa sannu da zuwan da mai gadi yake masa, ya buɗe front seat ya ɗauki basket din kafin ya nufi main building din gidan, keys ya ciro daga pocket ya buɗe door ya shiga ya mayar ya rufe still da muƙulli, ajiye basket din yayi nan palour kafin ya haura sama, wanka yayi ya saka Pajamas masu sweat pant masu shegen kyau, downstairs ya sakko da room slippers a ƙafarsa, kamar ce masa akay ya kalli wajen, ya ringa kallon papern dake kan Centre table, haɗe gira yayi kafin ya ɗauki papern ya buɗe a wulaƙance, beautiful handwriting din dake jiki ya fara karantawa.... "malam wai an gaya maka inada wata buƙata ne a wajenka in banda guda ɗaya, kawai ka sauwaƙe mana shine buƙatata..", tsaki yayi ya cukuikuiye takardar ya wurgar da ita, wani irin ƙauri ya fara perceiving, da sauri ya nufi kitchen, yana buɗewa yaja da baya ya toshe hancinsa, gaba ɗaya kitchen din ya gumame da hayaƙi da uban yaji, da hannu ɗaya ya rufe hancinsa ɗayan kuma ya ringa kore hayaƙin har ya samu ya shiga kitchen din, gaban cooking gas ya isa yana ƙoƙarin kashe wutar amma da yake hayaƙi yayi yawa baya gani sosai hannunsa ya jogali tukunya, da sauri ya janye hannun ya riƙe da other din, hkan ce tasa yayi perceiving ƙaurin har cikin lungs dinsa, tini ya fara tari at same time yana ƙoƙarin kashe gas din. Hajar ta saki pillow din hannunta bayan brain dinta ta amsa, shaf ta manta da kayan miyar da ta ɗora akan wuta, bata tsaya bi takan wani hijab ba ta gyara hular kanta ta fito daga room din, da sauri ta ringa sauka stairs har tana tuntuɓe, tin daga palour ta fara tari ga uban hayaƙi da ya rufe mata vision, gadan gadan kitchen ta shiga daidai lokacin da Nurain ya kashe gas din, da sauri ta juya kamar zata sa gudu sbd fitowar da tayi ba shiri, Allah yaso ma kayan baccin riga da wando ne kuma rigar ta saukar mata, tana fita daga kitchen din shima ya fito yasa ƙafa ya banke ƙofar, tana shirin hawa stairs taji an fixgo hannunta, figarta yayi zuwa dining area inda babu hayaƙin sosai, haɗe ta yayi da bango still bai sakar mata hannu ba fighting with his breathing, sosai ya shaƙi hayaƙin shiyasa numfashinsa har yanzu bai dawo normal ba, kiciniyar kwace hannunta ta fara yi tana turesa da iya ƙarfinta, sake matseta yayi da bango ta kasa motsi, heavily yake breathing har zuwa lokacin da yaji dama dama, a hankali take mayar da numfashi ta ɓalla masa harara tace "let go off me, ni ka sake ni..", ita babban tashin hankalinta kayan jikinta, muryarsa ma bata fita sosai yace "from today henceforth karna sake ganinki a kitchen, are you mad fire outbreak zaki ja min a gida, koda wasa na sake ganinki a kitchen saina sumar dake nonsense" yana kaiwa nan ya hankaɗeta saura ƙiris ta faɗi. da sauri ya nufi stairs ya haura sama don bazai iya ƙara koda 1minute a wajen ba, Hajar tabi bayansa da kallo zuciyarta ta ringa ƙuna kamar zata kama da wuta, zama tayi kan stairs din hawa dining ta haɗe kai da guiwa, after 10mins ta tashi ta haura sama kamar wacca kwai ya fashewa a ciki. washe gari da safe Nurain ya sauko downstairs, ta main door ya fita ya zaga can backyard ya kashe gas cylinder, cikin gida ya dawo bayan ya kashe gas din, ya shiga kitchen to make a cup of coffee, wani tsaki yayi ganin tukunyar dake kan cooking gas, tayi wani baƙi ƙirin ko kyan gani babu, cikin sink ya saka tukunyar ya sakar mata ruwa saida ta cika damm snn ya kashe pampon, ya jona coffee maker. A hankali Hajar ta ƙarasa sakkowa daga stairs idonta ƙur akan keys din dake jikin ƙofa, ta isa bakin ƙofar a hankali ta zare keys din, tana juyawa sukay ido huɗu dashi ya fito daga kitchen da cup a hannunsa, ta haɗe gira tayi sauri ta kunshe keys din a hijab, garin haka ji kake tass muƙulli sun faɗi a kan tiles, kallon keys din Nurain yayi snn ya kalleta, ta wani haɗe rai, yana kallon main door ita kuma ta samu opportunity ta sunkuya ta ɗauki mukullin ta kwasa a guje sai sama, a hannun kujera ya dungurar da Coffee din yabi bayanta da sauri, tana ƙoƙarin rufe ƙofa yasa ƙafa ya banke ƙofar, zaro ido tayi tace "na shiga uku" ta ruga can edge of the room ta boye hannunta a baya, daga bakin ƙofar ya tsaya yace "give me the keys..", ta murguɗa masa baki tace "wllh bazan bayar ba, ni ba tinkiyarka bace da zaka ringa kulleni", ƙofar bathroom ta kalla sai kuma ta kallesa tana banka masa harara, lokaci guda ta tafi da gudu zata shige bathroom din, ganin haka ya taho da speed ya fixgota ya haɗeta da jikin wardrobe, dunƙule keys din tayi a hannunta ta ɓoye a baya, tini ta ringa shaƙar scent dinsa da bata so, ta ɗaga lulu eyes ɗinta ta kallesa, shima kallon cikin idanunta yake da wani irin expression zuciyarsa na tafasa.......✍️ Chapter 49... on Arewabooks.. Click the link below to join my WhatsApp group 👇 💛 HAJAR 💛 {49..} Thick eyebrows dinsa a haɗe while still staring at her yace "i said give me the keys..", ta juyar da kai gefe tana turo baki tace "ni fa bazan bayar ba..", bata ankara ba taji hannunsa akan nata da ta ɓoye a baya yana ƙoƙarin dawo dashi gaba, ta cije iya ƙarfinta ta sake dunƙule keys din a hannunta, partially ya dubi fuskarta kafin ya murɗa hannun nata ya dawo dashi, ƙara ta fasa ta fara ƙoƙarin fixgewa, tana ji tana gani ya ɓamɓare keys din daga hannunta, ya bita da wani shegen kallo ya juya ya fita daga ɗakin, wani mugun takaici ne ya tokare mata a maƙoshi, ta sulale ƙasa ta rushe da kuka tace "wllh sai na maka rashin mutunci mai wasali, ba dai ni ka murɗewa hannu ba, na rantse da Allah saina rama, dala ba gammo ka ɗakkowa kanka idan baka sani ba saika sakeni zaka cigaba da rayuwa mai daɗi..", taci kukanta ta more ta tashi ta shiga bathroom ta wanke fuskarta da ruwa ta fito, fita tay daga ɗakin tana cika ta batsewa ƙiris take jira a taɓata ta sauke kwandon bala'i, downstairs ta sauka ta nufi kitchen tana cewa "duk abinda kace kar nayi toh yanzu na fara yinsa a gidan nan, dani da kai naga wanda zai sumar da wani, dan wllh tllh ni kaɗai nasan irin ayar da zan gasa maka a hannu..", plate ta ɗauka ta buɗe bucket din dubulan dana chin chin ta zuba, ta fito daga kitchen din, tsaye tayi tana kallon cup din Coffeen da ya ajiye a hannun kujera, Cup din ta ɗauka tana kallon coffen, ta gyaɗa kai ta haura sama da Kofin, a kan mirror ta ajiye plate da cup din taja stool ta zauna, taci dubulan da chin chin dinta tayi nak tana korawa da coffee, sosai combination din ya mata dadi sbd the coffe is creamy and yummy gashi babu sugar sosai sai hakan ya bada wani armashi. Nurain ya ringa kallon inda ya ajiye Coffeen sa wayarsa a kare kunne yana magana da Farooq, zagaye ya ringa yi yana duba each sofa a palourn, Farooq yace "are you listening..?", Nurain yana sake duba hannun kujeru yace "yeah", Farooq yace "alright" ya cigaba da bayanin da yake masa, after 5minutes suka gama wayar, Nurain ya shafa cikakkiyar sumarsa yace "damn it i misplace my coffee" da haka ya haura sama to get ready for work, dakatawa yayi da zuge glass door da ya fara ya kalli ƙofar ɗakinta da ta buɗe ta fito, idonsa ya sauka akan cup din dake riƙe a hannunta, ya ringa kallonta har ta ɓace masa bayan ta sauka ƙasa, slight hiss yayi ya juya ya shiga room dinsa, ƙarfe tara dot ya fito bayan yayi wanka ya shirya hannunsa riƙe da briefcase, ya sauka downstairs ya shiga kitchen ya ɗauki basket din abinci da yazo dashi jiya, bayan ya rufe main door ya isa parking space, ya shiga motarsa ya kunna, a booth ya saka basket din ya koma ya shiga motar tana gama warming ya fara driving ya fita daga gidan Inuwa na ɗaga masa hannu. sai ƙarfe uku Hajar ta fito ɗakinta zuwa kitchen, duk wnn lokacin ba ta ji yunwa ba sbd breakfast din yau ya riƙe mata ciki, ji take dama zata sake samun wnn creamy coffee din, saida ta gama jajjaga attaruhu da Albasa ta zuba a ƙaramar pot ta ɗora kan gas, ta ɗauki lighter ta kunna gas din amma babu wuta, ta canza wani shima dai wuta ba tazo ba, ta koma ta jingina da jikin cabinet tana tunanin yanxu yaya knn, me zata bawa cikinta, ta ringa kallon gas cooker din sai taga ashe akwai electric head ajiki har guda biyu, ta tuna lokacin da take gidan Anty Jamilah dashi ai take amfani most of the time sbd unguwar akwai nepa sosai, Hajar tayi ajiyar zuciya a bit relief, tana murɗa control knob din electric stove din luckily for her sai gashi ya kama, tinda a jone yake da wuta, wani dadi ne ya ratsa Hajar, tini ta hau yin girkinta, cikin kayan gararta ta farke buhun shinkafa ta ɗebi yadda zai mata ta dafa, bayan ta gama dafa shinkafar da ƴar sauce ta palm oil, gaba ɗaya ta juye a plate ta zuba Sauce din akai, ta buɗe fridge ta ɗauki ruwa da haka ta fita zuwa palour, da kyar ta iya cinye abincin, ta kai plate din kitchen, saida ta wanke komai da tayi amfani dashi ta mayar mazauninsa snn ta bar kitchen din ta haura sama, cikinta ɗam ɗam dan ji take ita da abinci kam sai gobe kuma. ★Maama na kallon Maimuna da take ƙoƙarin saka hijab tace "wai ina zaki a haka Mainuna.. jifa fuskarki ko gama saɓewa ba tayi ba..", Maimuna da tayi ɗaurin ɗan kwali har goshi tace "kai Maama ba fa daɗewa zanyi ba, nan nan zanje na dawo..", Maama tace "nan nan ina..?", Maimuna tace "kai jaraba" ta ciro wata fatattakakkiyar dari biyu daga bra ta linƙawa Maama a ƙirji tace "yanzun nan zan dawo..", Maama ta dafe ɗari biyun tace "karki daɗe", Maimuna ta ƙarasa saka hijab dinta ta fita, bayan ta saka takalmanta dake bakin ƙofa tayi soro, can ta gangara cikin lugunsa har ta ɓulla wani lungun, daga nan tayi tafiyar da bata wuce ta minti biyar ba sai gata a wani kango wanda aka zagayesa da blocks sai gate na langa langa, tin kafin ma ta ƙarasa cikin kangon ta fara jin warin kayan zuƙe zuƙe, haka nan ta dake ta shiga kangon, su biyar ne a zaune a kangon matasa dasu babu wanda ya haura ashirin da bakwai a cikinsu, wanda ya fara hangota ya cire cigarette da yake zuƙa yace "ke ubanki kika kalla anan...?", Maimuna tace "ƙwage nake nema..", wani daga can gefe wanda ya fisu shekaru bakinsa baƙi ƙirin ya kalleta a wulaƙance, Wiwin dake hannunsa ya yiwa mummunar zuƙa ya fesar da hayaƙin ta hanci da baki tamkar salansar tsohon babur yace "ke yarinya yane... kin kawomin kanki ne dan na tuɓeki..?", Maimuna tace "haba ƙwage ai kasan nafi ƙarfin ka... harƙalla na kawo maka..", Ƙwage ya tashi ya matsa kusa da ita yace "meye..?" yana cigaba da busa wiwi, ta fara lalube cikin hijab dinta ta ciro kuɗi masu ɗan kauri a ƙalla zasu kai 10k ta miƙa masa, wurgar da ragowar wiwin yayi ya murjeta a ƙasa ya amshe kuɗin, Maimuna tace "kasan Mu'azzam ɗan gidan gini..?", Wani ne ya taso yana kallon hannun Ƙwage yace "kai wnn yaron fa nunar rana take nufi, ke ba ƴar gidansu bace ai naga yayanki ne..?", Maimuna tace "Eh ɗan kishiyar Baabarmu ne..", yace "A'a malama baabarki dai ba tamu ba..", Ƙwage yace "kai zan feɗe ka da rai nace ka sako bakinka ne..?", Bisi ƙwale yace "haba gorun goruba naga harkar nan tare muke yinta ai karka mana eh yane faa..", Ƙwage yayi kwafa yace "ina jinki", Maimuna tace "Shi nunar ranar Mu'azzam nake so ku masa dukan tsiya..", Ƙwage yace "Au abin sauƙi, ai ko cewa kikai mu ƙaddamar masa wllh a yau sai yaro ya ziyarci barzahu..", Maimuna tace "ku lakaɗa masa na jaki..", zuciyar Maimuna ba tada maraba da kindirmon nono sbd fari haka ta koma gida, tana shiga ɗaki ta cire hijab ta bage akan gado, Maama ta bita da idanu tace "har kin dawo...?", Maimuna tace "gashi kin gani", Maama tace "sai naji kamar kina warin Wiwi", a hasale Maimuna ta miƙe zaune tace "wiwi kuma Maama..?", Nabilah dake zaune ɗakin tana tsince shinkafa tace "nima naji wllh...", harara Maimuna ta bisu da ita ta koma ta kwanta tana jan dogon tsaki. Da yamma Umma na zaune bakin murhu tana kwasar tuwo, Mu'azzam ya shigo gidan da sallama, ya durƙusa gaban Umma ya gaisheta, da fara'a ta amsa masa tace "an dawo lfy ya aiki..?", yace "Alhmdllh Umma, yau mun gama da gidan ma har an biya mu zuwa jibi zamu tafi Katsina wani aikin..", Umma tace "toh alhmdllh, Allah ya temaka..", yace "Ameen Umma ga wnn.." ya ajiye mata ledar da ya shigo da ita, tace "toh madallah, Allah yayi albarka, ga can abincinka a ɗaki", yace "toh" ya tashi ya shiga ɗakinta ya ɗauki warmern abincinsa, daga nan ya shiga ɗakinsu, Maimuna dake laɓe jikin window tana leƙensa tayi kwafa ta koma ta zauna, Umma ta gama kwashe tuwon ta ɗauka ta kai ɗaki tare da ledar da Mu'azzam ya kawo mata, ta buɗe ledar taga lemo da Ayaba sai kuma ɗan tsire ne ciki, murmushi tayi ta ajiye kan mirror, Sabra ce ta shigo da gudu tana haki tace "Umma Yaya ya dawo...?", Umma tace "ba zaki dena guje gujen nan ba ko dan kinga Addarki ba tanan ne?", Sabra tace "ya haƙuri Umma", Umma ta shafa kanta ta ɗauki lemo ɗaya Ayaba ɗaya ta bata tace "zauna kici". Mu'azzam na alwala bakin rariya zai wuce masallaci dan daf ake da kiran sallar magrib, yana idar da alwalar ya fita daga gidan, bayan Umma ta idar da sallahr Isha'i tana zaune kan darduma tana lazimi, sallama akay daga soro, Maama da ƴaƴanta babu wanda ya amsa Nabilah kuma da ta ɗan fara shiryuwa sallah take, ga Baba ma baya nan ya fita masallaci, Umma ta ajiye carbin da take lazimi ta fita, daga bakin ƙofar soron ta tsaya, bata kai ga magana ba Naseer ya shigo, gaisawa Sukay da Munkaila wanda shine yayi sallamar, Munkaila yace "ina Baban naku..?", Naseer yace "yana masallaci..", Munkaila ya numfasa yace "toh muje da kai, ban san me ya haɗa Mu'azzam da fitinannun yaran nan ba gashi can sun sassara sa, yanzu haka dai an wuce dashi emergency..." ganin Umma kawai sukay a soron tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un.. wane Mu'azzam din.." ★Nurain yayi parking motarsa a wani babban eatery, fitowa yayi daga motar ya shiga eatery din, a vacant table na two sitters ya zauna, tini waitress ta kawo masa food menu, bayan ya gama order abinda yake so waitress din ta tafi kawo masa, dice watermelon da Orange juice aka fara serving dinsa as a starter, gently yake sipping orange juice din yana latsa wayarsa, Tamkar ɓera a buta hka ta shigo Eatery din tana rarraba idanu, tana hangosa ta nufi table din da yake zaune, ta ja kujera ta zauna gami da zuba masa idanu, ajiye glass cup din lemon yayi ya fara shirin miƙewa, da sauri ta riƙo hannunsa tace "dan girma Allah listen to me ko sau ɗaya ne..", fasa tashin yayi da sigar ko in kula murya ƙasan maƙoshi yace "what..?", duk da Ruqayyah taji haushin yadda yayi treating dinta these days amma bata nuna ba, gyara zama tayi tana kallonsa tace "Dr dan Allah don't take grudge against me, ba wai na tafi bane sbd bana son na aureka, ba a fahimce ni bane from the start..", keenly yace "Ohk, then stop following me..", Ruqayyah ta haɗiye kukan da ya taho mata tace "shknn, nasan har yanxu fishi kake dani Dearest..", yana latsa wayarsa yace "not at all..", tace "nagode da ka tsaya, har yanzu ban canza daga Ruqayyahn da ka sanni ba, i still remains your first love and only kuma your wife to be, zan aureka Dearest, a shirye nke ko yanxu ma kaje wajen Daddy za ai mana aure Dearest..", a lokaci na farko da ya ɗago kansa ya kalleta kafin ya dauki orange juice yayi sipping yace "Ruqayyah..", murya na rawa tace "Na'am", yace "a lokacin da nayi dating dinki kinsan duk abinda na bari na barsa knn", ta gyaɗa kai idanunta na ciccikowa, yace "snn kin san banida ra'ayin auren mata sama da ɗaya..", nan ma ta gyaɗa masa kai tace "amma why are you saying that bayan baka da aure..?", ya girgiza kai yace "you are wrong" da haka ya kira waitress yace ai masa packaging abincin da yayi order, Ruqayyah dai ta kasa mgn cause tana buƙatar concrete explanation, wayarsa ya saka a pocket ya tashi zai biya bill, cashier ya nufa ya biya bill din ya amshi ledar abincin ya nufi exist, da sauri Ruqayyah tabi bayansa tace "wllh Allah ban fahimci me kake cewa ba, kuma baka bani enough time na maka bayani ba..", yayi ajiyar zuciya yace "i don't like it idan kina bina hka, please stay away from me, i don't have any feelings for you now, snn kuma i am married.. good luck..", da haka ya nufi motarsa ya shiga ya bar Eatery din, Ruqayyah taga kamar birds ne suke yawo a kanta kafin ta fara ganin harabar Eatery din bibbiyu daga nan kuma bata sake fahimtar halin da take ciki ba. farkawa tayi ta ganta a restroom na Eatery din mutum har huɗu akanta, ta miƙe zaune tana kallonsu kafin ta dafe kanta, wata mata ce tace "Alhmdllh sannu ko..", Ruqayyah ba ta iya cewa komai ba kawai binsu take da idanu, wani mutum wanda shima staff ne a Eateryn yace "ki bamu contact din wani naki a kira a gaya musu halin da kike ciki..", a hankali Ruqayyah ta girgiza masa kai tace "no need ngd sosai..", ta miƙe da kyar kanta na sarawa, waitress din da itama ke wajen ta miƙa mata ragowar bottle water da aka yayyafa mata ta farfaɗo tace "ga ruwa ko zaki sha..", Ruqayyah ta girgiza kai tace "nagode.." ta nufi ƙofa zata fita, mutumin ya sake cewa "da dai kin jira an kira ƴan uwan naki hajiya", bata tanka masa ba sbd ita kaɗai tasan abinda take ji, da kyar ta kai kanta bakin titi ta tsari napep, ba ta ma gaya masa inda zai kaita ba kawai ta shiga, saida suka fara tafiya snn ta gaya masa inda zata, Ruqayyah na zuwa gida direct hanyar room dinta ta nufa, Momy dake zaune palour ta bita da kallo tace "baki da lfy ne..?", gyaɗa mata kai Ruqayyah tayi, Momy tace "sannu..", room dinta ta wuce zuciyarta kamar an ɗora mata dutse, tayi wurgi da handbag dinta a kan bed kafin itama ta zube akan bed din, Momy ce ta shigo da plate din abinci da ruwa, ganin Ruqayyah a kwance ta ajiye plate din akan mirror ta iso bakin gadon tana feeling body temp dinta, jikin nata zafi ramm, with care Momy tace "zazzaɓi kike ne Ruqayyah..?", Ruqayyah ta yunƙure ta miƙe hawaye na zuba idanunta wani nabin wani, sosai hankalin Momy ya tashi ta zauna gefen gadon, Ruqayyah ta ɗora kanta a kafaɗar Momy ta fashe da kuka mai ƙarfi tace "Momy kiyi haƙuri, am so sorry". ★Ƙarfe takwas da rabi Nurain ya isa gidansa, basket din abinci da ya taho dashi daga gidansu ya ɗauka kafin ya fito daga motar, ya ciro ledar take away na abinci da ya siya baici ba dan tinda ya saka a motar baima bi takansa ba, Inuwa ya bawa ledar abincin ya wuce ciki da basket na abincin gidansu, upstairs ya haura yayi refreshing kansa kafin ya sakko sanye da white pajamas ya shiga kitchen ya ɗakko plate da spoon da drink, saida yayi powering TV snn ya zauna cin abincin, ko rabin abincin bai ci ba ya ajiye spoon din yana kallon stairs, lokaci guda ya miƙe ya haura saman, toh me tasamu taci bayan ya kashe mata gas, har ga Allah mantawa yayi ya bawa Inuwa ya siyo mata Charcoal ko firewood da safe in yaso sai tayi amfani dasu tayi girkin, still yayi a corridor yana kallon ƙofar ɗakinta, ya haɗe gira ya murɗa door handle ya shiga, yayi sallama ƙasa ƙasa, Hajar ta ajiye wayarta kan mirror ta dubi ƙofar, tin ɗazu take kiran Umma amma no respond, suna haɗa ido dashi ta murtuke fuska ta galla masa harara ta ɗauke kai, duk da ya lura da hakan amma he don't care, with a repartee yace "hey..", bata bari taji sauran maganar ba ta katsesa da fadin "can kaje ka nemo hey dinka nan Hajar ce ba Hey ba", Nurain was more than shock jin abinda ta faɗa, furiously yace "young lady, na fahimci kanki na rawa kuma baki da kunya, amma please enough don't try me..", wani irin yamutsa fuska tayi tace "Au haba, so kake na ɗauki mayafi na kirma a ka na rufe fuskata shine zan zama me kunya ko me.." haɗiye sauran maganar tayi ganinsa a gabanta, ita dai bata san lokacin da har ya taho yazo gabanta ba, wani mugun bugu zuciyarta ta fara yi, ta ja baya da sauri tana zare ido, tana ƙoƙarin sake ja da baya ya kama dukka hannayenta ya mayar dasu baya ya rutsasu duka da hannu ɗaya, riƙo bana wasa ya mata ba don ji tayi kamar shoulders ɗinta zasu karye, turo baki tayi tace "malam ni ka sake..", bata gama maganar ba yasa finger ya ɗalle bakin rashin kunyar, tini Hajar tayi shiru tana jin azaba a lips ɗinta, yana ganin ta fara motsa lips alamar za tay magana ya sake ɗalle bakin, gashi ta gagara motsi babban weapon dinta kuma an hanata amfani dashi wato her mouth, motsa lips din ta sake yi nan ma ya ɗallesa, tini lips din kwa sukay jajir, thick eyebrows dinsa a matuƙar haɗe yake kallon fuskarta, wani yunƙuri tayi zata fixge, da sauri ya kuma matseta ya ɗalle lips din a karo na huɗu, lulu eyes ɗinta ya kalla da suka cika taff da hawaye, lokaci guda tears din suka fara zarya kan kuncinta.....✍️ 💛 HAJAR 💛 {51..} Hajar tafi minti ashirin tsaye bakin titi tin fitowarta daga gida kafin ta samu abin hawa, ta gayawa mai napep din inda zai kaita, bayan tafiyar rabin awa suka iso, ta sauka daga napep din ta buɗe hand bag ta ciro 1k ta basa, ya bata canji da haka ta shiga gate din asibitin, can jikin wata bishiya ta tsaya ta ciro wayarta tayi dialing numbern Umma, Umma na picking Hajar tace "Umma kuna emergency room ko..?", Umma tayi jimm kafin tace "badai fitowa kikay ba Hajara..?", Hajar ta sunkuyar da kanta tace "fitowa nayi gani ma a asibitin..", Umma tayi ajiyar zuciya tace "toh kinga dai yanzu ni ina gida ban taho ba amma mal da Nasiru na nan..", Hajar tace "toh bari na shiga kafin kizo.." da haka ta katse wayar, wani worker ta tmbya ina Emergency room yayi leading dinta, gradually ta fara duba ko wane bed bayan shigarta E.R din, Naseer ta fara hangowa aikam ta nufi wajen, tana zuwa gaban gadon da Mu'azzam yake ta durƙusa har ƙasa ta gaida Baba, Baba ya amsa yana ƙare mata kallo, ta gaida Naseer ma, yace "lfy lou Hajar ykk, ygida..?", tace "lfy lou Yaya, ya aiki..?", yace "alhmdllh..", tashi tayi tana kallon Mu'azzam dake jingine da gado, shima kallonta yake, hankalinta ya mugun tashi ganin condition dinsa, ta dubi Naseer tace "Yaya hatsari yayi ne..?" don Umma bata gaya mata ainahin me ya faru ba kawai tace mata bashi da lfy suna asibiti, Naseer yace "ke karki ɗaga mna hankali..", ta ringa kallon Mu'azzam idonta ya ciko taf da ruwa tace "sannu Yaya". babu jimawa da zuwan Hajar saiga Umma tare da Sabra, da gudu Sabra taje ta rungume Hajar, Hajar tayi murmushi a takaice tace "ashe dai kina sona ƴar kanwata..", Baba ya tashi daga kan kujerar da yake ya ciro kuɗi daga aljihu ya bawa Umma yace "ko za a buƙaci wani abun", Umma ta karɓa tace "tom", yace "sai anjima..", Naseer ya tashi shima don tare zasu tafi da Baban yace "Umma saina dawo da daddare, zanje wajen police din ma akan case din, ya kamata a kama yaran nan...", Umma tace "toh Nasiru, Allah yayi albarka..", yace "Ameen" snn ya bar room din, Hajar tace "Umma hatsari yayi ne naji Yaya Naseer yace zaije police station...", Umma tace "ba hatsari yayi ba ƴan daba ne suka farr masa..", Hajar ta zaro ido tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un", sai kuma ta dubi Mu'azzam tana kallon inda aka sassaresa a jiki, Umma ta rausayar da kai ta buɗe ledar abinci da ta zo da ita, ta zuba masa abincin, da kanta ta ringa basa yana ci sbd karayar dake hannunsa. wajajen ƙarshe uku da rabi sai ga Anty Jamilah tare da Abdallah dake riƙe da basket, Anty suka gaisa da Umma ta mata ya me jiki, Abdallah ya russuna yace "Umma ina wuni, ya me jiki...?", Umma tace "alhmdllh, ya kasuwa..?", yace "alhmdllh..", Umma tace "madallah..", da mamaki Anty take kallon Hajar da ta gaisheta, Anty ta riƙe haɓa tace "ita kuma wnn har ta fara fita..?", Hajar ta sunkuyar da kanta ba tace komai ba, Umma tace "nima dai hka nagani, yanzu nke shirin ce mata ta tashi ta tafi ban kai ga gya mata ba sai gaku..", Anty tace "ai ya kamata dai ki tashi haka Hajar, ina ma laifi dan ma dai ɗan uwanki ne ba lfy..", wani tashin hankali ne ya baibaiye Hajar, ji take kamar ta kurma ihu tsabar baƙin ciki, itafa bazata koma gidan nan ba wlllh tllh, ko wace walle walle za ai ayita ta ƙare, da kyar ta iya cewa "ana yin sallar la'asar zan tafii..", Anty tace "ai la'sar din ta kusa..", tashin hankalin Hajar bai linku ba saida taji kiran sallah, Anty ta shimfiɗa dardumar da tazo da ita ta kabbara sallah, tana idarwa Umma ta miƙawa Hajar ƴar purse ɗinta tace "riƙe min nayi sallah". Hajar ta saka ƴar purse din a hijab, a hankali ta zuge zip dinta ta fara lalube, can ƙasan purse din ta jiyo keys, ta ciro keys din ta buɗe tata jakar ta saka a ciki, Umma na idar da Sallah tace "toh Hajara ayi harama..", Hajar tace "toh Umma bari nayi sallah..", tana idar da sallar tayi musu sallama ta fita, tana fita taji ance "Hajar..", ta juyo taga Anty ce, Anty ta ƙarasa har inda take tana mata kallon tsanake tace "Hajar Allah yasa dai baki ɗaga hankalinki a gidan ki ba.. idan da akwai matsala ki gaya min..", Hajar tayi rau rau da ido ta shanye kukan da yake shirin taho mata tace "A'a Anty babu wata matsala faa kawai dai nayi missing su Umma ne..", Anty tayi ajiyar zuciya tace "toh alhmdllh, toh ki kwantar da hankalinki kinji, karki sawa kanki damuwa ko wace mace a haka ta saba da gidan mijin, ai kowa yana son gidansu..", Hajar ta gyaɗa kai don huɗubar Anty bata shigeta ba bare tayi tasiri, abinda ta ƙulla shi zata warzar yanzu ma kuwa, tace "toh Anty ki gaida min da Hafsah" da haka sukay sallama, Hajar na fita bakin titi ta tsari napep tace "Dala zaka kaini..", mai napep ya gyaɗa kai ya gaya mata kudi, a bakin layin gidansu ta sauka bayan sun zo unguwar, a hankali ta shiga lungun ta wuce gida, da ido Maimuna da ta fito daga wanka ta bita tana taɓe baki, Hajar ko kallon inda take ba tayi ba ta wuce ƙofar ɗakin Umma ta ciro keys din da ta ɗauka ta buɗe padlock din ta shiga, rufe ƙofar tayi ta saka sakata, ta faɗa kan gado tana sauke ajiyar zuciya. Maimuna ta shiga ɗaki tana kallon Maama tace "ko me tazo yi oho..", Maama tace "wa knn..?", Maimuna tace "Hajara mna gata can ta buɗe ɗakin uwar ta shiga ta rufe..", Maama tace "ita Hajarar ce tazo gidan nan", Maimuna ta taɓe baki tace "ita fa", kwandon kayan shafa ta ɗakko ta zauna ta buɗe BSC cream ta lafta a fuska. saida aka kira sallar magrib Hajar ta fito tayi alwala ta sake komawa ɗakin ta rufe, ta haɗe kanta da guiwa bayan ta idar da sallar isha'i. wajen takwas da rabi Umma ta dawo, ta buɗe ƴar purse dinta zata ɗauki muƙulli, wayam taga babu alamar mukulli a jakar, ta kunna torch light din wayarta don babu nepa a gari tana haska alhargar ƙofar taga a buɗe, sai a lokacin ta lura da hasken dake ɗakin ta jikin window, jikin windown ta isa ta bankaɗa labule tana kallon cikin ɗakin tace "waye a nan", Hajar ta kalli window ta tashi ta buɗe ƙofar, Umma ta ringa kallonta don ta rasa ma me zatace mata, Sabra tace "laa Adda anan zaki kwana..?", Hajar dai na tsaye a inda take tamkar wacca aka dasa, Umma ta shiga ɗakin ta samu gefen gado ta zauna still idanunta na kan Hajar, Hajar ta sulale ƙasa daga nan inda take ta fashe da kuka tace "Umma... Umma.. bazan iya zaman auren nan ba wllh.." ★Nurain yayi folding din takardar da ya gama karantawa ya saka a pocket, ajiyar zuciya yayi yana kallon stairs kafin ya tafi ya haura, room dinta ya buɗe ya shiga to make sure, ya ƙarewa ɗakin kallo yaga dai babu alamarta anan, har bathroom ya buɗe ya duba, har zai fita daga ɗakin sai kuma ya dawo ya buɗe wardrobe, baiga alamar ta dauki kaya ba, fita yayi daga ɗakin ya sauka downstairs, ya shafa cikakkiyar sumarsa maganganun Abba na yawo a brain dinsa, compound ya fita thinking of what to do, ya sake shafa kansa kawai ya nufi ɗakin mai gadi, sallama ya masa, Inuwa ya fito ya russuna yace "Alhj", Nurain yace "kamar ƙarfe nawa ta fita daga gidan nan..", Inuwa yace "Hajiya..?", Nurain yace "Eh..", Inuwa yace "wajajen ƙarfe biyu..", Nurain ya gyaɗa kai yace "buɗe min gate..", Inuwa yace "tom" ya tafi ya fara buɗe gate din, Nurain ya nufi parking space, motarsa ya buɗe ya shiga, yafi minti biyar zaune a motar kafin ya kunnata, driving slowly ya fita daga compound din, yana hawa saman titi ya take accelerator, with speed yake driving, yana shiga unguwar ya rage gudun cause kwaltar a ragargaje take, gefen titi ya samu ya parker motar yana kallon lungun, unguwar duhu dunɗum sbd babu nepa sai fitilu na masu shagon chajin waya da provision, bai san wane bayanin zaiwa Abba ba hakan shine one Solution dinsa, buɗe motar yayi ya fito yana ƙarewa unguwar kallo, gently ya fara tafiya ya shiga lungun, tsaye yayi a ƙofar gidan, luckily for him yaga wani yaro zai wuce, kiran yaron yayi yace "shiga nan gidan kace Hajar tazo...", yaron yace "tom" ya shiga gidan da gudu, Umma na tsaye bakin ƙofar ɗakinta tare da Naseer da yake mgana ƙasa ƙasa kar Maama ta jiyosa, Umma tace "yanzu an kama yaran..?", Naseer yace "an kama mutum biyu saura uku, tinda an kama Ogan nasu suma za'a kamosu ɗaya bayan ɗaya..", Umma tace "dan Allah Nasiru a musu kwatankwacin abinda sukama yaron nan..", Naseer yace "ai sai sun ɗanɗana kuɗarsu Umma, na bawa ƴan sandar wani abu..", Umma ta gyaɗa kai tana jin wani sanyi a ranta tace "yauwa..", yace "bari na tafi asibitin..", Umma tace "toh da yake ma Abdallah na can tare dashi..", a daidai nan yaron ya shigo yace "wai Hajar tazo inji wani..", Naseer ya kalli Umma yace "daga asibitin nan tayo..?", Umma tayi ajiyar zuciya tace "Eh.." sai kuma tayi shiru ta rasa abin faɗa, Naseer yace "ai saita fito ko mijin tane yazo tafiya da ita.." sai kuma ya dubi yaron dake tsaye yace "kace gata nan..", yaron ya fita da gudu, har lokacin Nurain na tsaye bakin ƙofa ko soron bai shiga ba, tunani yake is he doing the right thing, ɗari biyar ya damƙa a hannun yaron yace "good boy", Naseer ne ya fito bayan ya yiwa Umma sallama, yana ganin Nurain a ƙofar gidan ya miƙa masa hannu sukay musabaha, kallon Nurain yake a tsanake yace "ko kaine kake kiran Hajar..?", Nurain yace "yeah..", Naseer yace "kai ne mijin nata..?", Nurain yace "yeah..", Naseer yace "kayi haƙuri fa na cika ka da tmbya, duba da yadda auren ya kasance shiyasa nake tamby tinda ban sanka ba, anyway ni yayanta ne..", Nurain yace "Okay nice to meet you..", Naseer ya sake miƙa masa hannu yace "same" sai kuma ya kalli cikin gida kafin ya koma ciki. Umma na kallon Hajar da take ta sharar hawaye tace "toh ni yanzu ya zan miki Hajara, na tmbayeki dalili kince min ba komai, komai fa saida dalili, haka kurum bazan tunkari mal nace akashe miki aure ba, yanzu idan kika gyamin dalili kinga na samu hujjar da zan goya miki baya a wajen mal, ba kiji farin cikin da mahaifinki yake ba da wnn auren, yace Allah ya zaɓa miki miji na gari, juma'ar da ta wuce mijin naki da mahaifinsa suka zo har nan yaron ya gaida mal, nutsuwa da hankali ai suna bayyana kansu, mal yace shi dai baiga aibun wanda ya aura miki ba, kema yanxu na tambayeki kin ƙi bani amsa, kin san dai mahaifinki ba lfy ya cika ba idan kina so ciwonsa ya tashi ta dalilinki toh maza ki ɗau harama Hajara..", Hajar ta cigaba da sharar hawaye nan ma ba tace komai ba, Umma tace "A zamanin da haka ake auren, toh kema mahaifinki ya miki zaɓi amma kina ƙoƙarin bijire masa, idan kina samun wata matsalar ne a gidan naki ki faɗa in yaso sai iyaye su shiga idan zaman naku bazai yiwu ba sai a raba, akwai matsala ne..?", Hajar ta girgiza kai, Umma tayi ajiyar zuciya tace "toh shknn, zan turo Jamilah kuyi magana da ita, mal din ma zan masa mgana, kinga ynxu hankalinsa ba a kwance yake ba, tashi ki tafi kar ya dawo ya sameki a gidan nan .." Naseer da ya shigo gidan ya tsaya bakin window yace "ke Hajar kin bar mutum a tsaye fa..", Umma tace "gata nan". saida Hajar ta share minti uku wajen saka hijab da ɗaukar jaka, kamar wata chameleon haka take acting, murtuke fuska tayi ta fita soro, tin kafin ma ta kai bakin ƙofa hancinta ya shaƙi scent dinsa, yana ganinta yaji wani relief cause he can't imagine abinda Abba zai masa, ba tare da ta dubesa ba tace "takardar ka kawo..?", yace "yeah ita na kawo miki..", wani sanyi taji har cikin ranta, ta juya ta zuba masa lulu eyes dinta ta miƙa hannu tace "kawo..", duk da duhun dare saida ya lura da hasken hannun nata da taimako hasken farin wata, yace "ohk, ai takardar na mota idan kina so kizo ki amsa", yana gama faɗin haka ya juya ya fara tafiya, tabi bayansa da harara sai kuma ta bisa walking slowly, yana fita bakin titi ya tsaya kusa da motar yana jira ta ƙaraso, tana ƙarasowa ya danna mabuɗin motar da keys din hannunsa, cike da tsiwa tace "bani", ya buɗe front seat ya ciro papern dake aljihunsa ya ajiye kan seat yace "pick it..", ta wani galla masa harara ta wuce ta ɗauka, da sauri ya koma ta bayanta ya turata cikin motar, ta zabura zata bar wajen hakan yasa yayi wrapping dinta a ƙirjinsa, tana shirin kwala ihu ya toshe mata baki, within few seconds ya sakata a motar ya kulle, saida ya zaga driver seat snn ya sake buɗe motar ya shiga, dukan glass din motar ta fara yi tana cewa "malam ka buɗe min ƙofa na fita", Nurain kam resting yayi da kujera yana sauke ajiyar zuciya, a hankali yace "damn it", tana jin ya kunna motar ta kwala wani uban ihu sai kuma ta fashe da kuka ta haɗe kanta da guiwa, shi dai baice mata ƙala ba ya fara driving dinsa, a wani eatery ya tsaya yayi take away snn ya fito, back seat ya buɗe ya ajiye ledar abincin kafin ya shiga driver seat, har suka je gida Hajar bata dena kuka ba, bayan yayi parking motar ya buɗe ya fito, ledar abincin ya ɗauka ya zaga side din da take ya buɗe yace "come down..", a hankali ta zuro ƙafafuwanta ta sakko, ya mayar da ƙofar ya rufe snn ya kulle motar, hannunta ya figa suka wuce ciki, saida ya haura har sama da ita snn ya saketa bayan sun shiga har room dinta, ledar abincin ya ajiye nan kan chest of drawers yace "ba takardar saki kika ce na baki ba toh ai gata nan na baki..", Hajar ta dubi papern da ta dunƙule a hannu sai kuma ta ɗago tana kallonsa, ya ɗaga shoulder ya fita daga ɗakin, da sauri ta shiga warware papern hannunta har na rawa, kawai ta tsinci rubutunta a jiki, wurgi tayi da ita ta sulale ƙasa ta fashe da kuka, ji tayi hijab dinta na ƙamshinsa, ta tashi ta cire hijab din ta shiga bathroom ta wanke fuskarta, sai kuma taji tana son tayi wanka, saida tayo wankan snn ta fito da wata azababbiyar yunwa, tin safe babu abinda ta zubawa cikinta ko ruwa, turo baki tayi ta ringa kallon ledar abincin da ya ajiye mata, ta saka kayan bacci snn tazo ta ɗauki ledar ta buɗe. washe gari da safe Nurain na zaune palourn downstairs yana shan Coffee, ga laptop gefensa yana operating, Hajar ce ta sauko ƙasa da ledar abinci a hannunta, kallo ɗaya ta masa ta ɗauke kanta, kitchen yaga ta shiga, ya ajiye coffee cup din ya tashi ya bita kitchen din....✍️ you can join my WhatsApp group by clicking the link below 💛 HAJAR 💛 {52..} Hajar ta ajiye ledar hannunta kan cabinet, juyowa tayi jin motsi a bayanta, ba tare da ya dubeta ba yayi folding hands yana kallon gas cooker yace "kin iya amfani dashi..?", ta kalli gas cooker din sai kuma ta dubesa tace "A'a saika koyamin..", nodding kansa yayi don ya gane kalar amsar da ta basa, now bazai biye mata ba, without looking at her yace "alright.." ya ƙarasa gaban gas din ya ɗauki lighter ya kunna sai kuma ya dubeta yace "like this.. idan zaki rage wuta da ƙarawa duk da control knob din za kiyi amfani.. kin gane..?", ta juya lulu eyes dinta tace "Eh nagane.." yace "fyn" ya bude fridge ya ɗauki raspberry drink na kwali, cupboard ya buɗe ya ɗauki glasscup, har zai bar kitchen din sai kuma ya dakata yace "i told you babu gage a nan duk abinda kika gani a kitchen din nan idan kina so ki dauka kici.." da haka ya buɗe ƙofa ya fita, ta taɓe baki ta riƙe haɓa tace "nida jangwangwan ai dole ka tmbyeni na iya amfani da gas sbd kaje gidanmu, toh koda nake ƴar malam shehu naje makaranta, koda ilimina ai na kunna shege gas..", Noodles ta dafa ta zauna nan kitchen din taci, tana gama ci ta buɗe fridge ta ɗauki ruwa ta sha, saida ta gyara kitchen din ta wanke komai snn ta fita, har lokacin Nurain na zaune palourn, daman ko gigin kallon position din da yake ba tayi ba ta haura sama, ya tashi ya shiga kitchen din yana ƴan dube dube, komai na nan a mazauninsa babu alamar anyi girki, ya fito kitchen din ya zauna yayi crossing legs ya cigaba da aikinsa jikin Laptop. Hajar ta kimtsa ɗalinta sama sama kafin ta shiga bathroom, ruwan zafi ta tara a bucket ta fito tana jiran ya kai yadda take so, wayarta dake jone a charge ta cire ta shiga kiran Umma, Umma na picking Hajar tace "Umma ina kwana..", a takaice Umma ta amsa tace "kunje gida lfy..?", Hajar tace "Eh Umma ya jikin Yayan..?", Umma tace "jiki alhmdllh..", Hajar tace "toh Allah ya ƙara afuwa..", Umma tace "Ameen, Allah ya miki albarka..", da haka suka katse kiran, Hajar na shirin ajiye wayar ta tina da ruwan zafin da ta tara a bucket, tsabar sauri bata iya ajiye wayar ba ta tafi da ita bathroom din, ai kam ruwan ya cika bucket din dam, ta zaro ido ta tafi zata kashe, wani irin santsi ne ya ɗebeta suuu tana shirin sulewa a ƙasa tayi sauri ta dafa kan pampo, pressure da ta bayar a pampon yasa wayar hannunta ta suɓuce ta faɗa cikin bucket din ruwan zafin, gwalo ido tayi tana shirin kelayar da ruwan zafin sai kuma ta fasa sanin hakan babu kyau, ga wayarta tsamo tsamo ta lume can ƙasan bucket din, bowl din diban ruwa ta ɗauka ta kanfato ruwan tare da wayar, da sauri ta tsame wayar ta hau bibbigeta a hannu, ta fito daga toilet din still tana bibbige wayar, ta zauna gefen gado tana gogeta da ƙasan rigarta, ta danna switch ta kunnata, sai gashi ta kawo few seconds da kawowarta sai kuma ta fara farfaɗiya daga nan kuma ta ɗauke gaba ɗaya, babu irin dabarar da Hajar bata gwada ba amma waya taƙi kamawa, daga ƙarshe ta ajiyeta kan mirror a daidai saitin AC, gaba ɗaya jikinta yayi sanyi yanxu idan wayarta bata tashi ba dame zata ringa communicating da ƴan uwanta, bathroom ta shiga tayi wanka da ruwan da ta tara don har ya huce, tana fitowa ta sake gwada kunna wayar amma bata tashi ba, ta gama shiryawa tsaf bayan ta saka wata doguwar riga material wacca akaiwa ɗinkin tsuke baby armless da tail, sai kace wata yarinya haka kayan suka mayar da ita. tanata zaune a ɗaki abin duniya ya isheta ƴar wayar da take rage mata zafi ma ta margaya, a haka har akay sallar Azahar ta tashi tayi, linke dardumar da hijab din tayi ta ajiye, ta gyara hular kanta ta fita daga ɗakin, a hankali ta sauka daga stairs tana jin kamar ta kurma ihu sbd a maƙoshi lalacewar wayar ya tsaya mata, tana kaiwa tsakiyar palour aka buɗe ƙofa aka shigo, tsaye tayi tana kallonsa don ita a tunaninta baya nan, kallon da ta lura yana mata ne yasa ta dubi kanta, wani irin gwalo idanu waje tayi ta ruga da gudu ta koma sama, Nurain ya taɓe baki ya ƙarasa shigowa ciki, yau Saturday babu inda yaje yanxun ma daga masallaci ya dawo, kan doguwar kujera ya hau ya kwanta ya miƙar da legs dinsa, a haka yake amfani da wayarsa, stairs ya duba jin footsteps, lokaci guda ya ɗauke kansa ya cigaba da kallon wayarsa, a zuciyarsa yace what is she covering, Hajar na shiga kitchen ta tattare hijab din da ta zumbula ta fara tunanin me zata girka, bai ɗauketa wani lokaci mai yawa ba ta fara sarrafa wata haɗaɗɗiyar jollof rice wacca ta zuba mata isasshen kifi da kayan miya exclude tomato. Nurain ya tashi daga kwancen da yake yana kallon ƙofar kitchen din, da hannu ya ja pointed nose dinsa jin wani aroma da yake hudasa, hancinsa ya ringa perceiving aroman ba ƙaƙƙautawa, ji yayi stomach dinsa na shaking ya tashi da sauri ya zura room slippers dinsa ya wuce sama. Hajar na gama girkinta tayi serving kanta a plate, ta juye ragowar a warmer ta haura sama da ita. wajen ƙarfe biyar da minti huɗu tana zaune kan stool tana combing hair dinta, gwara dai ta yiwa kanta qiyamul layli tinda ynxu ba ta gida bare Umma ta taimaka mata, don idan ta bari kanta ya danƙare saita gane kurenta, slowly take combing hair din tana yamutsa fuska, wai ma a hakan saida ta jiƙasa da oil, ƙofa aka buɗe aka shigo tare da sallama ciki ciki da murya mai zurfi, ɗaga kanta tayi sukay ido huɗu dashi, ta haɗe gira ta ajiye comb din hannunta kan mirror tace "nifa ka dena shigo min babu notice..", yayi folding hands dinsa a ƙirji yace "bayan sallamar da nayi akwai wani abu bayan ita ne..?", ta miƙe tsaye tana mayar da gashin daya rufe mata fuska baya tace "Amma dai kasan babu kyau, kai ba muharrami na bane dan haka bai kamata ka ringa shigo min ɗaki babu sanarwa ba..", yace "Ohh really, su iyayen naki basu gaya miki me suka miki ba kafin a kawoki nan din", ta yamutsa fuska tace "me kwa aka min din.. nidae ka dena shigomin ɗaki ehe..", sai kuma ta fara gunguni ƙasa ƙasa tana cewa "hka kurum zai kalleni a bati", zamm yaji abinda ta faɗa don yanada sharp hearing mechanisms, yace "ke!! kinje islamic school kuwa..?", cike da tsiwa tace "A'a jira nake kazo ka kaini aii..", tana ganin ya fara tunkarota tayi baya tana turo baki, ya ajiye wayarsa kan mirror, kafin ta ƙara one step backwards yayi wuff ya cafke hannunta, yace "idan bazaki gaji ba nima bazan gaji ba..", tana jin zai ɗaure mata hannaye a baya ta fara ƙoƙarin kwatar kanta, nan ya gwada mata ba ƙarfinsu ɗaya ba, duka hannayenta ya riƙe da hannu ɗaya ta bayanta, ɗalli ya kaiwa lips dinta yace "do i look like your mate ba..?", tini ta guntse lips din ta mayar dasu ciki yadda bazai iya ɗallesu ba, sakinta yayi yace "da kin cigaba dai..", ja da baya tayi tace "karka sake taɓani dan ni ba ƴar iska bace..", slight smirk yayi yace "ƴar iska ce mna tinda gaki nan zaune gida ɗaya da namiji..", ta gwalo idanu tace "chaɓɗi jamm wllh ni ba ƴar iska bace, dole akamin nake zaune a nan..", wani mugun kallo ya watsa mata ya ɗauki wayarsa ya nufi door, har zai fita sai kuma ya juya yace "thank God wanda suka kawoki sun san ina ne nan din a wajenki which is gidan aure..", habawa ai wani irin tafashe Hajar taji a zuciyarta, tini fuskarta ta canza tamkar wacca aka saukarwa da wahayin mutuwa, zuciyarta ta harzuƙa iya harzuƙa, sosai Nurain ya fahimci wnn sauyin don shima saida yaji tasa azabar da ya faɗi hakan amma ya lura ita har ta fisa shiga shock, muryarta na rawa tace "meye kuma wani aure.. wa aka kawo gidan aure.. kaika sansa wllh tllh ni kam banida wani aure, aure a ina.." sai kuma ta durƙusa ƙasa ta fashe da kuka tace "ƙarya ne wllh Allah, ba wani aure da aka min..", ya taɓe baki yace "Silly girl" yayi fitarsa daga ɗakin. downstairs ya sauka ya fita compound, parking space ya isa ya shiga motarsa ya bar gidan zuwa nasu. ★Ruqayyah na kwance kan gado tunani iri iri ke yawo a brain dinta, babu abinda take tunawa sai time din da sukay sharing da Dearest, ba ƙarya sun zuba soyayya mai danƙo mara algus, soyayyar da take ganin zata kaisu ga aure, soyayyar da take ganin bazata taɓa mutuwa ba, toh me yasa wnn soyayyar take ƙoƙarin tabarbarewa ne..?, me yasa dearest zai gaya mata magana mai zafi irin wnn, wai yana da aure, shin yanada auren ne ko kuma kawai so yake ya ƙuntata mata, a lokacin da ya gaya mata wnn mummunar kalmar tayi tunanin zuciyarta ta buga ne don ji tayi tamkar an ɗauki wuƙa mai shegen kaifi an tsagata gidan biyu snn aka barbarɗa mata gishiri, tin shekaran jiya batada wani kuzari tana kwance ne kawai a ɗaki, jiya ma ko aiki bata je ba duk da cewa tanada night duty, wasu hawaye suka cika mata idanu, lokaci guda suka fara bin gefen fuskarta suna shiga ramin kunnenta, door akay knocking kafin aka murɗa handle aka shiga, da sauri Ruqayyah ta goge hawayenta ta miƙe zaune tana kallon Momy da ta shigo, Momy ta dubeta tace "ya jikin..?", Ruqayyah tace "da sauƙi sosai..", Momy ta gyaɗa kai tace "Ohk sannu your father is calling...", Ruqayyah ta ɗan zaro ido tace "Momy lfy..?", Momy ta nufi ƙofa tace "idan kinje kya ji.." ta buɗe ƙofar ta fita, sakkowa Ruqayyah tayi daga kan gadon ta saka hijab dinta ta fita, palourn Daddy ta shiga da sallama tana rarraɓewa tamkar munufuka, kanta a ƙasa ta zauna kan carpet a hankali tace "Daddy ina yini..", Calmly yace "lfy..", tayi shiru tana wasa da laushin carpet, Daddy yace "Ruqayyatu..", sai a lokacin ta ɗago kanta tace "na'am Daddy..", Ruqayyah na kuka wiwi ta fita daga palourn bayan Daddy ya sanar da ita ya amshi kuɗin aurenta da Dauda, fagam fagam ta wuce room din Momy tana kuka, Momy dake gyaran wardrobe ta ajiye gogaggun kayan hannunta tace "ke lfy kike gursheken kuka haka...?", Ruqayyah ta jingina da bango tana kuka sosai tace "Momy na shiga uku na lalace da rayuwa, wllh da na auri Dauda gwara na mutu..", Momy tace "ce miki akay auren Daudan za kiyi ne..?", Ruqayyah ta tsagaita kukan tace "Daddy ne ya amshi kuɗin auren Dauda..", Momy ta tsuke ido tace "Daddyn ne ya gaya miki haka..", Ruqayyah ta gyaɗa mata kai, Momy ta fita daga ɗakin, zaman dirshan Ruqayyah tayi a ƙasa ta ringa rafsa kuka tamkar wacca uwarta ta mutu, after like 10mins Momy ta dawo ɗakin ranta busu busu, don basu wanye da Daddy ta arziƙi ba, cewa yayi yaga alamar so take ta shiga tsakaninsa da ƴaƴansa, duk wani hukunci da yayi ƙoƙarin zartarwa saita kawo nata tawilin wnda ada ba haka take masa ba, shi ya gaji da zama da Ruqayyah a gida ɗaya aurar da ita zaiyi, goɗai goɗai da ita me zai hana a aurar da ita tinda tanada manema ba babu ba, Momy ta zaune gefen gado tana jin tinda take da Daddy basu taɓa samun matsala kamar yau ba, Ruqayyah ce causative agent, tin farko ita taja komai don haka she must harvest what she planted, Ruqayyah ta rarrafa gaban Momy tayi kneeling tace "Momy kin basa haƙuri ko..?, ya haƙura bazai aura mim Dauda ba ko..?", tureta Momy tayi tace "na gaji Ruqayyah, kawai ki haƙura ki auri Daudan shine zaman lfy na da kuma naki..", daɓas Ruqayyah ta koma ta zauna ba shiri tana girgiza kai, ta wawaki ƙasa ta miƙe ta fita da gudu ta bar ɗakin, dole ta nemawa kanta solution, don wllh tllh bazata auri Dauda ba, safa da marwa ta ringa yi a ɗakinta tamkar wacca ta shirgawa sarki ƙarya, wata babbar dama ce tazo mata kwanya, shi kaɗaine zai iya dakatar da Daddy, gobe goben nan zata kama hanyar Kaduna da yardar Allah, yanzun ma dan yamma tayi ne da babu zai hanata ɗaukar hanya. ★Abba na kallon Nurain yace "ranar Monday zaka amso mna passport din..?", Nurain yace "tom Abba.. zuwa wani lokaci Visa zata fita..?", Abba yayi resting da kujera yace "bazata wuce nan da 3weeks ba insha Allah..", Nurain ya gyaɗa kai yace "harda Hajiya ne..?", Abba yace "yeah..", Nurain ya jinjina kai yace "alright.. can i excuse myself..?", Abba yace "sure", tashi Nurain yayi ya bar great room din, bayan sallar isha'i Nurain na zaune palourn Mami, Mami tace "dan ma dai angama processing komai ne aida da Hajar zamu wuce..", Nurain ya kalleta bai dai ce komai ba, Mami ta numfasa tace "Son i hope all is well..", ajiyar zuciya yayi yace "yeah Mami..", Mami ta ringa kallonsa don yayi losing weight, ba haka yake ba, tace "toh cut down on coffee yasa kana ramewa fa..", ya zaro ido yana shafa fuskarsa yace "Mami coffee ne zai ramar dani", tace "toh idan bashi ba mene ne, bayan ma kullum anan sai kayi ƙat da abinci..", dariya yayi wacca ta tsaya iya throat, Mami ta kalli Tv tace "toh ga gaskiya..", Noor ce ta shigo da box din doughnuts da tayi order a hannunta, ta ajiye box din tace "Mami ga doughnut..", Mami ɗauki one piece cikin pieces shida dake cikin box din mai filling din foam milk with chocolate, Noor ta ɗauki box din ta ajiye kusa da brother dinta tace "Yaya fa..", ya girgiza kai yace "A'a", tace "toh na kawo maka cake" bata jira cewarsa ba ta tashi ta fita, da plate ta dawo palourn mai ɗauke da variety na cake, akwai red velvet with whipped cream, milk coconut cake, sai kuma chocolate cake, miƙa masa plate din tayi ya amsa yana kallon abin ciki, spoon dake gefe ya ɗauka ya fara ci a hankali, Noor ta zauna gefensa tana cin doughnut ita kuma tace "Yaya ya kaji cake din...?", yace "not bad..", tayi murmushi tace "nifa nayi..", yace "gashi nan kam har kin fara shirga kiba tinda kin durfafi cin wnn tarkacen..", ta zaro ido tace "aikam basa sa kiba Yaya.." sai kuma ta fakaici kallon yadda yake cin cake din tace "Yaya na dakko system din..?", ya ajiye plate din yace "Au bribery aka bani knn.. toh am leaving..", ya tashi ya yiwa Mami sallama, kafin ya nufi door ya kalli Noor, ta fakaici kallon Mami tayi sauri ta ƙifta masa ido, fita yayi daga ɗakin, yana fita da kamar minti biyar Noor ta ɗauki plate din cake da ya ajiye tace "bari na mayar da abuna fridge.." ta tashi ta fita tana kallon Mami da wutsiyar ido, da sauri ta wuce kitchen ta zuba abinci a warmers ta jera a basket, ɗaukar basket din tayi ta buɗe ƙofar kitchen din ta baya ta fita, ta zagaya zuwa parking space, tana zuwa ta bude front seat ta ajiye basket din ta duƙa tace "kaga fa ni ba ruwana Yaya, gobe ka ƙarasamin gyaran dan Allah..", yace "ke close the door and get lost..", ta turo baki ta rufe ƙofar ta wuce cikin gida, tara saura Nurain ya isa gida, yana shiga main palour ya fara tunanin shirmen da ta masa ɗaxu, sai a lokacin ya sake gasgata tabbas akwai tsantsar yarinta a lamarinta, murya ƙasan maƙoshi yace "Silly girl", kitchen ya shiga ya ɗauki plate with spoon da ruwa da lemo ya ɗora kan basket din hannunsa, da haka ya fito ya haura upstairs. washe gari da safe Hajar ce take sakkowa a hankali daga stairs, takaici duk ya isheta na rashin waya don wayar ce ke ɗebe mata kewa, gashi so take ta kira Umma taji ya jikin Mu'azzam, Still tayi ta ƙurawa hannun kujera idanu tana kallon wayarsa dake kai, ta ƙarewa palourn kallo tana murza slim fingers dinta, a hankali ta matsa ta ɗauki wayar tana kallonta, tinda take bata taɓa ganin waya mai kyanta ba, waya gaba ɗaya glass, juya wayar take a hannunta tana neman ta inda ake kunnata, da sauri ta dubi ƙofa jin an murɗa handle, tini idonta ya faɗa cikin kaifafan nasa, wani irin harbawa zuciyarta tayi, hannunta ya kalla a takaice, tana ganin haka tayi sauri zata ajiye wayar, ai kam garin sauri ta ajiye ba daidai ba, ji kake tass wayar ta faɗi akan tiles, durƙusawa tayi ta ɗauka, tana ganin yadda screen din yayi kwatsa kwatsa tayi sauri ta ajiye a ƙasa ta miƙe tana zaro ido, Nurain ya ƙaraso ya duƙa ya ɗauki wayar, da wayar a hannunsa ya miƙe yana kallon yadda screen din yayi kwatsa kwatsa, har wani numfashi ya ajiye tsabar yadda ransa ya mugun ɓaci, ya ɗago idonsa ya kalleta, tinda take dashi bata taɓa jin tsoronsa irin na yau ba, ƙafarta ta fara karkarwa ta juya da mugun gudu zata haura sama, Nurain yayi wurgi da wayar kan kujera, fixgo hannunta yayi ya juyo da ita, habawa ai tsabar firgita kawai ta tafi luu sai kace wacca aka hankaɗa ta zube a ƙasa......✍️ Plxx share as widely as possible 🙏 💛 HAJAR 💛 {53..} Tsayawa yayi kawai yana kallonta, taja jiki ta koma can bayan kujera ta rakuɓe ta haɗe kanta da guiwa, tsabar yadda zuciyarsa take tafarfasa kasa cewa komai yayi, kuma baiyi yunƙurin taɓa ta ba, a lokacin idan yace zai taɓa ta to tsaf zai karya ta, Hajar kam ta tsorata iya tsorata har wani karrr jikinta yake, a yadda taga reaction din fuskarsa sai take tunanin yau ba ɗalle mata lips zaiyi ba tsaf zai rabata dasu, ɗago kanta tayi taga har lokacin yana tsaye a kanta, tayi sauri ta ɗora kanta kan knee tana sake takure jikinta, ajiyar zuciya yayi ya figi hannunta ya miƙar da ita tsaya, ƴar ƙara tayi tana zaro ido sai kuma ta fara yarfe hannu, gashi dai ta tsorata kuma tayi nadama amma kuma girman kai bazai barta tace sorry ba, shi kuma a ynxu sorryn ne zaisa ya yafe mata tinda ya lura ba tada shirin faɗa, figarta yayi zuwa cikin palourn, yana riƙe da hannunta ya tura Centre table da ƙafarsa zuwa daf fa kujera 2sitter, zaunar da ita yayi kan Centre table din shi kuma ya zauna kan kujerar suna fuskantar juna, ta haɗe legs dinta waje guda tana kallon ƙafarsa dake sanye cikin soft room slippers, gashi ya saka legs din nata a tsakiyar nasa, ƙoƙarin zamowa ƙasa tayi tana turo baki, da sauri ya mayar da ita ta zauna, zuciyarta na tsananta bugu ta ɗago idonta tana kallonsa, ya haɗe gira ya ɗauki wayarsa dake kan kujerar ya ɗora mata kan laps yace "biyani..", ta ringa kallon wayar ba tace komai ba, yace "uhmm am talking to you young lady, nace ki biyani..", ta juya lulu eyes dinta ta wani ci mur sai kace ita aka yiwa ɓarnar tace "nawa ce wayar taka ba sai na biyaka din ba..", ganin yadda tayi mganar ba tare da wata nadama ba yasa yaji ta matuƙar basa haushi, wai maimakon tace yayi haƙuri shine har tanada kwarin guiwar da zata tambayi nawa wayar, shi yasan ba tada kuɗin da zata biyasa a yanxu dai, kawai ya faɗi hakan ne to test her yaga irin girman kanta, ɗalle bakin yayi yace "wa ya gaya miki da kuɗi zaki biyani nonsense..", da sauri ta kai hannu ta shafa bakinta, ai kam ta dangwalo jini, tace "kai ka kai ka kai toh idan ba da kuɗi ba da mai ka sayi wayar da zaka dakar min baki haka..?, kuma naga ai ba ina sane na fasa ba.." tana gama faɗin haka ta yunƙura zata bar wajen, ya zaunar da ita da sauri, ƙafafuwansa da ya rutsa nata yasa ya matseta snn ya rutsa hannayenta da hannu ɗaya, kokawa ta fara yi dashi tana gunguni ita lallai sai ya saketa, dan kanta ta haƙura ganin bazata iya kwacewa ba, yace "har yanzu ba kiyi nadama ba young lady..", hijab dinta ya tattaro ya kawosa zuwa laps dinta, zaro ido tayi tana mutsu mutsu tace "malam meye haka... ni ka sake..", ya kalleta ba tare da yace komai ba, hijab din ya zare daga kanta ya sauka a wuyanta, nan da nan ƴan hanjin Hajar suka juya, idonta kamar zai faɗo tana turo baki tace "ka sake ni malam...", kwafa yayi ya cije lower lips dinsa painlessly yana kallon yadda take zabga masa harara, ba tay aune ba ya cire hular kanta, ta fasa ƙara a gigice ta kai masa cixo a hannu, gwaɓe bakinta yayi yace "karki kuskura..", tini idonta ya kawo ruwa jikinta na tsananta rawa, hijab din ya cire gaba ɗaya daga jikinta, wata gagarumar ƙara ta fasa har saida ya runtse idonsa sbd yadda ear drum dinsa yayi beating, he can feel yadda jikinta ke rawa, sbd kayan bacci ne ajikinta shiyasa ta razana sosai, ya ɗalle lips din yace "karki sake min ihu a nan, are you mad, by now kin fahimci da mai zaki biyani wayana..", wani numfashi ta sauke tamkar zata shiɗe ta fara girgiza kai, tama kasa yin magana tsabar yadda take shivering, bata sake firgita ba saida taji ya ɗaga ƴar rigarta sama, ta muskuta baya tana ƙoƙarin fixge kanta, janyota yayi da ƙarfi har kusancinsu yafi na da, bakinta na rawa sai kace an jona mata shocking tace "wayyoh Allahna na shiga uku na lalace... nifa ba ƴar iska bace..", sosai tayi mugun basa dariya amma ya shanye yace "nima ba ɗan iska bane amma saina fanshe wayana..", wnn furucin da yayi ba karamin ɗaga mata hankali yayi ba, hannunsa ya zura cikin rigarta, idonta yayi wani farrr sai kace wacca zata suma kafin ta kwallara ƙara da iya volume dinta tace "Allahumma ajirni fi musibati... na shiga ukuna..", ya ɗago kansa yana kallon yadda hawaye ya wanke fuskarta tass, gashi kuma tayi jajir sai kace jan ƙosai, a gigice tace "yi haƙuri don Allah, dan girman Allah kayi haƙuri", idonta a runtse bama ta kallonsa, yayi ajiyar zuciya kafin ya ciro hannun daga rigarta yace "maimaita..", lips dinta na rawa tace "kayi haƙuri dan Allah..", ya gyaɗa kai yace "ni sa'an kine da zaki ringa min rashin kunya..?", ta girgiza kai har lokacin bata buɗe idonta ba tace "A'a wllh kai ba sa'ana bane ka girmeni..", yace "good.. zaki sake min rashin kunya..?", nan ma ta girgiza kai tace "A'a wllh har abada bazan sake ba.. kayi haƙuri don Allah..", yana sakinta tayi baya luuu zata fada kan glass din center table din, fixgota yayi yace "open your eyes..", a daburce ta buɗe idon, samm taƙi yarda ta haɗa ido dashi, ta yayibi hijab dinta da ya wurgar kan carpet ta lulluɓe jikinta, a miliyan ta haura sama har tana zabga tuntuɓe, yabi bayanta da kallo yace "Silly girl..", wayarsa da ta faɗi nan kan carpet ya sunkuya ya ɗauka, ya ringa jujjuyata a hannunsa kafin ya tashi ya haura sama da ita. ★Ƙarfe Shida da rabi Ruqayyah ta fito wanka, bayan ta gama shafe shafenta ta buɗe wardrobe ta ɗauki doguwar rigar atamfa ta saka a jikinta, palour ta fita ta shiga kitchen ta haɗa thick tea ta fito, bread ta ɗauka a kan dining ta shafa masa strawberry jam sbd rashin appetite da ta tashi dashi, slowly take cin abincin tana turawa da kyar, da kyar taci slice biyu na bread din shima jam din ne ya taimaka mata taci, ta shanye tea din shima daman ba mai yawa ta haɗa ba, room dinta ta koma ta bude bedside drawer ta ɓalli 2tablets of paracetamol ta sha da bottle water dake kan mirror, daga nan ta saka hijab din da ta fito dashi ta ɗauki handbag dinta ta fita, ta shiga room din Momy ta tarar bata nan, she knows tana part din Daddy kawai ta juya ta fita compound, bayan ta bar layin gidansu ta samu wani pos ta cire cash sbd na jikinta ba zasu isheta ba, ta tsari napep ta shiga, bayan tafiyar 20mins ya ajiyeta a motor park, Ruqayyah bata shiga ko wace mota ba sai wacca taga ta kusa cika, tana shiga motar ta tashi cause itace ta cike wajen mutum ɗaya daya rage, ƙarfe takwas suka isa Zaria, wayarta ce ta fara ringing, ta cirota daga handbag ganin mai kiran tayi sauri ta ɗaga, from the other side Momy tace "kina ina Ruqayyah, na duba room dinki bakya nan..", Ruqayyah ta haɗiyi yawu tana neman ƙaryar da zata rangaɗa, jin shiru Momy tace "ba kya jina ne..?", Ruqayyah tace "Momy gidansu Meema naje..", Momy tace "da safiyar Allah kika je musu gida..", Ruqayyah ta sauke ajiyar zuciya bayan sun gama waya da Momy, bayan tafiyar almost 2hrs suka iso garin Kaduna, ta biya kuɗin motarta snn ta fito daga motor park din, napep ta tare, ya tambayeta ina zata tace "Malali..", yace "Malali wacce..?", Ruqayyah tace "Malalin har nawa ce ni Ruqayyah..", ya gaya mata, taɓe baki tayi tace "toh muje dai wataqila na gane idan mun shiga garii", da kyar Ruqayyah ta iya gane gidan bayan sun gama gallafiri tsakanin unguwanni, mai napep kam ya cajeta kudi da yawa, ta fello haƙƙinsa ta basa ita dai tinda ta gane gidan ai mgana ta ƙare, almost 3yrs fa rabonta da zuwa wata kaduna, wani gida mai bakin gate wanda yake da manyan bishiyar dogon yaro a gabansa ta isa, tayi knocking door, few seconds mai gadi ya buɗe mata, shiga compound din tayi ta wuce main building din gidan, sai a lokacin taji fargata tazo mata, ta dake ta shiga da sallama. yaran da suke zaune palourn su uku suka ɗaga kai a tare suna kallonta, kamar yadda bata ganesu ba suma haka basu santa ba, babban cikin kawai ta gane tace "Mujaheed..", yayi yaƙe ya gaisheta duk da dai bai santa ba, sauran ma suka gaidata, kan kujera Ruqayyah ta zauna tana raba idanu, courage dinta ma duk ya fara narkewa, Ruqayyah ta kira ƴar macen, yarinyar ta taso ta tsaya gefenta, Ruqayyah tace "ya sunanki..?", yarinyar tace "Hanan..", Ruqayyah tace "ina Mamamki..?", Hanan tace "tana gidan mu, ni jiya aka kawoni nan wajen Mammah..", Ruqayyah ta gyaɗa kai bata kai ga cewa komai ba aka buɗe wata ƙofa, wata dattijuwa ce ta fito da tray a hannunta an ɗora masa cups uku tana mita "wnn wane irin rikici ne, na gama ɗawainiya da iyayenku kuma yanzu na ɗora da taku, dan bala'i duk sati sai a kawomin ƴaƴa wai weekend, iyayen ku nacan suna tiƙar bacci ni an barni da tashin sassafe da guntuwar hamma..", sai kuma tayi shiru ganin Ruqayyah tana ƙanƙance ido, Ruqayyah ta zamo ƙasa tace "Mammah ina kwana..", Mammah ta ajiye trayn da ta haɗowa jikokin nata shayi tana kallon Ruqayyah da kyau, Mammah ta riƙe haɓa tace "Ruqayyatu hala dai ɓatan kai ki kayi ko..?", Ruqayyah tayi murmushin yaƙe tace "A'a Mammah zuwa nayi na gaisheku..", Mammah tace "toh sannu da zuwa daga kanon kike..?", Ruqayyah ta gyaɗa kai tana murza fingers, kitchen Mammah ta koma ta fito da plate din dankali da kwai ta ajiyewa jikokin nata da har sun afka kan shayin da ta ajiye musu, daga nan ta zauna suka gaisa da Ruqayyah da kyau tana tambayarta Daddyn ta. ƙarfe biyu da rabi Mammah ta shiga ɗakin da aka sauki Ruqayyah tace "kinci abincin..?", Ruqayyah tace "Eh naci..", Mammah tace "toh kixo ku gaisa da mijin naki, ni tsautsayi ne ma ya sani na kai kishiya har ɗaka..", Ruqayyah dai tayi murmushi ta tashi tabi bayan Mammah, ɗakin Kawu wanda yake ƙanin mahaifin Daddy Mammah ta kai Ruqayyah, kana ganin dattijon kasan sun haɗa dangantaka da Daddy don kamar shi ya haifi Daddy sbd resambulance, da ladabi Ruqayyah ta gaida Kawu, ya amsa yana tsokanarta a matsayinta na jikarsa, Ruqayyah ta duƙar da kai tana wasa da ƙafarta, a hankali ta shigar da ainahin abinda ya kawota Kaduna, Kawu ya gyaɗa kai bayan sauraronta yace "toh ko so kike ki zama tsohuwar guzuma babu aure ƴar nan.. naga tsohon naki gata zai miki..", Ruqayyah ta fara sharar hawaye tace "Kawu wllh wnda zai auramin ne banaso..", Kawu ya jinjina kai yana kallonta da kyau yace "ja'ira daman ba zuwan Allah da ma'aiki kikay ba, ashe takakkiyarki ce ta kawoki". kafin magrib Ruqayyah ta iso kano, a galabaice tazo duk tayi wani wiƙi wiƙi, daman ba wata lfy ta samu ba kuma shine ta tarki uwar tafiya. ★Bayan sallar la'asar Hajar ta buɗe ƙofar ɗakinta a hankali, saida ta gama ƙarewa corridor kallo taga babu kowa snn ta fito, walking slowly ta sauka downstairs, zuciyarta ta ringa bugawa cause ba ta son encounter dashi, luckily for her ta tarar babu kowa a palourn, da sauri ta shige kitchen ta dafa Noodles sharp sharp ta fito, tana rufe ƙofar saiga footsteps ana sakkowa ƙasa, ta ɗaga kai ta kalli stairs din, suna yin ido huɗu tayi sauri ta juya masa baya tana turo baki, runtse idonta tayi ta wawaki handle ta murɗa ta koma kitchen din ta rufe ƙofar, jingina tayi da ƙofar tana mayar da numfashi, kawai abinda ya mata yau da safe ke mata yawo a brain, idan ta tuna sai taji tamkar ƙasa ta tsage ta shige, bayan kamar minti goma ta buɗe ƙofar ta leƙa, ajiyar zuciya tayi ta fito ta haura sama bayan hancinta ya cika da ƙamshinsa da ya bari a palourn. washe gari Nurain ya fito daga room dinsa ya gama shirinsa na fita aiki, har zai sauka sai kuma ya duba tsadadden agogon dake wrist dinsa, ƙarfe tara da minti biyu, ƙofar room dinta ya buɗe ya shiga, Hajar dake zaune gefen bed ta ɗago ta kallesa, tin ɗazu ta tashi tayi wanka ta shirya, so take ta fita amma kuma ta kasa, tana ganin shine ta tashi da mugun gudu ta shige bathroom ta garƙama lock, Nurain ya haɗe thick eyebrows dinsa ya ringa kallon ƙofar bathroom din kafin ya juya ya fita, yana zuwa hospital din patient huɗu yayi attending suka shiga meeting, akan Seminar da nan da 3weeks zata zo akay meeting din, shi dai baiso ba kwata kwata, don har dashi acikin wadanda zasu, duk yadda yaso ya noƙe kar yaje amma haka Dr Mansoor yace ai shine zaiyi representing thoracic surgeon, bbu yadda Nurain ya iya hka ya fito meeting din under probability don yace sai yayi tunani tukun, baima koma office dinsa ba kawai ya bar hospital din, saida ya biya aiken da Abba ya masa na amso passports snn ya wuce gidansu, da yamma ya shiga wajen Abba ya kai masa saƙon tinda ya dawo a lokacin, da sallama ya shiga great room din, yana zama saiga Abba nan ya fito daga bedroom, bayan sun gaisa Nurain ya ajiye envelope din da ya shigo da ita yace "gashi Abba..", Abba ya buɗe envelope din ya fara ciro passports din, Nurain na kallon passports din yace "harda Noor ne..?", Abba yace "yeah..", Nurain ya gyaɗa kai yace "amma exams din fa..?", Abba yace "kafin nan ta gama ai, tace nan da 2weeks zata gama exams din..", Nurain yace "alright.. bari na wuce mosque..", Abba yace "Ohk" da haka ya tashi ya shiga bedroom to perform ablution. da misalin karfe takwas da rabi na dare Nurain na tsaye jikin motarsa yana jiran Noor, hannu na dukan cinya Noor ta fito compound din ta isa bakin motar tana kallonsa tace "Mami ta hana na zuba maka abincin wai kaci a gida..", kasa cewa komai yayi ya tsaya yana kallonta, Noor da taga reaction dinsa weird tace "Yaya wai Anty Hajar din bata iya girki bane..?", yace "just cut it good night...", motarsa ya shiga ya bar gidan with speed, yana zuwa gida yayi refreshing kansa ya sakko downstairs, cup of Café latte ya haɗama kansa, da cup din a hannunsa ya fita balcony ya zauna kan kujera dake wajen, slowly yake sipping coffee, kira yaga yana shigowa ta jikin smart watch dake hannunsa, daman yau duk dashi yayi amfani wajen calls, airpods ya ciro daga pocket dinsa ya saka one ear, Calmly yace "yeah sister..", from the other side Sakeena tace "brother tataccen mai kirki how are you..?", yayi murmushi don ya fahimci ba'a take masa yace "am fine alhmdllh..", tace "toh Yayi.. ya Hajar..?", yayi sipping coffee yace "kin bar mijinki shi kaɗai ni zaki hanani bacci nan haka..", tace "Yah c^mon bani amsana...", yace "ohh she's fyn..", tace "good..", dariya yayi yace "are you alone..?", tace "yess yess", ya sake yin wata dariyar yace "toh don kar kije kiyi ihu ki razana mutane...", tace "toh nidae ka gayamin mene..?", yace "hmm wai daman Umrahn babu ke za a..?", Sakeena ta miƙe daga kan kujerar da take kwance tace "bangane bani ba, harda ni mna..", Nurain ya gyara airpod din kunnesa ya ɗauki cup of coffeen sa ya shiga ciki, Sakeena tace "tafiyar tazo ne..?", yace "A'a ban sani ba fa, nida babu ni to what concern me da lokacin tafiya..", tace "Auho ai na dauka tafiyar ne yaxo..", dariya ya sake yi don ya hango ydda reaction dinta zai kasance yace "madam where is your passport..?", ta juyo hannu kamar yana kallonta tace "yana nan saina lalubo sa..", yace "hmm toh a nemo lfy", ɗaga kansa yayi yana kallon Hajar da take sakkowa, bata lura dashi ba saida ta gama sakkowa tass, tayi sauri ta sunkuyar da kanta sai kuma ta juya ta koma saman da sauri, Nurain yace "i will call you tomorrow insha Allah sister" ya cire airpod din kunnesa yana kallon stairs, ajiyar zuciya yayi ya nufi stairs din.....✍️ Join my WhatsApp group 👇 💛 HAJAR 💛 {55..} ★Washe gari Monday Nurain na zaune office dinsa yana duba patient, yana gama duba patient dake office din kira ya shigo ta wayar landline, picking yayi yace "yess", Secretaryn sa Haleema tace "sir A Nurse tana son ganinka..", yace "i thought it is something important, next patient ya shigo.." bai jira cewarta ba ya katse kiran, Haleema ta ajiye landline din tana kallon Ruqayyah da tayi tsuru tsuru a gabanta, duk ta rame kamar ba Nurse Ruqayyah ƴar gayu ba, yanzu gayun ma baya amsarta ko tayi, Haleema tace "A Nurse ki ɗan jira a waje yace Patients yake dubawa..", Calmly Ruqayyah ta gyaɗa kai tace "Okay", tinda dai yace ta jira ai mgana ta ƙare, knn zai saurareta idan ya gama duba patient din, fita tayi daga office din ta zauna kan silver chair dake waje, tanata zaune a wajen har patient din da suke bin layi suka ƙare daman su 20ne, wayarta dake cikin scrub pocket ce tayi ringing, ta ciro wayar tana kallon mai kiran kafin tayi picking ta kara a kunne tace "ina ji Jiddah..", Nurse Jiddah tace "haba Ruqayyah ina kika tafi haka, station din fa babu kowa, Amina ta riga tayi miki handing over fa, gashi can ma ward din da kike kula dashi lokacin yiwa diabetic patient din nan insulin ya cika, ya kamata kixo ki masa yaci abinci dan Allah...", Ruqayyah ta lumshe idonta dan kanta ne ya sara tace "Jiddah dan Allah kije ki masa allurar ni na ɗan fita ne bana nan, zan jima kafin na dawo in yaso nayi night duty...", Nurse Jiddah ta taɓe baki tace "Au haka kika fita bayan ga jakarki nan da Abayarki ina gani, ko dai haka kika fita ƙindu ƙindu with Scrub...", Ruqayyah tace "to dai bana cikin department din ina can Pediatric department..", Nurse Jiddah tace "Ohk, toh gsky this is the last tsakani ga Allah, ke kaɗai kike raɓarɓashe albashinki..", Ruqayyah tace "thank you..", Nurse Jiddah dai ta kashe wayar tana tsaki, Ruqayyah ta mayar da wayar pocket, ta ɗaga kai tana kallon ƙofar office din, tashi tayi kafin ta buɗe aka rigata ta ciki, Nurain ne ya fito riƙe da briefcase dinsa don ya gama gida zai wuce, Ruqayyah ta dubi hannunsa ganin briefcase tace "are you leaving...?", ko kallonta beyi ba ya wuce zai bar wajen, ta bisa da sauri ta riƙe hannunsa hawaye har ya ciko idonta, wani mugun kallo ya watsawa hannun nata with stern voice yace "hands off..", ta cikasa sai kuma ta sha gabansa tana kallonsa, tace "Do you know how much i love You..?, do you know how long i waited to see you...?, why do you not listen to me...?, i don't want to part from you again, so you must listen to me dearest.." tana gama faɗin hakan ta fashe da kuka tana dukansa a chest painlessly, kukan da ta fashe dashi ne ya janyo attention din few mutanen dake wajen, har lokacin bata dena rusa masa kuka ba, janta yayi zuwa office dinsa, Haleema da ta gama shiryawa itama zata tafi ta bisu da ido, Nurain ya ajiye briefcase din kan table ya shafa hair dinsa kafin ya zura both hands dinsa a pocket, juyowa yayi yana kallon Ruqayyah da take kuka bil haƙƙi, ya sauke ajiyar zuciya yace "damn it.. what are you doing Ruqayyah..", ta zuba masa jajayen idanunta da muryar kuka tace "ai ka ƙi ka haƙura sai haƙuri nake baka Dearest..", ya girgiza kai yace "we already sort it out Ruqayyah, am not keeping any grudge against you, ki dena bani haƙuri ni babu abinda kika min, in ma akwai toh na haƙura..", tana shessheƙa tace "ka haƙura toh me yasa kake avoiding dina, ka dena picking calls dina, idan nazo office dinka ba a barina na shigo..", ya dubi ceiling feeling confuse yace "Ruqayyah..", bata amsa ba amma ta zuba masa idanu, yace "Allah ma ya gani am done with you, I don't have any feeling for you now and forever, please let me be, bana so na miki abinda baza kiji daɗi ba so stay far away from me, kawai abinda ya wuce ya riga ya wuce, abu ɗaya na sani yanxu akanki shine kina cikin team members dina bayan haka babu komai... kiyi abinda zai fisshe ki A Nurse.." yana gama faɗin haka ya ɗauki briefcase dinsa ya bar office din with speed, like one living statue haka Ruqayyah ta daskare a tsaye, tamkar an dagargaza zuciyarta haka take ji, Haleema ce ta shigo tana kallonta tace "amm zan rufe office din..", Ruqayyah ta ja ƙafa ta fito, da ido Haleema ta bita tana girgiza kai tace "sai ki haƙura dai tinda tin farko kin yiwa kanki sagegeduwa..", Ruqayyah ta juyo ta kalleta dan ramm taji abinda ta faɗa, sai kuma ta juya ta cigaba da tafiya. Ruqayyah bata zauna a asibitin ba haka nan ta shirya ta tafi gida, Ruqayyah na zuwa gida ta gamu da tashin hankalin da ya shalleke tunaninta domin kwa saƙonta ya isa ga Daddy, daman tin kwanaki biyu da zuwan Ruqayyah kadunan Kawu ya kira Daddy yace yana son ganinsa, Daddy yace masa zaizo insha Allah ranar Litinin, toh yau Monday da wuri Daddy ya shirya ya tafi Kadunan don yaji kiran da ƙanin mahaifin nasa ke masa, ba ƙaramin fusata Daddy yayi ba, Kawu kawai mgana ya masa ba wata mai zafi ko ɗumi ba, shi takaicin Daddy wai har Ruqayyah ce zata kaisa ƙara wajen Kawu, knn ja dashi zatay, tinda ya ɗauko hanyar kano bayan ya bar Kaduna nan ya kira Momy a waya, tashin hankalin da ta shiga ba kaɗan bane, itama taji haushin abinda Ruqayyah tayi. Momy na zaune palour ta dafe kanta tace "Ruwayyah ki haɗa kayanki ki wuce gidan Safiya..", Ruqayyah ta ƙarasa palourn zuciyarta na bugawa tace "Momy sbd me dan Allah..?", Momy tace "kinje Kaduna wajen Kawu ko bakije ba..?", Ruqayyah ta sunkuyar da kanta tamkar munafuka, Momy ta daka mata wata tsawa tace "tambayarki nake malama", Ruqayyah ta koma ta manne da bango ta sunkuyar da kanta tace "naje..", Momy tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un, kin kyautawa kanki, ki wuce kiyi abinda nace..", Momy ta tashi ta shiga room dinta ta kira ƙanwarta Haj Safiyya ta sanar da ita Ruqayyah zata zo, bayan ta gama wayar ta fito ta shiga room din Ruqayyah, zaune ta tarar da ita kan bedside ta zabga tagumi, Momy tace "kin haɗa kayan Ruqayyah..?", Ruqayyah tayi firgigit bayan ta fito daga duniyar tunani tace "A'a", Momy ta gyaɗa kai tace "toh kar kiyi sauri ki zauna har ya dawo gidan ya sameki, wllh babu ruwana, dalla malama tashi ki shirya..", Ruqayyah na sharar kwalla ta gama haɗa kayanta set biyu a ƙaramar jaka, duk Momy na tsaye tana kallonta, da jakar a hannunta Momy ta iza ƙeyarta har palour, ganin batada niyyar fita Momy ta turata waje tace "maza ki tafi.." da hka tayi banging door, Momy na sane tace Ruqayyah ta bar gidan, tasan ran Daddy ya ɓaci matuƙa, gwara idan ya ɗanyi sanyi ta dawo koma wane hukuncin zai mata ita ta janyo amma dai banda lokacin da ransa yake tafasa. ★Bayan Hajar ta idar da sallar la'asar ta sakko downstairs, kitchen ta shiga ta ɗakko abincin da ta dafa tin ɗazu, har zata haura sama da warmer din sai kuma ta fasa ta zauna nan palour, tana fara cin abincin saiga ƙarar bell, ta ajiye spoon din hannunta tana kallon door, saida aka sake danna bell din snn ta tashi still tana kallon ƙofar, toh Allah yasa dai a buɗe take tinda dai tasan kullum a rufe take, da wnn tunanin ta isa kusa da ƙofar ta murɗa handle, zaro ido tayi jin a buɗe take, tana buɗewa tayi arba da Hafsah, Hajar ta gwalo ido don bata taɓa tsammani ba, cike da murna tayi hugging dinta tana welcoming dinta, Hafsah dai kawai binta take da kallo ganin yadda ta canza, ta kusa linka ainahin farinta har wani pink pink take, a palour suka zauna Hajar tace "yasu Humairah da Anty..?", Hafsah tace "suna nan lfy wllh.." sai kuma ta riƙe haɓa tace "kinyi luf luf abinki, wnn luƙui luƙui haka..", Hajar ta galla mata harara tace "ke nan din ya miki kama da wajen da mutum zai wani luf.." tashi tayi ta shiga kitchen ta kawo mata ruwa da lemo, Hafsah tace "ke kullum wayarki a kashe..", Hajar ta taɓe baki tace "hmm ta lalace..", Hafsah ta ringa kallon palourn tace "shi bai sayar miki wata ba..", Hajar ta yamutsa fuska tace "shi din wa.. Hafsah knn..", Hafsah ta ɗauki lemon ta zuba a cup tasha, after like 40mins Hafsah tace "toh na gaisheki Hajar, tafiya zanyi bazan kai magrib ba, unguwar nan napep wahala yake, kinga ma waccan karon da nazo ban samu napep ba..." sai kuma tayi shiru tana murmushi tace "kinsan kwa wane ya mayar dani gida a ranar..", Hajar tace "sai kin faɗa..", Hafsah tace "wnn mutumin da muka hadu dashi a Supermarket, Ahmad din nan..", Hajar tace "ohhh Allah sarki..", Hafsah ta sauka daga napep bayan tazo gida, handbag dinta ta bude ta basa kuɗinsa, kallon motar dake parke a gefen titi ta ringa yi, ta dai amshi canjinta ta zaga wajen slapp zata shiga gida, buɗe motar yayi ya fito yana kallonta, ya rufe motar yabi bayanta Calmly yace "Assalamu alaikum..", no doubt zamm ta ɗauki muryar, amma she was shocked, a hankali ta juya tana ƙirƙirar murmushi tace "Wslm..", ya shafa kwantaccen beard dinsa yace "how are you doing..?", tana ɗaga kanta taga Abdallah yana tsallakowa daga other side din titi, zuciyarta ta buga da ƙarfi, ɗauke kanta tayi tace "lfy alhmdllh ngd..", yace "masha Allah daman i am passing by nace bari mu gaisa da friend dita tinda bata picking call a gaisa..", daidai nan Abdallah ya tsallako, jimm yayi yana kallonta sai kuma ya wuce cikin gida, Hafsah tayi murmushi tace "toh ngd sai anjima", ta juya ta shige gida da sauri, Ahmad ya bita da kallo bayan wani lokaci ya shiga motarsa ya bar unguwar, Hafsah na shiga gida ta tarar da Anty zaune a palour, Abdallah ma na palourn zaune kan 1sitter yana cin abinci, ta kalli position din da yake sau ɗaya sai kuma ta dubi Anty tace "Anty na dawo..", Anty tace "toh sannu da zuwa ya Hajar din..?", Hafsah tace "wllh sumul take Anty, tayi kyau abinta..", Anty tace "masha Allah..", Hafsah ta dubi jakarta jin wayarta na ringing, tashi tayi ta shiga room dinsu tana satan kallon Abdallah da ya bita da kallo, Anty ta ɗauki wayarta dake gefenta ta kira Umma, bayan sun gaisa Anty tace "ya jikin Mu'azzam..?", Umma tace "jiki alhmdllh ai yaji sauƙi sosai..", Anty tace "toh an gode Allah, ai Hafsah na tura taje ta duban ƴar tawa kafin naje da kaina..", Umma ta numfasa tace "ba wata matsala ko Jamilah..?", Anty tace "lfy lou wllh Adda, kinsan ƴar tawa haƙuri wala, idan da gaske ba zaman lfyar da tini ta taho fa, amma tinda kika ga shiru toh lafiya ce gsky..", Umma tace "nima nayi tunanin hka..", Anty tace "yanzu idan an kwan biyu sai naje da kaina..", Umma tace "toh shknn ngd Jamilah..", Anty tace "ba komai Adda, sai anjima.." da haka sukay sallama. ★Bayan tafiyar Hafsah Hajar ta koma room dinta, two hijab sai kayan baccin da ta saka ta ɗauka ta shiga bathroom dasu ta wanke, bayan ta gama wankewa ta fito dasu a cikin bucket ta sauka ƙasa don ta shanya, ta main door ta fita daga building din, can backyard taje ta shanya snn ta dawo ciki, tana dawowa daman an kira sallar magrib don haka tayi sallarta, can wajen ƙarfe tara harta yada pillow zata kwanta ta tina da kayan shanyarta, tashi tayi ta leƙa window taga garin akwai hadari, hijab ta saka ta fito daga room dinta Walking like a chameleon ta sauka, tsaye tayi a palourn tana kallon Tv da ta gani a kunne, ga kuma Lap top kan hannun kujera itama a kunne, ta taɓe baki ta nufi ƙofa, zagawa tayi can backyard din ta kwaso kayanta, tana tafiya tana kallon gidan in it's night view, fitilu ko ina sai kace rana, tsaye tayi daidai window din kitchen tana kallon ciki, lokaci guda ta matsa gaban windown tana kallonsa, he is in his pajamas making coffee, ta ringa bin duk abinda yake da kallo tana taɓe baki, a gabanta ya gama haɗa coffeen ya tsiyaye a cup ya fita bayan ya kashe coffee makern, ta zagayo ta buɗe ƙofa ta shiga, Nurain ya juya yana kallonta, ɗauke kanta tayi ta nufi stairs abinda, ya haɗe thick eyebrows dinsa ya cigaba da abinda yake jikin Laptop. washe gari Hajar na idar da sallar asuba ta fito, har lokacin gari baiyi haske ba, tana shiga kitchen ta buɗe cupboard ta ciro coffee powder, har wani nishadi take yau zata sha abinda take marmari, switch din coffee maker ta kunna, No milk no sugar da tsurar cocoa powder tayi amfani, tana gamawa ta tsiyaye a cup, harda wani ɗan karkaɗa cup din wai ya huce da zafi, tana sha ta yamutsa fuska bayan ta guntsesa a baki, wani mugun ɗaci ne ya kaure mata a baki, da sauri ta tofar da na bakinta acikin sink, ta kunna pampo ta kuskure bakinta, kallon cup din worst coffeen da ta haɗa tayi tace "chaɓɗi jamm nida maɗaci..", tini ta sakar masa ruwan pampo ta wanke cup din ta fita daga kitchen din tana gyatsine. ƙarfe bakwai da rabi Nurain ya sakko downstairs, yana zaune a palour yana shan sahibin nasa, ya duba time ta faskeken agogon dake manne a palourn, tashi yayi ya fita compound zai sanar da Inuwa ya wanke masa wheels din motarsa kafin ya fita. tinda Hajar ta hango cup din daga sama tayi sauri ta sakko, ehen ai kam sai tasha kuwa, ta isa inda cup din yake ta ɗauka, tini ta kwankwaɗe tass ta ajiye kofin a inda yake, saidai tana ɗaga kanta sukay ido hudu dashi, yayi folding hands dinsa yana kallonta babu ko ƙiftawa, ɗauke kanta tayi ta sha kunu irin ai nawa ne din nan, ta juya zata bar wajen kawai taji saukar muryarsa mai zurfi a kunnenta "Ke.. dan kinga jiya ban miki mgana ba shine ma yau kika aikata ko..?", ta juyo tana ɗage gira babu ko nadama a fuskarta tace "Au akan wnn maɗacin...", ya tsuke ido irin what, ta juya lulu eyes dinta tace "toh wllh sai nasha wani yace ka ringa ajiyewa", ta galla masa harara ta wuce zata hau stairs, bai bata damar hakan ba dan tini yayi blocking front dinta, ta ɗaga kai tana kallon how huge he is, gata wata dwarft a gabansa, Calmly yace "yeah no problem tinda kinada abin biya young lady..", da sauri ta ɗaga kai ta kallesa, lokaci guda brain dinta tayi booting on, ta zaro lulu eyes dinta kafin ta ja da baya tana girgiza kai, a karo na farko da ta taɓa ganin murmushinsa amma kuma sai ya mata kama dana mugunta yace "sai kin biya..", da gudu ta koma cikin palourn tana ƙoƙarin zagayesa ta haura sama nan ma ya hana hakan, ganin zai cafkota ta tsala wani uban ihu ta ruga corridorn shiga guest room, sosai zuciyarta ta buga ganinsa a corridorn ya biyota, ai kam ta murɗa ƙofar guest room din ta shige da sauri tayi banging door, saidai fa unfortunately for her taga babu key ajikin ƙofar, ta jingina da jikin ƙofar ta danne with all her strength, sai kace wanda ya tura wani bicycle haka ya tura ƙofar ya buɗe, wani uban ihu ta tsala ta koma can ƙarshen ɗakin tana zaro ido tamkar ɓera a buta, ya mayar da ƙofar ya rufe ya tsaya yana kallonta yace "ke da kike da abin biyan bashi young lady mene kuma na tsorata, ohh c^mon ki biya ko na fanshe abina..", ta shiga yarfe hannu tace "na shiga uku".....✍️ ********************** ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** ************************* ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ************************** 💛 HAJAR 💛 {56..} Ko one step bai ƙara ba daga inda yake tsaye jikin ƙofa yace "mene kuma na shiga uku.. zaki biyani ko sai na fanshe..?", bakinta na rawa sai kace an jona mata shoking tace "zan biyaka..", yace "with what..?", tace "shi shayin naka dashi zan biya ka", yayi nodding kansa yace "alright muje ki bani", ta gyaɗa kai da sauri, har zufa ta jiƙa mata goshi gashin wajen ya sake kwanciya da santsi akan ydda yake na asali, ganin bata motsa ba sai muzurai take yace "kona fanshe ne..?", ta yarfe hannu ta girgiza kai tace "A'a dan Allah..", ya matsa daga bakin ƙofa yace "toh zo ki wuce..", ta gyaɗa masa kai kafin ta fara tafiya a hankali, tana zuwa bakin ƙofar tace "dan Allah karka taɓani..", yayi folding hands dinsa yace "wuce nace..", sum sum ta fita daga ɗakin yana biye da ita. tana zuwa palour ta fakaici kallonsa ta gefen ido, taga dai biye yake da ita kuma babu distance sosai a tsakaninsu, speed ta ƙara, ai kam yana ganin haka yasan akwai abinda take target, da mugun gudu ta ɗiba zata haura sama, tini ya fixgota ai kam ta tsala ihu ta fara kiciniyar kwace kanta, ya tsuke piercing eyes dinsa yace "Ke..! you think am joking ba..", ta girgiza kai tace "toh ba nace zan biyaka ba ai haɗa maka zanyii", tayi wani farr da dogayen eye lashes dinta, sakinta yayi ya ɗaure fuska ya nuna mata kitchen yace "ai nan za kiyi malama..", Kitchen din ta shiga tana turo baki, tsaye yayi a bakin ƙofa yana kallonta, haka nan ta buɗe cupboard ta ciro Cocoa powder ta matsa gaban coffee maker, kawai kallonta yake hannunsa zube a pocket, ƙasa ƙasa Hajar take ƙunƙuni tana jiran shirmen da ta haɗa ya kammala, wata glass kitchen Ware ta buɗe ta ɗakko Mug ta tsiyaye a ciki, shi dai kawai kallonta yake without blinking, juyowa tayi da Cup din a hannunta ta miƙa masa tace "gashi na biyaka", kallon cup din yayi sai kuma ya dubeta, ko kallonsa ba tayi taci mur, ganin bai amshi cup din ba ta kallesa, ganin kallon da yake mata ta ajiye cup din kan cabinet tace "gashi nan ka ɗauka", yace "shanye na bar miki..", ta gwalo idanu ta girgiza kai tace "A'a bana sha..", chab haka kurum ta ɓata bakinta, na ɗazu data haɗa saida ta kuskure bakinta da mouth rinks, ciro hannunsa yayi daga pocket walking towards her yace "ɗauka ki shanye", ta murguɗa masa baki tace "A'a wai ana dole ne, nifa bazan sha ba..", da baya ta koma ta manne da jikin cabinet, ya matsa daf da ita har ya mata rumfa, zaro ido tayi jin ƙamshinsa har throat dinta, tayi ƙoƙarin zillewa amma ya hana hakan ta hanyar saka hannayensa a sides dinta ya dafa cabinet din data manne da ita, wani mugun yawu ta haɗiya tana shaƙar scent dinsa tace "wai meye haka ne, bana biyaka shayin ba..", looking at her pink lips yace "shine nace ki shanye na bar miki..", ta kau da kanta tana turo baki tace "ni bazan sha ba..", yayi slight smirk yace "really..", ta gyaɗa kai irin yess, zaro ido tayi ganin abinda yake shirin yi ta tsala ihu tace "ni bana son irin haka wllh..", without care yace "for the last time i said drink it..", da sauri ta wafto mug din ta kafa a baki, a hankali ta kurɓa sbd akwai zafi, ta yamutsa fuska tana kakari bayan ta haɗiye da kyar, yana kallon reaction din fuskarta yace "good..", Mug din zata mayar ta ajiye yace "shanyewa fa za kiyi young Lady..", wani daram zuciyarta ta buga har tana jin bugun har maƙoshi, tini idonta ya ciko da hawaye, ta sake kafa kai ta kwalkwala bayan ta ɗauke numfashinta, yana kallonta saida ta shanye tass, ya sunkuya yana kallon empty cup din da har lokacin yake riƙe a hannunta tana mayar da numfashi tamkar wacca tayi gudun shekara, ta ɗaga idanunta da suka cika da hawaye ta kallesa, ido huɗu sukay tayi sauri ta sunkuyar da kanta, ajiye kofin tayi bata bari sun sake haɗa ido ba, ta sulale ƙasa ta raɓa ta wuce, bai dakatar da ita ba ya juyo yana kallonta thick eyebrows dinsa a haɗe, Hajar ta buɗe ƙofar kitchen din sai kuma ta fashe da kuka tace "Allah sai ya sakamin da ka bani maɗaci nasha.." with speed ta fita tana kuka sosai ta haura sama, murya ƙasan throat yace "Silly girl..", fitowa yayi daga kitchen din, ya kalli agogo ganin har takwas da rabi ta gota ya haura sama, ɓangarensa ya shiga ya wuce bathroom, bayan yayi wanka ya fito yana goge sumarsa da hand towel, yana gama shiryawa ya fito ya sauka downstairs, compound ya fita zuwa parking space, ya tarar har Inuwa ya gama wanke wheels din motar, buɗe motar yayi ya shiga ya fara warming dinta, yana jiran ta gama warming yace "hmm silly girl..", driving ya fara yi slowly ya fita daga gidan mai gadi na ɗaga masa hannu, yana isa hospital E.R ya wuce cause Haleema ta sanar masa akwai patient da zai duba a can din, Nurse Jidda ce a gefensa tana masa bayani, ya amshi stethoscope dake hannunta yayi listening bugun zuciyar patient din da yake unconscious, yana gama examining patient din ya fita bayan yace ɗaya daga cikin familynsa ya samesa a office, Calmly Nurain ya yiwa relative din patient din bayanin komai, snn ya masa tambayoyi akan tin yaushe patient din yake rashin lafiyar, a take Nurain ya sanar masa cewa surgery yake buƙata in not less than 48hrs in ba haka ba his life is in risk, godiya ya yiwa Nurain kafin ya tashi ya fita, daga haka Nurain ya fara attending patient dinsa, After 40mins Khaleel ya shigo da lab coat ajikinsa, he wasn't himself cikin damuwa yace "Dr Boss kaxo ka duba patient din nan he is gasping..", da sauri Nurain ya tashi ya fita, Khaleel yabi bayansa, E.R ya wuce da sauri, bayan ya samu patient din ya daidai snn ya fito, ya dubi Khaleel yace "get ready for surgery...", Khaleel yace "Yeah..", Nurain yace "A Nurse su shirya patient din zuwa surgery room..", Khaleel yace "tom". Nurain na tsaye gaban wash hand sink dake surgery room yana wanke hannunsa, har ya saka surgeon gown, Dr Marwan da zaiyi first assistance already ya gama wanke hannu ya shiga room din, Khaleel ne ya shigo a ƙarshe yana kallon Nurain da yake ta durje hannu da liquid soap yace "Ammm A Nurse fa ba tazo ba amma ga Nurse Jiddah...", Nurain ya ɗaga kai yana kallon Nurse din dake cikin surgery room din tana jera instrument acikin tray, ta saka nose mask a fuskarta, shi yasha ma Ruqayyahn ce ashe ba ita bace, keenly yace "Ohk.." ya cigaba da wanke hannunsa, yana gamawa ya shiga surgery room din ya saka nose mask da hand gloves, gaban surgery bed din ya isa ya tsaya a position dinsa na haed of the surgery. ★Umma na zaune tsakar gida a kan kujera tana tsince waken Alala, Sabrah ta fito daga ɗaki sanye da uniform da jakarta goye a baya, Umma tace "Auta kin gama shan kunun..?", Sabrah ta gyaɗa kai tace "Eh Umma nasha..", Umma tace "yawwa toh shiga ki gaida Baba saiki fito ki tafi karki makara kinji yarinyar kirki..", Sabrah ta shiga ɗakin Baba bayan ta gaishesa ya bata kuɗin makaranta ta fito, ta yiwa Umma sallama snn ta tafi, Umma tabi bayanta da kallo tana murmushi dan zamm yayarta. Sa'adatu ce ta fito ɗakin Maama da brush da toothpaste a hannunta, vest ce a jikinta sai zani, tayi wata wawuyar hamma babu ko rufe baki ta ɗaga hannu tayi miƙa, armpits din nan ba a cewa komai don kamar a kitsa, fatarta har wani shuni shuni take don taji chemical din allura, daman kana ganinta kasan sallah wala don batayi ba kuma batada niyyar yi, tukwanen ruwa ta buɗe ta zuba a buta ta tsugunna ta fara brush, tana gama brush din ta wanke fuskarta da ta cika da kwantsa, ta tashi ta shiga ɗaki, Maama dake zaune ɗakin tace "Sa'adatun Maama ba kiyi wanka ba fa haka zaki tafi kina tsami..", Sa'adatu tace "wllh bazan iya wanka a wnn kwaraɓaɓɓen banɗakin ba sai naje can zanyi..", Maama tace "toh shknn.. ina kwa ƴan albarkar ƙawayen naki..?", Sa'adatu ta ciro Uniform daga cikin Ghana most go wanda sukaci uban squeezing, tana bige uniform din wani bashi ya tashi tace "Mabruk da zeen suna nan sumul, kin manta rashin mutuncin da Baba ya musu da kuma abinda shegiyar gidan nan nunar rana ta musu..", Maama tace "ai kam yanxu zasu iya zuwa su gaisheni ranar da malam baya nan..", Sa'adatu ta taɓe baki tace "hmm wllh sunfi ƙarfin zuwa nan gidan, amma sbd yadda suke sona suka zo aka musu wulaƙanci, nidae bazan sake cewa suxo ba saidai ke kije ki gaishesu, in gaya miki babbar Hajiya mai gidan da muke zama ma ta dawo daga ƙasar waje, ashe gidan nata ne su Mabaruka da Zeenatu yaranta ne..", Maama tace "Aaaa sai naje ai..", Sa'adatu ta gama saka yamutsattsun kayan ta kwama jaka kamar gaske, alhalin jakar babu littafi ko ɗaya kayan sawa ne aciki, Nabilah dai ta taɓe baki don tana jin abinda suke cewa, Sa'adatu tace "toh Maama saina dawo.." da haka ta fita daga ɗakin, tin daga sama har ƙasa Umma ta dubeta kafin ta cigaba da tsintar wakenta, Sa'adatu ta ɗaga murya tana yamutsa fuska tace "Baba na tafi makarantar..", ko second ɗaya bata ƙara ba ta nufi soro ta cire higab din jikinta ta sauya da wani wanda ta fitar daga cikin jaka ta fita, Baba ya fito daga ɗakinsa yana kallon Umma yace "ina Sa'adatun..?", Umma ta nuna soro tace "ta fita..", Baba ya fita daga gidan, Maama ta fito daga ɗakinta tana baza zani ta kalli Umma tace "Munafuka Algunguma meye kuma nace masa ta fita ai cewa za kiyi ta tafi makaranta ba ta fita ba..", Umma ta ajiye farantin da take tsince wake tace "A'a baiwar Allah ya ina mgana da mai gidana zaki sako min baki.. nifa banason shisshigi da kwala kai a faranti, ko kinga ina shiga sabgarki ne...?", Maama ta ƙanƙance mici micin idanunta tace "Eh lallai Faɗima.. ni kike mayarwa da martani..?, Nii..?", Umma ta taɓe baki ta ɗauki farantin wakenta zata wuce ta wanke, Maama ta buga cinya tace "ahayye Eh lallai fa, yau ni naga muggun abu, wato ƴarki tayi aure gidan masu hannu da shuni shine kike fiffiƙalemin Faɗima..", da mamaki Umma ta juyo tana kallonta jin abinda ta faɗa, toh me ya kawo wnn magnar kuma, Maama ta cigaba da faɗin "toh ai saiki bari ƴar taki ta sha kafin ki fara fiffiƙalewa, dan da yardar Allah sai an gille mata kai an kawo miki gunduguilar a kwali..", Umma tayi murmushin ƙarfin hali tace "ki gani a ƙoƙon shanki, insha Allah babu abinda zai samu ƴata sai alkhairy da albarka..", Maama ta fito a fusace ta ɗauki taɓarya ta nufi Umma tace "ki sake cewa tak kiga idan ban jirga miki ita ba, shegiya ragowa.. dangin ubanki ma na Yola kasa zama sukay dake sbd baƙin hali..", Mu'azzam ne ya fito daga ɗakinsu idanunsa sunyi jajir, wajen mahaifiyarsa ya isa yace "Umma dan Allah koma ɗaki...", Umma tayi still tana kallon Maama ta kasa cewa komai, Mu'azzam ya sake cewa "dan Allah Umma", Umma ta kallesa sau ɗaya snn ta wuce ta shiga ɗakinta yabi bayanta, ganinta yayi zaune gefen gado hawaye na zuba idonta, ya isa gaban gadon ya durƙusa gabanta yace "Umma kiyi haƙuri dan Allah..", Umma ta share hawayen tace "Ibrahim idan tura ta kai bango ɗan Adam baya iya jurewa... kana ganin taɓarya ta ɗauka zata bugamin, me na mata ne a duniyar nan, ƙiyayyar bata tsaya iya kaina ba harku ta shafa, Hajara ma da ta bar gidan kullum sai an saka mata baki..", Mu'azzam yayi ajiyar zuciya yace "Umma insha Allah ba zaki ƙara wata biyar a gidan nan ba, akwai kuɗin da nake tarawa insha Allah zan siya miki gida ki koma can da zama..", Umma dai kawai kallonsa take kafin ta girgiza kai tace "ka gina gidan da zaka zauna dai Ibrahim..", ya girgiza kai yace "Umma saina gina miki gida snn zan iya gina nawa..", Umma tayi murmushi tana nuna masa kofin dake rufe kan mirror tace "ga kunun ka can..", ya tashi ya ɗauki Cup din yace "nagode Umma..", Umma tace "sai wani satin za a duba ɗaurin ko..?", ya kalli hannusa mai ɗaurin karaya yace "Eh" da haka ya fita a ɗakin da cup din kunun sa. ★Da misalin takwas na dare Nurain na zaune palourn Mami yayi resting da jikin kujera, Mami dake shan fruit salad ta dubesa tace "ai da zuwa kayi ka kwanta since you are exhausted..", ya buɗe idonsa dake a lumshe yace "yeah.. zuwa eight thirty zan wuce..", Mami tace "Okay.. wai hour nawa surgeryn ya ɗiba..?", ya sauke numfashi yace "5hours..", Mami ta gyaɗa kai tace "Ohk..", Noor ce ta shigo da plate a hannunta ta ajiye kan carpet tace "Yaya gashi..", plate din ya ɗauka ya buɗe, Mami ta leƙa ganin abinda ke ciki tace "wnn abar tana riƙe ciki ne, ko da yake ga protein a gefe..", Nurain ya ɗauki fork ya fara ci a hankali, yace "Mami i thought harda Sakeena a tafiyar naku..", Mami tace "yeah harda ita ai..", Nurain yace "opp amma babu passport dinta a wanda na amso..", Mami tace "Are you sure..", ya gyaɗa kai yace "sure", Mami tayi jim kafin tace "ohh zan tambayi Abba may be ya canza ne..", bayan Nurain ya gama cin abincin ya tashi ya wuce kitchen da plate din, wajen Mami ya shiga ya mata sallama ya fito, yana fita compound yaga wani gagarumin hadari ya haɗo, motarsa ya shiga ya kunna, agogon dashboard ya duba yaga nine dot, with his speed driving zai iya isa gida kafin nine twenty, yana kan hanya aka fara yayyafi, har dai ya isa gida ba a tsuge da ruwa ba, parking yayi a parking space ya fito yana amsa sannu da zuwan da Inuwa yake watso masa, balcony ya wuce yana murɗa door handle akai wata walƙiya mai shegen haske sai kuma wata tsawa mai burga ƴan hanji, tini ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya, a lokaci guda ji kake ɗiff wutar gidan ta ɗauke. Hajar ta fito daga wanka knn tana shirin buɗe wardrobe taji tsawar har ƙoƙon kanta, zuciyarta ta bugu da ƙarfi, bata gama daidaita ba wani mugun duhu ya kaure room din ko tafin hannunta bata gani, a hankali ta sulale ƙasa ta takure waje ɗaya, kawai saita tuna shekaran jiya da yace mata akwai Aljanu da dodo a toilet, wnn tunanin yasa ta sake firgita matuƙa, gashi batada waya ballanta ta kunna taga haske. Nurain ya tsuke piercing eyes dinsa dan wnn abu ne da bai taɓa faruwa ba, toh ai ko nepa aka ɗauke Solar da kanta take canzawa ba tare da an canza ba, wayarsa ya ciro daga pocket ya kunna torch, inda wutar gidan take ya wuce, yafi 20mins trying to figure out what is happening amma ya kasa cause it's out of his field, kwata kwata ya rasa mene ya jawo hakan, bayan ya gaji da taɓe taɓensa ya bar wajen ya wuce cikin gida, da fitilar wayarsa ya haska har ya haura upstairs ya shiga ɓangarensa, ba ƙaramin ɓaci ransa yayi ba gashi kuma ya gaji so yake ya kwanta ya huta, bathroom ya wuce yayi refreshing kansa ya fito yayi wrapping kansa da bathrope, after ya saka Pajamas dinsa kawai ya haye gado ya kwanta, yana lumshe idonsa yaji ta faɗo masa, zaune ya tashi ya zura room slippers ya fito daga bedroom din zuwa palour kafin ya fita long corridor din, after few seconds staring at the door ya buɗe ya shiga, kan bed ya fara haskawa yaga wayam, ya haska kan carpet nan ma yaga wayam, shiga ɗakin yayi sosai yana haska ko ina, shessheƙar kuka ya jiyo daga wajen wardrobe a ta gefen gado, wajen ya isa yana haskawa ya ganta ta haɗe kanta da guiwa ta dunƙule waje ɗaya, ɗauke kansa yayi ganin hasken fatarta, towel ne kawai a jikinta, Hajar ta ɗaga jajayen idanunta da suka kumbura tana kallonsa, ba tasan lokacin da ta miƙe ta faɗa jikinsa ba ta fashe masa da kuka, he just loose his stamina all of a sudden, ji yayi ƙafafuwansa kamar bazasu ɗaukesa ba, ita kam Hajar ƙanƙamesa tayi tana rusa kuka har kanta na sarawa, shoulder dinta ya taɓa yayi saurin ɗauke hannunsa daga wajen ya dafa bayanta, Calmly yace "Ke cikani..", ta girgiza kai ba tace komai ba, yana jin yadda zuciyarta ke bugawa, shi dai kawai yana dafe da bayanta trying to control himself......✍️ 💛 HAJAR 💛 {57..} A hankali ta zame jikinta a nasa kanta a ƙasa, sai kuma ta fara dube duben abinda zata yafa a jikinta tinda har lokacin towel ne a jikin nata, Nurain kam tinda ya ɗauke kansa bai sake kallonta ba, a hankali ta zaga ta bayansa ta wafci hijab dinta ta saka ta koma gefe tana zazzare ido, kawai gani tayi ya nufi ƙofa zai fita, afujajan tabi bayansa ta fashe da kuka tace "dan Allah karka barni a duhu..", ya juyo yana kallonta yace "toh ya kike so na miki..? dole ki zauna a darkness tinda baki jin tsoron yiwa elders dinki rashin kunya.." da haka ya murɗa door handle zai fita, tini Hajar tabi bayansa tana rusa kuka tace "na shiga uku wllh bana son duhu..", kallonta kawai yake wondering ydda kuka baya mata whala, duk wnn rashin kunyar ta ta abu kaɗan saita ɓare baki, komawa yayi cikin room din ya ajiye mata wayar akan mirror snn ya fita, Hajar ta sauke ajiyar zuciya tana turo baki sai kuma ta goge idonta, ta cire hijab ta ƙarasa shiryawa ta saka kayan bacci, riga ce wacca ta tsaya mata a knee, ta ɗakko pillow da duvet ta kwanta kan carpet, kasa bacci tayi don tsoro ma take ji a hakan duk da fitilar da ya bar mata, ga wani ruwan sama da ake ketawa shi kanshi sake firgita ta yake bare idan anyi tsawa, ta duƙunƙune a duvet idonta a runtse, har 11 idonta biyu kuma babu alamar bacci a tare da ita, a hankali Nurain ya buɗe ƙofar ya shigo, kallo ɗaya ya mata ganin idonta a rufe ya wuce ya ɗauki wayarsa ya nufi ƙofa, firgigit Hajar ta buɗe idonta ta miƙe tsaye, da sauri tabi bayansa ta fashe da kuka, still yayi bai juyo ba dan bai san idonta biyu ba, slight hiss yayi yace "ke wai kinada hankali ma kuwa, abin kuka baya miki kaɗan... c^mon wuce ki kwanta am leaving with my phone...", wani sabon kukan ta fashe dashi harda shessheƙa, Nurain ya maida duk attention dinsa kanta yana kallonta cike da mamaki, yarinyar nan kanta ɗaya kuwa, ya haska fuskarta wai yaga na ƙarya ne ko akwai hawaye, taɓe baki yayi ganin hawayen ma sai kace an buɗe famfo, da sauri ta juya masa baya tana ƙunƙuni wai ya haske mata ido, murya ƙasa ƙasa tace "ni ka dena haske ni..", ba tayi zaton ya jita ba kawai taji yace "ohh really... stay in the darkness" da haka ya fice daga ɗakin ya fita corridor, da gudu ta bisa still tana kuka amma kuma a hankali, bai juyo ya kalleta ba ya cigaba da tafiya yana jinta a bayansa har ya isa ƙofar ɓangarensa, yayi sliding door kafin ya juyo ya dubeta yace "yaya dai kike bina young lady...", ita dai ba tace masa uffan ba kanta na ƙasa tana jan fingers dinta tana shessheƙa a hankali, from head to toe ya dubeta da ƴar ɓingilar rigar baccinta iya guiwa, ko ina ta baro hijab din, Calmly yace "don't follow me...", kafin ya shiga ma ita ta rigasa shiga da mugun speed, buɗe baki yayi ya haɗe thick eyebrows dinsa strictly yace "hey get out before i smash you...", ta sunkuyar da kanta without saying anything, ja da baya tayi ta shiga palourn nasa sosai tana turo baki, ya sauke ajiyar zuciya ya isa kan three sitter ya zauna, sai a lokacin ta ɗaga kai ta kallesa sai kuma tabi palourn da kallo, duk da ba haske sosai amma tasan tsadadde ne huge and luxury, Nurain ya duba wayar yaga batteryn ta is running down, ajiyewa yayi kan hannun kujera yayi folding hands dinsa, after few seconds yayi slight hiss ya cire slippers din ƙafarsa ya kwanta kan kujerar, ba sai kuma yaga yadda za tay idan charge din ya ƙare ba, ya lumshe idonsa, nan inda take ta sulale ta zauna kan tiles ta jingina da bango, wani irin sanyi ne ya ringa shigarta, ga sanyin tiles ga kuma na gari da ake ruwa, tanata zaune a haka harta fara gyangyaɗi, takure kanta tayi ta kwanta a ƙasa, cikin bacci taji ana tapping dinta, a zabure ta miƙe tana zaro ido, ya mata nuni da kujera two sitter yace "hey koma can ki kwanta...", har ta turo baki zata lafta masa rashin kunya sai kuma ta fasa, tashi tayi ta tafi inda ya nuna matan ta kwanta, ko seconds 40 bata ƙara ba baccin ya sake ɗauketa, Nurain ya sauke ajiyar zuciya ya koma kan three sitter ya kwanta kafin ya janyo wayar ya kashe fitilar kar yaje ya rasa wcca zai haska da asuba tinda charge din ya kusa ƙarewa. ƙarfe biyar da minti uku Nurain ya farka, tashi yayi zaune yana karanto addu'ar da ma'aiki ya koyar damu, yayi stretching kansa ya lalubi wayar a inda ya ajiyeta ya kunna torch, slippers dinsa ya zura ya tashi ya shiga bedroom ya wuce toilet ya ɗora alwala, bayan ya fito ya saka wata light brown jallabiya ya fita palour, kallon Hajar dake dunƙule kan kujera yayi kafin ya ajiye wayar kan Centre table ya fita zuwa masallaci, koda ya dawo daga mosque a palourn downstairs yayi kwanciyarsa. Hajar ta buɗe idonta a hankali sai kuma ta miƙe zaune tana ƙarewa inda take kallo, kallon wayar dake kan Centre table tayi, ta ɗauki wayar sum sum sum ta nufi ƙofa ta fita, direct room dinta ta wuce, bayan tayi alwala tayi sallah, kan prayer mat din ta kwanta ta duƙunƙune da hijab ɗin da tayi sallah. shida da rabi ya shigo ɗakin, kallo ɗaya ya mata ya ɗauke wayarsa da ya gani gefenta ya fita, wayar harta mutu da kanta, ɓangarensa ya shiga ya ɗakko key din mota ya fito, downstairs ya sauka ya fita zuwa compound ya isa parking space, motarsa ya buɗe ya kunnata yayi plugging wayar a charge, a kunne yabar motar ya koma ciki ya shiga kitchen ya haɗa coffee, saida wayar ta ɗanyi chargi ya kira Engineer din da ya haɗa wutar gidan. kafin ƙarfe goma Engineer din har yaxo yayi fixing komai wutar gidan ta dawo. sai ƙarfe biyu na rana Nurain ya fita, hospital ya fara zuwa ya duba patient din da ya yiwa surgery jiya, alhmdllh patient din har ya farka kuma he is healing. ★Ruqayyah na kwance kan gado tunani fal zuciyarta, bude ƙofar ɗakin akay, Meema wacca take matsayin cousin dinta kuma age mate dinta ce ta shigo, Ruqayyah ta ɗaga kai ta dubeta, ƙarasa shigowa Meema tayi ta ajiye cup da plate dake hannunta a kan bedside tana kallon Ruqayyah tace "ga breakfast..", Ruqayyah ta tashi ta dafe kanta da ya sara, Meema ta ɗauki cup mai ɗauke da tea ta miƙa mata tace "ki daure kici abinci sai kisha drugs dinki..", amsar cup din Ruqayyah tayi ta fara shan shayin, sosai ya mata daɗi har taji appetite dinta ya dawo, da kanta ta ɗauki plate din dankali da kwai ta fara ci tana dangwalar ketchup, baifi rabi taci ba ta ajiye ta cigaba da sipping tea, Meema dake zaune gefenta tana latsa waya tace "yauwa kinga yanzu ai kyaji kwarin jikinki sister..", gyaɗa mata kai kawai Ruqayyah tayi, bayan tasha drugs dinta ta koma ta kwanta, kuka ta fara yi a hankali, tin Meema bata ankara ba har ta gane, with care ta ɗora hannu akan goshinta tana tambayarta is she okay, Ruqayyah ta girgiza kai da kyar tace "not at All.. zuciyata zata fashe Meema..", Meema tace "please tell me what happened..?", Ruqayyah ta tashi zaune ta jingina da allon gadon tana sauke silent tears tace "Meema bazan taɓa dawowa daidai ba indai Dearest bai dawo gareni ba..", da mamaki Meema ke kallonta tace "waye kuma Dearest...?", Ruqayyah tace "Dr..", Meema ta ƙanƙance ido tace "wai Dr Uthman wanda aka fasa aurenku..?", Ruqayyah ta gyaɗa kai hawaye na zuba idanunta, Meema was very shocked, kan uba anya Ruqayyah kalau take, Meema ta mayar da hankalinta sosai kan Ruqayyah tace "sister ba ke kika gudu sbd ba kya son auren ba..", Ruqayyah ta girgiza kai tace "wllh tllh ba guduwa nayi ba, wai wane mashahurin maƙaryacin ne ya laƙaba min wnn sharrin yake yamaɗiɗi dani wai bana son aure na gudu, nifa bance bana son auren ba wllh Allah..", Meema tayi ajiyar zuciya tace "what are you trying to say sister..?", Ruqayyah tayi shiru ba tace komai ba, Meema na kallonta da kyau tace "toh a fahimta ta yanxu dai so kike ki auri Dr ko..?", Ruqayyah ta gyaɗa kai tace "amma ya zanyi sister, na rasa inda zan dosa, Dr yaƙi ya kulani, Daddy yace zai auramin Dauda bacogala, har gidan sister Kulsoom naje itama wai tace na haƙura da Dr, kiji fa wai na haƙura.. anya kwa ta san mene ne so..", Meema tace "me sister Kulsoom din tace miki..?", Ruqayyah ta share hawayen idonta ta shiga gaya mata ydda sukay da Kulsoom lokacin da taje gidanta, Meema ta jinjina kai tace "gaskiya ta gaya miki wllh, kuma nima na goyi da bayanta, babu ta yadda za ai Dr ya dawo gareki Ruqayyah, karfa ki manta ranar aurenku kika tsallake kika barsa, yanzu dan yace baya sonki ni banga laifinsa ba wllh, ke kika jawa kanki, zan ƙara akan abinda Kulsoom ta gaya miki kawai kiyi haƙuri ki rungumi sorry, Allah ya baki wanda ya fisa...", katseta Ruqayyah tayi da faɗin "yaushe kika fara shan wiwi da Sholisho..?", Meema tace "what..?", Ruqayyah ta daka wani uban tsaki tana zabga mata harara tace "ki bari duk ranar da kika haƙura da justice sai ki gayamin haka..", ta sauka daga kan gadon ta shiga bathroom, Meema ta taɓe baki tace "kece za kiyi ta zama a ƙoshin wahala..", Ruqayyah ta fito wanka ta shirya cikin uniform dinta, gwara dai ta fita aiki duk da yau ma ba tayi niyyar zuwa ba, handbag dinta ta ɗauka ta fita ɗakin, Haj Safiyya ta tarar da Meema a palour suna breakfast, Ruqayyah ta durƙusa ta gaidata da ladabi, Haj Safiyya tace "lfy lou Ruqayyatu, ya jikin naki..?", Ruqayyah tace "da sauƙi..", Haj Safiyya tace "ba dai fita za kiyi ba..", Ruqayyah tace "wajen aiki zan tafi..", Haj Safiyya tace "toh za dai ki iya zuwa ko..?", Ruqayyah ta gyaɗa kai tace "Eh" da haka ta tashi ta nufi door, Meema ta bita da kallo. Ruqayyah na zuwa hospital ta fara aikinta, dan Nurse Jiddah ta gaya mata daf ake da bata query, tana tsaye gaban bed tana shirya post Anesthetic bed, forcep dake hannunta ta ajiye cikin tray tana jin wani jiri na ƙoƙarin ɗebeta, duk dai dagewa take tana so tayi aikin, luu tayi baya zata faɗa kan suction machine tayi saurin dafe bed, wani Nurse namiji da yake ward din ya iso inda take yace "are you okay...?", ta girgiza kai tace "partially", yace "alright ki wuce station i will handle it..", tace "thank you in 10mins za a kawo patient din daga surgery..", yace "alright..", Ruqayyah ta wuce station ta kwanta a room dinsu na female Nurses dake asibitin. ★Washe gari da yamma Nurain ya isa gidansu, yana shiga main palour ya tarar da Sakeena a zaune, daman yaga motarta a compound, ƙarasa shiga palourn yayi ya zauna opposite to her yana kallonta, tace "brka da shigowa brother, ya sister na..?", yace "she's great alhmdllh...", ta gyaɗa kai tace "good to yaushe zaka kawo min ita..?", ya ɗage thick eyebrows dinsa yace "sooner or later", Sakeena ta gyara zama tana kallonsa tace "brother serious talk how is the girl..? ba wani matsala ko..?", ya sauke ajiyar zuciya yace "i can't say all is well amma dai kinsan she is not my choice and not my type, alfarma kawai nake mata na zauna da ita snn kuma sbd Abba..", babu wani kwana kwana ya fadi hakan don yadda suka saba da Sakeena baya iya ɓoye mata komai kuma baya mata ƙarya, Sakeena tayi jim don tinda yace mata haka tasan hakan ne, shi kam wayarsa ya ciro yana dannawa, ɗaxu ne suke mgana da Mami shine Mami tace ta tmbayesa tinda tasan ydda suke dashi, dan Mami tana suspecting kamar auren is not stable, Sakeena tace "brother..", still yana latsa wayarsa yace "Na'am", shiru tayi ba tace komai ba, ya ɗago ya kalleta ganin kallonsa take ya waro ido yace "yess..", ta mayar da attention dinta kacokan kansa tace "why are you saying that... the words choice and type bai kamata ka ambace su ba, gwara ma dai favor din, brother idan fa baka saki jiki da ita ba babu ta yadda za ai ku saba, kaga ita maca ce zata ringa shakkarka ko kuma taƙi sakin jikinta da kai as her husband, kaga dai ba tada wani aibu physically and she is beautiful masha Allah, halinta kawai zaka karanta shknn fa kuma am very sure she must be a good girl with that innocent face..", wani murmushi yayi jin abinda ta faɗa, wai she must be a good girl with that innocent face, chab lallai ba tasan wace ce yarinyar nan ba, Calmly yace "Ohh yeah really..", Sakeena ta haɗe gira tace "bafa joke nake a nan ba..", yace "yeah nima ai ba wasa nake ba, wollah alfarma na yiwa yarinyar nan kuma sbd Abba nake zaune da ita, ni a yanzu ma aka bani pen da paper tsaf xan yankar mata ticket... ammafa sai Abba ya yarda.. kinga da zaki temakamin ki masa mgana ya yarda na saketa da na baki tukuici.." yana gama faɗin haka ya tashi ya nufi stairs yace "i have something to do..", Sakeena ta bisa da kallo tace "hey come back here am not done with you..", ya juyo yana kallonta sai kuma yayi murmushi yace "saidai ki canza topic bansan maganar wollah", Sakeena was shocked tace "ita kwa zamu cigaba..", bai ce mata uffan ba ya wuce zai hau stairs sai kuma ya fasa ya dawo palourn yana kallonta yace "where is our Mami..?", ta juya hannu alamar ban sani ba, ɓangaren Mami ya shiga, after like 10mins ya fito ya haura sama, babu jimawa Mami ta fito, tana kallon Sakeena tace "nan kika zauna daughter..?", Sakeena tace "dana fito wajen Abba shine na zauna nan kawai..", Mami tace "Ohk" lokacin da ta zauna, Sakeena ta buɗe wayarta ta shiga message ta haskawa Mami credit alert daya shigo 30mins back tace "from Abba", Mami tace "keda partner din naki za a bari knn..?", Sakeena tace "yeah, nasan damuwar Abba grandkids dinsa kuma fa da can wajen paternal grandma dinsu zan kaisu, nayi shirina mu keta haxo, amma yace nan da 5 months insha Allah sai mu tafi da Nurain with his wife..", Mami ta gyaɗa kai tace "Ohk", Sakeena tace "Mami i talk to him fa, in my view ba wani matsala insha Allah..", Mami tace "are you sure..?", Sakeena ta ƙirƙiri fake smile tace "Sure", Mami tayi ajiyar zuciya tace "toh alhmdllh, bana san wata tangarɗa ta faru a auren ne..", Sakeena ta sake yin wani fake murmushin tace "ba abinda zai faru sai alkhairy insha Allah". kafin magrib Sakeena ta tafi, as usual Nurain bai bar gidan ba saida ya yiwa Maminsa sallama. washe gari da safe Nurain na zaune palourn downstairs yana shan coffee, Hajar ce ke sakkowa daga kan stairs, saura step biyu ta kai ƙasa sai kuma ta dakata tana kallon palourn, Nurain ya sauke cup of coffee da ya kai baki ya dubi stairs din, da sauri ta sauke idonta ƙasa sai kuma ta juya a hankali zata koma sama, lower lip dinsa ya cixa painlessly, daga throat maganar ta fito bayan ya runtse idonsa ya buɗasu a hankali yace "Hajar..", cak Hajar ta tsaya amma bata juyo ba tana riƙe da railer, a hankali ta juyo ta kalli palourn sukay ido huɗu, ta juyar da kanta tana wasa da hannunta dake riƙe da railer, Nurain ya tashi daga kan sofa walking towards the stairs yace "let's work together", ta zuba masa lulu eyes dinta tace "work together as in how..?", yace "young lady nasan ba kya san zama anan ko..? i mean ba kya son auren..", gyaɗa masa kai tayi tace "sosai ma kuwa" ta haɗe girarta mai kyau tamkar wcca aka zana mata ita, ya jinjina kai yace "same here, as i said let work together, kina jina yanzu ki kawomin jotter da pen dana baki..", tsuro tayi tana kallonsa lokaci guda kwanyarta ta amsa, biro da takarda, da sauri ta juya ta haura sama, babu jimawa ta dawo da jotter with pen riƙe a hannunta, yana zaune kan exclusive sofa ta dawo, tunani yake is he doing the right thing, ajiye masa pen da jottern tayi ta koma gefe ta harɗe hannayenta, ya ɗaga kai ya dubeta yace "then listen, abinda nake shirin yi yanxu shine zanyi ending komai dake tsakaninmu, zan rubuta miki saki, ni da ke kowa yayi rayuwarsa munyi freeing juna, kin fahimta..", tinda ya fara magana take kallonsa, da sauri ta gyaɗa kai tace "da kwa ka kyauta idan ka sauwaƙe mana", yayi ajiyar zuciya yace "but idan na rubuta duk abinda ya biyo baya kece za kiyi bearing consequences din...", without thinking twice tace "na amince..", daman abinda take so knn, wani nishadin daɗi ne ya tsarga mata zuciya, Nurain ya dauki biron da jottern ya ɗora kan Centre table, buɗe jottern yayi ya ɗora pen ya fara rubutu.....✍️ Masu comments a ringa yi kullum Please ku sani ba doc ne a ajiye ba, sai nayi typing nake posting, snn kuma am occupied kawai dai ina squeezing inayi ne, plxx be patient... more love 🥰 💛 HAJAR 💛 {58..} A hankali yake rubutun, Hajar na tsaye ta ƙurawa hannunsa idanu, Alla Alla take ya gama ya miƙo mata, shknn tinda safiya ce sai ta fara haɗa kayanta da wuri, Allah ya rabata da wnn jarababben auren ta ruwan sanyi, Nurain ya dakata da rubutun ya ƙurawa papern ido, ya sauke numfashi lokaci guda ya ɗaga takardar ya fara yayyagata, Hajar ta zaro ido ganin abinda yake tace "meye haka kuma..?", bai ce mata uffan ba ya cigaba da yaga papern, saida ya mata gutsi gutsi ya watsar da ita nan kan Centre table din, with speed ya tashi ya haura sama, Hajar tabi bayansa da kallo wasu hawayen baƙin ciki suka ciko mata idanu, bata san lokacin da ta fashe da kuka ba, ita taga samu kuma taga rashi, shknn ya yaga shedar da zata nuna cewa babu aure a tsakaninsu, to wace shaida ma ai bata saku ba ma tinda ba taga me ya rubuta ba, jar uba knn dai auren yana nan daram ko girgiza bai yi ba, zubewa tayi a ƙasa ta shiga rafsa uban kuka sai kace wacca akaiwa mugun duka, saida taci kukanta ta ƙoshi sai kuma taja jiki ta matsa kusa da Centre table din tana kallon pieces din takardar, shessheƙa take a hankali ta fara ƙoƙarin arranging din papern wai ko zata gane mai ya rubuta, saidai fa abin yafi ƙarfin ƙwaƙwalwarta don kwata kwata ta kasa gane farko ma bare aje ga tsakiya ballantana ƙarshen rubutun, har alphabets din ma bata iya ganewa sbd yadda yayi rubutun sai kace prescription, takaici yasa ta tattare pieces din takardar ta shiga kitchen ta kunna gas ta barbarɗa takardar ta ƙoneta, fitowa tayi daga kitchen din tana cika tana batsewa, still ta tsaya a bakin ƙofa sakamakon amsawar da brain dinta tayi, gsky tayi ragon azanci, da ba saita ajiye pieces din in yaso ta nunata a matsayin shaida, sai tace itace ta yaga amma ba a cikin hayyacinta ba, da sauri ta koma kitchen din ta matsa gaban gas, ta ringa kallon tokar papern tana jin haushin kanta, tamkar wacca kwai ya fashewa haka ta fito ta haura sama, tsaye tayi tana kallon huge sliding door din shiga ɓangarensa, ta koma ta jingina da bango still tana kallon ƙofar, after like 10mins saiga shi nan ya fito, he changed into sweat pant and white shirt irin dai shigar da yake ta zaman gida, har wani coiled black hair dinsa yake sbd yadda yaji oil yana shining, kallo ɗaya ya mata ya dauke kai ya rufe ƙofarsa, ya zura hannunsa a pocket ya wuce zai sauka downstairs, da sauri tace "kace fa zaka rubutan takardar kuma fa baka bani ba...", cak ya tsaya kafin ya juya yana kallonta, ganin yadda idonta ya haura ya taɓe baki don yasan tabbas halin nata tayi, ya ɗage gira yace "wace takarda kike magana akai..?", ta haɗe rai ta buɗe baki da nufin lafto masa rashin kunya sai kuma ta fasa, ta sauke idanunta ƙasa tana jan slim fingers dinta tace "wacca kace na kawo maka jotter da pen zaka raba tsakaninmu..", yace "ohhh that i was only joking..", zaro ido tayi ta sha kunu tace "bangane ba.. meye kuma joking daman ana wasa da saki ne..?", ya ɗaga shoulder yace "wait ni cewa nayi zan sakeki ma, toh what's the point idan nace zan wani sakeki, all i know ni nasan banida wata mata bare na rubuta mata saki..", wata shegiyar harara ta galla masa tana yamutsa fuska tace "ai kwa dai kaji kunya.. sangameme da kai kana yin magana biyu, saura ƙiris ka zama maƙaryaci, toh wllh daka rubuta da kar ka rubuta nidae na saku kuma a yau ba sai gobe ba zan bar gidan nan, koda yake ma ai ka rubuta ka yaga kuma..." gumm tayi ganinsa gaf da ita, ba tayi aune ba sai jin wata mummunar gwabza tayi a bakinta, har taste din blood saida taji a bakin, habawa sai kace an fesawa wuta petrol haka ta hasala, ta murguɗa baki tace "toh ƙarya nayi ba magana biyun kayi...", bai bari ta ƙarasa ba ya sake buge bakin da ɗan ƙarfi, har cikin kwakwalwar kanta taji zafi, ta rutse ido tana buɗewa sai zirr hawaye suka fara zarya, tsit bakin tsiwar ya mutu duk da irin hargowar rashin kunyar da ke taso mata, yana kallon cikin idonta yace "yeah you can leave ko an gaya miki zan dakatar dake ne, the door is open young lady you are free, tinda kinada evidence din da zaki nuna.." yana gama faɗin haka ya barta tsaye a wajen ya sauka ƙasa, Hajar ta goge hawayen da ya jiƙa mata cheeks tace "hmmm kamar yadda kere ke yawo kaza ma take yawo toh haka takardar sakina take a hannunka, ko bajima ko ba daɗe saika sakeni wllh tllh, kai asuwa da zaka zauna da aurena" sai kuma tayi shiru kafin tayi kwafa tana jin haushin kanta da ta faɗi hakan, ta buɗe ƙofar ɗakinta ta shiga tana cewa "kai ka isa ka aureni". Compound Nurain ya fita, Inuwa ya ajiye watering can da yake bawa flowers ruwa yabi bayansa zuwa parking space, shi dai yasan ranar Asabar boss din nasa baya fita da wuri, ya ɗan russuna yace "Alhaji barka da fitowa", sama sama Nurain ya amsa masa don Silly girl dinsa ta hayaƙasa kafin ya fito, buɗe black car ɗinsa yayi ya shiga yace "buɗen gate..", da rawar jiki Inuwa ya tafi buɗe gate, Nurain ya zura key a ignition ya tashi motar, resting yayi da kujera yana jiran ta gama warming, motar na gama warming ya fara driving yabar gidan, after a ride of about 30mins ya isa inda zashi, parking yayi gaban wani ƙaton warehouse, bayan ya kashe motar ya fito, wasu mutane biyu ne kan benci a gaban warehouse din, Nurain ya isa inda suke, da sauri ɗaya ya miƙe don ya gane Nurain, russunawa zaiyi Nurain ya miƙa masa hannu, ya ɗan russuna yace "barka da zuwa Alhj..", Nurain yace "yauwa mal Ɗayyab..", gaisawa sukay da ɗayan mutumin wnda abokin mal Ɗayyab ne, mal Ɗayyab yace "wajen za a duba Alhaji...?", Nurain yace "Eh", mal Ɗayyab yace "toh" da haka yaje ya buɗe ƙatuwar ƙofar warehouse din. Nurain baifi 20mins a wajen ba ya wuce bayan ya yiwa mal Ɗayyab alkairi da ya saba a duk sanda ya ziyarci warehouse din nasa. daga nan Mall Nurain ya wuce yayo Grocery shopping, yana parking motarsa bayan ya iso gida ya buɗe booth, da kansa ya ringa ɗiban ledojin abinda ya siyo yana shigar dasu ciki, bayan ya gama sigar da komai ya buɗe kitchen ya shiga, saida yayi refilling freezer da fridge duk da cewa kaɗan aka ɗiba, ya ajiye coffee powder da ya siyo itama a cupboard. throughout the day yana ɓangarensa bai sake fita ba, saidai lokacin sallah ya je mosque, bayan ya dawo daga sallar la'asar ya shiga kitchen, tsaye ya ganta a bakin gas tana zuba seasoning a jollof rice da take dafawa, yayi kamar baima san da ita a kitchen din ba ita ma hakan tayi, plate ya ɗauka ya buɗe fridge ya ɗauki bunch of grapes one Apple sai kuma pea itama guda ɗaya, ya koma gaban sink ya buɗe tap ya sake wanke fruits din duk da cewa a wanke suke, Hajar dai ta masa kallon wutsiyar ido tana taɓe baki, wnn tarkacen ne abinci chaɓ, ita tinda take dashi ma bata taɓa ganin yaci abinci ba sai shan coffeen tsiya ma malam, yana gama wanke fruits dinsa ya bar kitchen din... washe gari da ta kasance Sunday da misalin ƙarfe sha ɗaya na safe Hajar ta fito wanka ɗaure da towel, as usual ta gama rubbing lotion a fatarta da a yanxu take wani azabar glowing, don shower gel da man da take shafawa masu kyau ne da tsada, warware jelar gashinta da ta tufke tayi domin tajewa za tay don bata son ya danƙare mata, saida ta jiƙasa da hair butter snn ta sharce, riga da skirt na atampa ta fiddo ta saka, tayi ɗaurin ture kaga tsiya, tsaf ta feshe jikinta da turare snn ta saka takalmi ta fita daga ɗakin, ido huɗu sukay dashi shima ya fito daga ɓangarensa waya kare a kunnensa, kallon da ta ga ya watsa mata ne yasa ta dubi kanta, ta tabe baki ta wuce ta fara sauka daga stairs tana cewa "uhmm gani ba taɓawa ba asarar ido". Nurain ya gyara wayar dake kunnensa bayan Hajar ta ɓace masa daga gani, duk da irin turaren da yake jikinsa amma saida yaji ƙamshin nata, Sakeena jin brother din nata yayi shiru na almost 40sec tace "hey Nurain kana ji kuwa..?", yace "yeah", tace "Au ko bazaka kawomin ita bane iyee... tin jiya fa nake maka magiya tinda dai kai bakayi hankalin kawota wajen next mother ba har saida na roƙa saika kawomin ita..", yace "ohh God ki bari sai next week ni yanxu har na shirya fita zanyi fa..", tace "and where are you heading to..?", yace "zanje gida snn kuma inada wasu appointments", Sakeena tace "Alright first dai gida zaka fara zuwa right..?", yace "Eh", tace "ba saika biyo tanan ka kawomin ita ba..", yace "Okay..", tace "yawwa.." da haka tayi breaking call din, Nurain ya sauke ajiyar zuciya ya saka wayar a pocket, toh shi ta ina ma zai fara ɗaukar yarinyar na ya fita da ita, ba ma wnn ba me zaice mata ne. palourn downstairs ya sauka ya zauna kan kujera yana kallon ƙofar kitchen, babu jimawa sai gata nan ta fito da cup din black tea sai plate na indomie, da yake idonsa akan ƙofar yake aikam sukay ido huɗu, ita ta fara ɗauke nata ta wuce zata haye sama, a ranta saida tayi danasanin fitowa without hijab, don sosai ta tsargu da kallon da yake mata, kawai saukar muryarsa taji a kunnenta "idan kin gama ki ɗakko veil dinki ki sameni a nan..", still tayi a inda take ba tare da ta waiga ba, ta wani taɓe baki ta haye sama abinta, bayan ta gama cin abincin ta sauka da plate da cup din, har lokacin yana zaune palour yana latsa wayarsa, agogon wrist dinsa ya kalla lokaci guda ya miƙe yace "damn it", tana fitowa daga kitchen yace "3mins kije ki ɗakko veil dinki", tayi kamar ba taji abinda yace ba tayi wucewarta, har 3mins ta wuce babu alamar zata sakko, thick eyebrows dinsa ya haɗe ya haura saman, da ɗan karfi ya buga ƙofar ɗakin nata har saida tayi ƙara, Hajar dake zaune gefen gado ta miƙe zumbur tana zaro ido, saukar da idanunta tayi ƙasa don sosai ya mata kwarjini, with stern voice yace "are you mad... me nace kiyi..", ba ta bari sun haɗa ido ba tana jan fingers dinta tace "toh wai ina ruwanka dani da za kace na ɗauko mayafi na sameka a ƙasa.. meye hadina da kai.." ta ƙarashe tana turo baki, wata tsawa da ya daka mata har saida ta tafi da baya ta ƙume da bango tsabar gigicewa, ba tasan lokacin da ta buɗe wardrobe ba ta ɗakko mayafin da hannunta ya fara taɓawa, shivering jikinta ya fara hawaye ya cika idonta, murya ƙasan maƙoshi yace "Silly girl.. zo ki wuce", ko yafa mayafin ba tay ba haka ta nufi ƙofa da sauri ta fita bayan ta saka takalminta, tini idanunta suka cicciko da ruwa, yana biye da ita har suka sauka ƙasa, sai a lokacin ta warware mayafin ta yafa, color dinsa ya shiga da zanen flower dake jikin atampar da ta saka, main door ya buɗe yace "wuce", ba musu ta fita tana turo baki, rufe ƙofar yayi da key ya zura a pocket, kallon dressing din nata yayi yaga ba wani aibu kafin ya wuce gaba, bayansa tabi zuwa parking space, ya buɗe motar kafin ya buɗe front seat yace "get in..", ƙasa ƙasa ta nasa masa harara kuma ya lura da hakan snn ta shiga, ya rufe mata ƙofar ya zaga driver seat ya shiga motar, already Inuwa ya buɗe gate, suna isa bakin gate din Nurain ya tsaya yana kallon Inuwa yace "ba kowa a gidan a kula sosai..", Inuwa ya russuna yace "Allah ya tsare hanya..", Nurain yace "Ameen" da haka yaja motar suka bar gidan, suna fita daga street din gidan Hajar ta ɗaga kai ta ɗan kallesa, ko ina zai kaita oho, a hankali ta koma ta jingina da kujera ta lumshe idonta sbd kanta da ya fara juya mata, tinda suka hau main road ya take accelerator kawai falfala gudu yake, wani burki yaci bayan ya kaucewa wani tricycle ya cigaba da falfala gudu abinsa, tini Hajar ta buɗe idonta ba tasan lokacin da ta riƙe hannunsa dake kan gear ba tace "ni wllh raina guda ɗaya ne karka salwantar min da abuna... na shiga uku, wayyoh Ummana..", sai kuma ta fashe da kuka ta kifa kanta kan hannunta data damƙe nasa, ya ɗan kalleta kafin ya ɗauke kai yana kallon road yace "hands off", gam ta riƙe masa hannu taƙi cikawa kuma bata dena rusa masa kuka a motar ba, shi dai baice mata uffan ba ya cigaba da driving din da hannu ɗaya, slowing down yayi, a hankali Hajar ta ɗago tana shessheƙa, tayi sauri ta goge hawayen cheeks dinta ta koma ta zauna da kyau tana jan zuciya, a bakin gate din wani gida yayi parking, ya kalli dogon hannun rigarsa da ta jiƙa masa da hawaye, ya juya yana kallon side view din fuskarta, idonta har ya haura, girgiza kai yayi yace "sauka", buɗe motar tayi ta fita, shima ya buɗe ya fito ya ciro wayarsa daga pocket yayi dialing numbern Sakeena, tana picking yace "gani a gate fa..", tace "haba ku shigo mna.." katse wayar yayi ya nufi gate din shiga gidan, da car key yayi knocking, mai gadi ya buɗe ƙofar gate din, ya waiga yana kallonta sai kuma ya juya ya shiga gidan, da sauri tabi bayansa. ba ƙaramin farin ciki Sakeena tayi ba, sosai tayi welcoming Hajar, Hajar dai murmushin yaƙe kawai take, bayan sun gama gaiswa da few minutes Nurain ya ajiye little Ayman da tin zuwansa ya makale masa yace "i gotta go...", Sakeena tace "Ohk.. bazaka jira na gama abinci ba..", yace "yeah am full" da haka ya miƙe yana jan rigarsa, Sakeena tace "uhmm inka dawa kaci toh don favourite dinka ne...", yace "Ohk" da haka ya nufi door, tsugul Hajar ta miƙe tana gyara yafen mayafinta, Sakeena ta sakar mata murmushi tace "Ai ke kina nan..", wani daram Hajar taji ya buga a zuciyarta, kawai sai taji ba ta son ta zauna a nan din, ganin bata koma ta zauna ba Sakeena tayi murmushi tace "Okay see him off dear", kafin Hajar ta fito har Nurain ya isa gate, ai kam da gudu tabi bayansa, har ya buɗe mota zai shiga yaga fitowarta, dakatawa yayi yana kallonta har ta iso gaban motar ta tsaya, yace "ina kuma zaki ki koma cikin gida", ta maƙe shoulder tace "A'a ni bazan zauna ba..", ya tsuke ido irin what sai kuma yayi smirk ya shiga mota, da sauri ta zaga driver seat ta riƙe handle din ƙofa, zirrr hawaye suka fara sauka idonta, ajiyar zuciya yayi ya buɗe motar ya fito, from head to toe yake kallonta, yace "ke wai kinada hankali ma kuwa... me aka miki..?", sai kace wnda ya zigata kawai ta fashe da kukan gaba ɗaya, ya kalli street din yaga dai babu kowa, ya rage murya yace "karki taramin jama'a malama, wani abun akay miki kike ɓarewa mutane baki..?, ko an gaya miki inda za a cuce ki na kawoki, you see that woman she is my elder sister kuma ita tace na kawo mata ke, and i can't say no to her, ki wuce ciki malama no one is going to harm you..", kukan take a hankali tana jinsa, lokaci guda ta fara tafiya a hankali ƙafarta na harɗewa ta nufi gate din gidan, bayanta yabi tana daf da shiga gidan ya riƙo hannunta.......✍️ 💛 HAJAR 💛 {59..} A hankali ta juyo tana kallon hannunta da ya riƙe, ya saki hannun nata fuskarsa ba yabo ba fallasa yace "Please kar kije ki ringa yiwa mutane kuka, i told you no body will harm you.. kinji ba..?", ta haɗe gira tace "naji..", hannu ya zura a pocket dinsa ya ciro handkerchief ya miƙa mata yace "wipe those tears..", kallon handkerchief din tayi ta kai hannu zata amsa sai kuma ta fasa tace "no thank you" da haka ta juya zata shiga gidan, still tayi a bakin ƙofar ba ta shiga ba, ta juyo tana kallonsa sai kuma ta kai hannu ta amshe handkerchief din daga hannunsa tana turo baki, daga nan bata ƙara ko 1sec a wajen ba tayi wucewarta, kafin ta shiga ciki ta tsaya ta goge fuskarta da handkerchief din da pure designer scent dinsa ne kawai yake tashi a jiki, tass ta goge fuskarta perceiving the scent kafin ta shiga cikin gidan, a bakin ƙofar palour ta tarar da Sakeena, Sakeena ta sakar mata murmushi tace "kin raka san..?", Hajar ta gyaɗa kai tana kallon ƙasa, sosai Hajar taji daɗin spending wnn ranar a gidan Sakeena, ta lura dai ƴan uwansa sun san darajar mutane kuma sun iya karrama su, haka Noor ma take kula da ita lokacin da take gidansu, ga Mami ma wacca take ganin a wajenta suka gado wnn sassanyan halin mai kyau, shi kaɗai ne ya fita bare a cikinsu don ta canfa shi mugun hali garesa, Hajar ta ajiye plate din hannunta mai ɗauke da snacks a ƙasan carpet, Sakeena dake zaune palourn tare da ita tace "toh taso muje ciki kiyi sallar ko..", Hajar ta miƙe tana gyara yafen mayafinta, ɗaya daga cikin three bedrooms da take dashi ta kai Hajar ta nuna mata toilet, a hankali Hajar ta cire veil dinta ta wuce ta shiga toilet din, bayan tayi alwala ta fito tana ƙoƙarin ɗaura ɗan kwalinta Sakeena ta shigo hannunta riƙe da babban hijab da prayer mat, da kanta ta shimfiɗa mata darduman snn ta ajiye mata hijab din a gefen gado, Hajar tace "nagode", Sakeena tace "you're welcome" da haka ta juya ta nufi door, Hajar tayi ajiyar zuciya kafin ta dauki hijab din ta saka ta tayar da sallah. tana idarwa ta naɗe dardumar ta linke hijab din shima ta ajiye gefe guda snn ta saka mayafinta ta fita, palour ta koma ta zauna tana kallon damfareriyar Tv dake aiki a palourn, bata jima da zama ba akai knocking door, saida aka sake knocking snn ta kalli ƙofar kafin ta tashi ta buɗe, wata budurwa ce wacca bazata wuce 23yrs ba, tace "wajen Anty Sakeena nazo..", Hajar ba tace mata komai ba ta matsa mata hanya ta wuce, kan carpet ta samu ta zauna, Sakeena ce ta shigo palourn tana kallon Hajar dake zaune kan sofa tace "na barki ke ka ɗai ko..?", Hajar dai tayi murmushi ba tace komai ba, yarinyar dake zaune kan carpet tace "Anty ina wuni..", Sakeena tace "lfy lou Bilkisu.. bari na ɗakko comb da kibiya", Comb da kibiya Sakeena taje ta dakko ta kawowa mai kitson nata, ana gamawa Sakeena kitson tace "saura ke Hajar..", Hajar ta nuna kanta tace "Ni", Sakeena tace "daga gani baki son kitso ai naga kan naki ba a kitse yake ba", medium kitson Kalba akaiwa Hajar wnda aka tsagasa kamar fashin kwakwa jelar ta yarfo ta gefen kunnenta har ƙasan shoulder dinta. Da misalin takwas na dare kiran Nurain ya shigo wayar Sakeena, picking tayi tace "yess brother..", yace "gani a ƙofar gida can i come in...?", Sakeena ta kalli Hajar tace "Au nasha ai anan zaka bar min ita ta ɗan kwana biyu", cire wayar yayi daga kunnensa ya kalli screen din kafin ya mayar kunnen yace "Ohk.. good night.." har zai katse wayar tace "ka shigo we need to talk", tana katse kiran ta kalli Hajar tace "kije kiyi sallar isha'i kafin yazo ko..", Hajar tace "toh" ta tashi tana noƙe kai sbd kitson da akay mata don ta tsani kitso. babu jimawa Nurain ya shigo, Aymana da brother dinta da suke kallon catoon suka ruga wajen uncle din nasu, murmushi yayi ya riƙo hannayensu suka ƙarasa shiga palourn, ya zauna kan kujera ya damƙa musu ledar sweet da chocolate da ya siyo masu, Aymana dake da wayo tace "thank you Uncle..", Ayman ma ya kwaikwayi sister din tasa yace "shenkiyu Anchul", Sakeena tace "oya go to your room kuyi game a tab", da gudu suka ruga zuwa room din nasu da ledar chocolate dinsu a hannu. Nurain na kallon sister din tasa yace "Amm Madam...", Sakeena ta ɗauki remote control na TV ta rage volume ta maida nutsuwarta kansa tace "please karka min wani wala wala brother, ranar nan muna mgana a gida ka ringa mayar da ita not serious", Shafa kansa yayi ya sauke ajiyar zuciya yace "ya subhanallah... in dai wnn mganar ne ai mun gama, nafa gaya miki komai..", ta haɗe gira tace "ka gayamin komai as in how...?", ya gyara zamansa yace "listen sister you need not to worry, your brother here bashi da wani matsala ke kinfi kowa sani aii..", tayi tsaki tace "in banda kafiya ba, idan ka kafe akan abu ai babu me iya juya maka ra'ayi..", yace "Nah..?", tace "yess you", yace "Okay fine, nasan duk mtsalan dai akan wnn yarinyar ne kuma na gaya miki ni favor kawai na mata nake zaune da ita cause she's not my type and choice..", Sakeena tace "but Abba's choice right...", ya ɗaga shoulder baice komai ba, Sakeena tace "sai dai ka saki jiki da ita snn zaka gane wace ce kuma kaima tasan wane kai.. i think I told you" ta ƙarashe faɗin hakan ne lokacin da ta miƙe tsaye, kitchen ta shiga ba ta daɗe ba ta fito, ta ajiye trayn da ta fito dashi kan Centre table ta koma ta zauna a position dinta tace "gashi nan na ajiye maka abincin da kace sai ka dawo zaka ci", ya shafa kansa yace "am full..", ta galla masa harara tace "open it first kafin kace wani am full..", ƙaramar warmer din ya buɗe yaga miyar spinach ce da taji lafiyayyen smoked fish da pure palm oil, medium warmer din kuma pounded yam da zafinta don da magrib ta ruɗata, kallonta yayi yace "Please serve me..", zuba masa tayi, kaɗan yaci ya ture ya zuba ruwa a glass cup yasha, few minutes ya miƙe yana jan rigarsa yace "Good night, a miƙan gaisuwa wajen Abban kids", tace "Ohk, baya gari ma next tomorrow zai dawo insha Allah", yace "Ohk", ganin ya nufi ƙofa kai tsaye ta bisa da kallon mamaki kuma da gaske fita zaiyi tace "Nurain your wife", ya juyo yace "Ai kince na bar miki ita ta kwana..", Sakeena ta buɗe baki kafin tace "we are not from same planet... ka jira matarka ku wuce gida" tana kaiwa nan ta shiga ɗakin da Hajar take, zaune ta sameta kan carpet ta jingina da jikin gado, tin ɗazu da ta idar da sallah ta tashi zata fita tana gaf da palour taji muryarsa da scent dinsa shiyasa ta dawo ɗakin tayi zamanta, har compound Sakeena ta raka Hajar da ledar da ta haɗa mata sha tara ta arziƙi, ganin fitowarsu Nurain dake tsaye bakin gate ya fita, Hajar ta yiwa Sakeena godiya tana riƙe da ledar da ta bata ta fita, ta ringa kallon motarsa da already ya bude ya shiga, sauke kanta tayi ta ƙarasa ta buɗe front seat ta shiga ta rufe, ya ringa kallonta kamar a lokacin ya fara ganinta, kaifin idonsa akanta yasa ta juya ta ɗan kallesa, ido huɗu sukay tayi sauri ta ɗauke kanta tana kallo window ta turo baki, murya ƙasan maƙoshi yace "nuna min inda aka gutsira a jikinki..", da sauri ta juya ta zuba masa lulu eyes dinta ba tace komai ba, yana kallon cikin idonta yace "uhmmm answer me young lady..", haɗe gira tayi ta zare idonta daga cikin nasa ta kalli window, ajiyar zuciya yayi ya kunna motar, a ɗan firgice Hajar ta juya jin saukar numfashinsa a saitin fuskarta, ta sake shigewa cikin kujera ganin fuskarsa gaf da ta ta, yasa hannu ya janyo seat belt ya mata fastening, ya ɗan kalli slim pointed nose dinta kafin ya sakko da idanunsa zuwa pink lips dinta, slowly ya kai dubansa kan wuyanta that is fair ya hango jelar gashi biyu da ta leƙo ta sauka akan fatar wuyan, Hajar ta sake shigewa cikin kujera da cracking voice tace "stop staring at me..?", gaba ɗaya hancinta ya cika da ƙamshinsa and she can even feel his breathing, ya ɗago idonsa yace "is there anything to stare at...", ya koma ya zauna a seat dinsa ya ɗora hannunsa kan steering, after few seconds ya sauke handbrake ya fara driving, ita dai tinda ta kalli window ba ta sake gigin juyo da kanta ba, kawai irin kallon da ya mata ne ya tsaya mata a rai, ta ringa nanata gani ba taɓawa ba asarar ido a zuciyarta, saida suka hau babban titi ta fahimci dalilinsa na ɗaura mata belt, ai kam ta runtse idonta gamm ta jingina da kujera ko kyakkyawan motsi ba tay ba. suna isa gida yayi parking motar, sai a lokacin Hajar ta buɗe idonta, ƙoƙarin cire belt din ta fara amma ta kasa, ganin tana kiciniyar cirewa ya matso ya cire mata yana lura da yadda ta runtse idonta, da sauri ta buɗe motar ta fita ta nufi entrance, shima fitowa yayi ya rufe motar da haka yabi bayanta, ya ciro key ya buɗe ƙofar entrance, ba ta ko kalli inda yake ba ta shige ciki direct kuma ta haura sama da ledarta a hannu, bayanta yabi da kallo yana sauke ajiyar zuciya, ya sakawa ƙofar lock ta ciki kafin ya haura sama zuwa ɓangarensa. ★Da safe Maimuna da Sa'adatu suna shirinsu na zuwa schl din gogi, Sa'adatu har ta saka uniform tana zaune ƙasan leda tana irga kuɗin da suke rage mata, kallon Maimuna dake shafa BSC cream a fuska tayi tace "wai ke Maimu me yasa kin fiya hauka da baragada ne, nace miki ki dena shafa irin wnn mayukan a fuskarki amma kinƙi ji, ba kya jin kunya a dubi hannunki da fuskarki aga uban banbanci...", Maimuna ta rufe robar man tace "ba kiga safa nake sakawa a ƙafa ba, hannun kuma na ƙunshesa a hijabi, wllh duk masifarka baka isa ka gane ainahin launi na ba", Sa'adatu ta taɓe baki bata ce komai ba, Maama ta shigo tana gyara ɗaurin ƙirji tace "Au baku gama shiryawa ba.. yakamata kuyi da jiki dan ga malam can tsakar gida yayi takkwaba nasan so yake yaga kun fita..", Sa'adatu ta tashi ta saka hijab dinta na uniform ta ɗauki jakarta, Maimuna na gama shiryawa suka fito tsakar gida tare, Sa'adatu ta ɗan haɗe rai ganin Baba kafin ta wurga masa wata shegiyar gaisuwa daga tsaye, kallonta kawai yake bai amsa ba, Maimuna ta gaishesa irin mai spring din nan wcca da ita gwara babu, itama bai amsa mata din ba, Baba yace "ina kuke zuwa idan kuka fita daga gidan nan da nufin makaranta..?", Sa'adatu tace "ina kwa zamu idan ba makaranta ba..." bata rufe baki ba Baba ya gaura mata mari, Maimuna ta kwalalo ido jikinta na rawa, Sa'adatu dake riƙe da kuncinta tace "daman ni nasan Baba ka tsaneni a gidan nan, kawai sai ka zabgan mari dan ka tambaye ni na baka amsa", Baba ya juya yana kallon ɗakinsu Naseer yace "Nasiru zo nan", daga cikin ɗakin Naseer ya amsa babu jimawa ya fito, tini marasa kunyar suka sha jinin jikinsu, Naseer ya ƙaraso kusa da Baba ya rage tsaho yace "gani Baba..", Baba yace "yaran nan kullum idan suka fita daga gidan nan da shirin zuwa makaranta toh ba ita suke zuwa ba, ranar Alhamis naje makarantar tasu wajen principal yake gayamin tin ranar da aka kaisu basu sake zuwa ba, wata bakwai knn basa zuwa makaranta", da wani irin takaici Naseer ya dubi ƙannen nasa, tsawa ya daka musu yace "ba zaku tsugunna ba kuka wani tsaya ƙerere", zubewa sukay a ƙasa ko wacce na zare idanu, Baba yace "su gaya maka inda suke zuwa, kuma daga yau na soke zuwa makarantar...", babu irin barazanar da Naseer bai musu ba amma ko wace shegiya taƙi faɗar inda take zuwa, Naseer na kallon Baba yace "Baba ka bari na naɗi halittar yaran nan tinda an bisu ta lallami da arziƙi sunƙi su bada haɗin kai..", Baba ya girgiza kai yace "A'a Nasiru idan icce ya bushe bazai tankwaru ba, duka na nawa kuma, da ace suna jin duka da babu wacca zata sake laifi a cikinsu, rabu dasu Allah ya shiryesu, kawai dai kar wacca ta sake fita a gidan nan...", sai kuma ya kallesu da wani irin takaici yace "ku tashi ku ban waje, Allah ya shiryeku..", bazar bazar suka miƙe suka shige ɗaki, Naseer ya bisu da kallo zuciyarsa na tafasa don ji yake kamar ya bisu ɗakin ya farfasa musu jiki. Maama dake tsaye jikin labule kaff ta ji abinda ya faru, hura hanci kawai take tana gyatsine, ta lura dai ƴaƴanta aka sakawa idanu a gidan nan, zanin data ɗaura a ƙirji ta kunce ta dawo dashi ƙugu, gaba ɗaya alherin nata sun zube sai kace slippers, wata Tshirt me warin dauɗa ta saka ta fita daga ɗakin tana hura hanci wnda ya kusan cika fuskar tsabar ydda yake kamar tukuba, ɗakin Baba ta afka babu ko sallama, Baba ya dakata da sargafe kayan da yake jikin raki ya juya yana kallonta, ta ƙarasa ciki still tana hura hanci tace "mal ka ringa jin tsoron Allah kuma ka ringa kwatanta adalci a tsakanin ƴaƴan da Allah ya baka..", Baba ya gyara tsayuwarsa yana kallonta da kyau, tace "kawai saika ringa bin diddiƙin yara kana musu bita da ƙulli duk dan ka gano laifinsu, meye na binsu kaga inda suke zuwa, tinda Hajara take zuwa makaranta ka taɓa bin bayanta ne sai su, sbd daman ka tsanesu kuma baka sonsu, toh rabbil izzati dai yana sama yana gani... haba dan Allah kuma hakan duk bai isheka ba saida kazo bainar nasi a tsakar gida ka titsiyesu kana musu terere, toh a gsky nagaji karka sake wulaƙanta min ƴaƴa..", Baba ya sauke ajiyar zuciya ya nuna ƙofa yace "fitar min daga ɗaki..", ta sake hura hanci tace "bazan fita ba saina gama amayar da abinda yake zuciyata, ita waccar shegiyar mai salalon tsiya ai harta gama karatun baka taɓa titsiyeta kace ina ta tafi ba sbd ita ƴar mowa ce, su kuma su Sa'adatu da suke borori har neman laifin da zaka liƙa musu kake, karfa ka manta kafin ayi ɗaran akay kwanɗi ehee saida ka samesu kafin ka samu ita Hajarar ƴar gaba da fatiha..", ba ƙaramin hasala Baba yayi ba, ƙirjinsa har zafi yake masa, da kakkausar murya yace "nace ki fitar min a ɗaki..", ta taɓe baki tace "nan nan kaje ka nannago uban kayan abinci munaji muna gani ka aikawa Hajara...", katseta yayi da faɗin "Rabi daga yau baki da dama ko hurumin shigo min ɗaki har abada kuwa, igiyar auren da ta rage a tsakaninmu itama na datseta kije na sakeki..", Maama ta kwalalo mici micin idanunta waje ta dafe ƙirji bakinta na rawa tace "Adamu ni ka saka...? Ni..?", ta fashe da matsanancin kuka, Baba yace "zan rufa miki asiri babu wanda zai san babu aure a tsakaninmu, idan kinga dama sai kije ki yiwa kanki terere a bainar nasin da kika faɗa, amma daga yau babu ni babu ke kuma na shata miki layi da shigowa ɗakina", kuka Maama take wiwi harda fyace majina tace "da girmana da gemu na saida tsufa ya fara kamani zakamin irin wnn sakin na wulaƙancin", a fusace Baba ya fita ya bar mata daƙin don ko ganinta baya son yi, bayan wani lokaci Maama ta fito daga ɗakin idonta sun suntuma sun sake ƙanƙancewa, Umma dake gaban rariya tana rege wake ta ɗaga kai ta kalleta, Maama tace "shegiya mayya uwarki kike kallo", Umma ta ɗauke kai tana taɓe baki, Maama ta shige ɗakinta tana cigaba da rusa kuka, ƴaƴanta sukay cirko cirko akanta suna tambayarta lfy, babu wnda ta tankawa, gaba ɗaya ta wani gigice ta susuce, abu ɗaya take ta maimaitawa wato "da girmana da gemu na". ★Da wuri Hajar ta farka da safe sbd jiya da wuri ta kwanta, ta shiga toilet ta tsala wankanta ta fito ɗaure da towel, gaban mirror ta tsaya tana kallon kitson kanta, ta warware jelolin da ta naɗe da zata shiga wanka, taja stool ta zaune tayi shafe shafenta, tana gamawa ta dakko kaya ta saka, kasa ɗaura ɗan kwalin kayan tayi sbd har wani zugi fatar kanta ke mata, wata hula mara nauyi mai santsi ta saka, daga haka ta feshe jikinta da turare mai sanyin ƙamshi wnda ke cikin kayan da Sakeena ta bata jiya, a hankali ta buɗe ƙofa ta fita, shima a lokacin ya buɗe ƙofar ɓangarensa, da sauri ta ɗauke kai ta wuce ta tsaya gaban stairs ba tare da ta fara sauka ba, juyowa tayi taga yana tunkaro stairs din, ba tare da ta kalli gabanta ba kawai ta saka ƙafarta zata fara sauka, ai kam ƙafar tayi gaba suu, kawai ji tayi an fixgota baya, yasa hannu ya tallafo ƙugunta ta baya yayinda ita kuma ta damƙe gaban rigarsa ta yiwa kanta support, wani juyin masa yayi da ita ya jinginar da ita da bango, har lokacin hannunsa ɗaya na riƙe da ƙugunta ɗayan kuma shoulder dinta, Hajar ta ajiye numfashi kafin ta buɗe idonta ta ringa kallon hannunta da har lokacin yake damƙe da rigarsa, da sauri ta sakesa ta haɗe rai, ɗago kanta tayi ta kallesa wnda hakan yasa ya dena ganin baƙin gashinta da hular kanta ta zame sbd santsinsa, kawai kallon eye balls dinta yake, ta sauke idonta tana jin ƙamshinsa har ƙwaƙwalwar kanta, a bazata ta sake ɗaga kai tana kallonsa jin yayi motsi da hannunsa dake ƙugunta, ta juya lulu eyes dinta tana kallonsa tace "please let go off me"......✍️ 💛 HAJAR 💛 {60..} Kallonsa take tana jira ya saketa, ta ɗan turo baki tana turesa da iya ƙarfinta amma ko gezau, zaro ido tayi jin ya janyota jikinsa sosai, zuciyarta ta buga da ƙarfi ta fasa masa ƙara da iya volume dinta, da sauri ya saketa ya toshe kunnensa, da gudu ta shige room dinta tayi banging door, ƙofar da ta rufe ya kalla yace "Silly girl..", ya zura both hands dinsa a pocket kafin ya sauka downstairs, kitchen ya shiga yayi making coffee ma kansa, riƙe da cup din coffee da saucer dinsa ya fito ya haura sama, a tsakiyar makeken bed dinsa ya zauna, ya janyo Laptop ya kunna, yana operating system din at same time yana sipping Coffee, he was just starting at the monitor while his mind was totally not there, wani thinking din yake daban, ya ajiye cup din kan bedside, ajiyar zuciya yayi yace "Silly girl..", ya kalli agogon da yayi tickling 8 dot, ya ɗauki wayarsa yayi dialing numbern mai masa wankin mota yace masa yazo ya ɗauki motar, yana gama wayar ya tashi ya shiga bathroom, tsaf ya gama shirinsa ya ɗauki briefcase dinsa ya sauka downstairs, compound ya fita ya wuce parking space, babu jimawa kira ya shigo wayarsa, mai wankin motar ne ke kira ya sanar masa cewa yazo, direct Nurain yace ya shigo, bayan me wankin motar ya tafi da black car dinsa ya shiga other car din tasa ya bar gidan, hospital ya wuce wajen tara saura, tini ya fara attending patient da suke Queue suna jiransa, ƙarfe sha biyu saura ya gama da patient din, zaune yake kan office chair dinsa yana kallon glass nameplate mai ɗauke da sunansa, yayi stretching kansa feeling a bit better don ya gaji da zaman, knocking door akay yace "yess", Dr Marwan ne ya shigo da file da big sealed envelope a hannunsa, ɗaya daga cikin kujeru biyu da suke gaban table ya samu ya zauna, exchanging greetings sukay, Dr Marwan ya ajiye file da envelope din kan table yace "here nayi recording komai, ga hoton thorac din nan shima..", Nurain ya gyaɗa kai yace "what about the heart..?", Dr Marwan yace "itama akwai hoton ta", Nurain yace "alright i will check it later..", Dr Marwan yace "Ohk.. this week ne zaku tafi symposium din ko..?", Nurain yace "yeah it's going to start next week monday toh i think before then zamu tafi...", Dr Marwan yace "Ohk Lagos ne ko Abuja..?", Nurain yace "Abuja ne", Dr Marwan yace "okay.. sai anjima" da haka ya fita daga office din. Da yamma Nurain na zaune palourn Mami, Noor ma na zaune itama da Apple Laptop dinta tana kallon wani Chinese movie tana cin croissant, Nurain yace "kun gama exams din ne Noory..?", Noor tayi pausing movie din tace "yeah..", yace "saura jiran result", tace "Eh", wayarta ce ta fara ringing, ɗaukar wayar tayi tana satar kallon Mami sai kuma ta miƙe a hankali ta bar palourn, Nurain na kallon Mami yace "Mami yaushe ne tafiyar naku..?", tace "ohh i think ranar Saturday haka naji Abba yace", Nurain ya gyaɗa kai bai ce komai ba, sai ƙarfe takwas ya yiwa Mamin tasa sallama kafin ya bar part din nata, ya fita babban compound din gidansu, Noor ce ta fito compound din itama da small carton box a hannunta tace "Yaya", ya dakata da tafiyar ya juya yana kallonta har ta ƙaraso tace "Ya ga wnn please ka kai ma Hajar" ta fada tana miƙa masa box din, amsar box din yayi yace "sure", tace "thank you... good night" da haka ta wuce cikin gida, Nurain na isa gida direct ɓangarensa ya wuce, bayan yayi wanka ya saka white pajamas masu sweat pant, yayi combing hair dinsa kafin ya zura room slippers ya fita paloun sa, ajiyar zuciya yayi ya ɗauki box din daya ajiye kan kujera ya fita ɗakin, murɗa ƙofar room dinta yayi ya shiga bayan yayi sallama ƙasan maƙoshi, Hajar dake zaune kan carpet ta rufe jikinta da duvet bayanta jingine da bed ta ɗago ta kalli ƙofa, da sauri ta ɗauke kanta, ya ajiye box din kan makekiyar chest of drawers dake room din, ganin ya fara tafiya towards her tayi sauri ta kwanta ta rufe har ka tana turo baki, ya duƙa kusa da ita muryar ƙasan maƙoshi yace "hey", wata shegiyar harara ta shiga bankawa daga cikin duvet sai kace wata psycho, tapping dinta yayi yace "hey..", tini ta yaye rufar ta miƙe zaune tace "ni ka dena taɓani babu kyau fa, it's not proper", ta matsa baya tana harararsa ƙasa ƙasa, yace "then who said ki ringa kwanciya a nan..?", tace "ra'ayi", yace "everyone thinks you are a good gal basu san cewa you are just a hyena with goat skin ba, you gat an innocent face but you are so harsh and rude...", ya nuna mata box din da ya ajiye yace "from Noor ɗaya daga cikin mutanen da kikay deceiving don nasan bata san bad attitude dinki ba..", Hajar ta ƙura masa idanu tana jin zafin kalamansa, da kyar ta iya cewa "are you done.. please off the light idan zaka fita", da haka ta koma ta kwanta ta rufa har ka tana jin raɗaɗin abinda ya gaya mata, hawaye ya ciko idanunta ta fara shessheƙa a hankali, yess tasha zagi sosai a wajen siblings dinta don shegiya ma suke kiranta, gashi dai shi ba zaginta yayi ba kawai mgana ce ya gaya mata amma sosai ta taɓa mata zuciya, har lokacin yana duƙe gefenta yana jinta, duvet din ya kwashe daga jikinta, tayi sauri ta tashi zaune ta haɗe kanta da guiwa, ya haɗe thick eyebrows dinsa strictly yace "shut up... me aka miki zaki ɓarewa mutane baki", chaɓ mgnarsa wofi don cigaba da tayi da kukanta a hankali, ɗago kanta yayi tana jin hakan ta fixge ta ja da baya, kanta a ƙasa tace "Please dan Allah na roƙeka kawai ka sakeni, ka bani takarda ta ko kuma ka furtan da baki nayi tafiyata..", kallonta kawai yake cike da mamaki kafin yace "amm young lady you are asking the wrong person, i think i told you ni banida wata mata bare na rubuta mata saki", ta ɗaga kanta ta ɗan kallesa sai kuma ta mayar tana kallon yatsun ƙafarta tace "Okay toh kawai just imagine ni matarka ce kace ka sakeni shknn..", duƙar da kansa yayi to cover the slight smile on his face kafin ya ɗago girarsa a haɗe yace "never... i will never imagine you as my wife and you will never be.." yana gama faɗin haka ya tashi ya nufi ƙofa saida ya kashe mata fitilar snn ya fita, Hajar ta gyaɗa kai ta koma ta kwanta. Ranar Friday ƙarfe 1 Nurain ya fita zuwa mosque kuma bai dawo gidan ba sai yamma, yana shiga palour yaji wani ƙamshin turaren wuta ya huda masa hanci, ya ringa ƙarewa palourn kallon deeply in his mind yana appreciating, ƙofar Kitchen aka buɗe sai gata nan ta fito tana kakkaɓe hannunta, turus tayi tana kallonsa dan yau three days knn rabonta dashi, ta yamutsa fuska ta haura sama walking slowly, ɓangarensa ya wuce direct ya shiga bedroom, farin yadin jikinsa mai kyau ya cire ya shiga wanka, bayan ya fito daga wankan ya shiga closet ya ɗakko black Shirt na polo with trouser, yana gama shiryawa ya ɗauki car key ya fita, har ya sauka downstairs sai kuma ya tsaya yana kallon stairs din, lokaci guda ya juya ya koma saman, ƙofar ɗakinta ya buɗe, zaune ya sameta kan tiles tana yanke farce with nail cutter, ta ɗaga kai ta masa kallo ɗaya sai kuma ta cigaba da abinda take, Calmly yace "ki ɗakko veil dinki zamu fita..", with weird expression ta kallesa ba tace komai ba, ta sunkuyar da kanta tana kankare farcen, yace "kinji me nace kuwa..", a hankali ta gyaɗa masa kai, yace "toh ai banga kin tashi ba", jimm tayi sai kuma ta tashi ta ajiye nail cutter din a kan mirror, well ironed hijab ta ciro daga wardrobe ta saka, fita yayi daga ɗakin tabi bayansa tana harararsa ƙasa ƙasa, tana biye dashi har zuwa parking space gaban motar da taga ya tsaya, ya buɗe lock ya shiga, tsaye tayi taƙi buɗe motar ta shiga, fitowa yayi yana kallonta yace "get in malama kina ɓatamin lokaci..", ta maƙe shoulder tana jan fingers dinta tace "nidae saidai mu hau Napep..", zaro ido yayi yace "what.. tricycle..?", ta gyaɗa kai ba tare da ta dubesa ba, yace "toh me yasa zan hau Napep bayan ga car dina..?", tace "toh shknn ka hau motar naka nidae napep zan hau", kawai kallonta yake, she's so childish, wataran idan ta maka abu sai ka dauka wata babbar macen ce, daga zarar ta kwaɓa maka wata shiriritar anan zaka gane yarinya ce shataf, haɗe gira yayi yace "kee!! shiga mota bana son shirme", harde hannu tayi ta juyar da kai tana ƙunƙuni, zagayowa yayi ya buɗe front seat, ba tay aune ba taji ya fixgi hannunta ya sakata a motar ya kulle, ya zaga driver seat ya shiga, hawayen da ya zubo cheek dinta tayi ƙoƙarin gogewa da bayan hannu don kar ya gani amma kuma saida ya ganin, har suka bar unguwar suka hau saman titi zuciyarta bugawa take da ƙarfi, sosai ya gane ƙin hawa motar da tayi yasan speed dinsa take tsoro, with minimum speed yake jansu don karta hargitse masa kafin su isa inda zasu, suna karya kwanar gidan Abba ya juya ya kalleta for the first time yace "Ke!!..", ta ɗan kallesa tace "Hajar", yana driving slowly har ya tsaya gaban makeken gate din gidansu yace "whatever... na kawoki nan don ki yiwa Mami sallama cause gobe zata bar gari, nayi hakan ne sbd yadda suka daukeki amma ni dai a wajena you don't worth it" yana gama faɗin haka ya danna horn, mai gadi ya zuge masa gate ya shiga yayi parking a compound, ya kashe motar yace "and behave yourself..", ya buɗe motar ya fita, fitowa tayi itama, shi yayi leading dinta har katafaren main palour wnda ba baƙonta bane, ya nuna mata kujera yace "sit" kafin ya wuce part din Maminsa, three minutes da zamanta a palourn taji footsteps ana sakkowa daga sama, ta ɗaga kai sukay ido huɗu da Noor, Noor ta ware ido tace "Ohh my God... is this you Hajar", murmushi Hajar tayi ta gyaɗa mata kai, Noor ta ƙarasa inda take tana welcoming dinta sosai, Noor ta zauna gefenta tace "yaushe kika zo..", Hajar tace "just now..", Noor tace "amma dai tare da yaya kike ko..?", Hajar ba ta kai ga amsa mata ba aka bude ƙofar part din Mami, Nurain ne with a repartee yana kallon Hajar yace "come in" ya juya ya koma ciki, Noor tace "muje can din", tare suka shiga ɓangaren Mamin, Hajar ta gaida Mami da ladabi, amsa mata Mami tayi with care ta tmbyeta lfyrta, Nurain dai kawai satar kallonta yake ganin yadda ta koma wata saliha sai kace gske. kafin Magrib hajjaju Hajiya ta iso gidan tare da Farooq da ya kawota, a main palour tayi branching don daman idan tazo gidan anan take fara zama, zuwan Hajiya yasa Mami ta fita main palour wajenta, Nurain ma ya tashi ya fita, Noor ta riƙe hannun Hajar tace "muje muma mu gaida Iron lady". Hajiya ta ringa kallon duk wanda ya gaisheta ta ƙasan kantamemen glasses dinta, sai kuma ta amsa a fixge alamar ƴan rigimar ne a kanta, Hajar na gaisheta itama ta ƙura mata ido sai kuma tace "Ahh ahha wai matar Usuman ce..", Noor tace "Eh itace", Hajiya tace "ywwa yanxu naga kiwo mai kyau.. da Usuman yaƙi sakin abinci a gidansa gaba ɗaya yarinya ta tsomare har ta fara fita hayyacinta, ynxu kam alhmdllh ai ta mayar da komaɗarta har ma ta ƙara", Hajiya ta kalli Mami tace "wnn tuwon naki na alkama nake son ci wllh", Mami tayi murmushi tace "toh Hajiya bari na duba garin" da haka ta tashi ta bar palourn ta shiga kitchen, Hajar dake zaune gefen Noor ta ɗaga kai ta kalli Farooq da yake kallonta, saukar da idanunta tayi tace "ina yini", da fara'a ya amsa yace "how are you doing..?", tace "fyn alhmdllh..", Nurain ya ɗago kansa daga latsa wayar da yake ya dubi Farooq, miƙewa yayi ya saka wayar a pocket yace "mu wuce mosque lokacin sallah yayi punk" bai jira cewarsa ba ya nufi door, Farooq ya tashi yabi bayansa, a tap din dake compound suka tsaya yin alwala, Farooq na tsaye bakin pampon yana jiran Nurain ya gama shima yayi yace "naga ma ai ba a kira sallahn ba", Nurain na wanke ƙafarsa yace "Eh mu zama ready kafin a kira..", Farooq yace "Ohk", Nurain na gama alwalar Farooq ma yayi, daga nan suka fita zuwa mosque wnda sai ynxu ma aka fara kiran sallah. Hajar na zaune kan darduma bayan ta idar da sallahr magrib a dakin Noor, cikinta ne ya ƙulle tana jin kamar cramps amma dai bata tabbatar ba, Noor ta shigo tana murmushi from ear to ear tace "kixo inji Hajiya", Hajar ta ɗan zaro lulu eyes dinta tace "Okay", ta tashi tabi bayan Noor suka wuce part din Hajiya, turus Hajar tayi a bakin ƙofa ganinsa a palourn Hajiyar shi da Farooq, Noor dai ta wuce ta zauna kan sofa ta cigaba da chatting dinta a phone, Hajiya dake zaune kan lallausan rug tace "ƙaraso ciki mana ƴar nan", a hankali Hajar ta wuce ta zauna kan Carpet, Hajiya tace "yauwa ko kefa ƴar nan", Hajiya ta juya tana kallon Farooq tace "mai gidannn..", Farooq yace "Amaryasss", Hajiya tace "ina dubulan da Alkaki da ka kwana biyu kana ci a wajena...", Farooq ya gyaɗa kai yace "yess wnn masu daɗin", tace "ƴar Albarkar yarinyar nan ce ta ciko min leda dasu, ai naji dadin kayan zaƙin nan don duk ranar da na cii saina shi mata albarka... mai gidann na gaya maka sam fa batada rowa wllh tllh..", Farooq yayi murmushi yana kallon Hajar yace "ni kam rowa tamin da naje..", Hajar ta ɗaga kai ta kallesa tace "Ai baka zauna ba kana zuwa ka tafi", yace "Okay dana zauna da za a ban..?", ta gyaɗa kai tace "Eh", Nurain da ke zaune sai kace an dasa sa ya kalli Farooq sai kuma ya kalli Hajar, haɗe gira yayi ya tashi sai kace wnda aka mintsila yana kallon Farooq yace "i gat something to tell you...", Farooq yace "Ohk then tell me", Nurain yace "privately.." sai kuma ya nufi ƙofa ya buɗe ya fita, few seconds Farooq ya tashi yabi bayansa, a main palour ya tarar dashi zaune kan sofa, ya ƙarasa ya zauna yana kallonsa yace "what is it that you want to tell me...?", Nurain yace "nothing let stay here..", Farooq ya tsuke ido baice komai ba kawai ya tashi zai bar palourn, Nurain yayi saurin dakatar dashi da fadin "lets go to my room i will tell you there", Farooq dai ya kallesa baice komai ba, Nurain yayi tapping shoulder din Farooq yace "c^mom punk". Bayan fitarsu Nurain Hajiya ta taɓe baki tace "yau naga jalala shifa wnn fel wayar bai fiya san jama'a ba, yazo ya zauna min a kujera yayi wani ƙwamm dashi ba uhmm ba umm ummm sai kace bebe, kuma wnda muke ƴar firar ma ya ɗauke mana shi.. Allah dai ya kyauta da wnn hali", sai kuma ta kalli Noor tace "jeki amsomin tuwo na", Noor tace "toh iron lady" ta tashi ta fita, Hajiya ta zura hannu a ƙatotuwar jakarta ta ɗakko kwalbar man zafi tace "temaka min ƴar nan..", Hajar ta amshi kwalbar ta buɗe, albarka Hajiya ta shiga ɓarkawa Hajar bayan ta gama mulke mata ƙafafuwa da man zafi, Hajiya tace "tararrabin hawa jirgin nan nake don bana son zama a kujera kumburan ƙafa yake...". Ƙarfe tara saura Nurain ya fito daga great room din Abba bayan ya yiwa Abba sallama da cewar gobe da safe zaizo ya ajiyesu a airport don jirgin 8 zasu bi, Hajar ta shiga part din Mami don mata sallama, da ladabi tace "Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy..", Mami tace "Ameen daughter Allah yayi albarka", har compound Noor ta raka Hajar, Nurain ya gama maganar da yake da Garba snn yaxo ya buɗe motar ya shiga, sallama sukay da Noor ta buɗe motar ta shiga, ta kalli window ko kallon position dinsa ba tay ba, driving ya farayi suka bar unguwar, koda ya hau babban titi baiyi irin gudun da ya saba ba amma dai gudun yake. gani tay kawai ya samu gefen titi ya tsaya, ita dai ta cigaba da kallon window ba ta kallesa ba, after few seconds taga dai basu cigaba da tafiya ba sai ta ɗan juya ta kallesa, kallonta taga yana yi without blinking, ta haɗe rai ta juyar da kanta, yace "So daman kinada manners..", ta juyo ta galla masa harara ta ɗauke kanta, yace "and kin kware wajen yiwa maza magana ko"......✍️ 💛 HAJAR 💛 chapter 61 👇 Arewabooks.... Eager to read go there ☺️ 💛 HAJAR 💛 {61..} Hajar dai kawai kallonsa take da wani irin expression, tama kasa gane me yake nufi bare ta fahimta, har lokacin bai dena kallonta ba thick eyebrows dinsa a haɗe, sai ynxu ya fahimci tmbyar da yayi mata which is meaningless to him, to me yasa ma zai mata wnn tmbyar, ta juya ta cigaba da kallon window da sigar ko in kula, kawai ji tayi ya fixgota ya juyo da fuskarta tana kallonsa, ɗan buɗe baki tayi ta sha kunu tace "ni ka dena taɓani", yace "is there anything to touch...?", ta haɗiyi wni miyau ba tace komai ba ta gasa masa harara, ya ajiye numfashi yace "one day one time" da haka ya kunna motar suka cigaba da tafiya, suna zuwa gida ta buɗe motar ta fita ta wuce entrance, a bakin door ta jirasa har yazo ya buɗe mata ta shiga. shi kam kitchen ya wuce ya haɗa Coffee kafin ya haura sama, saida ya gama shan Coffeen snn ya shiga wanka, after ya shirya cikin Pajamas ya rage wutar ɗakin yabar dim, Laptop dinsa ya dauka ya hau kan bed, operating system din ya fara, after 40mins ya gama abinda zai yi ya kashe laptop din, ya ɗauke remote din AC ya ƙara mata gudu snn ya kwanta ya lumshe ido, buɗe ido yayi bayan minti biyar sai kuma ya miƙe zaune, zuro legs dinsa yayi ya zura room slippers ya tashi tsaye, door ya nufa ya buɗe ya fita, ya ringa kallon ƙofar room dinta bayan ya isa corridor, ya kai hannu jikin handle amma bai murɗa ba, after few seconds kawai ya murɗa handle din ya shiga, a hankali ya saki handle din ya shiga ɗakin making sure baiyi making ko wane sound ba, he spent almost 3mins yana kallon innocent face ɗinta tana bacci, kwance take a inda ta saba kwanciya kan carpet, ta rufe da duvet har zuwa wuyanta tana bacci Calmly, duƙawa yayi kusa da ita still looking at her face. Da asuba Hajar ta farka, ta taƙune fuska ta shafa laushin da ta jita a kai, miƙewa tayi zaune ta fara ƙarewa room din kallo sai kuma ta kalli gadon da take kai, zaro ido tayi ta dafe kanta to yaushe ta hau gado, ita da ta kwanta kan Carpet toh ya ta tashi ta ganta a gado, yaye rufar tayi ta tashi ta kunna fitila ta ƙara hasken ɗakin, ta ringa kallon gadon kafin ta girgiza kanta ta shiga bathroom, alwala tayo ta fito ta shimfiɗa dardumar ta fara gabatar da raka'ataynil fajr. Ƙarfe Shida da ƴan mintina Nurain ya fita compound da car key a hannunsa, Hajar ta gyara tsayuwarta a jikin window ta buɗe curtain din da kyau tana kallon compound, idonta ne ya kai parking space kawai ta hangosa, ta sha kunu tayi sauri ta rufe labulen ta bar wajen tana yamutsa fuska. kafin shida da minti arba'in Nurain ya isa gidansu, Already matafiyan sun zama ready, yana shiga main palour ya tarar da Hajiya da kwanon tuwon alkama da tasa akay mata warming, gaisawa sukay ta amsa masa a takaice sai kuma ta fara tambayarsa Hajar, a fizge ya bata amsa ya wuce ciki, box din Mami yaje ya ɗakko ya fita da ita, Drivern Abba ne ya ringa arranging luggage a booth din motar gidan wacca zata kwashesu gaba ɗaya comfortably, Nurain ne yayi driving motarsu Abba while Drivern Abba yayi driving motar Nurain din, Nurain bai bar airport ba saida su Hajiya suka shiga filin jirgi, car key dinsa ya amsa hannun Drivern Abba ya damƙa masa na motar gidansu. yana komawa gida daman kwanciyarsa yayi ya huta, ko da ya farka abinda ya fara faɗo masa shine wnn workshop din, shaf ma ya manta da wani symposium, slight hiss yayi ya janyo wayarsa yayi booking flight, azabar yunwa ce tasa ya fita eatery yayo takeaway, koda ya dawo gida tsattsakurar abincin yayi ya ture. Tin fitar da yayi kafin azahar ya siyo abinci bai sake fita ba, daman yau Saturday ba ranar aiki bace, Hajar kam ko gilmawarta bai gani ba, itama dai ta fahimci a waɗan nan kwanakin ne yake zama a gida shiyasa bata fiya warkajami ranar asabar da lahadi ba. wajen ƙarfe takwas na dare Hajar ta buɗe ƙofar room dinta, a hankali ta fito ta sauka downstairs, kitchen ta wuce ta buɗe fridge ta dauki bottle water ta fito ta haura sama, tana gama haurawa stairs din shima a lokacin ya fito daga ɓangarensa hannunsa riƙe da empty cup da ya sha Coffee, saukar da idanunta tayi ta wuce ta shiga ɗakinta, binta yayi da kallo lokaci guda brain dinsa ta amsa, ya zaiyi da ita knn.. gobe zai wuce Abuja fa, ƙasa ya sauka ya kai cup din kitchen snn ya koma saman, a palourn sa ya zauna yana neman one Solution, toh ya zaiyi da yarinyar nan, shi dai bazai barta a gida ita kadai ba hkan ma beyi making sense ba gsky, toh ko dai gidan Sakeena zai kaita, girgiza kai yayi don hakan shima bai masa ba, yayi tunanin ya kaita gidan Aunt dinsa Zulaihah, shima dai hakan bai masa ba... toh ko dai yace ta tattara ta tafi gidansu ne kawai, chab duk ciki ma hakan shine worst. wayarsa ya ɗauka ya canza flight din daga na safe zuwa dare bayan yayi booking wani seat din, yayi ajiyar zuciya yayi resting da kujera. washe gari ƙarfe goma Hajar na tsaye kitchen tana dafawa kanta breakfast, bayan ta gama ta zauna kitchen din taci snn ta wanke komai da tayi amfani dashi ta fita, palour ta fita ta fara kakkaɓe cuisine tana arranging trow pillows, yamutsa fuska tayi sbd cikinta da ya murɗa a bazata, ajiye duster din hannunta tayi ta haura sama hannunta dafe da cikinta, tasan ma cramps ne yake shirin antayo mata, haka ciwon ya wuni yi mata saidai bai tsawaita ba shiyasa bata wahala kamar yadda yake mata ba, zaune take kan darduma bayan ta idar da sallar magrib, a ynxun ma dai cikin ne ya ɗan murɗa mata, kawai jira take ayi sallar isha'i ta tashi tayi ta kwanta kawai, ƙofar ɗakin aka murɗa kafin aka buɗe aka shigo, ta ɗaga kai tana kallonsa, tini pure men scent dinsa ya bulale ɗakin, yayi sallama ciki ciki kafin ya ƙaraso cikin ɗakin, yana kallonta yace "ki haɗa duk wani abu da kika san zaki buƙata idan zaki wani wajen kwana...", ta ɗago ta kallesa sai kuma ta ɗauke kanta ba tace komai ba, ya kalli tsadadden agogon wrist dinsa yace "you just have 10mins to do that.." yana gama faɗin haka ya juya ya fita, taɓe baki tayi ta jinginar da kanta da gado, after 15mins Nurain ya sake dawowa ɗakin, zaro piercing eyes dinsa yayi ganinta inda ya barta ɗaxu, kawai gani tayi ya shigo ɗakin ya wuceta ya tsaya gaban makekiyar wardrobe din kayanta, buɗe wardrobe din yayi ya ringa kallon ciki sai kuma ya rufe ya buɗe wani section din, boxes din lefe ya gani an jerasu a ciki, ƴar madaidaiciyar box ya sauke ya ɗora kan bed ya buɗeta, cike take da kaya ya zazzage kayan ya barta empty, daga nan ya fara sauke ragowar boxes din, Abaya set uku ya ɗiba ya zuba a empty box din, sai kayan bacci da ya kwashi wajen set shida suma ya zuba ciki, Hajar dai na zaune inda take tana binsa da ido, ya mayar da boxes position dinsu wacca ke kan bed kawai ya bari, ya sake buɗe section din kayanta ya fara janyo duk wnda hannunsa ya fara taɓawa, haɗe gira tayi ta miƙa tace "meye haka wai, ni ka dena taɓamin kaya..", banza yayi da ita har ya gama ɗebar abinda zai ɗauka ya jibga a box din, bathroom ya shiga ya fito da shower gel da spoonge, ya zuge ƙaramin zip na akwatin ya zuba a ciki, daga nan ya wuce gaban mirror, tsaye yayi yana kallon tarkacen kai ya rasa abinda zai ɗauka don mirror din a cike yake da kayan shafe shafe, juyawa yayi ya kalleta for the first time yace "zo ki ɗauki abinda kika buƙata a nan..", with confusion written all over her face take kallonsa, ya haɗe thick eyebrows dinsa strictly yace "Ba magana nake miki ba... you are wasting my time malama..", saukar da idanunta tayi ta isa gaban mirrorn ta fitar da body lotion din da take shafawa sai perfumes guda huɗu, ya kalleta yace "is that all you need..?", turo baki tayi ta ɗauki hair butter da oil tayi drawing drawer ta ɗakko comb, ya kalleta da gefen ido kafin ya kwashe kayan shafar ya zuba a box din ya zugeta ya ɗauka ya nufi door, juyowa yayi yana kallonta yace "get change right away" da haka ya fita, Hajar tabi ƙofar da ya rufe da kallo tana sauke ajiyar zuciya, toh meye haka ne wai, kawai sai tayi tunanin ko gidansu zai mayar da ita ne, hakan yasa taji wani mugun daɗi ta ringa fatan Allah yasa haka ne, within few minutes ta gama canza kaya, doguwar rigar Abaya ta saka tayi rolling kanta da veil din Abayar, ko 1mins ba tayi da gama shiryawa ba sai gashi nan ya shigo, daga bakin door ya tsaya yace "ki jirani a compound", ba tace komai ba ta wucesa ta sauka downstairs, ɗakin nata ya shiga ya kashe duk wasu kayan wuta snn ya rufe ya fita, daman already ya kashe electric appliances na palour dana kitchen, freezer da fridge ne kawai ya bari a kunne sbd perishable food da suke cikinsu, tsaye ya ganta a dan nesa da balcony, ya rufe entrance door kafin ya nufi inda mai gadi yake zaune, Hajar tabi bayansa da kallo har ya gama mgana da Inuwa snn ya wuce parking lot, dashare haƙora Inuwa yayi ya cusa uban kuɗin da Nurain ya basa a pocket, tashi yayi ya fara zuge gate. a hankali Hajar ta isa parking space din ta tsaya gaban motar, shiga motar tayi ta fakaici kallonsa tace "gidan mu zaka kaini ko..?", baiko kalleta ba ya sauke handbrake yace "close the door", sai a lokacin ta rufe ƙofar, driving Nurain ya fara yi bayan ya dubi agogon dashboard wnda ya haska ƙarfe takwas da minti ashirin na dare, Flight dinsu na ƙarfe tara ne so he have to make it there kafin time din, haka suka bar gidan Inuwa na ɗaga musu hannu. Hajar tana ganin ya fara sharara gudu tace "kabi a hankali dan Allah, unguwarmu akwai yara da suke tsallaka titi..", without looking at her yace "Ohk" amma bai rage gudun ba, can dai taga samm hanyar da suke bi ba tayi kama da ta zuwa unguwarsu ba, shan kunu tayi tace "where are you taking me...? nan fa ba hanyar gidanmu bace", yana driving dinsa yace "Ohk", Hajar ba ta sake mgna ba tana jiran taga destination din da zasu, suna isa Airport yayi parking wajen da ake ajiye motoci, ya bude booth kafin ya sauko daga motar, sauke box din kayanta yayi da bag dinsa, har ya gama Hajar ba ta fito ba tana zaune cikin mota, tini idonta ya ciko taf da ruwa, toh ina ne nan din ya kawota, itafa gida ta saka ran zai kaita, buɗe murfin motar yayi yana kallonta yace "come down", ta sauke kanta ta fito a hankali tana bin wajen da kallo, key din motar ya bawa wni ma'aikacin Airport din masu kula da motoci, da haka ya dubeta yace "wuce muje", zirr hawayen da suke maƙale idonta suka zubo tayi sauri ta goge da bayan hannu tace "dan Allah cewa fa kayi gidanmu zaka mayar dani..", ya ɗage gira yace "ni mukayi haka dake..?", shiru tayi can tace "toh idan ba gidan mu ba ina zaka kaini da kaya..?", yace "siyar dake zanyi dan naga za kiyi tsada..", zaro ido tayi tace "am not a toy aii..", bag dinsa ya rataya ya nuna mata box din kayanta yace "Ja muje", maƙe shoulder tayi ba tace komai ba, box din ya fara ja ya wuce ya barta a wajen, saida taga ya mata nisa sai kuma ta kyalla da gudu tabi bayansa, tana zuwa kusa dashi ta fashe da kuka tace "kawa Allah da manzonsa kazo ka kaini gidanmu..", ya cigaba da tafiyarsa, tana biye dashi tana kuka a hankali, da haka suka isa departure har aka gama musu checking aka tafi da kayansu za a saka a jirgi, sai kace wata jela haka take biye dashi tana kuka mara sauti, gashi har lokacin ba ta fahimci nan din ina ne ba, ya amsar musu tickets snn suka wuce filin jirgi don har jirginsu ya fara boading, sai a lokacin Hajar ta fahimci a inda take bayan taga manya mayan Aeroplane da suke a parke. da haka tabi bayansa suka shiga jirgi, seat dake kusa da window ya samu ya zauna ita kuma ta zaune seat din dake gefensa, babu jimawa aka fara announcing jirgi zai tashi, passengers suka fara fastening seat belts, Nurain ma yayi fastening nasa, ganin ba ta saka nata ba yace "ke.. ba kiji abinda akace ba..?", ta kallesa da idanunta da suka ɗan haura tana twisting pink lips dinta, ɗauke kansa yayi bai sake kallonta ba, har jirgin ya hau runway bata saka belt dinta ba, slight hiss yayi ya ɗaura mata da kansa ya koma ya zauna da kyau a seat dinsa, habawa ai jirgi na takeoff Hajar taji wani zimmm ya tsarga mata, ƴan hanjinta suka baro ciki sukay ƙabe ƙabe a kirji, ba ta san lokacin da ta ruƙunƙumesa ba, saida jirgin yayi labelling snn ta sakesa, ta jingina da seat dinta tana jin wani iri, ji take kamar za tayi amai, ta jima bata dawo daidai ba, throughout the journey idonta biyu, shi kam tinda ya kwama headphones a kunnensa ya saka karatun Alkur'ani ya lumshe ido, lokacin da jirgin zaiyi landing Hajar tafi shiga yanayi a kan lokacin takeoff, bayan ruƙunƙumesa da tayi saida ta kifa kanta a ƙirjinsa, a hankali ta fashe da kuka tace "na shiga uku na lalace", haka sauran passengers suka fara fita daga jirgin, Nurain ya cire headphone din kunnensa ya rage murya yace "ɗagani malama..", a hankali ta sakesa tana turo baki, ya ɗan kalleta kafin ya cire belt ya tashi ya wuceta zai fita, bin bayansa tayi da kallo sai kuma ta goge fuskarta ta tashi ta bisa, luggage dinsu ya amso musu da haka kuma suka fita wajen airport din, Cab ya tsarar musu suka hau suka bar Airport din, after a ride of about 30mins drivern Cab din yayi parking cikin wani danƙareren hotel wnda daman shine location da Nurain ya basa, Nurain ya biya mai Cab kuɗinsa da haka ya wuce zuwa reception, wani worker ne ya shigar musu da kayansu, ID card da wata paper Nurain ya nunawa receptionist din, tini ta gane manyan baƙin da akay musu booking ne tin last week, Keycard ta ɗakko ta basa harda ɗan russunawa, ya amsa yace "thank you", tayi saurin cewa "my pleasure sir", ta elevator suka haura zuwa room din nasu dake 15 floor, workern dake riƙe da luggage dinsu ya ajiye daga bakin ƙofa snn ya bar wajen, Nurain ya saka Keycard ya buɗe room din, the room is huge and luxury with big bathroom, Hajar dai tayi tsaye bakin ƙofa tana ƙarewa room din kallo, Nurain ya ɗauki jakar kayansa ya buɗe closet ya saka, bathroom ya shiga ya ɗauro alwala, ya fito yana jan hannun rigarsa, kallonta yayi yace "are you a soldier..?", tayi rolling eyes tace "yess", prayer mat da ya gani a cikin closet ya ɗakko ya shimfiɗa ya kalli direction din da akay indicating a jikin wall, har ya idar da sallar Hajar na tsaye inda take, Atm card dinsa ya ɗauka ya nufi ƙofa yace "excuse me Captain..", ta ɗan matsa kaɗan, ya kewayeta ya fita, saida ya rufe ƙofar ta fahimci fa ita kadai ce a nan din, ƙarasawa cikin ɗakin tayi ta zauna kan couch, tanata zaune a wajen sai kuma ta tashi ta shiga bathroom tayi alwala, ta fito ta kalli inda ya kalla tayi sallahr Isha'i, Sai 11 ya dawo a lokacin Hajar ta gama cika famm da tsoro, yana shigowa ta miƙe tace "ni karka sake barina ni kaɗai..", ya ajiye ledojin da ya shigo dasu kan carpet yace "are you a kid..", sai kuma ya nuna mata ledar abinci yace "take your dinner..", daga haka bai sake kallonta ba ya bude closet ya dauki Pajamas dinsa ya shiga toilet ya saka, yana fitowa ya matsa gaban makeken bed din da ya sha white bedding ya ɗauki pillow da ƙaramin duvet, kan couch ya hau yayi kwanciyarsa. Da asuba Nurain ya farka, vision dinsa na daidaita ya fara surveying kan gado with his sleepy eyes, wayam yaga bata nan kuma babu alamar an hau gadon, can ya hangota ƙasan carpet ta dunƙule waje ɗaya, har yayi sallah yayi wanka ya shirya bata farka ba don ba ita tayi bacci ba sai wajen 3 na dare, before 7 ya gama shirinsa, har ya kai bakin door da bag din laptop dinsa a hannu sai kuma ya dawo, ya ringa kallonta ganin ta takure kanta ya dawo da baya ya ɗauki duvet din da ya rufa ya lulluɓa mata, da haka ya fita daga ɗakin ya rufe, A restaurant din hotel din yayi mata order both breakfast and lunch, ya gaya musu room din da za a kai da kuma time, shi kuma anan ya zauna yayi breakfast din, da ya gama ya wuce babban conference hall dake hotel din inda a nan za ake duganar da training din.....✍️ 💛 HAJAR 💛 {62..} Bai daɗe da fita ba Hajar ta farka daga baccin da take sakamakon cramps din da yake sukarta a cikin baccin, ta yamutsa fuska ta miƙe zaune tana kallon duvet din jikinta, muttsuke idonta tayi ta kalli couch din ɗakin, ta fara yaye duvet din sai kuma ta tsaya tana kallonsa, a hankali ta kai duvet din hanci perceiving the scent, ta taɓe baki gami da yin wurgi da duvet din kafin ta tashi a hankali, ƙarewa ɗakin kallo kawai take sai kace mai neman wani abun, walking like a chameleon ta isa bakin ƙofar toilet, she want to use it amma kuma tana tunanin may be yana ciki tinda dai bata gansa a ɗakin ba, kara kunnenta tayi da jikin ƙofar wai ko za taji wani sound, ɗipp ba taji anysound ba don haka ta samu courage din murɗa handle, ta shiga toilet din tana jin kamar ana mata ruwan allurai a cinye, daman tin tini haka cramp yake wahalar da ita, ganin she is still clean kawai ta ɗora alwala ta fito, ta gyara rolling dinta da ya sakwarkwace wajen bacci da yin alwala kafin ta kabbara sallah, tana idarwa ta kalli ledojin dake kan carpet har lokacin, turo baki tayi ta fara buɗewa, rolls din satchet of white coffee ta gani wajen uku sai milk sai kuma black coffee, taɓe baki tayi ta janyo wata ledar, anan taga toothbrush and toothpaste da detergent, zamewa tayi ta kwanta ta ringa twisting toes dinta shallow in pain, after 40mins lokacin ma takwas ya gota taji ana knocking door a hankali, ta tashi zaune tana kallon ƙofar, saida aka sake knocking snn ta miƙe ta isa bakin ƙofar, tana buɗewa waiter dake riƙe da park din Abinci cikin leda yace "good morning maam..", tace "morning..", ya miƙa mata ledar hannunsa yace "here is your order", kallon ledar ta tsaya yi bata amsa ba, waiter yace "gashi fa Maam", sai a lokacin ta amsa ta mayar da ƙofarta ta kulle, jingina tayi da ƙofar, after few seconds ta bude ƙofar tana leƙa waje wai ko za taga waitern ta tambayesa whereabout din wnda take jira tin dazu, wayam taga long Aisle din mai ɗauke da ƙofofi rututu, idonta yayi rau rau ta juya ta koma ɗaki, a kan couch ta zauna ta fara buɗe ledar, Irish ne da kidney sauce sai golden yam, ga bottle water da lemon kwali, tashi tayi ta dauki ledar da ta ga toothpaste da toothbrush, without second thought ta farke brush din ta matsa masa paste ta shiga toilet, bayan ta gama brush ta kuskure bakinta da mouth rinks da ta gani gefen sink, fitowa tayi ta zauna taci lafiyayyen breakfast dinta, kuma sosai taci abinda don ya mata dadi, saida ta gama ci ta ajiye ragowar snn ta fara tunanin wanka, sai a lokacin ta dubi box ɗinta dake bakin ƙofa tin daren jiya, ta janyo box din ta shiga da ita cikin ɗakin sosai, a hankali ta zuge zip tana kallon kayan ciki, ta harari kayan bayan ta tina ydda aka haɗasu, zaro ido tayi ganin harda undies sai kuma ta juyar da kai tana turo baki, sponge da shower gel dinta ta ɗauka ta shiga bathroom, tayi amfani da towel din da ta gani a jikin hanger, bayan tayi wanka ta fito ta shirya abinda, zaune tayi kan couch ta idonta ƙif akan ƙofa, tunani iri iri ya ringa zuwar mata ka, toh ko dai nan ya kawota shi yayi tafiyarsa, da sauri ta miƙe ta isa gaban closet ta buɗe, tana ganin bag dinsa taji wani mugun relief, tayi ajiyar zuciya kafin ta rufe closet ta koma ta zauna, ƙarfe sha biyu cleaner mace ta shigo ta gyara ɗakin, Cleaner ta gama aikinta ta fita, Hajar dai ta gaji da zama ta kwanta, saida taga har biyu na rana ta gota amma babu alamar zai dawo, da sauri ta miƙe jin anyi knocking door, har tana harɗewa sbd sauri taje ta buɗe door din, tayi turus tana kallon waitern da ya kawo mata breakfast, this time around ma ya gaisheta kafin ya miƙa mata ledar hannunsa, ta amsa tana jin wani ƙululu ya tsaya mata a throat, har waitern ya juya zai tafi tace "dan Allah ji mna..", ya juyo yana kallonta baice komai ba, da kyar ta ƙaƙalo mganar tace "emm dan Allah wane yace a kawo min wnn...?", yace "daga restaurant ne..", tace "Amm shi ina wnda yace a kawo..?", yace "sorry maam but i don't know aikina kawai shine delivery..", wani irin saki guiwarta tayi tace "Okay" da haka ta rufe ƙofarta, ko buɗe abincin ba tayi ba ta ajiyesa kan mini fridge dake ɗakin, saida tayi sallahr la'asar snn ta ɗan ci abincin kaɗan, tin daga cin abinci sai ciwo kuma ya motsa, ta ringa murƙususu a kan carpet, gashi idan baizo ba toh fa cramps din bazai lafa ba, daga yazo mgana ta ƙare, da kyar ta samu ya lafa mata, ta jingina da jikin gado ta ɗora kanta a guiwa, after few minutes ta ɗago kanta ta kalli door, gani kake sharr sharr hawaye sun fara gudu a cheeks dinta wani na bin wani. ★Ruqayyah ce zaune a Nurse station ta zabga uban tagumi, yau tana shigowa hospital direct office dinsa taje taga baya nan, tin ranar Tuesday last week da tazo bata sake zuwa ba sbd bata jin daɗi, sai yau ne ta samu tazo wajen aikin, Nurse Jiddah ce ta iso station din, tapping Ruqayyah tayi tace "Rukky yada zabga tagumi haka..?", Ruqayyah exhale heavily bayan ta fito daga duniyar da ta lula, Nurse Jidda ta zaune still tana kallon Ruqayyah tace "what wrong friendy you look dull..?", Ruqayyah tayi ajiyar zuciya ba tace komai ba kawai kallon Nurse Jiddah take, Nurse Jiddah tace "Okay idan bazaki gayamin ba shiknn amma dai karki sakama kanki damuwa, naga duk ba kya cikin walwala ƴan kwanakin nan...", Ruqayyah ta dafe goshinta kafin tace "Jiddah", Nurse Jiddah tace "na'am", Ruqayyah tace "yau ke ce ku ka shekara sama da biyu da saurayinki kuna soyayya har an saka muku ranar aure, toh a ranar auren sai wani abu ya tasowa shi saurayin naki wcca a dole sai an fasa aurenku a ranar, sai ya turo miki da message ya baki haƙuri yace ki jirasa yana nan dawowa gareki, dan Allah Jiddah wani hukuncin zaki yanke..", Nurse Jiddah dake kallon Ruqayyah ta saki baki kafin ta tafe hannaye tace "chaɓɗi jam..", Ruqayyah ta gyara zama tace "wani mataki zaki ɗauka...?", Nurse Jiddah tace "toh kamar yadda na bar nonon uwata haka zan barka wllh tllh, nida kai saidai hange daga nesa..", Ruqayyah ta katseta da faɗin "haba Jidda akwai fa soyayyah mai ƙarfi a tsakaninku kun fahimci juna sosai snn ya baki haƙuri fa..", Jiddah ta taɓe baki tace "meye kuma haƙuri, aini bbu wani haƙuri da zaka bani na haƙura don ka gama tozarta ni duniya da lahira, ranar ɗaurin auren mu ka tsallake ka tafi ka barni chab..", Ruqayyah ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Nurse Jiddah, gaba ɗaya karsashinta ya zagwanye gami da tsiyayewa ta guiwarta, tace "toh naji, bayan wani lokaci sai ya dawo daga inda ya tafi, yazo har inda kike ya baki haƙuri bayan wnda ya ringa turo miki ta waya..", wani murmushin rainin hankali Nurse Jiddah tayi tace "hmm Rukky knn, ai na gaya miki kamar yadda na bar nonon uwata haka na barka, kuma soyayyarka wllh na riga nayi fatali da ita akan kwalta..", Ruqayyah tace "nidae idan nice zan haƙura.." Nurse Jiddah tace "sbd kin wurgar da zuciyarki kare ya lashe ko..?", Ruqayyah ta haɗe gira tace "let me land mna malama..", Nurse Jiddah tace "Ohk", Ruqayyah tace "zan haƙura sbd fahimtar da na maka da kuma girman soyayyar dake tsakaninmu..", Nurse Jiddah ta miƙe tana kallon agogon hannunta tace "haka fa... Rukky wnn tmbyar naki is meaningless.. kuma in gaya miki duk wnda zaki tambaya irin amsar dana baki zai bayar.. kinga tafiyata zan duba ward C" tana gama faɗin haka ta bar station din. Ruqayyah ta ciro wayarta dake ringing daga pocket, da sauri tayi picking ganin Momy ce ke kiran, bayan sun gaisa Momy tace "kina jina..?", Ruqayyah da zuciyarta ke racing tace "Eh", Momy tace "toh ki taho gida yau..", Ruqayyah tace "toh", da haka Momy ta katse kiran. bayan Ruqayyah ta gama dutyn ta ta wuce gidan Haj Safiyya, kayanta kawai ta ɗeba ta yiwa mutan gidan sallama ta tafi. tana isa gidansu haka nan saddan taji zuciyarta na bugawa, shahada tayi ta murɗa ƙofar palour ta shiga, tayi sallama a hankali kafin ta shiga, Momy dake zaune palour ta amsa ba tare da ta dubeta ba, Ruqayyah ta ƙarasa cikin palourn ta duƙa ta gaida mahaifiyarta, Momy ta amsa mata a fixge sai kuma ta tashi ta bar palourn, Ruqayyah ta saukar da kanta kafin ta wuce room dinta, wanka ta shiga bayan ta fito ta tarar da missed call from Kulsoom, saida ta shirya snn tabi bayan kiran, kiran na shiga Kulsoom ta ɗaga tace "ina kika shiga sai kira nake..?", Ruqayyah tace "i was taking my bath at that time..", Kulsoom tace "Okay... sai yau Momy ta gayamin kwaɓar da kika tafka.. wai ke wace irin dabba ce da baki san gabanki da bayanki ba bare kisan inda kika dosa, wai sama kike cizo ne ko kuma kin fara tsince tsince a bola bamu sani ba, shi mahaifin naki kika kai ƙara sbd yana ƙoƙarin saita miki rayuwa, banza kawai wcca bata san inda yake mata ciwo ba, toh ai sai a barki da maganar auren tinda daman ynxu ke kin zama tsohuwar guzuma, yo to tsohuwar guzuma mana shekara ashirin da shida kin ƙi auruwa kuma duk ke kika ja ma kanki don Allah ya baki dama kikasa ƙafa kikay fatali da ita... kuma ƙaryar da kika shirgawa Momy akan mganar Dr marmaza kije ki sanar da ita da bakin ki cewa ƙarya kika giggila mata idan ba haka wllh saina tayar miki da mummunan bomb kin ji na gaya miki..", Ruqayyah ta fara girgiza kai tace "Sister wllh bazan iya gaya mata ba, bazan iya ce mata ƙarya na mata akan cewa babu wani sasantawa da mukay da Dr", Kulsoom ta juya hannu tace "oho can ta matse miki a matsematsin matsalarki, ko ki faɗa da bakinki ko na bunka miki bomb nonsense.." tana gama faɗin haka ƙitt ta kashe wayarta, Ruqayyah ta ringa kallon wayarta da idanunta kamar zasu faɗo, tana ɗaga kanta sukay ido huɗu da Momy wacca take tsaye bakin ƙofa tana kallonta da wani irin expression, darammm zuciyar Ruqayyah ta buga da ƙarfi, tini lips dinta suka fara zikiri tana ƙif ƙif da ido, juyawa Momy tayi ta bar dakin without saying anything. ★Hajar ta ɗaga kanta sakamakon murɗa door handle da akay, ta zubawa ƙofar lulu eyes dinta da suka haura, yana shigowa tayi sauri ta miƙe tsaye duk da irin murɗawar da cikinta yayi, kallo ɗaya ya mata ya ɗauke kai yana taɓe baki yayi sallama ciki ciki, ba ta ko amsa ba sai wata shegiyar harara da ta shiga banka masa, shi ko baima san tana yi ba, Laptop bag dake hannunsa ya ajiye kan couch kafin shima ya zauna yana stretching kansa, ajiyar zuciya yayi ya fara massaging neck dinsa, Hajar ta koma ta zauna don tsayuwar na ƙoƙarin tayar mata da ciwo, after 10mins ya tashi ya buɗe closet, jakarsa ya zuge ya ɗauki black sweat pant da white shirt, bathroom ya shiga ya rufo ƙofar, Hajar na zaune inda take sai kace mage, bayan 15mins ya fito, yayi wanka kuma ya shirya a bathroom din kafin ya fito, sai a lokacin ya yiwa Hajar seconds look tin shigowarsa, yana kallonta yace "an kawo miki abinci..?", ta ɗan kallesa sai kuma ta haɗe rai ta juyar da kanta, ganin he start coming towards her tayi sauri ta gyaɗa kai tace "ai an kawo min fa..", yayi slight smirk murya ƙasan maƙoshi yace "Silly girl", Atm card da phone dinsa ya zura a pocket, Hajar na ganin ya saka takalmi ya nufi ƙofa zuciyarta ta buga, da wani irin zafi nama ta miƙe da gudu ta sha gabansa ta danne ƙofar da bayanta, da mamaki ya ringa kallonta, ta sha kunu tana turo baki, yace "ke.. get out of my Way", lips dinta na rawa tace "saidai mu fita tare... ni bana son zaman nan din, ka mayar dani gida", yace "anƙi ɗin...", cike da tsiwa tace "is that so.. to kwa kaima bbu inda zaka", smirk yayi yana auna ƙarfin halinta, ga ta dai wata ƴar tsugul a gabansa amma sai tsaurin ido, hannu ya kai zai matsar da ita, da sauri tace "haram.. karka taɓani.." tana karkaɗa ɗan yatsanta manuniya irin a'a din nan, kallon slim finger din nata yayi, tsaf zai karyasa idan bari ya riƙesa, girgiza kai yayi don baya son ya biye mata ya bar wajen, powering TV yayi ya zauna a kan couch yana latsa wayarsa, Hajar ta turo baki ta bar bakin ƙofar ta dawo ta zauna, har wani bouncing take wai ita ta hanasa fita, babu jimawa magrib tayi, Nurain ya tashi yana jan rigarsa, wuff mutuniyarku ta miƙe itama, gani tayi kawai ya shimfiɗa prayer mat ya kabbara sallah, hakan yasa taji relief ta koma ta zauna tana kallon Tv, ya idar da sallah ya gama addu'oinsa, yana ƙas ƙas da fingers ya tashi ya koma position dinsa ya zauna, a hankali Hajar ta miƙe tana satar kallonsa, saɗaf saɗaf take tafiya har ta isa ƙofar toilet wai ita a nata tunanin bai lura da ita ba ashe ba tasan yana kallon duk wasu moves dinta ta wutsiyar ido ba, da sanɗa ta shiga toilet din ta rufe ƙofa a hankali, ko second biyu bai ƙara ba ya tashi ya bar room din, bashi ya dawo ba sai takwas da rabi, ya ajiye ledar abincin dinner da ya taho mata dashi, Tv ma take kallo abinta don haka ko ma ƴar hararar ta na kula ba tayi masa ba, yana kallonta yace "hey.. ga dinner dinki..", tace "na ƙoshi", ya ringa kallonta kafin yace "ur cup of coffee", bathroom ya shiga ya canza kayan jikinsa zuwa Pajamas, bayan ya fito ne ya fara ƙoƙarin haɗa sahibin nasa, ruwan zafi ya jona a kettle dake kusa da fridge, a jakarsa ya ɗakko mug da spoon, ya shiga toilet ya wanko mug da spoon din, da white coffee powder da ya siyo da ita yayi amfani ya walwala sahibin, da cup din a hannunsa ya rage wutar ɗakin yabar dim, ya zauna kan couch ya kunna Laptop, Hajar dai har ta ɓingire nan kan carpet amma kuma ba bacci take ba, operating system din yake at same time yana sipping coffee, kallon inda take kwance yayi, kawai ya ajiye mug din hannunsa ya tashi ya isa inda take, ya duƙa yayi tapping dinta, ta buɗe idonta tana zarosu waje don ynxu baccin ya fara figarta, bed ya nuna mata yace "koma can ki kwanta..", ta buɗe baki zatay magana, da sauri ya ɗora yatsansa akan lips dinsa yace "shhhh do what i said ko kuma na fanshe duk rashin kunyar da kikay min", ai kam ba musu ta tashi tana turo baki ta hau gadon ta kwanta daga gefe, pillow da ƙaramin duvet da ya kwanta jiya ya ɗauka ya koma kan couch ya cigaba da abinda yake, har 11 bai kwanta ba yanata danna Laptop. Hajar tayi wani juyi mai kauri sbd azabar cramps, ba ta san lokacin da ta sakko daga kan gadon ba ta fara murƙususu tace "wayyo zan mutu cikina" sai kuma ta fashe da kuka, ture laptop din yayi daga gabansa, ya tashi ya kunna hasken ɗakin sosai, da sauri ya ƙaraso inda take durƙushe ya sunkuya yana kallonta yace "mene ne..?", ta yarfe hannu tana cigaba da kuka tace "wayyo Allah na zan mutu...", haɗe thick eyebrows dinsa yayi ya ɗan ɗaga murya yace "am asking mene ne..?", ganin yadda ta dafe lower abdomen dinta ya fahimci problem din daga ciki ne, ya ɗaga ƴar rigarta sai kawai ta ji soft palm dinsa a bare tummy dinta, tsabar shock da ta shiga ji kake ɗiff ta shanye kukan da take......✍️ Assalamu alaikum beautiful fans 🥰 zan dakata da posting cause I will be having exams insha Allah, please i need your prayers.... 🙏 💛 HAJAR 💛 {63..} Duk da irin azabar pain din da take ji hakan bai hanata firgita da taji hannunsa a tummy dinta ba, she was very shocked and frightened, ta ja baya tana zaro ido tace "ni ka dena taɓani dan Allah babu kyau" sai kuma ta yarfe hannu ta cigaba da kuka a hankali, a takaice ya kalleta yace "then tell me, me yake damunki..?", ba tace masa uffan ba ta cigaba da murƙususun da take, ya ringa kallonta trying to figure out what her problem is, after yayi realizing matsalar a hankali yace "is it cramps..?", wani irin turo baki tayi ta juyar da fuskarta, hakan da tayi yasa ya gasgata hasashensa, ya tashi ya isa gaban closet ya buɗe ya ɗauki kananan kaya daga bag dinsa, bathroom ya shiga ya cire Pajamas ya saka ƙananun kayan, ya fito ya zura atm card a pocket, wayarsa ya ɗauka yana duba lokaci yaga sha ɗaya da rabi, door ya nufa ya buɗe lock kafin ya murɗa handle, har zai fita sai kuma ya juyo yana kallonta, har lokacin tana durƙushe amma kuma ta dena yarfe hannu da kuka alamar dai ya lafa mata, a hankali ta ɗago kanta sukay ido huɗu, after few seconds of staring at each other tayi sauri ta saukar da idanunta ƙasa, Nurain ya ajiye numfashi yana jan rigarsa ya buɗe ƙofar ya fita, yadda ya fita ya barta haka take a durƙushe sbd zaman ya mata daɗi sosai taji relief, ta samu ta ɗan jinginar da kanta da jikin gado ta lumshe ido, kafin 12 Nurain ya shigo ɗakin da leda a hannunsa, rufe ƙofar yayi ya shiga ciki sosai, kallonta ya ringa yi har ya ƙarasa inda take, ya duƙa gabanta ya ajiye ledar da ya shigo da ita, peacefully take ajiye numfashi idonta a lumshe, ya ringa kallon innocent face ɗinta without blinking, a hankali ya kai dubansa kan small pink lips dinta wanda ya kware wajen tsiwa, tinda yake bai taɓa mata irin wnn kallon ba, sai kace wnda aka tsikara haka ya haɗe gira yace "hey..", ganin bata motsa ba ya kai hannu ya taɓa goshinta, ta buɗe idonta tana kallonsa gashi har lokacin bai cire hannunsa daga goshinta ba, ta muskuta baya tana turo baki gami da banka masa harara, yayi saurin dunƙule hannun da ya taɓa goshinta ya kawar da kansa yace "ki koma kan bed..", maƙe shoulder tayi don bazata iya tashi a gabansa ba don tana farkawa taji alamar abinda yake wahalar da ita for days yazo, ya haɗe gira yana kallonta yace "nace ki tashi daga nan ki koma bed malama...", saukar da kanta tayi tana turo baki ba tace komai ba, chaɓ saidai yayi abinda zai yi ita dai bazata tashi ba gsky, haka kurum ta tashi asirinta ya tonu, miƙewa yayi ya fara ƙoƙarin ɗagota, ta tsala masa wani uban ihu tace "ni dae ka barni a nan, ana dole ne...", ji tayi ya saketa sai kuma ya ɗauki ledar da ya ajiye ya matsar mata da ita gabanta ba tare da ya dubeta ba, wajen ya bari ya koma yayi zamansa kan couch ya cigaba da abinda yake jikin Laptop, after like 10mins ya ɗago kai ya kalli inda take ta saman couch din, zaune ya ganta a yadda ya barta don ko motsi ba tayi ba, ya taɓe baki yana girgiza kai, kashe laptop din yayi ya ajiye, ya tashi ya rage wutar ɗakin kafin ya koma kan couch din yayi kwanciyarsa, saida Hajar taga ya ɗan jima da kwanciya snn ta samu kwarin guiwar miƙewa tsaye, ta ɗan saci kallon couch din kafin ta sunkuya ta ɗauki ledar tana duba abinda yake ciki, wani daram zuciyarta ta buga ganin abinda ke ciki, sanitary pad ce pack uku manya manya, kawai sai taji dama ƙasa ta tsage ta shige, tafi minti biyu a tsaye da ledar a hannunta, a hankali ta fara tafiya cikin sanɗa ta wuce inda box dinta take, ta buɗe box din ta ɗauki abinda zata ɗauka ta rufe, a hankali ta wuce hanyar toilet, tana buɗe ƙofar bathroom taji tayi ƙara, ta zaro lulu eyes dinta sai kuma ta juya ta fakaici kallon couch, ba ta isa ta fahimci bacci yake ko ba bacci yake ba sbd wutar ɗakin ba tada haske, tana shiga bathroom din ya buɗe idonsa yana kallon ƙofar bathroom din, kwanciyarsa ya gyara ya lumshe idonsa, Hajar na gama abinda za tay a bathroom ta fito ɗaure da towel don ta wanke rigar da ta cire da jikinta, wata soft sleeping gown wacca ta tsaya mata iya guiwa ta saka, har ta kwanta kan carpet sai kuma ta tashi tana kallon bed, a hankali tace "uhmm bari na koma kan gadon kar azo ana taɓamin jiki a bati", ta tashi ta koma kan gadon ta kwanta ta rufe da duvet. Da aduba Nurain ya farka, ya tashi zaune yana stretching jikinsa tare da karanto addu'a, shi bai saba da kwanciya a kan couch ba, bathroom ya shiga ya ɗauro alwala ya fito, bayan ya idar da sallah ya shiga wanka tare da kayan da zai saka. tsaye yake bakin mirror yana combing hair dinsa bayan ya fito daga wanka, Hajar ta buɗe idonta, kallonsa ta ringa yi har ya gama combing hair din ya bar gaban mirrorn, wayarsa yayi plugging a charge kafin ya kunna kettle ya fara tafasa ruwa, few minutes ruwan ya tafasa ya haɗa white Coffee ya zauna yana sha a hankali, duk Hajar na ankare dashi, shi kam ko kallon gadon beyi ba harkarsa kawai yake, yana gama shan coffeen ya ɗauki wayarsa da jakar Laptop dinsa, agogon dake wrist dinsa ya kalla yaga bakwai da minti ashirin, Hajar na ganin ya nufi door ta wani hantsilo daga kan gado, da sauri ta sha gabansa ta sha kunu, from head to toe ya kalleta, yayi saurin kawar da kansa after looking at her fresh legs, twisting pink lips dinta tayi ba tare da ta dubesa ba tace "idan tafiya za kai nidae ka mayar dani gida, I don't like it here..", yace "is there anything da akay miki ko kuma akwai abinda kika rasa a nan din ne...?", ta turo baki ba tace komai ba, gani tayi ya koma cikin ɗakin ya buɗe closet, babu jimawa ya dawo inda take da waya a hannunsa ƴar shafal ƙirar Samsung edge, kunna wayar yayi tana gama booting ya shiga call log, yayi long pressing 1 a take wata number ta fito, dialing numbern yayi wayarsa dake pocket tayi ringing, yayi cutting call din yana kallonta yace "if you need anything sai kiyi yadda kika ga nayi ynxu ki kirani.." da haka ya miƙa mata wayar, ƙin amsa tayi ta ringa kallon hannunsa, ya tsuke piercing eyes dinsa yace "take malama...", sai a lokacin ta amsa tana ƙif ƙif da ido, still ya koma cikin ɗakin yayi powering TV kafin ya juya yana kallonta yace "ga kallo nan kiyi idan kinga dama, in kuma ba kya so sai ki zauna kiyi jugum kamar mai zaman makoki..", yana gama fadin haka ya nufi ƙofa ya buɗe ya fita, Hajar tabi ƙofar da kallon na wasu seconds din. bayan tayi wanka ta shirya tana zauna tana kallon tv din dole, ƙarfe 9 aka kawo mata breakfast, zama tayi ta fara ci bayan ta haɗa coffee kamar yadda taga yayi, wajen ƙarfe biyu tana kwance kan couch tana kallon wani american movie da ya ɗebe mata kewa, ta tashi zaune ta zame ƙasa ta dafe cikinta da ya murɗa, can dai bayan taji bazata iya coping ba ta tashi ta ɗauko wayar da ya bata wacca ta yasar akan mirror, ta kunna ta shiga call log ta danne 1, number na appearing tayi dialing, har ta gama ringing ta katse ba a ɗaga ba, ta sake dialing a karo na biyu. Nurain dake zaune a wani makeken conference hall tare da collegue dinsa da suka zo workshop din suma, ya dena kallon abinda aka haska musu a projector ya dubi wayarsa dake kusa da Laptop dinsa da take vibrate a karo na biyu, saida wayar ta katse snn ya tashi daga kan chair dinsa yayi excusing kansa ya ɗauki wayarsa ya nufi ƙofar fita daga conference hall din, a bakin ƙofar hall din ya tsaya ya shiga kiran numbern, Hajar ta kalli wayar hannunta jin tana ringing, har ta haƙura da taji ba a ɗaga ba, a hankali ta kai slim finger dinta tayi picking ta kara a kunne ba tace komai ba, silence ɗin seconds ne ya biyo baya kafin yace "what..?", shiru tayi masa taƙi mgana, ya ciro wayar daga kunnensa ya kalli screen dinta sai kuma ya mayar kunne yace "mene ne...?", tace "ni cikina ne yake min ciwo", jim yayi kafin yace "ohk.. na siya miki drug jiya sai ki sha..", juya lulu eyes dinta tayi tace "ni ban gansa ba..", yace "ohh ba kinyi amfani da abinda na kawo miki jiya at night ba.. so ki duba cikin ledar", Hajar tayi shiru tana tunani mene abinda ya kawo mata tayi amfani dashi, lokaci guda ta tuna ai kam ƙit ta kashe wayar tana turo baki, walking slowly ta isa gaban box din kayanta ta durƙusa ta buɗe, ledar da ta saka ciki ta buɗe ta fara ciro pack din sanitary pad din, a can ƙasa ta hango wata ledar tana buɗewa taga kwalin drug, ta ɓalli 2tablets ta sha da bottle water, ko 3mins ba tayi da sha ba ciwon ya sauka gaba ɗaya babu shi, ta koma ta zauna ta cigaba da watching movie din da take. ★Maama ta fito daga ɗakinta da wata fatattakakkiyar tabarma a hannunta wacca ta gama zarewa tass, inuwar dake gaban ɗakinta ta samu ta shimfiɗa tabarmar ta zauna, Nabilah dake zaune tsakar gida tana tankaɗe tace "Maama wace miyar za a kaɗa kuka ko kuɓewa..?", Maama ta juya hannu tace "duk wacca kika kaɗa..", Nabilah tace "bari na kaɗa kuɓewa kawai don Baba yafi sonta...", Maama dake susar kai ba ji ba gani ta dena susar tace "kuka zaki kaɗamin bana son wata kuɓewar banza kayan zawayi..", Nabilah tace "amma Baba yafi son kuɓewa kuma kinga baya jin daɗi...", Maama ta ƙunduma mata wani ashar harda daƙuwa tace "uban da ya haifeki ya hau fel waya ya diro, ni zaki yiwa tsarin banza, ince baya gidan tin safe ya fita da wani kike cewa baya jin dadi, wnda baya jin dadi ne zai fice tin safe..", Nabilah ba ta sake cewa komai ba ta cigaba da tankaɗenta, Sa'adatu ce ta fito daga ɗaki sai sharɓa uban gumi take, ta zauna kusa da Maama tana sharce zufa tace "kai ɗakin nan akwai zafin bala'i da masifa sai kace gidan burodi wllh..", Maama tace "uhmm tsakar gidan ma ba dama, idan iska ta kaɗo sai ta gama baɗaɗo zafin rana take zuwa sai kiji kamar daga jahannama ta huro", Sa'adatu tayi tsaki tace "shiyasa na tsani zaman gidan nan, zafi da kuɗin cizo ma kawai sun ishi bawa..", Nabilah ta ajiye rariyar hannunta ta juyo tana kallon Sa'adatu sai kuma ta taɓe baki tace "ya za kiyi tinda a nan Allah ya ajiye ki..", Sa'adatu ta hura hanci tace "Maama ki mata mgana kinga dai ban saka da ita ba ko", Maama tace "bari Nabilah..", Nabilah ta gallawa Sa'adatu harara ta juya ta cigaba da aikinta, Maimuna ce ta fito daga ɗaki fuskarta duk kumburin bacci da kwandon soso da sabulu a hannunta, ta wage baki tana zabga hamma babu a'uzubillahi bare ta rufe baki, bokiti ta ɗauka ta ɗebi ruwa ta shiga toilet. tin daga soro Balaraba ta shiga zabga sallama, ayam ta shigo gidan tana kiran sunan Maama, Maama ta turɓune fuska ta juyar da kai, Balaraba ta ƙarasa shigowa tana kallon Maama tace "haba ƙawalli romon jaɓa babu faɗa me ya kawo gaba Rabi", Maama ta haɗe rai tace "lfy zaki shigo gidan matan aure da hayagaga..", Balaraba ta wage baki tace "nidae zuwa nayi biko naga kwana biyu kin ɗauke ƙafa sam bana jin ɗuriyarki..", Nabilah ce kawai ta gaida Balaraba Sa'adatu kam ko kallon arziƙi ba ta mata ba tana danna wayarta, wayar nan da za a buɗe maka gallery ka shiga video to tsaf mutum zai iya makancewa don babu komai a ciki sai videos din batsa da shashanci, Balaraba ta zauna kan tabarma tace "kai wnn ma duk ta ruɓe cin jiki za tay..", Maama tace "da sai ki taho da wacca zaki zauna ai..", Balaraba tace "kyaji dashi dai.. idan da kinsan da mai nazo miki da tini kin fara nan nan dani wllh tllh..", Maama ta taɓe baki tace "haba Balaraba ke har akwai wani abin arziki da za ki zo min dashi har nayi rawar ƙafa nayi nan nan dake.. hmm wane dare ne jemage bai gani ba ai sai na mutuwarsa..", Balaraba tace "da dai kin taso mun shiga daga ciki..", Maama tace "mu shiga daga ciki a ina... dawa za a shiga daga cikin..?", Balaraba ta fakaici kallon Nabilah da Sa'adatu sai kuma ta marairaice fuska tace "haba Rabi ai kya bari kiji abinda nazo miki dashi tukunna", Maama ta tashi tana gyara haɓar zaninta ta shiga ɗaki Balaraba tabi bayanta. Maimuna ta fito daga wanka ta tsugunna gaban rariya tana goge kaushi, Nabilah da ta gama ruɗe tace "Maimuna ki ɗan temaka kiyi wanke wanke babu ko kwanunkan da za a ci abinci da daddare", Maimuna ta girgiza kai tace "chabɗi tin da baki gayamin ba saida nayi wanka..", Nabilah tace "knn dai baza kiyi ba..?", Maimuna tace "kwarai..", Nabilah tayi kwafa ta saka hijab ta fita zata siyo daddawa, Maimuna ta ƙarasa goge ƙafarta ta tashi zata shiga ɗaki, juyawa tayi tana kallon Sabrah da ta shigo gidan yanxu ta dawo daga islamiyya, Maimuna tace "ke zo nan..", a hankali Sabrah ta isa kusa da Maimuna tace "gani", Maimuna tace "ga can kayan wanke wanke wuce ki zauna kiyi", Sabrah ta kalli kayan wanke wanken tace "toh bari na cire kayan makaranta Umma tace ina dawowa na ringa cirewa..", Maimuna ta buɗe baki ta lailayo wata ashariya ta lafta mata tace "zaki wuce ko saina sumar dake shegiya..", Sabrah taja da baya tana ƙunƙuni tace "Umma tace na dena zama da uniform fa..", Sa'adatu dake kallonsu tace "kika tsaya wnn figigiyar yarinyar tana mayar miki da martani, shegiyar yayarta ma haka ta barmu bare wnn ƴar tsituwar, ci uwarta kawai..", babu tausayi Maimuna ta maƙure yarinya ta shiga gaura mata mari, Sabrah ta fasa wata gigitacciyar ƙara sbd har taurari take gani, cikin bacci Umma taji ihun ƴar autarta, ita bata ma san lokacin da baccin ya ɗebeta ba, da sauri ta fito tsakar gida, har lokacin Maimuna ba ta dena wankawa Sabrah mari ba, Maimuna na ɗago kai sukay ido huɗu da Naseer dake tsaye ya harɗe hannu yana kallonta, da sauri ta saki Sabrah ta kwasa a guje zata shiga ɗakin Maama, da sauri Umma da zuciyarta ke tafasa hundred degree Celsius tasa mata ƙafa. Maimuna saida tayi nadamar marin Sabrah da tayi, dan da Naseer ya ringa haskata da maruka saida ya fasa mata baki, kunnenta kam gaba ɗaya signal dinsa ta ɗauke, da kyar Maama ta kwaci Maimuna daga hannunsa, daman yanada cikinta, Umma dai tinda ta janye ƴar autarta ta wuce ɗaki da ita. ★Tini Hajar ta fara sabawa da zaman hotel room din, yau kwanansu huɗu kenan, tin ranar da ya bata waya kullum saita kira Ummanta sun gaisa, da daddare da misalin ƙarfe tara na dare, Hajar na zaune kan carpet tana kallon wani film na comedy mai suna home alone, Nurain na zaune kan couch da pajamas a jikinsa yana operating laptop, wayarsa ya ɗauka ya shiga lalubo numbern wani friend dinsa da sukay karatu tare a India, cikin numbers da yayi saving akan email ya samo numbern abokin nasa da yayi saving da Dr Hammad, dialing numbern yayi ai kam tana fara ringing akay picking, Nurain na sallama Hammad ya ganesa with his voice, bayan sun gaisa Hammad yace "how are you doing yasu Mami...?", Nurain yace "fyn alhmdllh..?", Hammad yace "to masha Allah sai yau aka tina dani kenan", Nurain ya shafa sumar kansa yace "Ai gani ma a garin ku", Hammad yace "really are you in town..?", Nurain yace "yeah, since Sunday ma ina..." shiru yayi jin wata dariya da Hajar ta sheƙe da ita, ya ringa kallonta tana dariyarta her eyes fixed on tv, ta ɗan juyo ta kallesa har lokacin annurin fuskarta beyi fading ba, ganin sunyi ido huɗu tayi saurin tsuke fuska ta juya ta cigaba da kallonta, jin shiru Hammad yace "hello are you there..?", Nurain yace "yeah" suka cigaba da magana, wani abin dariyar aka sake yi a film din, Hajar couldn't help it but to laugh hard, ta toshe bakinta da palm dinta tana ƙoƙarin tsaida dariyar, ta gefen ido ta fakaici kallonsa ai kam taga ashe kallonta kawai yake, ta turo baki tayi twinkling lulu eyes dinta, tashi yayi ya ɗauki remote din TV ya danna off ya koma ya zauna ya ajiye remote din a side dinsa, Hajar ta wani haɗe gira ganin ya kashe mata kallo, juyowa tayi tana kallonsa taga wayarsa ma yake ko a jikinsa, haka kurum don baƙin hali shine zai kashe mata jin dadinta shi kuma ya koma gefe yana wayarsa, wani irin turo baki tayi ganin yayi murmushi kawai zuciyarta ta bata ai da girlfriend dinsa yake waya, miƙewa tayi tana kallon remote din da ya ajiye gefensa, tafiya ta fara yi kamar zata wuce still tana kallon remote din, da sauri ta kai hannu zata wafci remote din, kafin ta kai ga ɗauka shi ya rigata ɗaukewa ya ɗaga sama, ai kam taci tuntuɓe da ƙafarsa gaba dayanta ta faɗa kansa, a gigice ta fara ƙoƙarin ɗagasa ta wani zaro ido, bai bata damar hakan ba yayi saurin dafe bayanta ta sake faɗawa ƙirjinsa, a hankali yace "i will call you back" da haka ya cire wayar a kunnensa ya ajiye gefe, mutsu mutsu kawai Hajar take alan a dole tana so ta sauka a jikinsa, daman da hannu ɗaya kawai ya riƙeta, jin yadda take motsi kawai ya zagayeta da ɗayan hannun, wani irin bugu zuciyarta ta shiga yi hancinta ya cika da ƙamshinsa gashi har saukar numfashinsa tana ji.....✍️ 💛 HAJAR 💛 {64..} Sosai yayi wrapping dinta a ƙirjinsa har saida ta dena mutsu mutsun da take, tayi lamo zuciyarta na tsananta bugu, gaba ɗaya ta gigice ta rasa sukuni, after a while taji ya sassauta riƙon da ya mata, ai kam tayi wuff ta fincike kanta ta ɗagasa, ta koma da baya tana jan fingers dinta murya ƙasa ƙasa tace "wllh bbu kyau haram ne..", tsuke piercing eyes dinsa yayi yana kallonta yace "mene babu kyau..?", ba tasan lokacin da ta galla masa wata shegiyar harara ba tace "me yasa zaka taɓani ai kasan haram ne..", ya haɗe thick eyebrows dinsa yace "Nah.. ohh naga ke kika faɗo kaina young lady or is it a coincidence", ta zuba masa lulu eyes dinta sai kuma ta haɗe rai, yayi slight smirk ya nuna remote din dake gefensa yace "you can take it..", kallon remote din tayi ta wuce ta bar wajen, juyawa yayi yana kallonta ganin ta nufi gado yace "hey ga remote din fa ko kin fasa kallon ne..", banza tayi dashi ta hau gado abinta ta rufa da duvet tana turo baki, taɓe baki yayi ya juya murya ƙasan maƙoshi yace "Silly girl..." ya ɗauki wayarsa ya kira Hammad, tinda Hajar ta kwanta take shaƙar ƙamshinsa da take jinsa a kayanta, ta ringa juye juye tana yamutsa fuska, lokaci guda ta miƙe zaune ta ja siririn hancinta, ko dai ta cire kayan ne ta huta, komawa tayi ta kwanta kawai bata dade ba bacci me nauyi ya ɗauketa wnda hakan yanada nasaba da ni'imtaccen ƙamshin da ta ringa shaƙa ita bata sani ba. da asuba ta farka, a hankali ta fara buɗe idonta jin wata qira'a mai daɗi tana shiga kunnenta, ta fara surveying ɗakin da ido, zaune ta gansa kan prayer mat sautin qira'ar yana tasowa daga wajensa alamar dai shi yake karatun, tarwal Hajar ta buɗe idonta tana kallonsa, a zuciyarta kam mamaki take ai tasha boko kawai ya saka a gaba, ita tinda take ma ta taɓa jin qira'a mai daɗin wnn, gashi kuma ba taga Alqur'ani a gabansa ba alamar da ka yake yi, ta yamutsa fuska a ranta tace ba wani nan ya sayyadi ya fisa, ta lumshe idonta tana tunanin ya sayyadinta wnda ɗaiɗaikun ranaku ne bata tinawa dashi. tashi Nurain yayi bayan ya hattama iya izifin da zaiyi, ya kunna hasken ɗakin sosai, ya ɗan fakaice kallon gado, da sauri ya ɗauke kansa ya wuce ya buɗe closet ya ɗauki kayan da zai saka ya shiga wanka, after 15 minutes ya fito already ya saka kaya a bathroom yana goge cikakkiyar sumarsa da small towel, Hajar da ta buɗe idonta tin bayan shigarsa bathroom tayi sauri ta rufe ganin ya fito, saida yasha white coffee snn ya ɗau jakar Laptop dinsa ya fita wajen bakwai da rabi, yana fita Hajar ta diro daga kan gado, da sauri ta shige toilet tayi wanka, tana fitowa ta kimtsa kanta tsaf don har combing hair dinta tayi, ƙarfe takwas da rabi aka kawo mata breakfast, kaɗan taci abincin don bata jin yunwa sbd tasha coffee, wayar da ya bata ta ɗauko tayi dialing numbern Umma, tana fara ringing Umma ta ɗaga, bayan sun gaisa Hajar tace "Umma yasu Baba da Sabra da Yaya...?", Umma tace "kowa lfy lou alhmdllh, kema ai lfyr kike ko..?", Hajar ta gyaɗa kai tace "uhmm", Umma tace "toh Alhmdllh... Allah yayi albarka sai anjima..", Hajar tace "toh sai anjima..", Umma ta katse kiran. har ƙarfe sha biyu Hajar na zaune kan couch tana kallon tv, daga wnn channel din zuwa wata channel din, ita zaman waje ɗayan nan ya fara isarta fa, ba chass ba Ass saidai kawai taci abinci tayi wanka sai kwanciya, ta dubi agogo taga ƙarfe biyu saura, ita lokacin ma baya mata sauri yanzu, kallon ƙofa tayi jin an murɗa handle, a hankali ya turo ƙofar ya shigo, ido huɗu sukay, da sauri Hajar ta ɗauke kanta, yayi sallama ciki ciki itama ta amsa masa ciki ciki, tini room din ya kaure da pure men scent dinsa, da yake yaune last day na symposium din shiyasa suka tashi da wuri, daman na kwana biyar ne so a yau da take Friday suka gama, tana ganin ya shiga bathroom ta tashi daga kan couch ta ɗauki ledar lunch da aka kawo mata ta koma bakin gado ta zauna ta fara ci, Nurain ya fito daga bathroom bayan yayi refreshing kansa, a fakaice Hajar ta dubesa, lokaci guda ta tsura masa ido tana kallon farar Shirt ƙal dake jikinsa, brain ɗinta ce ta amsa ta fara sinking, kallonsa take babu ƙiftawa tana so ta tina wani abu da yake mata yawo a brain, kamar fa ba lokacin da ya kusan bige yaron nan ta fara ganinsa ba, tabbas da ta ga wnn farar Shirt din tana ƙoƙarin tina wani abu, don ita gaba ɗaya ta manta encounter dinsu ta farko ta biyu da ta uku saita huɗu kawai take tinawa, ya juya ya ɗan kalleta, ganin kallon da take masa ya tsuke ido, wayarsa da tayi vibrate ya ɗauka yaga Hammad ne ke kiransa, bai ɗaga kiran ba ya sake kallon Hajar da har lokacin bata ɗauke idonta daga kansa ba, ya kalli Shirt dinsa wacca ya lura ita take kallo, jan Shirt din yayi kafin ya haɗe gira yace "hey what are you starting at..?", ganin bata amsa ba kuma bata dena kallon nasa ba kawai ya fara tafiya towards her, twisting fingers dinsa yayi a daidai fuskarta wnda ya bada sautin ɗas ɗas, ai firgigit ta dawo daga duniyar da ta lula, haɗe gira tayi ganinsa daf ta ita, ta ajiye spoon din hannunta kan takeaway din abincin da take ci, Calmly yace "what are you starting at..?", ta juya idonta tace "is there anything to stare at..", ya ringa kallon pink lips dinta da take mgana ta wani cokalosu, ya buɗe baki zai mgna knn wayar hannunsa tayi vibrate, ya ɗauke idonsa daga kallon lips dinta ya koma da baya, picking kiran yayi ya kara a kunne yace "ohh Hammad..", from the other side Hammad yace "are you coming..?", Nurain yace "wait ai nace ka turomin inda zamu hadu ko", Hammad yace "Oh c'mon gidana fa zaka zo Dr", Nurain ya sauke ajiyar zuciya yana shafa kansa yace "kawai mu hadu a wani Eatery or Coffee shop haka mna..", Hammad yace "No.. saidai ba ziyarar zaka kawomin ba..", Nurain yace "Alright you know i don't have the Address right...", Hammad yace "ohh i will send it to you right away", Nurain yace "better" da haka ya katse kiran yana sauke ajiyar zuciya, bbu jimawa message din Hammad da ya turo masa da address ya shigo, ya zauna kan couch bayan few seconds ya kwanta ya miƙar da legs dinsa, da hannunsa yayi pillow lokaci guda bacci ya ɗebesa, Hajar na gama cin abincin ta rufe ragowar, itama baccin ne ya tafi da ita daga ɗan miƙewa. Nurain ya farka wajen ƙarfe huɗu, stretching jikinsa yayi bayan ya miƙe zaune, da sauri ya wuce toilet ya dauro alwala gudun lokaci ya ƙure masa, yana idar da sallah ya juya yana kallon Hajar da ke bacci har lokacin bata farka ba, ya sauya kayan jikinsa daga ƙanana zuwa manya, text din da Hammad ya turo masa ya buɗe yana karantawa, shi kam dai yaso su haɗu a wani wajen ba gida ba, dama dai gidansu ne bazai damu ba, wayarsa ya saka a front pocket yace "damn it", ya sake kallon position din Hajar, duƙawa yayi gabanta yayi tapping dinta a hankali, ta buɗe sleepy eyes dinta, da sauri ta miƙe tana murza ido taja da baya, miƙewa yayi yace "hey ki tashi ki shirya.. idan kuma anan zan barki shknn", yana gama faɗin haka ya nufi door ya fita, reception ya wuce ya zauna, after 30mins ya dawo ɗakin ya tarar har ta gama shiryawa, black Abaya wcca bata taɓa sawa ba ta saka, tayi rolling kanta da mayafin Abayan, tanata faman zuge box dinta wacca ta gama shirya kayanta tsaf, tinda taji yace tafiya za suyi taji wani sanyi ya saukar mata don har ga Allah ta gaji da zaman nan din, yana kallon abinda take yace "are you done..?", ta gyaɗa kai tace "Eh" lokacin da ta miƙe tana gyara rolling din da tayi, door ya nufa yace "muje", box dinta ta fara ja tabi bayansa, juyowa yayi yana kallonta, ta saukar da kanta tace "ka manta bag dinka fa..", yace "kema ke kika sa kanki daukar wnn, lokacin da muka zo mu muka dauki kayan", girgiza kai tayi ba tace komai ba, ya buɗe ƙofa ya fita, sakin box din tayi tabi bayansa, bayan ta fito daga room din ya mayar da ƙofar ya rufe, wucewa yayi ya tsaya gaban Elevator tabi bayansa suka shiga tare, suna sauka ƙasa yana gaba tana biye dashi, ganin ya zauna a kujera bayan sun isa reception tayi turus tana kallonsa, shikam wayarsa ya ciro yana duba bolt da ya kira, can kujerar dake nesa dashi ta samu ta zauna, tinda Hajar ta zauna wani gentleman dake zaune opposite dinta ya zuba mata ido, ita kam kanta na ƙasa tana wasa da fingers dinta, Nurain ya ɗago kansa ya kalli mutumin, sosai ya lura da irin kallon da yake yiwa Hajar babu ko ƙiftawa, Nurain ya haɗe gira ya tashi ya koma kujerar dake kusa data ta, ɗago kanta tayi ta kallesa jin scent dinsa, yana latsa wayarsa ba tare da ya dubeta ba ya rage murya yace "baki taho da hijab ba..?", tace "ai baka sako hijab ba da ka haɗa kayan..", ɗago kansa yayi ya ringa kallonta without blinking, ta fakaici kallonsa ganin kallon da yake mata tace "ka dena kallona dan Allah..", yace "ohh really ke da wane idon kika san ina kallonki", tashi tayi ta bar masa kujerar ta koma inda ya taso a hankali tace "ai kallon batin ya isa haka", Nurain ya kalli mutumin a fakaice, gani yayi ya juya akalar kallon nasa zuwa inda ta koma, wani irin murtuke fuska yayi har saida thick eyebrows dinsa suka haɗe, kamar wnda aka fusata haka ya miƙe, babu wani jinkiri ya isa inda ta koma ya figi hannunta ya fara janta suka fita daga reception din, suna fita waje ta fixge hannunta tace "meye haka..", ta fara goge hannun a jikin kayanta, wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke ya shafa fuskarsa da palm dinsa, juyowa yayi yana kallonta from head to toe, wani irin haske ta ƙara barin ma da ta saka black din Abaya sai hasken ya ƙaru, sajen forehead dinta ya kwanta luf luf sai kace balarabiya, ya kalli ƙafarta that is so fair har wani ja take sbd haske ga nails dinta pink, da wata iriyar murya yace "wai ke ko socks baki ɗakko ba..", da mamaki ta kallesa tace "toh wai ni na haɗa kayan ne", idan ba ƙafa da hannu da fuska ba babu inda yake bayyane a jikinta, dressing dinta was more than decent, yana duba wayarsa yaga bolt din da ya kira tazo, a front seat Nurain ya zauna Hajar kuma back seat, da haka suka bar harabar hotel din, Hajar ta ringa kallon window wondering a wani gari take, wata unguwar masu hannu da shuni suka shiga, ƙerarrun gidajen dake unguwar sai kace a ƙasar waje, gaban wani danƙareren gida Nurain yasa mai bolt din yayi parking kafin ya fara kallon wayarsa yana duba house numbern na gidan dan ya tabbatar shi din ne, bayan ya tabbatar yayi dialing numbern Hammad, tana shiga Hammad ya ɗauka, Nurain yace "am at the gate..", Hammad yace "Ohk ka shiga mana Dr", Nurain yace "Amm ai bolt ne..", Hammad yace "Okay bari na yiwa gateman mgana kawai ya shigo ciki da kai", Nurain yace "Alright", babu jimawa aka zuge tafkeken gate din gidan, suna shiga fakeken compound din gidan drivern bolt ya parker motar, Nurain ya yiwa mai bolt transfer din kuɗinsa bayan ya masa doubling, back seat ya buɗe yana kallon Hajar da tayi wani lakur yace "come down", a hankali ta zuro ƙafafuwanta ta fito, daidai lokacin Hammad ya fito daga entrance din gidan, da sauri ya ƙaraso inda Nurain yake sukay hugging juna lightly, sai kuma sukay musabaha bakin Hammad har ear yace "i swear i pick a flag..", Hajar dai kawai kallon Hammad take don bai mata kama da ƴan Nigeria ba, kana ganinsa kaga halfcast, Hammad ya kalli Hajar yace "beauty Noor..?", Nurain ya dubi Hajar ya girgiza kai yace "she is someone else", Hammad yace "ohh", da haka yayi leading dinsu zuwa katafaren palourn gidan, Hajar dai ta samu sofa ta zauna bayan shigarsu palourn, sake gaisawa sukay, Hammad yace "ai this is better, koni da naje kano ai har gida naje muka gaisa kuma na gaisa da Mami..", Nurain yace "ya wajen su Ummi...?", Hammad yace "Ummi taje Yamen", Nurain yace "Ohk", Hammad ya dubi Hajar dake zaune kan sofa yace "Hi.. good afternoon..", Hajar ta saukar da kanta tace "ina yini", yace "lfy lou, how are you doing...?", tace "fine alhmdllh", Hammad yace "good", sai kuma ya dubi Nurain dake satar kallon Hajar yace "bari na kira my Madam tazo ku gaisa" da haka ya tashi ya haura sama, bai jima ba ya sakko ya zauna a position dinsa suka cigaba da fira da Nurain, after few minutes da basu kai huɗu ba matar Hammad Maysha ta iso palourn, she's so beautiful brown skin girl, gaisawa sukay da Nurain snn Hajar, bayan nan Maysha ta tashi ta shiga kitchen ta lafto snacks da drinks tray guda ta kawo palourn ta ajiye, ta sake komawa kitchen ta kawo warmers din abinci, Maysha ganin Hajar bata taɓa komai da ta ajiye musu ba ta ɗebar mata tace tazo su shiga ciki taci, Nurain kam yasha drink sai semosa guda ɗaya, Hammad na kallon Nurain bayan Maysha ta wuce da Hajar ciki yace "Please who is this young lady Dr, is she your wife..?", Nurain ya ajiye glass goblet din lemo da yake sha yace "wife.. no she's not", Hammad yace "then", Nurain yace "yah how will i get marry ban gaya mka ba, kasan zan gaya maka koda bazaka zo ba, kaima lokacin aurenka ina India ai ka gayamin right", Hammad yace "Okay then who is she..", Nurain yace "someone" da haka ya dauki lemonsa yana sipping. sai bayan magrib suka bar gidan wnda da ƙyar Nurain ya yarda ya kai time ɗin, bayan sun dawo hotel sun shiga Elevator Hajar dake riƙe da ledar da Maysha ta bata tace "waini ban gane ba fa me muka dawo yi anan?..", a lokaci na farko da ya dubeta, kamar bazai amsa ba can yace "zama mna", ta wani zaro ido tace "what zama fa kace", ya ɗaga shoulder irin yess, da haka ya fita daga Elevator din don sunzo floor din room dinsu, Keycard ya ciro ya buɗe ƙofar room din ya juya yana kallonta yace "get in", ta maƙe shoulder tana ƙoƙarin danne hawayen da yake shirin zubo mata, kallon few seconds ya mata kafin ya shige ɗakin ya barta tsaye nan, Hajar ta goge hawayen da ya zubo mata da bayan hannu, ajiye ledar hannunta tayi a bakin ƙofar ta juya ta koma cikin Elevator, bayan kamar minti biyar Nurain dake zaune kan couch ya miƙe ganin bata shigo ba, door ya nufa yana zuwa yaga wayam, ya kalli ledar da ta ajiye nan bakin ƙofa, lokaci guda ya kalli dogon Aisle din shima yaga babu kowa, da sauri ya shiga Elevator ya sauka reception, saida ya fara ƙarewa reception din kallo nan ma yaga bata nan, har zai fita daga reception din sai kuma ya dawo ya tsaya gaban receptionist yace "amm excuse me", receptionist din yace "yes sir" Nurain yace "Please ba kaga wata young lady ta fita ba..", receptionist din yayi jim yana tunani, Nurain da hankalinsa ya fara tashi yace "she is in black", receptionist din yace "ohh i saw her going out few minutes ago", Nurain ya juya yana kallon ƙofar fita da mamaki, direct exist door ya nufa ya fita harabar hotel din dake da haske tarwal kamar rana, ya sauke numfashi yana shafa kansa yace "damn it", kawai kalle kalle yake a harabar hotel din ko zai ganta, can ya hangota tana tafiya a hankali har ta kai babban gate din barin hotel din, bai san lokacin da ya fara zabga wani sauri ba ya nufi gate, lokacin da ya isa gate din ita harta jima da fita, hangota yayi har tayi nisa da tafiyar da take gefen titi, wani irin mugun gudu motocin da suke wucewa suke, duk motar da tazo a guje take wucewa, haɗe gira yayi yabi bayanta da sauri, yana daf da zuwa kusa da ita with husky voice yace "Ke!! where are you going are you mad...?", lokaci ɗaya ta dakata da tafiyar ta juyo sukay ido huɗu, tattare ƙasan rigarta tayi ta juya ta kwasa a guje, Nurain ya zaro ido ganin uban gudun fanfalaƙin da take wnda tayi masa muguwar zarra, ai kam bashi da wani option da ya wuce ya bita, gudu take ba ji ba gani, ta waiwayo taga ai ya kusa kamota, ganin zai cimmata kawai tayi crossing road, a lokacin da wata shimfiɗeɗiyar mota ta kwararo with high speed, Nurain yaci wani mugun birki yana jin tamkar an kwaɗa masa guduma a ka, da wata iriyar murya mai diri ya kwala kiran sunanta "Hajar"......✍️ 💛 HAJAR 💛 {65..} Saura ƙiris motar ta kwasheta amma duk da haka saida ta gogeta, wata iriyar hantsilawa tayi ta faɗi ƙasan kwalta, ta dauje a duka guiwoyinta da tafin hannu, da sauri Nurain ya ƙaraso inda take, damtsenta ya riƙo ya ɗagata kamar ƴar kaza, ba karamin tashi hankalinsa yayi ba kuma har lokacin kansa bai dena sarawa ba, tin daga sama har ƙasa ya ringa kallonta fuskarsa a matuƙar murtuke, sakinta yayi kafin yasa bayan hannu ya falla mata mari, bata gama dawowa hayyacinta ba ya sake mangareta, saida Hajar taga stars tsabar gigicewa, ta fashe da matsanancin kuka a gigice tace "na shiga uku", wata tsawa da ya daka mata saida ta koma ta zube a ƙasa sbd yadda ƴan hanjinta suka juya, with stern voice yace "you must be mad, wawuya kawai..", a lokacin drivern motar da ya samu ya tsayar da motar far away from them ya ƙaraso inda suke da ɗan gudu gudu, kana ganinsa kasan ƙuruciya ke ɗebansa don bazai wuce 25yrs ba, duƙawa yayi gaban Hajar dake rusa kuka kamar ranta zai fita yace "am sorry", Nurain ya figi hannunta ya miƙar da ita, sosai ta firgita ta sake fashewa da kuka, young man din yace "should I take her to the hospital...?", a taƙaice Nurain yace "no need" da haka ya ja hannunta suka bar wajen tana rusa kuka, a haka yana figarta har suka koma cikin hotel din, direct elevator suka shiga bayan sun wuce reception, har lokacin Hajar bata dena kuka ba, suna isa room dinsu ya wani wancakalar da ita a kan carpet, da sauri da haɗe kanta da guiwarta da take jin tana mata zugi, ya zauna kan couch ya dafe kansa, ynxu idan da motar nan ta bigeta fa sai yadda Allah yayi, ya ɗago kansa ya kalleta zuciyarsa na ƙuna, slight hiss yayi ya tashi ya shiga bathroom yayo alwala, bayan yayi sallah after taking his bath ya saka pajamas, making coffee yayi ya zauna kan couch, ajiye mug din hannunsa yayi kafin ya kalli inda take, har lokacin kanta haɗe yake da guiwa tana shessheƙa a hankali, ya taɓe baki yace "ke!!", ko motsi ba tayi ba bare ta amsa, ya ɗan daga murya yace "ke!", ta ɗago jar fuskarta ba tare da ta dubesa ba, ya haɗe gira yace "tashi kije ki cire wnn black kayan sai kace a palace din sheɗanu", ba musu ta tashi tana jan ƙafa ta janyo box din kayanta, wata soft sleeping gown ta ɗauka ta shige bathroom zuciyarta tamkar za tay bindiga, yabi bayanta da kallo kafin ya ɗauki mug din coffee ya fara sipping wnda daman haɗasa yayi don ya rage masa takaici, ba ƙaramin ɓata masa rai Silly girl tayi ba, sai kace wacca kwai ya fashewa a ciki haka ta fito daga toilet din, a hankali ta zauna gefen gado after few minutes ta kwanta ta rufe da duvet, babu abinda take hangowa sai irin stars din da ta gani, Nurain na gama shanye coffee ya juya ya kalli gado, lokaci guda ya miƙe ya isa bakin gadon, kallonta ya ringa yi kafin ya zauna gefenta, Hajar ta rintse idonta don ba bacci take ba, duvet din da ta rufe ya yaye, bata motsa ba duk da hakan yazo mata unexpected, tin daga ƙafarta zuwa knees dinta da suke a bayyane ya ringa kallo, ya lura da bruises din dake guiwoyinta, a hankali ya kai dubansa kan hannayenta, bai ga ciwo a hannun ba, ya janyo hannun da ta danne yana dubasa shima, a palm yaga taji ciwo, in banda bugu bbu abinda zuciyarta take, me yasa yake taɓata wai, wani azabar tsoronsa take ji shiyasa taƙi motsi, ya ringa kallon fuskarta musamman ma soft cheeks dinta da ya hango zanen yatsunsa uku, wajen yayi jajur, shiyasa ya saka mata bayan hannu idan da front ya saka mata tsaf zai fitar mata da haƙori, ya kasa withstanding abinda ta aikata ne, the girl is so stubborn, ji tayi ya dafa forehead dinta sai kuma ya tuge mayafin da ta rufe gashinta, tini ta buɗe idonta ta miƙe zaune, tashin da tayi bai hanasa cigaba da duba jikinta da yake ba, hakan ne ma yasa ya fara ƙoƙarin ɗaga ƴar rigarta don ya duba inda rigar ta rufe, wata gigitacciyar ƙara ta fasa ta fara ture hannunsa, ganin ko gezau so yake fa ya ɗaga rigar nan sai ta fara kokawa, haɗe gira yayi ya rutsa hannayen nata da hannu ɗaya, ɗayan hannun kuma ya ɗage rigar yana ƙarewa fresh bodyn ta kallo, ƙoƙarin sauka ta fara daga kan gadon ya hanata don katamau ya riƙe ƴar farka, ai kam ta rushe da kuka jikinta har na rawa tace "wayyo Allahna na shiga uku, dan girman Allah ka dena taɓani, Ummata...", sakinta yayi bayan ya tabbatar bbu ciwo a jikin, da sauri taja rigar ta rufe jikinta tana zaro ido, tashi yayi ya shiga bathroom ya fito da kwalbar Dettol, kwalin tissue dake ajiye kan table ya dauka snn ya koma gefen gado ya zauna, Hajar ta muskuta baya tana turo baki, sam bata bari sun haɗa ido ba, haka nan ya goge mata bruises din da taji a hannu da knees da ruwan dettol, tinda ya zare mata ido ta tsaya bbu wani noƙe noƙe, ya mayar da kwalbar Dettol din bathroom ya fito ya rage hasken ɗakin ya hau couch ya kwanta, wajen ƙarfe ɗaya ya farka, zaune ya miƙe ya ringa massaging neck dinsa da ya riƙe, yafi minti biyar yana massaging neck din, ya juya yana kallon gado, can gefen gadon yaga Hajar tabar space sosai, ya murza sleepy eyes dinsa ya tashi ya koma kan gadon, ya kwanta a other side din gadon ya juya mata baya, da asuba Nurain ya farka yaga Hajar daf dashi sai kace yayi cuddling dinta, kanta bisa hannunsa, sauke sleepy eyes dinsa yayi kan innocent face ɗinta, baccinta take peacefully, ya gyara kwanciyarsa getting even more closer to her, kallon fuskarta yake without blinking musamman cheek dinta, a bazata ya kai other hand dinsa ya shafa cheek din nata, tin daga ƙololuwar kai yaji tamkar ana masa ruwan allurai, yayi ajiyar zuciya a hankali ya zame hannunsa da ta danne making sure bai tasheta ba, ya miƙe daga kan gadon ya nufi bathroom yana ciccilla hannunsa da ta kwanta a kai alamar dai ta daɗe akansa, sai takwas saura Hajar ta farka, tana sauka kan gado ta gansa zaune kan couch already well dressed up yana latsa wayarsa, bata masa second look ba tayi wucewarta ta shiga bathroom, yana ganin haka ya tashi ya bar mata ɗakin, har ta fito wanka ta shirya a tsanake snn ya dawo, ledar takeaway dake kan fridge ya nuna mata yace "ga breakfast", shiru tayi masa ba tace komai ba, ya daka mata tsawa yace "ba kiji me nace ba..?", ta sunkuyar da kanta tana wasa da fingers dinta tace "toh", murya ƙasan maƙoshi yace "Silly girl", kaɗan taci abincin ta ture, yana latsa wayarsa ba tare da ya dubeta ba yace "kin gama haɗa komai naki..?", gudun kar ya sake mata tsawa ta gyaɗa kai tace "Eh", fita yayi bayan minti biyar ya dawo tare da wnda zai fitar musu da kayansu don already bolt na waje tana jira, Hajar na ganin an fita da box dinta taji wani daɗi har cikin ranta, Nurain ya nufi door ya murɗa handle, juyowa yayi yana kallon Hajar da take saka takalminta, tana ɗago kanta sukay ido huɗu, tayi sauri ta saukar da kanta, dawowa yayi ya tsaya gabanta, jin scent dinsa ta ɗaga kanta, a hankali ya kai hannu ya shafa cheek dinta yace "ba kya jin magana..", da sauri taja baya tana juya lulu eyes dinta, ya sauke numfashi yace "wuce muje..", ƙofa ta nufa da sauri yabi bayanta, saida ya rufe ɗakin snn suka shiga Elevator tare zuwa ƙasa, Nurain ya dakata a reception domin checking out ya ajiye key kuma, receptionist ya duba Keycard din ganin numbern room dake jiki ya dakatar da Nurain, wata leda ya ɗakko ya miƙa masa yace "perhaps is this yours..?", Nurain ya ringa kallon ledar snn ya amsa yace "yess", ledar da matar Hammad ta bawa Hajar ce. before 9:50 suka isa Airport don jirgin 10 zasu shiga, Hajar dai na fahimtar wajen ta haɗe rai, tunowa da wahalar da tasha a jirgi tayi, saida suka shiga filin jirji ta ɗan kallesa tace "dan Allah dama mota muka hau", yace "ba nida lokacin tafiya daga Abuja zuwa kano a mota..", bata sake ce masa komai ba har suka hau jirgi, kamar lokacin da suka zo tafiyar ma ga seat dinsa ga nata, tinda suka shiga jirgin take addu'a a ranta, ai kam taci sa'a lokacin da jirgi yayi takeoff ba taji kamar yadda taji da zasu zo ba, da suka isa ma wajen landing yazo mata da sauƙi, suna fitowa Nurain ya amshi motarsa suka bar airport din, sha ɗaya da minti goma Nurain yayi horn a gate din gidansa, tini mai gadi ya buɗe gate, bayan Nurain yayi parking a parking space ya fito daga motar yana amsa sannu da zuwan da Inuwa ke masa, har bakin balcony Inuwa ya kai musu kayansu, Hajar dai na tsaye bakin ƙofa tana jiran ya buɗe masa ta shiga, deep inside her mind taji daɗi da ta ganta a gida, yana buɗe main door ta kai hannu zata ja box dinta kawai taga ya ɗauka ya shiga da ita, bayansa tabi zuwa palour taga ya haura upstairs, slowly ta fara tafiya ta haura saman itama, a bakin ƙofar ɗakinta taga ya ajiye box din, ta buɗe ɗakin taja box din ta shiga ta mayar da ƙofar ta rufe. sai wajen 4 ta sauka downstairs ta shiga kitchen ta nemawa kanta abinda za taci, plain Noodles ta dafa da boiled egg ta ci a kitchen din snn ta wanke komai da tayi amfani dashi, tinda ta koma room dinta bata sake sakkowa ba, ƙarfe tara na dare tayi wanka abinta ta saka kayan bacci, pillow da duvet ta ɗauka tayi kwanciyarta kan carpet, ko minti biyu ba tayi da kwanciya ba aka turo ƙofar ɗakin, waya ce kare a kunnensa yana sake dialing numbern Mami wacca suna cikin waya network ya yanke, bai samu Mami ba don hka ya sauke wayar daga kunnensa yana kallon Hajar, with a repartee yace "ke!! tashi daga ƙasan nan", ta miƙe zaune tana turo baki tace "ni nafi son nan..", ware ido yayi yace "what..?, magana kike min..?", ta shiga girgiza kai sai kuma ta miƙe ta koma kan gado ta kwanta, yace "daga yau kar na sake ganin wani soul ya kwanta kan carpet..", sai kace yana kallonta haka ta shiga bunka masa harara tamkar sabuwar kamu, ya juya ya bar ɗakin bayan ya kashe mata fitila. washe gari da Hajar ta farka abinda ta farayi shine wanka biyu snn ta haɗa da wankin hair dinta tinda ta jiƙasa, nannaɗe gashin tayi da towel ta fito, bayan ta gama rubbing lotion a fatarta ta fitar da kayan da zata saka riga da skirt na atampa, tana gama oiling gashinta ta ɗauki kayan zata saka, zip din riga dai da kyar ya zugu, da tazo saka skirt shi kam zip dinsa bai zugu ba, sakin baki tayi tana kallon kanta a mirror, though ita ɗin ba mai jiki bace don ko chubby ba ta kai ba, amma kuma duk wasu point da yake fitar da kyan mace a jiki toh nata aciki suke dam dam, haƙura tayi da saka riga da skirt din ta saka doguwar riga A-line ta feshe jikinta da 3 different perfumes, tin daga room dinta ta fara shara har ta kai downstairs palour shima ta share ta kaɗe ƙura, bayan tayi mopping ta goge kayan kallo ta jona turaren wuta a burner, haba tini gida ya ɗau harami yana baza ƙamshi, kitchen ta shiga don samawa kanta breakfast, ƙarfe goma da rabi Nurain dake sanye cikin sweat pant da shirt sky blue ya sakko downstairs, ya ringa bin ko ina da kallo yana mamakin yadda yaga guri yayi fes fes, uwa uba kuma ƙamshin da yaji wnda a wajen Maminsa ya sansa, kitchen ya shiga, Hajar dake chopping onion ta ɗaga kai ta ɗan kallesa kafin ta ɗauke kanta ta cigaba da abinda take, sosai yajin albarsa da take yankawa ya addabi Nurain dake jiran coffee dinsa ya kammala, Hajar na ɗago kanta a karo na biyu ta lura da yadda yake micincina ido yana jan pointed nose dinsa, bata san lokacin da wata dariya ta kufce mata ba, ta sunkuyar da kanta tana cigaba da dariya, haɗe gira Nurain yayi lokaci guda ya kashe Coffee makern ya fita daga kitchen din don bazai iya withstanding yajin ba, yana fita kitchen din yayi wani kasalallen murmushi ya haura sama, semosa da meat pie wnda suka ji isasshen nama tayi, daman Hafsah ta koya mata yadda ake yin minced meat a blender, semosa biyu meat pie biyu ta soya ragowar kuma ta ajiye cikin fridge, daga nan ta tafasa black tea mai kayan ƙamshi ta zuba sugar ta fita. bayan Hajar ta idar da sallar azahar ta tuna da wayar da ya bata, box din da ta mayar wardrobe ta dakko, already tin jiya ta kwashe kayanta wayar ce kawai bata dauka ba, ƙaramin zip ta bude ta ciro wayar da charger dinta, ba tayi wata wata ba ta cire sim dinta na cikin wayarta da ta lallace ta ɗora kan wayar, amma dai bata cire na kai ba tinda wayar ba dual bace, numbern Hafsah ta nemo tayi dialing, bata daɗe tana ringing ba tayi picking, bayan sun gaisa Hajar tace "yasu Antyna..?", Hafsah tace "wllh lfy alhmdllh", Hajar tace "amma yaushe zaki zo Hafsah..?", Hafsah ta zaro ido tace "ranar da fel waya tayi gashi..", Hajar tace "ke dan Allah", Hafsah ta fashe da dariya tace "nifa na fadi hakan ne naji me zakice, wllh na ɗauka zaki rufeni da bala'i", Hajar tace "sbd ga jarababbiya dage sarkin faɗa ko..?", Hafsah tace "A'a ni bance ba..", Hajar tace "Toh yaushe zaki zo tare da Humairah..?", Hafsah tace "ina nan tafe karki samu damuwa", fira suka taɓa snn sukay sallama Hajar ta katse kiran, tashi Hajar tayi ta sauka downstairs ta shiga kitchen, store ta wuce ta ɗebo rice flour ta damasa a small bucket ta zuba yeast snn ta rufe da leda da kuma murfin to proof it, daga haka ta koma room dinta, ba ita ta sakko ba sai hudu da rabi bayan tayi sallahr la'asar da azkar da ta saba, tsaye tayi jikin kitchen island tana tunanin da mai zata haɗa abin, deep freezer ta bude ta ɗakko nama, saida ta bari naman ya saki snn ta shiga sarrafa pepper soup, wata daddaɗar aroma ce take tashi a kitchen din, pepper soup din na kan wuta ta ɗakko ƙullun da ta kwaɓa, har ya tashi fumm ya cika bucket din, babu ɓata lokacin ta fara soya sinasir din da tayi amfani da easy way of making it, ƙofar kitchen din taji an buɗe, ta juya sukay ido huɗu dashi, ƙarasowa yayi gaban gas din ya miƙa mata abinda ke hannunsa, ta tattare gira tana kallon hijab dinta da yake bata, amsa tayi tace "what for..?", gaba ɗaya hancinsa ya gama cika da ƙamshin abincin, yace "ki fito palour ku gaisa", yana gama fadin haka ya juya ya fita a kichen din, saida ta sauke wnda ke kan wuta ta kashe gas din snn ta fita, tare da Farooq ta gansa zaune a palourn, walking gently ta ƙarasa palourn ta zauna ta gaida Farooq, da fara'a ya amsa mata yace "how are you doing Amarya...?", Hajar ta saukar da kanta ta amsa a taƙaice, Nurain dai sai satar kallonta yake ya wani haɗe gira, after a while yace "kije ki cigaba da abinda kike" don even with hijab baiso ta zauna a nan din da dai da niqab ne is okay, kitchen ta koma within few minutes ta fito hannunta riƙe da tray na bottle water da drink, kan Centre table ta ajiye, Farooq yayi murmushi yace "thank you..", ba tace komai ba sai murmushi da tayi, Nurain ya haɗe gira yabi bayanta da kallo, Nurain yace "Amm kunyi waya da iron lady kam tinda suka tafi..?", Farooq yace "yeah vid call ma mukay da ita ta wayar Noor", Nurain ya shafa kansa yace "ohh i see", Farooq yace "Dr what exactly my problem is nifa har ynxu lower abdominal pain din nan bai barni ba..?", Nurain ya gyara zama yace "i think i told you... kayi aure kawai", Farooq ya haɗe gira yace "is a different casa malam, tin fa ina yaro wnn ciwon yake har akamin surgery.." jin an buɗe ƙofa yayi shiru, Hajar ce ta fito ta ajiye wani tray din mai ɗauke da two warmer da plates da kuma bowls, ta ajiye saman Centre table, Farooq yace "Ahh harda baƙin yamma..", murmushi tayi ba tace komai ba ta koma kitchen, da plate din nata abincin ta fito ta haura sama, Nurain ya bita da kallo sai kuma ya dubi Farooq yace "Am coming", bai jira cewarsa ba ya haura sama yana tsallake steps da bibbiyu, ƙofar ɗakinta ya buɗe, tana zaune kan carpet tana cin abinci, daga bakin ƙofa ya tsaya girarsa a haɗe yace "karki sake fitowa", ya rufe mata ƙofar, taɓe baki tayi ta cigaba da cin abincinta, tini Farooq ya baje harka ya fara ɗebar dabge, tin kafin Nurain ya ƙaraso palourn yake kallonsa ganin yadda ya tattare hannun riga yana shan pepper soup, Nurain ya zauna position dinsa yace "ynxu pain din ne ya dawo..?", Farooq yace "bari na gama karna ƙware gsky, your wife is a good cook kaji daɗinka dude...", Nurain yayi resting jikin kujera yana latsa wayarsa, bayan Farooq ya gama da pepper soup din da ya zuba yace "dude kai bazaka ci ba..?", Nurain yace "am not eating..", Farooq yace "Alright naka ai special ne, amma dai the food is yummy..", Nurain yace "stop exaggerating..", Farooq yace "am not wollah", Nurain bai sake cewa komai ba, kafin Magrib Farooq ya tashi tafiya bayan sun gama mgana da brother din nasa, Farooq yace "toh kiramin madam muyi sallama", Nurain ya nufi door yace "no need", Farooq yace "toh hka zan tafi without giving her anything, please ka kirata..", firr Nurain yaƙi kiranta sam, haka nan Farooq ya wuce amma yaso ya bawa Hajar kyauta. Nurain ya shigo palour bayan tafiyar Farooq, kallon abincin da Farooq ya rage yayi, lokaci guda ya matsa gaban center table din, spoon ya ɗauka ya buɗe warmer din pepper soup, ya ɗan ɗebi soup din ya kai baki, bari dai yaji me Farooq yaji yake zuba wnn zancen, ji yayi kunnensa ya tsira tamkar an caka masa allura, ya ɗauki tsoka daya ya saka a baki, ɗayar warmer din ya buɗe yaga wainar sinasir, yayi pinching sinasir din ya kai baki, kamar ydda ear dinsa ya tsira lokacin da ya sha soup hakama yayi this time around, ɗaukar warmers din yayi ya haura sama. washe gari Monday Nurain na isa hospital after 40mins ya shiga surgery, wani emergency patient aka kawo wnda yake buƙatar aiki cikin gaggawa, ya tsaye a position dinsa na head of the surgery, Ruqayyah ma na surgery room din tana miƙa instruments, kana ganinta kasan bata jin daɗi, Nurain yace "Artery forcep", yanata jira a basa amma shiru, ga bleeding Artery din da zaiyi clamping sai zuba take, maimakon ta basa Artery forcep saita basa Dissecting forcep shi da ba sutures zaiyi ba, Khaleel dake first assistant yace "A Nurse concentrate or you wanna be a quack", sai a lokacin Ruqayyah ta lura da abinda take miƙawa, da sauri ta mayar ta ajiye ta miƙa masa wnda ya buƙata, ana cigaba da surgery da minti 10 Ruqayyah tayi collapsing, da Nurse Jiddah aka ƙarasa surgeryn, Nurain ya zare hands gloves din hannunsa yayi disposing ya fita daga surgery room din, saida ya cire surgeon gown da soft Clog shoe da yayi surgery dasu snn ya fita gaba ɗaya, bayan Nurain ya koma office dinsa ya kira Khaleel a waya, tambayarsa yayi ina aka kai Ruqayyah, Khaleel yace "Amenity 5", Nurain yace "Ohk" kafin ya katse kiran, ajiyar zuciya yayi ya tashi ya bar office din, yana zuwa ƙofar ward din da Ruqayyah take ya murɗa handle din ya shiga, ya ƙarasa gaban bed din da take kwance yana kallonta, bakinta ya bushe kamar ƙanxo, idonta a rufe tana bacci, a wahale take ajiye numfashi, ya dubi Nurse Amina dake tare da ita yace "anyi checking BP dinta..?", Nurse Amina tace "yess Dr", yace "bring the Bp gauge..", Nurse Amina tace "Okay" da haka ta juya ta fita daga ward din, Nurain dai na tsaye gefen gadon, ji yayi an riƙe hannunsa, ya juya yana kallonta, idanunta sunyi jajir tana kallonsa a sanyaye, da kyar ta motsa lips dinta da suka bushe tace "Dearest".......✍️ 💛 HAJAR 💛 {66..} Nurain ya zare hannunsa da ta riƙe ya tattare girarsa yace "how are you feeling now..?", Ruqayyah dake kallonsa da jajayen idanunta ta girgiza kai tace "not fine... not okay", ɗauke kansa yayi daga kallonta yace "Alright you will be fine insha Allah...", Ruqayyah ta lumshe idonta tana jin suya a zuciyarta, hawaye ya ciko idonta tace "Dearest" sai kuma tayi shiru jin an buɗe ƙofa, Nurse Amina ce ta shigo da Bp gauge a hannunta, a gaban Nurain ta sake gwada Bpn ta nuna masa reading din wnda ya nuna jinin ne yayi low, ita dai Ruqayyah kawai kallonsa take sai kace tsohuwar mayya, shi kam bai sake kallon inda take ba yana kallon Nurse Amina yace "An kira familyn dinta..?", Nurse Amina tace "Eh", yace "Okay... sai a sa mata drip tinda Dr Marwan yasa an mata injection..." da haka ya juya ya fita daga ward din, Ruqayyah ta bisa da kallo tana jin wani hope yana taso mata, lallai an samu cigaba wai Dearest ne ya nuna damuwa akanta, har cikin ranta taji daɗin hakan kuma ba ƙaramin daɗi taji ba, ynxu kam ta samu ƙwarin guiwar da zata fara bar ruwa ga shukarta da ta bushe, Nurse Amina ce ta zauna da ita har Momy ta iso asibitin, Momy ta zauna gefen gadon da Ruqayyah ke kwance, da ladabi Nurse Amina ta gaisheta, Momy ta amsa mata da sakakkiyar fuska sai kuma ta dubi Ruqayyah tace "me yake damunta...?", Nurse Amina tace "sun shiga surgery ne shine ta faɗi, ashe bp dinta ne yayi low..", Momy ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Ruqayyah ba tace komai ba, Nurse Amina tace "Amma alhmdllh she is fine now, an mata allura ga drip nan ma an saka mata...", Momy tace "Alhmdllh, sannu da ƙoƙari Allah yayi albarka", Nurse Amina tace "ba komai, ni zan wuce gida Allah ya bata lfy...", Momy tace "Ameen.. Allah ya miki albarka", Nurse Amina tayi murmushi da haka ta fice daga ward din, Nurse Jiddah ma ta shigo duba Ruqayyah ta tarar tana bacci don haka suka gaisa da Momy kafin ta tafi, tin ƙarfe sha ɗaya Ruqayyah ke bacci ba ita ta farka ba sai biyu saura, tana buɗe idonta taga Momy ga two sisters dinta ma duk sunxo, a hankali Ruqayyah ta miƙe zaune ta jingina da jikin gado, Aisha tace "ya jikin..?", Ruqayyah tace "da sauƙi", Kulsoom dake goye da baby dinta ta ɗora hannu kan forehead din Ruqayyah sai kuma ta kalli Momy tace "babu fever..", a taƙaice Momy tace "Okay ya sauka knn.. saita faɗi abinda za taci ai", Ruqayyah ta sunkuyar da kanta, Kulsoom tace "na kawo miki offals pepper soup za ki ci..?", Ruqayyah ta gyaɗa kai a hankali, zuba mata farfesun kayan cikin Kulsoom tayi a bowl ta bata, Aisha tace "a haɗaki miki shayi..?", Ruqayyah ta girgiza kai tana cin farfesun a hankali, Aisha na kallon Momy tace "wai me yake damunta ne, ita kullum ba lfy..?", Momy tace "yo toh ba dole tayi ta rashin lfy ba ta ɗorawa kanta damuwa, ynxu fisabilillah me ya haɗa Ruqayyatu da hawa da saukar jini", Aisha tace "hawan jini kuma..?", Momy tace "abinda likita yace knn", Aisha ta saki baki ta kalli Ruqayyah da ta kasa cin farfesun gabanta kawai jujjuya spoon din take, Momy tace "dama ta kwantar da hankalinta wllh, ni wnn damuwar da har take ƙoƙarin jawa kanta cuta shine zai sa naji haushinta, ƙaryar da ta yimin wnn bata ƙonamin rai kamar wnn halin da ta tarka ba, tinda dai kanta ta yiwa duk wnda yayi na gari kansa, idan ma mganar Dauda ce toh shima ta sakawa zuciyarta salama don an riga an shafe babinta, shima daman aure ai ba farillah bane ƙarfaffiyar sunna ce, tinda ta nuna bata son auren ai shknn mgana ta ƙare bbu wnda zai mata dole, Daddy ya ajiye lamarinta a gefe, a haka dai dana haifeta sai mu cigaba da zama a gida nida ita muna haɗa kafaɗa, Dr yana shigowa zance ya sallamemu ni baxan yi zaman asibiti ba, ke da Kulsoom duk aure gareku ga kuma yara, nice dai zaman ya duba kuma bazan yi ba", Aisha tace "Ayi haƙuri Momy", Momy tayi tsaki tace "ni bbu abinda tayi min wnn dai damuwar ce da tke jama kanta bana so..", Aisha ta dubi Ruqayyah tace "toh kinji dai, saiki cire duk abinda ke zuciyarki..", Kulsoom tace "ya dai fiye mata". Da yamma aka sallami Ruqayyah don daman rashin lafiyar nata ba chronic bane, Ruqayyah kam tana komawa gida ta fara tsara yadda zata janyo hankalin Dearest dinta ya dawo gareta, wnn damuwar da ya nuna akanta ba ƙaramin tasiri yayi a zuciyarta ba, hakan ya nuna cewa har ynxu yana jinta a zuciyarsa knn, ta lashi takobi duk tsiya duk tsiya tsiya saita dawo da Dearest dinta. ★Nurain yayi parking motarsa a parking space din gidansa, ya cire key daga Ignition yana stretching kansa, ledar takeaway da ya siyo ya ɗauka snn ya buɗe motar ya fita, yana shiga palour daman direct sama ya haura ya shiga ɓangarensa, ya ajiye ledar takeaway din kan makeken Centre table dake huge palourn, bedroom ya wuce ya shiga wanka, yana fitowa ya saka ƙananun kaya da yake zaman gida dasu, fitowa yayi daga room din zai sauka downstairs, ya tsaya a corridor yana kallon ƙofar ɗakinta na wasu seconds din kafin ya sauka, ya buɗe ƙofar kitchen ya shiga, wani daddaɗan aroma ne ya fara masa maraba, ya kalli tukunyar dake kan gas wacca wuta take cinta amma kaɗan, plate da spoon ya ɗauka, har zai fita daga kitchen din ya dawo ya ɗauki lemon kwali da cup ya fita, upstairs ya haura ya shiga part dinsa, ledar takeaway ya buɗe ya juye abincin a plate, tinda ƙamshin abincin ya daki hancinsa ya yamutsa fuska, kwata kwata ƙamshin bai masa ba, wai nan saida ya zaɓi babban eatery snn ya siyo abincin a nan, toh ko dai tsanar da ya yiwa abincin siyarwa ne yasa yaji hakan, spoon ɗaya yaci yayi saurin wurgi da cokalin ya zuba lemo a cup ya fara sipping, mayar da abincin yayi cikin takeaway ya rufe ya koma ya jingina da kujera da cup din lemonsa a hannu, after 10mins ya ajiye cup din ya tashi ya fita, yana sauka ƙasa ya buɗe ƙofar kitchen, tsayawa yayi yana kallonta, tana tsaye gaban gas cooker tana serving, da sauri ya ɗauke idanunsa daga kallon bayanta sai kuma ya shiga kitchen din sosai, Hajar ta ajiye serving spoon dake hannunta ta juya tana kallonsa sbd motsin da taji, ido huɗu sukay tayi sauri ta janye nata ta cigaba da abinda take, Nurain ya tsaya daga bayanta yana leƙa tukunyar abincin, yanxu kam ƙamshin da yake tashi yafi na ɗaxu da ya shigo, harɗe hannu yayi ya tsuke fuska yace "har dashi kika dafa dai ko..?", jimm tayi ba tare da ta juyo ba tace "shi wa..?", Nurain ya sake tsuke fuska yace "shi wanda yaxo jiya yaci jagwalgwalon naki..", Hajar ta haɗe gira tace "A'a ba dai jagwalgwalo ba, ni ban iya jagwalgwalo ba" da haka ta rufe tukunyar ta ɗauki plate din abincin ta juyo, kallonta taga yanayi babu ko ƙiftawa, sosai idanunsu suka sarƙe staring at each other na almost 10secs, Hajar ta murguɗa masa baki tace "Please excuse me ni fita zanyi" don kallon nan da yake mata harta tsargu, ya matsa ya buɗe tukunyar, tini ya ajiye murfin sbd akwai zafi, dariyar mugunta Hajar ta tuntsire da ita tace "wa yace ka taɓamin", Nurain ya haɗe gira yana kallon hannun da ya ƙone yace "toh wai daman waye zaici wnn jagwalgwalon naki idan ba Farooq ba, look ki zuba masa zan fita sai na tafar masa dashi" da haka ya bar kitchen din yana yarfe hannu, Hajar tabi bayansa da kallo tana sauke murmushin muguntar da take masa, ajiye plate din hannunta tayi kan island, a medium warmer mai kyau ta zuba abincin, daman wnda ta rage ne za taci da daddare kawai ta zuba masa in yaso ta dafa Noodles da daddaren, Hajar na fita kitchen din da few minutes Nurain ya shigo, yana ganin warmern da ta ajiye yayi sauri ya buɗe, rufewa yayi ya ɗauki plate ya fita ya haura sama abinsa. Da daddare wajen ƙarfe tara Nurain na zaune kan makeken gadonsa, ya rage hasken ɗakin da Laptop a gabansa yana operating, wayarsa da tayi ƙarar shigowar message ya kalla, ɗaukar wayar yayi yaga number ce ta turo text din, bude message din yayi ya karanta, (Nagode sosai Dearest da kulawa..) shine kawai abinda ke rubuce, ajiye wayar yayi ya cigaba da abinda yake, sauka yayi daga kan gadon yana jan farar rigar Pajamas dake jikinsa, room slippers ya zura a soft legs dinsa, walking gently ya buɗe ƙofa ya fita, yafi minti biyu yana kallon ƙofar ɗakinta bayan fitarsa corridor snn ya buɗe, saida ya kai tsakiyar ɗakin kafin Hajar dake ɗaure da towel iya cinya ta lura dashi, fitowarta daga wanka knn, wata gigitacciyar ƙara ta fasa ta durƙushe ƙasa tana kare jikinta, Nurain kam tsaye yayi still yana kallonta ya fara tafiya towards her, Hajar da jikinta ke rawa ta ɗaga kai ganin yana nufota tayi saurin miƙewa, zumbulelen hijab dinta ta yayiba zata saka, kawai gani tayi yaxo kusa da ita aikam maimakon ta saka hijab din saita yaɓa masa a fuska, da mugun gudu ta juya da nufin shiga toilet, unfortunately for her yayi saurin fixgo hannunta bayan ya wurgar da hijab din, da iya volume dinta ta fasa ƙara hakan yasa ya wani fixgota tayi wata ramfa ya haɗata da bango, da sauri ta dafe towel din jikinta sbd kar ya kwance, ya sauke ajiyar zuciya yana kallonta from head to toe ya riƙe hannunta gam, tini ta manne da bango tana ƙoƙarin fixge hannunta daya riƙe don ta riƙe towel dinta da hannu biyu, matsowa kusa da ita yayi har tana jin breathing dinsa, muryarta na rawa tace "meye haka... ni ka sakeni babu kyau wllh Allah", da muryarsa da ta canza amo yace "mene babu kyau..?", yana jin yadda jikinta ke rawa, da kyar ta iya magana sbd yadda muryarta ke rawa tace "taɓani da kake wllh babu kyau haram ne...", sake manneta yayi da bango har jikinsu na gogar na juna, da wata iriyar murya yace "says who..?", ta bude baki za tay magana kenan ya kai hannu ya kashe wutar ɗakin, Hajar na ganin duhu ya gaure ɗakin ta wani zaro ido ta fara turesa da iya ƙarfinta, zagaye ƙugunta yayi ya janyota jikinsa yace "uhmm am asking you.. wane yace babu kyau...?", kasa magana tayi ta ringa ƙoƙarin fixge kanta, ya sunkuyo gami da ɗora goshinsa saman nata, dena kokawar tayi yayinda zuciyarta ta buga da ƙarfi, a bazata taji ya goga pointed nose dinsa a nata snn da muryar da ta tsaya iya ƙirji yace "Am asking you young lady", ina Hajar kasa mgana tayi in banda rawa bbu abinda jikinta yake, Nurain ya lumshe idonsa yana jin wani sabon abu yana kai ziyara brain ɗinsa, ajiyar zuciya ya sauke wcca tasa Hajar saurin lumshe idonta tare da kwarin guiwar hankaɗasa, saidai fa a banza don ko gezau beyi ba, sakinta yayi ya kunna fitila, da sauri ta sulale ƙasa ta tsala wani uban ihu ta takure kanta waje ɗaya, ya mata kallo ɗaya yace "bashi ne ko ba yau ba sai kin bani amsana Silly girl..", yana gama faɗin haka ya juya ya fita daga ɗakin with a hidden smile all over his face. washe gari Nurain ya fito daga ɓangarensa, briefcase ne riƙe a hannunsa, har zai sauka ƙasa sai kuma yaji bazai iya ba, dawowa yayi da baya ya murɗa ƙofar ɗakinta, Hajar dake kwance kan bed tayi sauri ta rufe idonta jin an bude ƙofa ga kuma ƙamshinsa da ya baza ɗakin, ko da idonta yake a rufe amma tana jin kaifin idonsa a kanta, after few minutes taji ya rufe ƙofar, ta mirgina ta kalli ƙofar tana turo baki gami da banka mata harara. Nurain na isa hospital ya wuce office dinsa, postion din secretaryn sa Haleema ya kalla yaga bata nan, that is unusual don kullum tana rigasa zuwa, da haka dai ya murɗa handle ya shiga ciki, tinda ya shiga yayi turus a bakin ƙofa yana kallonta, Ruqayyah ta ajiye frame din hotonsa dake hannunta ta miƙe, bayan oil control powder da ta shafa a fuskarta harda lipgloss da eye pencil, ga wani ɗan uhansun turare da ta baƙaƙa a jikinta, ta yalwata fuskarta da murmushi tace "welcome Dr", Nurain ya haɗe gira without looking at her for the second time yace "what are you doing here..?" sai kuma ya ƙaraso ciki ya zauna a chair dinsa, Ruqayyah ta bisa da kallo tana murmushi tace "Amm good morning", ko kallonta beyi ba yace "what brings you here..?", Mug din da ta ajiye kan table ta ɗauka ta miƙa masa tace "i just wanna say good morning and give this to you", sai a lokacin ya ɗaga kai ya dubi Mug din da take miƙa masa, girarsa a haɗe yace "please get lost my patients are waiting outside", tace "Ohh okay... amma please kasha coffee din", ya ɗaga kansa yana mata wani shegen kallo with stern voice yace "just leave", ta ɗaga shoulder sai kuma ta ajiye mug din kan table da haka ta juya ta fita da tafiyar da take motsa wasu sassan na jikinta, Nurse station ta wuce walking like a cat, tana zama station din tayi wani murmushi tace "yanxu ma aka fara", Nurse Jiddah ce ta fito daga wani room na female Nurses, tana ganin Ruqayyah ta saki baki tace "wai keda baki da lfy jiya har dasu kwanciya shine kike fito aiki yau", Rukayyah tace "dole na fito aiki Jiddah tinda na samu sauqi", Nurse Jiddah tace "toh Allah ya ƙara lfy", Ruqayyah tace "Ameen", Nurse Jiddah ta kalli agogon wrist dinta tace "Ohh nasan ynxu Dr Uthman yaxo bari naje na dauki Vitals din patient din na kai masa", Ruqayyah tace "wane patient..?", Nurse Jiddah tace "patient da ya yiwa aiki jiya, ai dake aka fara aikin baki kai ba hajiyata", Ruqayyah tace "Ohk, bari naje na duba kawai ke ki zauna", Nurse Jiddah tace "Okay tom shknn", miƙewa Ruqayyah tayi tace "A wane ward yake da bed number", Nurse Jiddah ta gaya mata, barin station din Ruqayyah tayi ta tafi ward din da patient din yake, saida tayi recording komai da ya kamata snn ta fito, riƙe da record book din ta kama hanyar office dinsa, daidai corridor da zai kaika office din ta tsaya, ta saka hannu a pocket ta ciro ƙaramar kwalbar turare, sosai take ƙamshi amma ta sake fesa wani, ta gyara wuyan ƙaramin hijab dinta da ya sha guga kamar Nurses Scrub dake jikinta, tana zuwa bakin office din ta tarar akwai patient a ciki don haka taja gefe ta tsaya, few minutes patient din ya fito, patient dake kan layi ya tashi zai shiga Ruqayyah tace "dan Allah ka ɗan jira na fito..", ganin itama ma'aikaciya ce bai mata musu ba, Ruqayyah ta shige office din gami da canza salon tafiya, Haleema dai ta bita da kallo sbd tana shigowa taji ƙamshi, a bakin ƙofa ta tsaya tana kallonsa yana rubuce rubuce, Nurain ya ɗago kansa da zummar ganin next patient sai kawai yaga akasin haka, ya sauke kansa fuskarsa ba yabo ba fallasa, ta ƙarasa walking like a cat ta ajiye record din hannunta kan table tace "here Vital signs na pat..", bata ƙarasa ba ya katseta da faɗin "i think Nurse Jiddah should do that", tayi twinkling eyes dinta tace "amma aikina ne Dr ita tamin handover", girarsa a haɗe ya ɗauki record din ya ajiye gabansa yace "Ohk", har cikin ranta taji daɗi after few seconds ta juya ta fita da shegiyar tafiyar da ta tarki yi. ★Da kyar Hajar ta iya raba kanta da gado, jin kanta take wani odd gani take shknn ta zama ƴar Air, ya za ai ya mata haka fisabilillah, ta samu tayi wanka tayi shafe shafenta, ba tayi attempting saka riga da skirt ba ta saka doguwar riga, ta zo fita kawai ta tsaya kallon bango, a take moment din jiya ya dawo mata fresh, ta runtse idonta ta dafe kanta, da sauri ta kawar da tunanin ta bar ɗakin, a ɗarare ta gama dafa breakfast taci a kitchen din, tana gama ci ta fara wanke duk wasu kwanuka da tayi amfani dasu, tinda ta koma ɗakinta bata sake fitowa ba har akay sallar azahar, bayan tayi sallah ta kira Anty da Ummanta suka gaisa, sai wajen ƙarfe uku ta fara jin yunwa, gashi kuma ba ta son fita sbd karta haɗu dashi, haka kurum ya ringa mata kallon ƴar air tinda ya kalleta jiya, da kyar tayi shahada ta fita, walking like a chameleon ta sauka downstairs tayi wuf ta shige kitchen, har da wani rufe ido da ajiye numfashi, kayan miya tayi blending wnda za tayi sauce, ta silala spaghetti kawai ya fiye mata sauƙi, har ta gama silala taliyar tayi sieving dinta ta zuba a plate, tana cikin zuba Sauce taji an buɗe ƙofa, da ƙarfin gaske zuciyarta ta buga sbd scent dinsa da ta shaƙa, wllh Allah shine, backing ɗinsa tayi amma kuma saita kasa cigaba da abinda take, lokaci guda ta juya ba ta bari ta hada ido dashi ba ta nufi ƙofa zata fita, da sauri ya riƙo hannunta, aikam tana juyowa ta gatsa masa cixo a hannu, yana sakinta ta kwasa a guje ta bar kitchen din.....✍️ 💛 HAJAR 💛 {67..} Nurain ya dubi hannun da ta gatsa masa cixo yayi kwafa ya juya ya kalli abincin da ta fara zubawa, plate din Abincin ya ɗauka ya ƙarasa zuba Sauce din ya soka fork a gefen plate din, saida ya ɗauki ruwa da lemo snn ya fita. da daddare wajen ƙarfe takwas Hajar ta idar da sallahr Isha'i, da kyar ta nannaɗe prayer mat din ta ajiye kan chest of drawers sbd wata azabar yunwa da take kartarta, bathroom ta shiga tayi wanka ta fito tana tafiya a hankali, ji take kamar an yashe mata ƴan hanji, doguwar riga ta kayan bacci mai laushi ta saka ko mai bata iya shafawa ba sbd ydda tayi weak, ta zumbula hijab har ƙasa tana tafiya a hankali ta fita a ɗakin, a hankali ta ringa sauka daga stairs tayi support da railer don ji take kamar iska zata iya ɗebeta, tin kafin ta kai ƙasa taji ƙarar TV, yana zaune palour da mug din coffee riƙe a hannunsa, tinda ya hangota ya dena kallon Tv ya zuba mata idanu, Hajar ta saukar da kanta ta wuce kitchen abinta, neman Spaghetti dinta ta farayi, sama ko ƙasa babu taliya a kitchen, jingina tayi da cabinet sbd bazata iya tsayuwa ba, ko strength din dafa shayi ma bata dashi a halin yanzu, da taliyarta na nan haka zata ci kayarta duk sandarewar da tayi, wani ƙululu ne ya tsaya mata a throat ynxu ina taliyanta, kafin kace me hawaye ya ciko idanunta, door aka buɗe ta ɗaga kai ta masa kallo ɗaya kafin ta saukar da idanunta, mug din hannunsa ya ajiye gaban sink without looking at her for the second time, da haka ya juya zai bar kitchen din sai kuma ya dawo da baya ya tsaya yana kallonta, speaking with a repartee yace "yah.. why are you standing here like one living statue...?", tana ɗago kanta hawayen da suke maƙale idanunta suka hau zarya, tayi sauri tasa bayan hannu ta fara gogewa, tsuke ido Nurain yayi ya ɗan matso kusa da ita yace "what happened..?", ta sunkuyar da kanta ba tace komai ba, ya duƙa ya leƙa fuskarta yace "ke mene ne..?", fashewa tayi da kuka tace "Taliyana na ajiye zan ci kuma ban ganta ba", still Nurain yayi yana kallonta cike da mamaki, ya harɗe hannu still looking at her yace "A ina kika ajiye...?", ta nuna masa kan gas tace "a nan fa na ajiye abuna..", ya kalli kan gas din sai kuma ya juyo yana kallonta, yace "toh ke wa yace ki ajiye a nan, baki san ba a ajiye abinci a kitchen din nan ba, don haka kin rasa Aljanun kitchen din sun cinye daman rabonsu ne", da sauri ta kallesa tace "ban gane Aljanu ba, daman Aljani yana cin abinci ne..?", ya ɗaga shoulder yace "ba gashi nan kin gani ba, so next time sai ki san inda zaki ringa ajiye abincinki...", sulalewa tayi ƙasa ta fashe da kuka tace "na rantse sai sun biyani abuna, ba Aljanu ba ko sheɗanu ne sai sun biyani abuna, su sun isa su cinye min abinci..", Nurain couldn't help it but to smile lightly, she's so childish, tsuke fuska yayi kamar ba shi ya gama murmushi ba yace "Au kina zaune a gidansu zaki ringa musu rashin kunya, idan suka miki wani abun ke kika jiyo... c'mon get up ki nemi wani abin ki dafa kici, ko babu abinci ne a store..?", ta dena kukan tana shessheƙa tace "Ni spaghetti na nake so bxn iya dafa wani ba..", ta ɗora kanta kan cabinet don ynxu strength din mganar ma babu, she start be coming more weak than before, Nurain ya buɗe fridge ya ciro ƙatuwar bottle din sweetened fresh milk, cupboard ya buɗe ya ɗakko glass cup ya wankesa a sink, tini ya ɓalle murfin bottle din saida ya kusan cika glass cup din da fresh milk snn ya mayar da bottle din fridge, ya duƙa gabanta ya ajiye glass cup din madaran, ta ɗan kallesa sai kuma ta dubi cup din madaran, miƙewa yayi yana jan rigarsa ya nufi ƙofa ya buɗe ya fita, after few seconds Hajar ta ɗauki cup din madaran tana turo baki, lokaci guda abinda ya faɗa akan Aljanu yayi hitting brain dinta, sai kace muzuru a lefe haka tabi kitchen din da idanu, ba tasan lokacin da wani ƙarfi yaxo mata ba ta miƙe bayan ta suri cup din madaran ta fita da sauri, still a palour ta gansa kan doguwar kujera yana latsa wayarsa TV da ya kunna tana aikinta ita kaɗai, Hajar dai ta rakuɓe ta zauna gefe guda ta kafa kofin madaran a baki, saida ta kwankwaɗe tass snn ta diri cup din, after 10mins bayan madaran ya faɗa mata ta miƙe ta shiga kitchen, a buɗe ta bar ƙofar ta ajiye cup din a sink ta fito da sauri, walking like a chameleon ta nufi stairs, Nurain ya bita da kallon wutsiyar ido har ta ɓacewa ganinsa, tashi yayi ya zura slippers dinsa tare da jan rigarsa ya kashe kayan kallon da duk wasu kayan wuta na palourn, da haka ya haura sama yana brushing sumarsa with his hand, yana haure stairs ya ganta tsaye bakin ɗakinta jingine da bango, har ya wuceta yaji tace "Ai a kitchen kawai suke ko..?", ya zuba both hands dinsa a pocket ya juyo yace "Su wa..?", tace "Aljanun..", har zai ce mata Eh sai kuma ya fasa don so yake yayi teasing dinta yace "No daman a waje biyu suke a gidan nan, da kitchen da kuma nan" yayi pointing ƙofar ɗakinta, zaro lulu eyes dinta tayi kamar zasu faɗo ta kalli ƙofar ɗakin, da sauri ya sunkuyar da kansa ganin yadda ta zaro ido sai kuma ya ɗago bayan ya haɗe gira, Hajar ta yarfe hannu tace "na shiga uku..", yace "A'a baki shiga uku ba tinda kin iya rashin kunya, don haka saiki zama ready kiga abinda zasu miki tinda kin yiwa ƴan uwansu rashin kunya..", wani irin zaro ido tayi tana girgiza kai tace "wllh ban musu rashin kunya ba, a ina na musu rashin kunya, kawai fa cewa nayi sai sun biyani abuna, kai kaji lokacin da na musu rashin kunyar..?", ya ɗaga shoulder yana taɓe baki, yadda ta wani gigice tana zaro ido ne yake basa dariya, daman gashi tubarkallah akwai idanun bare ta zarosu, tace "kuma ni yanxu ma na yafe musu na bar musu abincin halak malak..", yace "kin bar musu knn..?", ta gyaɗa kai sai kace lizard tace "Eh halak malak", yace "Alright shiga ki kwanta..", ta juya tana kallon ƙofar ɗakin sai kuma ta juyo tace "babu abinda za suyi min ko..?", yace "may be", har ta kai hannu zata buɗe ƙofar sai kuma ta fasa ta juya tace "dan Allah baza suyi min komai ba...", tsaki yayi ya buɗe ɗakin ya shiga yace "kin fi kowa iya rashin kunya da tsiwa amma ga tsoro sai kace me, c'mon malama shigo ki kwanta..", ba musu sum sum ta shiga ɗakin ta nufi gado, ya bita da kallo ganin yadda hijab dinta ke jan ƙasa kamar zai harɗeta yace "ba dai da wnn blanket dake jikinki zaki kwanta ba...?", nan ma ba musu ta kware hijab din ta ajiye ta wuce ta haye gado, saida ya tabbatar ta kwanta ta rufe legs dinta zuwa neck da duvet snn ya nufi switch din ɗakin, kashe hasken yayi ya bar mata dim, kawai sai Hajar taga kamar gaba ɗaya ya kashe wutan don duhu ta gani dunɗum, afujajan ta yaye rufar tayi kneeling kan gadon ta tsala ihu, bai san lokacin da ya bar bakin switch ba ya hau kan gadon ya toshe mata baki, tana jin present dinsa daf da ita ga kuma ƙamshinsa tayi sauri ta faɗa ƙirjinsa ta sakar masa kuka, ba wai a tsaye yake ba bare yace ƙafarsa ne ya shanye ji yayi kamar an zare masa spine gami da caka masa wani allura a ƙwaƙwalwa, bai san lokacin da ya tafi luu ya faɗa kan gadon da bayansa ba ita kuma ta faɗa ƙirjinsa fiye da da, ta wani lafe a jikinsa harda gyara kwanciya don wani secure take jinta a nan ɗin, gani take ba wani harm da zai zo gareta a jikinsa don haka tayi lakur abinta, after a while ba tasan ta yaya ba kawai taji hannunsa cikin rigarta, da sauri ta buɗe idonta da ta lumshe ta fara shirin ɗagasa, yayi saurin mirginasu ta koma ƙasansa, pillow ya janyo ya ɗora kanta a kai ya koma gefe ya zauna zuciyarsa na racing, ta ja duvet ta lulluɓe jikinta don gaba ɗaya rigar baccin ta kwaye, shi dai bai sake kallonta ba yana yaƙi da abinda yake ji, can dai ya juya ya kalleta ganin yadda take sauke numfashi ya rage murya yace "Hajar", sau uku yana kiran sunanta amma no response, ya tashi a hankali ya nufi ƙofa don har lokacin bai dawo normal ba. ★Umma na zaune tsakar gida tana tsince waken alale, Sabra ce kusa da ita da uniform tana cin wainar gero da ƙuli ƙuli da Umma ta bata kuɗi ta siyo, Umma tace "marmaza ki cinye ki tafi karki makara auta", Sabrah tace "toh Umma" sai kuma ta dauki rabin wainar da ta rage ta lunƙuma a baki, ta tashi ta wanke hannunta daga nan ta shiga ɗaki ta ɗakko jakar makaranta, saida ta shiga wajen Baba ta gaishesa ta amso kuɗin makaranta kafin ta wuce makarantar, Umma ta koma bakin rariya tana wanke gwangwanaye, Sa'adatu ce ta fito sai soshe soshe take sbd cixon sauro da kuɗin cizon da ta sha, ta ɗauki buta ta zuba ruwa tana gyatsine, tsaye tayi kan Umma ta riƙe ƙugu tace "malama ban hanya zan wuce", ko kallonta Umma ba tayi ba ta cigaba da abinda take, idan ba iskanci ba ga isasshiyar hanya nan da zata wuce ta shiga banɗakin amma sbd rashin mutunci wai sai ta inda Umma ke zaune zata wuce, har wani girgije girgije take tace "wllh ko a matsamin ko na bi tako ina ma, mutum da gidan ubansa anzo an baza shirgi ta ko ina, can an zube wake nan kuma an baza gwangwanaye, a matsa min ko in taka in wuce..", da sauri Sa'adatu ta waiga jin ana buɗe sakatar ɗaki, Naseer ya fito daga ɗakinsu fuskarsa a haɗe yace "waye yake mgana a tsakar gidan nan?", simi simi Sa'adatu ta kewaye Umma ta wuce toilet tana ƙunƙuni, Naseer ya koma ɗakinsu yana ƙwafa, don aikinsa na kwana ne wllh da sai ya gyarawa marasa kunyar yaran nan zama, tin jiya ma yaso tafiya amma bai tafin ba sbd Baba yace ya jira yau masu neman auren Nabilah zasu zo, Umma ta ajiye soson hannunta zuciyarta na mata zafi, ya za ai yarinya ƙarama ta giggilla mata wnn rashin kunyar, kawai sai Hajar ta faɗo mata, tabbas da Hajar na nan Sa'adatu bazata ci bulus ba saita mayar mata da martani, ynxu tinda babu Hajar akanta za suyi durango knn, daman Maimuna ta fara addabar Sabrah da ƙeta da mugunta. Da yamma Naseer ya shigo gida yana kallon Umma yace "Umma ki bada tabarma inji Baba", Umma dake tankaɗe tace "tom" ta tashi tana kaɗe hannunta ta shiga ɗaki, babu jimawa ta fito da tabarma ta basa, Maama da ta fito daga kewaye ta bi Naseer da kallo har ya fita, After like 20mins Baba ya shigo gidan tare da Naseer, Naseer ya miƙawa Umma tabarma yace "gashi Umma", amsa tayi ta shiga da ita ciki, Baba ya dubi ƙofar ɗakin Maama yace "ina uwar Nabilah", fitowa Maama tayi tana riƙe da labule tace "gani..", Baba yace "Alhmdllh an kawo kuɗin auren Nabilah gasu nan aljihu na..", Maama tayi kasaƙe don bata taɓa tunanin kuɗin ƴarta aka kawo ba amma aka zauna a tabarmar Umma, Maama tace "Amma an yimin adalci knn a matsayina na wacca ta haifi Nabilah", Baba yace "toh ko ke zaki fita ki amso kuɗin auren ne...?", a fusace Maama ta koma ɗakinta zuciyarta na zafi, Baba ya sanar da Umma abinda ya faru ita kuma tayi masa Allah ya sanya alheri. Maama ta kalli Nabilah da take linke kayanta tana jerawa cikin wardrobe tace "ba dai wnn matsolon bane ya kawo kuɗin aure...?", Nabilah ta saukar da kanta ba tace komai ba, Maama ta hangame baki jikinta har ya fara rawa tace "mgana nake miki kika wani sunkuyar da kai sai kace munafuka..", Maimuna tace "Maama dama kin dena ɓaɓatu don wllh shine, Tanimu mai pachi ba", Maama tace "kar dai kice min Tanimu da yake zaune bakin titi mai pachin tayar motoci", Maimuna ta tuntsire da dariya tace "shi fa", a fusace Nabilah tace "Eh shi ɗin zan aura ina ruwanki, ke zaki zauna min dashi iye, bana son shisshigi da kwala kai a faranti", Maama ta shiga tafe hannaye tace "Annabilatuwa ashe ba ki da hankali da tunani, ni kuka kai juyayi kika jajiɓowa kanki, ke mahaukaciyar inace..?", Nabilah ta zumburi baki tace "nidae ina sonsa a haka.. ai gwara ma ni an san sa kuma yana zuwa gida, itafa Maimuna ko layin gidan nan bai taɓa zuwa ba...", Maama ta katseta da faɗin "kin hau fel waya kin diro, shi wnda yake son Maimuna ba mai kuɗi bane, uban me zai haɗasa da layin nan ya shaƙi ɗoyin kwata da maƙaƙin hammatar su Iliya mai awo..", Nabilah ta ajiye kayan hannunta ta bar ɗakin da sauri, Maama ta cigaba da jaraba ita lallai Nabilah ba zata auri Tanimu ba, Sa'adatu kam ko ta tafasa sauke ba tace ba don ba shiri suke da Nabilah ba. ★Murɗa handle din ƙofar office din tayi kafin ta shiga da sallama tana tafiya like a cat, ya ɗaga kansa ya kalleta sai kuma ya haɗe gira, daga lokacin da yazo zuwa ynxu ta shigo office dinsa a karo na uku knn, kuma duk shigowar da zatay saita fesa different turare don haka da different ƙamshi ta shigo a ynxun ma, fuskarta a sake sai kace za tayi murmushi ta ƙaraso ciki ta ajiye file din hannunta kan table, a fakaice Nurain ya kalli file din yace "my secretary will do that", Ruqayyah ta dubi mug din coffee da ta ajiye masa tin shigowarta na farko, ta leƙa mug din tace "Amm baka sha Coffeen ba ai, alright sai mu canza brand tinda dearest baya son wnn..", tana gama faɗin haka ta ɗauki mug din ta nufi ƙofa tana tafiya kamar tarwaɗa, sai 3 Nurain ya bar hospital din kuma daga nan fita sukay da Farooq, ba shi ya koma gida ba sai takwas na dare, direct sama ya haura ya wuce part dinsa, after yayi refreshing kansa wajen ƙarfe sha ɗaya ya sauka ƙasa ya shiga kitchen ya haɗa Coffee, daidai inda ta jingina da cabinet jiya ya ringa kallo, to ko yau ya akay da Aljanu tinda yaga alamar ta shigo kitchen din, yana gama haɗa coffee din ya fita, bayan ya haura sama ya tsaya yana kallon ƙofar room dinta, har ya kai hannu zai murɗa handle sai kuma ya fasa, shi kaɗai yasan yadda yayi controlling kansa jiya, so solution dinsa ɗaya kuma shine to stay away from her, da wnn tunanin ya wuce room dinsa. haka nan kam acikin kwanaki uku bai saka Silly girl a idonsa ba, deep down his mind he want to see her amma action dinta kaɗai ma sosai suke jefasa a halin da bai san inda zai nemo solution ba, ranar Asabar da daddare suka tafi Airport tare da Farooq zasu taho dasu Hajiya da jirginsu yake daf da sauka, sai ƙarfe tara jirginsu Hajiya yayi landing, Hajiya na ganin Nurain abinda ta fara tmbyarsa shine ina matarsa, a takaice ya bata amsa yace tana gida, wajen parent dinsa ya wuce yana musu sannu da zuwan da Hajiya ta hanasa da tmbyar Hajar saida ya bata amsa snn ta barsa, bayan an gama musu checking suka wuce, already Abba part dinsa ya wuce Mami ma haka bayan sun isa gida, Hajiya kam branching tayi a main palour, daman Farooq bai shigo ba suna zuwa ya tafi gida, Hajiya ta daga kai ta kalli Nurain da ya fito daga part din Mami bayan ya shigar mata da kayanta, Hajiya tace "ina matar taka ne Usuman..?", Nurain yace "ohh Hajiya nace miki tana gida fa", Hajiya tace "Auho aini da kace tana gida na sha nan kake nufi, sai kace min gidanta ba wai gida ba..", Nurain yace "toh tana can", Noor ce ta shigo da ƙaramar jakar kayanta, Nurain yace "kayan sun ƙare Noor..?", Noor tace "Eh Yaya", da haka ta nufi hanyar ɗakinta, Hajiya tace "gobe da sassafe ka kawo min ita nan ta amshi tsarabarta don duk rabin kayan da na siyo ita na siyowa, sbd itace ta taimaka min na sakata na wala a kujerar jirgi, da bata shafamin man zafin nan ba ai bazan iya zaman kujera har na daɗe ba, shiyasa da naje Saudiyyar ma duk kayan da na gani ita nake tunawa, gashi nan kam na lafto mata kaya kuma babu wnda zan bawa sai ita, Noor ce ta tayani zaɓa tinda ta fini sanin birni..", Nurain yace "Ai kam saidai su raba dasu Aysha..", katsesa tayi da faɗin "wace kuma Aishan kake nufi wai Shatu..?", Nurain yace "Eh", Hajiya ta tsuke fuska tana kallonsa ta ƙasan glasses dinta tace "ba da wanda zasu raba, idan ta Shatu zan biye da tuni ƙafata ta daɗe da ruɓewa, sam sam wnn ɗiyar ta Ummi bata temaka min wajen shafa man zafi", Nurain ya kalli tsadadden agogon dake wrist dinsa, ganin dare yayi ya tashi ya miƙawa Hajiya hannunsa yace "muje na rakaki ɓangarenki kema ki huta", Hajiya ta kama hannunsa ta miƙe snn ta riƙe sandarta da other hand din tace "Eh gsky rakani nima na yada kwankwasona karka tafi ka barni ni kaɗai nayi ƙuƙi sai kace mayya tinda kowa ya ɗaɗe, su basu yi bacci ba a jirgin ni kuma na ɗan gyangyaɗa..", yana riƙe da hannunta har saida ya kaita ɓangarenta snn ya fito, ya yiwa Maminsa sallama Abba kam tinda ya shiga part dinsa ya kwanta, ƙarfe sha ɗaya da ƴan mintina Nurain ya bar gidansu zuwa gidansa....✍️ 💛 HAJAR 💛 {68..} Washe gari ƙarfe tara da rabi Hajar ta fito daga wanka ɗaure da towel, a hankali ta zauna kan stool tana rubbing lotion, wata doguwar riga armless ta saka bayan ta gama shafe shafenta, ta fesa perfumes masu sanyin ƙamshi, a hankali ta buɗe ƙofar room dinta ta fita tana ƙarewa corridor kallo, after few seconds ta ƙarasa fita ba tare da ta rufe door ba don ba ta so tayi ƙara, walking slowly cikin sanɗa har ta kai bakin door din ɓangarensa, ko takalmi bbu a ƙafarta wai don kar aji footsteps, tafi minti biyu a tsaye kafin ta kai hannu da nufin sliding door din sai kuma ta fasa, ta ciji lower lip dinta painlessly ta kara kunne a jikin ƙofar, wani irin turo baki tayi don ba taji motsi ba, ta juya ta koma room dinta still tana turo baki, toh ko dai ita kaɗai ce a gidan ynxu ne, three days fa ba ta gansa ba ko sau ɗaya, tana barin bakin ɓangaren nasa ya buɗe ƙofa, ya ringa surveying corridorn da idanunsa amma bai ga kowa ba, shi dai he is not mistaking tabbas yaga silhouette din mutum, har ya juya zai koma ciki sai kuma ya fasa ya cigaba da kallon wajen, pointed nose dinsa ya ja don sosai ya shaƙi sassanyan ƙamshin da ya karaɗe corridor din, after a while ya juya ya shiga ciki. Hajar ta zauna kan stool dake gaban mirror tana kallon kanta, toh wai yana ina ne, tsaki tayi a fili tace "ina ruwana ya tafi space ma", hular da ta rufe gashinta ta cire ta warware jelar gashin da ta naɗe, oil hair spray da Maysha matar Hammad ta bata ta ɗauka ta feshe hair dinta dashi, after that ta jiƙa kan da hair butter snn ta fara combing dinsa a hankali, jin an buɗe ƙofa tayi sauri ta ɗaga kanta, ido huɗu sukay dashi hannunsa daya cikin pocket din sweat pant dake jikinsa, miƙewa tayi still tana kallonsa sai kuma ta koma ta zauna, kallonta yake without blinking ya wani tattare thick eyebrows dinsa, Hajar ta saukar da kanta sai kuma ta ajiye comb din hannunta kan mirror, sosai ta masa kama da baby doll sbd armless gown da ta saka da kuma black coiled hair dinta dake a warware, da sauri ya ɗauke kansa speaking with a repartee yace "idan kin gama abinda kike ki shirya zan ajiyeki can wajen Hajiya...", ba tare da ta ɗago ba tana twisting slim fingers dinta ta gyaɗa kai tace "toh", yace "idan kin shirya sai kiyi yadda na koya miki a can garin da wayar da na ara miki..", nan ma tace "toh", bai ko ƙara 1sec ba ya juya ya fita ya rufe mata ƙofar, lumshe idonsa yayi yana sauke ajiyar zuciya sai kuma ya shiga ɓangarensa, saida Hajar ta gama combing din gashinta snn ta sauka downstairs ta shiga kitchen, sharp sharp ta dafa abinda za taci, bayan ta gama cin abincin ta wanke utensils din da tayi amfani dasu ta bar kitchen din, tana shiga room dinta ta bude wardrobe zata zaɓi kayan da zata saka, wata riga da skirt na atampa ta ciro, cikin kayan da Mami ta ɗinka mata ne lokacin da zasu dawo gida, kana ganin atampar kasan me tsada ce, ita dai tunanin ta kar taje sunyi mata kaɗan tinda riga da skirt ne, saidai kuma da ta saka suka mata chas chas harda space sosai a skirt din, har da pendant necklace mai dutsen white pearl ta saka, veil wnda ya dace da zanen flower din atampar ta saka kuma wnda ya rufe mata jiki sosai, ta ciro wayar da tayi plugging a charge babu wani ɓata lokaci ta shiga call log tayi long pressing 1, number na appearing tayi dialing ta kara a kunne, tana fara ringing ya katse few seconds saiga kira ya shigo, picking tayi da sanyin murya tace "Aslm..", can ƙasa taji muryarsa ya amsa, ta juya lulu eyes dinta tace "na shirya", a takaice yace "Ohk.. ki jirani a compound" da haka ya katse kiran, Hajar ta saka wayar a handbag dinta kafin ta tashi ta fita, yana kallon lokacin da ta fito ta glass door din ɓangarensa, tana sauka downstairs ya fito yabi bayanta, saida ya tabbatar ta fita daga palour snn shima ya sauka, bayan ya rufe main door ya zura key din a pocket, tsaye yayi yana kallonta babu ko ƙiftawa, tana tsaye a parking lot waiting, walking majestically ya isa parking space din ya buɗe motar da zai shiga, tana ganin ya shiga itama ta zagayo ta buɗe front seat ta zauna, tini hancinta ya ringa perceiving pure men scent dinsa mai azabar ƙamshi, Nurain ya sauke handbrake ya fakaice kallonta da wutsiyar ido, can after a while yace "saka mayafinki a head", ta ɗan kallesa ba tare da ta yi abinda yace din ba, fuskarsa a murtuke tamau ya kalleta yace "ba kiji me nace ba..", ba musu ta janyo veil din ta saka a ka sai kuma ta kalli window ta ɗaure fuska, har suka isa gidan babu wnda yace da wani ƙala, ita kam Hajar daman tinda ta kalli window ba ta sake juyowa ba, tinda ya ganta da veil yake jin wani suya a zuciyarsa, saidai kuma yasan inda za su zo bbu maza and glass din motarsa tinted ne, yana gaba tana biye dashi suka shiga main building din gidan, sosai Mami taji dadin ganin Hajar, da ladabi Hajar ta zaune ƙasan carpet ta gaida Mami snn ta mata barka dawowa kanta a ƙasa, Mami ta amsa mata da fara'a tana kallonta da kyau, ba taga damuwa a tare da ita ba hakama jikinta, Hajar ta gaida Sakeena da itama take zaune a palour tare da Mami, Sakeena tace "lfy lou alhmdllh Hajar.. ya gida..?", Hajar tace "Alhmdllh", Sakeena tace "toh masha Allah", bayan minti uku Hajar tace "zan je wajen Hajiya..", Sakeena tace "Okay toh wajen iron lady zaki..?", Hajar ta gyaɗa kai tace "Eh" da haka ta tashi ta fita walking gently, Sakeena tace "Mami yarinyar nan na da nutsuwa wllh", Mami tayi murmushi tace "sosai ma kuwa ni na gani da ta zauna a gidan nan", Nurain ne ya fito daga bedroom din Mami don suna shigowa tare da Hajar ya shige ciki. tinda Hajar ta shiga wajen Hajiya ta gaisheta tayi zamanta a can, Noor ce ta shigo tana ganin Hajar tayi murmushi tace "ynxu Yaya take gyamin kinxo..", Hajar tayi murmushi tace "An dawo lfy..?", Noor tace "alhmdllh", Hajiya na kallon Noor tace "wai ni waye zai buɗe min wnn jakar da aka nannaɗe min ita da leda da gam, duk anbi an ƙadabaibaiye min kaya sai kace na sata, daman Sa'udiyyar nan basu da yarda sam, ka bar ganin fatarsu jajir zuciyar ɓaka ce, inba baƙin hali ba meye na rufe min jaka salon dai sai an baka wahala kafin ka buɗe", Noor tace "Iron lady ba sai kin koma can gidan zaki buɗe jakan ba", Hajiya tace "Wane can gidan kuma... ga mai rabin kaya nan tazo mai ake jira, marmaza ki kirawo min wanda zai farke jakar nan na fitar mata da abunta..", Noor tace "bari na kira miki Yaya ya buɗe miki", Hajiya tace "Wai Usuman, toh ai kar naje ya gwada ƙarfi ya tsinke hannun jakar na riga na yiwa Asabe alƙawarinta", Noor tace "Iron lady mene kuma na tsinka hannun jaka kawai fa ledan za'a ɓare, nima don aiki nake a kitchen da ni zan cire miki", Hajiya tace "Au toh..", door aka buɗe Nurain ya shigo da sallama, Hajiya tace "shknn ma ba sai kin kirasa ba gashi nan yaxo", Nurain ya ƙarasa shigowa ciki ya zauna kan Sofa, Hajar na ɗaga kanta sukay ido huɗu dashi, da sauri ta miƙe tabi bayan Noor wacca ta fita ynxu, Noor ta juyo ta kalli Hajar tace "au tasowa kikay..?", Hajar tace "muje na tayaki aikin", tare suka wuce kitchen, Noor ta buɗe oven ta ciro cookies din da ta zuba tace "saura ƙiris ya babbake Hajiya ta riƙeni da surutu", Hajar dai tayi tsaye a kitchen din tana ta kallon Noor dake aikin flour, ta kwaɓa wancan ta soya wancan ta gasa wancan, ita dai tinda ba tasan me za tayi ba saidai ta temaka mata da kneading dough, suna cikin aikin Sakeena ta shigo, tana kallon Noor tace "An ɗora lunch..?", Noor ta girgiza kai tace "Garban bai dawo ba..", Sakeena tace "Alright plxx yana kawo perishable stuff din sai a ɗora", Noor tace "Sure", Sakeena ta kalli Hajar tace "you are here dear..?", Hajar ta gyaɗa kai tana cigaba da kneading dough din da take, Sakeena ta bar kitchen din bayan ta ɗebi doughnut da cookies, few minutes aka kawo perishable stuff din, mai aiki ce ta shiga dasu ta ringa ajiyewa a inda ya dace, Hajar ta matsa gaban sink ta wanke hannunta tace "me za a dafa..?", Noor ta ware ido tace "ke za kiyi girkin..?", Hajar ta ɗauki clean towel tana goge hannunta ba tace komai ba, Noor tace "Anything since you are the cook", Haɗaɗɗen Abinci mai rai da lafiya Hajar ta girka, tana gamawa Noor ta fara serving, ta zubawa Abba da Mami a different warmers, ta zubawa Hajiya potatoes porridge da Hajar din ta mata. Da yamma Mami na zaune main palour tana attending Son din ƙawarta Haj Fati, Noor ta fito daga part din Hajiya ta gaida baƙon dake palour tare da Mami, Mami tace "Noor kawo masa abinci da drink..", yace "A'a alhmdllh zan wuce ne ma..", Mami tace "A'a ka jira", Noor ta tashi ta shiga kitchen, ruwa da lemo sai snack din da ta yiwa boyfriend dinta da zai zo kawai ta ɗebar masa, don ko ƙwayar abinci ba a rage ba, an cinye tass, Nurain kam tana ganin plate biyu yaci, Noor na ajiye trayn ruwa da lemon ta wuce room dinta zata shirya zuwan saurayinta, Nurain ya sauko daga stairs yana ɗabi'arsa na jan riga, ganin Mami zaune palour tare da guest ya dakata, hannu ya miƙawa baƙon sukay musabaha, Mami tace "ka ganesa...?", Nurain yace "Sure" sai kuma ya dubi baƙon yace "Ahmad right..?", yace "yeah", Nurain har zai koma sama sai kuma ya shiga ɓangaren Hajiya, kan rug ya tarar da Hajiya ga Hajar gefenta tana yanka mata papaya, Nurain ya shafa kansa yace "ke da kika ce kin daina shan ta", Hajiya tace "Ai kaɗan zan sha yadda ba zata gundureni ba", yace "Ohk" sai kuma ya fakaici kallon Hajar da kanta ke ƙasa tana yanka papaya, key din mota ya ciro daga pocket ya jefar kan carpet daga kusa da ita, da wutsiyar ido Hajar ta kalli key din, Nurain ya duƙa kamar zai ɗauki key din ya rage murya sosai yadda Hajiya baza taji ba yace "karki fito palour" da haka ya miƙe ya fita, ko yanka uku na papayan Hajiya ba tasha ba tace "fita da ita ƴar nan ta gundureni wllh", Hajar tace "tom", har zata fita sai kuma ta dawo ta ajiye plate din papayan ta rufe, Hajiya tace "du Allah fita da ita", ba yacca Hajar ta iya haka ta ɗauki plate din ta fita, saida tazo tsakiyar main palour snn ta lura da baƙon dake zaune kan Sofa, shi kaɗai ne a palourn Mami ta shiga ciki zata ɗauko masa saƙon da zai kaiwa Mother dinsa, yana ɗago kansa daga latsa wayar da yake sukay ido huɗu da Hajar, sosai zuciyarta ta buga ganinsa a nan ɗin, ya ringa kallonta babu ko ƙiftawa, Nurain dake tsaye can ƙarshen stairs yana kallon palourn ya wani irin murtuke fuska, saida eyebrows dinsa suka haɗe, da sauri ya fara sakkowa daga stairs din, kafin ya kawo ƙasa Mami ta fito daga part dinta da paper bag a hannunta, Hajar ta saukar da kanta ta wuce kitchen da sauri, Ahmad ya bita da kallo wnda ya sake fusata Nurain dake tsaye daga bakin stairs, har wani yaji yaji zuciyarsa ke masa, innalillah babu fa veil a jikinta ya subhanallah, Ahmad ya yiwa Mami sallama bayan ya amshi bag din da ta basa, ya yiwa Nurain ma sallamar wnda ya amsa sama sama da haka ya wuce, Mami ta kalli Nurain ganin yadda ya ɗaure fuska tace "Ah ah Son this is not you, why are you frowning...?", ajiyar zuciya ya sauke ya shafa kansa, Mami tace "Come" da haka ta tashi ta shiga part dinta, bayanta Nurain yabi yana kallon ƙofar kitchen. After 20mins Hajar na zaune palourn Hajiya duk jikinta yayi sanyi sbd ganin Ahmad da tayi, toh ko dai ɗan uwansu ne, ƙofa aka buɗe, Nurain ne ya shigo har lokacin fuskarsa ba ta saki ba, yace "we are going home now", ta gyaɗa kai ba tace komai ba, ya ɗaga murya da ɗan tsawa yace "ba kiji bane..?", ba Hajar ba har Hajiya dake gyangyaɗi saida ta farka a firgice, Hajiya ta micincina ido tace "waye wnn ya ɗauki haƙƙina..?", Nurain ya ajiye numfashin da yafi kama da huci yace "Am waiting outside saura ki daɗe" da haka ya fita yayi banging door, Hajiya ta saki baki tace "bari ubanka ya dawo wllh saina gaya masa abinda kamin, ji fa fuskarsa sai kace tsohon hadari, wai yaushe Usuman ya zama haka ya mayar da fuskarsa ta Sa ƙarfi da yaji". Hajar dai tini ta yafa veil dinta ta ɗauki hand bag dinta, Hajiya ta dubeta tace "ke kuma lfy kike saɓa jaka..?", Hajar ta duƙa tace "tafiya za muyi Hajiya..", Hajiya ta buɗe baki sai kuma ta rausayar da kai tace "toh ai shknn, shiga ƙurya za kiga wasu ledoji gaban madubi ki ɗakko babbar ki kawomin..", Hajar tace "tom" da haka ta tashi ta shiga bedroom din Hajiya, babu jimawa ta fito tana jan ƙatuwar ledar da Hajiya tace ta ɗakko, Hajar tace "gashi Hajiya", Hajiya tace "Ai naki ne ƴar nan tsarabarki ne..", Hajar was shocked ta ma rasa me za tace, wnn uban kayan duka nata ne, ko da ta fara yiwa Hajiya godiya katseta tayi tace "A'a ƴar nan bafa maula kikay ba, lokacin da kike shaƙe yajin man zafi da loko babu wnda yaji babu wnda ya gani", Nurain ya sake shigowa ya tsaya daga bakin ƙofa yace "ke!!..", Hajiya tace "ka fita idona Usuman ya zaka ringa firgita ƴar mutane", yace "Hajiya cewa nayi fa ta fito..", da haka Hajar ta yiwa Hajiya sallama ta fita, ɓangaren Mami ta shiga don yi mata sallama, nan ma dai Hajar da leda ta fito wcca Mami ta bata, saida Hajar ta gayawa Mami cewa Hajiya ta bata kaya, tana fitowa Nurain dake tsaye main palour ya sunkuci ledar da ta ajiye a palourn wcca Hajiya ta bata yayi waje with speed, ita dai tabi bayansa walking gently, ikon Allah da kariyarsa ce ta kaisu gida, don gudun da Nurain ya ringa falfalawa ba a cewa komai, Hajar taga izaya iya izaya kuma taga ƙarshen walagigi a mota, a palour ya dangwarar da ledar da ya temaka mata da ita ya haura sama, Hajar ta taɓe baki ta bisa da kallo, mutum sai kace mai Junnu ko me akay masa oho, ita dai taja ledarta ta haura sama abinta. bata sake fitowa ba har dare yayi, bayan tayi sallar isha'i ta shiga wanka, tana fitowa ta tarar da missed calls from Anty Jamilah, ta zauna gefen gado ta shiga calling back, da sauri ta kalli door jin an buɗe, ta ajiye wayar ba tare da tayi ending call din ba, hijab dinta ta fara wawake zata saka, ya shigo ɗakin girarsa a haɗe yace "A can gidan me nace miki akan fitowa palour...?", turo baki tayi tace "ni ka dena shigo min ɗaki kuma ka dena kallona babu kyau haram ne" da kyar ta ƙarashe tana kallon hijab dinta dake can nesa kuma so take ta ɗakko, kawai ganinsa tayi a gabanta, ba ƙaramin bugu zuciyarta tayi ba ta tashi zumbur ta ja da baya, ganin yadda ya haɗe fuska ta buga ƙafarta a ƙasa tace "wai ni na maka laifi da zaka zo ka huce a kaina, ai Hajiya ce ta aikeni...", ya katseta da faɗin "da Hajiya ta aikeki sai akace ki fito palour without veil or hijab, ko baki san kinada aure ba...", wani kallo ta wurga masa tace "Aure kuma.. wace take da auren..?, toh saidai wata ba ni ba don ni ban taɓa aure a rayuwata ba", tsuke idanunsa yayi yace "really..", tace "yess kar kaga don kace na saka mayafi a ka na saka hakan baya nufin komai..", ba ta ankara ba sai gani tayi hasken ɗakin ya ragu, tana ganin ya taho inda take ta wani zaro ido, da gudu ta kyalla da nufin shiga bathroom amma ina don tini ya fixgota gami da haɗata da jikin wardrobe, ta tsala ihu ta fara turesa da duka hannayenta har da ƙoƙarin cixo, kawai saukar warm lips dinsa taji a nata, tsabar shock da firgita sai ta dena tura san, after few seconds ta dawo daga duniyar daskarewar da tayi, ta daddage da iya ƙarfin da Allah ya bata ta hankaɗasa, idan yayi gezau toh tabbas ya raba lips dinsa da nata, da hannu ɗaya ya riƙe duka hannayen da take kokawar dasu, ɗayan hannun kuma ya zare ribbon din da ta ɗaure gashinta kafin ya nutsar da yatsunsa cikin lallausan gashin nata still kissing her passionately, rawar da jikinta yake ce tasa towel dinta da daman ya fara sakwarkwacewa yabi jikinta ya faɗi ƙasa, da kyar Nurain yayi controlling kansa ya raba lips dinsu, sai a lokacin Hajar ta samu wani chance din kurma ihu, ƙoƙarin zubewa tayi a ƙasa yayi saurin ɗaukarta calak ya ajiyeta bisa gado, tsoron kar ya kalleta a haka yasa tayi saurin rumgumesa ta fashe da kuka tace "wayyoh Allahna na shiga uku na lalace, Ummana", Hajar ba tasan cewa wani ruwan ta janyo ba, Ehen a yau dai an fitar da part one na raini, bai kyaleta ba saida ya tabbatar ya firgita ƴar farka, a hakan ma saida ya kai zuciyarsa nesa don bai mata komai ba, tamkar zata shiɗe haka take jan shessheƙa, ganin zata sauka daga gadon ya janyota jikinsa a kasale, ta sakar masa kuka da dasasshiyar muryanta, bai saketa ba ya kuma rungumeta, da sauri ta ɓoye fuskarta a ƙirjinsa tana shessheƙa, ya ɗora kansa a kan nata hugging her tightly, lumshe idonsa yayi yana shaƙar ƙamshin da gashinta ke fitarwa, ya sauke ajiyar zuciya kafin ya rage murya a saitin kunnenta yace "har ynxun ma baki da auren Silly girl?"......✍️ 💛 HAJAR 💛 {69..} Sam Hajar taƙi ta buɗe idonta bare ta fahimci me ya faɗa, jikinta har rawa yake cause ba tayi tsammanin hakan da yayi mata ba, why did he touches her body that way, sosai yake jin ydda jikinta ke kyarma, tsoron da yake so taji din taji knn, a daidai saitin kunnen nata ya sake mgana yace "ki bani amsana Silly girl... are you still single...?", nan ma dai ta masa banza ta cigaba da shessheƙa a hankali, yace "Alright since you don't have an answer now shima na bar miki bashi, next time dole sai kin bani amsana", yana gama faɗin haka ya saketa ya tashi daga kan gadon, ya nufi door yana buttoning rigar Pajamas dake jikinsa, Hajar na jin fitarsa ta wani irin mirgina ta shige cikin duvet ta rushe da kuka, sabo fil abinda ya mata yake yawo a brain dinta, gashi skin dinta ma ƙamshinsa take bare ta yage ta cillar da ita ko ta samu ta manta, da kyar ta iya miƙewa ta nannaɗe jikinta da duvet ta ɗauki kayan baccinta ta saka, komawa tayi ta kwanta ta dunƙule waje ɗaya sai kace mage. Da asuba ta tashi tayi sallah ta sake komawa ta kwanta, har ƙarfe bakwai idonta biyu bata koma bacci ba, ji tayi an buɗe ƙofa ai kam ta runtse idonta da sauri, walking gently ya ƙarasa shigowa ya isa bakin gadon, kallon fuskarta ya ringa yi sai kuma ya duƙa ya kalli eye lashes dinta da suke rawa, bai san lokacin da wani murmushi ya kufce masa ba ya juya ya bar ɗakin ya rufe mata ƙofa, downstairs ya sauka don daman fita zaiyi yanada appointment da safe daga nan kuma zai wuce hospital. Ƙarfe sha biyu da few minutes Hajar na tsaye gaban sink a kitchen tana wanke utensils da tayi amfani dasu, tana gama wanke wanken ta ciro vegetables daga fridge za tayi blending, stew mai ɗan yawa za tayi saita ajiye a fridge ta ringa amfani da ita na 2days, tana wanke pot da za tayi amfani da ita taji ƙarar bell, fitowa tayi daga kitchen din taje ta buɗe ƙofar, ta waro ido ganin Anty sai kuma ta rungumeta tace "Anty sannu da zuwa", a takaice Anty tace "yawwa", kan Sofa Anty ta zauna tana bin palourn da kallo, Hajar ta duƙa gabanta tace "Anty ina yini", Anty ta amsa a fixge, Hajar ta ɗago kanta sai kuma ta zauna kan kujera tace "yasu Humairah...?", nan ma dai a fixge Anty ta amsa mata, tini Hajar ta fara shan jinin jikinta a hankali ta tashi ta nufi kitchen, Anty ta bita da kallo ganin yadda ta canza, ba iya fatarta ne ya canza ba har jikinta, tayi wani luwai luwai abinta alamar dai hankalinta a kwance yake, babu jimawa Hajar ta fito ta ajiyewa Anty ruwa da lemon da ta ɗakko, Anty tace "sannu Hakima", Hajar dai ta saukar da kanta ba tace komai ba, Anty ta zuge handbag dinta ta ciro wayarta, tana kallon Hajar ta ajiye mata wayar daga gefenta, da sauri Hajar ta ɗago kanta jin muryanta na fitowa daga cikin wayar, conversation dinta ne dashi na daren jiya, muryarta raɗau tana cewa kar ya sake kallonta haram ne, sau ɗaya muryarsa ya fito inda yake cewa ba tasan tanada aure ba ta fito without veil or hijab shima ɗin ƙasa ƙasa, sai na muryarta da ya kusa fasa speaker din wayar tana cewa ita sam ba tada wani aure, daga nan voice din ya ƙare kuma daman anan Anty ta katse kiran, Anty ta ringa kallon Hajar da ta sunkuyar da kai kamar munafuka tace "Daman baki da hankali Hajar, a gidan aure akwai wani abu da yake haram ne, ko ba a kan idona wnn abun ya faru ba inaji nasan cewa da mijinki kike, Islamiyyar da kika je ta tashi a banza a wofi knn, wancan allon naki da ke sargafe ɗakin Umma ba shi da wani amfani, ko a Islamiyyar naku hka aka koya miki...?", Hajar tayi shiru ba tace komai ba zuciyarta na bugu, Anty ta daka mata tsawa tace "Amsa min tambayana shashasha kike wani sunkuyar da kai sai kace ta Allah bayan ga rashin hankalin da kike giggillawa", ba shiri Hajar ta girgiza kai tace "A'a", da faɗa Anty tace "ba haka aka koya miki a Islamiyyar ba knn naki salon iskancin ne a haka, ashe abinda kike aikatawa a gidan mijin naki knn, wnn wane irin hauka ne ka ringa cewa mijinka haram sbd shirme, toh ynxu kallon me zai miki da kika aikata haka, kai tsaye zai kiraki da jahila wacca ba taje Islamiyya ba, bayan wnn ma baki amshi ƙaddara ba, idan da kin amshi ƙaddara kya aikata haka a gidan aurenki, aure an wuce wata ɗaya wata biyu na uku ma an kusa fita daga cikinsa amma kin ƙi ki saukar da kanki, Mijinki na faɗa kema kina faɗa sbd baki da hankali har wni cewa kike baki da aure, wllh tllh Allah ya temake ki zuciyata tayi sanyi da ace jiya na sameki da saina kwakkwaɗa miki mari, kuma dman daga nan wajen Umma da Baban ki zan wuce na wassafa musu abinda ke faruwa kinga sai su san wace irin tarbiyyar kike nunawa a gidanki don wnn tarbiyyar ba nasu bane...", a gigice Hajar ta zamo daga kan kujerar ta fashe da kuka tana yarfe hannu tace "na shiga uku don Allah Anty ki rufamin asiri..", Anty ta murtuke fuska tace "Ja can mara kunya fitsararriya waye zai rufa miki asirin bayan ke kina nan kina tona mana namu asirin", habawa ai a gigice Hajar ta riƙe legs din Anty tace "wayyo Allah dan Allah Anty kiyi haƙuri..", Anty tace "sakarmin ƙafa ko na mangareki, haƙurinki na banza haƙurinki na wofi ni ina ruwana da haƙurin ki, can dai kije ki riƙe carbi ki nemi gafarar Ubangiji dana mijinki don zunubin da kika kwasarwa kanki ba kaɗan bane", saida Anty ta yiwa Hajar wankin babban bargo, ciki da bai ta wanketa fess da sosa da sabulu, Hajar na shessheƙar kuka tace "Anty dan Allah kiyi haƙuri wllh na dena", Anty tace "Allah yasa iya abinda naji kike aikatawa babu wani wanda ban sani ba, toh a ydda kike masa mganar nan gatsal Allah yasa kina dafa masa abinci bare ta kai ga gaisuwa ko sannu da zuwa, ko kina yi ne...?", Hajar ta duƙar da kanta hawaye na zuba cheeks dinta, Anty tace "innalillahi wa'inna ilayhirraji'un abin naki is too much Hajar, tabarbarewar yayi yawa, gsky wnn mijin naki ma mai haƙuri ne wllh don ba ko wane namijin zaka yiwa wnn haukan ya ɗauka ba, da tini ya baki red card ya kaɗaki gidanku, kinga idan kika koma gida sai kije ki zauna dasu Sa'adatu ku ɗora daga inda kuka tsaya, kuma kinci baya a rayuwa don duk macen da tayi sagegeduwa aurenta ya mutu haka nan saddan wllh taci baya, ke bazaki duba liɗifin da Allah ya miki ba, kalli fa gidan da Allah ya baki mai yalwa da wadata, amma kin daddage kina shirin saka ƙafa kiyi fatali da damarki, wllh da jiya na sameki da saina bibbigeki..", Anty na gama faɗin haka ta ɗauki wayarta ta saka a jaka ta miƙe, tini Hajar da hannunta yayi jajir tsabar mutssukasan da tayi ta miƙe har lokacin kuka take tace "Anty dan Allah kiyi haƙuri ki rufamin asiri wllh na dena", Anty taja wani dogon tsaki tace "Abin naki yayi yawa Hajar, saidai kici ki kwanta ko sharar arziƙi ba kya yi a gidan naki ma...", Hajar tace "wllh ina yin aiki Anty ina shara...", katseta Anty tayi da faɗin "rufe min baki da murya sai kace tsanya, ƙarya kike ba kullum kike sharar ba", with serious note Anty tace "this is the first and the last da zan sake zuwa gidan ki na tarar da shirme, wawuya kawai" da haka ta nufi door tana tafiya da sauri, Hajar tabi bayanta tana kuka ta buɗe baki za tay magana knn Anty tace "karki kuskura ki fito, ni da ke munyi hannun riga duk ranar da kika nutsu kika gyara halinki ma shirya...", Anty tayi tafiyarta bayan ta rufe ƙofa, Hajar ta sulale ƙasa ta fashe da kuka, ai da an tsaya anji ta bakinta ai shima yanada laifi, me yasa zata ringa dafa masa abinci bayan yace ita ba matarsa bace and she will never be, me yasa idan ya taɓata baza tace haram ba tinda yace ita ba matarsa bace, me yasa zata ringa gaishesa bayan yace ita ba matarsa bace, tinda bai ɗauketa matsayin matarsa ba itama ba taga dalilin da yasa zata ɗaukesa matsayin miji ba. After 10mins ta tashi ta haura sama zuciyarta na zafi, Abincin ma da take mararin dafawa duk ya fice mata a rai. ★Nurain na fita direct warehouse dinsa ya wuce don kayansa da yayi order from China sunxo, shi dai yana tsaye sai shiga ake da kayan, gaba daya mind dinsa ma ba a wajen take ba ya lula wani planet din, moment din daren jiya ne ya ringa yawo a brain dinsa, har aka gama sauke kayan tass snn ya shiga ya duba, sai ƙarfe tara da rabi ya isa hospital kuma immediately ya fara attending patient dinsa, knocking door akay ya bada umarnin shigowa don shi ya zata next patient ne zai shigo sai yaga akasin hka, kallo ɗaya ya mata ya ɗauke kai, Ruqayyah ta ƙarasa shigowa tace "good morning Dr", a takaice yace "morning what's up...?", tayi twinkling eyes dinta kafin ta ajiye masa wani envelope a gabansa, kallon envelope din yayi yace "this is not part of your work A Nurse", tace "yeah just to see you" da haka ta juya ta fita, few patient Nurain ya sake gani kafin yasa Haleema ta sallami ragowar don Surgery zai shiga next, walking gently Nurain ya shiga surgery room din, after ya saka hands gloves da nose mask ya tsaya a postion dinsa, Ruqayyah dake tsaya a right dinsa da tray na instruments a hannunta ta miƙa masa scalpel, Nurain ya amsa making sure bai taɓa hannunta ba, lokaci guda brain dinsa ta amsa, moment din da tin safe yake dakonsa ne ya shiga kai kamo a head dinsa, ya lumshe idonsa yana ƙoƙarin yakice abin amma he can't, the way she reacted and cried like a baby ne yafi tsaya masa, must part of it kuma her soft body and lips, her soft hair that's so good in brushing, ganin almost 5mins da basa scalpel bai fara aikin ba Khaleel yace "Dr", Nurain ya sauke ajiyar zuciya ya ajiye Scalpel din, yana kallon Khaleel yace "please call Dr Marwan instead" yana gama fadin haka ya kwaɓe nose mask din fuskarsa snn ya fige cap da ya rufe cikakkiyar sumarsa itama, saida ya cire hands gloves yayi disposing snn ya fita daga surgery room din, Ruqayyah tabi bayansa da kallo wondering me ya hanasa surgery din, wnn shine first time da taga ya fasa surgery, yana komawa office dinsa ya saka laptop dinsa a briefcase da sauran tarkacensa ya fita harabar hospital din, with speed yake driving zuwa gida, a daidai wani roundabout wayarsa ya fara ringing, yana dubawa yaga Mami ke kiransa, picking yayi ya kara a kunne gami da yin sallama, Mami ta amsa sallamar tasa tace "idan ka taso aiki kaxo gida", jimm yayi sai kuma yace "Sure Mami", Mami tace "Okay" da haka ta katse kiran, haka nan Nurain ya juya kan motar ya ɗebi hanyar gidansu, yana zuwa gidan ya shiga part din Mami, mgana sukay da Mami akan auren Noor da ya taho, ranar Thursday ma za a kawo lefe, daman tintini an kawo kuɗinta two years back, zuwa lokacin da ta gama karatu shi kuma mijin ya dawo daga abroad, main palour Nurain ya fito bayan sun gama mgna da Mami, Noor dake zaune palourn tana cin spicy Noodles tace "Yaya ina yini", ya amsa gaisuwar nata yana kallon part din Hajiya yace "Iron lady na nan..?", tace "yeah", part din Hajiya ya shiga da sallama, zaune ya tarar da ita kan rug ga jakar kayanta a gefe, tayi shigarta na asun da asun, Hajiya ta dubi mai aikin gidan dake tattare kwanukan abinci tace "yauwa ke Lauriyya idan kin fita da kwanukan nan sai ki biya kice da driver ya cigaba da wasshagare walle dinsa Usuman ya kaini...", mai aikin tace "tom Hajiya", Nurain ya haɗe gira yace "wane Uthman din..?", Hajiya tace "ga ka nan a tsaye ƙerere da kai nake..", yace "Ah ni gida zan tafi fa", tace "idan ka ajiyeni ka zarce gidan naka..", ajiyar zuciya Nurain ya sauke yana jin dama bai shigo ba, Hajiya tace "in taso mu tafi ne..?", girarsa a haɗe yace "Nope ina zuwa", da haka ya juya ya fita, room dinsa na gidan ya shiga, saida yayi wanka ya canza kaya snn ya fito, ya saka Noor ta zubo masa abinci yaci, saida yaje mosque yayi sallar la'asar kafin ya waiwayi Hajiya, tinda suka fito compound take zabga masa mitar ya shanyata kamar kayan wanki, shi dai baice mata uffan ba ya temaka mata ta shiga motar, with minimum speed yake driving har ya ajiye Hajiya a gidansu Farooq, ko shiga gidan be yi ba ya juya sbd he was so eager ya koma gida, gudunsa ya falfala a mota zuwa gida tinda ya ajiye iron lady, yana parking motar ya fito ya nufi entrance ya shiga ciki, da bibbiyu ya ringa haura stairs, kai tsaye ya buɗe ƙofar ɗakinta, ido huɗu sukay tayi sauri ta janye nata bayan zuciyarta ta buga, ajiye spoon din hannunta tayi ta miƙe afujajan ta shiga bathroom ta banke ƙofar tana turo baki, Nurain ya shafa kansa a bit relief after seeing her ya bar wajen, ƙarfe takwas na dare da few minutes Nurain ya dawo daga masallaci sallar isha'i, a palourn downstairs yayi zamansa bayan yayi powering TV, though ba kallon yake ba wayarsa yake dannawa, ƙarar rufe ƙofa yaji ya kalli stairs, kife wayarsa yayi kan kujera ya tashi ya koma dining section, a hankali Hajar take sakkowa daga stairs sai kace mai taka ƙaya, saida ta gama surveying palourn da ido snn ta wuce da sauri ta shiga kitchen, har wani ɗif ɗif zuciyarta ke mata, ta ajiye plate din da taci abinci ta buɗe fridge ta ɗauki bottle water, da bottle water din hannunta ta fito walking like a chameleon ta nufi stairs, babu tsammani kawai taga yayi blocking front dinta, ba tasan lokacin da bottle din hannunta ta faɗi ƙasa ba, sosai zuciyarta ta buga after their eye contact, tayi ƙoƙarin wucewa ta gefensa ya sake blocking dinta, sake ƙoƙarin wucewar tayi ta other side din nan ma ya hanata, a duk wnn abun kanta na ƙasa taƙi ta bari su haɗa ido, ya zuba mata piercing eyes dinsa yana mata wni irin kallo, ganin bazai matsa mata ba ta fara tafiya da baya tana komawa cikin palourn, duk step din da tayi shima sai yayi hakan yasa ta ringa tafiya da baya har ta kai bakin kujera bata sani ba, ƙugunta ya riƙe snn ya janyota jikinsa, ihu tayi shirin tsalawa yayi wani juyin masa da ita ya zauna kan kujerar ita kuma ta faɗa ƙirjinsa, tini ta fara ƙoƙarin miƙewa ƙarfi da yaji, da kyar ta iya cewa "meye haka ne ni ka sakeni...", kallonta ya ringa yi ganin sam taƙi bari su haɗa ido, yace "me yasa kike guduna young lady...?", haɗe fuska tayi perceiving his pure scent ba tace komai ba, ya sunkuya ya leƙa fuskarta, da sauri ta juyar da kanta gefe tana turo baki, Nurain yayi murmushin da ya tsaya iya lips yace "and why are you avoiding my eye contact..?", nan ma ta masa shiru tana sinne kai, yace "ko wnn ma no answer ya zama bashi..?", lokaci guda yayi wrapping dinta sosai ya kai lips dinsa kunnenta yace "i will not let yesterday's night question slide", wani irin runtse ido Hajar tayi tana jin tamkar ta nutse a wajen, after a while taji ya saketa ai kam ta ɗagasa da sauri, sai kace walƙiya ta haura sama harda tuntuɓe, Nurain ya bi bayanta da kallo murya ƙasan throat yace "Silly girl", wayarsa ce tayi ringing, yayi ajiyar zuciya ya ɗauki wayar ya ringa kallon numbern dake kiransa, tattare thick eyebrows dinsa yayi sai kuma yayi picking ya kara a kunne, muryar mace yaji tace "Aslm Dr, i hope you are doing well tin..." bai bari ta ƙarasa ba ya katse kiran, nan ta shiga kiransa babu ƙaƙƙautawa sai kace masifa, daga ƙarshe ma silencing wayar yayi ya tashi ya haura sama. Washe gari da safe Nurain na tsaye kitchen yana making coffee, buɗe ƙofar kitchen din akay har zata koma ganinsa sai kuma ta fasa ta shigo, ba tare da ta dubesa ba da sanyin murya tace "Ina kwana", lips dinta Nurain ya kalla da wani irin expression, ko dai kunnensa ne yaji ba daidai ba, juyawa yayi yana ƙarewa kitchen din kallo wai ko akwai wani a kitchen din, bai ga kowa a kitchen din ba alamar dai su kaɗai ne, Hajar bata damu da rashin amsawar da yayi ba ta ɗauki abinda zata ɗauka ta fita ta bar Nurain with different thoughts running in his mind......✍️ 💛 HAJAR 💛 {70..} Wajen ƙarfe goma Hajar ta sauko downstairs ta ɗauki sweeper da packer ta wuce room dinta, sai da ta share room dinta snn ta fito corridor shima ta share daga nan kuma tayi ƙasa, tass ta gyara ko ina yayi fess snn ta zuba turaren wuta a burners tabi kan hayaƙin da freshener mai sanyin ƙamshi, saida ta gama gyara gidan snn ta shiga kitchen ta dafawa kanta breakfast taci, shima kitchen din ta gyara sa bayan ta gama amfani dashi, room dinta ta koma ta kwanta gefen gado, sosai bayanta ya riƙe don aiki tayi tuƙuru mara algus, a hankali ta tashi ta ɗauki wayar aron daya bata ta koma ta kwanta, har wani fargaba ta ringa ji tana tsoron kiran Umma, da kyar dai tayi shahada ta kirata, har suka gama waya da Umma ba taji wani canji ba, Hajar ta sauke ajiyar zuciya tana jin daɗi har cikin ranta knn Anty bata gayawa Umma ba, bayan Hajar ta idar da sallahr Azahar ne ta sake sauka downstairs, direct kitchen ta wuce, tsaye tayi ta jingina da cabinet tana tunanin me zata dafa, at last dai ta ciro froze chicken daga freezer ta fara girkin, before 3 na rana ta gama girkin, wata irin aroma ce ta bulale girman kitchen din, wasu sabbin warmers ta ciro daga kwalinsu ta wanke ta zuba abincin, bisa kitchen island ta jere warmers din, ta juye ragowar abincin a plate da haka kuma ta kimtsa kitchen din ta fita. Sai ƙarfe biyar Nurain ya dawo, kana ganinsa kasan he is exhausted, ɓangarensa ya wuce ya ajiye briefcase din hannunsa, refreshing kansa yayi ya fito daga bathroom yana goge sumarsa da towel, yana gama shirya kansa cikin ƙananan kaya ya fito corridor yana jan rigarsa, kallon few seconds ya yiwa ƙofar ɗakinta kafin ya sauka downstairs, kitchen ya shiga zai dauki ko da fruits ne yaci kafin anjima ya wuce gida yaci solid food, idonsa akan warmers dake jere kan island ya fara sauka, ya ringa kallon warmers din kafin ya ƙarasa ya buɗe, aroman data daki hancinsa kaɗai ma ta isa ta ƙara masa yunwar dake cinsa, tini ya manta da wani batun fruits ya dauki plate ya zuba abincin daga haka ya bar kitchen din. ƙarfe takwas na dare Hajar ta fito daga wanka, tayi shafe shafenta ta fesa perfume mai sanyi kamshi, kaya ƴan sawai sawai ta saka don ba kwanciya za tayi ba akwai abinda za tayi a kitchen kafin ta kwanta, ta saka hula ta rufe baƙin gashinta ta fita a ɗakin, walking gently ta sauka downstairs ta shiga kitchen, tana riƙe da door handle ta ƙarewa kitchen din kallo, surely bai daɗe da fita ba don sosai taji pure scent dinsa, taɓe baki tayi bayan ta lura da coffee maker a jone, murmushi Hajar ta saki bayan ta buɗe warmers din abincin taga kaɗan ya rage, daman abincin ba wani yawa ne dashi ba, tayi kwafa har lokacin murmushin beyi fading a beautiful face dinta ba. Nurain na zaune a balcony yana waya da Mr Lee from China, suna gama wayar Nurain ya tashi ya shiga ciki, ba tare da ya cire airpod din dake right ear dinsa da ya gama wayar ba ya buɗe ƙofar kitchen, coffee dinsa ya tsiyaye a mug ya ɗauka zai fice a kitchen din sai kuma ya juyo jin motsi, Hajar ce ta fito daga store da roba a hannunta, da sauri ta saukar da kanta ta ajiye robar kan cabinet, a hankali tace "ina yini", Nurain ya dawo da baya ya jingina da cabinet ya ringa kallonta without blinking, lokaci guda ya cire airpod dake kunnensa still staring at her, tana ɗago kanta sukay ido huɗu, turo baki tayi ta saukar da kanta, knife ta ɗauka ta fara feraye dankalin da ta debo, da gefen ido ta fakaici kallonsa kawai taji wata azaba a hannunta, ba shiri ta saki wuƙar gami da yin ƴar ƙara, da sauri Nurain ya ajiye mug din hannunsa ya isa inda take, riƙe hannun da take yarfewa yayi yana so yaga inda ta yanke, ƙoƙarin amshe hannun ta ringa yi, lokaci guda ya saki hannun nata ya rutsa flat tummy dinta ya ɗorata kan cabinet, ya riƙe hannunta with care, tamkar robot da aka dannawa remote haka ta ƙame, ta ringa kallonsa without blinking, wnn shine karo na farko da tayi masa wnn kallon, yana ɗago kansa sukay ido hudu, suka ringa kallon juna after few seconds Hajar ta janye idonta, zamowa tayi zata sauka yayi saurin haɗe goshinsu waje ɗaya, tayi saurin runtse idonta, ya sauke ajiyar zuciya yace "Please be more careful..." da haka ya janye goshinsa a nata ya dauki mug din coffee da airpod dinsa ya fita, saida Hajar taji ƙarar rufe ƙofa snn ta samu kwarin guiwar buɗe idonta da ta lumshe, numfashi ta sauke tana turo baki ta diro ƙasa, ta duba finger dinta inda ta yanke taga kaɗan ne ma yankan, ko jini babu sosai sai wnda ya tsattsafo yanxu, ta isa gaban sink ta buɗe tap ta wanke ciwon, kasa yin aikin tayi kawai ta buɗe ƙofa ta fita, tana zuwa room dinta ta saka kayan bacci tabi lafiyar gado, uhmm saidai tinda ta kwanta ta kasa baccin juyi kawai take tana naɗewa waje ɗaya tamkar ƙadondoniya, lokaci zuwa lokaci take turo baki ta juya lulu eyes dinta. Ranar Thursday da yamma Nurain ya isa gidansu, yana shiga main palour ya tarar da baƙi, both his paternal and maternal Aunties na zaune palourn da kuma close friends din Maminsa, da ladabi Nurain ya gaishe da mutanen palourn, Mama Mardiyya ƙanwar Abba tace "Uthman ya iyali...?", yace "Alhmdllh" yana shafa kansa, da haka ya tashi ya wuce part din Mami, Sakeena ya tarar a palour tana sealing envelope da aka cika da sabbin kuɗi, Nurain ya ƙarasa palourn yace "wani abun ake ne naga ƴan uwa..?", Sakeena tace "kai komai baka sani ba, yau fa za a kawo lefen Noory", ya waro ido yace "Oh right... Mami ta gayamin", Mami ta fito daga bedroom dinta da 2 notes na kudi a hannunta ta miƙawa Sakeena tace "suma kisa a envelope", Sakeena ta amshi kuɗin tace "Ohk", bayan Nurain sun gaisa da Mami yace "Abba na nan...?", Mami tace "Nope yaje Abuja sai 7 nake jin zai dawo", Nurain yace "Alright". wajen ƙarfe biyar masu kawo lefen Noor suka iso, aka tarbesu da girmamawa snn aka musu shimfiɗa ta fuska da kuma ta tabarma, da suka tashi tafiya ma aka bisu da abin arziƙi. Da daddare wajen ƙarfe takwas Mami na zaune main palour tare da Sakeena, ga uban kayan lefen da aka kawo zube kan Carpet, Sakeena tace "Our Mami baki ga kayan ba kona ɗaɗɗaga miki...?", Mami tace "No dear zan duba later", Sakeena tace "Tom" ta cigaba da duba box din kayan shafa, Nurain ya fito daga great room din Abba, paper din hannunsa ya miƙawa Mami snn ya zauna kan Sofa, Mami ta kalli papern sai kuma tace "i don't understand, wane calculation ne wnn..?", Nurain yace "kayan da nace miki zasu zo to nasu ne...", Mami tace "Masha Allah, Allah yasa rabo ne yasa albarka", yace "Ameen", Mami ta miƙawa Sakeena papern ta tashi ta shiga great room din Abba don daman so take suyi mgana dashi akan bikin, buɗe baki Sakeena tayi tace "Brother wane irin houses zaka siyamin a Villa..?", ya waro ido yace "irin wnda kike so", Sakeena tayi murmushi tace "Toh wai me kake a hospital?", straight forward yace "Help", Sakeena ta ajiye papern kan kujera tace "saidai hakan", ta cigaba da duba kayan da take, can after few minutes tace "Yauwa bani kuɗin kayan Hajar ma", Nurain ya dubeta ya ɗage gira yace "kayan me?", tace "Outfits da zata saka a biki mna", yace "Outfits kuma is she the bride?", tace "yeah she's your bride wcca kake ma favor" ta ƙarashe tana galla masa harara tace "kaga babu enough time saura 2weeks", yace "2week sukay fixing..?", tace "yeah", yace "ohh account digit", ta gaya masa account digit dinta, bayan ya tura mata ya ajiye wayar yace "done", wayarta ta duba bayan alert din ya shigo, ganin kuɗin daya turo tace "bafa 20set za a dinka ba", yace "sunyi kaɗan ne..?", tace "No sunyi yawa sosai zan maka refunding half", yace "no need", a lokacin Mami ta fito tana kallon Nurain tace "Abba yace zaka wuce China..?", Nurain yace "yeah..", Mami tace "when..?", yace "insha Allah on Monday", Mami tace "hope ba zaka daɗe ba", yace "Sure 10days zanyi", Mami tace "Alright... sai ka kawo Hajar nan..", yace "Tom". Before 10 Nurain ya koma gida, sharp sharp yayi wanka ya saka white pajamas don so yake ya sauka downstairs ya zuba abinci, a gidansu yana ganin ana ci yaƙi ci don ynxu sosai taste din abincinta ya kama masa baki, yana buttoning rigar jikinsa ya sauko downstairs ya shiga kitchen, tini ya ɗauki plate ya fara zuba abincin da yau kwana uku knn sai ya tarar a ajiye, yana gama zuba snow rice ya buɗe warmer din stew, yana fara zuba stew din aka buɗe ƙofa, daskarewa yayi a yacca yake da serving spoon a hannu, Hajar tafi seconds biyar tana kallonsa sai kuma ta taɓe baki ta wuce ta ɗauki ruwa, har ta nufi door zata fita sai kuma ta juyo, wata shegiyar dariya ce ta taho mata ganin ya kasa cigaba da zuba abincin sai jujjuya serving spoon din hannunsa yake, tayi gyaran murya tace "kai ma kana tayasu ci knn...?", haɗe gira yayi yace "what are you talking about...?", Hajar ta fashe da dariya tace "Aljanun kitchen fa na ajiyewa shine ka cinye musu..", Nurain bai san lokacin da ya ajiye serving spoon din ba yace "yah... i was only helping them sai an zuba a plate suke ci ai idan a warmer ne baza....", shiru yayi jin ta tuntsire da dariya, ita za a yiwa wayo bayan ita take wanke plate din da yaci, kallonta yake without blinking har tana riƙe ciki, Nurain yayi blushing ya shafa kansa, ya harɗe hannu yana kallonta, saida ta more dariyarta snn ta ɗago tace "wayyoh Allahna", ganin yana tahowa kusa da ita tayi sauri ta buɗe ƙofar kitchen din ta fita, saidai dariyar da take tayi weakening dinta tasa kafin ta hau stairs yayi nasarar fixgota, ta tsala ihu tace "i know your were just helping them, daman su suke cin jagwalgwalo kai baka ci", sakinta yayi ta haura sama da sauri, yabi bayanta da kallo sai kuma ya juya ya koma kitchen yana blushing, stew din ya ƙarasa zubawa ya ɗauki ruwa da lemo ya fita, a palour ma yayi zamansa yaci abincin, sha biyu da rabi na dare Nurain ya rufe laptop din da yake operating, ya tashi daga kan gadon bayan ya zura room slippers ya fita palour, yayi sliding door ya fita daga ɓangaren nasa, a hankali ya murɗa ƙofar ɗakinta ya shiga walking gently without making any sound, kwance ya ganta kan gado ta rufe da duvet, hasken ɗakin ya rage yabar dim, ya matsa gaban gadon yana kallonta da ɗan hasken ɗakin, a hankali ya kwanta daga bayanta ya ɗora kansa a pillow dinta, yana ɗaga duvet Hajar ta farka don daman baccin nata beyi nisa ba, ganin zata miƙe yayi saurin rumgumota ta baya, scent dinsa da ta shaƙa ne yasa taji relief amma kuma saita fara ƙoƙarin fixge kanta, da taga dai bazata iya kwacewa ba ta marairaice tace "please let go off me this is not proper fa..", ya sake haɗata da ƙirjinsa har tana jin bugun zuciyarsa, lumshe idonta tayi jin saukar numfashinsa a gefen wuyanta tace "dan Allah let me go..", murya can ƙasa yace "No.. sai kin faɗi wa kike yima dariya ɗaxu", turo baki tayi tace "nifa ba da kai nake ba, Aljanun ne suke bani dariya..", tummy dinta ya riƙe ya mirginasu suka koma suna fuskantar juna yace "really.. Aljanun kike yima dariya..?", da sauri ta runtse idonta ta gyaɗa kai don idan tace zata buɗe baki tayi mgana toh tabbas dariya ce zata biyo baya, a bazata taji ya haɗe goshinsu waje guda sai kuma yayi brushing lips dinsu, yace "lokacin da kike dariya ai buɗe baki kikay so now answer me bana son nodding talk Silly girl", tini zuciyarta ya fara racing, ta daddage tana matsawa baya don ta raba goshinta da nasa, da sauri ya tallafo kanta ya hanata raba goshin nasu, tana buɗe baki da shirin tsala masa ihu ya rufe bakin da nasa, this time around ba iya brushing lips dinsu yayi ba he sucked her small lips deeply, tini Hajar ta fashe da kuka jikinta har na rawa tace "Ummana wayyo Ummana...", Nurain yayi murmushi mai sauti yana kallon lips din nata da bai gaji da sucking ba, yace "Shhh in ana dariya ba a kuka fa", ba tasan lokacin da ta shiga banka masa harara ba tace "Ni ka sakeni dan Allah, ni fa ba kai nake yiwa dariya ba", yace "Ohh really su Aljanun da kike jin tsoro kike ma dariya knn..?", da sauri ta gyaɗa masa kai, ehen ai kam da kiss din da ya matuƙar firgitata ya gigitata ya mata tinin ba nodding saidai tayi mgana, yana sakar mata lips ta fashe masa da kuka harda shessheƙa, garin riƙeta sbd fincikewar da take ne ya kasa controlling kansa, abu daga tsokana sai kuma ya fita daga sahun tsokana har ya wuce gejin kiss, firgitar da tayi yafi na ranar nan, don wnn karon anje inda ba'a aje ba ranar nan, da kyar ta samu chance din da ta kwala uban ihu sai kuma ta ja numfashi tamkar zata shiɗe tana kiran Ummanta, sai a lokacin Nurain ya sarara mata, gefenta ya kwanta yana sauke nannauyan ajiyar zuciya, Hajar ta ja rigar baccinta data koma wuya tana shessheƙa, daman ba a maganar bra don ita cilli akay da ita may be ma ta kai gaban mirror, gaba ɗaya jikinta rawa yake tamkar an jona mata shoking, yau ita taga jalala da ƙarshen tashin hankali, hantsilowa tayi daga gadon ta kwanta kan carpet ta ringa rusa kuka kamar ranta zai fita, Nurain ya lumshe idonsa yana jinta, idan yace zai rarrasheta to tabbas ba rarrashi zai yi ba wani kukan zai sakata ko kuma ma ya sumar da ita tinda ya lura matsoraciya ce, after 30mins yaji ta dena kukan saidai shessheƙa time to time, da kyar ya tashi zaune snn yayi buttoning rigarsa, a hankali ya sauka daga gadon ya duƙa gabanta, ya rage murya yace "Hajar... Hajar... Hajar", jin shiru bata amsa ba ya ɗauketa ya mayar da ita gado ya rufa mata duvet, daga haka ya fice walking slowly don ya kunnowa kansa ruwa. Washe gari Hajar tayi gurgumi a ɗaki taƙi fita ko ina, daga taji motsi saita kyalla bathroom, tsoron encounter dashi take har cikin zuciyarta, gashi tana so ta sauka kitchen don yunwa take ji amma kuma bazata taɓa iya fita ba, tin safe ruwa kawai ta ringa ɗurawa kanta, wajen ƙarfe biyu na rana ta miƙe a hankali ta matsa gaban window, curtain din ta yaye ta leƙa waje tana kallon compound, parking space ta kalla taga babu motarsa guda ɗaya, hakan ne ya bata hope din baya gidan knn, ai da sauri ta nufi door ta buɗe ta fita, sharp sharp tayi frying egg ta tafasa black tea, jikinta har wani ɓari yake don tayi sauri ta gama ta fita, haka ta shanye shayin da zafinsa yana ƙona mata baki, tana gamawa ta buɗe ƙofa ta fita, a lokacin shima ya shigo palourn da leda a hannunsa, sanye yake da manyan kaya farare tass sbd yau Friday kuma daga mosque ya dawo, Hajar ji tayi kamar zuciyarta ta koma ciki ganinsa, da sauri ta koma kitchen don hawa saman ma ya mata nisa, ta yarfe hannu kamar zata fashe da kuka tace "na shiga uku", jin an murɗa handle ta koma da baya tana zaro ido, sai taji dama ta iya irin magic din nan na cikin films din da Noor take kallo, da babu abinda zai hana ynxu tayi applying dinsa a wnn taƙin ta ɓace ɓat ta huta, sulalewa tayi ƙasa after realizing tabbas shine ta haɗe kanta da guiwa, Nurain ya ajiye ledan fruit da ya shigo dashi, ya ringa kallonta kafin ya fara tafiya gently towards her, ya duƙa gabanta yace "yau ba gaisuwa?"......✍️ 💛 HAJAR 💛 {71..} Hajar dai taƙi tace masa komai kanta na bisa guiwarta, after a while yace "ko nima na zama masquerade ne...?", turo baki tayi ta gyaɗa kai, Nurain ya waro ido yace "why...? me yasa na zama masquerade all of a sudden..?", ta masa shiru ba amsa, yasa hannu ya ɗago kanta, suna haɗa ido tayi sauri ta mayar da kanta, Nurain yayi blushing ya shafa kansa ya miƙe yace "Alright i know daga yesterday's night na zama masquerade din nan", ta sake takure kanta tana jin dama ƙasa ta tsage ta shige kawai, wai daman yana sane da abun be manta ba, yace "Hajar", ba ta ɗago kanta ba amma kuma ta amsa a hankali, yace "i bought some fruit, make a fruit salad", ta gyaɗa masa kai, after few seconds Nurain ya fita daga kitchen din, saida Hajar ta tabbatar ya fita snn ta iya ɗago kanta ta tashi tsaye, ledan da ya ajiye kan Island ta buɗe ta ringa kallon fresh fruit dake ciki, gaba daya fruit din ta wanke snn ta zuba a fridge bayan ta ɗebi wnda za tayi salad din dasu, within few minutes ta gama haɗa yummy fruit salad din wnda ta jefa guda gudan green and purple grapes a ciki, a tsadadden transparent bowl ta juye ta saka a fridge, daga haka ta bar kitchen din ta koma room dinta, nail cutter ta ɗauka ta zauna tana yanke farcenta da bai wani fito sosai ba, tana gama yanke farcen ta tashi ta shiga bathroom ta wanke hannunta ta dawo ta zauna gefen gado, tana zama aka buɗe door, ta san dole shine don haka ta saukar da kanta taƙi kallon door din, ga kuma pure men scent dinsa da already ya cika room din shima ya tabbatar mata da shi din ne, daga bakin door ya tsaya yana kallonta yace "kin gama making fruit salad din ne...?", a hankali ta gyaɗa kai tana wasa da slim fingers dinta, yace "Ohk then bring it to my room" bai jira amsarta ba ya juya ya fita, Hajar ta ɗago kanta ta kalli ƙofar sai kuma ta turo baki, bata gane ta kai masa room dinsa ba, saida ta gama muhawara da zuciyarta snn ta tashi walking gently ta fita, downstairs ta sauka ta shiga kitchen, a tray ta ɗauro bowl din fruit salad din wnda yayi sanyi ƙau, ta saka spoon kan trayn bayan ta rufe bowl din da marufinsa, walking gently ta fita daga kitchen ta haura sama, tsaye tayi bakin door din part dinsa without making any move, da kyar tayi shahadar knocking a hankali, muryarsa taji yace "Come in", tayi ajiyar zuciya ta shiga kanta a ƙasa, zaune yake kan one of the exclusive Sofas dake palourn, yana kallon monitor din laptop dinsa da ya haska hoton posterior view of the heart, kallo ɗaya Hajar ta masa tayi saurin ɗauke kanta tayi sallama, Nurain ya ɗago daga kallon monitor ya dubeta ya amsa sallamar da tayi, ta ƙaraso ta ajiye trayn saman Centre table dake gabansa ta juya zata fita, da sauri ya riƙo hannunta ya janyota ta zauna kan kujerar daga gefensa, yace "are you eager to leave..?", da sauri ta gyaɗa kai, slight smirk yayi yace "Ke!! sai kin jama kanki ciwo ko..? kina ta wani nodding head sai kace lizard.. ko sai na maimaita abinda na masa last night zai buɗe..?" ya ƙarashe yana kallon lips dinta, da sauri ta girgiza kai tana turo baki tace "Ni fa aiki nake a kitchen", yace "Oh i thought sai na buɗesa za kiyi mgana ai", ɓamɓare hannunta da ya riƙe tayi ta miƙe ta nufi door, Nurain yabi body figure dinta da kallo har ta fice, ya dauki fruit salad din ya fara sha, har wani lumshe ido yake sbd yadda dadin ya shigesa. Kitchen Hajar ta koma ta shiga dafa abinci, before 4 ta gama girkin ta ɗebi nata ta bar masa nasa a warmers ta fita. Washe gari wajen ƙarfe sha ɗaya Nurain ya dawo daga unguwar da yaje, thick eyebrows dinsa a haɗe alamar dai ransa ya ɗan ɓaci, tafiyar da zaiyi ranar Monday ashe jirgin ba ta Kano zai tashi ba tacan Abuja ne, don haka yau Saturday ya kamata ya wuce Abuja ranar Sunday yayi clearing komai a can Abujan kafin ranar Monday da jirginsu zai ɗaga zuwa China, kafin ma ya dawo gida yayi booking flight ticket zuwa Abujan, sama ya haura ya murɗa ƙofar room dinta, surveying ɗakin yayi da ido yaga bata nan, rufe kofar yayi ya wuce part dinsa kawai, after like 20mins ya fito in a hurry ya sauka ƙasa, zai buɗe kofar kitchen knn aka rigasa ta ciki, da sauri ta fito ta basa hanya sai kuma ta dan yi bowing tace "ina kwana..", bata taɓa tsammanin zai amsa mata ba sai gashi ya amsa, wucewa tayi zata haura sama yace "Hajar", ta juyo tare da amsawa a hankali, yana kallonta da kyau yace "kije ki haɗa kayanki zamu wuce gidan Mami", ba tace komai ba ta ɗan kallesa, yace "belongings naki da za kiyi amfani dashi na two weeks", tace "tom" da haka ta juya ta fara hawa stairs, Nurain ya lumshe ido yana sauke ajiyar zuciya sai kuma ya shiga kitchen. haka nan Hajar ta haɗa duk wani abu da tasan zata buƙata a box, kayan sawa har cikin tsarabar Hajiya da ta Mami ta kwashi wasu, tana cikin zuge box din ya shigo, ganin tana fama da zip ya ƙaraso ya zuge mata yace "kin gama packing komai da zaki buƙata..?", tace "Eh", yace "Alright ki fita compound" da haka ya ɗauki box din nata ya fita, Hajar ta ɗauki handbag data saka waya da wasu ƴan tarkacen nata, bayan ta saka well ironed hijab da ta fitar ta nufi ƙofa, saida Nurain ya kashe duk wasu electric appliances na gidan ya rufe ko ina snn ya fito compound hannunsa riƙe da car key, wajen mai gadi ya wuce, da sauri Inuwa ya miƙe ya russuna yana gaishesa, Nurain yace "yawwa mal Inuwa yaushe zaka tafi gidan...?", Inuwa yace "insha Allah gobe da sassafe zan ɗau hanya", Nurain yace "Okay" ya ciro kuɗi masu kauri sosai daga aljihunsa ya basa, hannun bibbiyu Inuwa yasa gami da russunawa can ƙasa ya amshi kudin yace "Allah ya saka da alheri", Nurain yayi murmushi yace "toh Allah ya tsare hanya" bai jira mai zaice ba ya wuce parking space yana kallon Hajar dake tsaye jikin mota tana jiransa, Inuwa dai ya saki baki yana kallon uban kuɗin, jiya fa ya basa Albashinsa yau ma gashi ya ƙara masa wasu, ga kuma kayan abincin da ya basa yace ya kai gida, shiyasa Garba yace aiki gangariya ya samo masa, a gsky kam yayi sa'ar uban gida na gari. Hajar ta bude front seat ta shiga bayan shima ya shiga driver seat, saida motar ta gama warming snn ya fara driving slowly yabar harabar gidan, ko da suka fita main road Hajar tayi mamakin da ba taga yana fella gudu ba, da minimum speed yake jan motar, tinda suka baro gida ya kunna qira'ar Sheikh Abdul Baseet don haka har suka je gidan Abba babu wnda yace uffan, yana gama parking ya buɗe motar ya fita, Hajar ma ta buɗe ta fito tabi bayansa zuwa cikin gidan. Mami tace a kai box din kayan Hajar zuwa room din data zauna lokacin da bata da lfy amma ina tini Noor tasa mai aiki ta kai box din ɗakinta don tace anan zata sauka, Bayan sallahr magrib Nurain na zaune palourn Mami, Mami ta fito daga bedroom dinta tana kallonsa tace "sai yaushe zaka wuce Abujan ba flights din dare bane..?", yace "yeah ynxu zan wuce", Mami tace "Ohk kar dai kayi missing flight", yace "kafin time zan isa Airport insha Allah", Mami tace "ka tafi da warm sweater da Jacket don ynxu China wnn snow din ake musu", yace "Tom Our Mami", tace "ka ringa shafa mentholated cream kar sanyi ya kamaka Nurain kasan dai yadda mura yake maka", yace "Tom Mami". Hajar na zaune kan prayer mat bayan ta idar da sallahr magrib a room din Noor, Noor ta shigo tana kallon Hajar tace "kixo inji Yaya..", Hajar tace "tom" ta miƙe tabi bayan Noor suka fita main palour, Hajar ta ringa bin palourn da kallo don bata gansa ba, Noor tace "meet him outside", Noor na gama fadin haka ta wuce can room din da mai mata gyaran jiki ke jiranta, a hankali Hajar ta fara tafiya har ta fita balcony, Tinda ta fito bai ɗauke idonsa akanta ba, yana zaune cikin motarsa ya bar door a buɗe snn ma legs dinsa ma basa cikin motar kawai dai zama yayi a driver seat din, walking gently yaga ta nufi wajen motar, kallonta yake har ta ƙaraso bakin motar, ta tsaya daga jikin motar without saying anything, after the silent of about 1mins Nurain yayi ajiyar zuciya yace "you will be staying here for the meantime...", ta ɗan kallesa da wutsiyar ido taga ita yake kallo, a hankali ta gyaɗa kai, ya waro ido yace "ko saina buɗe bakin za kiyi mgana", ta sunkuyar da kanta tana wasa da ƙasan hijab tace "Tom", yace "Good... if you need anything don't hesitate to ask Mami", tace "Tom", envelope da ya ajiye kan dashboard ya ɗauka ya fito daga motar, ya tsaya daf da ita leaning against her, tini Hajar ta sake mannewa da jikin motar perceiving his pure scent, hannunta ya kamo ya damƙa mata envelope din yace "if you need anything", sai a lokacin Hajar taji wani iri a zuciyarta tana so ta fahimci wani abu, bata fito daga duniyar tunani ba ya ɗan janyota kamar zaiyi hugging dinta, ya sunkuyo a saitin kunnenta yace "be good Hajar", sosai mganarsa tayi hitting eardrum dinta tare da kai electric shock brain dinta, ba tasan lokacin da ta lumshe idonta ba tana jin breathing dinsa, After a while ya matsa daga kusa da ita yace "you can go", ko 1sec bata ƙara ba ta wuce ta bar wajen, Nurain yabi bayanta da kallo har ta shiga ciki, rubbing face dinsa yayi da palm snn ya shiga motar. Sosai Hajar taji daɗin zaman gidan, sosai take comfortable bbu abinda ta nema ta rasa, yau kwananta na shida knn a gidan, shirye shiryen bikin Noor ake a gidan ka'in da Na'in, ɗaiɗaikun ranaku ne Sakeena bata zuwa su fita tare da Mami, ita dai Hajar tana kallon ikon Allah taga ya masu kudi suke nasu bikin, ita dai tasan an ɓatar da kuɗi wnda zata iya kiransu da mazaje. Da yamma Hajar ta gama cin abincin da ba taci da rana ba sai ynxu, da plate a hannunta ta fito zata kai kitchen, turus tayi ganin baƙi a palour, Anty Zulaihah ce sai Khausar wnda zuwansu knn, Sakeena dake zaune palourn tin bayan dawowarsu da Mami daga kasuwa ce tare dasu, Hajar ta ƙarasa cikin palourn ta duƙa ta gaida Anty Zulaihah da ladabi, Anty Zulaihah na kallonta da kyau tace "lfy lou alhmdllh" sai kuma ta dubi Sakeena tace "Matar Nurain ce ko...?", Sakeena ta gyaɗa kai tace "Eh Anty", sai a lokacin Khausar dake danna waya ta dubi Hajar sai kuma ta ɗauke kanta, though ta taɓa ganinta sau ɗaya ranar da aka kawota amma kuma bata san haka take ba, Hajar ta miƙe ta wuce kitchen da plate din. Noor ta sauko daga upstairs, hugging juna sukay da Khausar, Noor ta gaida Anty din ta ta da ladabi, bayan sun gaisa Anty Zulaihah ta wuce part din Mami, Noor na kallon Khausar tace "banga box naki ba hajiyata..", Khausar ta mata nuni da jakar kayanta tace "gata can ai nazo knn", room din Noor suka wuce tare Khausar na gaya mata ydda suke tsarin cocktail party da friends dinsu, Noor ta zuge closet ta saka jakar Khausar ciki, Khausar tace "ki saka min a ɗaya side din mna nafi more aware and comfortable with it", Noor tace "Oh box din Hajar ne a wajen", Khausar tace "Ohk... wai waccar farar da ta shiga kitchen itace matar Ya Nurain..?", Noor tace "dman baki santa ba..?", Khausar tace "Nope kawai dai ban ganeta ba", a lokacin Hajar ta shigo Khausar ta bita da kallo, Noor tace "Ehmm Hajar meet my sisto Khausar..", Hajar tace "sannu ko", Khausar ta miƙe daga gefen gadon da ta zauna ta kalli Hajar tace "Hi" sai kuma ta nufi door tana cewa "zanje mu gaisa da Mami". after 10mins Khausar ta dawo, Hajar ganin suna firarsu wcca bata shafeta ba ta dubi Noor tace "zanje palour nayi kallo sai kin taho", Noor tace "Ohk". Da daddare Noor ta zubo musu abinci su uku, da farko Khausar cewa tayi baza taci ba sai kuma ta tashi ta fita sai gata ta dawo da plate ta ɗebi nata ta koma gefe tana ci, Noor ta bita da kallo tace "Au you like to eat alone", Khausar tace "yeah you know bana cin abinci sama da mutum biyu", Hajar ce ta tattara plate din da suka gama cin abinci ta fita dasu, tana dawowa ta shiga bathroom don yin wanka cause da wuri take so ta kwanta, Khausar tace "Noor amma the bed will not be enough", Noor tace "sai kace wasu elephants even 4 people can sleep on this bed comfortably", Khausar ba ta sake cewa komai ba ta haye gado bayan ta saka nities dinta, wani irin bararrajewa tayi ta kwashe rabi da quartern gadon, Hajar na fitowa wanka ta bude box dinta ta dauki kayan bcci ta saka, kallon position din da take kwanciya tayi taga Khausar tayi ɗai ɗai tana latsa waya, Noor tace "Khausar matsa zata kwanta ne fa", Khausar ta matsa kaɗan, Noor ta tashi daga position dinta tace "Hajar zo ki kwanta anan", Hajar tace "A'a ku kwanta kawai" da haka ta buɗe closet ta ciro wani blanket da ta gani tayi kwanciyarta kan carpet, babu yacca Noor ba tayi da ita ba akan ta tashi daga ƙasa amma tace she is Okay, Khausar tace "Omo she said it's okay please let her be.. kin san wani yafi son ƙasan", Noor dai ta ɗan haɗe gira ta koma ta zauna, ba ta son wnn acting din da Khausar take gsky, Khausar tace "The bride to be nifa banga Ya Nurain ba, ɗaxu ma da zanje gaida Mami na biya na gaidashi a room dinsa baya nan", speaking with a repartee Noor tace "ohh he is not around yana China", Khausar tace "Ohk when is he coming back...?", Noor tace "i don't think zai ƙara 1week bai dawo ba", Hajar dake kwance kan carpet duk tana jin conversation din nasu, ita sai ynxu ma tasan tafiya yayi ashe baya ƙasar ma, shiyasa bata ganinsa knn. washe gari Hajar ita kaɗai ce a gidan, da wuri Mami suka fita tare da Sakeena da alama dai so suke su gama shirye shirye kafin lokacin bikin ya shigo, Noor ma sun fita tare da Khausar ba dai tasan inda zasu ba, duk da Noor tace tazo suje tare amma taƙi sbd ydda Khausar ta nuna bata so a tafi da ita, ita kam daman ba son fitar take ba. Hajar ta shiga ɓangaren Mami don yi mata sannu da zuwa kamar yadda ta saba, bayan ta musu sannu da zuwan Mami tace "why are you all alone at home baki bi su Noor ba..?", Hajar tace "Eh", Mami tace "Okay.. je ki kawo mna abinci", Hajar tace "tom" da haka ta tashi ta fita, Sakeena ta fito daga small room din Mami inda suke ajiye kayan da suka siyo, wayar Mami kare a kunnenta tace "You catched cold brother", from the other side Nurain da muryansa ta dashe yace "yeah", don yana isa China wani muku mukun sanyi ake, daga airport kafin ya isa masaukinsa anan yayi catching cold, sosai mura ya kamasa ya riƙe masa murya shiyasa bai kira kowa ba, though ya yiwa Mami message yace mata ya sauka lfy, sai ynxun ne da muryan nasa ya bude ya samu ya kira, Sakeena ta miƙawa Mami wayar tace "Nurain ne", Mami na jin muryansa ta haɗe gira tace "ba kayi abinda nace ba ko..?", Nurain ya ja pointed nose dinsa don mganar ya fito sosai yace "No Mother wollah nayi abinda kika ce, tin a plane na saka Jacket dina, akwai sanyi ne sosai Mami", Mami tace "Ohk", suna gama wayar Mami ta katse kiran, saida Hajar ta kawowa Mami abincin da lemo da ruwa snn ta koma room din Noor, wayarta da ta ajiye kan mirror ce tayi haske, tana ɗaukan wayar taga 4 missed calls da number wcca ba ta ƙasar nan ba, Hajar ta ringa kallon numbern kafin ta ajiye wayar ta shiga bathroom don yin alwala. Da daddare wajen ƙarfe tara Hajar na durƙushe gaban box dinta zata ciro kayan bacci da zata saka, Khausar na kwance kan bed tayi rub da ciki tana latsa waya, door aka bude Noor ta shigo ta miƙawa Hajar wayarta tace "Yaya ne", Hajar ta ringa kallon wayar bata amsa ba, Khausar ta taso ta amshe wayar a hannun Noor tace "bari dman za muyi mgana dashi" da haka ta kara wayar a kunnenta ta fita, Noor ta bita da kallo hakama Hajar, Noor ta juya ta fita itama, Hajar ta ƙarasa ciro kayan baccinta ta saka, daga nan tayi kwanciyarta kan carpet ta rufe legs dinta da blanket, bata daɗe da kwanciya ba Noor ta sake shigowa, a hankali Noor tayi tapping dinta tace "Hajar har kinyi bacci", Hajar ta buɗe idonta sai kuma ta miƙe zaune, Noor ta miƙa mata wayarta tace "ga Yaya", Hajar na amsar wayar Noor ta tashi ta fita, a hankali ta kara wayar a kunnenta tayi shiru ba tace komai ba, after a while jin shiru ta ciro wayar tana kallon screen din taga seconds sai tafiya suke alamar dai bai katse kiran ba, turo baki tayi ta mayar kunne, ajiyar zuciya taji ya sauke sai kuma yace "Hajar", ji tayi muryansa ya canza amma still tasan shine, ta haɗe kanta da guiwa da sanyin murya tace "ina yini"……✍️ Please Masu neman complete din Hajar toh ku dena whalar da kanku don bbu complete ynxu nake rubutashi, snn kuma a wajena Ni Nafeesah Yusuf Nagoda (Feenerh feeche) kawai zaki samu book din don nawa ne mallakina. 💛 HAJAR 💛 {72..} A hankali Hajar ta daga kanta jin an buɗe door, ido huɗu sukay da Khausar wacca ta shigo, Khausar ta haye gado ta cigaba da danna wayarta, Nurain yace "ina wayan dana ara miki ba kya picking call ko..?", Hajar ta girgiza kai kamar yana kallonta tace "A'a ban gani ba", yace "ohh All is well right..?", ta gyaɗa kai ba tace komai ba, ai kam kamar yasan me tayi ya tsuke ido yace "ohh nodding head kikay ba zaki yi mgana ba, idan na dawo fa bxan buɗesa ta sauƙi ba, gwara ma kiyi mgana yarinya", Hajar ta kifa kanta a knees dinta tace "Ni fa bacci zanyi..", wani dogon tsaki Khausar taja ta tashi zaune ta jingina da allon gado don tana jiyo mganarsa sosai sbd the room was so silent, Hajar dai ko kallonta ba tayi ba waya na kare kunnenta, Nurain ya ja nose dinsa yace "hmm your lips are aching surely i must brush them when am back..", wani irin turo baki tayi tace "Allah kuwa Ni bacci zanyi", yayi slight smirk yace "nayi gluing eyes dinki ne", kawai dai latsa waya Khausar take amma all her mind yana kan Hajar ne, lokaci guda ta tashi daga kan gadon taje ta kashe fitila, sosai room din yayi duhu sai hasken wayar Khausar da take latsawa, Nurain yayi ajiyar zuciya yace "you know what Hajar..?", ba ta kai ga basa amsa ba Khausar ta kunna waƙa a wayarta ta ƙure volume, bayan song din data kunna har wani bi take tana ɗaga murya, hakan yasa Hajar ba tajin me yake cewa tinda muryansa ba sosai take fitowa ba, Hajar tace "saida safe" bata jira cewarsa ba ta katse kiran don tasan ko yayi mgana ba ji za tayi ba, snn kuma idan ba ɗakin Noor ba taga inda zata iya waya dashi a gidan ba, Hajar ta ajiye wayar a gefenta ta sauke ajiyar zuciya sai kuma ta kwanta, Khausar ta rage volume din wayar bayan ta lura da kwanciyar Hajar, har bacci ya ɗauke Hajar mganarsa ta ƙarshe take tunawa ko me zai gaya mata. washe gari tinda Khausar ta tashi take wani cin magani, sai wani murtuke fuska take da ƙananun tsaki, har saida Noor ta tmbyeta lfy lokacin da ta kirata yin breakfast, fuska a ɗaure Khausar tace "nothing am just moody today", Noor tace "Ohk ki fito muyi breakfast", Khausar tace "tom am coming", Noor ta juya ta fita, Khausar na fita palour ta tarar da Noor da Hajar zaune kan carpet ga Variety na breakfast a gabansu, Khausar ta zauna ta haɗa shaya a mug, irish da kwai ta ɗeba ta matsa ketchup snn ta fara ci, Noor tace "ga croissant fa", Khausar na shan shayinta ta girgiza kai, Noor tace "akwai cheese sosai fa", Khausar tace "am not eating sister", Noor bata sake cewa komai ba, daman Hajar tinda Khausar ta fito bata ko kalli position dinta ba, ta lura yau ɗaɗɗaga kan nata yafi na jiya, Hajar na gama yin breakfast dinta ta kai plate da cup din kitchen, da ta fito bata zauna a palour ba tayi wucewarta ɗaki, bai fi 20mins da zamanta ba Khausar ta shigo, ta zauna gefen gado ta ɗauki wayarta dake kan bedside tayi dialing number ta kara a kunne, tsaki tayi ta wurgar da wayar kan bed, Hajar ta tashi ta fita ba tare da ta kalli inda take ba, through out the day hka Hajar ta ringa avoiding Khausar, mgnar da ya gaya mata kafin ya tafi ce ta ringa mata yawo a brain wato be good Hajar, idan ta tina saita share lamarin Khausar da take ƙoƙarin fusata ta. wajen ƙarfe biyu Hajar taje kiran da Sakeena ke mata, mai aikin gidan ce tazo kiran ta, Hajar ta shiga room din Sakeena na gidan da sallama, Sakeena dake zaune kan carpet da kaya baja baja zagaye da ita ta amsa, Hajar ta ƙarasa ciki ta zauna, wata leda Sakeena ta bata tace "Outfits dinki ne na biki, nasan size din zasu miki tailor Salmah ce ta miki tinda tasan size dinki amma dai ki gwada", Hajar tace "Toh ngd sosai", Sakeena tace "you're welcome dear", Hajar ta koma room din Noor don ta ajiye kayan, Khausar kawai ta tarar Noor ta tafi ɗakin da ake mata gyaran jiki, Hajar ta buɗe closet ta sauke box dinta zata jera kayan aciki, sosai laces din sukay mata kyau gasu kuma colors din da za suyi fitting dinta sosai, duk kayan da ta zaro saita ɗaga sai kuma ta mayar ta linke ta saka a box, by doing that har ta gane zasu mata ko bata gwada ba, Khausar tayi pausing Movie da take kallo jikin Laptop jin wayarta na ringing, tini tayi picking call din ta kara a kunne tace "Ya Nurain i have been calling you since morning..", sai kuma ta karyar da kai tace "Okay... hope you are not busy now..", tinda Khausar ta ambaci Ya Nurain Hajar ta dena abinda take na almost 10sec kafin ta cigaba, a handsfree Khausar ta saka wayar don ba ta jinsa sosai wnda hakan yasa Hajar ta tsinkayo muryansa ainun, taji yace "what were you saying yesterday lil sis..?", tini Hajar ta ɗauke hankalinta daga kansu ta cigaba da abinda take, ƙasa ƙasa taji sautin dariyarsa sbd tazarar dake tsakaninsu da Khausar, Hajar na ɗago kanta taga Khausar na murmushi sai kuma ta kwanta tace "Am serious fa Yaya", da sauri Hajar ta tutsa ragowar kayan ta dannasu cikin box din, ta mayar da box din cikin closet da haka ta nufi door ta fita kuma har lokacin basu gama wayar ba, Hajar har zata zauna palour sai kuma ta fasa ta tafi wajen Sakeena, ta gaya mata cewa ta gwada kayan kuma sun mata, Sakeena tace "where is Khausar...?", Hajar tace "tana can ɗaki", Sakeena tace "call her for me", har Hajar ta tashi kirantan Sakeena tace ta barshi, a nan Hajar ta cigaba da zamanta har ta taya Sakeena shirya wasu kaya da aka kawo a cikin Souvenirs box, wajen ƙarfe huɗu Mami ta shigo don daman bata nan sun fita da Anty Zulaihah, sannu da zuwa Sakeena ta mata Hajar ma haka, Mami na kallon Sakeena tace "har kin gama da wnn shima...?", Sakeena tace "yeah.. ai nafi so na gama komai ydda zan zama free a lokacin biki", Mami tace "su little Abba na wajen grandma dinsu ko...?", Sakeena tace "Eh", Mami tace "Alright please a ware 100 pieces daban", Sakeena tace "Sure", da haka Mami ta juya ta fita, Sakeena ta kalli Hajar tace "je kici Abinci kiyi sallah sai mu ƙarasa", Hajar tace "Toh" da haka ta tashi ta fita. the same time daya kira jiya ta wayar Noor yau ma haka ya kira saidai ta wayar da ya bata, shi asuba ce a can nan kuma ƙarfe tara na dare, Hajar ta ciro wayar da ta ajiye cikin handbag dinta tin safe jin tana ringing, ta ringa kallon exact number da ta kirata jiya, turo baki tayi bayan tayi wani tunani, gashi da Sim 1 ake kiran snn kuma numbern ba ta Nigeria bace, lokaci guda ta makawa wayar harara ta dannata a silent ta mayar cikin jaka, bathroom ta shige tana turo baki gami da juya lulu eyes dinta, tana fitowa daga wanka ta tarar da Noor na jiran fitowarta, da sauri Noor ta miƙa mata wayar hannunta tace "take it Yaya ne zai kira ynxu" tana gama fadin haka ta fita da sauri don kallon stuff na Kdrama data saba take yi ya kira, gashi yace lallai lallai ta bar abinda take ta kaiwa Hajar waya, tana zuwa ta tarar da Hajar na wanka gashi sai azalzalanta yke sai kace zai fito daga wayar, Noor na fita kiransa ya shigo, Hajar ta ringa kallon wayar har kiran ya katse wani ya sake shigowa, kan mirror ta ajiye wayar ta barta sai ringing take, ta dauki kayan baccinta ta saka tayi kwanciyarta tana ji wayar nata ringing, bayan wani lokaci taji kiran ya dena shigowa, kasa bacci Hajar tayi duk da baccin da take ji, idonta ne kawai a rufe amma ba baccin take ba, jin an buɗe door ta ɗan buɗe idonta, azatonta Khausar ce sai taga Noor ai kam tayi sauri ta rufe ido, Noor ta duba sides din Hajar tana neman wayarta tinda jiya ma anan ta ganta, ganin bata ganta ba saita fara dube duben ɗakin har ta hangota a kan mirror, zaro ido tayi ganin 10+ missed call, wani kiran nashi ne ya kuma shigowa, Noor tayi picking ta kara a kunne tace "Hello", from the other side Nurain ya haɗe thick eyebrows dinsa da muryansa da bata daidaita ba yace "Hey Noor kin kai mata wayar..", Noor tace "wllh na kai mata hand to hand..", ya sauke numfashi yace "where is she..?", Noor ta dubi Hajar da take baccin ƙarya tace "she's already at sleep", yace "wake her up", Noor tace "Ohk" da haka ta durƙusa gaban Hajar ta fara tapping dinta, tamkar sumammiya haka Hajar ta naɗe samm taƙi ta motsa ma, Noor tace "Yaya she's deeply at sleep taƙi tashi fa", yayi ajiyar zuciya tace "ki san yacca za kiyi ki tasheta nan da 5mins" ƙit ya katse kiran, Noor tayi tagumi tana kallon Hajar tace "na shiga uku", ganin lokaci na tafiya Noor ta kai hannu tayi tapping dinta tace "Please Hajar wake up ki rufamin asiri", sau ɗaya ta sake tapping dinta sai ta fara mutstsuka ido kamar gaske ta miƙe zaune, Noor tayi ajiyar zuciya don wani relief taji tace "Sorry Yaya ne yace na tashe ki", Hajar dai sai mutstsuka ido take ta gyaɗa kai, 5mins na cika dot ya kira, Noor tayi picking tace "gata nan na tasheta ynxu zan bata wayar", yace "Better", tini Noor ta miƙa mata wayar, Hajar ta amsa ta kai kunne ba tare da tace komai ba, fita daga ɗakin Noor tayi tana jin daɗi Allah ya rabata dashi, almost 1mins wayar na kare kunnenta taƙi tace masa komai, ya rage murya yace "Hajar are you there...?", shiru ta masa taƙi mgana sam, slight breathing dinta da yake jiyowa ta wayar ne ya basa assurance cewar tana ji mgana ne dai baza ta masa ba, yayi ajiyar zuciya yace "Hajar are you hearing me", ta haɗe gira ba tace uffan ba, babu yacca Nurain baiyi ba akan ta masa mgana amma taƙi, daga ƙarshe yace "i must open that small mouth of yours until you beg for mercy", da haka ya katse kiran, Hajar ta turo baki ta koma ta kwanta zuciyarta wasai. Haka nan two days Hajar taƙi sauraron Nurain, idan ya kira ta wayarta daman bata picking, ta wayar Noor kam zata dauka amma ba za tayi mgana ba, sosai Nurain ya damu da hkan da take masa, lafiyar Allah fa ya baro Silly girl dinsa toh me ya faru ne, wayar da sukay na farko ma harda sassanyan gaisuwar da kwana biyu take masa tayi fa, wai what is exactly happening ne, tini ya fara shirin dawowa 9ja duk da bai gama abinda zaiyi a can ba ya bar Mr Lee zai ƙarasa masa shikam ya kamo hanyar gida Nigeria. Zuwa wnn lokaci gida ya fara cika da ƴan uwa na nesa wnda suka zo biki, gobe ne za'a fara gudunar da ƙananun shagulgulan na bikin wnda Amarya da ƙawayenta ne zasu warwasa. Khausar ta dubi Noor dake zauna kan hannun kujera tace "Please Noor kixo mu tafi wajen Salon din nan don mu dawo da wuri", Noor tace "Hajar nake jira ynxu zata fito", Khausar ta haɗe gira tace "wace Hajar kuma ita amarya ce da sai kunje wajen Salon tare", Noor tace "Yaya Sakeena ce tace muje tare", Khausar tace "Ohk alright amma ai komai na bride is different from others", Noor tayi dariya tace "wankin kai ne fa kawai ba make up ko Outfits ba", Khausar ta taɓe baki ba tace komai ba, Hajar ta fito sanye da hijab da handbag dinta a hannu, da haka suka wuce wajen Salon din bayan sun sanar da Mami. ƙarfe 11 na safe Nurain ya iso gida, direct part din Mami ya wuce wacca ya tarar da ita tayi shirin fita, don haka suna gaisawa Mami ta fita don already driver dinta ma ya gama warming mota, Nurain na fitowa part din Mami ya buɗe room din Noor after knocking for almost 1mins, haɗe gira yayi ya juya ya koma bangaren Mami kuma saida ya duba ko wane room na part din snn ya fito, at last ya shiga kitchen ya duba shima dai baiga abinda yake nema ba, infact ma ya lura da babu kowa a main house din don ko baƙin da suka fara zuwa suna can Cabins din gidan, a ransa ya ayyana may be suna tare da Noor tinda bai ga kowa a gidan ba. Sai wajen huɗu su Hajar suka dawo daga wajen Salon, Noor cewa tayi ba zata shiga ciki ba sai taci abinci, Khausar sai wani cin mur take tin bayan da aka gama musu gyaran gashin, gani tayi na Hajar yafi na kowa kyau duk da cewa assistance din me Salon din ce ta mata, shiyasa tace kar aje da ita ai ga irinta nan nata yafi na amaryar ma kyau, ita dai ce taga hakan don kowa da zubin gashinsa amma na Noor yafi tsada da cin lokaci ai, a palour suka zauna cin abincin, Hajar da Noor eating from the same plate Khausar na cin nata daban, a kusan tare suka ɗago jin an fito daga great room din Abba, wani irin bugu zuciyar Hajar tayi after their eye contact, Khausar ta waro ido tace "Laa Ya Nurain", Hajar kawai yake kallo wacca ta sunkuyar da kanta tana juya spoon din hannunta, Khausar tace "Yaya yaushe ka dawo..?", speaking with a repartee yace "Since 11..", tace "Okay welcome", Noor ta masa snnu da zuwa tare da gaishesa, kaf saida ya amsa gaisuwar tasu banda ta Hajar, da haka ya nufi door hands dinsa zube a pocket don daman mosque zai fita sallar la'asar, tini Hajar taji ta tsani abincin, ta ajiye spoon din ta zuba ruwa ta sha, Noor tace "kin ƙoshi ne?", Hajar ta gyaɗa kai sai kuma ta ɗauki handbag dinta ta shiga ciki. bata sake fita ba sai after magrib da ta ɗakko shoes dinta a motar Sakeena, tinda ta koma ɗaki tayi zamanta sai kace prisoner, yau ko ɗan kallon ma bata fita palour tayi ba, wajen ƙarfe goma ta tashi ta shiga wanka, bayan ta fito ne ta tsaya gaban mirror tana kallon gyaran gashin da akay mata, zaro ido tayi ganin babu ear ring a kunnenta na hagu, sharp sharp ta ƙarasa shiryawa ta saka nities dinta, hijab ta zumbula saman nities din snn ta nufi ƙofa ta buɗe ta fita don ta duba ear ring dinta, main palour kitchen duk saida ta duba ba taga ɗan kunnen ba, tunawa tayi ai ɗaxu ta fita ko wajen ɗakko shoes dinta ta yar a compound, tana buɗe door abinda ta fara ji shine pure scent dinsa, sai kuma ta hango Khausar zaune kan kujera a balcony din, bata fita ba ta ɗan leƙa balconyn ai kam ta hangosa, shima yana zaune kan kujera suna facing juna da Khausar wacca take ta zuba masa zance, ya bata rabin attention dinsa while the other half yana kan wayarsa, and worst part of it the smile on his face, ba shiri Hajar ta juya ta koma ciki, ƙafarta har harɗewa take tayi sauri ta zauna kan tiles, saida abinda take ji ya ɗan ragu snn ta miƙe still ƙafarta na harɗewa ta shiga room din Noor, sulalewa tayi kan carpet tana jin wani iri a zuciyarta, duk yacca taso ta daure amma kasa jurewa tayi, ba tasan lokacin da ta fashe da kuka ba, samm bata iya danne kuka indai ya taho mata toh sai tayi, door aka buɗe Noor ta shigo, da sauri Noor ta ajiye bowl din farfesun kazar da ta shigo dashi ta duƙa gaban Hajar da ta kasa danne kukan da ya ci ƙarfinta, with care Noor tace "Ya salam what happened Hajar...?", Hajar ta girgiza kai tana ƙoƙarin tsayar da hawayen dake zuba cheeks dinta, Noor tace "please tell me Hajar me ya faru..?", da ƙyar Hajar tace "kai na ne yake ciwo", Noor tace "Ayya Sorry bari na kawo miki drug", Noor ta tashi ta fita bbu jimawa ta dawo da glass of water da satchet din Panadol, Hajar na yamutsa fuska haka tasha maganin, zata kwanta kan carpet Noor ta mata dole ta hau gado ta kwanta, sosai zuciyarta take mata wani iri wnda bata san a yadda zata fasaltasa ba. sai wajen ƙarfe sha ɗaya Khausar ta shigo, ta ringa nunawa Noor abinda Nurain ya taho mata dashi daga China, Hajar da idonta ke lumshe duk tana ji tayi sauri ta juya musu baya tana turo baki. Washe gari da safe Khausar ta fito daga kitchen da mug a hannunta, stairs ta dosa zata hau, dakatawa tayi ganin Sakeena na sakkowa daga stairs din, Sakeena ta kalleta a takaice tace "Khausar ina zuwa haka..?", Khausar tace "Ya Nurain ne yace na kai masa Coffee", Sakeena ta ƙarasa sakkowa tace "kawo Coffee din", Khausar tayi jim sai kuma ta miƙa mata mug din, Sakeena ta amshi mug din snn ta miƙa mata paper bag din data sakko da ita tace "take it to Mami", Khausar tace "sure" da haka ta bar wajen, ita dai Sakeena tasan Nurain ba zai sa Khausar ta kai masa Coffee room dinsa ba saidai cewa yayi ta haɗa ta ajiye masa zai zo ya amsa, kamar kwa ta san hkan sukay dashi, har Sakeena ta juya zata koma saman ta hango Hajar ta fito palour, Hajar na ganin Sakeena tayi bowing tace "ina kwana", Sakeena tace "morning how are you doing...?", Hajar tace "Alhmdllh", Sakeena tace "masha Allah, Noor tace jiya kanki na ciwo how are you feeling now...?", Hajar tace "ya dena alhmdllh", Sakeena tace "Ohk toh Allah ya ƙara sauƙi", mug din Coffee ta miƙa mata tace "ki kaiwa Nurain", daram zuciyar Hajar ta buga ta amshi mug din, Sakeena ta ringa kallonta ganin bata motsa ba tace "yana room dinsa..", Hajar ta gyaɗa kai tace "ai bansan room din nasa ba", saida Sakeena taji hakan odd kafin ta kwatanta mata room din nasa, a hankali Hajar ta haura stairs din zuciyarta na ɗif ɗif, tana isa ƙofar room din nasa ta kai hannu tayi knocking a hankali, tafi minti biyu a tsaye amma no respond, tunani tayi may be ma baya ciki don haka bari ta shiga ta ajiye masa idan yaxo ya gani, da wnn tunanin ta murɗa handle ta shiga, ɗakin sanyi ƙau sai kace freezer, kaɗan ta shiga tana ɗaga kanta sukay ido huɗu dashi ta cikin mirror, a tsaye yake bakin mirror yana taje sumar kansa da towel ɗaure a waist dinsa alamar daga wanka ya fito, Hajar ta fasa ƙara ta rufe idonta da other hand dinta, a miliyan ta juya ta nufi door saida tayi karo da bango sbd idonta dake a rufe snn ta wawaki ƙofar ta fita, rabin coffee din kam duk ya zube mata a legs kuma taji zafi sosai, Nurain yayi wani murmushi irin zaki shigo hannu ne, yayi kwafa ya cigaba da combing hair dinsa, zai kamata ne wllh sai ta nemi mercy kamar yadda ya faɗa mata, duk ta gama guje gujenta da zille zillenta ai zasu koma gida ne sai yaga ƙarshen gudu. A gigice Hajar ta sauka stairs kawai taji tayi karo da mutum, Khausar ta hangame baki tana kallon jikinta da Hajar ta wanke mata shi da ragowar Coffeen, Hajar tace "please kiyi haƙuri ban...", katseta Khausar tayi da ɗan tsawa bayan ta ƙarewa palourn kallon tace "Shut up.. I don't need your apology..", Hajar ta maka mata wata shegiyar harara tace "Au haba toh kar Allah yasa ki haƙura sai kije can kisha wankin madara" tana gama faɗin haka ta kewayeta ta wuce gami da jan dogon tsaki, Khausar ta saki baki galala tabi ta da kallon mamaki.......✍️ 💛 HAJAR 💛 {74..} A fusace Hajar ta juyo ta fixge veil dinta tace "Am not single..", murmushi yayi yace "ai ko idan duk jikina kunne ne i will not believe you An mata", bata sake ce masa ƙala ba ta juya ta nufi ƙofar hall din, bai haƙura ba ya sake bin bayanta, Nurain da zuciyarsa take tafasa hundred degree Celsius sai a lokacin ya iya buɗe motar ya fito, ya riga da yayi mistake din farko da ya riƙe mata veil, wnn time din kam hannunta yaso kamowa da nufin tsayar da ita, saidai me bai kai ga riƙe hannun nata ba yaji saukar wani mugun punch a fuskarsa, tini Abokin ango ya riƙe gefen fuskarsa yana jin taste din blood a bakinsa, a gigice Hajar ta juyo tana ganin Nurain jikinta ya hau shivering, da sauri tasa hannu ta rufe bakinta gami da yin ƴar ƙara ganin bakin abokin Ango na zubar da jini, with husky voice Nurain da idonsa ya rine yace "daga yau bazaka sake mistake din riƙema wata veil ba.." da haka ya fixgi hannun Hajar zuwa inda ya yasar da motar, saura ƙiris taci da ka sbd yadda ya finciketa, fashewa tayi da kuka jin kamar zai ɓalla mata hannu tace "ni ka sakeni wayyo Ummana zai karya min hannu", front seat ya buɗe ya cillata ciki ya rufe ƙofar saura ƙiris ya haɗa da hannunta, ya zaga driver seat ya shiga da haka ya fita da motar daga event center din da reverse, wani irin cin taya yayi a kan kwalta snn ya fixgi motar with high speed ya bar area din, Hajar ta fasa ƙara ta haɗe kanta da guiwa don harta saddaƙar yau sai ya kifar dasu, gaba ɗaya Nurain daina ganin gabansa yayi sbd yadda zuciyarsa take tafasa, kawai hango yacca wnn banzan ya riƙe veil din Silly girl dinsa yake, how dare him da zaiyi ƙoƙarin riƙe mata hannu, a lokaci guda ya gangara bakin road ya tsayar da motar gami da kifa kansa ga steering, ya lumshe idonsa trying very hard to control himself, Hajar ta ɗago kanta jin ya tsaya da tuƙin, ta ɗan kallesa har lokacin kansa na haɗe da steering, after a while ya ɗago sukay ido huɗu tayi saurin janye nata, zuciyarta ta hau lugude ganin yanayinsa, Nurain exhale heavily his eye fixed on her, ya dubi dressing dinta da kyau, ji yayi kamar ya wanka mata mari amma bazai yi hakan ba, not in this situation gsky, ko a Abuja da ya mareta yasan bata ji da daɗi ba, toh this time around ma yace zai mangareta wllh sai tayi jinya, dunƙule hannunsa yayi ya sauke ajiyar zuciya, after few seconds ya furzar da iska ya cigaba da driving din, koda wasa Hajar bata sake ɗago kanta ba har suka je gida, a daidai main door ya tsayar da motar ba tare da ya dubeta ba yace "get out", jikinta har rawa yake tayi sauri ta zura takalmanta ta bude ƙofa ta fita, ɓangaren Hajiya ta shige walking gently, Hajiya da har lokacin take tare da Farooq ta kalleta tace "Ah ah ƴar nan har kun dawo daga wajen chasun da wuri haka...?", Hajar ta gyaɗa kai tace "Eh Hajiya", Hajiya ta taɓe baki tace "yo wnn ai ba chasun akai ba du du mintinku nawa da tafiya", Hajar ta ɗanyi bowing ta gaida Farooq, ya amsa da sakakkiyar fuska yace "how are you doing..?", tace "fine alhmdllh", yace "Good anata shan biki..", door aka buɗe aka shigo, Hajar na ganin wnda ya shigo tayi sauri ta shige bedroom din Hajiya, Nurain yayi kwafa ya bita da kallo sai kuma ya ƙaraso ciki ya zauna gefen Farooq ya ajiye masa key din mota, Farooq ya ringa kallonsa ganin ydda ya wani haɗe rai sai kace bai taɓa murmushi ba a rayuwa, rage murya Farooq yayi yace "ka kyauta da ka hana yarinya morewa Dinner", Nurain ya tamke fuska yace "what are you talking about...?", Sosai Farooq yayi dariya yace "Oh yeah ni dae kasan bazaka min wasa da hankali ba..", Nurain yace "Whatever", sai a lokacin Nurain ya kalli Hajiya da tin shigowarsa take kallonsa ta ƙasan glasses dinta, ya waro ido yace "Iron lady barka..", Hajiya ta katsesa da faɗin "kkkk riƙe abinka bana so, Man zafin da ka kawomin ma kazo ka amshi abinka bana so", Nurain ya sauka kan carpet ya zauna gefenta yace "ba kyau fa mayar da hannun kyauta na bar miki", tace "ka matsa daga kusa dani ko na saka sandar nan na raɗe ka wllh", Nurain ya riƙo hannunta yace "ya haƙuri idan kika buga min sanda wa kika kama", Hajiya tace "azabar son da nake yiwa jikoki shiyasa suka sami ƙofar yimin wulaƙanci barin ma kai da Al'ameen", Nurain yace "nidae nace kiyi haƙuri duk da bansan laefin da nayi ba", Hajiya ta rausayar da kai tana micincina ido. ƴan Dinner kam basu dawo gida ba sai wajen 11 don neman Hajar aka ringa yi tin kafin ma a gama Dinnern, Farooq Sakeena ta kira tace masa idan yana tare da Nurain ya gaya masa suxo ba a ga Hajar ba, saida Farooq ya gama cin dariya snn ya gaya mata cewar ai Hajar ta daɗe da dawowa gida. washe gari Friday kuma itace ranar ɗaurin auren, bayan an sakko daga masallaci aka ɗaura auren, zuwa bayan sallar la'asar gida ya kuma cika maƙil da jama'a sbd an shiga sabgar yini, a duk wnn bidiri da ake Hajar na maƙale part din Hajiya, ita dai da safe take zuwa wajen Mami ta gaisheta, Sumayyah ce ta shigo tayi kiran Hajar tace taje inji Mami, Hajar ta yafa veil dinta ta tashi ta fita, ta ringa wuce jama'a tana kutsawa harta samu ta shiga part din Mami, shima nan din a cike yake maƙil da mutane, sai ga Mami nan ta fito daga bedroom dinta, da hannu ta yiwa Hajar alamar tazo, Hajar ta ƙarasa har gabanta suka shiga bedroom din tare, wasu mata su biyu Hajar ta tarar a room din an jere musu kayan abinci, sai kuma Haj Fati da take zaune room din itama, Hajar ta durƙusa har ƙasa ta gaishesu da ladabi, ɗaya daga cikin matan tace "Masha Allah, matar Nurainin ce..?", Mami ta gyaɗa kai da murmushi kwance fuskarta, bayan sun gama gaisawa Mami tace da Hajar ta wuce abinta, har ta tashi zata fita Haj Fati ta dakatar da ita, box din souvenir ta bata tace ta rakata compound dashi, Hajar na biye da Haj Fati da box din souvenir har suka fita compound, Ahmad da yayi parking din motarsa can kusa da gate ya fito ganin mahaifiyarsa, da sauri ya taho inda take da wata leda a hannunsa, Hajar na hangosa tayi still a inda take har ya ƙaraso, sai da yaxo daf dasu snn ya lura da Hajar, Haj Fati tace "Good.. hope baka mnta komai ba..?", yace "Sure Ammie.. Husnah ce ma ta bani", Haj Fati tace "Alright.. ga wnn ka tafar min dashi", da haka ta juya ta amshi box din hannun Hajar ta miƙa masa, ya amsa yana kallon Hajar without blinking sai kuma yace "Hi Hajar..", Hajar ta saukar da kanta tace "good afternoon..", Haj Fati tace "you know her..?", Ahmad ya gyaɗa kai yace "yeah", Haj Fati tace "A ina ka santa..?", yace "ba kin aikoni wajen Mami ba three weeks back", Haj Fati tace "Ohk..", ita dai Hajar na jinsu ba tace komai ba har suka gama mganar snn ta koma ciki tare da Haj Fatin. Sakeena na attending guest dinta da suka zo biki wnda su din in-laws dinta ne, kiran Nurain ne ya shigo wayarta, saida tayi excusing kanta snn ta ɗaga kiran, Nurain ya sanar da ita ai Hammad ne yaxo tare da matarsa suna Mini palour, Sakeena tace "Alright" don daman tasan Hammad, haka nan taje suka gaisa dasu Hammad din snn ta tasa aka kai musu abinci ita kuma ta wuce ta kira Mami don su gaisa, Sakeena ta shiga mini palour tare da Mami, Mami na gama gaisawa dasu Hammad ta koma wajen nata baƙin da suke kan zuwa, Maysha ce ta tambayi ina Hajar don tana so su gaisa, Sakeena ta kira Aysha a waya tace ta kira mata Hajar, su Hammad basu wani jima ba suka tafi don dman suma wani bikin suka zo kano shine suka biyo tanan, Bayan tafiyarsu Hammad Nurain ya dawo daga rakasu ya tarar da Sakeena bakin main door, sosai ya tsargu da irin kallon da take masa, ya ɗage gira yace "why..", Sakeena tace "wai kai har wani extinct kaje sbd taurin kai brother..?, me yasa kake ɓoyewa mutane Hajar matarka ce...?", ya waro ido yace "Nah..?", Sakeena ta haɗe gira tace "bafa wasa nake ba Nurain..", ya zuba both hands dinsa a pocket yace "Nah too, kin san dai mun gama mgnar nan dake", Sakeena ta saki baki tace "i thought ka janye wnn shirmen Nurain", ya ɗaga shoulder yace "kince fa ina da taurin kai so taya za ai na janye", Sakeena ta sauke ajiyar zuciya ta koma ciki. kafin magrib aka hau shirin kai Amarya gidanta, dangin Ango har sunxo daukar abarsu da convoy din manyan motoci, hka aka fito da Noor data sha lafaya daga ɓangaren Abba tana gursheƙen kuka, da kyar aka ɓanɓareta daga jikin Mami snn aka miƙata dangin mijinta, Mami kawai daurewa take don itama harta fara missing ƴarta ta, sai a lokacin Hajiya ta fito tace ita ce nan zata kai jikarta har ɗakin mijinta, ai kam ba wnda yayi musu haka Hajiya ta riƙe hannu Noor har compound, daman duk jikarta mace da akai aurenta toh ita ta kaita ɗakinta, tin daga kan Sakeena ma kuwa, idan kuma namiji ne da ita ake zuwa ta rungumo matar ta kaita har ɗakinta, shiyasa lokacin auren Nurain ta ringa mitar ƙafarta ta cuceta da bata je ta rumgumo matar Usuman ba. Hajar na gani ana ta rawar ƙafar zuwa gidan Amarya ita dai ko a jikinta hasalima guduwa tayi can bedroom din Hajiya tayi kwanciyarta don kanta ke ciwo, har wajen ƙarfe takwas na dare gida bai dawo daidai ba don wasu ma sai a lokacin suke tafiya gidan Amaryar wasu kuma na dawowa, friends din Amarya kam da shiri biyu suka tafi don za ai cocktail party ne bayan an kai Amaryar, ita dai Hajar har tayi bacci ba tasan dawowar su Aysha ba. washe gari kam an gama biki tin safe gidan ya fara bajewa don da yawan mutane da safe suka tafi, kafin yamma tass gida ya ɗaɗe bbu kowa sai asalin mutanen cikinsa, tin safe daman ma'aikata suke ta share share da goge goge suna so su mayar da gidan normal self dinsa. bayan Hajar ta idar da sallahr magrib ta fito main palour da ƴar wayarta a hannu, tini tayi dialing numbern Umma ta kara a kunne, gaisawa kawai sukay da Umma kiran ya katse, Hajar ta sake kiranta nan taji switched off, Contact ta shiga ta nemo number Mu'azzam wnda tayi saving da Yayana, da sauri ta katse kiran bayan tayi realizing wnda ta kira, ashe maimakon ta danna Yayana saita danna Ya Sayyadina a rashin sani, unfortunately for her don kiran ya shiga, Tinda Nurain ya fito daga great room din Abba yake kallonta, don ita bata ma san yana nan ba ta juya masa baya, walking majestically ya matso inda take, tayi sauri ta juyo after perceiving his pure scent, wayar hannunta ce ta fara ringing, ta kalli screen din wayar kawai taga Ya Sayyadina ɓaro ɓaro, tana ɗaga kanta taga Nurain shima yana kallon wayar, a bazata ya fixge wayar daga hannunta yayi picking ya kare a kunne, wani irin sauyawa shimfiɗar fuskarsa tayi bayan ya tsinkayo muryar namiji a wayar, wani mugun yawo Hajar ta haɗiya ta kwasa a guje zata shige ɓangaren Hajiya saidai ina tini ya fixgota da ƙarfi saida ta bige da kujera, girgiza kai ta shiga yi tana son yin mgana amma rawar da lips dinta suke ta hana mganar fita, sosai idon Nurain suka kaɗa ya fara losing control, gaba ɗaya temper dinsa ta tashi, ya buga wayar da ƙasa ta tawarwatse kafin ya daka mata tsawa yace "Waye wnn din..?", Hajar ta numfasa da kyar bakinta na rawa tace "Allah yaso dai wayar taka ce kai kayi asara bani ba", slightly ya buge bakin da bayan hannu, habawa ai tini Hajar ta durƙuse a ƙasa ta fashe da kuka don ji tayi kamar guduma aka buga mata a bakin, ta kai hannu ta shafa lips dinta ai kam ta dangwalo jini hakan yasa ta kuma rushewa da kuka, da sauri Sakeena ta ƙarasa sakkowa daga stairs don akan idonta ya gwabjewa Hajar baki, ta durƙusa ta ɗago Hajar da bakinta ke fitar jini, Sakeena ta zaro ido tace "innalillah", shi ma kansa saida hankalinsa ya tashi da yaga jini, slightly fa ya bige bakin ba da wani ƙarfi ba, idan da yasan za taji ciwo ai bazai bigeta ba, ya cije lower lip dinsa ya haura sama girarsa a haɗe, Sakeena tabi bayansa da kallo sai kuma ta tallafi Hajar da tke kuka har lokacin ta wuce da ita part din Mami, gsky Mami zata gayawa abinda ta fahimta a zaman auren nan nasu, Mami ta ringa furta subhanallah bayan taga fashewar da bakin Hajar yayi, Mami tace "faɗuwa tayi ne..?", Sakeena ta girgiza kai tace "ko ɗaya Nurain ne ya bigeta", Mami was very shocked, Nurain ne ya bigeta kuma, Nurain din har yaushe ya fara duka, Mami ta wuce da Hajar bedroom snn ta shiga da ita toilet tasa ta wanke bakinta da fuskarta, Mami ta zaunar da Hajar daga gefen gadonta tace ta zauna anan, da haka Mami ta fita zuwa palour, Hajar ta kasa zama a kan gadon ta tashi ta nufi ƙofa ta buɗe, bata fita ba ta rakuɓe jikin ƙofar ta jingina da ita, har lokacin Sakeena na zaune palour tana jiran fitowar Mami, Mami na kallon Sakeena bayan ta zauna tace "what exactly happened Sakeena..?", Sakeena ta juya hannu tace "Mami nidae ban sani ba kawai naga lokacin daya bigeta ne a baki", shiru Sakeena tayi after few seconds tace "Mami", Mami tace "mene ne", Sakeena tace "Ni dae a nawa view din ya kamata ayima Nurain mgana akan yacca ya ɗauki auren nan", nan Sakeena ta wassafawa Mami komai, ta gaya mata yadda yace shi favor kawai yakema Hajar don ba choice dinsa bace kuma ita ba type dinsa bace, har yadda sukay jiya da Hammad da Nurain ya ɓoye masa Hajar matsayin mata saida Sakeena ta gayawa Mami, abinda yafi tsayawa Mami shine favor din nan da kuma yacca yake gayawa jama'a ita din ba matarsa bace, Mami ta numfasa tace "Ina Nurain din yake..?", Sakeena tace "yana room dinsa", Mami tace "Abbanku bai fita ba..", saida Sakeena tayi sak kafin tace "Eh banga fitarsa ba", Mami ta yunƙura ta nufi ƙofa, Sakeena tace "Mother dan Allah karki gayawa Abba ke ki masa mgana", Mami ta girgiza kai tace "A'a gara na gayawa wnda ya aura masa ita" da haka ta fice daga palourn. da sauri Hajar ta sulale ƙasa hawaye ya cika mata ido, surely bbu abinda ba taji ba na mganar da Sakeena ta gayawa Mami, ita ba Choice dinsa bace yess tasan da hakan ai kamar yadda shima ba Choice dinta bane, and yess ita ba type dinsa bace sbd ya fita ta ko ina, daman taya za ai ta zama type dinsa bacin irin tazarar da yayi mata, ita ba ƴar gidan kowa bace babanta mai rauni ne wnda sai ya fita kullum yake nemo musu abinda zasu saka a bakin salatinsu, Shifa Babansa is super rich wnda ya bawa talauci baya, ko daga unguwar da suke zaune ai tasan dole yace ita ba type dinsa bace, ita ƴar ghetto area shi kuma ɗan GRA, ta fashe da kuka mai taɓa zuciya, da Ya Sayyadi Nura ta aura bbu ta inda zaice alfarma yake mata, amma fa wai zaman da take duk na alfarma ne, lokaci guda brain dinta ta sarƙe da irin kalaman da ya gaya mata, (never.. i will never imagine you as my wife and you will never be, Amm young lady dman nace miki inada mata ne abinda na sani shine ni banda wata mata a rayuwa). Hajar ta lumshe idonta hawayen da suka taro suka hau zarya bisa kuncinta, bayan kamar minti ashirin saiga Sakeena nan ta shigo, Hajar ta ɗaga kai ta kalleta, Sakeena tace "Come with me", a hankali Hajar ta tashi tabi bayan Sakeena suka fita daga part din Mami, Sakeena ta nufi great room din Abba ta buɗe ta shiga, saida Hajar ta shiga snn ta rufe ƙofar, Abba da fuskarsa ke a haɗe ya kalli Hajar har ta zauna kan carpet kusa da Sakeena, Mami tayi ajiyar zuciya itama dai fuskar nan bbu annuri, Babu jimawa aka buɗe ƙofa Nurain ya shigo, har ya fara shigowa ciki sai kuma yayi still bayan ya lura da Hajar dake zaune kan carpet, ya dake ya ƙarasa shigowa yana satar kallon Mami da ya lura ranta a ɓace yake, Nurain ya zauna kan carpet ya sunkuyar da kansa baice komai ba, fuska ba yabo ba fallasa Abba yace "who is that lady..?", Nurain ya ɗago ya kalli inda Abba ke masa pointing, a hankali yace "Hajar", Abba ya gyaɗa kai yace "and mene matsayinta a wajenka..?", Nurain ya saukar da kansa baice komai ba, Abba exhale heavily ya tashi ya shiga ɗakinsa, few seconds ya dawo da pen da jotter a hannunsa ya wurgawa Nurain, strictly yace "rubuta mata sakinta..", da sauri Mami da Sakeena suka dubi Abba don basu taɓa zaton hukuncin da zai yanke ba knn, Shi kam Nurain wani irin faskarawa kansa yayi tamkar an buga masa guduma, tini zufa ta fara keto masa bbu shiri duk da sanyin Ac da yake busowa, Mami tace "Amma yallaɓai ba..", Abba ya ɗaga mata hannu yace "Please madam ba dai nina ƙulla wnn auren ba toh ni zan warwaresa, ko ke favor nake miki a gidanki..?", sai kuma ya dubi Nurain yace "you are wasting my time Uthman kayi abinda nace", Nurain bai taɓa sanin cewa akwai ranar da hannunsa zaiyi rawa ba sai wnn moment din, da kyar ya ɗauki pen din ya buɗe jottern amma ya kasa rubutu, lokaci guda idonsa ya rine ya juya ya kalli ƙofa yana fatan Iron lady ta shigo, ina ma dai ta shigo kamar ranar da yazowa da Abba batun sakin Hajar tazo ta hana, muryar Abba ce ta dawo dashi daga duniyar fatan da ya afka, Abba yace "ni zaka yiwa favor ba ita ba Uthman, tinda favor kake mata rubutamin sakinta ka bani..", Nurain ya sauke ajiyar zuciya mai karfi ya ɗan kalli Hajar da tinda ya shigo kanta ke ƙasa, Abba yace "i don't want to repeat my self Uthman", A hankali Nurain ya fara rubutu a paper, rubutun da ya ɗaukesa minti 4 yana yi, yana gama rubutawa ya felle papern ya miƙawa Abba, Abba ya amsa yace "Good you can go to any extinct ka auri wcca bazaka yima favor ba Uthman, and as a father na baka go ahead hundred percent..", Nurain ya shafa fuskarsa da palm dinsa ya tashi ya fita da sauri, Abba ya miƙawa Mami papern yace "keep it with you" da haka ya wuce bedroom dinsa, Samm Mami bata so haka ba don ko riƙe takardar ma bata son yi, Sakeena ta miƙawa tace ta ajiye mata a closet dinta, Sakeena tazo amsar papern ta faɗi a ƙasa, Hajar da hawaye yake zuba daga idanunta ta kalli rubutun jiki, lokaci guda taji kamar an cinna mata wuta a zuciya, ba tasan lokacin da ta fashe da kuka ba, Sakeena da jikinta yayi mugun sanyi ta duƙa ta ɗauki papern bayan Hajar ta gama karancewa tass, Sakeena tayi folding papern tana kallon wani position din, da haka ta ɗaga Hajar dake kuka harda shessheƙa suka bar great room din.......✍️ 💛 HAJAR 💛 {75..} Bangaren Mami Sakeena ta wuce da Hajar wcca har lokacin tke kuka a hankali, Sakeena ta shiga bedroom din Mami bayan ta zaunar da Hajar akan sofa, Closet din Mami ta shiga ta ajiye papern snn ta fito palour, gani tayi Hajar ta zamo daga kan kujerar ta haɗe kanta da guiwa still tana kuka, Sakeena ta zauna gefenta tace "please stop crying dear", da kyar Hajar ta tsayar da kukan don wani suya zuciyarta ke mata, Sakeena tace "have you take your dinner...?", Hajar ta girgiza kai tace "Am not hungry..", Sakeena tace "Ohk Alright". wajen ƙarfe tara Mami ta fito daga ɓangaren Abba, har zata shiga nata sai kuma ta juya ta shiga na Hajiya don ta dubata, tarar da Hajiya tayi ta mimmiƙe ƙafafuwa sai matsa su take, Mami ta zauna gefenta tace "Hajiya barka da dare..", Hajiya na cigaba da matse ƙafarta tace "barka dai ƴar nan", Mami tace "ya hidima", Hajiya tace "Ayyo ai kune masu hidima kuka sha gwagwarmaya, ni kam tinda na jaɓe me na aikata in banda miƙa Noor gidan miji, ai kune da sannu Mami..", Mami tayi murmushi tace "ƙafar ne yake ciwo Hajiya..?", Hajiya tace "wllh kuwa kin san bata son whala ko kaɗan, da muka je gidan Noor wai ashe ɗakin nata na sama ni kuma nayi alƙawari saina dangana da ita har ɗakinta, Toh dai in taƙaice miki saida na hau saman nan da kyar ina jinjina da kuma tara tarar jama'a snn na hau..", Mami tace "ya subhanallah Hajiya ai da baku whalar da kanku ba..", Hajiya tace "Ahap ynxu ba gashi ya wuce ba, ni nan ƴar Albarkar yarinyar nan matar Usuman ma nake jira ta zo ta shafa min man zafi ko naji sassauci, tin ɗaxu da ta fita ban sake ganinta ba", Mami tace "tana can wajena ta kwanta bata jin daɗi ne..", Hajiya ta gwalo ido tace "Allah sarki, nidae tinda ake hidimar nan sai naga tana abu lagwai lagwai duk ba tada wani kuzari ko dai ciki ne da ita..?", Mami tace "ina man zafin na shafa muku Hajiya..?", Hajiya ta saƙa hannu cikin ƙatuwar jakarta dake gefenta ta ciro kwalbar man zafin da Nurain ya kawo mata ta miƙawa Mami tace "kinga man zafin Usuman ne ya bani", Mami ta amshi kwalbar ta buɗe ta fara shafa mata a hankali, Hajiya tace "kin san shi Usuman baya son yaga ina cikin farin ciki da walwala sai ya fara kowa abinda zai ɗaga min hankali, nan yaxo yamin ƙerere a ka wai kar na bari ayi saki a gidan nan, toh wane irin saki ana zaune ƙalou salon a tarwatsa kan ahali, saida dai ya ɗaga min hankali wllh, da kyar na rarakasa da sandata na kaɗasa waje, kuma naji daɗi dana samesa a hannu don shammatarsa nayi..", Mami dai tayi shiru tana mamakin Nurain, wato wajen Hajiya yxo bayan ta faru ta ƙare, Mami na gama shafawa Hajiya man zafin ta mata saida safe ta tafi ɓangarenta. Hajar a wajen Mami ta kwana, washe gari da safe wajen ƙarfe goma mai aikin Mami ta kai mata box dinta, wanka Hajar ta shiga bayan ta fito ta fitar da kayan da zata saka, tana cikin shiryawa mai aikin ta kawo mata breakfast, ko da Hajar ta gama shirin bata kalli abincin ba, bata jin zata iya cin wni abu don maƙogoronta ciwo yake, ga idanunta da sukayi luhu luhu suna mata zafi, After 30mins da kawo mata abincin Mami ta shigo, ganin ba taci ba Mami tace "ya baki ci abincin ba dear..?", Hajar ta saukar da kanta ba tace komai ba, Mami tace "ko ba kya son wnn a kawo miki wani..?", Hajar ta girgiza kai tace "A'a", Mami tace "ko a dama miki Oat..?", Hajar ta janyo abincin gabanta tace "zanci wnn..?", Mami tace "Ohk.. eat a lot kinji dear" da hka ta juya ta fita, da kyar Hajar taci abincin kaɗan ta ture, Shayin ma sip baifi huɗu tayi ba ta ajiye, a hankali ta tashi ta saka hijab dinta ta ɗauki abincin zata kai kitchen, bata son Mami ta dawo taga ba taci sosai ba, bata tarar da kowa a palourn Mami ba don haka direct ta nufi door ta buɗe ta fita, main palour ma bbu kowa ta zaga ta bayan kujera ta shiga kitchen, ajiye abincin tayi kan island ta matsa gaban sink ta buɗe tap tana wanke hannunta, door aka buɗe ya shigo ya mayar da door din ya rufe, sak Hajar tayi after perceiving his scent ta kashe tap din ta juyo kanta a ƙasa ta nufi door zata fita, kallonta ya ringa yi without blinking, kwata kwata jiya bai rintsa ba, yacca yaga rana haka yaga dare, bai taɓa shiga ɗimuwa ba irin ta jiya da Abba ya tarfasa yace ya saki Hajar ba, sosai ya shiga damuwar da har wayewar gari bai samu sassauci ba, sosai ya lura da haurawar da idanunta sukay duk da cewa bata kallesa ba, tana zuwa kusa dashi zata wuce yayi saurin riƙo hannunta, da iya ƙarfinta ta fara fincikewa ta wani murtuke fuska, sakinta yayi da wata iriyar murya yace "Hajar", ta rufe fuskarta da tafukan hannayenta ta fashe da kuka, ya ringa kallon slim fingers dinta da suka ji jan lalle, lokaci guda ya janyota jikinsa ya rumgumeta, da ita a jikinsa yaje ya sakawa door lock kafin ya fara patting din bayanta a hankali, har lokacin kuka take rusa masa don wni irin zafi zuciyarta ke mata, ya sauke ajiyar zuciya a saitin kunnenta yace "Please please stop crying Hajar..", bai saketa ba duk da irin attempting din kwace kanta da ta ringa yi, almost 10mins tana jikinsa stiil yana patting bayanta har saida ta dena kukan ta dawo jera ajiyar zuciya, ya saketa a hankali ya ringa kallon fuskarta kafin ya kai babban finger dinsa ya share mata ragowar hawayen da suke kwance cheeks dinta, hannunta ya riƙe ya nufi ƙofar kitchen din wcca tayi leading zuwa backyard, ya buɗe ƙofar ya fita hannunta cikin nasa, ganin sun fito waje Hajar ta turje, ai kam without second thought ya sunkuceta ya zaga ta baya har zuwa parking space, babu wnda ya lura dasu har ya buɗe motarsa ya sakata, Hajar ta kurma ihu tace "meye haka, where are you taking me..?", tini ya zaga driver seat ya buɗe ya shiga motar da haka ya bar gidan bayan mai gadi ya buɗe masa gate, tin Hajar na bubbuga glass din motar tana cewa ya ajiyeta har ta haƙura ta haɗe kanta da guiwa tana hawaye, habawa ai Nurain saida ya gansu a ƙofar gidansa snn ya samu relief, fita yayi yaje ya buɗe gate ya dawo ya shigar da motar ciki, yana gama parking ya lumshe idonsa yana sauke ajiyar zuciya, ya fakaici kallon Hajar kafin ya buɗe motar ya fita, entrance din gidan ya nufa ya ciro key ya bude main door, dawowa yayi wajen motar ya bude side dinta ya ɗauketa ya nufi cikin gidan da ita, har room dinta ya kaita ya ajiyeta bisa gado yace "we are home Hajar", ta ɗago kanta tana ƙarewa room din kallo sai kuma ta taɓe baki tace "this is not my home and it will never be", ya waro ido yace "really", ta gyaɗa kai tana turo baki tace "everything da ake maka favor dashi there is no way da zaka kirasa da naka..", yayi blushing yace "are you sure Silly girl..?", ta gyaɗa kai tace "Eh dan haka nan din is not my home", Nurain ya kalli lips dinta yace "your lips are aching right", juya masa baya tayi bata sake cewa komai ba. Sakeena ta miƙawa Mami papern hannunta snn ta samu waje ta zauna, a hankali Mami ta fara warware takardar zuciyarta na sinking, gwara dai ta duba taga saki nawa ya mata duk da tasan bazai wuce ɗaya ba, Mami ta ƙanƙance ido bayan ta gama karanta papern, Sakeena dake ankare da expression dinta tace "Saki nawa ne..?", Mami ta miƙa mata takardar without saying anything, Sakeena ta amsa ta karanta, tana gamawa ta kwashe da dariya tace "Abinda ya rubuta knn.. toh ai ni banga saki ba", Mami ta girgiza kai ta sake amsar papern ta karanta, samm bbu alamar saki a jiki don ko ambaton sunan Hajar din ma beyi ba, kawai dai ya cewa Abba he is very sorry amma bazai iya sakin matarsa ba, Mami ta tashi ta fita da takardar a hannunta, ɓangaren Abba ta wuce, a bedroom dinsa ta tarar dashi, ba wani wala wala ta basa papern, saida Abba ya saka glasses dinsa snn ya duba, ya kalli Mami ya kalli takardan yace "what is this..?", Mami tace "Papern da kace na ajiye maka jiya ce..", yace "I don't understand ba divorce paper na baki ba..?", tace "not at All abinda Nurain ya rubuta knn", Abba ya cukuikuiye papern yace "how dare him play with our intelligence, where is your Son Mami..?", Mami ta numfasa ganin Abba na shirin fusata ta saukar da murya tace "yallaɓai dan Allah mubi komai a hnkali Please, tinda kaga Nurain bai saki yarinyar nan ba toh yana son zama da ita wllh, i know him wllh tinda yaƙi sakinta yana son zama da ita..", Abba ya haɗe gira yace "yana son zama da ita ya cigaba da mata favor knn..?", Mami ta girgiza kai tace "No yallaɓai ba dai zaman Alfarma ba, saidai ya zauna da ita don ta isa kuma ta kai a zauna da ita matsayin mata, wnn shine chance dinsa na ƙarshe, please a masa haƙuri this one, i will handle the case now..", Abba exhale heavily yace "daga wnn moment din kar Nurain ya sake cewa favor yake ma my daughter, this is my last warning..", Mami tace "Sure". Mami na komawa ɓangarenta ta tarar da Hajiya zaune kan sofa da sandarta a hannu, Hajiya tace "hankalina yaƙi kwanciya wllh tin jiya da kika ce yarinyar nan ba lfy, gashi yau da safe nayi ta zuba ido naga ta shigo amma shiru kake ji, shine na wanko sayyadata naga yata kwana..", Sakeena ta fito daga room din da Hajar ta kwana tana tattare gira, Hajiya tace "Sakeenatu ya kika fito ke kaɗai ince yarinyar kika shiga kira..", Sakeena tace "bata nan, nasha ma tana toilet na tsaya jira ta fito toh ashe ma bata ɗakin gaba ɗaya", Mami ta kalli Sakeena tace "where did she go..?", Sakeena tace "bari na dubata waje da Kitchen", duk inda ake tunanin Hajar zata shiga a gidan an duba amma bata nan, har ɓangaren Hajiya Sakeena ta sake dubawa wai ko sun samu saɓani amma bbu Hajar, Sakeena ta dawo a bit confuse tana kallon Mami tace "this is weird I can't find her", Hajiya ta ringa salati da sallallami tace "yarinyar allura ce da za a ce ba a ganta ba a gidan nan", Mami ta tashi ta shiga room dinta, wayarta ta ɗauka tayi dialing numbern Nurain, tana daf da katsewa ya ɗaga, Mami bata basa chance din mgana ba tace "where is she Nurain..?", Nurain ya tashi daga gefen gadon ya nufi door da wayar a kunnensa, Hajar tabi bayansa da kallo ta haɗe fuska, Nurain yace "tana gida", Mami tace "wane gida..?", shiru yayi baice komai ba, tini Mami ta sake gasgata hasashenta, strictly tace "i want to see you now" bata jira cewarsa ba ta katse kiran, Nurain ya ciro wayar daga kunnensa tare da sauke ajiyar zuciya. Hajar ta miƙe zaune gami da murje fuskarta a hankali, ba tayi wata wata ba ta buɗe wardrobe ta ɗauki box din da aka kawota da ita, tini ta bude section din da kayanta suke, duk kayan da ta san nata ne wnda tazo dasu gidan saida ta cirosu ta zuba a box din, tana gama kwashe kayanta tass ta zuge box din, bathroom ta shiga ta wanke fuskarta ta fito, da haka ta sauke box din ta jata ta fita daga room din, har wani bugu zuciyarta take tana fatan kar Allah ya haɗata dashi, daga nan sai gidan ubanta inda zata zauna ta sakata ta wala wnda baza ace alfarma ake mata ba, da kyar ta sauka downstairs da box din, direct ta nufi door ta murɗa handle, wani irin bugu zuciyarta tayi bayan taji ƙofar a kulle, ta sake murɗawa ta jita a kulle, wata ball ce ta tsaya mata a throat mai taurin bala'i, da sauri ta shiga kitchen ta duba ƙofar fita backyard ita ma dai taga a rufe take, walking like a chameleon ta fito hawaye ya cika idonta, wllh saita tafi gidansu, tasan ubanta bai aurar da ita don a mata alfarma ba. Nurain na isa gidansu direct wajen Maminsa ya shiga, sallamar da yayi ma Sakeena ce ta amsa, walking gently ya shiga palourn ya zauna kan Carpet, Mami ko kallon position dinsa ba tayi ba her eyes fixed on tv, Sakeena ta tashi ta shiga bedroom da plate din dice pineapple da take sha, Nurain ya shafa kansa yace "Mami barka da rana", ko kallonsa ba tayi ba bare yasa ran zata amsa masa, pen da jotter da ta ajiye a side dinta ta dauka ta miƙa masa tace "saura nima ka rubuta min irin abinda ka rubutawa baban ka", Nurain ya sauke numfashi yana kallon jotter da pen din, Mami tace "take now ka rubuta abinda kaƙi rubutawa jiya", ya shafa kansa yace "Mother wllh bxn iya sakinta ba, i can't do that", Mami ta gyaɗa kai ta ajiye jotter da pen din gefenta don daman so take ya faɗa da bakinsa cewa bazai iya sakinta ba, full attention dinta ta mayar kansa tana kallonsa da kyau tace "kasan bazaka iya sakinta ba shine kake iƙirarin cewa favor kake mata, kasan bazaka iya sakinta ba kake cewa ita ba choice dinka bace, duk kasan da hkan kuma kasan ba type dinka bace amma ka ƙi sakinta", Nurain dai baice komai ba fatansa dai kar a rabasa da Silly girl, Mami wasn't easy on him, saida ta tabbatar ta kwashe masa wnn girman kan tass, don kawai hangowa take ai ƴarta ce mijinta yake cewa ai alfarma yake mata, saida ta sule Nurain tass snn ta ƙare da faɗin "this is the least we expected from You Nurain, babanka bai taɓa sanin zaka watsa masa ƙasa a ido kamar haka ba shiyasa ya amso mka auren yarinyar nan", Nurain yace "Am so sorry Mother", Mami tace "don't mother me Uthman", Nurain ya ajiye numfashi yana jin kamar an watsa masa garwashi a zuciya, Mami ta nuna masa room din da box din Hajar take tace "wuce ka ɗauki box din tinda ka ɗauke me ita, and wnn shine last warning da zan mka akan Hajar, snn kuma Abba na jiranka a great room", Nurain bai iya cewa komai ba ya tashi ya shiga room din ya fito da box dinta, bai tarar da Mami a palour ba koda ya fito, door ya nufa ya fita main palour, yana jan rigarsa sai kace mai son ƙara mata tsaho ya shiga great room din Abba, dman yasan Abba bazai masa wani mgana ba tinda already Mami tayi, as expected Abba bai ce masa komai ba kawai ya amsa apology da ya nema. Hajar dake zaune kan stairs ta ƙurawa ƙofa lulu eyes dinta da suka haura matuƙa, da sauri ta miƙe jin an zura keys a ƙofar alamar za'a buɗe, kallonsa ta ringa yi har ya shigo ya ajiye ledar takeaway da ya tsaya a eatery ya siyo mata lunch don yasan da kyar idan ta dafa, ya sake komawa wajen ya dauko box dinta da ya ajiye a balcony, da haka ya mayar da ƙofar ya rufe ya zare keys din ya zura a pocket, Hajar ta saukar da kanta tace "why did you do that bayan mun sami chance..?", Nurain yayi folding hands dinsa yace "wani chance..?" yana kallon box din da ke gefenta, tace "Chance din da aka baka jiya na datse alaƙar dake tsakaninka da wcca kake yima favor, am not asking for much wllh just a piece of paper can end this relationship", Nurain yayi blushing moving towards the stairs yace "really.. but I can't divorce my wife..", Hajar was very shocked jin abinda ya faɗa, ta ringa kallonsa without blinking kafin ta haɗiyi wani yawu tace "your wife.. where is she...?", harda wani ƙanƙance ido ta faɗi hakan, bai ce mata uffan ba ya fara hawa stairs din, saida yaje step din dake kusa da wnda take kai snn ya dakata, ya ɗora hannunsa kan nata dake riƙe da railer, ta fara ƙoƙarin zame hannunta amma ya hana hkan, a hankali tace "let go off my ha...", maganar bata ƙarasa fita ba sakamakon saukar lips dinsa a forehead dinta, da sauri ta lumshe idonta don hakan yazo mata a bazata, after a while ya janye lips dinsa daga forehead dinta, ya rage murya yace "Delete all those stuffs from your head..", ta haɗe gira tana buɗe baki da shirin yin mgana ya haɗe lips dinsa da nata, and he gave her french kiss din da ya matuƙar firgitata ya kwance mata notin kai wnda ya ratsa har zuwa yatsun ƙafarta, saura ƙiris ta zube a ƙasa amma kuma bata zube din ba sbd riƙon da ya mata, he kissed her for almost a minute kafin ya haɗe forehead dinsu waje guda, ya goga karan hancinsa a nata yace "Tonight i will surely show you that you are my wife", yayi ajiyar zuciya yace "Tonight"......✍️ 💛 HAJAR 💛 {76..} ★Bayan sallar la'asar wajen ƙarfe huɗu da rabi Naseer ya shigo gida da sallama, Nabilah dake zaune tsakar gida tana jajjaga kayan miya ta amsa sallamar tasa, tace "Yaya sannu da zuwa..", yace "yauwa Baba ya dawo..?", tace "Eh ya dawo amma ya fita masallaci har yanxu bai dawo ba", yace "Maama fa..?", Nabilah tace "ita tin ƙarfe uku ta fita", Naseer ya jinjina kai bai sake cewa komai ba ya buɗe ɗakinsu ya shiga, Umma ma bata nan don ɗakinta a rufe yake da padlock, Naseer na zaune ɗakinsu yana cin abincin da ya siyo yaji sallamar Baba, saida ya gama cin abincin snn ya tashi ya fita, kai tsaye ya wuce ɗakin Baba ya shiga da sallama, Baba ya dubesa yace "A'a Nasiru har ka dawo..?", Naseer ya zauna kan tabarma yace "Eh Baba", ya ciro wata paper daga aljihunsa ya miƙawa Baba yace "gashi Baba", Baba yaƙi amsar takardar yace "ba sai naga takardar ba yimin bayani kawai", Naseer yace "tom" daga haka ya fara yiwa Baba bayanin filin da aka siyar da kuma adadin kuɗin, Baba ya gyaɗa kai yace "masha Allah... sai a raba kuɗin gida uku, a ɗauki kaso ɗaya a yiwa Nabilah hidimar aure kamar yacca aka yiwa Hajara", Naseer yace "toh Baba sai a cire lissafin katifa ni zan siya", Baba yace "Allah yayi albarka", Naseer ya shafa kansa yace "Ameen", da daddare Baba na zaune tsakar gida bisa darduma yana cin abincin da Umma ta ajiye masa, Maama ta fito daga ɗaki zata shiga kewaye, ɗaga kai Baba yayi ya kalleta yace "Rabi", banza tayi dashi ta ɗauki buta tayi gaba abinta, bayan ta fito har zata koma ɗaki Baba ya sake kiranta, juyowa tayi tace "wai waye yake min shegen kira ne sai kace tsohon makaho", Baba ya rausayar da kai yace "idan kinga dama kixo idan kuma baki ga dama ba kar kizo", ƙasa ƙasa taja tsaki ta nufi inda yake ta zauna kan kujera ɗan nesa dashi, Umma dake zaune tsakar gidan itama ta tashi ta shiga ɗakinta, Maama ta bita da kallo sai kuma ta taɓe baki tace "gani fa mal Adamu", Baba yayi gefe da kwanon abincin yace "A matsayinki na uwar Nabilah nawa kike buƙata wnda zaki tsinto mata tarkacen kitchen da sauran su..?", Maama ta haɗe fuska tace "ban gane ba kuma ban fahimta ba, ji nake an mayarwa da yaron nan kuɗinsa", Baba yace "A sbd me za'a mayar masa da kuɗinsa", Maama tace "sbd ni uwar Nabilah banyi na'am dashi ba, bana sonsa kwata kwata don haka dole a fasa auren nan", Baba yace "toh baki isa ba auren Nabilah ba fashi..", Maama ta hura tukubar hancinta tace "mal Adamu karfa ka wani zaƙalƙale ehe, ita Nabilahr ai cewa tayi ta fasa auren", Baba ya kwalawa Nabilah kira bbu jimawa ta fito bayan ta amsa, ta duƙa gabansa tace "Baba gani", yace "kina son auren Tanimu ko ba kya so", Nabilah tayi shiru ba tace komai ba, Maama tace "Ahap ai na gaya mka", Nabilah ta kalli Maama wcca take ƙifta mata ido wai tace eh, Nabilah ta sunkuyar da kanta, Baba yace "Rabi ki bari yarinya tayi mgana da bakinta", Maama ta rausayar da kai tace "Toh ai gata nan", Baba ya sake kallon Nabilah yace "ba kya so..?", Nabilah ta girgiza kai, Baba ya sauke ajiyar zuciya yace "jeki abinki", Maama ta saki baki tabi Nabilah da kallo harta koma ɗaki kafin tace "amma dai yarinyar nan kin shammaceni... shekaran jiya na gama mgana dake ringiɗi ringiɗi kika ce kin fasa auren mai pachi shine ynxu zaki baɗamin ƙasa a ido", da haka ta tashi tabi Nabilah ɗakin tana sababi, Nabilah kam tayi mata shiru, Sa'adatu kam sai zabga tsaki take don Maama ta cika ɗakin da zance, Sa'adatu da ta gaji tace "haba dan Allah Maama sai ihu kike mna", Maama tace "ba dole nayi ihu ba, kina gani wnn yarinyar mai ƙwaƙwalwar kifi wai har ynxu bata bar mganar Tanimu mai pachi ba, so take tayi auren da zata ringa dawomin tana cewa na bata masara...", Maimuna tace "duk wnda yace zai haɗiyi gatari ai sai a sakar masa ƙota, ba dai ita tace taji ta gani ba", Maama tace "mai pachi fa ƴar nan ta jajiɓo...", Maimuna tace "A'a ai ynxu naga yana ƙulla gawayi ma", tashi Nabilah tayi ta bar musu ɗakin, zama tayi tsakar gida tana share hawayen dake zuba idonta, Baba na gama cin abincinsa ya ajiye kwanon yaje ya wanke hannu, duk yana sane da Nabilah dake matse hawaye. wajen ƙarfe goma Naseer ya shigo gida har zai shiga ɗakinsu ya tarar da Baba a ƙofar nasa ɗakin, Baba yace "Mu'azzam ya shigo..?", Naseer yace "ynxu na gansa wajen mai shayi amma nasan ba zai jima ba zai taho", Baba yace "Toh... Abinda nake so da kai Nasiru ko bayan raina kar a fasa auren Nabilah indai ba da wani ƙwakkwaran dalili ba, wnn wasiyya ce na bari..", Naseer yace "insha Allah ma kai zaka ɗaura auren Baba", Baba yace "ko dai bayan raina kaji dai me nace", Naseer yace "Eh", Baba yace "Port Harcourt din zaka wuce gobe..?", Naseer yace "insha Allah", Baba yace "toh saida safe" da haka ya juya ya koma ɗakinsa. ★Tinda Hajar ta idar da sallar la'asar take kwance inda tayi sallar, lokaci zuwa lokaci saita turo baki sai kuma ta harari iska, zaune ta miƙe ta kalli box din kayanta da ya shigo mata dasu, da wcca ta hada da kuma wcca ya taho mata da ita daga gidansu, a kan chest of drawers taga ledar abinci da ya ajiye mata wnda ƙamshinsa ya cika ɗakin, a hankali ta tashi taje ta ɗakko ledar ta buɗe, fried rice ce da taji kayan lambu sai rabin peppered chicken a gefe da plaintain, shinkafar kawai ta ɗan tsattsakura ta ajiye don ba tada appetite ma, kan chest of drawers ta mayar da abincin ta koma ta cigaba da kwanciya, bayan sallar magrib ta ɗauki ledar abincin zata kai kitchen don ƙamshinsa ya takura mata, a hankali ta buɗe ƙofa ta ƙarewa long corridorn kallo, bayan ta gama surveying corridorn da ido tayi ajiyar zuciya ta fito, walking slowly ta sauka downstairs, a hankali ma ta murɗa handle da zata shiga kitchen, ta ringa kallon kitchen din ganin shopping bags kan island da cabinet harda wasu ma a ƙasa, ta tsallake ta samu guri ta ajiye abincin da haka ta buɗe fridge, tana buɗe fridge din shima ta gansa a cike, ita dai ta ɗauki ruwa abinta ta zagaye ta fita, tana fita palour ta isa gaban main door ta murɗa, ta ajiye numfashi bayan taji ƙofar a kulle, wani ƙululu ne ya tsaya mata a throat don da a buɗe take kawai fecewa za tay abinta, da takaici ta haura sama ta koma room ɗinta, tin ƙarfe takwas da minti goma dman ta haye gado ta rufe da duvet har kai, hka nan saddan taji gabanta na faɗuwa shiyasa ma ta kwanta da wuri, ji tayi an buɗe ƙofa tayi sauri ta runtse idonta, zuciyarta har wani ɗif ɗif take after perceiving his scent, Nurain yafi minti uku yana kallonta kafin ya juya ya fita, ta sauke ajiyar zuciya bayan taji fitarsa, har goma saura Hajar ta nemi bacci ta rasa a idonta ta ringa juye juye tana so bacci ya ɗauketa amma ta kasa, lokaci guda ta sauko daga gadon, box din kayanta da ta kudurce bazata mayar dasu wardrobe ba har zuwa lokacin da zata samu chance din tafiya gidansu ta buɗe, showel gel da sponge ta ɗauka da haka ta shiga bathroom don yin wanka, gani take wankan da ba tayi bane yasa ta kasa bacci, bayan ta fito ta zauna kan stool, sharp sharp tayi rubbing lotion dinta wnda shima ta fitar daga box, perfume da take shafawa da daddare mara hayaniya ta shafa, tana gama fesa hair spray a gashinta zata ajiye gwangwanin knn aka buɗe ƙofa, sosai zuciyarta ta buga ta kalli ƙofar da sauri, Nurain ya daskare a inda yake tsaye riƙe da handle yana binta da kallo from head to toe, fararen pajamas ne a jikinsa masu riga armless da sweat pant, a gigice ta miƙe ta nufi inda hijab dinta yake, sai dai kafin ta kai ga ɗaukar hijab din har ya shigo ɗakin yayi sama da ita, Hajar ta tsala ihu jinta akan isa tace "Ni bana son haka ka ajiyeni", ko sauraronta beyi ba ya juya ya fita da ita daga ɗakin, bai tsaya a ko ina ba saida ya dangana har huge bedroom dinsa snn ya ajiyeta kan makeken gadonsa da yasha pure white bedding, tini ta hantsilo ƙasa ta miƙe tsaye gami da riƙe towel dinta tamau hannu bibbiyu, Nurain ya zuba hannayensa a pocket yana kallonta yace "Hey a kan wuta na ajiyeki ne..?", idonta har ya ciko da ruwa ta juya tana kallon ƙofa, ai kam kamar yasan abinda za tay shima ya kalli ƙofar, lokaci guda ta kwasa a guje ta nufi door har ta murɗa handle yayi saurin fixgota bayan ya hadata da jikin door din ya rufe, tini ta sakar masa kuka jin ya sakawa ƙofar lock, ya duƙa ya kalli lips dinta da suke rawa yace "Tin ynxu ma kin fara kuka yarinya... even before a kiss that you must beg for mercy", Hajar ta yarfe hannu har ta jiƙa cheeks dinta da hawaye tace "dan Allah dan Allah... ni wllh room dina zan tafi", ya ɗage gira his eyes fixed on her face yace "No you must spend the night here", in banda bugu bbu abinda zuciyarta take, a hankali ta gyaɗa kai tace "Naji toh i need to wear my clothe first", slight smirk yayi yace "you don't need ta wear anything tonight..", ta haɗiyi wani yawu ta share hawayen da yaƙi tsaya mata, sosai ta marairaice murya tace "dan girman Allah da manzonsa... dan darajar iyayenka ka taim...", kafin ta ƙarasa ya ɗora finger dinsa a lips dinta ya girgiza kai yace "don't", da haka ya barta tsaye bakin ƙofar ya shiga huge Closet dinsa, few seconds ya fito da farar Shirt a hannunsa ya ajiye gefen gado, yana kallonta yace "ba dai clothe zaki dakko a room din naki ba toh gashi nan kisa wnn", maƙe shoulder tayi tace "Ni bana son wnn nawa nake so", ya tsuke piercing eyes dinsa yace "ohh really", ya matsa kusa da ita, ba tayi aune ba sai jin hannunsa tayi zai kwance mata towel yace "lets remove this one ma", tini ta zille ta matsa gaban gado ta wafci shirt din sai kuma ta koma can side din gadon tana turo baki, wani muskilin murmushi yayi ya nufi door ya buɗe ya fita ya saka lock ta waje, Hajar ta sauke ajiyar zuciya sai kuma ta kalli Shirt din hannunta, room din ta ƙarewa kallo wnda yayi biyun nata, ga wani mugun sanyi da yake ratsa mata fata, rigar ta warware wcca ta shaƙo scent dinsa, har rabin cinya rigar tazo mata da ta saka, after like 10mins ta gaji da tsayuwa ta zauna gami da takure kanta waje guda, ɗago kanta tayi jin an buɗe door, ya ƙarasa shigowa ciki bayan ya saka lock a ƙofar, ya ajiye hijab dinta da ya biya ɗakinta ya ɗakko a gefen gado, sai kuma ya ajiye ledar da ya ɗauro kan plate a kan carpet, Hajar ta tashi tana kallon hijab dinta da ya ajiye, Nurain ya sauke ajiyar zuciya yabi fresh laps dinta da kallo, ai kam tini Hajar ta zaga ta inda hijab din yake ta dauki abinta ta kirma, shi dai bai ce mata komai ba, taga ya wuce inda ya shiga ɗaxu da zai ɗauko mata Shirt, bai wani jima ba ya fito yana jan hannun jallabiyan da ya ɗora kan Pajamas da alamar ruwa a fuskarsa, ba tare da ya dubeta ba yace "go and perform ablution..", ta wani tsaya sai kace soja tace "Ah ni nayi sallah na", yace "toh wnn is different tare za muyi", ta maƙe shoulder ta koma jikin door tace "dan Allah ka bude min na tafi room dina..", yace "Ohk okay idan kinyi sallah sai na buɗe miki", ta saki baki tana kallonsa zuciyarta na wasiwasin abinda ya faɗa, ta saukar da murya tace "dan Allah idan nayi sallahn zaka budemin..?", ya gyaɗa kai yace "Sure", walking like a chameleon ta dawo ta tsaya kan lallausan carpet din da ya shimfiɗa babbar prayer mat a kai, yana kallonta bbu ko ƙiftawa yace "Ablution..", ta turo baki tace "Ni nayi alwala na", don duk lokacin da tayi wanka da daddare sai tayi alwala, ba dai Sallah ce zata rabasu ba toh taji za tayi sallah ya bude mata ta tafi, kamilar Sallah raka'a biyu ya jasu wcca ya biya surori masu ɗan tsaho, bayan sun idar da Sallahn taga sai Addu'a yake, Alla Alla take ya shafa ya bude mata ta ƙara gaba, saida ya kwashe almost 5mins yana addu'a snn ya shafa, ya juyo yana kallonta, tana ɗago kai sukay ido huɗu ya sakar mata murmushi mai kyau, Hajar was so surprised with that smile ta kasa dena kallonsa, lokaci guda ta saukar da kanta tana wasa da fingers dinta, Nurain yayi ajiyar zuciya ya tashi ya cire jallabiyan jikinsa ya bar ainahin white pajamas, ya buɗe ledar roasted chicken da ya shigo da ita, cinya ya ɗauka ya miƙa mata without saying anything, ta girgiza kai murya ciki ciki tace "Nayi sallahn Please open the door", yace "why would i open the door...?", tini ta ɗago ta kallesa da mamaki, ya ɗaga shoulder yace "Ohh i will only open it idan kika ci wnn", ta girgiza kai lulu eyes dinta suka ciko da ruwa tace "please am begging you ka bude min na tafi", yace "Ohh i will amma eat first", Hajar ta amshi kazar ta riƙe a hannu after few seconds ta kai baki, yaga uku tayi ta ajiye tace "toh open", ya ture ledar kazar daga gabansu ya matso daf da ita har tana jin breathing dinsa yace "have you forgotten Silly girl... i have to show you that you are my wife remember", tini ta fara muskutawa baya ai kam ya riƙo hijab dinta, habawa saita miƙe zumbur unfortunately saiga hijab din a hannunsa bayan ya sule daga jikinta, ta fashe da kuka tace "Allah kuwa ba haka mukay da kai ba, kai fa kace idan nayi sallah zaka buɗe min na tafi", murmushi mai sauti yayi ya miƙe tsayen shima yace "na fasa", tana ganin ya fara tunkararta ta ringa tafiya da baya har saida ta kai bango, still dai taga zai biyota bangon ai kam tayi gefe zata zille amma ina don tini ya riƙota, ta tsala wani uban ihu ganin ya mata rumfa tace "Ummana... wayyoh Ummana", lips dinta da suke shivering kawai yake kallo, ya ajiye numfashi ya riƙo ƙugunta getting even more closer to her, turasa ta fara yi tace "kar fa ka mnta kace am not your wife and I will never be..", ya manna mata kiss a right Cheek da muryarsa da har ya fara canzawa yace "Now i will show you who am i to you... you are my Halal..", kuka take harda shessheƙa ta girgiza kai tace "please No... Hajar ce fa wnn ba choice dinka ba...", ya sake manna mata wani kiss din a left cheek yace "Action speak louder than voice" daga nan bai sake bata damar mgana ba ya haɗe bakinsu waje ɗaya, passionately yake kissing dinta babu wani sassauci, tini ya fara loosing stamina dinsa, tsayuwar ma ta fara gagararsa ballantana ita da daman shi ya riƙeta, don haka ba wani jinkiri ya ɗauketa sai gado, remote control dake kan bedside ya ɗauka ya rage hasken ɗakin ya bar dim, Hajar da numfashinta ya ɗauke na wucin gadi ta danna wani ihu jikinta na ɓari kamar an jona mata mazari, bakin ihun ya rufe snn kuma ya zafafa lamarin, da haka ya rabata da kayan jikinta wnda ma basu samu fita ta arziƙi ba don farkesu akay, daga nan shima ya rasa control, Hajar ta kwallara ƙara bayan taji azabar da bata taɓa jin irinta ba tinda uwarta ta haifeta, bama gentle yabi da ita ba extra gentle ne amma saida taji azaba, lokaci guda ta fara magiya tana haɗasa da Allah amma ina bai ma san tanayi ba, da taga magiyar bazai kaita ba sai ta fara kokawa, anan ya gwada mata ba ƙarfinsu ɗaya ba, cixo yakushi da mintsili bbu wnda ba tayi ba amma a banza an yakushi kakkausa, And at that night bummmm the bomb exploded, ba part one ko part two na raini aka fitar ba, shi rainin gaba ɗaya aka fitar don anyi mai kankat.......✍️ Join my WhatsApp group to read page 77, or go to Arewabooks.... 👇 https://chat.whatsapp.com/JQi46zH5Se3IvhrdEGHdIA 💛 HAJAR 💛 {77..} Nurain ya buɗe lumsassun idanunsa tare da yin ajiyar zuciya, juyawa yayi ya dubi Hajar dake gefensa, ya miƙe zaune ya kunna hasken ɗakin yana kallonta da kyau, kana ganinta kasan tayi laushi tamkar flour da ta sha bugun gardi, shi dai bai san tayi laushi hka ba amma he vividly remember what just happened, yasan shi ya ƙarar mata da strength, ya kalli fuskarta da tayi jajir tare da lallausan gashinta da ya baje kan pillow wnda shi ya hautsinasa, ya lulluɓeta da duvet snn ya tashi ya shiga bathroom, da sauri ya gama kimtsa kansa ya fito yana goge sumarsa da ƙaramin towel, sharp sharp ya saka white singlet da short nicker don so yake ya kula da yarinyar kuma, shi yayi aika aika don haka shi zai gyara, kan gadon ya isa ya zaune gefe yana kallon innocent face dinta, ya shafa cheek dinta da hawaye ya bushe a kansa, a hankali yayi tapping dinta gami da rage murya ya kira sunanta, ko motsi Hajar ba tayi ba bare yasa ran zata amsa, ya kamo hannunta ai kam yaji she's very weak don baya tinanin tana cikin conscious dinta, da sauri ya miƙe daga gadon ya shiga bathroom bbu jimawa ya fito da ruwa a bowl, kaɗan ya zuba ruwan a hannunsa ya yayyafa mata a fuska sai kuma ya hura mata iska ya kira sunanta, haka ya cigaba da mata har saida taja numfashi, yana ganin haka ya ɗora goshinsa saman nata yace "open your eyes baby girl" sai kuma ya ɗago yana kallonta, after few seconds Hajar ta buɗe idonta da suka kumbura wnda suke mata wani zugin barkono, suna haɗa ido dashi tayi saurin kawar da kanta gefe lokaci gudu hawaye suke fara zarya bisa kuncinta, ga wata azaba da ta yanko mata tin daga waist har zuwa laps dinta, ji take kamar ana mata ruwan allurai, tinda yaga ta farafado bai tsaya wani jinkiri ba ya ɗauketa kawai, ya ringa kallon inda ya ɗagata kafin ya wuce bathroom, a wnn dare Hajar taga jalala, ji tayi kamar a ruwan jajjagaggen attaruhu ya sakata, ba iya Umma ta ringa kira ba har yayanta da little sister dinta saida suka sha kira, Nurain pity her don yasan she's in pain, haka dai ya cije ya gasa abarsa don hakan shine zaisa taji dama dama, A kan couch ya ajiyeta tana nannaɗe da bathrobe dinsa, sai jan zuciya take idonta a runtse don tinda ta farka sukay ido hudu bata sake buɗe idonta ba, closet ya wuce ya dauko mata wata shirt dinsa mai laushi, inda take kan couch ya nufa ya kai hannu zai kwaye bathrobe din, tini ta ƙanƙame bathrobe din, sakar mata yayi ya ajiye mata Shirt din akan cinya, ta wani turo baki ta cukuikuiye shirt din a hannunta, upper bedsheet din gadon ya kware ya shiga dashi bathroom, After like 10mins ya fito, idonsa a kan couch ya fara sauka, yaga ta saka rigar ta jinginar da kanta a couch din, walking gently ya isa gaban couch din ya duƙa, ya ringa kallonta without blinking, wato an samu sauƙi tinda gashi bacci ma take saidai kuma har ynxu jan zuciya take, ya tuna ranar daya fara ganinta da rashin kunyar da ta zabga masa a duk wasu encounter dinsu kafin a aura masa ita, yayi blushing bayan ya tina dramas dinta da yasha bayan aure, duk wata rashin kunya da ta masa yaji tayi fading a zuciyarsa don gani yake shafar mai ne akan abinda ya mata, he took away her valuable item her honor her pride wnda a ynxu yasa yake matuƙar ganin kimarta, he found his wife intact wllh, murmushi yayi bayan ya tuna yadda ta kasance ɗaxu a hannunsa, yafi minti goma yana a haka kafin ya miƙe ya ɗauketa gami da haɗata da ƙirjinsa zai mayar da ita gado, Ai kam ta buɗe idonta bayan ya ajiyeta a kan gadon, a gigice ta fara shirin miƙewa har jikinta na rawa, ganin yacca ta tsorata kawai ya rumgumeta ya kwanta da ita a jikinsa, ta fashe da kuka tana ƙoƙarin kwace kanta ƙarfi da yaji don sosai ta firgita, gam ya riƙeta motsin ma ta kasa sai kuka, yayi ajiyar zuciya yace "wollah i will not hug pillow bayan i have my wife" da haka yaja duvet ya rufa musu, ya kai lips dinsa saitin kunnenta yace "let me give you warm baby girl", tayi lamo listening to his heartbeats, lumshe idonta tayi tana jin ydda yke shafa tin daga bayanta zuwa wet hair dinta, few minutes kam ta koma bccinta deeply in his arms. Da Asuba Hajar ta farka ta buɗe idonta a hankali, ta ringa bin room din da bbu wani haske sosai da kallo, sai kuma ta juya ta kalli both sides dinta taga ita kaɗai ce a makeken gadon, da kuzarinta ta yunƙura ta miƙe zaune gami da zuro ƙafafuwanta ƙasa, tana taka ƙafarta a ƙasa taji wata azaba data shallake tunaninta wccca ta ratsa har brain dinta, ta fasa ƙara a gigice sai kuma ta tafi luuu ta faɗa kan gadon da baya, ji tayi kamar ana mata ruwan allurai a laps dinta, lokaci guda brain dinta tayi booting on hawaye suka fara sakko mata, tafi minti biyar a kwance kafin zugin da jikinta yake mata ya ragu still dai bata dena hawaye ba, tana ji aka buɗe ƙofa aka shigo amma bata motsa ba, Nurain ya ƙarasa shigowa ɗakin yana kallon position dinta, a yacca take kwance gefen gadon yasan cewa ta farka ne, yana isa kusa da ita ya tabbatar sbd hawayen da ya gani kwance cheeks dinta, ya duƙa ya kalli lumsassun idanunta da tinda taji shigowarsa ta rufe yace "Hajar", haɗe fuska tayi gami da turo baki sai kuma ta kawar da kanta, murmushi yayi cause yasan fushi take kuma baiga laifinta ba don tayi fishi dashi, ya rage murya yace "let me take care of you baby girl" da haka ya fara tattare hannun button down shirt da ya saka da zai fita mosque sai kuma ya nufi bathroom, ruwan zafi ya tara a tub ya sirkasa kamar na daren jiya. This time around Hajar ji tayi kamar a ruwan jajjagaggen tattasai ya sakata, though ba taji azaba kamar na daren jiya ba amma dai ta ɗanɗana shima, saida ya tabbatar ta gasu snn ya fito ya barta a bathroom din don tayi alwala, walking slowly Hajar ta fito daga bathroom da rigarsa dake jikinta wcca ta tsaya mata a rabin cinya, yana zaune tsakiyar gado yana operating laptop, suna haɗa ido tayi saurin janye nata zuciyarta ta buga da ƙarfi, ji take kamar ta nutse a wajen, bai ɗauke idonsa daga kallonta ba yana lura da yanayin tafiyarta har ta ƙaraso cikin ɗakin, hijab dinta ta ɗauka ta saka without looking at him for the second time ta kalli qiblah, yana ganin ta kabbara sallah ya tashi ya nufi door, after 15mins ya dawo ya tarar har ta idar da sallar tana zaune kan darduma, inda take ya nufa ya duƙa ya ajiye mug din hot chocolate da ya shigo dashi, da sauri ta haɗe kanta da guiwa don bazata iya haɗa ido dashi ba ga kuma azabar tsoronsa da ya cikata, ya kamo hannunta da taushin murya yace "yau ma ba gaisuwa...?", sai kace an ƙunduma mata zagi haka ta fashe masa da kuka bil haqqi, ya waro ido yace "Laa me aka miki..?", ita dai taƙi mgana kawai kuka take kamar an aikota, ganin har ta fara jan shessheƙa yace "stop crying and tell me what happened... ko masquerade din ya sake zuwa ne..?", mganar ma bata fita sosai sbd muryarta ta dashe tace "Ni gidanmu zan tafi... i don't like it here, i want to go home please", yayi blushing don shi da tayi mgana ma daɗi yaji yace "where are you going from your husband's house Silly girl..?", a hankali tace "i don't have one..", ƙoƙarin ɗago fuskarta yayi ya kalli cikin idonta amma taƙi ɗagowa, ya jingina kansa a nata gami da mgana in a whisper yace "you don't have one After last night", turo baki tayi ba tace komai ba, yace "yesterday's night was so amazing, super sweet, i really enjoyed it.. i hope today's night will be more sweeter", yana gama fadin haka ya janye kansa a nata sai kuma ya fara ƙoƙarin ɗago kanta, firr taƙi yarda don har wani shivering take, da kyar yayi nasarar riƙe haɓarta tana jin haka ta faɗa ƙirjinsa snn ta rufe fuskar a nan, tini ya sauke ajiyar zuciyar da bai shirya mata ba, gaba ɗaya sensory nerves dinsa saida suka kai electric shock brain dinsa, mug din hot chocolate din dake gefensu ya matsar sai kuma ya dafe bayanta yana daɗa shigar da ita jikinsa sosai, tayi lamo a jikinsa ita dai she don't care indai za tayi avoiding eye contact dinsa, patting bayanta yke with one hand yace "Thank you for yesterday's night... Sorry for the pain..", ita dai ta lafe a jikinsa sai kace anan aka halicceta perceiving his pure scent, after 5mins yace "baby wife here is your free breakfast" da haka ya zameta a jikinsa, sam bata bari sun haɗa ido ba, mug din chocolate din ya dauka ya kamo hannunta ya damƙa mata, ya ajiye numfashi ya tashi ya nufi door ya buɗe ya fita palour, kan sofa ya zauna yayi resting yana sauke ajiyar zuciya, so yake ya bata hutu don ƙarama ce baya so ya sake taɓata sai tayi healing, iya hugging dinta da yayi ynxu har lissafinsa ya fara kwancewa shiyasa ya bata space snn shima yayi calming kansa down, sai after 1hour ya koma ɗakin, ya tarar ta sha rabin chocolate din ga ragowar nan ta ajiye, ta koma baccinta nan kan carpet, kan gado ya mayar da ita ya rufa mata duvet sai kuma taɓa goshinta to feel her body temp, yeah temp dinta ya ɗanyi high amma ba sosai ba dman dole sai hakan ta faru. ★Maama ta saki baki har miyau na shirin zuba tana kallon Maimuna da ta shigo ɗaki tana yamutsa fuska tace "wai Aman kika sake yi..?", Maimuna da tayi wani lakwam ta faɗa kan gado tayi rub da ciki tace "Eh", Maama tace "gsky ba lfy.. ko dai wnn cutar da ake ta amai da gudawa ce ta kamaki", Maimuna ta girgiza kai tace "Amai kawai nke fa..", Maama tace "na kawo miki kunun tsamiyar za ki sha..?", Maimuna ta girgiza kai tace "A'a na ƙoshi...", Maama tace "wane irin kin ƙoshi iyeeh, yau tinda garin Allah ya waye ubanki kika sakawa cikinki salon dai cutar ta miki muguwar illa", Maimuna da take mgana tana yamutsa fuska tace "zan sha anjima..", Maama tace "Allah ya kaimu anjiman" ta tashi tana baza zani ta fita, wajen ƙarfe sha biyu Maimuna na farkawa daga bacci Maama ta ciko kofi da kunu ta kawo mata, ai Maimuna na yiwa kunu kurɓa ɗaya ta toshe baki sai kuma ta zura da gudu ta fita waje, nan bakin rariya ta durƙushe ta ringa kakarin amai, Umma tayi sauri ta janye robar gwangwanayenta da take wankewa, Nabilah tayi kasaƙe da tsintsiya a hannu tana kallon Maimuna da har lokacin take kakarin amai, Nabilah ta ajiye tsintsiyar ta zuba ruwa a buta ta ajiye gefen Maimuna sai kuma ta koma ta cigaba da tattare tsakar gida, Maimuna ta kuskure bakinta ta tashi sai kace wcca ta shekara tana jinya ta shiga ɗaki, Maama ta tarar ta sauya kayan jikinta tana shirin saka hijab, Maama tace "kar ma ki kwanta saka mayafinta na kaiki Chemist", Maimuna ba tayi musu ba don itama lfyr take nema ta canza kaya, Maama tace "Akwai kuɗi a hannunki..?", Maimuna ta girgiza kai, Maama tace "Au tsimilmilar ma har kanki za ki yiwa, toh ki fito da kuɗin da za'a siya miki mgana dan nidae ɗari biyar ce kawai a wajena", Maimuna tace "wllh Allah ba nida ko kwandala", Maama tace "ina kuɗin da Alhaj din naki yake baki..?", Maimuna tace "Ni yau sati biyar knn rabona dashi wllh, ko na kira wayarsa ma bata shiga", Maama ta ringa kallonta don ta lura gsky take gya mata ba tada kuɗi, Maama tace "dena ɗaukar wayarki yayi...?", Maimuna tace "Eh dman yace min aiki ya masa yawa bxn ringa samunsa ba", Maama ta gyaɗa kai tace "Au toh", tsakar gida suka fita Maama na kallon Nabilah tace "zan kai Maimuna chemist tana fama da masassara", Nabilah tace "toh sai kun dawo", Maama tace "yawwa" da haka ta nufi soro tana riƙe da Maimuna wcca take tafiya a hankali, suna isa chemist Maimuna ta zauna kan benjin dake cikin Chemist din, mai Chemist na gamawa da mutumin da suka tarar ya waiwaye su, ƴan tambayoyi ya yiwa Maimuna ta ringa basa amsa, ya kalli Maama yace "A kaita asibiti su mata gwaje gwaje kawai", Maama tace "kai bazaka iya mata gwaje gwajen ba anan, masassara ce fa take damunta", yace "A'a aje dai asibiti, ni Strip kawai zan iya baku", Maama tace "meye kuma sitirif..?", Strip din ya ɗakko yace "gashi", Maama ta amshi ledar Strip din tace "kai da zaka bani magani sai kuma ka miƙomin robar banza", mai Chemist ya amshi Strip dinsa yace kawai suje asibiti, Maama na sababi suka bar Chemist din tace su tafi wani, Chemist biyu suka je bayan wnn shima dai abinda ake ce musu knn, Maimuna kam har ta jigata ta dawo jan ƙafa, jingina tayi da bango tace "Maama dan Allah mu tsaya gidan Balaraba na huta", Maama ta haɗe fuska sai kuma ta saki fuskar bayan ta tuna har gida Balaraba tazo ta bata haƙuri, gidan Balaraba suka wuce wcca ta saukesu a tsakar gida, Maimuna ta sheme kan tabarma zuciyarta na wani irin hautsinawa, bayan Balaraba sun gaisa da Maama tace "lfy dai na ganku da ranar Allah..?", Maama tace "uhmm tinda kika ga haka ai ba lfy", nan ta gaya mata ai Maimuna ce ba ta jin daɗi shine suka fito Chemist, Balaraba tace "Ayyah Allah ya bata lfy", a kasale Maimuna ta yunƙura tana toshe baki ta nufi gaban rariya, ba tayi aman ba ta dawo ta kwanta, Balaraba ta ringa kallonta kafin ta jinjina kai ta kalli Maama tace "Rabi kawai kuje asibitin", Maama tace "toh idan munje asibitin shekaruna zan lalo na basu, kuma da rana tsage tsage zamu tafi asibitin ma'aikatan lfy da basu da kirki ai sai su kaɗomu..", Balaraba tace "inada kuɗin da aka kawomin ajiya sai na ranta miki ai, ita lfy ai yar sarki ce gwara a nemeta", dubu biyar Balaraba ta rantawa Maama da wajewar nan da sati ɗaya zata biyata kuɗinta, Maama tace "ba zai ma kai sati ba ko gobe sai na kawo miki kuɗinki don ubanta na dawowa zan amso kuɗin a wajensa, amma dai ynxu wani asibitin za mu nufa..?", Balaraba tace "nan nan ma asibitin gangare zasu dubata.. bari na raka ku", haka nan Balaraba ta raka su Maama can wani karamin asibitin gwamnati, kuma suna zuwa aka ɗebi jinin Maimuna za'a mata test din abinda ake zargi, Balaraba na zaune kan benci tare da Maimuna a inda suke jiran result, Maama ta tafi siyowa Maimuna ruwa don tace ƙishi ruwa take ji, wata Nurse ce ta fito da takardar result din test din ta kira sunan Maimuna, Balaraba tace "gata nan", Nurse din ta isa inda suke ta bawa Balaraba takardar tace "nasan dai ku manya ai kun san me yake damunta kawai dai kunxo nan ne dan ku tabbatar", Balaraba tace "me yake damunta..?", ba yabo ba fallasa Nurse din tace "Ciki ne da ita na tsahon sati uku... Allah ya raba lfy", Balaraba da ta gasgata zarginta ta saki fuska kamar ba komai tace "toh Alhmdllh mun gode likita", Nurse din bata daɗe da tafiya ba sai ga Maama nan da ledar pure water biyu, Balaraba ta ringa kallonta har ta iso, Maama ta tashi Maimuna da bacci ya kwasheta don ko zuwan Nurse din bata sani ba ta bata ruwan tasha, duk Balaraba na kallonsu saida ta gama shan ruwan snn tace "mu tafi gida kawai", Maama tace "ai bamu gama ba", Balaraba ta nunawa Maama takardar tace "gashi nan sun rubuta mta magunguna muje gida kawai na miki bayani", haka dai suka sake runtuma suka wuce gidan Balaraba, Maama ta fixge hijab dinta snn ta tuge ɗan kwalinta tana kallon Balaraba da idonta kamar zasu faɗo, ƙiris ya rage ta kurma ihu ta ƙundumawa Balaraba wata mummunar ashariya tace "Ƙarya kike billahillazi la'ilaha illa huwa", Balaraba ta wurga mata takarda tace "toh duba ki gani da idonki idan karya nake ƴarki bata kwaye zani an ɗirka mata ciki ba, dman shiyasa nace mu taho gida don nsan tsaf zaki tonawa kanki asiri a cikin jama'a", kafin kace me gumi ya jiƙa Maama har yana ɗiga, habawa ai da Maama ta wani zabura sai kace wcca aka kaɗo daga dawanau tayi kan Maimuna ta ringa loda mata hannu tana fatali da ita, Balaraba ta ringa ƙoƙarin kwace Maimuna tana cewa "ki rufamin asiri kar kiyi kisan kai a gidana na shiga uku", ina saida Maama ta yiwa Maimuna lilis har ita kanta ta gaji da duka snn Balaraba tayi nasarar amsheta ta wurgata banɗaki, mala mala Maimuna tayi a ƙasan dauɗaɗɗen banɗakin don ba tada maraba da sumammiya, Maama ta ɗora hannu bibbiyu a ka ta kurma wani uban ihu sai kuma tayi rimi tayi zaman ƴan bori a ƙasa ta fara tumami, wiwi ta ringa kuka irin na takaicin nan don ko hawaye bbu sai wata azaba da maƙogoronta ke mata, Balaraba ta juyar da kai tana dariya ƙasa ƙasa don yacca Maama ta zaro harshe tana kuka sai kace Akuya mai naƙuda ba ƙaramin dariya ta bata ba, saida Balaraba ta gama dariyarta wcca Maama bata lura ba snn ta matsa kusa da ita tace "ƙawata ki bani hankalinki nan, mu tone ƙasa mu rufe sirrin nan bbu wnda yaji bbu wnda ya gani kamar yacca muka saba". ★Hajar bata farka daga baccin da ta koma ba sai sha ɗaya da minti goma, a hankali ta miƙe zaune tana mamaki da ta ganta a gado, da kyar tayi shahada ta zuro ƙafafuwanta ƙasa amma kuma sai taƙi taka ƙasa don tsoro take ji kar taji zafi, ta lallaɓa ta miƙe tsaye sai kuma taga ba taji zafin ba, walking slowly ta nufi door ta murɗa handle, wata ajiyar zuciya ta sauke jin ƙofar ta buɗe, ai kam tini ta nufi ƙofar fita daga ɓangaren tayi sliding ta fita, sai kace mai tafiya akan ƙaya har ta isa room dinta, wani sanyi ne ya ratsa mata zuciya sai kace wcca ta shigo inuwa daga rana, ta mayar da ƙofar ta kulle ta jingina da ita, turo baki tayi don ƙamshinsa kawai take ji duk da cewa ta baro room dinsa, lokaci guda ta kalli kanta taga shirt dinsa ce fa a jikinta, bathroom ta shiga ta cire rigar ta daura pink towel, wanka tayi da warm water ta fito, bata iya zama kan stool ba ta zauna gefen gado tayi rubbing lotion, ta ringa kallon inda box din kayanta suke taga basa nan, kamar da wasa ta bude wardrobe ai kam sai ga kayan a jere intact, she was very shocked haka dai ta fitar da wata gown mara nauyi da hula ta saka, lipbalm ta goga a pink lips dinta da sukay pink sosai, sama sama ta fesa perfumes masu sanyin ƙamshi, gyara arrangement din kayan kan mirror din ta fara duk da cewa basu wani hargitse ba, door aka buɗe ya shigo tare da yin sallama, ai ko da wasa bata kalli ƙofar ba, lips dinta suka motsa lokacin da ta amsa ciki ciki sai kuma ta haɗe fuska, ya ƙarasa shigowa ciki ya ajiye ledar hannunsa kan chest of drawers, tini ƙamshinsa ya baza room din, kallonta yake bbu ko ƙiftawa and he was so happy da ya ganta a hka, tinda ya shigo ta kasa cigaba da jera cosmetics din cause hannun nata ma rawa yake, gaban mirrorn ya ƙarasa ya tsaya daff da bayanta har jikinsu na gogar na juna, a bazata ta ɗago kanta sukay ido huɗu ta cikin mirrorn, da sauri ta saukar da kanta tana jin kamar ta nutsu a wajen, zagaye flat tummy dinta yayi yana kallonta ta cikin mirror yace "how are you feeling now..?", ba tace uffan ba ta ringa kallon hannunsa daya ritsa cikinta, ɗan girgizata yayi yace "uhmm ynxu kin dena jin pain din...?", a hankali ta gyaɗa kai tana turo baki, yace "Good, i bought your breakfast.. eat alot kinji baby girl", nan ma kai ta gyaɗa masa, lips dinsa ya kawo saitin kunnenta har tana jin breathing dinsa, ba shiri ta lumshe idonta tana jin kamar an kwara mata ruwan ƙanƙara, yayi pecking cheek dinta lokaci guda ya saketa yace "Sai na dawo" da haka ya fita daga ɗakin, after few seconds da fitarsa Hajar ta sulale ƙasa ta ajiye numfashi. Shi kam direct downstairs ya sauka ya shiga motarsa ya bar gidan zuwa gidansu zaije wajen Abba da yake kiransa, with minimum speed yake jan motar time to time sai yayi blushing a haka har ya isa gida, yana shiga gida dman direct ɓangaren Abbansa ya shiga, suna gama mgana da Abba ya fito da envelope a hannunsa ya wuce wajen Mami, a bedroom dinta ya sameta ya zauna kan carpet ya gaisheta, with care ta amsa masa kmar ba ita bace ya sha faɗa a wajenta jiya ba, ita da Abba hka suke daga sunyi faɗa toh a wajen suke barinsa basa sake tayar da zancen ko kuma su ringa canzawa mutum fuska, No idan abu ya wuce toh ya tafi knn a wajensu, tace "how is my daughter...?", Nurain ya shafa kansa yace "She is great", Mami tace "Masha Allah", sai kuma ta kalli envelope din hannunsa tace "where are you taking that..?", yace "house of assembly", ta gyaɗa kai tace "Ohk baka je work ba..?", yace "yeah", Nurain beyi tunanin zai daɗe a wajen da Abbansa ya aikesa ba, sai yamma liƙis ya dawo gidansu in a hurry kawai zai bawa Abba abinda ya amso ya wuce gida, gaba ɗaya hnkalinsa yayi kan Hajar da ya bari a gida, sharp sharp ya fito daga ɓangaren Abba har zai fita sai kuma ya juya ya shiga wajen Mami don mata sallama kafin ya tafi, ko zama ma beyi ba ya tsaya ta bayan kujerar da take zaune yace "Our Mami saida safe..", Mami ta juya ta kallesa tace "Ohh you are leaving already..?", da sauri yace "yeah", Mami ta ɗage gira tana kallonsa, tace "Ohk.. go in za kaga blue leather bag kan bedside ka kaiwa Hajar... tin jiya Sakeena da zata tafi tace na baka idan kazo", yace "tom" da haka ya shiga bedroom din, after few seconds ya fito hannunsa wayam ba ledar yace "Mami ban gani ba..", Mami tace "A kan bedside din..?", yace "Eh", Mami tace "A kan right bedside fa", bai ce komai ba ya sake komawa ɗakin nan ma ya fito bbu ledar, Mami ta haɗe gira ta tashi ta shiga room din da kanta, bbu jimawa sai gata nan ta fito da ledar a hannunta, ta ringa kallon Nurain da yake ta murza palms sai kace mai jin sanyi tace "where is your sense Nurain..?", ya sauke ajiyar zuciya gami ta shafa kansa yace "ban gani bane Mami", Mami ta girgiza kai ta miƙa masa ledar tace "Goodluck", da kallo ta bisa har ya fita daga palourn nata, ko saurin me yake oho. Daf da sallahr magrib Nurain ya isa gida, da bibbiyu ya ringa tsallake stairs har ya haura sama, kai tsaye room dinta ya buɗe, ya ringa ƙarewa room din kallo don bai ganta ba, saida ya shiga ciki snn yaji ƙarar ruwa a bathroom, juyawa yayi ya fita ya shiga ɓangarensa, kafin yayi wanka ya shirya har an kira sallah don haka sharp sharp ya gama shiryawa ya fito, ya sauka downstairs zai wuce mosque kar sallah ya wucesa, yana dawowa mosque ya shiga room dinta ya tarar ta idar da sallah knn, ya ƙarasa shiga ciki ya duƙa gabanta, tayi saurin kawar da kanta gefe, yace "have you eaten..?", slowly ta gyaɗa kai, yace "me kika ci..?", Calmly tace "Noodles", yace "you cook it..?", ta gyaɗa kai, ajiyar zuciya yayi wato har ma ta iya sauka kitchen tayi girki. Washe gari da Asuba Hajar ta buɗe idonta, a zabure ta miƙe zaune tana tattaɓa gadon da take kai, sai kuma ta fara ƙarewa ɗakin kallo, ita dai tasan jiya da daddare da tayi wanka ba'a nan ta kwanta ba, ita da ta kwanta a ɗakinta toh me ya kawota nan, can ta hangosa kan couch yana karanta Holy Qur'an, tini ta diro daga gadon tana gyara silk sleeping gown din jikinta, sum sum ta nufi door yace "where are you going..?", tini zuciyarta ta hau lugude don wani azabar tsoronsa take ji, muryarta na scratching tace "ɗakina zan tafi nayi sallah", yace "shi nan din ba'a Sallah..?", ta girgiza kai tana jan slim fingers dinta tace "bbu hijab a nan", yace "says who..? wancan ba hijab bane", saukar da kanta tayi ba tace komai ba, after a while ta shiga bathroom tayo alwala ta fito, hijab dinta wnda tinda tin daren shekaran jiya yake room din ta zumbula tayi sallah, Nurain ya cigaba karatunsa, tana gama azkar dinta kanta a ƙasa tace "ina kwana", ƙasa ƙasa ya tsinkayo muryarta, saida ya kai Aya snn yace "morning how was your night..?", a hankali ta amsa don ma bai ji me tace ba, after 5mins ta tashi ta nufi door zata fita don ɗakin da mai shi tsoro suke bata, a hankali ya rufe Al'qur'anin yace "shi hijab din da shi kika zo da zaki fita dashi..?", turo baki tayi ta dawo ta cire ta ajiye inda ta ɗauka, ga hijab nan ita dai bazata zauna ba, sai dai me tana murɗa handle taji ƙofar a rufe, a bazata taji zuciyarta ta buga ta juya ta kallesa, wani murmushi ta tsinta a fuskarsa kamar wnda zaiyi dariya, habawa tini ta fara bubbuga legs dinta a ƙasa kafin kace me hawaye suka hau zarya bisa kuncinta tace "Ni wllh bxn zauna a nan ba room dina zan tafi", saida Nurain ya kusa melting a inda yake tsabar yacca shagwaɓar da take masa ta shigesa, yayi resting kansa gami ta taɓe baki yace "ohh really, toh an riƙe maki ƙafa ne", bata fasa abinda take ba tace "Ni dae ka buɗe min", ya lura ma ko kallonsa ba tayi duk wnn abun amma take cewa ya buɗe mata ƙofa, yace "Na ƙi din", sulalewa tayi ƙasa sai kuma ta fashe da kuka, ya waro ido yayi slight smirk ya tashi ya durƙusa gabanta, idonsa ya sauka akan ƙirjinta da yake sama yana ƙasa, kasa ɗauke idonsa yayi daga wajen, within few seconds har idonsa ya canza, ya ja doguwar ajiyar zuciya ya kai hannu ya riƙe haɓarta ya ɗago fuskarta, tini ta haɗiye kukan ta runtse idonta eye lashes dinta sai rawa suke, ja da baya za tayi ta zille amma ina kawai ya haɗe bakinsu waje ɗaya, igiyar rigar baccin nata ya kunce ai kam rigar ta zame daga jikinta don dman silk ce, sai kuma ya zuge ribbon din da ta ɗaure lallausan gashinta, sosai jikinta ya fara ɓari tasa hannu bibbiyu ta ringa turesa tana so ta kwace lips dinta, wata razananniyar ƙara ta fasa bayan ta samu chance tace "wayyoh Ummana na shiga uku na lalace, dan Allah kayi haƙuri..", ya kalli bare chest dinta don bbu wani abu da yayi masa shamaki duk ya ciresu, tana shirin miƙewa ya janyota ya manna mata wani lafiyayyen kiss a neck wnda ya sake turning dinsa on, daga nan kuma zancen ya sauya bayan yayi jarumtar kaisu gado, this time around gentle yabi da ita ba extra gentle ba, ba kamar encounter dinsu na farko ba wnn karon bai sarara mata ba, yau dai ya ɗanɗana abinda yafi Coffee din safe daɗi, toh wa ma zai haɗa, bayan ƙura ya lafa ya ɗora forehead dinsa saman nata yana jera ajiyar zuciya pleasantly, da wata iriyar murya yace "Hajar" to know if she is conscious, da ragowar strength din da ya rage mata ta fashe da matsanancin kuka......✍️ 💛 HAJAR 💛 {78..} Babu wani pleading word da Nurain bai yi amfani dashi ba wajen consoling Hajar amma taƙi shiru, daga ƙarshe ma juya masa baya tayi ta duƙunƙune da duvet ta cigaba da rusa kukanta, bayan jikinta da yake mata ciwo har zuciyarta ma zafi take, Nurain ya tashi ya shiga bathroom, har ya fito bata dena kukan ba, singlet da short nicker kawai ya saka, wurga towel din da yake tsane sumarsa yayi kan couch snn ya nufi gadon, gefenta ya zauna ya bude fuskarta da ta rufe da duvet, ta muskuta da shirin juya masa baya yayi saurin riƙeta, idonta a runtse yake gamm sai jan zuciya take tamkar zata shiɗe, ya kamo hannunta yace "Baby girl..", ta fincike hannunta sai kuma ta mirgina ta koma can ƙarshen gadon, lokaci guda ta sake rushewa da sabon kuka sbd azabar da taji da ta mirgina din, Nurain ya sauke ajiyar zuciya don yasan ba sauraronsa za tayi ba, amma still ya zagaya ta side din da ta koma ya durƙusa yana kallon fuskarta, ya kai hannu ya shafa lallausan gashinta da ya hargitse yace "Baby wife listen to me..", da sauri ta tankwaɓar da hannunsa daga kanta ta wani turo baki, har lokacin idonta a rufe yake, ya cije lower lip dinsa painlessly gami da sauke wani ƙayataccen murmushi mai sauti, lokaci guda ya kware duvet din daga jikinta, ta tsala wani uban ihu ta cure kanta waje guda, tini ya wuce bathroom da ita don ya tara warm water a tub kafin ya fito, yasan she need warm water don she is still tight, yana ganin ko nan da encounter dinsu na biyar ma saida sitz bath, Hajar ta sha azaba don ruwan na yau sai taji kamar na barkono ne, yana ajiyeta kan gado bayan sun fito daga bathroom ta bige hannunsa daga jikinta, haushinsa take ji na gasken gaske shiyasa ma bata so ya taɓata, murmushi yayi ya kalli hannun nasa da ta bige yace "Eh naji... thank you... you make my morning today Baby wife", ya rage murya yace "it is sweeter than day before yesterday's night..", pecking cheek dinta yyi ya tashi ya fita, sai a lokacin Hajar ta buɗe idonta, ta miƙe a hankali ta zauna a ɗofane don bazata iya zama da kyau ba, room dinta take son komawa, ta miƙe tsaye da kyar tana cije lips, walking slowly sai kace mai taka ƙaya ta nufi door ta fita, tana tafiyar tana hutawa a haka har ta kai kanta ɗakinta, ta zube kan gado hawaye masu zafi na sauko mata, Anya kwa zata iya barin lokacin da ta ƙidaye yaxo kafin ta wanzar da ƙudirinta, Eh sbd favor yake mata shiyasa ya rufe ido ya ɗanɗana mata wnn azabar, sbd favor yake mata shiyasa bai saurari magiya da raƙon da ta ringa masa ba, wato ya gama da salon ɗalle mata baki da gaya mata maganganu ynxu ya dawo azabtar da gangar jikinta kuma, wnn tunanin yasa hawaye suka kasa tsaya mata, idanunta har zugi suke gashi kuma sun ƙanƙance, tana ji aka buɗe ƙofa amma taƙi motsawa zafin da zuciyarta take ya ƙaru, walking majestically ya zauna gefenta yace "Baby girl here is your Coffee", banza ta masa ta wani haɗe gira, yace "the Coffee you like wnda kike shanye min fa.." da haka ya ɗagota, afujajan ta fixge jikinta tana jan shessheƙa tace "please leave me alone", ta koma ta kwanta, yayi slight smirk yace "Ohk then get some rest..", da haka ya miƙe ya fita da mug din coffeen, ɓangarensa ya wuce ya zauna palour yana shan Coffeen, time to time sai yayi blushing sai kace zautacce, ji yake kamar an cire masa wani burden da yake damunsa yana jin kansa sakayau ynxu, yana gama sha ya ajiye cup din ya shiga bedroom, wayarsa dake kan bedside ya ɗauka, missed calls ya gani from 2 people, na Ruqayyah wnda daman ya saba ganinsa don kullum saita kirasa sau goma ko sama da haka, sai kuma missed call din Dr Marwan, na Dr Marwan din yabi, wayar almost 5mins sukay da Dr Marwan kafin Nurain ya katse kiran yana sauke ajiyar zuciya, knn yau sai ya shiga hospital, ya dubi makeken wall clock dake tickling yaga ƙarfe takwas da rabi, ƙarfe tara ya fito cikin shirinsa tsaf da car key a hannunsa ya sauka downstairs, Nearby Eatery yaje ya siyo mata breakfast snn ya dawo, da ledar abincin da kuma wcca Mami ta basa jiya tace ya kawo mata ya shiga palour, direct room dinta ya buɗe ya shiga bayan ya haura sama, ido biyu ya tarar da ita saidai a kwance take, suna haɗa ido tayi saurin janye nata, ya ƙarasa kusa da gadon yana kallonta without blinking yace "how are you feeling now...?", ba tayi niyyar amsa masa ba amma tsoronsa da ya shigeta yasa tace "much better", da kyar ma tayi mgnar ta wani sha kunu, duk yana ankare da yanayinta yaga dai har ynxu fushi take dashi bata sauko ba, don dai sauri yake da sai ya sauko da ita snn zai fita, amma dai bari ya dawo tinda ba wani daɗewa zaiyi ba, yace "Good... gashi Mami tace a baki wnn", ta gyaɗa kai a hankali, yace "i bought your breakfast", nan ma ta gyaɗa kai, after a while ya sunkuyo yayi pecking forehead dinta ya juya ya fita, saida taji ƙarar rufe ƙofa snn ta buɗe idonta, ta kai hannu ta goge forehead dinta inda yayi pecking tana turo baki. Nurain na isa hospital ko office dinsa bai shiga ba ya wuce surgery room, bayan ya gama shirin surgery ya saka surgeon gown ya shiga surgery room din, patient din da zai yiwa aiki har ya zama ready, tinda ya shigo surgery room din Ruqayyah ke kallonsa ta wani haɗe gira, position dinta ta tsaya don yau Vital signs zata ringa dubawa, Nurse Amina kuma ta ringa miƙa instruments, Good 3hours surgeryn ya ɗauka kafin aka gama, tini Nurain yayi disposing hand gloves da nose mask ya fita, throughout the surgery tunanin Hajar da ya bari a gida kawai yake, Allah yaso ma surgeryn ba wanda ake buɗa ciki bane da zai iya barin wani small instrument din a cikin patient, Ruqayyah ta bisa da kallo ta gyaɗa kai, ita da Nurse Amina ne suka mayar da patient din ward, da sauri Ruqayyah ta fita daga ward din bayan ta gama checking Vitals din patient din after surgery, direct hanyar office dinsa ta ɗiba, tana isa bakin office din ta tarar da patients wajen su goma, ta zauna kan silver chair tana jiran ya gama attending patients din kafin ta shiga, wayarta ta ciro daga pocket din Scrub dinta ta shiga messages. Nurain dake zaune office dinsa yana duba patient ya kalli wayarsa da tayi haske, ignoring message din da ya shigo yyi ya cigaba da aikinsa, 1hour ya ɗauka kafin ya gama attending ma patients din, har lokacin kuma Ruqayyah na zaune tana jira, last patient na fitowa ta zura wayarta cikin pocket din Scrub ta shiga office din, ko kallon Haleema ba tayi ba ta wuce ciki, ta mayar da ƙofar ta rufe ta jingina da ita, kallonsa ta ringa yi bbu ko ƙiftawa kafin tace "Assalamu alaikum", bai ɗago kansa daga kallon monitor din laptop da yake ba yana imputing data ya amsa sallamar ƙasa ƙasa, after few seconds din da suka kusa jingine 1mins ta ƙarasa shigowa, kan chair dake gaban huge table din ta zauna, a lokacin ya gama shutting down laptop din don ya gama abinda zaiyi, ya miƙe tsaye yana jan rigarsa, Ruqayyah ta ɗaga kai ta kallesa da mamaki ba dai tace komai ba, taga ya ɗauki car key alamar dai tafiya zaiyi, tace "Dr..", ya ɗan kalleta yace "what's up..?", tace "baka ga message dina ba nace zanyi mgana da kai Please", ya girgiza kai yace "ban gani ba... mene ne akan patient ne or something else...?", tace "please we need to talk", yace "Ohk not now, i will give you time next week Monday.." da haka ya zagayo ya nufi door, tini Ruqayyah ta miƙe tabi bayansa tace "why..?, me yasa ba ynxu ba..?", Calmly ya juyo yace "because my wife is waiting for me.. i can't give you even 1sec from her time" da haka ya buɗe ƙofa ya fita ya barta tsaye nan a daskare, shin da gaske ne wai Dearest dinta yayi aure, na farko da ta bisa Eatery yace mata yayi aure wnda sam sam bata yarda ba, ynxu kuma gashi yace mata ai matarsa na jiransa kuma ba taga wasa a yanayinsa ba. Wajen ƙarfe ɗaya da rabi Nurain ya fito daga wani haɗaɗɗen wajen siyar da wayoyi da wata yellow transparent leather a hannunsa, motarsa ya shiga ya bar harabar wajen, after a ride of 15mins ya isa gida, parking motar yayi snn ya buɗe ya fito, ya amsa sannu da zuwan da mai gadi ya masa kafin ya wuce cikin gida, ya buɗe ƙofar palour ya shiga, Hajar da take ƙoƙarin saukowa daga stairs a hankali tayi saurin kallon ƙofar, ai kam sukay ido huɗu zuciyarta ta buga da wni irin speed, ba shiri ta juya ta koma room dinta ta shiga toilet ta saka lock, wani mugun tsoronsa take ji, bayanta yabi ya haura upstairs din shima, a buɗe yaga ƙofar ɗakinta ya shiga bai ganta ba, ya kalli door din bathroom yyi slight smirk don yasan nan ta shige ya juya ya fita, ɓangarensa ya wuce yayi refreshing kansa ya saka ƙananun kaya riga polo da sweat pant. haka nan Hajar ta ringa gudun Nurain sai kace mage da ɓera har dare yayi, ynxu kam ta dena guduwa bathroom room din nata take rufewa da key snn ta bar muƙullin a jiki, wajen ƙarfe takwas Nurain ya dawo daga mosque sallar isha'i, ya kalli ƙofar ɗakinta yayi slight smirk, kafin ya fita saida ya murɗa handle yaji a rufe, tinda yake da ita a gidan wnn shine first time da ta sakawa ɗakinta key, girgiza kai yayi ya zura both hands dinsa a pocket ya wuce part dinsa, inda ya ajiye spare keys din gidan ya nufa, da kyar ya lalubo na room dinta, da key din a hannunsa ya fito corridor, sau uku yayi attempting saka key din a ƙofar amma yaƙi shiga, sosai yayi realizing ai akwai wani key din a jiki shiyasa yaƙi shiga, ajiyar zuciya ya sauke ya fara knocking door din, tini Hajar dake zaune gefen gado ta miƙe zumbur ta ringa kallon ƙofar, ta haɗiyi wani yawu jikinta ya fara rawa don gani take kamar zai shigo ne, Nurain yayi knocking door din da ɗan ƙarfi yace "Hajar..", idonta kamar zai faɗo ta ringa murza fingers dinta, lokaci guda ta afka toilet ta rufe da keys tana turo baki, after 5mins Nurain ya bar wajen ya sauka downstairs, kitchen ya shiga yayi making coffee ya fito ya haura sama. washe gari da sassafe Hajar ta ringa jin yunwa, jiya ba wani abincin arxiƙi taci ba tin breakfast da ya kawo mata ne acikinta sai kuma plain Noodles da ta dafa, A ɗarare tayi unlocking ƙofa ta buɗe ta fita cikin sanɗa ta sauka downstairs, ynxu kam tana iya tafiya ba taji zafi ba cause sau biyu tana yin sitz bath yau da safe da kuma jiya da daddare, kitchen ta shiga zuciyarta na bugawa don a tsorace take gani take kamar zata gansa a nan, sharp sharp ta tafasa ruwan tea ta haɗa shayi mai kauri ta shanye abinta a kitchen din, bata so ta wuce da cup din room dinta don tasan idan ta koma ta rufe ƙofar kuma sai 12 Noon, tana gama sha ta fito zuciyarta wasai ta haura sama ta shiga ɗakinta, still tayi ta ringa kallon jikin ƙofar ganin bbu keys, sosai zuciyarta ta buga don taji scent dinsa a ɗakin, bata gama lissafin da take ba kawai aka turo ƙofar ta waje, saida zuciyarta ta koma stomach after their eye contact, da baya ta koma sai kuma ta juya a miliyan zata shiga toilet, tini ya fixgota tayi landing a ƙirjinsa yace "Ke... ni Masquerade ne da zaki ringa guduna..?", ta yarfe hannu sai kuma ta fashe masa da kuka tace "wayyo Allahna na shiga uku..", jikinta har ya fara karkarwa don da gaske ta tsorata dashi, ya zaunar da ita gefen gado to calm her down ya duƙa gabanta, ya kamo shaking hand dinta ya riƙe a tafukan nasa yace "look at me Baby wife", kaudar da kanta tayi taƙi ta kallesa duk da yacca ya ringa leƙa fuskarta yana so suyi ido huɗu, yace "Hajar..", ta ɗaure fuska samm taƙi ta kallesa, murmushin kan lips yayi yace "wai har ynxu fushi kike Baby wife, After tough punishment din da kike min, you left me yesterday all alone, i couldn't even sleep comfortably..", ita dai ba tace komai ba, yace "sorry bazan sake ba sai kin gama healing Baby girl, i promise...", fashewa tayi da kuka sosai, wani irin sai tayi healing kuma, shi da zaice ya dena gaba ɗaya sai yace sai tayi wani healing, ta fara ƙoƙarin fincike hannunta amma yaƙi sakinta, murmushi mai sauti yayi don ya gane kukan na mene, yasa palm dinsa ya share mata hawayen yace "i promise you this Baby wife", ledar da ya shigo da ita ya dauka ya dora mata kan laps, ta ringa kallon ledar bbu ko ƙiftawa, yace "Open it", a hankali ta ciro kwalin tsaleliyar wayar daga cikin leda, tin daga kwalin ma kasan wayar me tsada ce, yace "you like it...?", ta gyaɗa kai a hankali sai kuma ta ɗago ta ɗan kallesa, saukar da kanta tayi tace "Thank you.." ta ɗanyi jimm kafin tace "Allah ya saka da Alkhairy", ya ringa kallonta yana jin wani abu mara misaltuwa na figarsa, zamm yarinya nan ta juye irin yacca yake mafarkin matarsa ta kasance, ba tin yau ya fara lura da hakan ba, ta ɗago kanta taga har lokacin kallonta yake, suna haɗa ido ta saukar da kanta, ya kamo hannunta yayi pecking for almost 10secs, a hankali ya ringa murza hannun nata yace "you need anything...?", da sauri ta gyaɗa kai, yace "tell me what is it..?", kanta a ƙasa tace "ina so naje gidanmu dan Allah", yayi ajiyar zuciya yace "Is that what you like..?", ta gyaɗa kai, yace "Ohk then insha Allah on Saturday sai nayi dropping dinki kiga Umma ko..?", ta ɗaga kai ta kallesa, ya sakar mata murmushin da tayi nadamar ɗagowa jin wani abu ya cakar mata zuciya, yace "yeah... Umma da ake kira daga anji wuya mna", turo baki tayi, ya ɗauke kwalin wayar daga laps dinta ya miƙe tsaye sai kuma ya riƙe hannunta ya ɗagota, rumgumeta yayi yana sauke ajiyar zuciya yace "missed you soo much yesterday..", a tare suka lumshe ido, ta kwantar da kanta sosai a ƙirjinsa. Sosai Nurain yayi keeping promise dinsa don bai sake taɓata ba, amma kuma bai sake barin sun raba shimfiɗa ba don baya ma iya bacci sai yayi Cuddling abarsa, itama ƴar farkar tafi jin daɗin bacci a jikinsa, kamar yadda ta saba a da yanzu ma haka take zata dafa abinci ta ajiye masa nasa a warmers, sai dai yanxu ba da kansa yake zubawa ba sai ya kirata ta zuba masa, Abu ɗaya ne yake sukar zuciyarta daga ta tuna cewa favor ake mata, wnn abu sosai ya tsaya mata a rai, ranar Saturday kamar zata zuba ruwa a ƙasa tasha don murna yau zata je gida, kafin ƙarfe goma ta gama duk wani aiki da za tayi, tana komawa ɗakinta ta faɗa bathroom ta fesa wanka, kayan da bata taɓa sakawa ba ta saka cikin na fitar bikin Noor da aka ɗinka mata, ta saka ƙaramin hijab dinta wanda yake tsaya mata a guiwa da kuma Charger din sabuwar wayarta a ƙaramar hand bag da ta fitar, sosai tayi kyau kamar a saceta, ta kalli door jin an buɗe, bai shigo ba ya tsaya daga waje ya waro ido yace "Hey ina zaki da sassafen nan", ta marairaice murya tace "yau ne fa zanje gida", yace "Ohk Okay... Amma dai ba ynxu ba", ta langwaɓar da kai tace "toh Ni yaushe zan tafi ƙarfe goma fa ya wuce", Nurain yayi slight smirk yace "where is my breakfast... bring it to my room". haka nan Hajar ta shiga kitchen ta hada masa breakfast sharp sharp ta kai masa ɓangarensa, ita da ta shirya tin goma da wani abun amma basu bar gidan ba sai sha biyu, Alla Alla take taga sun shiga unguwarsu don yau ma sai taga kamar gudun da yake bai wadaceta ba, Saida ya tsaya wani super market yayi shopping snn suka cigaba da tafiya, wani sanyi ne ya ratsa Hajar lokacin da yayi parking a daidai lungun gidansu, da sauri ta fara ƙoƙarin buɗe motar sai ta jita a kullu, ta juya ta kallesa ba tace komai ba, ya ɗauki envelope din daya ajiye kan dashboard ya miƙa mata, ta girgiza kai tace "Akwai tin wnda ka bani ranar nan", bai saurareta ba ya janyo jakarta ya zuge zip ya saka mata ba tare da ya lura da abinda ke cikin jakar ba, yace "idan na dawo zan shigo na gaida Umma", ta gyaɗa kai a hankali, da haka ya buɗe motar ya sauka, itama sauka tayi taga ya buɗe back seat ya fara ciro shopping bags, yara uku ya biya yace su ɗaukar mata kayan, Hajar ta saki baki tana kallonsa don ba tayi zaton gidansu za a kai ba, saida Hajar ta ɓacewa ganinsa snn ya koma mota yabar unguwar. Nabilah dake bakin rariya tana wanke wanke ta dena abinda take tabi yaran da suka shigo da kaya da kallo, Maama da ta fito daga bayi knn itama kallon yaran tayi baki a sake, Umma na zuba ƙullu cikin gwangwanaye Sabrah na shafa mata manja suma suka dubi yaran, duk cikinsu aka rasa wnda zai yi mgana, walking gently Hajar ta shigo tare yin sallama cikin murya mai sanyi, Umma dai tini ta ɗau muryar ƴarta ta, Sabrah ta micincina ido lokaci guda ta fasa ƙara tace "Addah.." sai kuma ta tashi da gudu taje ta rumgume Hajar, wani kukan farin ciki ne ya tahowa Hajar ta rumgume little sister dinta, Maama ta saki butar hannunta Nabilah kuma ta saki kwanon da take wankewa don sai ynxu suka gane Hajar, da farko sun sha wata balarabiyar ce tayi shigar hausawa, Maama ta dafe ƙirji murya a sama tace "wai Hajara ce", Hajar ko kallon inda take ba tayi ba ta wuce wajen Ummanta ta duƙa ta rungumeta, sai kuma ta fara hawayen farin ciki tace "Umma.. Ummanmu", Umma tayi murmushi tace "Hajara", Hajar na ɗago kai taga Sa'adatu da Maimuna sunyi cirko cirko a bakin ƙofa suna kallonta sai kace tsofaffin mayu sunji yunwa, Maimuna tayi wani baƙi fuska duk ƙuraje sai wata uwar rama da tayi gayau haƙora sun fito sai kace za tayi cixo, tini Umma ta rufe ƙullun alale taja ƴarta sukay ɗaki, gani kake yuuu Maama da ƴaƴanta suka bi Hajar da idanu, Sabrah ce ta ringa kwaso ledojin ta shigar dasu ɗaki, Hajar was more than happy da taga Ummanta, Umma taji daɗin ganin ƴarta ta data canza matuƙa, Hajar dai ta zama wata tauraruwa abar kallo a wajen Maama da ƴaƴanta, da ta fita yin alwala za tayi sallah har saida tayi tuntuɓe tsabar kallo, ita kam ko bi ta kansu ma ba tayi ba don bbu wnda ta kula, da yamma Baba ya shigo gida, Hajar na jin muryarsa ta ji wani mugun dadi, saida ya shiga ɗakinsa snn ta tashi ta fita ta tsaya bakin labule tayi sallama, da sauri Baba ya juya ya kalli labulen don ya gane muryar favorite din ƴar tasa, har ƙasa Hajar ta duƙa ta gaida mahaifinta wnda ya amsa mata gami ta saka mata albarka bayan ya dafa kanta, farin cikin da Hajar tayi a ranar bazai misaltu ba don rabonta da yin farin ciki kamar na yau har ta manta, bayan sallar magrib ne kiran Nurain ya shigo wayarta, dman contact biyu ne a wayar daga tasa wacca ma ko saving ba tayi ba sai na Umma, ita throughout the day ma bata bi takan wayar ba tana wajen Sabrah sai game take, basu wani jima suna wayar ba kawai ce mata yayi yana kan hanya zaizo ya ɗauketa, tace masa toh Allah ya kawosa lfy, after 15mins kam ya sake kira yace mata yaxo yana ƙofar gida, Hajar tayi wani murmushin gefen baki sai kuma ta saka veil dinta ta fita, bata wani jima ba ta dawo, Hajar ta duƙa gaban Umma wacca take zaune kan darduma tana jan carbi tace "Umma yace wai zaku gaisa", daga bakin ƙofar ɗakin Umma Hajar ta shimfiɗa darduma guda biyu, gashi kuma anyi sa'a yau an kyallaro wutar Nepa, Hajar ta fita soro bayan ta gama shimfiɗa darduman, tare suka shigo dashi ya zauna kan ɗaya daga cikin darduman, Umma ta fito suka gaisa kansa a ƙasa, da haka ya tashi ya nufi soro, Maama dai wuyanta kamar zai karye sbd leƙe daga ɗaki, lokaci guda ta koma gefen gado ta zauna sai kuma ta fashe da kukan baƙin ciki. Hajar ta gyara yafen mayafinta tayi hanyar soro, ta tsaya gami da tattaro courage don abinda za tayi sai da courage, ta ajiye numfashi a hankali, walking gently ta ƙarasa inda yake kanta a ƙasa, har ta isa kusa dashi kallonta yake, dukkansu shiru sukay bbu wnda yace komai, shi yayi breaking silence din da faɗin "shall we..?", ta jingina da bango speaking calmly tace "Thank you", ya tattare thick eyebrows dinsa yace "for what..?", ta kallesa a karo na farko tace "for everything... from the beginning till now that is the end", ya gyara tsayuwarsa yana kallonta da kyau, tace "A watanni huɗu da muka zauna tare nasan cewa na maka laifi dan Allah ka yafemin, i know i wronged you many times please forgive me.. however it seems i won't be able to do any of that now, bxn sake zama burden a kanka ba, ngode da favor din da kayimin na good 4months, nsan cewa Babana yamin aure amma ba auren Alfarma ba", Nurain ya tsuke piercing eyes dinsa yace "Hajar", ta haɗiyi wata ball da ta tsaya mata a throat tace "yess, kace zaka nunamin am your wife and you did that, still dai it won't change the fact that you are doing me a favor", kallonta yake bbu ko ƙiftawa, tace "ban san me yasa kake min favor ba ko don sbd ni ba choice dinka bace ko kuma sbd background dina ne i don't know, ngd da ka dawo dani inda ba favor ake min ba...", ta ɗan ja da baya ganin zai riƙo hannunta, ya ajiye numfashi yace "what are you saying Baby wife...?", da kyar tace "Nurain let me go, i will also let you go, from now on we won't own each other anything", tana gama faɗin haka ta juya ta shiga gida.....✍️ 💛 HAJAR 💛 {79..} A tsakar gida Hajar ta tsaya tana jin wata ball ta tsaya mata a throat, har lokacin akwai ragowar pure scent dinsa da ya bari, lokaci guda idonta ya ciko da ruwa, after a while ta juya ta kalli ƙofar soro sai kuma ta saukar da kanta ta shiga ɗakin Umma, wayarta ta amsa a hannun Sabrah ta dannata a Airplane mode ta mayar mata ta cigaba da game dinta, ta cire veil dinta ta koma gefen gado ta zauna, Umma ta kalleta tace "ya kuma naga kin zauna karfa ki barsa a tsaye yana jira", Hajar ta kwakwalo murmushi tace "Laaa ai ya tafi Umma", da mamaki Umma ta dubeta tace "ya tafi kuma...?", Hajar ta gyaɗa kai tace "Eh... ni anan zan kwana", Umma ta haɗe gira tace "bana son sakarci wane irin anan zaki kwana, tin tini baki zo da shirin kwanan ba saida kika zo nan za wani kice a nan zaki kwana, toh maza tashi ki bi mijinta tin kafin ma ya tafi..", Hajar ta marairaice tace "Umma shi yace fa na kwana wllh... kinga daga nan ma Airport zai wuce wani aiki ne ya taso masa, shine yaxo ya gaya min snn ya tambayi ra'ayina yace ya mayar dani gida ko kuma zan zauna a nan, shine nace masa a nan zan zauna, Umma yaushe rabona da ganin ku wllh nayi missing dinku over..", da kyar ta ƙarashe don muryarta har ta fara rawa kar a rafko jirginta, Umma tayi ajiyar zuciya tace "Amma baki taho da komai wnda zaki buƙata na kwana ba", Hajar tace "ba komai Umma, i will manage...", Umma bata sake cewa komai ba, Hajar ta tashi ta buɗe wardrobe inda take ajiye kayanta kafin aure taga kayan Sabrah ne aciki, Hajar tace "Umma an bayar da kayan dana bari ne...?", Umma tace "A'a duba ƙasa zaki gansu..", Hajar ta durƙusa tana duba ƙasan wardrobe din taga kayanta wajen set 7 da ta bari, sosai taji daɗi na ganin kayan, tini Hajar ta cire kayan jikinta ta linkesu ta ɗauki wani material mai laushi cikin kayan ta saka, wajen ƙarfe tara Hajar ta jiyo muryar Mu'azzam a tsakar gida suna mgana da Umma, tashi tayi ta fita tsakar gidan ta tsaya daga bakin ƙofa tace "Yayana...", Mu'azzam ya juya ya kalleta sai kuma ya tsuke ido yace "Wnn kuma daga ina..?", Hajar ta waro ido tace "Yaya ni din ce baka gane ba..?", yace "Eh kwarai..?", Hajar ta turo baki tace "knn ma ba kayi missing dina ba Yaya..", yace "Toh na sanki ne", Umma tayi murmushi tace "shiga ki ɗakko masa kwanon abincinsa wataqila ya tuna wace ce ke", Hajar ta shiga ɗaki ta ɗauko warmer din abincin nasa ta kai masa, ya amsa yace "toh yawwa ngd yar ƙanwata..", Hajar tayi murmushi tace "daman nasan tsokanata kake..", yace "Toh ykk..?", tace "lfy lou Yaya", yace "Toh masha Allah haka ake so" da haka ya shiga ɗakinsu. Washe gari wajen ƙarfe bakwai Hajar ta fita tsakar gida, tinda tayi sallar asuba ta kasa komawa bacci shine da taga Umma ta fita tsakar gida itama ta miƙe tabi bayanta, tasan aikace aikace za tayi don haka ita dai bazata kwanta ta bar Uwarta na aiki ba, tini Hajar ta kama aikin da Umma za tayi, ta share tsakar gida snn ta haɗa kwanuka tayi wanke wanke, Charcoal ta hura ma wuta ta dora ruwan shayi, yana tafasa ta juye a flask ta koma ɗaki ta tarar da Umma na tsince wake, zama tayi tana tayata tsintar waken, Sabrah na tashi Hajar ta ciro kuɗi a jakarta ta bata tace ta siyo musu bread da kwai, murna a gun Sabrah ba'a cewa komai ta tafi siyowa, Hajar na zaune kan kujera gaban Mangal tana soya kwan da Sabrah ta kawo, Maimuna ta fito daga ɗakin Maama tayi zugum tana kallon wainar kwan yawunta na tsinkewa, cikin bacci taji ƙamshin kwan ai kam a duniya taji shi kawai take son ci, Maama ta fito daga ɗakin itama da ɗaurin ƙirji, wani irin yamutsa fuska tayi ta kalli Hajar sai kuma ta zubawa Maimuna wani mugun ranƙwashi ta ƙunduma mata ashar tace "Shegiya wuce ɗaki kona ɓarar dake, yau kika fara cin wainar kwai da zaki fito ki tsira mata idanu sai kace tsohuwar mayya, da wata ƙonanniyar fuskarki", Maimuna ta juya ta shige ɗaki da sauri tana sosa inda Maama ta rankwasheta, babu ranar da rana zata fito ta faɗi Maama bata rankwasheta ko kuma mintsili ba, wataran har marinta take ko kuma ta fasa mata baki, Maama ta ja wani dogon tsaki tamkar tsohuwar tsaka tana hura hanci tace "ko wa za'a nunawa wata shegiya wainar kwai" ta shige ɗakinta tana baza zani, Hajar na gama suyar kwan ta tashi ta shiga ciki, Shayi mai kauri ta haɗa musu da kayan shayin data zo dasu jiya. Da yamma Maama na tsaye a soro sun keɓe da Balaraba da tazo, Balaraba tace "ke ni wata fa na gani kamar balarabiya a ciki", Maama ta taɓe baki tace "hmm ba wata balarabiya wnn shegiyar yarinyar ce yar wajen Faɗima..", Balaraba tace "wai Hajara ce yar kishiyarki..?", Maama tace "Uhmm itace wllh tllh... nima da tazo jiya ban ganeta ba", Balaraba tace "jar uba amma dai ba'a ƙasar nan suke da zama ba ko..?", Maama ta taɓe baki tace "Wllh a ƙasar nan suke anan garin ma kuwa", Balaraba tace "Chabɗi jam ai ƙafarta na gani kamar bata taka ƙasa wata irin fara ƙal ƙal ƙal sai kace tumatir", Maama tace "gidanta fa sama da ƙasa tayal ne, ga lantarki ta ko ina kamar zata fasa fitilu ba dole ki ganta kamar daga ƙasar waje ba, yoh gidan nata ma kika shiga ydda kika san a ƙasar wajen", Balaraba ta gyaɗa kai tace "Wnn dama malamin makarantar ta aura wllh tllh..", Maama ta sauke ajiyar zuciya tace "Ni hankalina ma duk ya tashi tsaye cur wllh, so nake na haɗa kuɗin nan muje a ɓarar da cikin jikin Maimuna kona samu nayi bacci da munshari, snn kuma zan koma wajen malamin nan na tsamiya da ƙudi masu kauri don so nake yayi min aiki mai kyau, wnn shegiyar yarinyar a kaɗota daga gidan mijin sai a manna Maimuna a wajenta, ni dai ynxu burina a fige cikin Maimuna kar ya bayyana na shiga uku", Balaraba tace "Gsky dai kiyi da jiki ƙawata tin kafin lokaci ya ƙure miki, kamata yayi ma tin ynxu a cire cikin don ya haura wata ɗaya, snn kuma baki da labarin Malamin tsamiya ya haukace watanni biyu da suka wuce..", Maama ta dafe ƙirji tace "na shiga uku ynxu wa zai min aikin kaɗo wnn yarinyar daga gidan mijin..?", Balaraba tace "Oho can ta matse miki a matsematsin matsalarki, ina ruwana duk inda zaki ki nemo malami sai kije ki nemo, nida ke anyi ta yanke anyi ta gille indai akan harkar malami ce, wancan karon ma haka kika wulaƙantani kika tijartani kika yagani sbd kince aikin da akay miki bai ci ba, ynxu ni ba ruwana dake akan wnn lamarin wllh" ta ƙarashe da jan guntun tsaki, Maama tace "Toh shknn... ynxu dai bazaki temaka min ba Balaraba, kina gani zan zama abin dariya a bainar nasi..", Balaraba tace "kinga ni tafiya zanyi bani kuɗina na ƙara gaba..", Maama ta sosa kanta tace "Wllh bani dasu banida dalilinsu kiyi haƙuri ki ɗaga min ƙafa zuwa wani lokacin", Balaraba ta saki baki tace "ban gane ba, haka mu kayi dake tsakani ga Allah, cewa fa kikai a washe gari ma zaki dawomin da kuɗina, kuma na gaya miki kudin nan ba nawa bane na mutane ne suka kawomin ajiya..", Maama ta juya hannu tace "haƙuri za kiyi Balaraba..", Balaraba tace "ni dae ki bani kuɗina tin muna shaida juna Rabi", Maama tayi kasaƙe tana kallonta kafin tace "Toh shekaruna zan lalo na baki iyee", Balaraba bata sake cewa komai ba ta juya ta fita fuuu kamar zata tashi sama, Maama ta taɓe baki ta juya ta koma gida. ★Walking slowly Nurain ya sauko daga stairs da farar Shirt a jikinsa da black sweat pant, kitchen ya shiga ya jona coffee maker, jingina yayi da jikin cabinet yana ƙarewa kitchen din kallo, haka nan yaga tana masa gizo a ko wane angle na kitchen din, ya dafe kansa da yayi masa nauyi gami da lumshe idonsa, daren jiya bai rintsa ba even a nap bai samu yayi ba, shi kansa saida yayi mamakin yacca idonsa ya soye ya kasa bacci, sai wajen biyu snn ya ɗora alwala ya fara yin sallah ganin bacci yaƙi zuwa, har asuba bai rintsa ba haka ya wuce mosque yayi sallah ya dawo, a tunaninsa zai iya bacci da safe ashe ba haka bane, daga karshe shine ya taso zai haɗa Coffee ko zai samu relief, ya dauki mug din Coffee ya fice daga kitchen din bayan ya gama haɗawa, direct sama ya haura ya shiga ɓangarensa ya zauna kan Sofa, after a while ya ɗauki mug din Coffeen ya kai baki, yana sipping yaji ɗaci sai kace ruwan bitter leaf, lokaci guda ya sauke cup din ya kalli Coffee din, sai da yaga baƙin Coffeen snn ya tuna ashe fa bai zuba milk da sugar ba haka nan ya haɗa tsura, ya haɗe thick eyebrows dinsa sai kuma yayi slight smirk bayan ya tuna ranar da ya ɗura mata irin wnn coffeen, yacca ta ringa yamutsa fuska and she cried tace Allah sai ya sakamin da ka bani maɗaci nasha... wayarsa dake kan Centre table ya dauka, ya shiga call log ya kira layinta a karo na ba adadi, abinda aka kwana ana gaya masa yaji wato switched off, Nurain bai ƙara ko 2hours a gidan ba ya fita, gaba daya gidan ya zamar masa wani empty, gidansu ya wuce kuma yana zuwa bbu wnda ya lura dashi don haka kawai ya haura upstairs ya shiga room dinsa, sai a lokacin ya samu bacci, ba shi ya farka ba sai ƙarfe biyu na rana, abinda ya fara yi shine daukar wayarsa ya sake kiran layinta, ajiye wayar yayi yana sauke ajiyar zuciya murya ƙasan maƙoshi yace "Baby wife". wajen ƙarfe huɗu da rabi Nurain ya shigo main palour ya tarar da Farooq suna gaisawa da Mami, ƙarasawa yayi ya miƙawa Farooq hannu sukay musabaha snn ya zauna kan Sofa, Mami ta ɗan kallesa tace "ka ɗauki Abincin da kace a zuba mka..?", Nurain ya gyaɗa kai yace "Eh..", Mami tace "Ohk then..", da haka ta tashi ta nufi ɓangaren Hajiya, Nurain ya dubi Farooq yace "kaxo tafiya da Amaryar taka ne...?", Farooq ya gyaɗa kai yace "Sure ita ta tasoni fa..", Nurain yace "Ohk" sai kuma ya koma yayi resting da kujera yana shafa kansa, Farooq ya gyara zama yace "That girl.. umm I can't recall her name daughter din sister din Mami..", Nurain yace "what about her..?", Farooq ya shafa kansa yace "what's that her name..?", Calmly Nurain yace "Khausar..", Farooq ya gyaɗa kai yana maimaita sunan, after few minutes of silence Farooq ya ɗago kansa daga latsa wayar da yake ya ringa kallon Nurain yace "Dude...", Nurain yace "why Punk..?", Farooq yace "you look dull and moody..", Nurain ya girgiza kai yace "Am perfectly alright", yasan idan ya gayawa Farooq damuwarsa toh sai ya masa dariya ma kafin ya basa solution, toh shi a wnn Mood din dariya ce baya so a masa, Nurain na jin alamar Hajiya zata fito ya tashi ya bar palourn ya shiga na Mami, definitely yasan saita masa mganar Hajar shi kuma baya so a ringa taɓo weak point dinsa a ynxu, haka nan Hajiya ta bar gidan tare da Farooq da yxo ɗaukarta, Washe gari Monday da wuri Nurain ya isa hospital, first abinda ya fara yi shine cancelling duk wni surgery da akay scheduling da zaiyi, ina zai iya wani surgery a wnn halin da yake ciki, patient kawai yake attending suma ba wasu da yawa ba ragowar yace Haleema ta sallamesu su dawo gobe, wajen sha ɗaya da minti hamsin ya gama duba patients din da zaiyi, wajen Haleema ya fita yace ta kira Nurse station yana son ganin A Nurse, da haka ya koma office dinsa ya zauna, after 10mins aka buɗe ƙofar office din Ruqayyah ta shigo, walking gently ta ƙarasa shigowa ta zauna kan kujera dake gaban table dinsa, Nurain ya taso daga chair dinsa ya ja kujerar dake kusa da wcca ta zauna, saida yayi nesa da kujerarta snn ya zauna opposite to her yana fuskantarta yace "Good afternoon A Nurse", ta ɗan kallesa tace "Afternoon" sai kuma ta saukar da kanta tana wasa da ring din hannunta, speaking calmly yace "You wanna to talk to me right...?, nace i will make time for you on Monday ko, so now ina jinki", sosai Ruqayyah tayi mamaki don bata taɓa tunanin zai kirata akan hakan ba, ita tasha ma ya manta ashe ba haka bane, A hankali tace "Dr ba sai na tsaya maka wani dogon jawabi ba kasan dai duk akan me nake binka, so nake kayi haquri akan laifin da nayi mka dan Allah", Nurain ya sauke ajiyar zuciya yace "If that's the case toh na haƙura, please stop disturbing my slumber..", har cikin ranta taji daɗi kuma hakan ya nuna a fuskarta, tace "Thank you very much Dearest..", ya girgiza kai yace "Take that name off your mouth Ruqayyah, ki manta da duk wani abu da ya wuce Ruqayyah, ba wai na haƙura bane sbd don mu dawo da relationship din mu na baya ba A'a na haƙura ne na abinda kika min, Ruqayyah bana so a ta dalilina kiyi ruining rayuwarki, ni na riga nayi moving on nayi aurena and ina zaune cikin farin ciki da matana, sai a ynxu nasan cewa ban dace dake ba from the start Ruqayyah, ina so kema ki ajiye komai kiyi moving on don gyara future dinki, wollah Ruqayyah I don't have any feeling left for you, kuma har abada bazan sake waiwayenki ba just know that, ki dena ɓata golden time dinki wajen yin abinda bazai fissheki ba", hawaye wasu nabin wasu haka suka fara zarya akan cheeks dinta, Nurain ya figi tissue paper ya miƙa mata, a hankali ta amsa ta goge hawayen, tana gogewa wasu na sauko mata, shi dai gsky ya gaya mata gwara tasan inda dare yayi mata tin wuri, After a while ta ɗago tace "Thank you for letting me know what is in your mind... ngd da ka yafemin laifin da na mka, tabbas some opportunities comes once in life, nima opportunityn aurenka sau ɗaya tazomin a rayuwa amma nasa ƙafa nayi fatali da ita, insha Allah Ni Ruqayyatu ba zan sake shiga rayuwarka ba Dr..", Nurain yace "Better", a hankali ta tashi ta nufi door har lokacin hawaye bai dena sauko mata ba, ta juya tana kallonsa sai kuma tace "Allah ya baka zaman lfy with your wife..", speaking with a repartee yace "Ameen.. please Shut the door", ta gyaɗa kai a hankali tace "Tom" da haka ta fice ta kullo masa ƙofar. Ƙarfe tara na dare Nurain na kwance kan doguwar kujera a palourn Maminsa, ceiling kawai yake kallo ya ɗora left hand dinsa a forehead, thick eyebrows dinsa a haɗe thinking of what to do, toh ynxu idan yarinyar ta gayawa parent dinta da wne idon zai kallesu, bama wnn ba Babanta wane irin kallo zai yiwa Abba, shiyasa ya rasa courage din zuwa gidan nasu don bai san me zai tarar ba, kuma shima rashin zuwan nasa matsala ne, wayarsa dake side dinsa ya ɗauka ya ringa kallon screen dinta, after few seconds ya ajiye ba tare da yayi komai da ita ba, don yasan ma idan ya kira switched off zai ji, lumshe idonsa yayi gami da sauke ajiyar zuciya, Mami da ta fito daga bedroom ta ringa kallonsa without blinking, ƙarasawa kujerar da yake kwance tayi ta kai hannu forehead dinsa tace "Are you sick Son..?", ya buɗe lumsassun idanunsa sai kuma ya miƙe zaune yace "No", Mami tace "Ohk amma ya baka tafi gida ba ko baka san dare yayi ba..?", ya kalli clock yace "ban san dare yayi haka ba", Mami tace "Alright sai ka tashi ka tafi dare na kuma yi, ka bar ƙaramar yarinya a gida", yace "Toh" da haka ya tashi yana jan rigarsa yace "Saida safe", tace "Allah ya tashemu lfy", ta bisa da kallo har ya fice, definitely tasan akwai abinda yake damunsa, ko ta tmbyesa ma ba gaya mata zaiyi ba sbd shi lamba ɗaya ne a fannin zurfin ciki da taurin kai, da kansa zaizo ya gaya mata idan abun ya ishesa dman haka yake. ★Yau kwanan Hajar uku a gida, sosai take jin daɗin zamanta da Ummanta da little sister dinta, lokaci zuwa lokaci abinda ta ajiye ƙasan zuciyarta ke tsikararta kuma nan da nan take yakice sa daga ranta, tinda tazo Baba bai mata mgana akan kwana ba sai yau, kuma shima cewa yayi ta tafi gidanta ko mijin nata bai dawo ba, da ta koma ɗaki tana kumbure kumbure ma Umma bata goyi bayanta ba tace ai tayi na Allah da ma'aiki kawai ta tafi, gashi bata gayawa Umma ainahin me ya faru ba, haka dai ta ƙudurce a ranta yau da daddare zata sanar da mahaifiyarta gskyr lamari, Hajar na zauna kan darduma tin bayan da ta idar da sallar magrib, daga tsakar gida taji Umma na yiwa Sabrah mgana tana cewa "baza kije ki kai mata wayarta ba iye... kullum waya na hannunki sai game kike bbu kama ƙafar yaro", Mu'azzam dake tsakar gidan shima yace "Ai wcca ta bata ce ba tada hnkali... bata san tsadar wayar bane shiyasa, Samsung ce fa ynxu ta faɗi screen dinta ya fashe sai taja kuɗi sama da dubu ɗari wllh... a Samsung din ma fa tata babba ce..", Umma ta riƙe baki tace "wuce ki kai mata wayarta", Sabrah tace "Toh", sum sum sum ta tashi ta kaiwa Hajar wayar, Hajar ta amsa tace "Anjima kaɗan saina baki ki cigaba da game din", Sabrah tace "Toh Addah" sai kuma ta juya ta fita, Hajar ta kalli wayarta ta a karo na farko tinda garin Allah ya waye, sam sam bata bi takanta don har Chargi ma Sabrah ce take sakata idan an kawo wuta, kuma tinda ta sakata a Airplane mode bata cire ba, a hankali ta kai hannu ta kunna wayar, tattare gira tayi bayan taga notification din messages, da sauri ta janyo labulen wayar ai kam taga ba a Airplane mode take ba, Sabrah ta cire garin danne danne, Hajar ta kwanta tana kallon messages din amma bata buɗe ba, ta sauke numfashi a hankali ta kai hannu ta buɗe guda ɗaya, saida zuciyarta ta buga kafin ta fara karanta message din, guda biyu kawai ta karanta taji idanunta sun ciko da ruwa, lokaci guda hawaye suka fara gangaro mata ta kife wayar don bazata iya cigaba da karantawa ba, ko minti goma ba ai ba wayar ta fara ringing, ita tsorata ma tayi don tayi nisa cikin tunanin da take, ta ɗago wayar tana kallon screen dinta ba tare da tayi picking ba, a haka har kiran ya katse wani ya sake shigowa, ta kai hannu za tayi rejecting call din amma ta kasa, ba tasan lokacin da tayi picking ba sai kuma ta kasa kaiwa kunne, a hankali ta kara a kunnenta ba tace komai ba, ta jiyo muryarsa yace "Baby wife..", turo baki tayi ta masa banza, yace "Hajar..", tayi jimm kafin tace "Na'am", ajiyar zuciya taji ya sauke tayi sauri ta lumshe idonta tana jin tsigar jikinta na mimmiƙewa, yace "har ynxu baki huce ba Baby wife..?", ta masa banza tana wani turo baki, yace "please talk to me", nan ma shiru ta masa, Calmly yace "Am sorry Hajar, i shouldn't have said All that stuff, delete All that stuff from your head please, Am sorry Baby wife", Sosai jikinta yayi sanyi ta kasa ce masa uffan, hawaye ya cika idanunta, yace "Can i come for you now..?", ta girgiza kai kmar yana kallonta tace "No..", yace "Why..?", tace "Sbd kaxo ka tafi dani ka cigaba da min favor ko", ya sauke numfashi yace "Hajar.. wollah i take back all what I said", tace "Okay good night...", yace "Toh can i come and pick you tomorrow..?", katse kiran tayi without answering, nan ya ringa kiranta taƙi yin picking, message ta shiga ta tura masa Yess, daga hka ta danna wayar a Airplane mode. Washe gari sai yamma liƙis Hajar ta cire wayarta a Airplane mode, dman tace da Umma ai yau ma zaizo su tafi ya dawo daga tafiyar. wajen ƙarfe takwas na dare kiransa ya shigo wayarta, tana picking yace "how are you doing Baby wife..?", tace "Alhmdllh", yace "Good, Am here already", tace "Ohk" sai kuma ta katse kiran, Umma ta shigo ta ajiye warmer din abincin hannunta gefe guda snn ta kalli Hajar tace "baizo bane..?", Hajar ta girgiza kai tace "yaxo yana ƙofar gida", Umma tace "toh tashi ki tafi mna kin barsa yna jira", Hajar tace "Umma ba muyi sallama da Baba fa", Umma tace "Topa kin san dai ba ynxu zai dawo ba sai Anjima", Hajar tace "nidae zan jirasa", Umma ta buɗe baki knn saiga sallamar Baba, yace "Ina Hajarar ne..?", Umma ta fita tsakar gida tace "gata nan mal", Hajar ta tashi ta tsaya gaban mirror zata ɗauki handbag dinta, zuge handbag din tayi ta ciro duka kuɗin da suke jakar ta ajiye kan mirrorn ta danne da robar mai, ta kalli Sabrah da ta bita da ido tace "Shhh karki gayawa Umma", da haka Hajar ta fita tsakar gida Sabrah tabi bayanta, Hajar ta duƙa gaban parent dinta tana musu sallama, Baba ya dafa kanta yana saka mata albarka kamar yacca ya saba, tini hawaye suka cika idon Hajar don ji take kmar idan ta tafi bazata dawo ba, Maama da ke tsaye tsakar gidan itama tace "Au ai na sha kaɗota akay da naga kwana biyu ta zaune a gida", daga Baba har Umma bbu wnda ya tanka mata, Sabrah kam fashewa tayi da kuka ita sai tabi Hajar, Hajar kam ta cake tace ta ɗakko kayanta su tafi, Umma tace A'a makaranta fa, Baba kam daman bai yarda ba tin farko ya girgiza kai, Hajar tace "A cewa Yaya na tafi", Umma tace "zai ji". Walking slowly Hajar ta nufi soro zuciyarta na wani irin harbawa tamkar zata fito, tin daga bakin soron taji ƙamshinsa da tayi mugun missing, ta saukar da kanta ta ƙarasa fita, ko da wasa bata kalli position dinsa ba ta tsaya nesa dashi, ta ɗanyi bowing tace "ina yini", kallonta yake without blinking sai kuma ya sauke ajiyar zuciya, one thing came to his mind cewa bata sanar da parent dinta ba. The ride was so silent bbu wnda yace uffan a cikinsu, ita kam Hajar window ta kalla ta ringa kallon titi, suna tsaye a wani traffic kafin a basu hannu Nurain ya juya Ninety degree yana kallonta, sosai taji kaifin idonsa a kanta amma taƙi ta juyo, slowly ya kamo hannunta ya ringa murzawa a tafin nasa, ta ɗan juya ta kallesa, yayi pecking hannun nata yace "kinyi shiru", ta saukar da kanta ba tace komai ba, ya sake pecking hannun nata ai kam ta ɗago ta kallesa, yace "ko saina buɗe bakin", turo baki tayi zata fixge hannun yaƙi ya sakar mata, da haka ya juya ya cigaba da driving don an basu hannu, da hannu ɗaya yake driving din ɗayan hannun kuma yana riƙe da nata, suna shiga palour bayan sun isa gida Hajar ta nufi stairs, da sauri Nurain ya ajiye ledar roasted chicken da tsire daya siya a hanya ya riƙota, kan kujera ya zaunar da ita yace "Are you still mad at me..?", ta girgiza kai, ya duƙa gabanta yace "Hajar bana so ki haura upstairs baki huce ba..", Kneeling yayi yace "please forgive me Baby wife", tini ta zamo ƙasa daga kan kujerar ganin abinda yayi tasa soft palm dinta ta toshe masa baki tace "wllh na haƙura", lokaci guda ta faɗa ƙirjinsa ta sakar masa kuka tace "Wllh na haƙura.. nima kayi haƙuri", tini yayi wrapping dinta sosai tamkar zai ɓallata, ta lumshe idonta tana sauraron bugun zuciyarsa tana kuka a hankali wnda ta rasa dalilinsa, in a whisper tone yace "I missed you Baby wife"......✍️ 💛 HAJAR 💛 {81..} Saida Hajar taji fitarsa masallaci da asuba snn ta buɗe idonta, a hankali ta muskuta ta sauko daga gadon tana ƙarewa kanta kallo, rigarsa ce a jikinta wcca ta tsaya mata a rabin laps, bata san lokacin da wani murmushi ya kufce mata ba, sai kuma ta saukar da kanta tana jin wata azabar kunya, ilahirin jikinta ya kwaso ainahin ƙamshin mijinta mai sanya nutsuwa, sleeping gown dinta dake yashe kan tiles da ribbon dinta ta dauka ta nufi door da sauri, bata so ya dawo ya tarar da ita a room dinsa cause bazata iya haɗa ido dashi ba, room dinta ta wuce direct ta shiga bathroom ta dauro alwala, tana idar da sallah ta koma gefen gado ta zauna don har ynxu tana jin slight pain, gaba ɗaya memory din last night ne yake mata yawo a brain, komai fresh yake dawo mata, ai kam ta ringa zabga murmushi ba kama ƙafar yaro, tana ji aka buɗe ƙofa amma taƙi ɗagowa cause tasan shine, Nurain na riƙe da door handle yana kallonta without blinking, murmushi yayi ya shafa cikakkiyar sumarsa still yana kallonta, bayan watanni huɗu da aurensa sai yanxu kyallin Angonci yake haskawa a goshinsa, kulle ƙofar yayi ya ƙaraso har inda take ya duƙa, da sauri ta kawar da kanta tace "ina kwana...", Calmly ya kamo hannunta yace "Good morning Sweet pie..", ta saukar da kanta sam taƙi bari su haɗa ido, yayi blushing yana lura da yanayinta yace "how was our steamy night...?", da sauri ta amshe hannunta ta kwanta ta cusa kanta cikin pillow tana jin wata azabar kunyarsa, tafin fararen ƙafarta yabi da kallo sai kuma ya kai hannu yabi zanen ƙunshin da akay mata da bikin Noor wnda har ynxu bai gama ficewa ba, Hajar ta janye ƙafarta jin yana mata tafiyar tsutsa ta turo baki, lower lip dinsa ya ciza painlessly, hawa gadon yayi ya ɗagota lokaci guda ya cire zumbulelen hijab din dake jikinta yace "I hate this blanket..", ta zaro ido tana turo baki tace "Ni ka bani abuna..", cilli yayi da hijab din har saida ya kai gaban mirror snn ya juya ya zubawa chest dinta idanu, yace "Toh ina ne ban gani ba... abarni na kalli properties dina ehe..", ji tayi kamar ta nutse a wajen, ta ɗaga kai ta kallesa suna yin ido huɗu ta saukar da kanta tana murmushi, ta turo baki tace "Ni dae ka bani abuna..", yace "wollah baza a rufemin properties dina ba..", tini ta fara ƙoƙarin sauka daga gadon ya fixgota yayi wrapping dinta a ƙirjinsa, ya cusa kansa a wuyanta ya ringa shaƙar ƙamshinta, after a while ya sauke numfashi yace "Toh muyi fira about our sweet yesterday's night" da haka ya sauke mata wni hot kiss a neck, ba shiri ta maƙe wuya ta shige jikinsa tana ajiye numfashi don wni electric shock ne ya ratsa veins dinta, ya kai lips dinsa saitin kunnenta yace "shall we have one romantic morning.." da haka yayi kissing kunnen nata, ta maƙe shoulder tace "Ni dae A'a...", yace "please Baby wife..", nan ma ta maƙe shoulder, bai sake cewa komai ba ya ɗago kanta yayi kissing lumsassun idanunta, sai kuma yayi kissing karan hancinta, murmushi tayi idonta a lumshe ta riƙe rigarsa gamm, kallon lips dinta yayi sai kuma ya sunkuya yayi brushing dinsu da nasa, ta tamke riƙon da ta yiwa rigarsa tana ajiye numfashi, kallon fuskarta yayi na few seconds sai kuma ya sake sunkuyawa yayi sucking lips dinta deeply, tini ya fara fita daga duniyar itama yana ƙoƙarin fitar da ita, da kyar ya janyo pillow ya kwantar da ita slowly, daga haka kuma ya fara smooching dinta a hankali, tayi masa lamo ta riƙe rigarsa gamm as if her life depend on that, saida taji yana ƙoƙarin rabata da ƴar rigarta snn ta farga, ai kam tini ta hantsila gefe ta gyara rigarta da ta tattare tana turo baki, ita fa har ynxu azabar tsoronsa take ji har cikin ranta, ita kaɗai tasan azabar da take sha idan ya taɓata, last night ma saida ta ɗanɗana don ruwan citta ta shiga, Nurain ya sauke ajiyar zuciya sai kuma ya tashi daga kan gadon yana buttoning rigarsa, blushing yayi yace "Ohk then bari na nemi alternative...", ya zagayo ta inda take ya duka yana kallon fuskarta, turo masa baki tayi, yayi murmushi yace "Au duk da na kyaleki shine kike turamin baki, tinda ban samu morning Coffee from you ba bari naje nayi making na alternative..", ta saukar da kanta ba tace komai ba, slowly ya kamo hannunta yace "you want some...?", ta gyaɗa kai a hankali, yaja hancinta yace "Ohk Coffee or Chocolate...?", ta langwaɓar da kai tace "Coffee..", yace "Alright" da haka ya tashi ya nufi door hannunsa zube a pocket, Hajar tabi bayansa da kallo sai kuma tayi murmushi tana juya lulu eyes dinta, After 15mins taji ana knocking door, tashi tayi taje ta buɗe ƙofar, yana riƙe da 2 Coffee cups a both hands dinsa, ya miƙa mata ɗaya yace "here..", ta amsa tace "thank you..", ya ɗaga cup din hannunsa yace "Enjoy.." da haka ya juya ya wuce ɓangarensa, Hajar ta rufe ƙofarta a hankali, gefen gado ta samu ta zauna ta ringa sipping coffee din, sosai ya mata daɗi don har wni lumshe ido take fuskanta a sake, tass ta shanye ta tashi zata kai cup din kitchen, bai ɗauketa wni lokaci mai yawa ba ta gama gyara kitchen da downstairs palour, daga nan ta haura room dinta shima ta gyara snn ta baza turaren wuta a ko ina, towel ta ɗaura ta faɗa wnka, yau yadda ta tattale jikinta na musamman ne, kolacca da humra da Sakeena ta bata tin lokacin da taje gidan ta ɗakko, ta shafe jikinta da kolaccan bayan tayi rubbing lotion dinta, snn tabi kan kolaccan da humra itama mai azabar sanyin ƙamshi, tayi Oiling gashinta snn tayi parking dinsa ta saki jelar da ta sauka har mid back, ta tsaya gaban mirror tana ƙarewa kanta kallo bayan ta saka gown din da ta fitar, sosai tayi kyau snn kuma body figure dinta sun fito sosai duk da cewa kayan ba kwasassu bane, wall clock ta kalla taga takwas saura, zaro ido tayi ta saka takalminta ta nufi door, tini ta shiga kitchen ta fara shirya breakfast, tana tsaye gaban sink tana wanke dankalin da ta feraye aka buɗe ƙofar kitchen din, bata juya ba don tasan shine tinda tayi perceiving pure scent dinsa, saida Nurain ya zagwanye a tsaye tsabar yacca ta masa kyau, kawai kallon back view dinta yake without blinking wata kasala na ratsasa, ajiyar zuciyar da bai shirya mata ba ya sauke lokaci guda yaje ya rumgumeta, Hajar ta zaro ido tace "What are you doing...?", ƙamshin da yayi perceiving ne a jikinta yasa ya cusa kansa a wuyanta perceiving it even more, gaba ɗaya Hajar sai taji ta kasa cigaba da abinda take, ga tap din ruwa da ta buɗe yanata zuba, da kyar ta iya cewa "dan Allah ka bari kaga fa aiki nake..", a kasale yace "Continue what you're doing am not stopping you Baby wife...", yana gama faɗin haka ya kwantar da kansa a nata har dasu lumshe ido, ta kalli ydda ya ritsa cikinta da hannayensa, a hankali tace "But i can't work like this..", yace "Ohh really toh abar aikin nidae bxan rabu da partner dina ba..", murmushi tayi ta ƙarasa wanke Irish din ta bar sa a colander zai tsane, buɗe idonsa yayi jin ta cigaba da aikin yace "Baby wife...", tace "Uhmm", ya shafa flat tummy dinta yace "I think yesterday's night I left something precious here.." ya ajiye mata wni combo kiss a neck yace "right..?", runtse ido tayi tana jin kamar ta nutse a ƙasa ta huta kawai, wai shi baya jin kunya ne, ta wni irin turo baki lokaci guda ta fara bubbuga ƙafarta a ƙasa da muryan shagwaɓa tace "Kaga bana so..", yyi blushing yace "Eh mna..", bubbuga ƙafar ta cigaba da yi tace "Ni A'a ba haka bane", sakinta yayi sai kuma ya sunkuceta sai kace baby yace "Muje upstairs sai kimin shagwaɓan da kyau snn kuma ki bani amsana da others ma da nake binki bashi", da haka ya fita daga kitchen din da ita sai ciccilla ƙafa take tace "Ni fa girki zanyi", yayi pecking lips dinta yace "let feed on each other... symbiotic mode of nutrition..", direct ɓangarensa ya wuce da ita bayan sun haura sama. ★Ƙarfe biyar da wni abu na yamma Maama na tsaye kan Maimuna dake zaune gefen gado ta toshe baki da duka hannayenta, Maama ta zuba mata wani mugun ranƙwashi tace "cinyesa shegiyar banza, wllh bxa ki fita ki tona min asira a bainar nasi ba saidai ki cinye amanki..", Maimuna dai ta guntse baki hawaye na zuba idonta don amai ne cike a bakinta ta kasa haɗiyewa, bazar bazar Balaraba ta afko ɗakin bbu ko sallama, Maama dake ƙundumawa Maimuna ashar ƙasa ƙasa ta juyo ta kalli Balaraba, lokaci guda Maama ta haɗe rai tace "A'a lfy zaki bankaɗo min ɗaki ba sallama..", Balaraba da ta wani murtuke fuska tace "Ke Rabi bani kuɗina..", Maama ta yamutse fuska tace "Ah aha toh meye kuma na miƙo hannu bayan abin rabo ya ƙare, kuɗi dai zan biya amma ba ynxu ba sbd bani dsu", Balaraba ta kalli sama tana jinjina abinda Maama ta faɗa snn tace "kut melesi.. billahillazi la'ilaha illa huwa bazan bar gidan nan ba sai kin biyani kuɗina Rabi..", Maama da ta fara fusata ta baza zani tace "na ƙarfin arnan da ne ehe.. idan kinada ƙarfi saiki kwata..", kafin kace me cacar baki ta kaure a tsakanin Maama da Balaraba, Balaraba ta cokalo kallabinta gaba ta daddage ta dungurewa Maama kai tace "Ai saina nuna miki ƙarfin arnan da din idan shi kika zaɓa", saida Maama tayi taga taga kamar zata faɗi tsabar yacca kan nata ya dunguru don har saida wuyanta ya amsa tamkar zai karye, Maama ta mulmulo ashar bayan ta gama recover, ba tayi wata wata ba ta cukuikuiye Balaraba ta tankaɗata waje, nan suka shiga musayar mugayen kalamai suna laftawa juna, Nabilah da take tsakar gida tana tankaɗe tayi kasaƙe tana kallonsu, Maama tace "Dalla malama fitar min daga gida..", Balaraba ta buga cinya tace "Ahayye riii ba dai kince kuɗi na ƙarfin arnan da bane toh kwa zaki gani", Maama ta zage ta ringa ƙoƙarin tura Balaraba soro amma firr taƙi fita, Umma ta fito daga ɗakinta jin hayaniya taƙi ta ƙare, Balaraba na ganin Umma tace "yawwa Faɗima..", nan Balaraba ta bankaɗa sirrin Maama wnda tayi asiri lokacin bikin Hajar har aka fasa aurenta da Ya Sayyadi Nura, Balaraba tace "Itace nan munafuka algunguma annamimiyar da ta shiga ta fita aka fasa auren Hajara wai duk don sbd karki cigaba keda ƴarki, Toh da aka fasa auren ma ba kyaleki da ƴarki tayi ba don tinda ta kyallara ido taga gidan yarki da maiƙo ta gigice tana neman hanyar da zata bunka wani asirin don a sako ƴarki ita kuma ta manna tata ƴar", sosai Umma ta sha mamaki ta tsinci kanta da furta "innalillah wa'inna ilayhirraji'un..", Balaraba tace "kuma ƴarta ta da tayo cikin shege...", sai a lokacin Baba da bai daɗe da dawowa ba ya fito yana kallon Balaraba yace "Fita..", Balaraba tace "Toh mal Adamu ko baka san cewa ƴarka Maimuna ta kunshi cikin shege ba ita da uwarta suka ɓoye, ynxu ma haka neman kuɗin da za'a cire cikin suke kafin ya fito fili", gaba ɗaya Maama gigice tayi ta wani susuce tamkar psycho, jikinta har rawa yake ta rasa mai zata yiwa Balaraba, sai dukanta take da guiwar hannu amma Balaraba taƙi yin shiru, daidai nan Huzaifa ya shigo gidan, jiya ya dawo gida sbd an musu hutun session, Nabilah ta matso inda yake tace "Yaya dan girman Allah fita da wnn matar..." shiru tayi sakamakon bangazar da Maimuna ta mata wcca ta fito daga ɗaki da gudu, ko bakin rariya Maimuna bata iya kaiwa ba ta durƙushe nan tsakar gida ta shiga kwarara amai, duk mutanen da suke tsakar gidan suka ringa kallonta kowa da abinda yake saƙawa a ransa, hatta Maama tsayawa tayi tana kallon Maimuna wcca har lokacin take kakari, Balaraba ta taɓe baki ta buga cinya tace "ga zahiri nan kun gani ehe, cikin shege dai gashi nan a jikin ƴarku...", wata kururuwar baƙin ciki Maama ta kurma ta rarumo bokitin ƙarfe ta ɓaurawa Balaraba a goshi, tini jini ya tsinke a goshin Balaraba, Maama ta sake ɗaga bokitin zata buga mata a karo na biyu Huzaifa ya amshe, da haka yayi waje da Balaraba dake ƙundume ƙundumen ashar tana cewa "Ni kika fitarwa da jini ko... kwarankwatsa dubu saina rama baza kici bulus ba", a sukwane Maama ta juya ta kalli Baba lokaci guda ta rushe da kuka tace "ƙarya take yi wllh tllh... masharraciya ce algunguma..", Baba da yake jin ƙirjinsa kamar an cinna masa wuta ya juya ya shiga ɗakinsa yana dafe bango, Umma ta kalli ɗakin Baba sai kuma ta saukar da kai ta shiga nata, wnn wni irin bita da ƙulli ne hka, dman Maama ce ta kawo tangarɗa lokacin auren Hajar, Maama tayi zaman ƴan bori a ƙasa tana rusa kuka kamar ranta zai fita tana cewa "ƙarya take wllh tllh..", Nabilah ta ringa ƙoƙarin ɗagata amma taƙi tashi, a fusace Huzaifa ya dawo gida bayan ya kaɗa Balaraba har kusa da lungun gidanta, fuskarsa a ɗaure ya dubi Maimuna da har lokacin take durƙushe ta kasa tashi yace "Ke durƙushen me kike yi anan da bazaki koma ɗaki ba..?", a kasale Maimuna tace "bazan iya tashi ba", wata irin fusata Huzaifa yayi da tace haka, don a zafin zuciya ya linka Naseer, wani harbi ya kai mata a ruwan ciki, dga nan ya zare belt ya ringa shauɗa mata kamar Allah ne ya aikosa, ihu Maimuna take tana neman agaji amma daga Maama har Nabilah bbu wnda ya ceceta, ta ko ina Huzaifa ya ringa sauke mata ruwan belt yace "dan uwarki ni zaki gayawa ba zaki iya tashi ba..", tin daga soro Sa'adatu da ta dawo gidan ynxu ta ringa jin ihun Maimuna, leƙowa tayi taga abinda yke faruwa ai kam ta koma ta rakuɓe a soron tana raba ido tamkar ɓera a buta, Maimuna ta rasa inda zata sosa a jikinta sbd duk inda Huzaifa ya samu lafta mata belt yake, da sauri Umma ta fito jin duka yaƙi karewa ta riƙe belt din hannun Huzaifa, sai a lokacin Maimuna ta samu chance ta rarrafa ta shige ɗaki tana jin wni abu mai ɗumi yana bin cinyoyinta, gaba ɗaya Umma ta kasa sukuni tin bayan da Baba ya shiga ɗakinsa, Ai kam tana shiga ɗakin nasa ta tarar ba lfy don Baba har ya fita hayyacinsa, a gigice ta kira Huzaifa suka koma ɗakin tare, ranga ranga Huzaifa da Mu'azzam suka wuce da Baba Asibiti Emergency, tini aka amshi Baba domin basa taimakon gaggawa, saidai me kamar ana zubawa wuta fetur ne don bbu wni cigaba da aka samu don jikin Baban ma yafi sauƙi a gida, BP dinsa ne ya haye fiye da kima ga kuma zuciya da itama ta motsa sosai, ƙarfe bakwai na dare Naseer ya iso asibitin shima don dman yana kan hanya Mu'azzam ya kirasa a waya ya gaya masa, bayan minti ashirin da zuwan Naseer suna zaune a bakin Emergency room din da likitoci sukace a basu guri, wata Nurse ce ta fito tayi describing Baba tace ana buƙatar relative dinsa guda ɗaya ya shiga, wata gudumar tashin hankali ce ta doka akan Naseer bayan ya hango gadon da Baba yake kai, da sauri ya ƙarasa gaban gadon yana kallon Baba da already an lulluɓesa har kai, Naseer bai san lokacin da ya zauna kan kujerar dake gaban gadon ba, a hankali ya kai hannu ya buɗe fuska mahaifin nasa wcca tayi kamar ta mai bacci cikin nutsuwa, after a while ya rufe masa fuskar yace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un", ya saukar da kansa hawaye na sauko masa yana jin wata ƙuna a zuciyarsa, Dr din da yake cikin duba Baba har Allah ya masa rasuwa ya dafa shoulder din Naseer, Calmly Dr din yace "Allah ya gafarta masa..", After 15mins Naseer ya fita daga E.R din, Huzaifa na zaune kan kujera ya dafe kansa with both hands, Mu'azzam kam sai zagaye yake ya kasa zama don Umma ce take ta sirfa masa kira, dman da kyar ta yarda suka barta a gida, tinda suka zo asibitin yake lafta mata ƙarya don ta kwantar da hankalinta, da sauri Mu'azzam ya nufi Naseer yace "Yaya ya jikin nasa...?" sai kuma yayi shiru ganin yacca idon Naseer din yayi jajur, Huzaifa ya taso shima yana tambayar jikin Baba, Naseer yana kallonsu duka yace "Allah ya yiwa mahaifinmu rasuwa". ★Nurain ya dubi wayarsa da tayi ring wcca take side dinsa, dakatawa yayi da operating laptop da yake ya ɗauki wayar, ganin Abba ne ke kiransa ya duba lokaci yaga ƙarfe goma saura, picking yayi ya kara a kunne, ko minti biyu ba suyi ba suna wayar, Abba ya gaya masa cewa Allah ya yiwa mahaifin Hajar rasuwa gobe zasu fita jana'izarsa, shi ma Abba yana zaune yaga an turo masa message ta numbern din Baba, toh anan yaga rasuwar wnda Naseer ne yayi amfani da wayar Baba ya tura message ga duk Contacts din Baba don a samu sauƙi wajen sanar da mutane, Nurain ya tashi da sauri ya nufi door yana jan rigarsa, corridor ya fita ya buɗe ɗakinta, tarar da ita yayi tana linke hijab din da ta idar da sallah, already har ta saka kayan baccinta riga da wando, kallonta ya ringa yi without blinking sai kuma ya shiga ɗakin, ajiye hijab din tayi bayan ta gama linkewa, ta ɗaga kai ta ɗan kallesa, suna haɗa ido ya sakar mata murmushi, ta saukar da kanta tana twisting slim fingers dinta, ya ƙaraso inda take yace "Sweet pie have you eaten..?", ta gyaɗa kai, yace "hope da yawa kika ci little love ma ya samu nasa...?", turo baki tayi ta juya masa baya, murmushi mai sauti yayi ya rumgumeta ya shafa tummy dinta yace "idan kinyi denying bbu a daren jiya toh yau da safe fa..?", ƙoƙarin fixge kanta ta ringa yi don kar ya yiwa kunnenta fyaɗe, ya sauke ajiyar zuciya yace "where is your phone...?", ta nuna masa kan bedside, sakinta yayi yaje ya ɗauki wayar ya zura a pocket, ita dai ta bisa da idanu ba tace komai ba, yace "Muje ki kwanta Dear..", gado ta nufa tace "Anan zan kwanta ni..", bai saurareta ba ya riƙo hannunta yace "Toh ni kuma fa pillow zanyi hugging tonight...", yana riƙe da hannunta har suka isa ɓangarensa, kwantar da ita yayi kan gado ya gyara mata pillow, yaja duvet ya rufa mata zuwa shoulder, pecking forehead dinta yayi yace "Sleep tight.." da haka ya nufi door ya fita, yana fita palour ya ciro wayarta daga pocket, ya tarar bbu message ko missed call, ajiyar zuciya yayi don yasan ba'a kai ga kiranta daga gida ba, but yasan dole za'a kirata kuwa, da shike sim din Hajar sabo ne kuma bbu wnda yasanta dashi sai Umma da Mu'azzam, kuma a cikinsu bbu wnda ya kira. gaba ɗaya daren nan Nurain bai rintsa ba yana gadin Hajar, ko motsi tayi sai ya sani don sosai yayi cuddling abarsa, sau uku yana jin tana firgita, sai jikinta yayi wani karrr kamar mai jin sanyi, yawan firgitar da ta ringa yi ne yasa ya fara mata karatun Alkur'ani a kunne, ai kam bata sake firgitar ba, wajen ƙarfe uku Hajar ta farka sakamakon Cramps din da yake kartarta har cikin bacci, mutsu mutsu ta ringa yi don sosai cikin ke mata ciwo, Nurain ya buɗe lumsassun idanunsa yace "Mene ne..?", a hankali tace "Cikina", tashi yayi da ita a jikinsa ya kunna hasken ɗakin, yace "ina ne yake ciwon..?", ta masa pointing lower abdomen dinta hawaye ya ciko idanunta, wani magani ƙwalli ɗaya tak ya bata ta haɗiya, ai kam ɗipp taji ciwon ya ɗauke ta koma ta kwanta, bata sake farkawa ba kuma sai asuba, Tinda ta tashi da asuba gabanta yake yankewa yana faduwa haka nan saddan, har wni jiri jiri ta ringa ji tsabar ycca gabanta ke faɗuwa, a haka dai tayi sallar asuba bayan ta idar ta haɗe kanta da gado tana Azkar, Nurain na dawowa masallaci ya duba ɗakinsa yaga bata nan don haka ya biyota room dinta, ya ƙaraso inda take jigine da gado ya duƙa gabanta, da sanyin murya tace "barka da Asuba...", Calmly yace "Good morning how was your night...?", tace "lfy alhmdllh..", yace "Masha Allah... ya ciwon cikin..?", tace "ya dena", ya ringa kallonta ganin kamar tayi weak, ya sauke numfashi a takaice sai kuma ya ɗagota ya zaunar da ita gefen bed, a gefenta ya zauna ya kamo hannunta with care yace "Hajar..", tace "Na'am..", slowly yake murza hannunta yace "kin san dai duk wni mai rai mamaci ne, kuma Allah baya barin wni don wani muddun sa'insa yaxo ko..?", wni irin bugu zuciyarta tayi ta ringa kallonsa bbu ko ƙiftawa, ta gyaɗa kai a hankali, yace "ki shirya zamu fita tare before 7 kinji..", shida da rabi Nurain ya sake dawowa ɗakinta ya tarar har tayi wnka ta shirya, amma kana ganin yanayin kasan a tsorace take snn ga gabanta da yake ta faɗuwa, mug din da ya shigo dashi mai ɗauke da thick tea ya miƙa mata yace ta shanye yana dawowa, Hajar ta zauna da nufin shan tea din amma ƙiri ƙiri ta kasa haɗiya, da ƙyar ta iya shan rabi, next dawowar da Nurain yayi da car key a hannunsa, hijab din data fitar ta ɗauka tasa akan doguwar rigar jikinta ta atamfa, A motar ma lallaɓarta ya ringa yi yana gaya mata maganganu masu taushi, ita dai kawai jinsa take don har ynxu bai gaya mata ainahin me ya faru ba, tini zuciyarta ta karye a karo na farko da tayi mgana tace "dan Allah me ya faru...?", tayi saurin goge hawayen da suka hau zarya kan cheeks dinta without her consent, Calmly ya kamo hannunta yace "Ba komai, just say Allahumma ajirni fi musibati wa aklufuli khairan minha..", wnn ne time na farko da Nurain yaji yana shakkar faɗar abu, bai san how she will react bne idan ya gaya mata kai tsaye, baya so ya karya zuciyar Baby wife dinsa, Hajar taji zuciyarta ta dawo maƙogoro har tana jin bugunta a kunnenta bayan taga inda motarsu ta tsaya, wni irin kyarma jikinta ya fara wnda ya ratsa har zuwa lips dinta, tini ta zare hannunta daga nasa ta juya ta ɓalle murfin motar ta fita, tini shima ya buɗe motar ya fita don da zafin nama ta amshe hannunta snn ta buɗe motar wnda bai san tana dashi ba, har wani gurɗewa ƙafafuwanta suke ta nufi lungun gidansu, habawa ai tini Hajar ta kwasa a guje don gani take tafiyar bazata kaita ba, bata ma lura da mutanen da suke soro ba kawai ta afka cikin gida, shima tsakar gidan a kusan cike yake da mutane, da ƙarfi ta ƙwala kiran "Umma..!!" sai kuma ta afka ɗakin Umman, Anty dake riƙe da Umma wcca ba ta san inda kanta yake ba ta ɗaga kai ta kalli Hajar, shima ɗakin Umman a cike yake da ƴan uwanta, Anty da idanunta sukay jajir ta dubi Wasilah da Hafsah tace "ku riƙeta..", Hajar kam tinda taga Ummanta a wnn halin zuciyarta ta fahimci me ya faru, ji tayi mararta ta wani mugun ɗaure tamkar zata tsinke ta fita daga jikinta, ta fasa wata ƙara har saida kunnenta ya dauɗe, lokaci guda ta sulale ƙasa idanunta suka wulƙile.....✍️ 💛 HAJAR 💛 {82..} Ana idar da sallar juma'a aka sallaci gawar Baba, abinda yasa aka jinkirta jana'izar sbd ƴan uwansa na Yola da suka roƙa a ɗaga musu ƙafa suma su samu jana'izar dan uwansu, jana'iza kamila aka yiwa Baba kuma ya samu ɗumbin mutane, daga nan aka wuce dashi gidansa na gsky, Sosai mutuwar Baba ta wujijjiga mutune musamman ma dai iyalansa, Hajar na kwance ɗakin Umma bata ma san inda kanta yake ba tin bayan da aka fitar da gawar mahaifinta, suman da tayi na farko bata farfaɗo ba saida aka yi ta yayyafa mata ruwa ana mata fifita, tini fashin watanta yaxo bayan ɗaurewar da mararta tayi don it was behind the corner, ta samu dai taga fuskar mahaifinta kafin a fita dashi, kawai Allahumma ajirni fi musibati wa aklufuli khairan minha take furtawa, don bakinta ya kama addu'ar tin a mota da yace ta ringa faɗa, addu'ar ce tasa ta ɗan ji sassauci amma hakan baisa ta dena rusa kuka ba har saida ta fita daga hayyacinta, Umma kam har aka fita da gawar Baba ba ta san inda kanta yake ba, Nabilah kam wni lungu ta shige ta ringa kukan rashin mahaifinta kamar ranta zai fita, gaba ɗaya ta tsani ganin Maama da Maimuna da ita kanta Sa'adatu don gani take su suka kashe Baba, shiyasa ma taƙi zama a ɗakin Maama don bata son ganinsu, wajen ƙarfe biyu ana cikin jimamin mutuwa sai ga Balaraba ta shigo da wasu mata police biye da ita, fuskar nan ta Balaraba ta suntuma suntum kamar an buga mata iska da ƙatuwar bandage a goshi, idonta ɗaya saida ya nutse tsabar yacca fuskarta ta kumbura, tini Balaraba ta ringa kallon mutanen dake tsakar gida tana neman Maama, da bata ganta ba ta wuce ɗakinta da police women din biye da ita, ɗakin Maaman bbu wasu mutane sosai don ba tada wasu shaƙiƙan ƴan uwa duk karume karume ne, Balaraba ta kyallaro idonta da ya nutse ciki ta kalli Maama wcca tayi wni wujiga wujiga don sosai mutuwar Baba ta taɓata, shekaru talatin da wni abu sune tare da bawan Allahn nan, Balaraba tayi nuni da Maama tace "gata can..", ɗaya daga cikin ƴan sandan tace "Baiwar Allah zamu tafi dake can police station sbd muna tuhumarki da ƙoƙarin kisan kai", wata daga cikin karumen ƴan uwan Maama mai suna Jummai tace "ku kam ba ku san gidan mutuwa ba, baiwar Allahn nan fa mijinta ne ya rasu ko dawowa daga kaisa...", ƴar sandar ta ɗaga mata hannu tace "mu hukuma kawai aikinmu muke, an bamu umarnin kamota daga sama dole mu wanzar da aikinmu", haka nan ƴan sandar nan suka kaɗo Maama daga ɗaki tana rusu kuka kamar ba gobe tace "Dan girman Allah karku gwadamin wnn rashin imamin, ku barni da jimamin rashin mijina mna..", Balaraba tace "Ni imamin kika gwada min da kika tsiyayarmin da ruwan ido..", kuka wiwi Maama take tana turjewa don tini ƴan sandan suka fara janta, gashi jama'a bbu wnda yace uffan kawai kallon Maama suke suna taɓe baki, toh daman wa zai ce wni abun halinta ne yaja mata, gashi bata zauna lfy da maƙota ba bare su dubeta, da kyar Maimuna ta rarrafo daga ɗaki ta maƙale jikin ƙofa, ilahirin jikinta shatin belt ne da Huzaifa ya lakaɗa mata duka, ga kuma cikinta dake azabar ciwo kamar zai tsinke, lokaci zuwa lokaci kuma tana yin bleeding kuma shima tin jiya, Sa'adatu ma maƙalewa tayi daga jikin window tana kallon yadda ake jan Maama sai kace Akuya, Balaraba na cewa "Ni kaɗai nasan irin nakasta ni da kika yi, saida na zubar da jini yafi gwangwani huɗu ga uban ɗinkin da akay min ruɓi shida a goshi..", haka nan ƴan sandar suka tisa ƙeyar Maama daga gidan tana kuka Wiwi, hijabinta ya wani waskace ya koma gefen kunne sai haɗa gumi take tamkar tsohuwar kuturwa, Maama ta haɗa hannayenta tana kallon Balaraba tace "ki duba irin halin da nake ciki Balaraba kar kisa a kaini chaji Ofis da ɗanyen mutuwar mijina..", Balaraba ta taɓe baki ta kalli yan sandan tace "Ofisa ku kaɗata du Allah" don so take a kai Maama police station a sakata a cell, kuɗi sosai Balaraba ta biya domin a zane Maama idan an kaita cell. Sai yamma liƙis snn Naseer yayo bailing Maama, ko da yaje police station din sai ya tarar sun jibgi Maama sai kace jaka, da yayi mgana akan dukan sai suka ce ai gardama ta musu, saida Naseer ya biya dubu ashirin don Balaraba cewa tayi sai an bata kuɗin da ta kashe na magani, Balaraba dadi har cikin ranta don ta sami kuɗin da zata biya bashin da ta ciyo ta bawa ƴan sanda don su nakaɗawa Maama duka, ranta washar tinda an jibgi Maama. Sai a washe gari snn Umma ta fara watsakewa, ynxu kam har tana iya amsa gaisuwar wnda suka zo mata ta'aziyya ba kamar jiya ba, Hajar ta ɗan samu kuzari amma ba wni sosai ba, bata iya jimawa a zaune saita kwanta, manyan idanunta duk sun ƙanƙance kuma still bata dena kuka ba, gsky ta amshi tsumangiyar mutuwar mahaifinta, da yammacin ranar saiga Mami tare da Sakeena, a ɗakin Umma Anty ta saukesu, bayan sun gaisa da Umma suka mata ta'aziyya, Hajar dake zaune ɗakin ta gaida Mami, Mami ta amsa with care snn ta mata ta'aziyyar mahaifinta, Hajar suka gaisa da Sakeena snn ta mata ya dadin haƙuri, sosai Sakeeena taji wni mugun tausayin Umma da Hajar don saura ƙiris kukan da take dannewa ya taho mata, bayan wni lokaci Sakeena ta dubi Mami tace "Mami su shigo ynxu..?", Mami na kallon Anty da ta kawo musu ruwa ta zauna gefen Umma bayan sun gaisa tace "Za'a shigo a muku gaisuwa", After few minutes Nurain ya shigo shi da Farooq, suna gaisawa dasu Umma snn suka musu ta'aziyya, Farooq ya dubi Hajar ya mata gaisuwa, ta amsa kanta a ƙasa don ita ko gaisuwar ma aka mta sai ta fara kuka, ynxun ma dai kukan ne ya taho, Nurain ya sauke numfashi yana kallonta da wutsiyar ido, gaba ɗaya jiya bai samu ya ganta ba don tinda akai jana'iza suka wuce gida tare da Abba, da yamma ma dai da ya dawo bai samu ya ganta ba har ya tafi after magrib, gashi wayarta na wajensa though yasan ma ko tana wajenta bazata ɗauka ba, Farooq ne ya fara tashi snn Nurain ya bisa suka fita, su Mami basu wni jima ba suka tashi zasu wuce, Umma tace "Toh mun gode sosai..", Mami tace "Allah ya kara muku hƙuri shi kuma ya masa rahasa yasa can tafi nan..", Umma tace "Ameen..", Sakeena ta matsa kusa da Hajar tana mata mgana a hankali, kawai gyaɗa kai Hajar take tana share hawayen dake zuba cheeks dinta, Umma ta ringa kallonsu hakama Anty, Sakeena ta saki hannun Hajar da ta riƙe tace "sai munxo gobe dear... Allah ya ƙara haƙuri..", Hajar ta gyaɗa kai sai kuma ta miƙe, Mami tace "yi zamanki daughter kinji..", Hajar ta saukar da kanta ta koma ta zauna, zaune kan tabarma su Mami suka tarar da Nurain da Farooq a soro, Farooq yabi bayan Mami da har ta fita, Nurain ya rage murya yana biye da Sakeena yace "Sister please how is she...?", Sakeena ta juyo ta kallesa tace "Toh partially..", ya sauke numfashi ya ciro wayarta da yake ta yawo da ita a pocket ya miƙawa Sakeena yace "please ki bata kafin mu wuce..", Sakeena ta amshi wayar ta juya ta koma cikin gida, bbu jimawa ta fito bayan ta kaiwa Hajar wayar. Da daddare wajen ƙarfe takwas Anty ta shigo ɗakin Umma, direct gado ta nufa inda Hajar ta duƙunƙune waje ɗaya, tapping dinta Anty tayi don tasan ba bacci take ba, Hajar ta miƙe zaune sai kuma ta kai hannu ta goge hawayen cheeks dinta, Anty ta girgiza kai tace "kinci Abincin kuwa Hajar...?", Hajar ta gyaɗa kai tace "Na ci", Anty ta duƙa ta bude plate din abincin sai kuma ta ɗago ta dubi Hajar, Hajar ta saukar da kanta ba tace komai ba, Anty ta sauke ajiyar zuciya tace "tinda kin ƙi cin wnn toh me zaki ci..?", Hajar tace "na ƙoshi ne..", Anty ta ɗan haɗe gira tace "A'a wne irin kin ƙoshi Hajar, na kawo miki kunun gyaɗa da Umma ta rage...?", Hajar ta saukar da kanta sai kuma tace "Toh..", Anty tace "yauwa bari na kawo miki tare da maganinki..", Anty na fita Hajar ta juya tana kallon wayarta da ta fara ringing, da fitilar wayar ta haska ɗakin don bbu Nepa, gashi kuma ana zafi shiyasa duk su Umma suka fita tsakar gida sai ita kaɗaice a ɗakin, tana ɗaukar wayar kiran ya katse, bbu jimawa wni kiran ya sake shigowa, a hankali tayi picking ta kara a kunne, da dasasshiyar muryanta tayi sallama, Nurain ya lumshe idonsa don he can feel the bitterness in her voice da sanyin murya yace "Baby wife...", ta saukar da kanta ta amsa a hankali, yace "please can you come out..?", ta gyaɗa kai a hankali sai kuma ta ajiye wayar bayan ta katse, saukowa tayi dga gadon ta gyara hijab dinta, Anty ta shigo da cup din kunu ganinta a tsaye tace "Ina zaki...?", Hajar tace "shine yaxo..", Anty tace "Ohk.. idan kin dawo sai kisha kunun kinji...", gyaɗa kai Hajar tayi walking slowly ta fita tsakar gida, ta duƙa gaban Umma da ke zaune kan tabarma, ga Sabrah kusa da ita tayi bacci, ta gayawa Umma zata fita ƙofar gida, Umma ta jinjina kai a takaice, Hajar ta tashi ta nufi soro tana tafiya a hankali, bbu kowa a soron don tin bayan sallar magrib masu zama a nan din suke watsewa, su Naseer kuma ta gansu a cikin gida, ta saukar da kanta ta shiga soron da ya gama cika da pure scent dinsa, Nurain dake riƙe da wayarsa ya haska soron ya ringa kallonta without blinking, ta ɗan tsaya nesa dashi, with cracking voice tace "Ina yini...", ya juya ya kalli waje sai kuma ya ƙarewa soron kallo, lokaci guda ya janyo hannunta ta tafi gaba ɗayanta ta faɗa jikinsa, a hankali ya shiga patting bayanta yace "Ya haƙuri Baby wife..", ta kwantar da kanta hawaye na zarya cheeks dinta, ai kam tini ta jiƙa masa gaban riga da ruwan hawaye, haka ya cigaba da consoling wife dinsa har saida ya tabbatar nauyin zuciyarta ya ragu, tana jin bbu wanda ya mata rarrashin da ya shigeta kamar na mijinta, surely ta rarrasu don more than 60 percent na raɗaɗin da take ji ya ragu, ya kai soft palm dinsa ya goge mata ragowar tears din yace "please stop crying Allah ya jiƙan Abba..", sai wajen takwas da rabi Hajar ta shiga gida da bag din kayanta da ya taho mata dasu, other hand din nata kuma ledar kayan ciye ciye ce. Washe gari akay sadakar uku tinda kwanan keso Baba yayi, wajen sha daya na safe sai ga su Mami harda Hajjaju Hajiya da Noor da kuma Umminsu Farooq da Aysha, suka zo da uban abinci kala kala na sadaka, Anty da Umma ba ƙaramin mamaki suka sha ba ganin yacca surkan Hajar suke sonta, ga Iron Lady da suka ga tana mata wni tarairaya na musamman, Umma har cikin ranta take jin daɗi da Allah ya kai ƴarta gidan da ake sonta, yoh toh so mna idan dangin miji basa yi da kai ta ina zasu ringa maka irin wnn mutuncin, bayan 20mins da zuwansu Mami Anty Zulaihah ma tazo don tasan gidan tinda tare da ita aka zo ɗaukan Hajar, Khausar dake biye da mahaifiyarta ta ringa bin gidan da kallo tana yamutse fuska, tinda taji cewa gidansu Hajar Anty Zulaihah zata zo shine tace itama zata zo, Hajar ta duƙa ta gaida Anty Zulaihah wcca ta amsa mata da sakakkiyar fuska snn ta mata ta'aziyya, Khausar dai bata ko kalli Hajar ba bare ta mata gaisuwa, Hajar na lura da yacca ta ɗauke kai da ta ganta, ita kam bata damu ba don duk wnda ya wanko ƙafa yaxo gidansu sbd mutuwar Babanta ya gama mata komai, Hajar na kallon Khausar tace "Sannu Khausar", Khausar ta ɗan kalleta tace "Ya ƙarin haƙuri, Allah ya jiƙansa..", Hajar tace "Ameen..", ko 10mins su Anty Zulaihah basu ƙara ba suka tashi zasu tafi, zuwa lokacin har Khausar ta fara fifita da handbag dinta tana yamutsa fuska, kafin sallar Azahar su Mami ma suka tafi. Da yamma lokacin jama'a sun rage tururuwar zuwa Mu'azzam ya shigo gidan, kwaraɓaɓɓen kitchen din gidan da basa amfani dashi duk ya mutu sai uban shirgi ya buɗe, girgiza kai yayi ya bar bakin kitchen din, ɗakin Baba ya buɗe ya shiga bayan wni lokaci ya fito, wajen Naseer dake tsaye bakin titi tare da Huzaifa ya wuce, Mu'azzam na kallon Naseer yace "Yaya saidai a ajiye a ɗakin Baba a ynxu dai kafin a gyara kitchen din", Naseer yace "Tom.. ku shiga dasu", tini Huzaifa da Mu'azzam suka ringa ɗaukar Foodstuffs din da suke shaƙure a ƴar ƙurƙura suna shiga gida dasu, bayan sun gama kwashe uban kayan Abincin tare da ƴan tayi Naseer ya bisu gidan shima, duba yadda suka ajiye kayan yayi snn ya rufe ɗakin Baban ya bawa Sabrah muƙullin yace ta kaiwa Umma, Maama da akan idonta aka ringa jibgi Foodstuffs din don tana tsakar gida ta dubi Naseer da wni irin yanayi bayan taga ya bawa Sabrah key yace ta kaiwa Umma, Maama tace "Nasiru..", Naseer ya dubeta a karo na farko tin shigowarsa gidan, tace "Zo nan ina son ganinka" da haka ta tashi ta shiga ɗakinta tana ɗingishi, har ynxu ƙashin cinyarta ciwo yake sbd bugun da ta sha a hannun police, Naseer da zuciyarsa take zafi don har cikin ransa ya tsani halin mahaifiyarsa, da ƙyar ya tausashi kansa ya bita ɗakin, kallo ɗaya ya yiwa Maimuna dake malelekuwa a ƙasan leda tana murƙususun ciwon ciki, Sa'adatu ta cusa wayarta da take dannawa ƙarƙashin pillow ta hau baccin ƙarya, haɗe fuska yayi don ya lura da ita, ya duƙa gaban Maama yace "Gani..", Maama ta ringa kallonsa jin yacca yayi mgnar a daƙile, ta girgiza kai tace "Nasiru na lura kai da Huzaifa da Nabilah kun ƙullaceni a cikin ranku, kar ku manta dai ni uwarku ce ko da kuwa tsince tsince nake a bola..", Naseer ya sauke numfashi yace "ba hka bane Maama..", tace "Ai ni ba mahaukaciya bace da za kace min ba hka bane Nasiru, toh ba dai a canzawa tuwo suna, idan ma gani kuke ni na kashe mahaifinku toh wllh ba ruwana, lokacinsa ne yyi snn kuma dukkanku na fiku sonsa don tare kuka ganni dashi..", shi dai Naseer yayi shiru baice komai ba, Maama ta gyaɗa kai tace "Wccan Uban kayan abincin tuli guda a ina ku ka samosa..?", yace "Abokin Baba ne ya kawo..", Maama ta micincina ido tace "Abokin Baba kuma...?, ina mal yaga Aboki mai arziƙin da zai nannago uban kayan abincin nan ya bamu..?", Naseer yace "Alhj Muktar fa", nan ma Maama ta ƙanƙance ido tace "waye hka..?", yace "Surkin Hajar", saida zuciyar Maama ta koma ciki tsabar ruɗu amma bata nuna ba ta rausayar da kai tace "ba shakka shiyasa ai ka damƙa mukulli hannun masu abincin", Naseer ya shafa kansa yace "zan koma soro kar azo ana nemana..", bai jira cewarta ba ya tashi ya fita with speed, takaici ma bazai barsa ya gaya mata sauran Alkhairyn da Abba ya musu ba, ga kuɗi masu yawa ya bayar yace su riƙe a hannunsu snn yace duk abinda ake buƙata a gidan Naseer yaje ya samesa ya gaya masa, a wnn lokacin ai da wuya a samu mutum irin Abba wnda zai waiwayi iyalan Abokinsa bayan rasuwa, kowa ta kansa yake nafsi nafsi. Hajar ta raka Zainab da tazo mata gaisuwa har soro, Hajar tace "Ngd sosai Zainab..", Zainab tayi murmushi tace "ba komai Hajar, Please karki manta ki kirani anjima sai nayi saving number dinki tinda bakya amfani da wncan..", Hajar tace "insha Allah.. ngd sosai Zainab ki gaida Ummi dan Allah..", Zainab tace "zata ji". Hajar na gida har saida akai bakwai, kullum Nurain sai yaxo to check on her, gashi kuma suna waya frequently, yau ne akay sadakar bakwai, da yamma bayan gida ya watse bbu kowa don da yawan mutane sunxo sunyi gaisuwarsu, Anty ce tare da Umma a ɗaki, tin ranar uku Anty ta tafi gidanta sai ranar biyar da ta kuma zuwa sai kuma yau bakwai da tazo, Anty tace "Yau gashi har Baba yayi kwana bakwai a ƙasa, Allah ya jiƙansa ya gafarta masa yasa aljanna ce makomarsa..", Umma da Hajar suka amsa da Ameen, Anty tace "Addah saidai wni hanzari ba gudu ba, zaman gidan nan a gsky ba naki bane ya kamata mu fara tunanin inda zaki koma, baza ki cigaba da zama da waccar matar mai zuciyar kafurai ba..", Umma ta numfasa tace "gskyr ki Jamilah, tabbas bazan cigaba da zama da Rabi ba a gidan nan, zanyi tunani akan hakan..", Anty tace "Yauwa kar ki ja tunanin nan ya daɗe don ni ko sati biyu bana so ki ƙara nan gaba wllh, wccar matar abin tsoro ce tsakani ga Allah", Umma tayi shiru ba tace komai ba, Anty tace "idan gidan Iya zaki koma toh..", Umma tayi saurin girgiza kai tace "A'a bazan koma gidan Iya ba gwara na tafi Yola kawai..", Anty ta zaro ido tace "Yola kuma Addah, wajen wa zaki a Yola..?", Umma tayi murmushi tace "haba Jamilah ya kike mgana sai kace wasu marasa dangi, wajen Gwaggo Habiba zan tafi..", Anty ta sauke ajiyar zuciya tace "haka ne Addah, wllh Gwaggo Habiba tana son mu kuma na tabbata bazata ƙi zama dake ba, lalurar da take da itace ma tasa bata zirga zirga wajen zuwa inda muke wllh", Umma tace "zan dai yi tunani Jamilah", Anty tace "Toh", tini idanun Hajar suka ciko da ruwa jin Ummanta za tayi nesa da ita, Anty ta kalli Hajar tace "ke kuma yaushe zaki koma gidanki..?", Umma tace "Ni nasha ma yau zata koma wllh..", Hajar ta saukar da kanta ba tace komai ba, Anty tace "Ya kamata dai ki tafi tinda anyi bakwai kar kuma a shiga haƙƙin aure..", Hajar bata iya cewa komai ba sai gyaɗa kai, Anty tace "Hajar na jinjina miki Allah ya miki Albarka, yadda naga dangin mijinki na tarairayarki suna ji dake nasan cewa kinyi riƙo da tarbiyyan da mahaifanki suka baki, Allah yasa ki cigaba da ɗorewa a haka kuma kar kiyi sagegeduwar da soyayyar nan da suke nuna miki zata ƙare..", Hajar tace "Insha Allah..", Daf da magrib Hajar na zaune kan kujera gaban rariya tana alwala don ynxu she's clean jiya tayi wankanta, Nabilah tazo ta ɗebi ruwa a buta ta durƙusa nan kusa da Hajar itama za tayi alwalan, Hajar dai bata ko kalli inda take ba ta cigaba da alwalanta a hankali, a hankali Nabilah tace "Hajara..", Hajar ta ɗaga kai ta kalleta sai kuma ta cigaba da alwalanta, Nabilah ta sake kiran sunanta a karo a biyu, da mamaki Hajar ta kalleta sai kuma tace "Na'am..", Nabilah da idonta ya ciko da ruwa tace "ya haƙurin mahaifinmu..", Hajar tace "Mun gode Allah..", Nabilah ta ɗanyi jimm sai kuma tace "Toh ayi haƙuri da duk wni abu da ya faru a baya, irin saɓanin da muka samu a matsayinmu na ƴan uwa, dan Allah kiyi haƙuri komai ya wuce Hajara..", Hajar tace "Ni kam a cikinku bbu wnda na riƙe a raina Nabilah, nice ƙarama acikinku amma kuka nuna bakwa sona a koda yaushe cikin kyarata kuke, snn kuka ringa haɗemin kai samm ba kwa nuna cewa ni ƴar uwarku ce..." sai kuma tayi shiru kafin tace "bazan manta ba shegiya kuke kirana duk da cewa ubanmu ɗaya, bbu damuwa komai ya wuce ni bbu wnda na riƙe a cikinku Nabilah..", Nabilah ta goge hawayen da ya zubo mata tace "haƙiƙa ba mu yiwa mahaifinmu adalci ba, ke kam bbu ruwanki sbd mu muke fara janyo duk wata fitina, duk wata matsala mu muke janyota wllh, dan Allah Hajara kiyi haƙuri mu manta da komai ko don mahaifinmu..", Hajar tace "ba komai kema kiyi haƙuri don ƙarfe ɗaya baya amo" tana gama fadin haka ta wanke ƙafarta ta tashi ta shiga ɗaki. Washe gari Umma tace da Hajar ta shirya ta tafi da wuri ido na ganin ido ba sai dare ba, haka nan Hajar ta hau shirya ƴan kayanta a jaka jiki a sanyaye, wajen sha biyu Abdallah ya kawo saƙo yace inji Anty kuma saƙon na Hajar ne, ai kam Umma bata buɗe ledar ba haka ta miƙawa mai ita, ita dai Hajar ta amshi ledar tana tunanin mene ne a ciki, Abdallah ko zama beyi ba yace zai wuce don kasuwa zai tafi Anty ta bashi saƙon ya kawo, bbu jimawa da tafiyar Abdallah kiran Anty ya shigo wayar Hajar, bayan sun gaisa Anty tace "Abdallah ya kawo miki sako ko..?", Hajar tace "Eh..", Anty tace "Ohk.. akwai paper acikin ko wanne wcca aka rubuta ydda ake amfani dashi..", Hajar tace "Toh ngd Anty" duk da bata san mene ne abinda Anty take mgana akai ba, Anty tace "Yau din zaki tafi..?", Hajar tace "Eh insha Allah da yamma..", da haka sukay sallama. Hajar ta saka hijab dinta a hankali, duƙawa tayi ta saka wayarta cikin bag din kayanta, idanunta cike taff da ruwa ta juya ta kalli Umma, da sauri ta tafi ta faɗa jikin Umma ta fashe da kuka tace "Umma dan girman Allah karki tafi Yola ki barni..", Umma ta daure tace "A'a bazan tafi ba Hajara..", Hajar ta ringa rusa kuka don mikin mutuwar ne ya wani taso mata, ynxu shknn bazata sake ganin Babanta ba, indai tazo gida bazata ga Baba ba, Mu'azzam ne ya shigo ɗakin ya tsaya yana kallonsu, sai kuma yace "kin fa bar mutum yana jira Hajar..", Hajar ta zame jikinta daga na Umma tana jan zuciya, Mu'azzam ya ɗauki jakar kayanta ya fita da ita yana cewa "ki fito hka nan..", haka nan Hajar ta fito tsakar gida da ledar kayan da Anty ta bata a hannu, Umma na biye da ita tace "Allah ya kaiku gida lfy..", Hajar ta kalli Nabilah dake zaune a ƙasa bbu ko tabarma ta zabga uban tagumi sai kace me fama da cutar depression, walking gently Hajar ta isa inda take ta duƙa gabanta tace "Nabilah..", Nabilah tayi firgigit don tayi nisa a tunanin da take, Hajar tace "Ni zan tafi sai na sake zuwa kuma..", Nabilah ta numfasa tace "Toh Allah ya kaiki gida lfy, zan amshi lambarki a wajen Umma sai mu ringa gaisawa..", Hajar ta gyaɗa kai da haka ta miƙe, hannun Umma ta riƙe tace "Umma na tafi..", Umma tace "Allah ya miki albarka Hajara ya kaiku gida lfy..", Hajar tace "Ameen Ummanmu..", Nabilah ta ringa kallonsu tana jin dama ta ta uwar ce a hka. Har bakin mota Mu'azzam ya raka sister dinsa, sai a lokacin Nurain ya amshi bag din kayan daga hannun Mu'azzam ya saka a booth, kafin ma ya gama saka jakar tini Mu'azzam ya juya ya shige lungunsu, Nurain ya zagayo side din da Hajar ta tsaya, ta ɗan kallesa sukay ido huɗu, murmushi ya sakar mata sai kuma ya kai hannu ya buɗe mata front seat, saida ta shiga ya rufe snn ya zaga driver seat ya buɗe ya shiga, ya rufe murfin motar sai kuma yayi stretching kansa sosai yace "Alhmdllh..", bai kunna motar ba ya juya yana kallonta, sosai ya lura da kumburin da idanunta sukay, ya sauki wni boyayyen ajiyar zuciya, Calmly ya kamo hannunta yace "Baby wife..", ta kallesa a takaice tace "Ina yini..", yayi pecking hannun nata yace "Ni har ynxu ba nida suna", ta saukar da kanta ba tace komai ba, ya sake pecking hannun nata na almost 10secs har saida ta ɗago ta kallesa, yace "Uhmm ba nida suna a wajen matana har ynxu..", ta kalli hannunta dake cikin nasa, yasa other hand dinsa ya riƙe haɓarta ya ɗago kanta, kallon eye balls din juna kawai suke, ya lumshe idonsa ya sake buɗasu a kanta, kashe mata ido daya yayi yace "A taimaka min da suna..", yacca ya kashe idon sai kace wni abu ne ya faɗa masa da kuma yacca yayi mganar ne ya bata dariya, bata san lokacin da wni murmushi ya kufce mata ba, ta ɗora forehead dinta kan hannunsu dake maƙale tare still tana murmushi, yaushe rabonta da wni abu wai shi murmushi, shima murmushin yayi ya ɗago kanta ya haɗe forehead dinsu waje guda yana murza hannunta yace "I like it when you smile"......✍️ 💛 HAJAR 💛 {83..} Good 4 days Nurain ya dauka yana cheering Baby wife dinsa up, sam baya barinta ta zauna jigum bare ta shiga damuwa, a kullum yana tare da ita though yana fita aikinsa amma baya daɗewa aikin 3hours kawai yake ya dawo, daga nan zai zauna da ita a gida har sai yamma snn yaje gidansu ya gaida parent dinsa, a gida yake sallar magarib da isha'i ma, bayan nan kuma sai ya ɗauketa su fita su zaga gari, hka nan suke dawowa gida da uban kayan maƙulashe da ya siya mata, kullum da Asuba kam tare suke yiwa Baba Addu'a, sosai Hajar ta sake raɗaɗin zuciyarta ya ragu saidai kuma ciwone da bazai taɓa warkewa ba a zuciyarta har itama ta koma ga mahaliccinta, Addu'a ba kama ƙafar yaro take yiwa Babanta cikin duka kamsu salawat da take gabatarwa. walking gently Hajar ta fito daga bathroom da towel ɗaure ribs dinta ta yafa wni a shoulder dinta, lulu eyes dinta ta sauke akan gadonta sai kuma tayi murmushi ganin har ynxu yana kwance a nan din bai tashi ba, tin Asuba da ya shigo nan din ya kwanta, A ɗakinsa suka kwanta itama da asuba ne ta taho nan, gashi dai har ta sauka downstairs ta kimtsa komai, har part dinsa ma ta gyara ta gama breakfast amma bai farka ba, a tunaninta kafin ta fito dga wnka zata tarar ya tashi sai kuma ta tarar bccin yke har ynxu, gaban mirror ta zauna ta shiga rubbing lotion, tana shafe shafenta tana kallon gado ta cikin mirror, da hka dai ta gama ta bar gaban mirrorn wni sassanyan ƙamshi na tashi a jikinta, a hankali ta buɗe wardrobe without making any sound ta ɗauki kayanta, tana gama saka kayan ta kalli agogo, ƙarfe tara da rabi ta gani, ta zaro ido toh ko dai yau bazai fita bane, ita dai bazata tashesa ba gsky, kallon gadon tayi lokaci guda ta isa gaban gadon, ta sauke idanunta a kan fuskarsa, kallonsa ta ringa yi without blinking, zama tayi gefen gadon a hankali ta sunkuya daidai fuskarsa tana kallonsa, wnn shine karo na farko da ta masa irin wnn kallon, dman haka mijinta yake, words can't express handsomeness of her husband, kawai ganin idonta tayi a cikin nasa, wani irin bugu zuciyarta tayi, ya subhanallah kar dai ya kamata tana kallonsa, wayyoh Allah ta shiga uku, tini ta ɗaga kanta tana inda inda, sai kuma ta ɗan kallesa, kallonta taga yanayi with his sleepy eyes, ta kalli gefe da murya ƙinƙina tace "Amm... daman.. naga.. lokaci..", murmushi yayi ya mirgino ya ɗora kansa kan cinyarta, yana kallonta da kyau yace "daman me Baby wife...?", ta ringa kallon thick eyebrows dinsa sai kuma ta girgiza kai tace "ba komai..", pink lips dinta ya kalla da tayi mganar yace "ban yarda ba", ita dai bata kalli cikin idonsa ba kawai thick eyebrows dinsa take kallo, ta girgiza kai ba tace komai ba, shiru ne ya gifta for some seconds, slowly ya riƙo hannunta ya ɗora kan forehead dinsa, ta ɗan yi tsam kamar zata janye hannun daga goshinsa sai kuma ta fasa, ya gyara kansa sosai a laps dinta yace "Toh gashi dai na kama wata yarinya tana kallona, So ynxu sai a bani suna..", juya lulu eyes dinta tayi tace "A mafarki ko..", ya tattare girarsa yace "Nope in reality mna..", ba ta san lokacin da tasa finger ta fara shafa eyebrows dinsa ba tana bin zanenta, lumshe ido yayi yana jin ydda take yawo da slim finger dinta a girarsa, after a while ya buɗe idon yana kallonta, wni abu yaji yana sukar masa zuciya ya kasa dena kallonta, ta turo baki ganin kallon da yake mata sai kuma ta rufe masa idanu da palm dinta, murmushi yayi gami da sauke ajiyar zuciya, ta turo baki still bata bude masa idanu ba tace "Ni ka dena kallona haka..", ya rutsa tsintsiyar hannun data rufe masa ido ya fara ƙoƙarin zamar da hannun nata daga idonsa, ruff ta sake rufe masa idon ta hana ya buɗe, ai kam ya haƙura da buɗe idon amma kuma bai sakar nata hannu ba yace "Ohh really, Toh ni da aka mayar dani TV fa..", murmushi tayi tace "Allah Ni karka hango muni na kamin dariya..", murmushi mai sauti yayi yace "Nope... you know there's no water in desert..", a hankali ya zamar da hannunta ya buɗe idonsa yace "right..", ta langwaɓar da kai tace "yau ba aiki naga 9 ya wuce..?", da sauri ya miƙe zaune ya kalli clock, ya sauko daga gadon yana jan rigarsa yace "Omo me yasa baki tasheni ba wife...?", ta sauka daga gadon itama tace "Toh ai bacci kake ni bazan iya tashinka ba..", room slipper dinsa ya zura ya matsa daf da ita, cheek dinta yayi patting with one hand yace "really..", ta gyaɗa kai, soft smile yayi ya ja pointed nose dinta a hankali yace "bari na shirya.." da haka ya nufi door ya fita, Hajar tayi ajiyar zuciya sai kuma ta saka nata room slipper din da ya siya musu jiya irin ɗaya ta fita, downstairs ta sauka ta shiga kitchen, breakfast din da ta dafa ta fiddo dinning tayi setting table, palour ta dawo ta zauna kan Sofa tana jiran fitowarsa, after 10mins ta kalli stairs sai kuma ta tashi ta haura upstairs, ɓangarensa ta shiga da sallama, direct ta nufi bedroom ta buɗe ta shiga, tsaye ta gansa gaban mirror yana ƙoƙarin saka maɓallin riga, ta saukar da kanta ta matsa inda yake, dakatawa yayi da saka maɓallin ya juya yana kallonta, tayi murmushi ta matsa daf dashi, sosai tayi ɗage don ya kere mata a tsaho ta kai hannu ta ɓalle masa maɓallin, ta ɗauki Links dake kan mirror ta saka masa shima, tana ɗaga kanta taga kallonta yake, ta waro ido tace "Za fa kayi letti..", ya sunkuyo yayi pecking lips dinta lightly yace "Thank you", tare suka sauko downstairs tana riƙe da briefcase dinsa, duk da tasan sauri yake amma haka ta jasa dinning tace sai yaci abinci zai fita, tini tayi serving dinsa golden yam da offals pepper soup da ta dafa as breakfast, sharp sharp yaci fiye da rabin abincin, a kullum daɗin abincin matarsa ƙaruwa yake, har balcony ta rakasa tana riƙe da briefcase dinsa bayan ya gama, da haka ya wuce parking space bayan yayi pecking both cheeks dinta, Hajar ta juya ta koma ciki, ragowar abincin da ya rage a plate ta ɗauka ta kara kaɗan a kai taci, tea ma a mug dinsa ta haɗa tasha, bayan ta gama tayi clearing tables din ta haura sama tinda ta gama gyara gidanta tin sassafe, wayarta ta ɗauka tayi dialing numbern Umma, daman kullum ne saita kira Ummanta take samun sa'ida, suna gama waya da Umma ta kira Anty ma suka gaisa, saida suka gama waya da Anty ta tuna da abinda ta bata, ita bata san mene ne ba shiyasa bata basa wni muhimmanci ba, tashi tayi ta dauko ledar inda ta ajiyeta, ɗaya bayan ɗaya ta ringa duba robobin da suke dauke da wasu gari sai kace herbs, wni tunani ne yaxo mata, ko dai maganin ciwon mara ne Anty ta bata tinda taga azabar da tke sha, wnn tunanin yasa ta wuce kitchen da ledar tarkacen, bbu wnda bata ɗiba ta sha ba, wni soaking ake a ruwan zafi snn a sha wni kuma a zuba a madara, har wnda ta ajiye a fridge da yake liquid ne ta buɗe tasha, ita dai fatanta ciwon marar nan ya lafa mata, kafin ma ta bar kitchen din taji canji a jikinta don ba ƙaramin gabje gabje ta yiwa kanta ba, she don't care don ita gani take ai wni maganin sai anji zafi yake aiki, upstairs ta koma ta shiga ɗakinta ta kwanta kan gado don bacci take ji tinda bata koma ba tin Asuba. ★Ruqayyah ce ƙarshen fitowa bayan sun gama surgery din wajen ƙarfe biyu da rabi, slowly take tafiya tana kallon soft Clog shoe din ƙafarta, tasan cewa wnn shine last surgery da za tayi tare da Dr Uthman inba wni ƙudiran na Allah ba, Scalpel din hannunta ta kalla sai kuma tayi murmushi, slowly ta nufi washroom ta wanke hannunta da liquid soap, snn shima Scalpel din ta wankesa, wnn shine kaɗai memory din da zata bari nasa, wnn Scalpel din shi zata ringa gani ta tuna da abinda ya mata muguwar zarra a rayuwa, abinda a da nata ne amma tayi fatali dashi sbd rashin Sa'a, surgeon gown din jikinta ta cire ta zura Scalpel din cikin Scrub dinta, da haka ta nufi Nurse station, Nurse Jiddah ta tarar a station din tana rubutu jikin record book, Nurse Jiddah tace "kun fito daga surgery din..?", Ruqayyah tace "Neh..", Nurse Jiddah ta gyaɗa kai tace "how was it..?", Ruqayyah tace "Alhmdllh it was successful, you know Dr Uthman work..", Nurse Jiddah tace "Alhmdllh", Ruqayyah ta shiga wni room nasu na female Nurses da suke amfani dashi, bayan kamar 10mins ta fito ta saka black Abaya saman Scrub dinta da handbag a hannunta, Nurse Jiddah ta ɗaga kai ta kalleta tace "Are you leaving Rukky..?", Ruqayyah ta ja kujera ta zauna tace "Neh..", Nurse Jiddah tace "Ohk ai ya kamata ki huta gsky..", Ruqayyah tayi jimm sai kuma tace "Jiddah please can you move to our team..?", Nurse Jiddah tace "Laa toh bayan ga ki me zanyi a team din...", Ruqayyah tace "Am transferring from here, am leaving this hospital..", with weird facial expression Jiddah tace "Transfer..?", Ruqayyah tace "Eh kinga daga yau ma bazan sake zuwa ba, tin ranar Monday ma ya kamata na dena zuwa amma na ƙara lokaci..", Nurse Jiddah ta ajiye pen din hannunta tace "But why Ruqayyah..?, Salary dinki fa mai tsoka ne anan Asibitin..", Ruqayyah tayi ajiyar zuciya tace "Na sani Jiddah, muddun na cigaba da zama a asibitin nan toh ba zanyi moving on ba, zan ta zama ne wayaƙifa ba wni cigaba, barin asibitin nan shine salamata Jiddah", Nurse Jiddah dai duk jikinta yayi sanyi amma bata tmbayi Ruqayyah dalilinta na barin aikin ba, may be tanada wni personal issue ne daya danganci aiki a asibitin, haka dai ta yiwa Ruqayyah fatan Alkhairy jikinta duk a sanyaye, sunyi zaman lafiya da Ruqayyah wllh don batada wata matsala ko baƙin hali, ko irin gulmar nan ta asibiti da Nurses ke yi ita Ruqayyah ba ruwanta, gata da mutunci bata taɓa jin anyi faɗa da ita ba, snn kuma patients basu taɓa complain da ita ba duba da yadda Nurses suke zuba rashin mutunci a asibiti sai kace na ubansu, Ruqayyah tace "ngd sosai Jiddah insha Allah zamu cigaba da zumuncinmu..", Jiddah tace "Insha Allah kuwa..", Ruqayyah tace "Toh ya kin amshi position din nawa..?", Jiddah tace "Toh waye zai ƙi shiga surgery team din Dr Uthman, it's my pleasure wllh", Ruqayyah tayi murmushi don sosai taji daɗi da Jiddah ta amshi position dinta. saida Ruqayyah tabi duk colleagues dinta that were around a lokacin ta musu sallama, walking gently ta nufi office din last person da zata yiwa sallama, cike da nutsuwa ta shiga office din, ta dakata suka gaisa da Haleema, Ruqayyah tace "Dr yana ciki..?", Haleema tace "yeah..", da haka Ruqayyah ta nufi door din office din ta buɗe ta shiga da sallama, Nurain dake tsaye gaban table yana packing kayansa don gida zai wuce ya amsa sallamar ba tare da ya juya ba, daga bakin door Ruqayyah ta tsaya tace "Are you leaving Dr..?", yace "Yeah A Nurse is there any problem..?", ta girgiza kai tace "Not at All.. kawai dai zan maka sallama ne sbd na bar aiki a asibitin nan nayi transfer zuwa wni..", ya ɗan tattare thick eyebrows dinsa sai kuma ya juya yana kallonta da kyau yace "Why..?", ta saukar da kanta trying very hard not to burst into cry tace "Dr in other to move on i have to leave this hospital", ya ɗan kalleta na few seconds kafin yace "Ohk.. wish you best of luck A Nurse..", tace "Thank you Dr.." da haka ta juya har zata buɗe ƙofar ta fita sai kuma ta dawo tace "B Nurse, i mean Nurse Jiddah will take my position..", ya gyaɗa kai yace "Alright she is not bad..", tace "Sure Goodluck.." tana gama faɗin haka ta buɗe ƙofar ta fita, wata ball ce ta tsaya mata a throat kawai taji tears a cheeks dinta, da sauri tasa hannun ta goge, walking slowly ta bar wajen ta kama hanyar fita daga department din, Khaleel ta hango sai zabga sauri yake da file a hannunsa ya nufi hanyar wards, ta dan ɗaga murya ta kirasa, dakatawa yayi har ta iso inda yake tace "Saurin me kake..?", yace "Ohh kamar fa naji ana kiran Code blue ne..", ta ɗan yi murmushi tace "i think you need hearing aids fa..", ya shafa kunnensa yace "Koh.. ba wni Code blue da aka kira knn..?", ta gyaɗa kai tace "yeah kunnenka ne gsky..", ya sake shafa kunnensa yace "Dole a nemo hearing aids..", tace "Toh nidae da haka da hka sai nace sai wataran...", ya gyara tsayuwarsa yace "Department aka canza miki ne..?", ta girgiza kai tace "Ko ɗaya na bar aiki a hospital din nan ne..", shima dai kamar sauran bai ji daɗi ba, yace "What about our team..?", tace "B Nurse ta cike spot dina". Da yamma Ruqayyah ta shiga room din Momy, Ruqayyah na kallon Momy dake neman abu drawer din bedside tace "Momy me za'a dafa for dinner..?", Momy tace "Tuwon semo koh..?", Ruqayyah tace "Sai ayi Okra soup cause Daddy yafi sonta", Momy tace "Okay..", har Ruqayyah ta kai bakin ƙofa Momy tace "Amma are comfortable da canjin wajen aikin nan Ruqayyah daga Federal zuwa State..?", Ruqayyah tace "Ba komai Momy banbancin fa kaɗan ne shima wajen salery ne kuma kinga wnn hospital din da aka dawo dani yafi kusa da gida, few minutes ride naje bbu nisa..", Momy tace "Okay fine", Ruqayyah ta juya ta fita. ★Da daddare wajen ƙarfe goma Nurain na zaune palourn ɓangarensa da bowl din fruit salad da Hajar ta haɗa masa yana sha, kallon door yayi a wajen karo na uku, daga bari taje ta dawo shine har ynxu shiru almost 30mins da fitarta, ajiye bowl din fruit salad din yayi ya tashi ya nufi door ya fita, direct room dinta ya buɗe ya shiga, he automatically get froze ya kasa ƙarasa shiga, kawai kallon freshness of her body yake hancinsa na shaƙar ni'imtaccen ƙamshin da yake tashi a room din, Hajar dake zaune kan stool gaban mirror ta saukar da kanta ta cigaba da shafa manta, Nurain ya sauke ajiyar zuciya yana kallon duk inda ya bayyana a jikinta, ita dai tinda sukay ido huɗu ta ɗauke kanta, scratching kansa yayi sai kuma ya ɗauke idonsa dga kanta yace "Am waiting for you Baby wife..", ta ɗan kallesa tace "Toh", juyawa yayi ya bar wajen zuciyarsa na racing, yau fa 11days knn rabonsa da matarsa, he miss her over wllh, zaune yayi palour yayi resting da Sofa snn ya lumshe idonsa, fruit salad din ma ya haƙura da sha, shi a ynxu baya son komai sai Baby wife dinsa, after like 10mins ta shigo, saukar da kanta tayi ta ƙarasa shigowa ciki, can edge din kujerar da ya zauna ta zauna itama, ya bita da kallo cause rigar baccin da ta saka ƴar ɓingila ce, bowl din fruit salad din ya ɗauka ya matsa kusa da ita yace "want some..?", ta kalli bowl din ganin bai sha da yawa ba tace "baka sha ba... ko wnn bai maka daɗi ba..?", ya tattare gira yace "Wollah ba fruit salad nke so ba", ta waro ido tace "Toh me kake so naje na dafa mka..?", sosai ya matsa kusa da ita har jikinsu na gogar na juna, bai san lokacin da ya lumshe ido yana kallon wuyanta ba, Calmly yace "I need you wife..", turo baki tayi tana ƙoƙarin matsawa ya sauke mata wni chilled kiss a wuya, tini taji wni shock ya ratsa mata jiki tayi ajiyar zuciya, bata gama daidaita ba ya sake manna mata wni yana fesa mata numfashinsa a wuya wnda shima yke sake sakata shiga yanayin da bata shirya masa ba, muryarta na rawa tace "ka bari dan Allah..", ya ɗago kansa yana kallon fuskarta sai kuma ya amshe bowl din hannunta ya ɗora kan Centre table, yace "Okay fine.. gsky ina jin bazan ƙarasa baki labarin jiya ba..", ta langwaɓar da kai da muryar shagwaɓa tace "please ka ƙarasa min..", ya maƙe shoulder yace "Naƙi din" da haka ya tashi ya nufi bedroom, murmushi tayi sai kuma ta tashi ta bisa bedroom din, zaune ta gansa kan makeken gadonsa ya jingina da allon gadon yana latsa wayarsa, walking slowly ta isa gefen gadon ta zauna, ya ɗan kalleta sai kuma ya cigaba da latsa wayarsa, after a while bbu wnda yace uffan a cikinsu, ita dai tini sanyi ya fara ratsata, bata jurar zama a room din ba tare da ta lulluɓe ba, rubbing damtsenta ta ringa yi tana zuƙar baki, ya ɗan kalleta yayi slight smirk, tashi tayi daga gadon da nufi komawa room dinta, tini ya riƙo hannunta ya fixgota jikinsa, ai kam tini ta lafe ta kuma shige masa, yace "i can give you warm Baby wife..", ta lumshe idonta perceiving his scent, zamar da hular kanta yayi snn ya fara shafa soft hair dinta a hankali, ya kashe wayar ya ajiye kan bedside, lips dinsa ya kai saitin kunnenta ya raɗa mata wni abu, ɓoye fuskarta tayi a ƙirjinsa tace "Allah bana so..", yace "Ni ina so..", ta maƙe shoulder ba tace komai ba, yace "Okay only this.." da haka ya ɗago kanta ya fara kissing dinta slowly, he kissed her for almost 2mins, ta masa lamo bata hanasa ba duk da electric shock din da yake shigarta, ya haɗe forehead dinsa da nata yana ajiye numfashi, itama numfashin take ajiyewa a hankali, tini ya mirginata ta koma ƙasansa ya shiga kissing neck dinta, jin bata hanasa ba tayi masa lamo ya ɗago ya dubeta, sosai ya fahimci tana amsar saƙonsa ne, ya goga karan hancinsa a nata in a whisper yace "May I..?", a hankali ta gyaɗa kai sai kuma ta runtse idonta, saida taga yayi nisa snn tace "please off the lights..", da muryarsa da ta canza yace "No i wanna see my properties...", tace "Ni A'a..", ganin idan bai kashe fitilar ba zata masa gardama kawai ya danna control din lights din dake daf da gadon ya bar dim, lips dinta ya haɗe da nasa, lokaci guda ta zagaye wuyansa da dukka hannayenta ta mayar masa da martani a hankali, Uhmm At that night saida Nurain ya zagaye The Nine planets, ba karamin susucewa da zaucewa yayi ba, shima bai barta ba saida ya kaita har Pluto bayan ya zaga da ita sauran Planets din, bbu kalan sunan da bai kirata ba har dasu Empress, kyautar da ta sha kam ba a cewa komai don kaff arzikin duniyar ya mallaka mata. washe gari samm ta kasa haɗa ido dashi don wata masifaffiyar kunyarsa take ji, ga last night dinsu ya kasa barin brain dinta, memories din fresh suke dawo mata kwanya, bayan sunyi sallar asuba tare don yau a gida yayi sallahn sbd yana ma Alwala aka kabbara sallah a mosque, shiyasa yayi tare da matarsa a gida, yau kam gaisuwar ma juya masa baya akayi, shi dai sai blushing yke yana binta da kallo, gado suka koma suka kwanta, har yayi bacci ita kam ta kasa komawa, a hankali ta buɗe idonta taga fuskarsa daff da ta ta hakan yasa ta kafesa da idanu, After a while tayi murmushi sai kuma ta zame daga jikinsa a hankali, ta sauka daga gadon ta nufi door walking slowly, room dinta ta wuce ta faɗa kan gado, daga ita har shi saida Ni Feenerh feeche na yankar musu ticket a dawanau don na kasa gane wane irin murmushi suke tin wayeyar gari. ƙarfe takwas da rabi ta gama gyara gidan har breakfast ma tayi, room dinta ta dawo ta shiga wanka, bayan ta fito daga wankan tayi shafe shafenta, wardrobe ta buɗe ta ɗakko kayanta ta saka, gaban mirror ta koma ta yiwa gashinta boy and girl, da haka ta feshe jikinta da perfumes tana kallon yacca armless gown din ta mata a jiki, soft room slipper dinta ta zura ta fita, saida ta dubi door din ɓangarensa snn ta sauka downstairs, kitchen ta shiga after few minutes ta fito, tsaye tayi tana kallon stairs jin footsteps, saura stairs biyu ya kawo ƙasa ya dakata yana kallonta, ta riƙe ƙugu da hannu ɗaya ta langwaɓar da kai tace "Good morning My husband..." sai kuma ta sakar masa wani murmushi mai kyau, step ɗaya ya ƙara ya sauko, tsabar mamaki ya kasa cewa komai, Anya ba kunnensa ne yaji ba daidai ba, buɗe mata hannaye yayi alamar ta taho, ai kam da sauri ta isa inda yake tayi ɗage ta zagaye wuyansa tana murmushi, ƙugunta ya rutsa yayi hugging dinta sosai, lumshe idonsa yayi ya fara ɗan juyi dasu yace "please say it again Baby wife..", ta sake ƙanƙamesa snn tace "My husband..", tamke riƙon da yayi mata yayi tamkar zai ɓallata, lokaci guda ya rabata da ƙasa yana dariyar da bata taɓa jin yayi irinta ba......✍️ 💛 HAJAR 💛 {84..} After a while ya direta ya ringa kallonta without blinking, har lokacin murmushi ne kwance fuskarta, ya tallaɓi both cheeks dinta snn ya matso yayi pecking forehead dinta, lumshe idonta tayi a hankali ta ɗora hannunta kan nasa da ya tallaɓi cheeks dinta, slowly ya janye lips dinsa yana kallon eye ball dinta yace "Morning Sweet pie, how was your night..?", tace "fine alhmdllh..", yana patting cheeks dinta yace "Good..", da haka ta saki hannunsa da ta riƙe ta janye fuskarta ta juya ta shiga kitchen, bayanta yabi shima ya shiga kitchen din, Hajar ta juyo jin motsi a bayanta, ya ɗage gira yace "you need any help...?", ta waro ido sai kuma tayi ƴar dariya tace "No..", warmers biyu ta dauka akan Island ta nufi door, tana zuwa kusa dashi ya amshi guda ɗaya, tare suka kai warmers din dining, kitchen ta sake komawa zata dauko ragowar warmer din da plate da cup, footsteps taji a bayanta, ta ɗan juya ai kam taga shine biye da ita, tayi murmushi tace "why are you following me.?", yace "Cause you are my heart beat, I can't live without you..", ta ɗan kallesa sai kuma ta saukar da kanta ba tace komai ba, plates da cups ta miƙa masa ita kuma ta ɗauki warmer, da haka suke sake fita daga kitchen din zuwa dining, Chair ta ja masa tace "Sit", tini tayi serving dinsa abinda ta dafa snn ta haɗa masa tea, tana gamawa dashi ta ɗauki wni plate din ta zubawa kanta, duk abinda take yana kallonta kuma bai fara cin abincin ba, Chair din dake kusa dashi ta ja ta zauna, ta kai hannu zata ɗauki plate din abincin da ta zubawa kanta yayi sauri ya janye ya ɗaga plate din ya juye abincin cikin nasa, ta ringa kallonsa without saying anything, ya tura plate din tsakiyarsu yace "Eat alot..", ta dauki fork tana juyasa a hannunta tace "you too" da haka ta fara ɗeban abincin tana kaiwa baki, time to time suke haɗa ido su sakarwa juna murmushi, ita ta fara gamawa ta dauki shayinta tana sipping, tass ya cinye ya ture plate din yana hamdala, tashi yayi yace "let's me make A call upstairs..", ta gyaɗa kai tace "Ohk", yana haurawa sama ta tashi tayi clearing table din, gaban sink ta tsaya ta wanke duk kwanukan da suka ɓata, da haka ta haura upstairs itama, direct ɓangarensa ta wuce, bata tarar da shi a palour ba don haka ta nufi bedroom, shima nan din ba ta gansa ba, door din balcony ta gani a buɗe ai kam ta nufi wajen, tana leƙa balconyn ta gansa with Airpod still making a call, ya mata alama da hannu, ta girgiza kai ta dawo cikin ɗakin, dman nan ne kawai bata gyara ba don hka ta fara ɗame gado, kawai jinta tayi a kan iska an ɗagata sama, tayi ƴar ƙara tace "please let me down..", kan mirror ya ajiyeta ya tsaya daf da ita yace "yah... ba kya gajiya da aiki", ƙoƙarin sauka tayi daga kan mirrorn ya hanata, ta turo baki tayi pointing clock tace "Kaga..", ya kalli agogon sai kuma ya juyo yana kallonta yace "Mene..?", tace "ba kaga time ba ko yau ba aiki..?", ya ɗage shoulder yace "Nope bbu aiki a waje amma akwai a gida..?", ta ɗan juya lulu eyes dinta tace "Aikin mene a gidan..?", ya kwantar da kansa a chest dinta yace "you wanna me to show you..?", ta gyaɗa kai ba tace komai ba don sosai ta zama uncomfortable, After few seconds ya ɗago kansa ya ringa kallonta, itama kallon nasa take don haka tini idanunsu suka sarƙe staring at each other, ba tasan lokacin da ta kai hannu ba ta shafa thick eyebrows dinsa tare da kwantaccen sajensa ba, lumshe ido yayi snn ya sake buɗasu a kanta, tana shirin janye hannunta daga fuskarsa ya riƙe hannun ya cigaba da yawo dashi a fuskarsa da kansa, da haka ya kai hannun nata lips dinsa yayi pecking a hankali, ya sauke ajiyar zuciya yace "Am all yours wifey... and you're mine too..", ta saukar da kanta tana jin yadda zuciyarta ke racing, ya ɗago kanta da ta saukar lokaci guda ya kai babban ɗan yatsansa lips dinta ya fara shafawa a hankali, tana ganin ya fara kusanto da fuskarsa ga ta ta tayi sauri ta lumshe idonta, slowly lips dinsa yayi landing akan nata, gently ya fara kissing dinta kafin ya zama passionate, ta sake rutse idonta ta damƙe rigarsa da hannun bibbiyu, lokaci guda ta sauko daga kan mirrorn kafin ta shiga mayar masa da martani, tini ya dafe kan mirrorn don ji yayi kamar zai zube a wajen, habawa ai tini kiss ya koma french, after almost a minute ya haɗe forehead dinsu waje ɗaya yana ajiye numfashi, ita kam wni murmushi ne kwance fuskarta, ya ɗago ya kalli cikin eye balls dinta yace "I Love you", kawai kallonsa take tana jin kamar an saka zuciyarta a gidan ƙanƙara, ya tallaɓi cheeks dinta yace "I Love you so much my wife..", ɗage tayi snn ta fada jikinsa tana murmushi. A cikin sati huɗu da suka shuɗe wata narkakkiyar soyayya wcca ta amsa sunan ƙauna suke gwadawa junansu, yoh toh ƙauna mna don ta wuce a kirata da soyayya, within that period Hajar ta fahimci mijinta sosai tasan me yake so da kuma wnda baya so, ta lura cewa he is a simple person ba shi da da damuwa, ashe da don bata fahimcesa bane shiyasa take ganinsa rude, A fanin Nurain kam ynxu yasan cewa Hajar was more than his choice and type, tayi fice snn kuma tayi zarra a ycca yke son matarsa ta kasance, she's so good in every aspect, wajen Abincin kam ba'a cewa komai don she can cook varieties, ga kuma tsafta da take da ita ba'a cewa komai, snn kuma ga ƙoƙari wajen kula da bedroom things, a kullum kuma sai yaji taste din da bai taɓa ji ba shiyasa he can't get enough of her, kullum cikin sabon sauƙinta yake sai kace sabon Ango, yoh ko sabon Angon bazai nuna masa farin ciki ba. A tare suke saukowa daga stairs suna dariya, Hajar dake riƙe da briefcase dinsa ta waiga ta ɗan hararesa tace "you are teasing me...", ya ɗage gira yace "should I show you..", ya matso zai kamota, da gudu ta zille ta ƙarasa sauka daga stairs din tana dariya tace "Don't..", ya ƙarasa saukowa shima yace "please Baby wife be careful, kinga our little love beyi kwari ba...", dariya tayi har dasu riƙe ciki tace "Stop dreaming fa... ba wani little love", ya haɗe gira yace "ke wa ya gaya miki bbu..?", ta langwaɓar da kai tace "kai wa gaya maka akwai..?", waro ido yayi sai kuma ya nuna kansa yace "Am A Doctor you know..", tayi murmushi tace "Fake Dr ba" da haka ta juya ta buɗe ƙofa ta fita balcony, bayanta yabi ya fita balconyn shima yace "ba zaki dena denying ba..", collar din rigarsa ta gyara masa tace "Am not denying", ta matsa daf dashi ta saukar da kanta, slowly ya sunkuyo yayi pecking forehead dinta, da haka ta miƙa masa briefcase din tace "Allah ya tsare My Moon..", yace "Ameen Baby girl", har ya juya zai tafi tace "Amm Moon..", ya dakata, ta ƙarasa inda yake tace "Na manta ban gaya mka zan shiga nan neighbor house na yiwa matar gidan barka ba..", yace "Ohk Okay..", tayi murmushi tace "A dawo lfy". Wajen ƙarfe sha ɗaya na safe Hajar ta shirya zata shiga ta yiwa makwabciyar ta ta data haihu barka, 3 week da suka wuce ne ta samu ta shiga makwabtan nata suka gaisa, Ashe ma sun sha zuwa zasu shigo sai ace musu matar gidan bata nan, wataran kuma da suka zo ko mai gadi basu tarar ba, da suka gaya mata lokacin sai taga ai lokacin bikin Noor ne da kuma lokacin da suka tafi Abuja, daman tin farkon kawota abinda yasa taƙi shiga makwabta sbd gani take gidan ba wajen zamanta bane don haka mene na shiga neighbors, ynxu kam mene zai rabata da mijinta ai saidai mutuwa, Hajar na isa gate mai gadi ya buɗe mata door bayan ya gaisheta ta amsa, gidan da ke opposite din nata tayi knocking, A madaidaicin palourn gidan da yake kamshin turaren wuta ta zauna, few minutes matar gidan wacca ake kira Oum Sulthan ta fito, tana ganin Hajar ta mata murmushi snn ta zauna suka gaisa, Hajar ta mata barka, Oum Sulthan tace "Wanka ake yiwa Babyn..", Hajar tace "Okay tom.. ina Boy..?", Oum Sulthan tace "wai Sulthan yana Schl..", Oum Sulthan da kanta taje ta kawowa Hajar Babyn bayan an gama mata wnka, Hajar ta ringa kallon Baby girl din tana jin kamar ta tafi da ita, the Baby is so cute amma kuma ba fara bace, kana kallonta kaga Maamanta don kamarsu ɗaya, Oum Sulthan baƙa ce ƴar Maiduguri amma kuma kyau ba'a cewa komai, Hajar na shafa soft cheeks din Babyn tace "kamar na tafi da ita wllh..", Oum Sulthan tace "Na bar maki ki tafi da ita, indai Sulthana ce ko 1hour ba za tayi ba zaki nemi hanyar nan gidan..", Hajar tayi murmushi tace "wnn cutie din ce za ace tana rigima..", Oum Sulthan tace "Uhmm shiyasa nace ki tafi da ita kinga idan ta nuna miki halin shknn", Hajar ba ta wani daɗe ba ta yiwa Oum Sulthan sallama ta tafi gida bayan ta ajiye mata ledar da ta shigo da ita. Da daddare wajen ƙarfe takwas da rabi Hajar na tsaye gaban wardrobe tana mayar da boxes din da ta fiddo ta ɗauki new Sleeping gowns, slowly take yin aikin tana humming song, buɗe ƙofa akay Nurain ya shigo, daga bakin door ya tsaya hannunsa ɗaya cikin wandon white pajamas dake jikinsa yace "Baby yau ba kallo naga lokacin fara Stuffs dinki ya kusa..?", tace "Am coming My Moon", yace "Ina downstairs palour..", ta ajiye abinda ke hannunta ta nufi inda yake walking like a cat, tana zuwa kusa dashi ta zagaye wuyansa with both hands ta ɗan yi kissing karan hancinsa tace "Mr Coffee..", yace "Neh Sweet pie..", tace "yau ma akwai wnn yummy coffee din..?", ya goga karan hancinsa a nata yace "shi little love yake so knn..?", tayi twinkling eyes dinta ta gyaɗa kai, ita dai tasan bbu wni little love kawai ta gyaɗa kai ne don ta sha coffee din, sosai ta hango annuri a fuskarsa, yace "do you like it with Popcorn...?", ta gyaɗa kai, yace "Ohk..", A hankali ta janye hannunta daga wuyansa tace "Thank you Cappuccino..", murmushi yayi kafin ya kullo mata ƙofar ya sauka downstairs, tini Hajar ta ƙarasa mayar da kayan, gaban mirror ta matsa ta sake shafe jikinta da turare bayan wnda ke jikinta, room slipper ta saka ta nufi door, Walking gently ta sauka downstairs, palourn bbu haske ko ɗaya sai na TV dake aiki, ta kalli kan Centre table taga Popcorn, ta zauna kan Sofa gami da daukar remote ta canza channel zuwa wacca take so, cup din Popcorn ta ɗauka ta fara watsawa a baki, kamar wcca aka mintsila haka ta ajiye Popcorn din ta tashi da sauri ta nufi kitchen, tana buɗe kitchen din ta gansa yana tsiyaye Coffee din a mug, a hankali ta mayar da ƙofar ta rufe ta koma palour ta zauna tana murmushi, she's very proud of her husband wnda sam ba shida rawanin tsiya wato girman kai, After like 2mins ya fito daga kitchen din, a kusa da ita ya zauna ya miƙe mata Mug din, ta amsa da murmushi a fuskarta tace "Thank you..", Shi dai yana zaune palourn ne amma ba kallon yake ba danne danne yake jikin laptop, ita ce take kallon tana shan Coffee dinta, time to time yake kallonta sai kuma ya cigaba da abinda yake, wnn dai haɗin sai aikin little love ace Popcorn with coffee, kuma ya lura daɗin abinta take ji, saida taci wajen rabin Popcorn din ta juya tana kallonsa tace "Moon", yana operating laptop yace "Uhmm", tace "baka ci ne..?", ya juyo yaja hancinta yace "sai Baby love ya ƙoshi..", guda ɗaya ta ɗauki Popcorn din ta kai saitin bakinsa tace "Haaa", ya buɗa baki ta saka masa, hka nan ta cigaba da yi indai za taci shima sai ta basa, dena operating laptop din yyi snn yayi gefe da ita yace "This is not romantic..", Cup din popcorn din ya amsa, ita dai ta bisa da kallo, Uhmm ai kam tini ya fara gwada mata romantic one. ★Ranar da akai Arba'in din Baba a masallaci akai Addu'a snn akay sadaka, Hajar ma taje gida a ranar kuma da wuri Nurain ya ajiyeta, washe gari Huzaifa ya koma schl don tintini ma hutunsa ya ƙare, Sa'adatu kam tafi sati uku rabonta da gidan kuma ranar arba'in ma ba tazo ba, Maimuna kuma cikin jikinta ya tsiyaye wnda hkan ya haifar mata da wni azababben ciwon ciki, Nabilah kuma har yau zaman doya da manja suke da Maama da Maimuna, gaba ɗaya ta ɗauke musu wuta sam bata shiga sabgarsu, a fannin Umma kam bata samu wata matsala ba sam a gidan, don Maama bata shiga huruminta saidai kallon banza, Abincin ya wadata a gidan don ko rabin wnda Abba ya kawo ba suci ba, Naseer ne yke bada kuɗin cefane. Umma na zaune kan darduma bayan ta idar da sallar la'asar Nabilah tayi sallama, Umma ta bata izini snn ta shigo, Nabilah ta sunkuya tace "Umma tsintsiya zan ɗauka zanyi shara", Umma tace "Toh ga ta nan a bayan ƙofa", Nabilah ta tashi ta ɗauki tsintsiyar snn ta fita, Umma tabi bayanta da kallo sai kuma ta girgiza kai, ynxu yaushe rabonta da shara da wanke wanke duk Nabilah ce ke mata, bbu jimawa da fitar Nabilah sai ga Mu'azzam ya shigo, ya duƙa ya gaida Umma da ladabi, Umma ta amsa snn tace "yau da wuri aka taso aiki knn..?", ya shafa kansa yace "Eh ai ba ma aikin naje ba..", Umma tace "Au toh..", Mu'azzam ya gyara zamansa sosai yace "Umma kwanakin baya nace zan siya miki gida idan Allah ya bani iko, Toh Alhmdllh yau Allah ya bani iko na siya miki gida Ummanmu" ya ƙarashe yana ciro keys daga Aljihunsa, hannunta ya kamo ya damƙa mata keys din, Umma ta sauke ajiyar zuciya tana kallon keys din, Addu'a sosai ta masa ta saka masa Albarka sai kuma ta girgiza kai tace "Ibrahim sai ka ƙunduge kuɗin da kayi shekara da shekaru kana tarawa ka siya min gida, A'a Ibrahim ka ajiye gidan..." da sauri ya katseta da faɗin "Dan girman Allah Ummanmu..", Umma dai na riƙe da keys ta kasa cewa komai. Sabrah na dawowa daga islamiyya Umma ta aiketa ta siyo mata katin waya, tini Umma ta loda katin a waya ta shiga kiran Anty, Anty na picking bayan sun gaisa Umma ta gaya mata komai, Anty tace "Alhmdllh Allah yayi masa Albarka ya buɗe masa hanyoyin samunsa ta ko ina..", Umma tace "Ameen..", Anty tace "kinga shknn mgnar inda zaki koma da zama ta mutu ynxu kawai gida za muje mu gani sai mu saka ranar tarewa...", Umma tace "tarewa kuma Jamilah A'a nikam nafi son na gama takaba a nan..", Anty tace "Haba Addah a sabon gidan ma ai zaki cigaba da takabarki, wllh kwata kwata zamanki da wnn matar beyi min ba kullum cikin fargaba nake", Umma tace "Wllh bbu abinda yake haɗani da ita, ba ruwan kowa da kowa", Anty tace "Ah a fa muka san me take ƙullawa tinda Allah ya kawo miki liɗifi ɗan albarkar yaronki ya siya miki gida toh ba zaki cigaba da zama a gidan nan ba", kwana biyu bayan nan Anty tazo ta amshi muƙulli taje ta gano gidan tare da Mu'azzam, Tinda Anty ta dawo takewa Umma santin gidan, ɗan madaidaici ne mai 2 bedrooms da palour sai kuma wni ƙaramin ɗaki a soro, sosai Anty tayi mamaki da taga anyi furnishing gidan da funiture masu rangwamin kuɗi, wnn funiture kam da kuɗinsu na gado shi da Hajar aka siyesu, tini aka tsayar da ranar tarewar Umma nan da kwana biyu, ranar tarewa kuwa tin wuri Umma ta shirya ta shiga makwabta ta musu bankwana, kayan sakawa kawai suka ɗauka, gwalegwajin funiture din Umma kam an fita dasu an siyar dasu a hka duk da cewa ba suyi wata daraja ba, Mu'azzam ya shiga ɗaki ya ɗauki jakar kayansu zai fita da ita, kasaƙe yyi yana kallon Nabilah dake zaune kan cement din ɗakin tana kuka Umma sai bata baki take, shi dai yayi waje abunsa da jakar kaya, Umma tace "Toh Nabilah nace kije ki dauko kayanki mu tafi...", Nabilah na sharar hawaye tace "Wllh Maama bazata barni ba..", Umma tayi ajiyar zuciya tace "bari na gwada sa'a ta na tmbayeta", da haka Umma ta nufi ƙofa ta fita, bakin ƙofar ɗakin Maama ta tsaya tayi sallama, Maama ta kalli labulen tace "waye ne..?", Umma tace "Nice..", Maama ta fito da ɗaurin ƙirji tana hura hanci tace "Ince dai lfy..?", Umma tace "zaman tare dai ya ƙare tinda Allah ya ɗauke wnda ysa muke zaune a tare, Ni zan tafi ina miki fatan Alkhairy, zaman da akay tare kuma a yafi juna..", Maama ta yamutse fuska tace "Au toh Alla raka taki gona can ƙauyen naku zaki koma..?", Umma tace "dan Allah ina roƙonki wata alfarma guda ɗaya a rayuwa..", Maama tayi kasaƙe tana kallonta, Umma tace "ki bani Nabilah na tafi da ita", wni kallon hadarin kaji Maama ta mata kafin tace "Eh ba shakka da yake ke kika durƙusa kika haifarmin ita dole kice hka, lokacin da na leƙa lahira na haifeta kina wajen ne, ko an gaya miki ƴar kyanwa ce da za kice na baki, yoh Allah na tuba ko ɗan karena bazan baki ba ballantana ƴar ciki na", Umma ba ta sake cewa komai ba tabar wajen, daman dai karambani tayi don tasan ko sama da ƙasa zasu haɗe Maama ba yarda za tayi ba, Nabilah kaf taji abinda ya faru ai kam ta sake fashewa da kuka, Sabrah sai binta take da kallo, Umma ta bawa Nabilah muƙullin ɗakin nata tace ko za tayi amfani dashi, Umma na hawaye ta kama hanyar soro Sabrah biye da ita, Nabilah dake kuka sosai sai kace uwarta ce zata barta ta wafci hijab akan igiya zata fita, Maama dake tsaye tsakar gidan tace "Alqur'an kika fita saina tsine miki albarka", Nabilah ta durƙushe wajen tana hawaye, har ga Allah Umma kawai take gani a gidan nan ta samu salama. ★Nurain ya juya yana kallon Hajar wcca take bubbuga ƙafarta a ƙasa tana kuka wnda yasan na shagwaɓa ne, ya sauke numfashi yace "Baby girl what now..?", ta buga ƙafarta a ƙasa tace "Ni dae zan bika..", yace "gidan Mami fa zanje, ki bari idan na dawo sai na kaiki kici seafood ai kinji daɗin na rannan ko..?", ta maƙe shoulder tace "Ni gidan Mami nake son zuwa..", yayi slight smirk ya haska mata agogon wrist dinsa yace "kinga fa ynxu ƙarfe huɗu da rabi before 6 insha Allah zan dawo", habawa ai tini hawaye suka hau zarya cheeks dinta tace "dan Allah Moon ka tafi dani..", ya sauke ajiyar zuciya yana kallon yacca ta jiƙa fuskarta da ruwan hawaye, ya girgiza kai yace "you're for real Baby wife ɗakko veil dinki", da sauri ta juya ta fara hawa stairs, yace "be careful fa..", ta juyo ta kallesa sai kuma ta juya ta haura saman, few minutes sai gata ta dawo sanye da hijab da handbag a hannu, ya ringa kallonta sai kuma ya girgiza kai yace "kin fiya rigima Baby wife..", ta turo baki ta wuce ta nufi door don kar ma yace ya fasa zuwa da ita, bayanta yabi ya rufe gidan da key snn suka wuce parking space, saida ya gama warming mota suka bar gidan, with minimum speed yake driving din, ya ɗan kalleta yace "kin ce dai ba kya son seafood din ko..?", ta girgiza kai tace "A'a ni bance bana so ba fa..", yace "what do you mean..?", tace "Ni dae cewa nayi ina son zuwa wajen Mami amma bance bana son seafood ba", yace "Uhmm ni zaki yiwa wayo yarinya", ta kyalkyale da dariya tace "kaga idan muka dawo daga gidan Mami da daddare sai muje yawo ma..", yace "hmmm yarinya ai yau kam kinci taliyan ƙarshe..", Nurain yayi parking bayan sun isa gidan, tana biye dashi suka nufi entrance, buɗe ƙofar palourn yayi ya shiga da sallama, da sauri Khausar dake zaune ita kaɗai a palourn da Laptop gabanta ta amsa sallamar, ta ɗan yi murmushi ta buɗe baki za tayi mgana knn ta hango Hajar, lokaci guda ta ɗaure fuska ta ɗauke idonta daga kallonta.......✍️ 💛 HAJAR 💛 {85..} Khausar na kallon Nurain tace "Ya sannu da zuwa, ina yini...", a takaice yace "lfy lou Lil sis.. yaushe kika zo?", tace "ɗaxu da safe..", ya gyaɗa kai ya nufi part din Mami, Hajar tabi bayansa da kallo sai kuma ta kalli Khausar da ta cigaba da abinda take jikin laptop, Hajar tace "Hi Khausar...", ko kallonta Khausar ba tayi ba tace "Sannu fa", Hajar bata sake mata mgna ba ta zagaye ta shiga part din Mami, bata tarar da kowa ba a palourn Mamin don hka ta samu kan carpet ta zauna, kawai saita fara tunanin shin me ta yiwa Khausar ne da take mata haka, ita dai a iya saninta tasan bbu abinda ya taɓa haɗasu tin farko, ta taɓe baki ta zuge handbag dinta ta ciro wayarta, ƙofar bedroom aka buɗe Mami ta fito Nurain na biye da ita, Mami ta karkaɗa ɗan yatsa tace "kaga Nurain ka fita daga idona na gaya maka..", ya shafa kansa yace "Please our Mami just this one..", Mami ta haɗe gira tace "No" da haka ta ƙaraso cikin palourn tana kallon Hajar fuskarta ƙumshe da murmushi, Hajar ta ɗan russuna tace "Mami barka da fitowa...", Mami tace "yau daughter.. sai kuma kika zauna a ƙasa", Hajar tace "ba komai nafi son ƙasan ne", saida Mami ta zauna kan Sofa snn Hajar ta gaisheta cike da ladabi da nutsuwa, Mami ta amsa mata tana tmbyarta ya take, Nurain dai yana tsaye ta bayan kujerar Mami sai kallonsu yake, ƙofar palourn aka buɗe Khausar ta shigo da sallama hannunta riƙe da Laptop, ta ƙaraso ta zauna kan Sofa ta ɗora Laptop din kan laps dinta, Mami tace "rubutun project din ne dai..", Khausar ta langwaɓar da kai sai kuma tace "Eh.. wllh duk na gaji Mami..", Mami tace "Bature ne ya riga ya bar mu da kazar whala..", Nurain yace "project take yi ne..?", Mami tace "Eh... gashi kuma next week zasu fara exams shiyasa akay tafiyar bbu ita", Nurain ya gyaɗa kai yace "Su Aunt Zulaihah sun tafi knn..?", Mami tace "yeah yau da safe suka wuce", ya kalli Khausar yace "A chapter na nawa kike..?", tace "Two", zagayowa yayi ya zauna kujerar dake kusa da nata yace "Muga Chapter 1..", tace "Ohk" da haka ta fita duba inda Slide din yake, Mami tace "yauwa ka duba mata kafin tayi submitting...", Hajar dai na zaune palourn tana kallon wayarta, Khausar na nemo Chaptern ta miƙe masa Laptop din ya fara duba mata, ta zauna hannun kujerar da yake, Hajar ta ɗaga kai ta kallesu sai kuma ta kaudar da kanta, knocking door akay mai aikin Mami ta shigo, saida ta gaishe da kowa na palourn har Hajar snn tace "Hajiya an kawo kayan marmarin..", Mami tace "Ohk.. An gama haɗa garin kunnun..?", Laure tace "A'a shi dai nake haɗawa..", Mami tace "Jeki ki cigaba da aikinki don gobe da safe zanyi amfani dashi insha Allah..", Laure tace "Toh Hajiya" da haka ta tashi ta fita. Bayan sallar magrib Mami na zaune kan prayer mat da ta idar da sallah a bedroom dinta Khausar ta shigo, a hankali ta ƙarasa ciki ta duƙa gaban Mami, Mami na kallonta tace "ya akai daughter..?", Khausar ta saukar da kanta tana twisting fingers tace "Mami dman cewa nayi zanje gidan Yaya sbd na samu ya ringa dubamin chapters din dana rubuta, ko 5days nayi sai na dawo kafin mu fara exams..", Mami tayi ajiyar zuciya tace "Toh shknn ai kam sai kinfi samun lokacinsa a can gidan nasa tinda nan sai yamma yake zuwa, kin gaya masa ne..?", Khausar ta girgiza kai tace "No i ask you first..", Mami tace "Alright i will tell him..", Khausar tace "Toh" da haka ta tashi ta fita. Nurain na dawowa daga mosque sallar isha'i yaga Hajar ta shiga kitchen, murmushi yayi ya bita kitchen din, tarar da ita yayi ta buɗe fridge ta ɗauki ruwa tana zubawa a glass cup, ya ƙarasa inda take ya rutsa cikinta, sosai ta firgita don ba taji shigowarsa ba, ta zaro ido after perceiving his scent tace "This is not proper nan fa gidan Mami ne...", yayi kissing neck dinta yace "Toh mu tafi gidanmu..", zaro ido tayi don gani take tsaf wni zai iya shigowa ya gansu, ta marairaice tace "Moon ka bari please... Allah wani zai iya shigowa", ya sake manna mata wani kiss din yace "Toh ina ruwana, nida matana", habawa ai tini ta fara ɓamɓare hannunsu daga cikinta, sakinta yayi sai kuma yayi Chuckling yace "bari na yiwa Mami sallama sai mu tafi" yana gama faɗin haka ya juya ya fita, tana ganin ya fita ta sauke ajiyar zuciya, ta ƙarasa tsiyaya ruwan ta sha. Direct Nurain ya wuce part din Mami don yi mata sallama, bai sameta a palour ba don hka ya shiga ɗaki, sallah ya tarar tana yi, kawai ya ɗan kwanta rigingine a kan gado yana jiran ta idar, tana idar da sallahr ta juya ta kallesa sai kuma ta fara jan counter, Nurain ya ɗan ɗago kansa sai yaga ashe ta idar, Mami ta gaya masa cewa Khausar zata bisu gidansa, ɗan jimm yayi bai ce komai ba, Mami tace "Any problem with that..?", ya girgiza kai yace "No.. not at all..", tace "Okay", Hajar ma ta shigo ta yiwa Mami sallama snn ta ɗauki handbag dinta ta fita compound don already Nurain ya fita yana jiranta, a mota ta tarar dashi, ta buɗe front seat ta shiga snn ta kullo ƙofar, ya kamo hannunta yace "Baby wife..", ta juya ta kallesa tace "Moon..", yayi murmushi yace "Tare da Khausar zamu tafi, i hope baki da damuwa akan hakan ko?", ta girgiza kai tace "Ba komai ƙanwarka ce fa", babu jimawa sai ga Khausar nan ta fito da jakar kayanta a hannu, back seat ta buɗe ta saka jakar snn itama ta shiga, Nurain ya juya kaɗan yace "baki manta komai ba ko..?", tace "Eh i think so", slowly yaja motar suka bar harabar gidan, suna hawa saman titi ya ɗan kalli Hajar yace "Sweet pie mu siya seafood din ne..?", da mamaki ta dubesa sai kuma ta gyaɗa kai tace "yess", yace "Okay" da haka ya ɗauke kan motar ya canza hanya, firarsa kawai yake da matarsa cikin farin ciki da ƙaunar juna, Khausar dai na maƙale a baya tana danna wayarta amma fa kunnuwanta na kan firarsu, haba ai Nurain har sakin layi yke don a zahirin gsky ya mnta da wata Khausar a motar, Hajar ta juya idanunta ta matsa kusa dashi ta rage murya tace "Moon akwai fa back sitter..", sai a lokacin ya farga ya shafa kansa yana murmushi, bayan sunyi tafiya mai nisa yayi parking a katafaren wajen da foreigners din suke siyar da seafood, kashe motar yayi yace "what do we do... muci anan ko kuma muyi takeaway..?", Hajar tace "Takeaway..", yace "Okay", tace "with lot of Shrimp Moon", ya ja hancinta ya rage murya yace "shi Baby love yafi so knn..?", ta turo baki ba tace komai ba, Khausar dake back seat ya kalla yace "Lil sis kema kina cin seafood..?", Khausar tace "Eh Yaya", yace "Ohk", buɗe motar yayi ya fita, After 5mins Hajar tace "Khausar duk ciki Shrimp yafi daɗi ko..?", Khausar tace "Nope ni kam Octa yafi min daɗi..", Hajar tace "Ohk ni kam Shrimp din nafi so", Khausar ta taɓe baki tace "Toh ke kam ai ynxu bazaki gane wanne yafi daɗi ba tinda yaushe ma kika fara cin seafood din, nasan ba ci kike ba a da, koda yake a inama kika gansa bare kici, Ai sai kayi kamar 1yr haka kana ci kake gane best..", samm Hajar bata gane mgana Khausar ta gwaɓa mata ba, tace "Okay", 15mins Nurain ya ɗauka kafin ya fito, leda biyu yayo shi da Hajar sai kuma na Khausar ita kaɗai, Tara da rabi suka isa gida, Hajar tini ta wuce ɗakinta don so take tayi wnka saita zauna zaman cin seafood din, Khausar ta ƙarewa palour kallo sai kuma tace "where am I staying..?", Nurain ya nuna mata hanyar guest room yace "that room..?", ta gwalo ido tace "Na shiga uku, ni kaɗai zaku bari a downstairs..", yace "Ashe matsoraciya ce... Alright come with me..", da haka ya nufi stairs, ta ɗauki jakar kayanta tabi bayansa, extra room dake upstairs ya nuna mata yace "Are you Okay with this one..?", ta buɗe ɗakin ta leƙa sai kuma ta juyo ta gyaɗa kai tace "Sure", yace "Akwai bedsheet da blanket a closet, and if you need anything let me know...", ta gyaɗa kai tace "Toh", ta ɗauki jakar kayanta ta shiga ciki, ɗakin Hajar ya buɗe bai ganta ba, motsinta ya jiyo a bathroom don haka ya juya ya fita. Ƙarfe goma da minti shida Hajar ta sauka downstairs, hijab ne har ƙasa a jikinta wnda ta ɗora saman kayan bacci da ta saka, kitchen ta shiga ta buɗe fridge ta ciro lemon kwali da bottle water, ta ɗauki plate ta ɗora kan tray tare da ruwa da lemon, tana fitowa kitchen din taga Khausar na saukowa daga stairs, Khausar na matsawa kusa da Hajar taji wni shegen ƙamshi yana tashi a jikinta, Khausar tace "Amm ina house help room dina is so dusty inaso a sharemin..?", Hajar tace "we don't have one..", Khausar ta rumgume hannaye tace "ban gane ba toh waye yake aikin gidan...?", Hajar tace "Nice nake gyarawa", Khausar ta taɓe baki tace "chab snnu ni kam bazan iya donkey work din nan ba, anyway maybe kin saba da whala shiyasa", Hajar ta ɗan kalleta sai kuma tace "Uhmm ko baka saba da whala ba ai dai ka gyara gidanka", Khausar ta juya idanunta tace "Ohk ni ynxu wane zai gyara min ɗakin ina so na kwanta ne..?", Hajar tace "wa kwa zai gyara miki ke zaki gyara abinki ai" da haka ta zagayeta ta nufi stairs, da sauri Khausar ta sha gabanta tace "kince fa ke kike gyara gidan so ki gyara min room din mna", Hajar tayi ɗan murmushi ta wurga manyan idanunta tace "kin shekara ba'a gyara miki ɗaki kin kwanta ba, ki shiga kitchen a store akwai broom da packer da Mop ki gyara abinki Khausar, idan kuma hka zaki kwana ba gyaran saiki rubuɗa a ƙura..", Hajar na gama faɗin haka ta haura sama abinta, direct kuma turakar mijinta ta shige, haka dai Khausar ta ɗauki kayan shara taje ta gyara ɗakin fess. Washe gari as usual bayan Hajar ta idar da sallar asuba ta fito ta gyara gidanta, ta bulala masa turaren wuta mai mugun ƙamshi, ynxu samm ba tada case a fannin ƙamshi don Oum Sulthan makwabciyarta sana'ar siyar da turaruka take na gida da kuma jiki, turarenta kam ba'a cewa komai sbd ƙamshi, har na Sudan India da sauran ƙasashe da suka san turare tana siyarwa. Hajar na gama gyaran gidan ta shiga kitchen ta shirya lafiyayyen breakfast, dining ta kai ta ajiye snn ta wuce room dinta ta fesa wnka, daga hka ta wuce ɓangarensa don taimaka masa wajen shiri tinda yau zai fita aiki, tare suka sauko downstairs tana riƙe da briefcase ta cokala hularsa a kanta, dining suka zauna ta zuba masu Irish a plate ɗaya, sai kuma ta ɗauki bowl ta zuba masu Offals pepper soup, da haka ta ja kujera ta zauna, yace "Heartbeat ina Khausar..?", tace "ina jin bata tashi ba..", yace "Ohk", tace "Na ajiye mata nata a kitchen..", yace "Thank you..", tayi murmushi tace "Eat alot", ta ƙarƙashin table din ya zura hannu ya shafa tummy dinta yace "you too, baby love ma yaci da yawa", ta juya idanunta ba tace komai ba, jin footsteps alamar ana saukowa daga stairs ta fara ƙoƙarin cire hannunsa daga tummy dinta, Khausar ta ƙarasa saukowa ta ɗanyi bowing tace "Good morning Yaya", yace "Morning how was your night..?", tace "great Alhmdllh", ita dai Hajar abincin ta kawai take ci, juyawa Khausar tayi zata koma saman Nurain yace "come join us..", walking gently Khausar ta isa dining din taja kujera ta zauna, sai a lokacin Hajar ta ɗago kanta ta ɗan kalli Khausar tace "kin tashi lfy..?", a takaice Khausar "Eh lfy..", Nurain ya tura mata warmers din abincin gabanta, Khausar ta buɗe ƙaramar warmern tana kallon farfesun da yake fitar da wani ƙamshi mai daɗi, tini yawunta ya tsinke amma saita yamutsa fuska ta rufe, warmer din Irish da kwai ta buɗe itama ta rufe, cup ta ɗauka ta haɗa shayi ta fara sha, Khausar ta ringa satar kallon Hajar don har ynxu hularsa ce a kanta, ganin Khausar na shan shayi bata zuba abincin ba Nurain yace "ki zuba abinci fa..", ta girgiza kai tace "Amm bana cin offals..", ya gyaɗa kai yace "Ohk then, you should cook something else karki zauna da yunwa...", tace "No am okay with the tea", bai sake cewa komai ba suka cigaba da cin abincinsu, Hajar ce ta fara gamawa don haka ta jirasa har ya gama, miƙewa yayi ya riƙo hannun Hajar itama ta miƙe, ya kalli Khausar yace "saina dawo sai muyi karatun ko..?", tace "Toh a dawo lfy..", tabi hannunsu dake riƙe cikin na juna da kallo kafin ta cigaba da shan shayinta, suna fita balcony ya rage tsaho ta ciro hularsa dake kanta ta kafa masa, hannunta dake cikin nasa ya murza yace "stay safe wife..", ta matsa gaff dashi ta sunkuyar da kanta, a hankali ya sunkuyo yayi pecking forehead dinta, yace "Then your turn..", tace "What..?", ya taɓa lips dinsa yace "Peck", ɗaya daga cikin kujerun dake balcony din ta taka ydda zata kamo tsahonsa, murmushi tayi ganin yacca ya wni lumshe ido wato yana jira, saida ta goga karan hancinta a nasa snn ta basa light peck a lips, da uban gudu har dasu tuntuɓe Khausar dake maƙale jikin ƙofa ta koma ta zauna kan sofa, Hajar ta shigo da murmushi a fuskarta, kallo ɗaya ta yiwa Khausar ta haura upstairs tana humming song. Hajar ba ta sake sakkowa ba sai sha ɗaya da rabi, kasaƙe tayi tana kallon palour, an wurgo da kaf throw pillows din kujeru kan carpet, ga ɓawon Abaya da seeds din Apple kaca kaca a ƙasa, Khausar ce zaune kan doguwar kujera ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, ga Orange nan a gefenta tana sha ta tara ɓawon akan hannun kujerar, ko a jikinta kawai typing dinta take a jikin laptop, Hajar tafi 50secs tana kallonta kafin ta juya ta shiga kitchen, turus tayi a bakin kitchen din ganinsa kamar anyi yaƙin badar, gaba ɗaya cupboard a buɗe suke, ga uban kayan wanke wanke da suka cika sink, everywhere was untidy, 30mins ta ɗauka tana gyara kitchen din, toh wai hka ake girki ko kuma dai wulaƙanci ne, gaba ɗaya an ƙone tukwanen da akay girkin, da tazo mopping kam saida tayi da gaske don wni uban vegetables oil ne malale kan tiles, saida ta gama gyaran kitchen din snn ta ɗora lunch, snow rice din da tayi draining ta mayar kan wuta don tayi steaming, fita tayi daga kitchen din, at that time Khausar bata nan, Hajar ta girgiza kai tana kallon palourn lokaci guda ta duƙa tayi picking ɓawon Ayabar ta kai dustbin, throw pillows din kuma ta mayar dasu kan kujera, room dinta ta koma tayi sallar Azahar, downstairs ta sauko don tasan shinkafar ta gama steaming, Khausar ta tarar A palour still dai Laptop take operating, sukay ido huɗu, Khausar ta ɗauke kanta kamar bata ganta ba, itama Hajar din bata kulata ba ta wuce kitchen, sosai tayi mamaki da taji kitchen din ya cika da ƙauri, gani tayi an ƙure wutar gas din bayan kuma ta rage sosai, da sauri ta isa gaban gas din ta kashe wutar a bit confuse, sama sama ta yaɗe shinkafar wcca bata ƙone ba ta juye a warmer, Allah yaso ba tayi ƙauri ba. Wajen karfe uku Khausar taji ƙarar bell, tsallake throw pillows din da ta sake wurgowa ƙasa tayi ta nufi door ta buɗe, murmushi tayi ta koma gefe tace "Yaya sannu da zuwa", ya amsa kafin ya shigo yana ƙarewa palourn kallo, wnn shine karo na farko da ya shigo gidansa ya tarar da hka, sai ya fara neman matarsa a palourn don ya saba idan ya dawo ta taho da gudu ta rumgumesa tana masa snnu da zuwa, tini ya nufi stairs yana cewa "Baby wife.. Sweet pie.. Honey" da haka ya haura saman. Tinda ya dawo Khausar take zuba ido taga ya sauko don suyi karatun amma shiru, ai kam sai wajen sallar la'asar ya sauko shima kuma mosque zai fita, da kansa yace ta jira idan ya dawo zai duba mata, bbu jimawa Hajar ma ta sauko ta haura sama da kayan abinci, sake saukowa tayi ta ɗauki ruwa da lemo daga nan bata sake dawowa ba. Da daddare Hajar na naɗe jikinsa tana kallon stuff dinta, A hankali yake shafa lallausan gashinta yace "Baby wife wai su duk kamarsu ɗaya wadan nan mutanen..?", tayi ƴar dariya tace "A'a fa kowa da kamarsa", kallon Tv yayi yace "Ga wni can kamar Mr Lee", ta ɗaga kai ta kallesa tace "Wanne..?", yace "the one in black and red..", tace "Chab ai shine boss..", yace "Ohh toh a bani spoiler so that i can catch up..", zaune ta miƙe ta fara surfa masa bayani, shi dai kawai kallonta yake yana nodding head don ba fahimta yake ba, shi dai kawai daɗin kallonta yake ji a haka, ya shafa kansa yace "Mene ne ma kika ce sunan actor din..?", ta gaya masa, tuntsirewa yayi da dariya harda jingina da kujera yace "wnn wane irin suna ne sai kace za'a zura da gudu..", dariya tayi ta kwanta a ƙirjinsa listening to his heart beat tace "kaga fa sunansa da daɗi..", yayi wrapping dinta sosai yace "wollah ba daɗi", a hankali ta ɗagasa ta kalli Tv, yace "ita kuma Actress din fa..?", ta maƙe shoulder tace "dariya zakamin wllh..", yace "Toh idan ban san sunansu ba taya zan gane series din", sai da tayi gyaran murya snn ta gaya masa, pointed nose dinsa ya ja ya gyaɗa kai sai kuma ya zuƙe lips don baya so yayi dariyar da ta taho masa, ai gwara ma sunan Actor din, Hajar ta ƙura masa ido without blinking tana jiran reaction dinsa, ya miƙe daga kan kujerar ya nufi door yana jan rigarsa, tini ta tashi tasha gabansa, bai san lokacin da dariyar ta kufce masa ba, ya ɗora forehead dinsa saman nata da haka ya fara turata har saida ya kaita bango still yana dariya, ta turo baki tace "daman nasan dariya zakamin..", ya ɗago ya kalli eye ball dinta yace "you're the best sweet pie..", ta juya kwayar idanunta ta fara wasa da rigarsa tace "Moon... kawai dai baka son sunan nas..", slight kiss ya sauke mata a lips yace "bari na dawo sai a gayamin sunan supporters suma.." da haka ya bar wajen ya nufi door, downstairs ya sauka, sosai yayi mamakin ganin Khausar, yace "Ohh baki kwanta ba..", ta sosa forehead dinta tace "Eh", yace "Ohk" ya buɗe ƙofa ya fita, After 10mins ya dawo, har zai wuce sama Khausar ta miƙe tace "Yaya don Allah ko zaka ƙarasamin chaptern ynxu in yaso gobe sai mu buɗe fresh, i only have 4days left..", ya ɗanyi jimm sai kuma yace "Ohk" ya dawo palourn ya zauna. Hajar ta kalli door a wajen karo na biyar sai kuma ta kalli agogo, almost 2hours fa da fitarsa, tashi tayi ta nufi door tana tare hammar da ta yanko mata, tana isa gaban stairs ta hango haske sosai a palour kafin ma ta sauka, step ɗaya ta sauka ta hangosu, tafi 50sec a tsaye kafin ta juya ta koma saman, 11 dot Nurain ya haura sama bayan ya gama da Khausar, itama ta haɗa komai nata ta tafi zata kwanta, yana shiga palourn sa ya tarar Hajar tayi bacci kan kujera, ajiyar zuciya yayi don yaso ya cigaba da cin dariyarta, duƙawa yayi gaban kujerar ya ringa kallon fuskarta, daukarta yayi ya shiga bedroom da ita ya kwantar da ita kan gado snn ya rufa mata duvet, ta ɗan motsa ta gyara kwanciyar. Washe gari da Asuba ya shigo ya tarar da ita ta idar da sallah knn, suna haɗa ido ta juyar da kanta tace "Ina kwana..", still yayi a inda yake don ba haka ta saba gaisuwar ba tana haɗawa da My Moon or something romantic, ƙarasowa yayi ya duƙa gabanta, tayi gefe da fuskarta don bata so su haɗa ido, Calmly ya kamo hannunta, a hankali ta amshe hannunta sai kuma ta miƙe tare da prayer mat din da tayi sallah, miƙewa yayi yace "Baby wife", ta juya masa baya ta fara linke prayer mat din.......✍️ 💛 HAJAR 💛 {86..} Ya dawo ta gabanta yana ƙoƙarin leƙa fuskarta ta sake juya masa baya, lower lip dinsa ya ciza painlessly ya riƙo hannunta zai juyo da ita, afujajan ta fixge hannunta kawai ta faɗa kan gado ta takure waje ɗaya, ajiyar zuciya yayi ya hau gadon ya kwanta side dinta, tana jin present dinsa daf da ita ta muskuta zata matsa, da sauri ya riƙota ya janyota jikinsa yace "Me nayi da aka ƙi kulani..?", ji tayi kamar ta rushe da kuka wato ma tmbya yke me yayi, idonta yayi rau rau hawaye suka cikosa, hijab din ya tattaro ya cire mata, duk tana jinsa amma bata motsa ba, duvet ya janyo ya lulluɓa musu tare don yasan bata resisting sanyin ɗakin, a hankali ya fara brushing gashinta da yatsunsa, ta lumshe idonta sai kuma ta fara ƙoƙarin kwace kanta, gam ya riƙeta motsin ma ta daina, ya kai lips dinsa saitin kunnenta yace "Baby wife please talk to me", kamar mai koyar mgana tace "Ni bacci zanyi", yayi pecking forehead dinta sai kuma ya ɗora kansa saman nata yana sauke numfashi a hankali yace "sleep tight Baby girl.." da haka ya lumshe idonsa yana cigaba da brushing hair dinta, ta gyara kwanciyarta perceiving his pure scent tana jin daɗin taɓa gashinta da yake, buɗe idonta tayi don bata so ta koma bacci, idan ta kuskura ta rufe ido toh ynxu zata jita a jihar barno don komai rashin baccin da take ji daga yayi cuddling dinta yana mata hka bacci yake zuwa, bayan ta tabbatar ya koma bacci ta zame jikinta a hankali ta sauka daga gadon, ta ɗauki hijab dinta ta saka ta buɗe ƙofa ta fita, downstairs ta sauka, tsayawa tayi tana kallon palourn da yayi uban datti, palournta bai taɓa datti kamar yau ba, har da noodles ta gani akan kujera da marmasasshen biscuit, a hankali take aikin don wta kasala take ji, kitchen ma ba laifi a ɓace yake saidai bai kai na jiya ba, da rashin kuzari take aikin harta gama, breakfast din da ta dafa sai taji ƙamshinsa yana tayar mata da zuciya, da kyar dai ta juye a warmers ta fita, daga nan room dinta ta koma ta shiga wanka, bayan ta fito tayi shafe shafenta snn ta baza turare a jikinta, doguwar rigar atampa mara nauyi ta saka, ta hau gado ta kwanta ta lumshe ido, time to time take buɗe idonta ta kalli agogo, ƙarfe takwas da rabi taji zuciyar nata ta dena tashi kuma bata jin kasala kamar ɗaxu, bathroom ta shiga ta kuskure bakinta da mouth rinks ta fito, walking gently ta fita ta nufi ɓangarensa, tana shiga bedroom ta gansa gaban mirror already dressed up yana combing hair dinsa, ta cikin mirrorn suka haɗa ido tayi sauri ta saukar da kanta, beyi buttoning rigarsa ba snn ma bai saka links ba don wnn aikin na Baby wife ne, ta ƙarasa gaban mirror din kanta a ƙasa, ya ajiye comb din ya juyo yana kallonta, bata bari sun haɗa ido ba sai juyar da kai take, tayi ɗage kamar yacca ta saba ta ɓalle masa buttons din, shi kam kawai kallonta yake without blinking har ta gama, ta ɗauki links din ta kamo hannunsa ta saka masa, Calmly ta saki hannunsa bayan ta gama saka masa links din, ta juya zata bar wajen, ya sauke wta ɓoyayyiyar ajiyar zuciya ya riƙe damtsenta ya fixgota, gaba ɗaya ta taho kamar zata faɗi ƙasa sbd yacca ya fixgotan, saidai bata faɗin ba don tini yayi wrapping dinta cause ya fixgota ne sbd hkan, tayi ƴar ƙara cause ta tsorata sai kuma ta fara mutsu mutsu zata fixge, yace "fushi kike dani wife...?", ta girgiza kai tace "A'a", yace "Hmmm i know you are angry at me", ta juya idanunta tace "please let go off me if not kayanka za suyi squeezing..", tamke riƙon da yayi mata yayi yace "let them be", After a while ya saketa sai kuma ya juyo da ita ya tallaɓi cheeks dinta yace "Look at me wife", ta ɗaga kanta ta kallesa a taƙaice, yace "Am sorry I left you all alone last night", ta saukar da kanta tace "It's Okay..", lokaci guda ta ɗago kanta ta ringa kallon eye ball dinsa, ɗage tayi ta zagaye wuyansa sai kuma ta turo baki tace "Ai baka amsa gaisuwana na yau ba", murmushi yayi ya rutsa ƙugunta zuwa bayanta yace "say it again..", tace "Good morning My Moon..", ya goga karan hancinsa a nata yace "Morning Baby girl..", ya daɗa haɗata da ƙirjinsa ya haɗe lips dinsu waje guda ya shiga kissing dinta, lumshe idonta tayi after a while ta shiga mayar masa da martani, hannayenta dake zagaye da wuyansa tasa ta fara wasa da sumarsa, da sauri ta janye lips dinta don tasan ynxu sai abun ya girmama, yayi murmushi snn ya rumgumeta yace "I Love you..", ta cusa kanta a wuyansa tace "I Love you more". Downstairs suka sauka tare as usual, zaune suke kan dining suna yin breakfast a tare, loma biyu tayi ta ajiye spoon din hannunta don tini zuciyarta ta hau tashi, ganin ta dena ci yace "what's wrong wife..?", ta girgiza kai tace "Na ƙoshi..", tini shima ya ajiye spoon dinsa yace "Why ba kya son wnn ne..?", ta gyaɗa kai snn ta ɗauki spoon din ta damƙa masa tace "Noodles zan dafa later ynxu bana jin yunwa..", yace "Ohk ita Baby love yake so", ta langwaɓar da kai tace "Yeah" ita ynxu ma dai kawai biye masa take aje a hkan, ina taga wni abu wai shi ciki a ynxu, Khausar ce ta sauko daga stairs tana tafiya a hankali, fuskarta duk kumburin bacci don bata daɗe da tashi ba kuma shima ƙishi ruwa ne ya tasheta, hijab ne a jikinta har ƙasa, ta ɗanyi tafiya towards dining din da suke kai, sosai tayi bowing ta gaida Nurain, ya amsa yana tmbyrta ya ta kwana, tace "fine alhmdllh..", da haka ta juya zata shiga kitchen, yace "Khausar..", ta juyo sai kuma ta dawo position din da ta tsaya tace "Na'am", thick eyebrows dinsa ya haɗe yace "Kin gaisheni baki gaisheda matana ba ko baki ganta bane..?", Khausar ta ɗago ta kalli Hajar sai kuma ta dubi Nurain tace "Yaya ai mun gaisa da ita ɗaxu..", ya kalli Hajar da ta saki baki tana kallon Khausar yace "Sweet pie hka ne..?", Hajar na kallon cikin idon Khausar tace "A'a wllh ni kam ynxu ma na ganta tinda garin Allah ya waye...", sosai mamaki ya cika Khausar don ba tayi tunanin Hajar zata ƙaryata ta ba, Nurain ya ringa kallon Khausar snn yace "Then do it now..?", wata ball ce ta tsayawa Khausar a throat, da kyar ta buɗe baki tace "good morning..", Hajar ta juyar da kai tace "Morning..", Nurain yace "karki sake maimata wnn mistake din, respect My wife as you respect me...", ta saukar da kanta tace "sure" sai kuma ta juya ta shiga kitchen, though yasan ta girmi Hajar tinda Sa'ar Noor ce amma dai hkan bazai bata ƙofar raina masa mata ba, wnn ai raini ne ya tabbatar idan Noor ce baza tayi hkan ba, ko da Hajar ƙarama ce still dai matar Elder Brother dinsu ce, yana sane ma yaƙi inviting dinta yau wajen yin breakfast don sarai yasan me tayi jiya, sai wni yamutsa fuska take tana aibata yummy abincin matarsa, saida Hajar ta rakasa har balcony tana masa Allah ya tsare, ya tambayeta da me zai taho mata, finger dinta ta zura a baki ta rutsa da haƙoranta tana tunani, lokacin guda tace "Rake..", ya waro ido yace "Sugarcane..?", ta gyaɗa kai tace "Eh shi nake so..", yace "Ohk then.. saina dawo". Noodles din ma da Hajar ta dafa wajen ƙarfe goma kasa ci tayi, kitchen ta kai bayan ta tsattsakura ta rufe, room dinta ta koma ta kwanta, ko 10mins bata ƙara ba wni mugun bacci yayi awon gaba da ita, ba ita ta farka ba sai 1 da wni abun, wasai taji jikinta, duk da cewa ba taci abinci ba sai taji bata jin yunwa, ganin lokaci tayi sauri ta shiga bathroom tayo alwala ta gabatar da sallar azahar, tana idar da sallar ta fita don yau ta makara bata ɗorawa mijinta abinci da wuri ba, da shigarta kitchen din ta wni mugun daskare, har yafi jiya ɓaci don na yau da manja akai badaƙalar, jingina tayi da bango tana tunanin ta ina zata fara, ga palour can shima ya sha nashi hargitsin daidai gwargwado. Ƙarfe ɗaya da minti ashirin Nurain ya dawo gida, haɗe thick eyebrows dinsa yayi ganin palourn a hargitse kafin ya haura sama, direct room dinta ya buɗe ya shiga, ya ajiye ledar Sugarcane da ya taho mata dashi kan chest of drawers, saida ya tabbatar bata ɗakin snn ya fita ya shiga ɓangarensa, wanka yayi ya shirya cikin ƙananan kaya na zaman gida, room din nata ya sake dubawa a karo na biyu still dai bata nan, kawai sai yaji hakan Odd gashi ya kirata tin yana hospital bata ɗaga ba, yana fitowa daga room din nata Khausar ma ta buɗe ƙofar room din da take ta fito, gaishesa tayi snn ta masa snnu da zuwa, a takaice ya amsa kafin ya tmbyeta ko taga Hajar, ta girgiza kai tace "No ban ganta ba ni tin ɗazu ina ɗaki kum..." bai tsaya sauraronta ba ya gangara ya sauka ƙasa, Khausar ta ɗan taɓe baki tace "shegiya mayya... tinda nake da Yayana bai taɓamin faɗa ba sai a kanki, banza ƴar ghetto kawai", can gaban sink a durƙushe Nurain ya hango Hajar bayan ya buɗe ƙofar kitchen, bai san lokacin da ya ƙarasa inda take durƙusa ba ya ɗagota, hawaye ya jiƙa cheeks dinta tana yarfe hannu a hankali, ba ƙaramin rikicewa yayi ba yace "My Hajar.." sai kuma ya fara tattaba fuskarta yace "mene ne Baby..?", ta fashe da kuka ta damƙe hannunsa tace "Cikina..", miƙewa yayi ya miƙar da ita itama, ta koma ta naɗe a ƙasa tace "i can't..", without second thought ya sunkuceta ya fita da ita daga kitchen din, baki a sake Khausar dake tsaye palour ta bisa da kallo har ya haura sama, kuka kawai Hajar take don ji take kamar mararta zata tsinke, gaba ɗaya Nurain rasa inda zai sakata yayi, ji yake kamar ya kwashi ciwon nata ya dawo dashi jikinsa, gashi dai Dr amma tini ya zama quack, wni magani kwalli ɗaya tak ya bata, after 5mins da shan mganin tana murƙususu a jikinsa taji dama dama, lamo tayi tana sauke numfashi har dasu gumi ya tsattsafo mata a goshi, sannu kawai yake jera mata, a hankali ta zame dga jikinsa ta kwanta sosai a kan gadon, hannunsa ya kai tummy dinta yace "Sorry", kwalam yaji cikin nata har ya rufta, ya kalli yacca take ajiye numfashi a hnkali yace "kin ci abinci kuwa..?", ta gumtse baki don wni amai ne ya taho mata da ya ambaci kalmar Abinci, ya dafa goshinta yace "Love you need to eat something..", ta girgiza kai kawai, yace "Toh me kike son ci..?", nan ma ta girgiza kai, she must eat gsky cause in ba haka ba zata sha whala, yayi ajiyar zuciya yace "Toh zaki sha Sugarcane din dana kawo miki.?", tayi shiru sai kuma ta gyaɗa kai, yace "Aha bari na kawo miki..", ya shafa kanta da haka ya juya ya nufi door, room dinta ya shiga ya dauko ledar Sugarcane din da ya ajiye ya sauka downstairs ya wuce kitchen, ya ƙarewa kitchen din kallo sai kuma ya ɗauki plate ya juye raken ya wanke a sink, da plate din ya fito, saida ya kai daf da stairs snn ya juya ya kalli Khausar yace "Khausar kina zaune a guri duk datti, c'mon tashi ki gyara and do the dishes shima kitchen din ki gyarasa.." with comand ya ƙarashe mganar ya haura sama, Khausar tayi still zuciyarta kamar za tayi bindiga, bbu yacca ta iya haka ta tashi ta gyara palourn da ta ɓata da gayya, tana wanke wanke tana tsaki, bayanta har riƙewa yayi sbd tsayuwa, haka dai taci uban wanke wanke da ta tara snn ta gyara kitchen din shima, hannun rigarta ya jiƙe sharkaf da ruwa, fuska a matuƙar murtuke ta fito ta haura sama don ta cire rigar. Sai kace wni nama haka Hajar ta dilliƙi Sugarcane dinta, sosai ta sha ta rage ragowar wai sai Anjima, shi dai kawai kallonta yake don tini yayi confirming zarginsa, sai dai kuma yana so ya tabbatar, Calmly ya kamo hannunta yace "how are you feeling now...?", tace "Much better", yace "Good Alhmdllh, taso muje hospital Baby", ta kallesa ta turo baki tace "Ni am Okay", ya kwantar da murya yace "We have to Baby wife, kinga zasu rubuta miki drugs wnda zaki ringa sha sbd ciwon cikin, ynxu pain reliever ne na baki kar muje later ciwon ya dawo..", ta langwaɓar da kai tace "Ni bana son hospital... kai ka dubani a gida", murmushi yayi ya ɗora hannunsa a chest dinta yace "This is my field, i only chop hearts..", daga ƙarshe yayi convincing dinta ta yarda suje asibitin, hijab dinta ya dauko mata a room dinta da takalminta, wni private hospital ya kaita kuma ya buƙaci test kawai yake so a mata, tini wata Nurse ta dauki blood sample dinta ta wuce dashi lab, bai ɗauki wni 30mins ba result ya fito, bai tsaya bin wni procedure ba ya amshi result din test din suka bar asibitin, basu koma gida ba saida ta gaya masa me take son ci ya siya mata snn suka wuce, suna isa gida ta wuce room dinta ta kwanta, kasalar da ta tashi da ita ce ta dawo mata amma dai bata jin ciwon komai. Nurain ya ciro papern result din daga pocket snn ya zauna kan kujera, ya shafa fuskarsa da both palms dinsa sai kuma ya kalli papern, sai kace me shakkar ganin abinda ke ciki hka ya shiga buɗe papern, yana ganin result din ya sauke wni ajiyar zuciya, ya koma ya jinjina da sofa yace "Alhmdllh... Am going to be a Father..", lokaci guda ya dauki takardar ya fita, kwance ya ganta kan gado bayan ya shiga room dinta, ya ƙarasa gaban gadon ya ƙura mata ido, a hankali ya kai hannu ya kwashe rigarta ya ringa kallon fair tummy dinta, Hajar ta buɗe lumsassun idanunta a hankali, yana ganin haka ya zauna gefen gadon ya ɗagota ta zauna, ita dai kawai kallonsa take don wni yanayi mara misaltuwa ta hango a fuskarsa, bbu inda beyi kissing ba a fuskarta, ita dai tayi lakwan tana ganin iko Allah, duk hkan bai masa ba ya sunkuceta ya fara hajijiya da ita a tsakar ɗakin, saida yayi me isarsa snn ya ajiye a kan gado ya rumgumeta very tight, ya kai lips dinsa saitin kunnenta yace "Congratulation Baby girl you're going to be a Mother..", shiru ta masa don har ynxu hajijiyan da yayi da ita bai gama sakinta ba, a hankali ya rabata da jikinsa ya dauki takardar ya bata, ta kalli content din ciki wnda ya nuna cewa she's 4weeks pregnant, ya riƙe haɓarta ya ɗago kanta ya kalli cikin idonta yace "ynxu kin yarda na cilla kwallon kin caɓe..?", ta saukar da kanta wni murmushi na shirin kufce mata kawai ta faɗa ƙirjinsa, ya rumgumeta sosai yana patting bayanta yace "I Love you..", after few seconds tace "Me too". Tarairaya na musamman Nurain yake gwadawa Hajar, daga tayi motsi zai tmbya me take so, ita dai tin tana mamaki harta dena don taga abin nasa azimun ne, toh wai daman hka maza suke yiwa matansu idan sunada ciki ko kuma nata mijin ne yake mata hka, ta lura ma lfyrta yafi damuwa da ita snn kuma he also love the unborn baby. ɓangaren Khausar kam tin tna jiran yaxo ya duba mata chaptern da ta gama rubutawa jiya har ta gaji ta haƙura, ga takaicin uban wanke wanken da tayi, sai pass 11 snn Nurain ya tuna da wata Khausar, gashi fitar da yayi zuwa mosque da siyo ma Hajar abinda take so bai ganta ba a palour, tinda gobe Friday kuma ba zai fita ba sai ya duba mata. Washe gari Khausar na zaune palour ita kaɗai sai kace mayya, yau kam palourn tsaf tsaf don bata hargitsa ba tana tsoron kar Nurain yace ta gyara, gashi yau tinda ta sauko palour ba taga Hajar ba, Nurain din ma tin safe da suka haɗu a kitchen yana haɗa coffee ita kuma taje dafa breakfast bata sake ganinsa ba, ƙarar mota taji alamar an shigo compound, da sauri ta wurgar da wayar da take latsawa ta kunna Laptop dake side dinta, dman da zai fita mosque yace idan ya dawo zasu cigaba, after 10mins taji ƙarar bell, da sauri ta tashi ta nufi door ta buɗe, ga mamakinta sai taga ba shi bane Hajjaju Hajiya ce riƙe da sandarta a bakin ƙofar bayanta kuma Farooq, Farooq ya ringa kallon Khausar da mamaki don bai taɓa zaton zai ganta a nan din ba, Hajiya ta kalli Khausar ta saman glasses dinta tace "Ah a ya naga hka, baƙa matar Usuman din ta koma ne...", Farooq yace "A'a wnn ai ba ita bace Khausar ce fa... ya dai idon naki Amarsu wnn din ma ai ba baƙa bace", Hajiya tace "Akan matar Usuman ai baƙa ce", Khausar ta ɗan russuna tace "Hajiya snnu da zuwa", Hajiya tace "fara bani hanya na wuce idan na yada kwankwasona ma gaisa", tini Khausar ta matsa gefe, Farooq na bawa Hajiya support da kuma sandarta ta samu ta shiga palourn, Khausar ta mayar da ƙofar ta rufe, a hankali Hajiya take takawa tana cewa "kar ka jani da sauri mai gidan, yanxu sai kaga ƙafafuwan sun lankwashe duk holoƙwayen banza ne..", Farooq dai bai ce komai ba ya kaita har kan sofa ta zauna, ya ajiye mata jakarta a gefenta, Khausar ta ƙaraso ta zauna kan carpet ta gaida Hajiya, Hajiya ta kafeta da ido kafin ta amsa, Khausar ta gaida Farooq wnda yake ta kallonta ta ƙasan ido, Farooq ya amsa snn yace "yasu Umma..?", tace "Suna lfy alhmdllh", yace "Masha Allah... ya karatu..?", tace "fine alhmdllh..", yace "Good" daga haka bai sake cewa komai ba, bayan wni lokaci Khausar ta tashi ta shiga kitchen Hajiya ta bita da kallo, few seconds ta fito da tray mai dauke da ruwa da lemo ta ajiye musu, Hajiya na kallon trayn ruwa da lemon tace "Wnn aiki ai na matar gida ne, tinda nazo banga gilmawarta ba..", Khausar tayi murmushin yaƙe tace "Ai tin safe bata sauko ba Hajiya", Hajiya tace "Au tun safe bata sauko ba... ke din nan kika kwan..?", Khausar ta gyaɗa kai, Hajiya tace "Eh ba shakka", Farooq ya ciro wayarsa yayi dialing numbern Nurain, tana fara ringing Nurain ya ɗaga yace "Why punk..?", Farooq yace "We are here already..", Nurain yace masa ai ya kusa isowa, Ai kam bbu wani jimawa Nurain ya shigo palourn, Hajiya ta dire kofin ruwan da take sha tace "Au toh ashema Usuman din shima bayanan", Nurain ya ƙaraso inda take ya gaida ita, bata ma amsa ba tace "Ina matar taka ne Usuman naxo gida tin ɗaxu ban ganta ba..", Nurain ya kalli stairs sai kuma ya juya ya miƙawa Farooq hannu sukay musabaha, bayan sun gaisa da Farooq ya tashi ya haura sama, bai sameta a part dinsa da ya barta tana bacci ba don haka ya nufi room dinta, zaune ya sameta kan stool tana rubbing lotion, ya sakar mata murmushi yace "kin tashi Baby..?", ta gyaɗa kai tana kallon manyan kayan jikinsa, ya isa inda take ya dafa goshinta yace "you're okay..?", ta gyaɗa kai, yace "Iron Lady tazo tana jiranki a ƙasa", tace "Tom", ya sunkuya yayi pecking cheek dinta snn ya fita, sharp sharp Hajar ta gama shiryawa ta saka hijab dinta ta fita, walking slowly take sauka daga stairs duk da garau take jin kanta, Khausar ta ɗan kalleta sai kuma ta ɗauke kai, direct wajen Hajiya Hajar ta nufa, Hajiya ta ringa kallonta har ta iso gareta, cike da ladabi Hajar ta gaida Hajiya, Hajiya ta amsa tana kallonta da kyau tace "ya naga kina tafiya lagwai lagwai sai kace mara laka ince dai lfy ƴar nan...?", Hajar tace "lfy na lou Hajiya..", Hajiya tace "Toh madallah ai ita ake so ta daure", sai a lokacin Hajar suka gaisa da Farooq, Hajiya ta kyallaro Khausar dake can ƙarshen carpet lokaci guda ta kalli Nurain tace "Wai Usuman in ma hutun za azo gidanka ai sai ƙanana suzo ba wai firɗa firɗa ba, toh ita matar taka nawa take da za a kawo mata gansamemiyar budurwa ta zauna da ita, wnn ai sai a rasa matar gidan a cikinsu, ina ma dai laifin yara ƙanana kamar na Sakinatu wnda baza a sa yarinya whla ba, idan ta sulala musu ƴar taliya ma suka ci shknn, amma an kawo mata wcca saita zage damtse kafin ta dafa mata abinda za taci, sai kace daga garin gaɓa gaɓa", Nurain ya shafa kansa yace "Hajiya karatu ne muke yi tare da ita", Hajiya ta kallesa tace "Toh wai kai din malamin makaranta ne, naga dai farke cikin bil Adama ka karanta", yace "Eh ai nima zan iya duba mata..", Hajiya tace "A gsky ana ƙwarar yarinya, ya za ai a kawo mata gardiya cikin gida haka kurum fisabilillah", tini Khausar ta sulale ta bar palourn ta fita compound, Farooq ya bita da kallo bayan ya lura da reaction dinta, murmushi Nurain yayi da yaga Khausar ta fita, lallai ba tasan Hajiya ba, ai ba a ɗaukar maganar da ta faɗa personal in ba haka ba ka sha haushi, Hajar dai ta saukar da kanta don wata dariya ce ta taho mata wai gansamemiya, Hajiya ta cigaba da zuba sababi wai Khausar tayi girma da zama a gidan, shi dai Nurain tin yana ƙoƙarin nusar da ita har ya gaji ya dena don yaga ba fahimta za tayi ba, toh mene don Khausar ta zauna a gidansa, shi dai baiga aibun haka ba, ko shekara za tayi shi dai bazai ce ta tafi ba, Farooq ya tashi zai fita, Nurain yace "ina zuwa..?", Farooq yace "just a minute" da haka ya buɗe ƙofa ya fita, Hajiya ta janyo jakarta ta ciro kwalbar man zafi tana kallon Hajar tace "yi taimakon da kika saba wllh kamar zasu tsinke". Can jikin flowers Farooq ya hango Khausar bayan ya fita compound, har ya isa kusa da ita ba ta sani ba, handkerchief ya miƙa mata fuskarsa a sake yace "forget about what Iron Lady said and don't take it personal", ta ringa kallonsa sai kuma ta amshi handkerchief din ta goge hawayen da suka zubo mata......✍️ 💛 HAJAR 💛 {87..} Bayan tafiyar su Hajiya Hajar ta haura sama abinta, don tare suka fita da Nurain shi kuma zaije gidan Mami, ita da Khausar kawai aka bari a gidan, kuma daman tinda ba shiri suke ba meye na zama tare da ita, tsaf zata iya irga mganar da sukay da ita tin zuwanta gidan, room dinta ta shiga ta dauki wayarta dake kan chest of drawers, tana kunna wayar taga missed call din Oum Sulthan, tini tabi bayan kiran, kiran na shiga Oum Sulthan ta ɗaga, bayan sun gaisa Hajar tace "ya baby Sulthana..?", Oum Sulthan tace "Arigimatu gata nan na samu tayi bacci", Hajar tace "bana kusa da wayar ne lokacin da kika kira", Oum Sulthan tace "Ohk it's fine, daman cewa zanyi kayanki sun zama intact, jiya da daddare ragowar kayan suka sauka..", Hajar tace "Okay toh..", Oum Sulthan tace "na bawa mai aikina ta kawo miki ynxu..?", Hajar tace "Eh", Oum Sulthan tace "Okay ynxu zan turota..", Hajar tace "Toh ngd sosai..", Oum Sulthan tace "nice da godiya", da haka suka gama wayar, tini Hajar ta tashi ta buɗe ƙofa ta fita ta sauka downstairs, Sofa ta samu ta zauna bata ko kalli position din Khausar ba, wani dogon tsaki Khausar taja ta wni ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, ina irin itace mai palourn tana yiwa ƴan aiki izza, daman haushi take ji tin jiya da ta sha uban wanke wanke, sosai yin wanke wanken nan ya mata ciwo, gashi kuma yau Hajiya taxo tana wni ce mata gardiya, amma sai wni lallaɓa Hajar take sai kace wata ƴar shugaban ƙasa, ƴar ghetto area din mai kai a tukunya ake lallaɓawa, ita dai Hajar ba tace mata ta tafasa sauke ba, in dai tsaki ne ta shekara tana yi tinda ba fito mata zaiyi a jiki ba, kamar yacca Anty da Umma sukay mata nasiha akan tayi haquri a gidanta kar ta bari soyayyar da dangin mijinta suke mata ta kufce toh ko insha Allah zata kamanta, wnn dai mai shafaffen ƙirjin sai kace Allon mayya ba zata zame mata cikas a dangin mijinta ba, ta riga ta zuba banza a kwandon shara, Hajar dai na zaune palourn tana jiran mai aikin Oum Sulthan, after 10mins da zamanta sai ga ƙarar bell, Hajar ta tashi taje ta buɗe mata, da ladabi mai aikin ta gaisheta snn ta miƙa mata ledar hannunta, Hajar ta amshi ledar tace "kice mata ngd", mai aikin tace "Toh" da hka ta juya ta tafi, Hajar ta kulle ƙofarta, tana juyowa taga Khausar ta zuba mata ido, ba tasan lokacin da ta juya manyan idanunta ba ta wuce ta haura sama abinta, room dinta ta shiga ta buɗe ledar, sosai turarukan suka tafi da imaninta sbd ƙamshinsu, turaruka ne ta siya a wajen Oum Sulthan kala kala, na gida da nata da na kabbasa snn da kuma na gashi sai kuma na tsugunno, ga kuma humra wajen kala shida duk ta siya, ita dai burinta tayi ƙamshi ita da gidanta, tin last week tayi ordern kayan a wajen Oum Sulthan kuma tini ta biyata kuɗinta cash, tanada kuɗi sosai a wajenta don duk month sai ya ajiye mata envelope ta kuɗi kuma ba ƙadan ba, kawai ajiyesu take don bata san amfanin da za tayi dasu ba tinda bata rasa komai ba, burner din dake room din ta jona ta ɗebi turaren ta zuba, haba ai kafin kace me wni ƙamshi mai dadi ya fara tashi, da kwalbar turaren ta fita ta shiga ɓangarensa ta zuba turaren a burners din bedroom da palour, da haka ta fito ta sauka downstairs, shima dai hka ta jona burner din palourn ta zuba turare, ƙamshi na fara tashi Khausar tayi gyaran murya sai kuma ta tashi tace "meye hka ina zaune a waje kinzo kin bunka min hayaƙi, bana son turaren wuta...", Hajar ta juya idanunta tace "Oho idan ba kya so sai ki tashi ki bar wajen don baki isa ki hanani sakawa gidana turaren wuta ba", Khausar ta haɗe fuska tace "dalla malama kashe wnn ƙaurin..", Hajar tace "you can't tell me what to do in my house, ki bari idan kinje nki gidan sai kiyi yacca kike so amma ba dai a gidan mijina ba" tana gama faɗin hka ta maka mata wata shegiyar harara ta haura sama, da sauri Khausar ta matso bakin stairs din tana cewa "hey come back here and face me ba wai ki haura sama ba", Hajar ta juyo tace "A'a wllh ni inada aure bazan biye miki ba" tini ta ƙarasa hawa stairs din ta shige ɗakinta, a matuƙar fusace Khausar taje ta fige burner din daga jikin socket, hakan bai mata ba ta ɗaga burner din ta damfara da ƙasa. Wajen ƙarfe biyar da rabi kiran Nurain ya shigo wayar Hajar, turo baki tayi ta kara a kunne, yace "how are you doing My Baby..?", ta juya idanunta tace "fine alhmdllh My Moon", yace "have you eaten..?", ta girgiza kai tace "Ni na ƙoshi..", yace "Toh me kike so na taho miki dashi..?", tace "Algwaluma da green guava..", ya waro ido yace "Baby wife wnn fa duk ba solid food bane", da muryan shagwaɓa tace "Uhmm ni su zanci..", ya sauke numfashi yace "Toh shknn... Please Baby ki zaɓi wni abun ko kinaso Baby love ta zauna da yunwa..?", tayi murmushi da taji yayi inkiyar mace toh wa yasan mene ne ai tukunna dai, tace "Zanci Noodles", yace "Good you want me to order it for you ko kuma da kanki zaki dafa?", tace "zan dafa da kaina", yace "Ohk.. take care of yourself for me", tace "Sure", yace "I Love you..", tayi murmushi tace "Same". Sai ƙarfe shida snn Hajar ta wuce kitchen da nufin dafa Noodles din da tace, tana shiga kitchen din taji bata son cin Noodles din ta fita daga ranta, fridge ta buɗe ta yanko watermelon ƴar madaidaiciya ta yanka ta zuba a cikin blender, madaran gari mai yawa sosai ta zuba da Sugar kaɗan, ta haɗa ta markaɗe with high speed bayan ta zuba ice block, A kullum sai tasha wnn haɗin banda jiya da shekaran jiya da ta rasa appetite, Milk shake din tasha tayi nak don taji daɗinsa sosai. Da daddare wajen ƙarfe takwas da minti goma Hajar ta sauka downstairs walking gently, waro ido tayi ta ƙarasa cikin palourn tace "Moon kana nan daman..?", yace "yeah kin gama gyaran..?", tace "Eh" da hka ta juya ta shiga kitchen, bata jima ba ta fito da plate da kuma green guava da ya siyo mata ɗaxu, kusa da shi ta zauna ta fara cin guava din, ya ɗan kalleta yayi murmushi, few minutes saiga footsteps ana saukowa daga stairs, ita dai Hajar ko kallon stairs din ba tayi ba tana cin guava dinta a hankali, Khausar ta ƙarasa saukowa da shirin fita, black Abaya ce a jikinta da handbag, cikin palourn ta iso ta zauna opposite to them, tace "Yaya dman ina so in gaya mka ne zanje shopping akwai abubuwan da zan siyo...", Nurain ya kalli makeken agogon palourn yaga ƙarfe takwas da minti ashirin, yace "ke kaɗai zaki fita shopping din..?", tana wasa da ring din hannunta tace "Eh ai baxan daɗe ba, bolt din da ta kaini ce ma zata dawo dani insha Allah..", yace "Ohk.. kin kira bolt din..?", tace "A'a ynxu dai zan kira", yace "Ohk" sai kuma ya juya ya kalli Hajar "Baby wife ko zamu fita shopping ki siyo chocolates..?", sai a lokacin Khausar ta kalli Hajar sai kuma ta taɓe baki, Hajar ta ɗan fakaici kallon Khausar sai kuma tayi murmushi tace "i like it Moon..", yace "Ohk alright get ready..", tace "Tom", Nurain ya juya ya kalli Khausar yace "bari mu fita shopping din tare", tace "Ohk", Nurain da Hajar suka haura sama Khausar tayi zaune palourn tana jiransu, shi ya wuce part dinsa ita kuma ta shiga room dinta, wni tunani tayi kawai ta buɗe ƙofa ta fita ta shiga ɓangarensa, a palour ta tarar dashi da waya kare kunnensa, kawai ta wuce bedroom, Closet dinsa ta nufa ta buɗe, komai intact tinda yau 4days knn da ta gyara masa, section din shirts ta buɗe ta ɗauki wata fara ƙal snn ta rufe ta fito, still dai wayar yake bai gama ba, ya kalli hannunta bai dai gane abinda ta ɗauka ba, Hajar na shiga room dinta ta faɗa wanka, bata wni jima ba ta fito ɗaure da towel, da kolaccan da humran da ta siya wajen Oum Sulthan tayi amfani ta shafe jikinta, habawa ai tini wni mahaukacin sassanyan ƙamshi ya bulale ɗakin, ta warware gashinta tayi boy and girl, uhmm maimakon ta saka manyan kaya tinda fita za suyi saita dauki white shirt dinsa da ta dauko ta saka, a rabin cinya shirt din ta tsaya mata, ta kalli kanta a mirror snn ta shafa tummy dinta tayi murmushi, ita tasan me ta shirya shiyasa take wnn murmushin, ta feshe jikinta da perfumes kafin ta nufi door walking like a cat, tana buɗe ƙofa taga Khausar ta nufi hanyar bangarensa, habawa ai da gudu tasha gabanta tayi banga banga a bakin ƙofar ɗakin ta riƙe ƙugu tace "malama ina zuwa hka kanki tsaye..?", Khausar ta gyara tsayuwarta cike da mamaki take kallon Hajar from head to toe, ta haɗe fuska tace "hey... kin isa ki hanani shiga wajen Yaya na..", Hajar ta buɗe baki da irin rainin hankalin nan tace "Ayyah a iya sani na nasan mijina bashi da wata ƙanwa da ta wuce Noor don hka ja jiki wllh bazaki shigar min turakar miji ba", Khausar was more than shock tama kasa cewa komai, can dai tace "ba a auro wcca zata hanani zuwa wajen ɗan uwana ba wllh, before I count 10 ki matsa kafin nayi smashing dinki..", Hajar ta taɓe baki tace "kiyi tafiyarki shopping dinki ke kaɗai ni Mijina baya fita da daddare, may be kafin ki gama irgen kin isa compound" tana gama faɗin hka ta zuge door din, Khausar ta kai hannu zata hanata aikam ta haɗa da hannun nata, ƙara Khausar tayi ta koma da baya, Hajar ta ɗan buɗe ƙofar tace "Am not a psycho da zan bar gardiya ta shiga ɓangaren mijina", ta banke door din snn ta saki curtain ta bar wajen tana juya lulu eyes dinta, wllh ba za aje shopping din nan ba, saita nuna mata limit dinta, ita ta isa tazo gidanta tana mata iya shege da ƙirjin sai kace babe, da tafiyar mage ta nufi bedroom, tsaye tayi bakin ƙofa tana kallonsa, tsaye yake gaban bed already dressed up, ta kalli kayan jikinsa taga dai ba Pajamas bane, ya juyo ya ɗan kalleta yace "Baby wife ya baki shirya ba..?", shiru ta masa ta kalli gefe, ta turo baki sai kuma ta rufe ido ɗaya da bayan hannu ta fara shessheƙa, ya waro ido yace "what happened..?", nan ma bata tanka masa ba ta cigaba da shessheƙar kuka, ya zauna gefen gado yace "come and tell me Baby", a hankali ta taho tana murza idonta da bayan hannu, tana zuwa ta ɗale kan cinyarsa ta rufe fuskarta a ƙirjinsa ta cigaba da kukan, ya ajiye ajiyar zuciyar da bai shirya mata ba bayan ya shaƙi ƙamshinta, ya shiga patting bayanta yace "Mene ne..?", a hankali tace "Ni cikina ne yake ciwo", ya zura hannu cikin rigarta ya shafa cikin yace "here..?", ta gyaɗa kai, yace "Sorry.. gashi baby love bata fara kicking ba bare nace ita ta takura miki", tayi shiru ba tace komai ba tana sake shigewa jikinsa, shi kam gaba ɗaya ƙamshinta da laushin jikinta ya fara saukar masa da kasala, yayi ƙoƙarin ɗagata amma taƙi ta sake komawa ta kwanta, yace "magani fa zan dauko miki Baby wife..", ta maƙe shoulder tace "Ni A'a", yayi chuckling sai kuma ya miƙa hannu ya janyo pillow ya koma da baya ya kwanta, tini tabi jikinsa ta kwanta itama, after few minutes ya ɗago kanta yana kallon fuskarta, wni irin juyi yayi ya kwantar da ita kan gadon ya haɗe forehead dinsa da nata, daga nan kuma zance ya sauya. Tin Khausar na jira har ta haƙura ta koma ɗakin da aka sauketa, ba ƙaramin haushin Hajar ta shaƙa ba a wnn ranar, tinda take ba'a taɓa mata abinda ya ƙona mata rai kamar hka ba, zaune tayi kan gado bayan ta saka pajamas dinta ta cire Abayan, wni ƙululu mai shegen tauri ya tsaya mata a throat, ba tasan lokacin da hawaye ya fara zarya a cheeks dinta ba, ta koma ta kwanta ta rufe fuskarta da pillow tana hawaye. Washe gari ranta busu busu ta tashi, tayi zamanta a ɗaki taƙi fita sai kace wata sabuwar Amarya, tabbas idan ta fita ta haɗu da Hajar toh wllh saita tata mata rashin mutunci mai wasali, wajen ƙarfe sha ɗaya Khausar ta tashi ta shiga wanka, tin ƙarfe takwas da ta tashi take zaune tana latsa wayarta, tana gama shiryawa ta buɗe ƙofar ɗakin ta fita, kanta tsaye ta sauka downstairs, sosai taji daɗi da taga bbu kowa a ƙasan don haka ta buɗe kitchen ta shiga, tsaye tayi bakin ƙofa tana kallon Hajar dake tsaya gaban gas, Hajar kam da taji ƙarar ƙofa tasha shine ba tare da ta juyo ba tace "Moon har ka siyo sausage din..?" sai kuma ta juyo, ido huɗu sukay da Khausar, Hajar ta ɗauke kanta ta cigaba da juya soup din dake kan wuta, Khausar ta taɓe baki ta ƙarasa ciki, cabinet ta buɗe ta ɗakko small pot ta wanke snn ta kunna tap ta zuba ruwa rabin pot din, gaban gas kin ta matsa ta jera da Hajar wcca ba ta sake mata second look ba, Khausar ta kama handle din tukunyar dake kan wuta tinda na plastic ne ta ajiye gefe, pot din da ta zuba ruwa ta ɗauka ta dora a wajen ta koma gefe, mamaki yasa Hajar ta saki baki sai kuma ta juya ta kalleta, Khausar ta rumgume hannaye tana wni karkaɗa kai, haɗe gira Hajar tayi ta juya ta sauke tukunyar ta mayar da ta ta, Khausar ta sake matsowa ta dauke ta mayar da ta ta, saida sukay haka sau uku, A karo na huɗu Hajar tace "meye hka..?", Khausar taja wni dogon tsaki tace "Abinda yayi hka shi yayi hka, a nan nayi niyya zan dafa abinci...", a fusace Hajar ta juyo tace "wllh baki isa..." sai kuma tayi shiru sbd Nurain da ta hango a bakin ƙofa, zuwansa knn wajen, da sauri Hajar ta saukar da kanta tayi kamar bata gansa ba, Khausar kam ta juyawa ƙofar baya don hka bata san yana wajen ba, Khausar tace "baki isa kimin gage a gidan Yayana ba na gaya miki, ke asuwa bloody witch, ke kin isa zanyi girki ki hanani, naga dai Yayana ne ya sayi Foodstuffs din kuma yayi refilling gas, ba daga wnn slum din aka kawo ba, i mean wnn rubabben gidan naku...", Hajar ta rufe fuskarta da hannayeta kamar gaske ta fara shessheƙa a hankali tace "Khausar me na miki kike gayamin wnn mganar..?", Khausar ta taɓe baki tace "Ai ba ƙarya nayi ba, kinxo kin wani bararrashe a gidan Yayana sai kace na ubanki, just know this cewa nan ba gidanku bane da zaki ringa wni zaƙewa, anytime za'a iya kaɗaki ki koma can ghetto area a cigaba da tallan gyaɗa...", habawa ai Nurain kasa withstanding wnn words da take sukar matarsa dasu yayi, tini ya daki ƙofar kitchen din ya shigo ya daka mata wata tsawa mai burga ƴan hanji, ita kanta Hajar saida ta tsorata ta koma can karshen bango tana rarraba ido, tini jikin Khausar ya hau ɓari har lips dinta ma rawar suke, Nurain was burning in and out don wllh yafi Hajar din ma jin zafin maganganun, ya tsuke piercing eyes dinsa yana kallon Khausar yace "Are you talking to my wife that way..?", ta girgiza kai tace "Yaya please let me explain... i.", da ɗan ƙarfi ya gwaɓe mata baki yace "Shut up... you must be Mad", tsabar azaba saida Khausar ta ɗaga ƙafa ɗaya sai kace mai shirin kwaso shoki ta kai both hands ta rufe bakinta da take jin tamkar zai faɗo ƙasa, kukan ma kasawa tayi sbd azaba don ji take kamar harshenta ya datse gida biyu, Hajar na maƙale da bango sai zaro ido take, kawai saita tuna ita azabar da ta sha lokacin daya gwabje mata baki, amma tasan Khausar sai ta fita jin jiki, Khausar ta haɗiye jinin da ya taru a bakinta ba tare da tasan ta haɗiye din ba kafin ta rushe da kuka, nan ma wata tsawar ya daka mata ya nuna door yace "get out...!!", da mugun gudu Khausar ta nufi ƙofa tana zabga tuntuɓe ta fita, Nurain ya juya ya kalli Hajar da tayi wni tsilli tsilli, da sauri ta saukar da kanta, after few seconds ya fita with speed, a ƙasa mala mala kan tiles ya tarar da Khausar tana gursheƙen kuka, da ɗaci a muryarsa yace "pack your belongings now and leave my house..", Khausar ta tashi ta nufi stairs cikin sauri tana gurɗe ƙafa, yabi bayanta da wni mugun kallo, yau da ace same parent suke da Khausar Allah kuwa saita ɗanɗana kurenta, wnn wane irin rashin hnkali ne, ko wata yaji ta yiwa irin wnn mganar sai ya tsawatar mata ballanta beloved wife dinsa, few minutes saiga Khausar da jakar kayanta ta rufe fuskarta da hijab din data saka still tana kuka, Nurain ya shafa pocket dinsa ya ciro car key, kallon key din yayi sai kuma ya haura sama don ya dauko na other car din, Hajar dake maƙale jikin ƙofar kitchen ganin ya tafi sama Khausar ce kawai ta fito, tashin farko wata dariya ta tuntsure da ita tace "Yayan naki ne da kansa ya kaɗaki gida knn, Allah sarki ynxu ai kin tantance tsakanin tsakuwa da Aya, shi Yayan naki ya gwada miki value dina, from now henceforth kar na sake ganin tsumman ƙafarki in my house, Gorilla kawai..", da haka ta koma kitchen din ta rufe ranta fess, Nurain ya sauko da sauri thick eyebrows dinsa a haɗe, ya nuna door yace "i said get out nonsense", da sauri Khausar ta fita, saida ta fita snn yabi bayanta, ya rufe ƙofar ya wuce parking space, a hankali take bin bayansa tana kuka, ya nufi motar da zai shiga ya buɗe, tana isowa yace ta shiga back seat ita da jakarta, bazata zauna a spot din wcca ta gama wulaƙantawa ba, da reverse ya fita da motar daga gidan, few minutes of ride suka isa gidansu sbd uban gudun da ya falfala, a bakin main building din gidan nasu ya tsaida motar with stern voice yace "Get out", Khausar ta lalubi handle ta buɗe ta fita, tana fita ya juya kan motarsa ya bar gidan, Khausar ta shiga main palour da gudu, lokaci guda ta zube a ƙasa ta kurma wni uban ihu sai kuma ta fashe da wni matsanancin kuka, Mami da Noor wacca zuwanta knn suka miƙe a tare, Mami ta nufi Khausar tana tmbyarta lfy, ina kawai kuka Khausar take rusawa kamar ranta zai fita, Noor tayi sauri ta tsugunna gabanta tace "What happened sister..?", Khausar ta kasa cewa komai, Mami ta ƙaraso wajen tace "What happened My daughter?"........✍️ 💛 HAJAR 💛 {88..} Noor ta ɗago Khausar ta temaka mata ta koma kan kujera, gefenta Mami ta zauna tana tmbyarta lfy, har lokacin Khausar kuka take kamar wacca uwarta ta mutu, Noor ta kalli Mami tace "ba gidan Yaya ta tafi ba..?", Mami tace "Eh can taje sbd karatunta..", Mami ta saukar da murya ta dafa kan Khausar tace "Tell me what happened dear..?", da kyar Khausar ta tsaida kukan tace "Matar Yaya ce..", shiru Mami da Noor sukay suna kallonta don basu fahimci me take nufi ba, Noor tace "wai Hajar..?", Khausar ta gyaɗa kai tace "Eh ita", Mami dai kawai kallon Khausar take kafin tace "me Hajar din ta miki..?", Khausar ta nuna bakinta da ya fara suntuma gashi yayi jajir tace "kunga fa abinda ta min" sai kuma ta sake rushewa da kuka, Noor ta kalli Mami don taga reaction dinta, Mami tayi ajiyar zuciya don bata gane me Khausar ke nufi ba amma dai taga bakinta ya kumbura alamar ya fashe, Mami tace "Khausar ki nutsu ki gayamin me ya faru", Khausar ta ɗan tsagaita kukan tace "hankaɗoni tayi daga sama shine na faɗo na fasa baki and my ankle is also paining me...", Mami ta zaro ido tace "innalillah... was it a coincidence or intensional..?", Noor dai kasaƙe tayi tana kallon Khausar da mamaki, kawai ji tayi bata yarda da mganar ba, Hajar ba zata turo Khausar daga stairs ba gsky saidai idan wni abun ne ya faru, Khausar ta girgiza kai tace "No Mami tana sane ta turoni sbd mun sami slight misunderstanding kuma na bata haƙuri ashe bata haƙura ba, gashi tinda naje gidan ta mayar dani house help, nice nake komai ita nata kawai girki kullum tana upstairs, bata bani abinci idan ta dafa saita kwashe ta kai room dinta, idan Yaya ya dawo ya tmbyi naci abinci sai tace Eh, shine ni kuma na fara shiga kitchen ina dafawa da kaina, da ta lura ina shiga kitchen din shine ta rufe store ta wuce da key din, most of the time saidai nasha tea ko kuma naci biscuit dina dana tafi dashi, shine yau ta manta bata rufe store ba ni kuma na samu chance na dafa Noodles, zan wuce sama da Noodles din na tarar da ita zata sauko, shine tace wai me yasa na shigar mata kitchen ni kuma na bata haƙuri, bayan na gama cin Noodles din ne zan kai plates din kitchen ashe tana bayana shine ta hankaɗoni ƙasa..." ta fashe da kuka tace "ban san me ya faru ba kawai Yaya yace na haɗa kayana na bar masa gidansa tinda matarsa nake yiwa wulaƙanci, am very sure itace ta haɗamin sharri a wajensa..", Mami tace "ya isa.. sorry ki dena kuka kinji", da haka Mami ta shiga share mata hawayen cheeks dinta, deep down her mind tana jujjuya mgnar Khausar, Noor dai tsabar shock ta kasa cewa komai, Mami ta shafa kan Khausar tace "kinyi breakfast ko a kawo miki..?", Khausar tace "A'a..", Mami ta ɗanyi shiru tana wni lissafi, ynxu fa tace mata ai ta dafa Noodles shine ma abinda yasa suka samu misunderstanding da Khausar, Mami tace "Ohk... bari a kawo miki kinji, wuce part dina ki zauna kafin a kawo miki..", Khausar tace "Toh" ta tashi a hankali ta wuce part din Mami, Mami ta bita da kallo hakama Noor, Noor ta ɗan kalli Mami sai kuma tace "Our Mami plxx karki yanke hukunci sai kinji ta bakin both parties..", Mami tayi ajiyar zuciya tace "ki haɗawa ƴar uwarki breakfast ki kai mata..", Noor tace "Sure", Mami ta tashi ta shiga great room din Abba, Noor kam kitchen ta shige, Laure ta saka tace ta jere mata breakfast a tray, tini Laure ta gama haɗa komai, Noor ta ɗauki trayn ta fita dashi, part din Mami ta shiga ta tarar da Khausar kwance kan doguwar kujera, Noor ta ajiye trayn tace "sister ga abincin..", Khausar ta miƙe zaune tace "Thank you", Noor tace "na haɗa miki shayin..?", gyaɗa kai Khausar tayi, tini Noor ta haɗa mata tea mai kauri ta miƙa mata, Khausar ta amshi mug din ba tare da ta sha ba tace "yaushe kika zo..?", Noor tace "ban daɗe da zuwa ba..", Khausar tace "Ohk.. ya husby naki..?", Noor tayi murmushi tana cire veil din Abayarta tace "fine Alhmdllh shi yayi dropping dina ma, bai daɗe da fita sun gaisa da Mami ba kika shigo", Khausar ta gyaɗa kai ba tace komai ba, Noor tace "sister kin dai ƙi yarda da Aliyu ko..?", Khausar ta yamutsa fuska tace "waye kuma Aliyu..?", Noor tace "Aliyu fa abokin Abdul dina..", sai a lokacin Khausar ta gane kuma har waya ma suna yi kwanaki amma dai ynxu tayi blocking contact dinsa, Noor tace "he is a good person sister", Khausar tace "Ohk i will think about it" da haka ta kai cup din shayin baki tayi sipping, habawa ai da sauri ta mayar dana bakin nata cikin cup din shayin tsabar azabar da taji, kamar fatar bakinta zata ɓaɓɓako haka taji, tini ta ajiye cup din idonta ya ciko da ruwa, Noor tace "ba zaki iya shan shayin ba..?", da sauri Khausar ta gyaɗa kai tace "it is paining me so much, I can't take the tea", Noor ta ringa kallonta, can dai tace "Sister are you sure about what you told Mami earlier..?", Khausar tace "Sure..", Noor ta gyara zama tace "Ni dman tintini nasan jininku bai haɗu da Hajar ba sister, a time din bikina dai kece me kawo problem kina mata abubuwa amma ban san this time around me ya faru ba..", Khausar ta ɗanyi tsam tace "Toh me na mata lokacin bikin naki..?", Noor ta juya hannu tace "Nope bance kin mata komai ba amma ke kinsan yacca kikai mata", a ɗan fusace Khausar tace "wai me kike nufi ne..?", Noor tace "A gsky sister baki kyauta ba, koda abinda kike faɗa gsky ne toh baki kyauta ba, Mami fa uwar Mijin Hajar ce me yasa za ki faɗi irin wnn maganganun akanta a gaban Mami, kin san irin fitinar da hakan zai kawo..", a bit pissed up Khausar tace "Ohh i see dman ko time din bikin naki na lura ita kike backing, ynxun ma kinaso kice laifina ne knn?", Noor tace "Not at All.. kawai dai you shouldn't have told Mami all this...", Khausar tayi tsaki tace "Enough sister, ni dai kawai ki barni, ki bari idan ke aka fasawa baki sai kice hakan nagani" tana gama faɗin hka ta miƙe ta fita, ba ta jima ba ta dawo da jakar kayanta ta shiga room din da take zaune a gidan. Sam Mami bata kira Nurain ta tmbyesa ba'asi ba, tasan definitely zai zo da yamma toh saita masa mganar, kuma dman ita bata yanke hukuncin cikin fishi saita huce, gashi kuma wnn abune da ya faru na farko don hka dole sai ta tabbatar kafin ta ɗauki wni action din, 6 months knn da Hajar ta kasance daughter in law dinta bata taɓa jin wata matsalar daga gareta ba sai wnn moment din, daga side din ƴan uwa ma ba taji an faɗi aibunta ba saima kirkinta da ake faɗa, Iron Lady ma kaɗai ta isa hujja don ita tamkar littafi take bata ɓoye komai, gashi dai tinda take da Hajiya ba ta taɓa kawo mata complain din Hajar ba, jikokinta kam kullum sai tace ga abinda wane yayi mata, Mami dai bata sake yiwa Khausar mgnar ba tana jiran yamma Nurain yaxo, ai kam biyar saura few minutes Nurain ya iso gidan, ko a fuska Mami ba ta nuna masa komai ba har suka gaisa kamar kullum, ta tmbyesa Hajar, yace mata tana lfy, bayan wni lokaci Mami ta nisa tace "Sai kuma baka kira kaji ya yarinyar mutane tazo gida ba", ya ɗan tattare gira cause bai gane ba, har ga Allah ya manta da wta halitta wai ita Khausar, Mami tace "Khausar da ka kora daga gidanka baka kira kaji lfy tazo ba..", Nurain ya sauke numfashi baice komai ba, Mami ta haɗe gira tace "ka taɓa jin ranar da Abbanku ya taɓa korar ɗan uwansa daga gidansa ko kuma ni ka taɓa jin nasa ya kori wni nasa...?", ya ajiye numfashi yace "A'a Our Mami..", tace "wato baka taɓa ji ba sai kai tattabara sarkin ƴan aure shine zaka kori ƴar uwarka a gidanka sbd matarka ko..?", yayi ajiyar zuciya yace "Mami please do you know what happened..?", tace "if i didn't know how will I asked you such question Uthman..", ya shafa kansa bai ce komai ba, nan Mami ta zayyana masa kaff ƙaryar da Khausar ta giggilla mata, tsabar mamaki saida wni murmushin gefen baki ya kufce masa, Mami ta murtuke fuska tace "You think it's a joke ba..?", ya girgiza kai yace "Ƙarya take... wllh ƙarya take Mami, store din nan kullum a buɗe yake infact ma bbu key a jikin door din, keys din na wajena, kuma ina shiga kitchen din anytime to make a coffee ban taɓa ganin store a rufe ba, mganar abinci kam ƙarya take da kanta take dafa abinda take so taci, mganar ma ta cillota daga stairs ƙarya take nine na bigeta, mganar ta zama house help ƙarya take shima sau ɗaya ta taɓa share kitchen da palour kuma shima nina sakata, All what she said is a lie", Mami ba tace komai ba kawai kallonsa take, tashi tayi ta shiga room din da Khausar take, tana tare da Noor a room din, Mami ta kalli Khausar tace "kin iya shan Oat din..?", Khausar tace "Eh na sha da ya huce..", Mami tace "Ohk come with me..", a bazata Khausar taji zuciyarta ta buga haka kurum, da kyar tace "Toh", Noor tace "Mami kamar naji muryan Ya Nurain shine yaxo..?", Mami tace "Eh", Noor tace "bari naje mu gaisa" da haka tabi bayan Mami suka fita, ita kam Khausar wani irin kullewa cikinta yayi da taji Mami tace Nurain yaxo, da kyar tayi shahada ta fita walking slowly, kanta a ƙasa ta shiga palourn ta zauna kan carpet kusa da kujerar Mami, a fakaice ta kalli Nurain da suke mgana da Noor tace "Yaya ina yini..", bai ko kalleta ba yace "lfy", After few minutes Mami na kallon Khausar tace "Dear ki faɗi duk abinda kika gayamin da safe, me ya faru da kike je gidan Nurain ki faɗa shima yaji don yace bai sani ba", daram zuciyar Khausar ta buga ta sunkuyar da kanta, Nurain kam tini ya zuba mata piercing eyes dinsa yana jiran tayi mgana, sam Khausar taƙi cewa komai sai murza hannu take, Mami tace "Uhmm talk now..", nan ma Khausar tayi ƙumus, Noor ta ɗan kalleta sai kuma ta tashi ta bar palourn ta koma ɗaki, ba yacca Mami ba tayi ba akan Khausar tayi mgana amma taƙi, shi dai Nurain kawai kallonta yke cike da mamaki, shiru palourn ya ɗauka, Mami kam tini ta rafko jirgin Khausar, Nurain yace "Ohk Mami since she won't talk let me tell what exactly happened...", Mami was more than shock ta ringa kallon Khausar bayan Nurain ya gaya mata me ya faru, Khausar ta fashe da kuka tace "Yaya dan Allah kayi haƙuri wllh sharrin shaidan ne..", ta haɗe kanta da kujera tana cigaba da rusa kuka, Mami tayi wni nazari akan hkan da Khausar tayi, tabbas ta gano dalilin da yasa take yiwa Hajar hka, Mami ta sauke numfashi tace "you may leave", Khausar ta miƙe kanta a ƙasa ta shiga ɗaki, after few seconds Nurain yace "Mami dman nace miki ƙarya take..", Mami ta numfasa tace "Naji... Amma am not in support da dukanta da kayi akan matarka Uthman, yess bata kyauta ba bai kamata ta yi wnn furucin ba, and karka sake korar ɗan uwanka daga gidanka just like that, both of them are young kamata yyi ka yiwa Khausar din faɗa ka nuna mata kuskurenta ba wnn tough action din ba", ya shafa kansa don shima sai daga baya yaga bai kyauta ba, yace "insha Allah hkan bazai sake faruwa ba Mami", tace "ywwa itama Khausar din zan mata faɗa ba kyaleta nayi ba..", Nurain yayi ta attempting sanar da Mami cewa Hajar is pregnant amma kunya ya hanasa, hka dai ya tafi bai gaya mata ba, Ai kam da daddare Mami ta samu Khausar ta nuna mata kuskurenta, bai dace ba abinda tayi snn kuma worst part of it ƙarya, snn kuma ta gaya mata cewa ynxu Hajar is part of them tinda tayi aure cikin family nasu, ynxu Hajar kamar daughter dinta take, little sister din Noor, Mami taji daɗin yacca Khausar ta amshi laifinta kuma tace bazata sake ba sharrin shaidan ne, ita dai Mami tasan bbu wni sharrin shaidan sharrin kishi ne tinda yarinyar taso Nurain a baya kuma tana tunanin son nasa ne yaja abinda take yiwa matarsa. ★Hajar ta fito daga Kitchen da plate din gasasshiyar kazar da tayi warming a microwave, ga kuma fresh milk ta ciko glass cup da ita, ko good 2hours ba tayi da cin abinci ba gashi ynxu ma ta kwaso wni za taci, shima abincin ma kwaɗayi take ci, har mamakin kanta take, kan carpet ta zauna ta baje ta fara aika kazarta tana korawa da fresh milk, ita kwaɗayin nata ma sai ita, rannan ta haɗa Popcorn da Coffee yau kuma Kaza da madara, yanka uku taci taji har ta fara ƙoshi kuma, wayarta ta ɗauka ta buɗe data ta shiga whatsapp, message ne suka fara shigowa, chat dinta da Hafsah ta buɗe don taga ma ta turo mata wni saƙon kuma voicemail ne, Online ma Hafsahn take, Hajar ta kunna voicemail din tana ji, dariya tayi ta shiga kiran Hafsah video call, tini Hafsah ta ɗaga don dman Online take, Hajar tana ganin fuskar Hafsah a screen ta sake fashewa da dariya tace "sister nidae ban gane voicemail din nan ba ki gayamin ta nan..", Hafsah ta tashi daga palour da take zaune ta shiga ɗakinsu ta kulle da key, kallon Hajar tayi tace "Wllh duk ke kika ja min..", Hajar tace "wai me naja miki bayan ban gane me kike nufi ba..", Hafsah tace "ba kin sa nayi unblocking dinsa ba da naxo gidanki..?", Hajar tace "Toh wai shi wa..?", Hafsah tace "Ahmad mna..", Hajar tayi murmushi tace "Okay ngane", Hafsah tace "Wai ɗan mutumin nan dan yaga ina ɗan saurararsa muna gaisawa har wataran muyi fira, in gaya miki shine yayi min diren mikiya, ban san dai yacca akayi ba ɗan mutumin nan kawai ya wni turo uncles dinsa wajen Abba, ban san hawa ba ban san sauka ba jiya daddare Anty da Abba suka kirani suna tmbyata wai nasan wni Ahmad, ni dae nace musu na sansa shine suka ce in tashi in tafi, sai daga baya Anty take tmbyata wai ko nice na basa chance ya turo ni kuma nace A'a, toh dai in taƙaice miki zance Abba yace zaiyi bincike a kansa idan bashi da matsala sai magabatansa suxo da kuɗin aure..", Hajar tayi wni kyakkyawan murmushi tace "Alhmdllh wnn lamari yayi min daɗi..", Hafsah ta haɗe fuska tace "Toh ni cewa nayi ina sonsa da zai min hka..", sosai Hajar tayi dariya tace "ba sai kin faɗa ba mu mun gani..", Hafsah ta juya idanu tace "Ni shiyasa ma na kashe wayar tin jiya don kar ya kira don haushi nke ji..", Hajar tace "Ah a meye haka dan Allah.. Allah yasa ma Abba yace ya turo next week Friday, mu sha biki nan kusa wllh, nan gidana zaki taho inada Oum Sulthan wcca zata mayar dake kamar kwai, ƙamshi kam ko gonar flowers albarka", Hafsah tayi kasaƙe tana kallon Hajar sai kuma tace "Uhmm nidae ban yarda ba", sun ɗan jima suna fira kuma duk tsahon lokacin nan Hafsah taƙi yarda cewa tana son Ahmad, bayan sun gama wayar Hajar tayi murmushi tace "ƴar farka zama ki saukar da kai ne", sai kuma ta tashi ta nufi kitchen. Da daddare Hajar na tsaye gaban wardrobe zata fitar da kayan bacci ta saka don already tayi wnka kwanciya za tayi, Nurain ne ya shigo, ta juya ta kallesa, kananun kaya ta gani a jikinsa instead of pajamas, ta kalli agogo taga ƙarfe goma saura, ƙarasowa yayi ya tsaya daga bayanta yace "me zaki saka ne..?", tace "night wears..", ya buɗe section din manyan kayanta ya ciro Abaya ya miƙa mata yace "wear this..", ta kalli kayan tace "dasu zan kwanta..?", ya shafa cheek dinta yace "we are going out Baby wife..", tace "Ohk", tini ta zura Abayan ta koma gaban mirror tayi rolling veil, shi dai yana tsaye yana jiranta har ta gama shiryawa, ya riƙe hannunta suka fita ɗakin tare, ita dai tasha ƴar fitar daren da suka saba ce a siyo kayan maƙulashe, compound suke fita zuwa parking space, ya buɗe motar snn ya buɗe mata front seat ta shiga, ya zaga driver seat ya shiga, kallonsa ta ringa yi har saida ya juyo sukay ido huɗu, ya ɗage gira yace "why..?", ta girgiza kai tace "bkomae", ya kamo hannunta a hankali ya shiga mirzawa sai kuma yayi pecking, tayi murmushi tace "where are we going..?", ya mayar mata da murmushin yace "you will see", da haka ya fara driving slowly suka bar gidan, tafiyar almost 20mins sukay snn yayi parking gaban wni katafaren building, shi ya fara buɗe motar ya fita snn itama ta fita, ta ɗaga kai ta karanta sunan wajen wato Baby's World, kana ganin wajen kasan sabon buɗewa ne kuma wajene da ake siyar da kaya designers masu kyau da aminci haka zalika kuma wajen ƴan ƙarya ne masu aljihu da nauyi, yace "muje Baby wife..", siyayya sosai sukay ta kayan baby from infant size zuwa 6months, ita dai Hajar ba ita tayi zaɓen ba shine ya ringa kwasar kayan, kuma duk ɓangaren da yaje sai yace a bashi na baby girl maimakon unisex tinda har yau ba'a san gender din babyn ba, uban kayan kam sai kace na triple, saida suka je wajen cashier ya biya bill snn aka musu packaging kayan, har mota aka kai musu kayan, saida suka hau saman titi Hajar tace "Moon wai wne yace mka mace ne..?", ya ɗan kalleta yace "i have strong feeling about that..", almost 11:30 suka isa gida. Washe gari Nurain ya shiga room din Hajar bayan ya dawo daga mosque, kwance ya ganta kan gado, ya ƙarasa gaban gadon yana kallonta, scent dinsa da ta shaƙa ne yasa ta buɗe idonta, ya zauna side dinta ya kwaye duvet din da ta lulluɓa, rigarta ya ɗaga ya sunkuya yayi kissing flat tummy dinta yace "Good morning princess".......✍️ 💛 HAJAR 💛 {89..} 6 MONTHS LATER ★Hajar na zaune room dinta cikin doguwar rigar Atampa wcca aka yiwa ɗinkin maternity, girman rigar ya rufe turtsetsen cikinta dake da wata bakwai, sosai cikin ya amsheta don bai muzanta mata kamanni ba sai ma wni kyau da ta ƙara, tayi wni irin haske mai kyau snn jikinta ya sake cika ta ko ina musamman ma ƙugunta, plate ne akan cinyarta mai ɗauke da dice fruits, a hankali take cakar fruits din da fork tana sha, saida ta gama shanyewa snn ta kalli agogo, ƙarfe sha ɗaya da rabi ta gani, tashi tayi daga gefen gadon da take, saida ta miƙe snn cikin nata ya sake bayyana, ta gyara rigarta da ta tattare ta nufi door da empty plate din da ta gama shan fruits, downstairs ta sauka walking gently, duk da girman da cikinta yayi bata jin nauyin jikinta, haka take sintirinta tsakanin sama da ƙasa kamar ycca ta saba kafin cikinta ya girma, ko ina na gidanta tsaf tsaf ƙamshi ya ratsa ko ina sbd azababben turaren da take bunka masa frequently, kitchen ta shiga ta wanke plate din kafin ta kife ta fito ta haura sama, room dinta ta wuce ta buɗe wardrobe ta ciro hijab da ya shiga da flowers din kayanta ta saka, wayarta ta saka a handbag ta ɗauki handbag din ta nufi door bayan ta saka flat shoe, ɓangarensa ta shiga da sallama, ya fito daga bedroom knn ta shigo, ta turo baki tace "Allah ka daɗe..", yayi murmushi yace "Afwan Momma princess", ƙarasowa yayi inda take ya riƙe hannunta ya jata zuwa kan Sofa, gefenta ya zauna yana kallonta yace "Ohh yarinyar Umma duk sanda za'a je wajen Umma tin asuba ake fara shiri", ta juya idanunta gami da turo lips dinta da suka sake ciza color dinsu, yace "Toh bari muyi daily routine namu kafin mu wuce ko..?", ta gyaɗa kai, tashi yayi ya shiga bedroom after few minutes ya fito da rechargeable Bp gauge, ya koma position dinsa ya zauna snn ya fara measuring Bp din nata, kullum ne sai ya duba cause yana sane da lokacin da jininta ya hau, farkon aurensu har ta zauna gidan Mami, Alhmdllh a kullum zai duba BP din nata yaga normal, ynxun ma dai normal din ya gani as usual, ya ɗage hijab dinta ya shiga shafa turtsetsen cikin nata yace "Hi Princess..", shafa cikin itama tayi tace "Hi Prince..", yayi chuckling yace "Princess give her a slight punch if she call you prince again..", tayi ƴar dariya tace "Ah am telling you is a boy", ya ja hancinta yace "ni kuma nace girl", ta ɗauke hannunsa daga cikinta ta gyara hijab dinta, sosai ake shan musu a tsakaninsu akan gender din unborn baby din nasu, shi yace girl ita kuma tace boy, To prolong the musu shiyasa ba'a duba gender din babyn ba a ciki wai idan yaxo ya raba gardama, shi kam yace idan baby boy ne zai bata presence, sai ƙarfe sha biyu saura suka fita compound, saida suka ɗauki hanyar gidan Umma yace "bamu siyawa Sabrah sweet ba..", tace "Ohh ai sauri muke sai next time kuma", yace "A'a fa we have to get her something", ai kam saida suka tsaya wani bakery suka sayi snacks snn suka cigaba da tafiya, Nurain yayi parking a ƙofar gidan Umma yace "Greet Umma well later in na dawo zan shigo mu gaisa", Hajar ta gyaɗa kai tace "Toh" da haka ta ɗauki ledar snacks din da handbag dinta, ya matso yayi pecking lips dinta yace "Take care..", tace "Sure Allah ya tsare Moon..", yayi nodding head yace "Ameen" sai kuma ya buɗe motar ya fita, zagayowa yayi side dinta ya buɗe mata ƙofa ta fito, tace "Moon i can do this", yace "No let me do it" da haka ya rufe murfin motar, tace "Thank you" da haka ta nufi ƙofar gidan walking slowly, saida ya tabbatar ta shige snn ya zaga ya shiga driver seat ya bar layin. Umma ta fito daga ɗan madaidaicin kitchen din gidan dake tsakar gida jin sallama, sakin baki tayi tana kallon Hajar da ta shigo, Hajar tayi murmushi tace "Ummanmu..", Umma ta kalleta from head to toe tace "La'ilaha Hajara..", Hajar ta ƙarasa ciki ta rumgumeta tace "Na'am..", Umma ta janyeta daga jikinta tana sake kallonta tace "Hajara kinyi nauyi bazaki zauna a gida ba ko..?", Hajar tace "Wata fa wajen biyu banzo ba", Umma tace "Toh ke ba kiga halin da kike ciki ba", Hajar tace "A'a Ni ba komai" da haka ta wuce ƙofar palour, Umma ta bita da kallo, Hajar na shiga palourn ta cire hijab dinta, Sabrah ta leƙo daga ɗakin Umma tace "Addah snnu da zuwa..", Hajar tace "yauwa... fito mna kike laɓewa a jikin labule", Sabrah tace "wanka nayi zansa kaya", Hajar tace "Okay", Umma ta shigo palourn ta zauna bayan ta ɗora sanwar rana, Hajar ta gaida Ummanta da ladabi, Umma ta amsa tana tmbyarta ya take, bayan wni lokaci Hajar tace "Yaya fa..?", Umma tace "Mu'azzam ya tafi Abuja wni aiki", Hajar ta waro ido tace "Abuja..?", Umma tace "Eh ai kinsan ynxu aikin nasa ba iya kano bane har wasu garuruwan suna zuwa aiki", Hajar ta gyaɗa kai tace "Toh Allah ya dawo dashi lfy", Umma tace "Ameen", Hajar tace "Nabilah ta tafi ne..?", Umma tace "Tin yaushe ai shekaran jiya ma Bappa yaxo aka ɗaura aurenta anan masallaci bayan sallar juma'a, bbu wni taro da akay sbd uwar baso take ba, haka akay komai lami bbu wni shagali sai kace ba auren budurwa ba, ƙannen mahaifinku mata suka miƙata gidan mijin", Hajar tace "Ynxu anyi auren Nabilah... Umma kinje gidan nata toh..?", Umma ta girgiza kai tace "A'a banje ba gsky sai nan gaba insha Allah zan dai daure naje idan tayi sati", Hajar tayi shiru ba tace komai ba tana wni tunani, toh ko ya labarinsu Maimuna da Sa'adatu, Allah yasa dai suma sunyi hankali kamar Nabilah, Sabrah ta fito bayan ta gama shiryawa suka gaisa da Yayarta, Hajar ta bata snacks da suka siya mata, sosai Sabrah ta dashare haƙora tace "ngd Addah", Hajar ta mata murmushi sai kuma ta kalli Umma tace "Umma dan Allah yau ma ki bani aron Sabrah na tafi da ita..", Umma ta girgiza kai tace "yaushe ta dawo daga gidan naki, daga ke har ita ku ka yaudareni dan sati ɗaya nace tayi ta dawo gida amma saida ku ka cinye sati uku..", Hajar ta marairaice murya tace "plxx Umma wnn karon baza mu ƙara ba..", Umma ta girgiza kai tace "A'a wai ance miki bayar da ɗa sauki ne dashi iyeh, ki bari idan kin haifa akace ki kawo sai kiji yacca akeji", Hajar tayi murmushi tana hasaso ycca take son unborn babynta tin kafin ma yaxo duniya, ta rasa a tsakanin ita da uban ɗan wane yafi son babyn, so da dama idan ta kissima yacca za tayi raising babyn bayan yazo duniya idan kuma taji yacca uban yake mararinsa sai taga kamar ya fita son babyn, toh dai mgnar Umma gsky ce don itama fa da alama rowar ƴaƴan nan za tayi, ko zata bayar toh fa tsaf Nurain zai hana. Ƙarfe uku da minti hamsin Umma taji ana sallama a soro, ta san ko waye don ta gane muryarsa, tashi tayi ta fita tsakar gida tana cewa "ka shigo mna Naseer sai kace wni baƙo..", Naseer ya shigo yana sake yin wata sallamar, Umma tace "saika tsaya a soro sai kace baƙo... Bismillah shigo ciki" da haka ta juya ta shiga palour, Naseer ya ajiye doyar da ya shigo da ita snn ya ƙarasa palour da ƙatuwar ledar hannunsa, ya zauna kan kujera yana shafa kansa, da sakakkiyar fuska Umma tace "Sannu da zuwa..", ya russuna yace "Umma barka da yamma", Umma ta amsa with care snn tace "ya hanya..?", yace "Alhmdllh ai kwana na uku da dawowa sbd auren Nabilah..", Umma tace "Eh fa hka ne, Allah ya sanya Alkhairy", yace "Ameen..", tashi Umma tayi ta shiga ɗakinta, ta kalli Hajar dake zaune kan darduma tana zaman tahiya tace "idan kin idar da sallar kixo ga Yayanki.." da haka ta juya ta fita, Hajar na idar da sallah ta miƙe ta fita palour, Naseer ya ɗaga kai ya ɗan kalleta sai kuma ya mata murmushi, Hajar ta samu guri ta zauna tace "Yaya ina yini", yace "lfy lou Hajar... ykk ygida...?", tace "lfy alhmdllh", yace "Masha Allah hka akeso", tayi shiru ba tace komai ba, Umma tace "kawo masa abinci da ruwa", Hajar tace "Toh" snn ta tashi ta fita, Umma ta maida dubanta ga Naseer tace "Allah yyi Albarka naga doya", ya shafa kansa yace "ba komai", tace "ya can wajen Huzaifa ba wata uku ya rage masa ba a karatun..?", yace "Eh ai ya gama ma... saidai yace bazai dawo ba don ya samu aiki mai kyau a can", Umma tace "Masha Allah shi kam ya fita da Sa'a wllh ace kana gama mkaranta ka samu aiki..", Naseer yace "Wllh kam ai da offer dinsa ya fito", Umma tace "Masha Allah..", ya janyo ledar da ya shigo da ita yace "ga wasu kayan ma", Umma ta ja ledar kusa da ita tace "Alhmdllh Naseer ai ka kusa gama haɗa lefen ma", ya waro ido yace "bafa a siyi kayan shafa ba", tace "Toh ai anyi mai wuyar tinda an haɗa sutura da takalma da jakunkuna, kayan Shafa ba masu wni whala bane..", ya shafa kai yace "gani nake kamar kayan basu da yawa", Umma ta riƙe baki tace "Lalala siff dita ai ta zama kantin kwari, kaya kam ka haɗasu ba kaɗan ba Naseer, bari Hajar ta kawo mka abinci kaci saina fiddo mka kaga yawansu..", yace "A'a kar a fiddo in na gansu zan iya shagala", Umma tace "Toh shknn, ai kayi mai wuyar ma wllh, ka gama gini tass har an sakawa gida padlock, a marrar nan ka samu gidan kanka ai ba ƙaramin luɗifi bane", a lokacin Hajar ta shigo masa da abinci a plate da kuma jug din zoɓo mai sanyi. Biyar da ƴan mintina Nurain ya kira Hajar a waya yace mata yaxo, Hajar ta fita palour don da za tayi wayar ɗaki ta shiga, har lokacin Naseer bai tafi ba don dman idan yxo yana jimawa sbd sai ya daɗe baizo ba, tini Hajar ta gayawa Umma cewa zai shigo su gaisa, Umma tace "Toh kawomin hijab dina", Hajar ta koma ɗaki ta kawowa Umma hijab dinta snn ta fito, bbu jimawa suka shigo tare da Nurain, Nurain ya gaida Umma da ladabi, Umma ta amsa da sakakkiyar fuska, bayan sun gaisa da Umma ya juya ya miƙawa Naseer hannu sukay musabaha, Nurain ko minti biyu bai ƙara ba ya yiwa Umma sallama ya fita, Umma tace "marmaza ki shirya ku tafi karki barsa yana jira", Hajar ta shiga ɗaki ta ɗakko handbag dinta ta fito, tace "Umma na tafi, idan Sabrah ta dawo Islamiyya zan kira", Umma tace "Allah ya kaiku gida lfy, saura kuma na sake ganin ƙafarki nan kusa", Hajar ta turo baki tace "next week ma zanzo..", Umma tace "karma ki kuskura na gaya miki", Hajar ta dubi Naseer tace "Yaya ka gaida gida", yace "Aha, Allah ya kaiku gida lfy", tace "Ameen" da haka ta nufi tsakar gida ta fita, cikin mota ta tarar dashi don haka ta buɗe front seat ta shiga, kallonta kawai yake har ta rufe ƙofa ta gyara zamanta, ta ɗan kallesa sai kuma ta buɗa lulu eyes dinta tace "how was your day My Moon..?", yace "Totally dull without you by my side", ya kamo hannunta ya kissing deeply yace "I missed you", tayi murmushi ta sarƙe yatsunta cikin nasa tace "Same", Ai kam hka ya fara driving ba tare da ya saki hannunta ba, saida suka hau saman titi yace "bari mu tsaya mu sayi chocolates ba..?", tace "Ai basu ƙare ba", yace "yeah it is better mu ajiye extra kar ya yanke mna Princess ta mna rigima", tayi ƴar dariya tace "Ohk", A wani mall suka tsaya, tana gaba yana biye da ita suka shiga cikin mall din, direct Aisle din Chocolate da Crunchy biscuits suka tsaya, ya bata basket yace ta ɗebi wnda take so zai duba wni abu, Hajar ta fara dubawa tana ɗebar abinda take so tana sakawa a basket, kukan baby ta jiyo daga jikin Aisle din da take, ai kam da sauri ta zagaya, wata mata ta gani durƙushe a ƙasa tana kwashe kayan da suke zube tana zubawa a basket, babyn da yake hannunta sai tsanyara kuka yake tana ɗan jijjigasa, Hajar ta isa inda take ta ajiye basket din hannunta, matar ta ɗago ta kalli Hajar, Hajar tace "ya Baby yake kuka" da haka ta sunkuya ta amshi babyn ta fara jijjigasa, ai kam tini yayi shiru, Mamansa ta ƙarasa kwashe kayan ta miƙe tana kallon Hajar tace "ngd", Hajar tayi murmushi tace "mention not" sai kuma ta ciro babyn daga shoulder dinta zata miƙawa Mamansa, ba ta miƙa mata ba ta tsaya tana kallon fuskar babyn wcca ta mata kama da fuskar wni mutum da ta sani a rayuwa, muryan namiji suka ji ance "Habibty are you done..?", Matar ta juya gun wanda yayi mgnar tace "Eh Habiby..", Hajar ta ringa kallonsa still tana riƙe da babyn har ya ƙaraso, shima kallon nata yake bbu ko ƙiftawa, Hajar ta saukar da kanta sai kuma ta ɗan russuna tace "Ya Sayyadi ina yini", ya ringa kallonta yace "Hajar Adam Gini..?", Hajar ta gyaɗa kai, Nura ya kalli kyakkyawar matarsa Maryam yace "Ɗalibata ce", Maryam ta kalli Hajar tace "Allah sarki sannu ko", Hajar tace "Ashe matar Ya Sayyadi na kawowa temako..", Maryam tayi murmushi tace "Ai kuwa dai", har Nurain zai wuce Aisle din da suke ciki sai kuma ya dawo sbd ya hango Hajar, ya shigo Aisle din walking majestically, saida ya kusa zuwa kusa dasu snn yace "Baby wife..", Hajar ta juya tana ganinsa tayi wni kyakkyawan murmushi tace "My Moon", shima murmushin ya mata kafin ya ƙaraso ya dafa shoulder dinta yace "what are you doing here..?", tace "Ya Sayyadin Islamiyyarmu da mukay sauka a hannunsa ne..", Nurain ya kalli Nura for the first time yace "Okay" sai kuma ya miƙa masa hannu sukay musabaha, briefly suka gaisa, Nurain ya kalli Hajar yace "let go wife..", tace "sure" da haka ta miƙawa Maryam baby boy din tace "Allah ya raya", Maryam ta amshi babyn tace "Ameen ngd", Hajar ta sunkuya zata ɗauki basket din da ta ajiye amma tini Nurain ya rigata, ya riƙe hannunta suka bar wajen, shopping din suka ƙarasa snn suka bar mall din. Haka rayuwar ta cigaba da garawa Couple din cikin jin daɗi da annashuwa suna rainon unborn dinsu tare, kuma har zuwa wnn lokacin ba a duba gender din babyn ba kuma suma basu dena musu ba, kowa yana kan bakarsa, shi yace baby girl ita kuma tace boy, a haka cikin Hajar ya shiga wata tara, saida ya shiga wata na tara ne snn ta fara jin nauyin jikinta, ba ta iya wnn hawa da saukar kamar da amma dai ta kan sauka downstairs twice a day. Yau da wuri Hajar ta kwanta cause tin safe take jin slight pain sai ynxu ta samu ya lafa mata shine ta kwanta, tana kwance kan gado shi kuma Nurain yana zaune kan couch yana aiki jikin laptop, wajen ƙarfe sha ɗaya Hajar ta farka, ba tasan lokacin da ta kwaye duvet din jikinta ba tana so ta miƙe zaune amma ta kasa, ji take kamar bayanta zai ɓalle, ta shafa both side dinta wai ko za taji present din mijinta, tana jin wayam ta buɗe idonta tarwal tace "Moon", da sauri Nurain ya taso ya isa gaban gadon, ya ɗagota yace "Mene ne..?", ta shiga yarfe hannu don ciwon gaba gaba yake, kawai girgiza kai take sideways ta kasa cewa komai, hasken ɗakin ya kunna sosai, Hajar ta muskuta tayi kneeling kan gado sai kuma ta kwallara wata ƙara tace "Nurain..!!", da sauri ya dawo ya zauna, ta riƙe hannunsa da iya ƙarfinta tace "ka ciremin wnn cikin.. Princess ce ko Prince ni dae bana so na bar maka", habawa ai tini Nurain ya fahimci cewa labor ne, ya tashi ya fita daga ɗakin yana jin yacca take kwala masa kira, bai wni jima ba ya dawo, gani yayi har ta kifo daga kan gadon, ya duƙa gabanta ya fara ƙoƙarin cire mata rigarsa dake jikinta, kawai daurewa yake don har ya fara rikicewa, ita kam Hajar kawai cewa take Nurain ka cire Princess din na bar maka, da kyar yayi jarumtar saka mata ƴar shawalwalar rigarta da ya ɗakko mata, ya mayar da ita kan gado yana jera mata sannu, ƙoƙarin hantsilowa take yayi saurin riƙeta, ta fashe da kuka tace "wayyo na shiga uku na lalace nace ka ciremin", da kyar ya samu ya cire hannunsa a nata ya fita, box din da ya shirya 2weeks ago mai ɗauke da duk wani abu na baby da mother sbd zuwa asibiti ya ɗauka ya fita, bai wani jima ba ya dawo bayan ya kai box din mota, da bibbiyu ya haura stairs, a ƙasa ya sameta malala ta sake sakkowa daga gadon, da ita da turtsetsen cikin nata ya haɗa ya ɗauka, ko gidan ma bai iya rufewa ba ya ajiyeta gaban mota ya kwantar da seat din, gida biyu hankalin Nurain ya rabu, ɗaya yana kan tuƙin da yake ɗayan kuma yana kan Hajar da take cikin raɗaɗin ciwo, da haka suka isa private hospital din Dr Mansoor, tini Midwives suka amshi abarsu aka wuce da ita labor room, Nurain ya ringa shawagi tsakanin ƙofar labor room din, After 20mins wata Midwife ta fito, Nurain yace "how is my wife..?", Midwife din tace "Sir please go in your wife need you..", bai ƙarasa jin ta bakinta ba ya buɗe ƙofar labor room din ya shiga.......✍️ Read page 90 and 91 👇 https://chat.whatsapp.com/CjtDNv3iMzmFhMVE9jTZzW 💛 HAJAR 💛 {90..} Nurain na shiga labor room din ya tarar da Hajar kwance kan gado, ya ƙarasa gaban gadon ya shafa fuskarta, ta buɗe idonta a hankali, duk gumi ya tsattsafo mata a goshi tana ajiye numfashi a hankali, ya kamo hannunta yana murzawa with care yace "Sorry wife", hawaye ne suka fara sauko mata tace "Nurain bana son nan wajen ka kaini wajen Ummana", ya shafa kanta yace 'Sorry, Allah ya saukeki lfy wife", lumshe idonta tayi ba ta sake cewa komai ba, wata Nurse ce ta shigo instead of Midwife tace "Amm za'a mayar da ita ward tinda labor din ya tsaya..", Nurain ya dan yi jim duk da cewa yaji abinda Nurse din ta faɗa, yace "idan laborn ya dawo sai kuma a dawo da ita nan..?", Nurse din tace "Sure", ya girgiza kai don bai yarda ba duk da yasan cewa hka tsarin hospital yake, gsky ba za a wahalar masa da mata ba a ringa wni walagigi da ita, yace "A barta a nan din har zuwa ta haihu mna..", Nurse din ta rausayar da kai tace "Ohk" sai kuma ta juya ta fita, Nurain ya janyo kujera ya zauna ya sake kamo hannunta ya riƙe, a haka bacci ya ɗan kwashe Hajar, shi kam yana zaune tunkurkur yana gadi don dman ya saba, ya ciro wayarsa ya duba lokaci yaga 12:30 na dare, yana nan tare da matarsa, duk bayan 20 to 30mins sai Midwife ko Nurse sun shigo to check on Hajar, ƙarfe huɗu da rabi lokacin asuba ta kunno kai toh a lokacin ne Hajar ta farka, kuma kai tsaye naƙudar ta taho mata gadan gadan, An sha gumurzu iya gumurzu, daf da sallar asuba Hajar ta silloɓo ƙatuwar baby girl dinta bayan ta leƙa lahira, gidan glass kam saida ta shigesa sbd girman ƴar, a duk wnn gumurzun Nurain na room din don hannunsa ta yiwa mummunar riƙo da haihuwar tazo, tini aka gyarata ita da baby dinta aka mayar dasu Amenity ward, bayan fitar Nurse da Midwife din da suka kula da ita Nurain ya taka gaban gadon, ya ɗaga fuskarta da tayi jajur, pecking forehead dinta yayi, ya ɗago yana sake kallonta yace "Thank you so much wife", ita dai ba tace masa komai ba sai aukin lumshe ido, yayi pecking hannunta deeply yace "Thank you for making me a Father..", ya sake pecking hannun yace "Thank you for giving birth to my child..", a kasale ta masa murmushi sai kuma ta lumshe idonta, sai a lokacin Nurain ya ɗauki babyn tasa dake kwance kan gadon jarirai, ya ringa kallon fuskar babyn wcca tke baccinta peacefully, kumatunta a cike ɓul ɓul ga kuma nauyi tubarkallah sai kace ba first born ba, rumgumeta yayi sosai a jikinsa for a while, bai mayar da ita kan gadon jariran ba ya kwantar da ita kusa da Mother dinta wcca baccin whala ya kwasheta, sai a lokacin Nurain ya samu chance din kiran Mami, ai kam bugu ɗaya ta ɗaga tinda asuba tayi, Mami kam da taga kiransa saida gabanta ya faɗi, tini ya sanar mata abin alkhairy da ya faru, ta tmbyesa suna gida ko asibiti yace asibitin Dr Mansoor daga hka suka katse wayar, Saida ya kira Nurse ta tsaya a room din tare da Hajar da babyn sa snn ya wuce mosque dake kusa da hospital din don yin sallah. Ƙarfe shida da minti sha biyar na safe Mami ta iso asibitin tare da Sakeena wcca a harabar asibitin suka haɗu itama tazo, Mai aikin Mami ta shigo da basket din abinci, Nurain ya tashi daga kan kujerar da yake zaune yana kallon Hajar da baby dinsa da suke bacci har lokacin yace "Mami snnu da zuwa", Mami tace "yawwa" sai kuma ta matsa gaban gadon tana kallon fuskar Hajar, Sakeena ta ƙarasa shigowa ta ɗauki Babyn ta zauna gefen gado tana kallonta, sai kuma ta kalli Nurain tace "Mace ko namiji..?", yace "Baby girl..", Sakeena tace "Masha Allah, Ya ilahi wllh kamarku ɗaya brother..", Mami ta juyo ta kalli Nurain tace "Tin yaushe take bacci..?", yace "Tin Asuba", Mami tace "Ohk", saida Mami ta zauna a position din da Nurain ya bata snn Sakeena ta kawo mata Baby, Mami ta ringa kallon Babyn snn tace "Tubarkallah Masha Allah..", Babyn kamarta ɗaya da ubanta bbu abinda ta bari, har thick eyebrows dinsa saida ta kwaso saidai ita komai nata na mace ne, even complexion na ubanta ta ɗakko saidai ynxu akwai hasken jinjirantaka shiyasa tayi haske, Sakeena ta tsaya daga gefen Mami tana cigaba da kallon Babyn, the baby is so cute, gata ƙatuwa masha Allah, duk da cikar fuskarta da cheeks amma hancinta bai nutsu ba, hancin ya fito sosai gashi ɗan ɗos masha Allah, wani motsi babyn tayi ta yamutsa fuska har saida dimple din da take dashi ya bayyana kansa for the first time, Sakeena tace "Woah Masha Allah har da dimple...", Mami tayi murmushi tana jin son yarinyar, Nurain dai ganin gaba ɗaya hankalinsu na kan Babyn kamar ma sun manta dashi ya duƙa ya gaida Mami, Mami ta kallesa da murmushi kwance fuskarta ta amsa snn tace "An samu ƙaruwa.. Toh Allah ya raya mna ita bisa sunnar manzo..", ya shafa kansa bai amsa ba, Sakeena ce tace "Ameen", After 30mins Hajar ta farka, Sakeena ta haɗa mata shayi mai kauri ta kai mata, ganin taƙi shan shayin Mami tace "ko ba kya son wnn dear..?", Hajar ta ɗago idonta da suke a kumbure tace "A'a", Sakeena tace "ko ya miki zafi ayi diluting..?", Mami tace "A'a da zafin sai yafi.. try and take it even small daughter..", a hankali Hajar ta fara shan shayin, har saida taji ɗuminsa a cikinta da take jin tamkar an yashe mata ƴar hanji, Nurain ne ya shigo ya ajiye ledar da ya shigo da ita, sosai yaji daɗi ganin ta farka, ya matsa gaban gadon yana tmbyrta how she is feeling, Mami tace "kira likita ya dubata", yace "sure", ya nufi door ya fita, bai jima ba ya dawo tare da Nurse da Dr, both the Mother and the Baby were fine haka likitan ya faɗa, snn yace nan da 12 idan an sake tabbatar da lfyrsu za a sallamesu. Kafin ƙarfe takwas su Umma suka zo tare da Anty da Hafsah, tini Sakeena ta miƙawa Anty babyn bayan sun gaisa, Hajar ta gaida Umma da Anty, Umma dai kawai kallon ƴarta ta take, Hafsah ta koma kusa da Hajar ta zauna tace "Sannu sister..", Hajar tayi murmushi kawai, daga kan su Umma bbu wnda ya sake zuwa, don duk wnda ya kira yace zaizo Mami take cewa ya wuce can gidan suma gasu nan dawowa, Hajjaju Hajiya ma can gidan Mami tasa aka wuce da ita, kamar yacca Dr ya faɗa hakan kuwa akay, 12 aka sallamesu bayan an tabbatar bbu wni matsala, gidan Mami aka wuce da Hajar snn aka bata ɗaki guda, kafin kace me ɗakin ya cika sai zuwa ake ganin baby da duba Hajar, Umma dai bata biyosu gidan ba ta wuce gida duk da cewa tana son kasancewa da ƴarta, taso ace an bata ƴarta ta tafi gida da ita amma kuma kawaici yasa tayi shiru, ai suma taga yacca suke taraiyar Hajar din suna bata kula ta musamman, ai soyayya ce ta jawo har suka tafi da ita, Hajar na zaune kan gadon ɗakin, Anty kuma na zaune kan kujerar room din, Hajiya ce ta shigo tana dogara sandarta, Anty ta tashi daga inda take tace "Hajiya ga waje..", Hajiya ta zauna kan kujerar tace "yewwa" sai kuma ta kalli Hajar tace "Sannu Hajaru.. haihuwar fari ki haifo wnn narkekiyar ƴa ai dole a miki sannu", Hajar dai ta saukar da kanta ba tace komai ba, Sakeena ce ta shigo da Babyn a hannunta wcca take tsanyara kuka don ta farka ne, Hajiya tace "A'a lfy..?", Sakeena na jijjiga babyn tace "Tashi tayi ne Hajiya", Hajiya tace "miƙata ga uwarta ta bata Nono", Sakeena ta miƙawa Hajar Babyn, Hajar bata amshi Babyn ba tayi kamar bata san ana miƙo mata ba, amma kuma har cikin ƙahon zuciyarta take jin kukan yarinyar, Sakeena ta ajiye mata ita akan laps tace "feed her", Hajar ta saukar da idanunta tana kallon babyn, tinda taxo duniya sai ynxu ta kalleta da kyau, wni gurmi ne taji ya buɗe a zuciyarta wnda wnn shine karo na farko da ya buɗe, ta ringa kallon jinjirar dake wutsil wutsil a cinyarta tana ƙishin ƙishin, lokaci guda ta fara kuka, ɗaukarta tayi ta sakata a shoulder ta ringa shafa bayanta, still dai babyn bata dena kuka ba, Anty ta zauna kan gadon tana kallon Hajar da kyau tace "ki bata mna", Hajar ta saukar da kanta tace "Ni me zan bata", Hajiya ta caɓe zancen tace "ki bata Nono ko saita shiɗe ne..", firr Hajar ta kasa feeding babyn a gaban mutane, yama za ai tayi feeding gaban mutane, Sakeena tayi murmushi don ta gane manufar Hajar, itama haka tayi wnn wautar a haihuwarta na fari, Sakeena ta amshi babyn daga hannunta, feeder dinta na ruwan zam zam ta dauka ta zauna tana bata ruwan, daidai nan Mami ta shigo, Mami ta kalli Sakeena tace "ya take kuka har ynxu..?", Sakeena tace "Mami a siya mata formula first ynxu naga kamar ruwan mimin bai zo ba", Mami tace "Ohk bari na yiwa Nurain mgana ya kawo mata madaran..", Hajiya ta kalli Mami tace "yau naga jaraba, wace irin madara ana zaune ƙalou, jaririya da Nonon uwarta sai ace a siyo mata madarar kanti, ku bar ganinta ƙatuwa indai ku ka fara bata madara toh wllh duk saita tsiyaye, wnn kumatun da tazo dashi duk saiya zazzage wllh, kar a wni bata wata madara Nonon uwarta ne kawai zaisa jikinta ya cigaba da ɗorewa...", Mami ta saukar da murya tace "Hajiya ai ba madaran za'a bata ba, na wni lokacin ne kafin abincinta yaxo", Hajiya tace "Toh ta yaya zaizo bayan ba'a barta ta zuƙa ba, sai tana ja snn zaizo da wuri, snn kuma jegon zamani na shirme wai sai a bawa mai jego wni banzan shayi ina muka bar kunun kanwa", Mami tace "Toh sai a mata kunun kanwar..", Hajiya tace "Eh da yafi, jinjira sai tsanyara ihu take", da haka Mami ta fita zata saka a damawa Hajar kunun kanwar da Hajiya tace. bayan sallar la'asar Hajar ta fito daga bathroom Anty biye da ita, wanka Anty ta taimaka mata tayi da ruwan zafi snn kuma tayi deep sitz bath tinda bata samu tear ba, Hajar ta kalli babynta dake kan gado tana bacci, tin ɗaxu da aka bata madara take bacci abinta, Anty ta ciro mata kaya cikin box din kayansu, Hajar na gama saka kayan Anty ta shaƙe mata bowl da chicken pepper mai bitter leaf da Anty Zulaihah ta kawo mata, knocking door akay snn aka buɗe, Nurain ne ya shigo, ya ƙaraso cikin ɗakin snn suka gaisa da Anty, ido huɗu sukay da Hajar ya sakar mata murmushi, tayi sauri ta ɗauke idonta ta cigaba da shan pepper soup dinta, Anty ta buɗe ƙofa ta fita, tana fita Nurain ya matsa kusa da Hajar ya sunkuya yana kallonta, ta ɗan kallesa sai kuma ta turo baki tace "Why the look..?", yace "Mamah bear how are you doing..?", ta turo baki tace "bayan wnn princess din taka ta bani whala..", yayi ƴar dariya sai kuma ya zaga side din da babyn take ya ɗauketa, ai kam yana ɗagata ta wni tsanyare da kuka sai kace wcca aka kunna da remote, waro ido yayi snn ya mayar da ita ya ajiye, habawa ai tini Hajar ta taso saura ƙiris tayi fatali da pepper soup din, ɗaukar babyn tayi ta fara jijjigata, saida babyn tayi shiru snn ta zauna gefen gado ta ajiyeta a laps dinta tana kallonta, Nurain ya zauna kusa da ita yana kallon babyn shima, ya taɓa small soft lips din babyn yace "Finally dai Princess ce..", Hajar ta ɗan kallesa sai kuma tayi murmushi, koma dai mene ne ita tana son abarta. ★Ruqayyah na zaune tsakiyar gado ta haɗe kai da guiwa sai rusa uban kuka take, ɗakin nata cike yake da ƴan uwanta, Meema dake kusa da ita tace "haba Ruqayyah wai bazaki dena kukan nan ba, yau fa ranar murna da farin ciki ce a wajenki amma ki zauna kina kuka", Ruqayyah dai ba tace mata uffan ba ta cigaba da rusa kuka, tabbas murna ya kamata tayi a wnn rana amma kuma zuciyarta zafi take, Meema ta taɓe baki tace "Toh Allah ya kyauta" daga haka bata sake cewa komai ba, bbu jimawa Kulsoom elder sister din Ruqayyah ta shigo, sakin baki tayi tace "what is this, wai ba tayi wankan ba..?", Meema tace "yeah", Kulsoom ta zauna gefen Ruqayyah ta dafa shoulder dinta tace "Ruqayyah ki tashi kiyi wnka mna.. dangin Angon fa sunxo", wani tashin hankali ne ya sake baibaiye zuciyar Ruqayyah, Kulsoom ba ta bar ɗakin ba saida ta tabbatar Ruqayya ta shiga wanka, saida Ruqayyah ta kwashi lokaci mai yawa snn ta fito, tini Kulsoom ta kawo mata lafayar da zata saka da kuma kayan ciki, Meema ce ta taimaka mata wajen shiryawar, Ruqayyah ta saka hannunta da yaji zanen ƙunshi ta goge hawayen dake sauko mata, Haj Safiyya ce da ƙanwar Daddy suka shigo ɗakin tare, da haka suka fita da Ruqayyah da aka lulluɓe mata fuska da lafaya, wajen Momy aka kai Ruqayyah domin ta mata faɗa snn suyi bankwana, Momy ba ta iya cewa komai ba bayan fatan Alkhairy da tayi mata da zaman lfy a gidan mijinta, daga wajen Momy aka kai Ruqayyah Amarya wajen Daddy shima ya saka mata Albarka, wajen dattijan gidan aka kaita daga ƙarshe snn aka miƙata hannun dangin mijinta da suke jiran a basu ita, gursheƙen kuka kawai Ruqayyah take har aka fita da ita, aka sakata a motar da take matsayin ta Amarya suka bar gidan da convoy din motocin rakiyarta. Finally Ruqayyah tayi aurenta cikin aminci, a sabon asibitin da ta dawo aiki ne Allah ya haɗata da mijin aure, Mijin nata babban Likitan yara ne, tinda ta fara aiki a asibitin ya nuna interest akanta, farko dai sharesa ta ringa yi har zuwa wni lokaci ta ɗan fara kulasa, da haka har ta basa digit dinta da address din gidansu, soyayya mai tsafta Dr Sa'eed yake yiwa Ruqayyah, ita dai Ruqayyah kawai dai tana kulasa ne ba wai don zuciyarta naso ba, she wants to move on din, ranar da Daddy ya ganta tare da Dr Sa'eed ai kam a ranar ya masa mgana, da yake Dr Sa'eed ba da wasa yaxo ba da gske aurenta zai yi aikam tini ya turo magabatansa, aka saka lokacin auren ba mai tsaho ba cause Dr Sa'eed yace a shirye yake, har week din aure ya kama abin mamaki shine Ruqayyah ba taji tana son wnda zata aura ba, kwata kwata ta kasa buɗe zuciyarta ta bada ƙofa wni ya shigo, ga dai Dr Sa'eed din bashi da wni matsala ga kyan hali saidai kuma ba yaro bane don ya haura hamsin, snn kuma yanada matarsa har da manyan ƴaƴa ma, Ruqayyah dai tayi accepting dinsa ne sbd ta goge black spot din da tayi a wajen parent dinta, kuma don dole ma ta amshesa sbd bazata taɓa samun abinda take so ba, ya riga da ya mata nisa nisan da bazata iya kamosa ba, amma dai ta ɗauki hkan a matsayin darasi mai ƙarko da inganci na rayuwa, yeah some opportunities comes first in life, toh itama hkan ne, sau ɗaya damar auren wanda take so tazo mata amma tasa ƙafa tayi fatali da ita, wnn ya zame mata izina snn kuma ta dauki lesson har ma ta zama teacher, zata iya koyar da duk wcca taga ta dauki step irin nata don ta taimaka mata kar ta aikata abinda za tayi nadama a nan gaba.......✍️ Wanda basu samu sun shiga group ba don ya cika kuma suna son karanta 91 and 92 suyi joining wnn 👇👇 https://chat.whatsapp.com/HOOyHDJCXyO8Uxz5VFhVSU 💛 HAJAR 💛 {91..} ★Sosai Hajar ta saɓe tayi luƙui abinta ita da baby, gata ta ko wace kusurwa ake gwada mata, mijinta ya mata haka zalika ma yan uwansa, ga nata ƴan uwan suma, ƴan uwan Umma ma da suke nan kano duk saida suka zo, yau kwananta huɗu da haihuwa, yau ma Ummanta taxo tare da Iya da Wasilah da kuma Nabilah, Nabilah na riƙe da babyn tace "Masha Allah... Allah ya raya", Anty tace "Ameen", Wasilah tace "Ni kam na sha zasu bamu itane mu tafi da ita tinda dai hka al'adar haihuwar fari take..", Anty tayi ajiyar zuciya tace "Toh dai gashi nan din ma bbu abinda ta rasa na uwa, wllh suna kamantawa", Iya tace "yoh wne kamantawa kuma.. kawai su bamu ɗiyarmu mu wuce da ita gsky..", Umma duk tana jin su ba tace kanzil ba, Anty tace "Ni kam banga aibun hkan ba wllh, duk so ne fa yasa suka riƙeta..", Iya ta gyaɗa kai tace "sai dai hkan, amma dai gsky ya kamata a duba uwar ƴa", Umma dai ba tace komai ba hakama Nabilah dake riƙe da baby, ƙofa aka buɗe Noor ta shigo da fara'arta, da ladabi ta gaishe da mutanen ɗakin, ta ƙarasa wajen Hajar tace "Hajar..", Hajar tayi murmushi tace "kun dawo..?", Noor ta amshi babyn daga hannun Nabilah ta zauna gefen Hajar tace "Azalzalansa nayi muka taho, hka kurum ayi suna bbu ni..", Noor ta shafa cheek din babyn tace "Masha Allah so cute" sai kuma ta rumgumeta tace "Hajar ki bar min ita..", Hajar tayi murmushi kawai, Noor ta rage murya sosai tace "Hajar ya kika ji a labor room..?", Hajar tayi wni murmushi tace "words can't express the pain na rantse, kawai dai na ganni a gidan glass", Noor ta kyalkyale da dariya tace "Na shiga uku..", kawai hango kanta take nan da wata biyar, Mami ce ta shigo ta samu waje ta zauna suka gaisa dasu Umma bayan gaisawar da sukay ɗaxu, Sakeena ce ta shigo ma'aikata gidan mata biye da ita da kayayyaki, boxes ne aka lubge da kaya masu yawa a tsakar ɗakin, su Umma dai suka bi kayan da kallo bbu wnda yace wani abu, tini Mami ta musu bayani cewa kayan barka ne, kaya iya kaya aka zubawa Hajar da Babynta masu uban tsada, bbu abinda babu na kayan baby, har da set din danƙareren gold aka sakowa Hajar cikin kayanta, itama baby an saka mata ɗan kunnen gold guda biyu masu kyau. Daren ranar Nurain ya shigo kamar yacca ya saba, babyn sa ce rumgume a hannunsa yana kallonta, Hajar tace "Papa bear..", ya kalleta yace "Uhmm Mamah bear..", tace "daman Noor ce tace tana son na bar mata baby, ni kuma i can't say no to her nace tazo ta ɗauka..", tini Nurain ya haɗe gira yace "She must be crazy, my princess is not a toy..", Hajar tayi murmushi don tasan za'a kwata, wnn yarinya mai rabata da ubanta a ynxu ai sai Allah, wayar Nurain ce ta fara vibrate, ya karkata yace "Mamah bear help me with my phone..", Hajar ta zura hannu cikin aljihunsa tana cewa "ka ajiye wnn princess din mna", yace "A'a saidai kar a ɗaga wayar", tana ciro wayar yace "Who..?", ta kalli screen din tace "Punk..", yace "Ohk", tace "In ɗaga..?", yace "Sure Farooq ne", picking tayi snn ta kara masa a kunne, ita dai kallon mamaki take masa, toh wai don an ɗauki baby shine baza ayi amfani da hands ba, ko dai nasa salon ɗaukar yaran ne hka, suna gama wayar yace "Farooq zai shigo..", tace "Okay", ta tashi ta ɗauki zumbulelen hijab dinta ta saka, sai a snn ya ajiye babyn kan gado ya tashi ya fita, bbu jimawa ya dawo tare da Farooq, Farooq ya samu guri ya zauna kan kujera, gaisawa sukay da Hajar snn ya mata barka, ita dai kanta na ƙasa ta amsa a taƙaice, Nurain na zaune position din da ya tashi ya rumgume baby, Hajar ta ɗan saci kallonsa ganin bai bawa Farooq ita ba, Farooq yayi gyaran murya yace "Dude..", Nurain ya kallesa da gefen ido yace "why..?", Farooq ya murtuke fuska yace "The Baby..", Nurain yace "ka makara duk wnda bai zo ba 2days ago to ba ganin baby", Farooq yace "i was not in town you know..", Nurain ya miƙe da babyn a hannunsa yace "really" sai kuma ya miƙa masa ita, ashe Farooq bai iya ɗaukar jarirai ba gwara ma Nurain, ai kam ya riƙe babyn a hnkali don gani yake idan ya riƙeta da kyau zai iya ɓallata, babyn ta ɗan karkace a hannun Farooq, habawa ai da sauri Nurain ya taro abarsa sai kuma ya amsheta, Farooq yayi dariya sosai yace "riƙe abunka..", Nurain ya koma ya zauna yace "ko baka faɗa ba", Farooq yayi slight smirk bai ce komai ba, few minutes after that Farooq ya ɗauki wayarsa yayi dialing numbern da yayi saving da Baby with love emoji, kara wayar yayi a kunne yace "Baby where are you..?", daga ɗaya ɓangaren da muryar mace aka ce "Ohh Darling muna gaisawa ne da Mami..", yace "Ohk you have to be fast kar Ummi tace munyi dare..", tace "Alright am coming.." da haka ta katse kiran, few minutes aka buɗe ƙofar ɗakin, da sallama ta shigo kafin ta ƙaraso ciki, tinda ta shigo Farooq yake kallonta, ita dai sau ɗaya ta kalli position dinsa ta ɗauke kai, sosai tayi bowing tace "Yaya ina yini..", Nurain ya ɗan kalleta yace "lfy lou Khausar... how are you doing...?", tace "fine Alhmdllh" sai kuma ta kalli Hajar tayi murmushi tace "Ina yini Maman baby", Hajar ta mayar mata da murmushin tace "mun yini lfy", Khausar tayi murmushi tace "lfy alhmdllh.." da haka ta ajiye medium ledar hannunta ta amshi babyn a hannun Nurain, bbu jimawa Khausar ta kwantar da babyn ta ɗauki ledar da ta ajiye ta miƙawa Hajar tace "Allah ya rayata", Hajar ta amshi ledar tace "Ameen thank you", sosai Hajar tayi mamakin yacca Khausar ta sauya mata, ba tin yau ta fahimci hkan ba, ynxu suna gaisawa cikin mutunci bbu wni ɗagawa, Khausar tace "Yaya saida safe" da haka ta nufi door, Farooq ya tashi ya ciro note din ƴan ɗari biyar biyar ya ajiyewa Hajar snn ya fita. bayan tafiyarsu Farooq Nurain ya kamo hannun Hajar yace "you need anything Love..?", ta gyaɗa kai, yace "Name it Baby wife..", ta kwantar da kanta a shoulder dinsa tana turo baki tace "Seafood", yace "Ohk", ta ɗaga kanta tana kallonsa, yayi kissing lips dinta lightly yace "let me buy it for you", ya duƙa yayi pecking cheeks din baby kafin ya fita, bayan fitarsa da few minutes Hajar taga babyn ta fara saƙa da hannunta alamar ta tashi, ɗaukarta tayi ta fara breastfeeding dinta, tana gama breastfeeding dinta ta sakata a kafaɗa, after few minutes ta kwantar da ita don har ta koma bacci. Ranar suna gida cika yayi maƙil da ƴan uwa da abokan arziki na both side, yarinya taci suna Nanerh Khadijah amma ana kiranta Nanerh sbd sunan Mami ne, gsky an zuba shagali mai lasisi, Hajar har ta gaji da kyau sai shiga take tana fita cikin sabbin ƴan ubansun kayan da aka ɗinka mata, kyau mai sanyi tayi don bata kwaɓa kwalliya ba, komai nata natural ta barshi, kitso kawai akai mata sai jan ƙunshi, sosai Hajar taji daɗin zuwan Oum Sulthan da sauran neighbors dinta. Daren ranar sunan ne Nurain ya shiga part din Maminsa da take kiransa, a bedroom dinta ya tarar da ita, Mami tace "What is your next plan after the naming ceremony..?", ya shafa kansa yace "Nothing Mother..", Mami tace "Okay, sai Hajar ta tafi gida ta ƙarasa 40days dinta", habawa ai tini Nurain ya zubawa Mami idanu, shi da yake so a basa matarsa da ƴarsa su tafi gida ya yaji ana mganar 40days, Mami tace "kasan dai hkan al'ada ne ko, kuma nasan suma iyayenta kawai kawaici sukay mna ta zauna a nan na sati guda, bana so a shiga huruminsu da yawa, itama nasan tana so taje wajen mahaifiyarta..", Nurain dai ya kasa cewa komai don ji yake kamar ana zare masa spine, Mami tace "Any problem with that...?, idan fa kace baka so toh ba zata ba", ya girgiza kai, Mami tace "ba kace min zaka tafi China ba ko ka fasa ne..?", ya girgiza kai yace "A'a zan je", Mami tace "Ohk... shknn ma kaga kayi tafiyarka lfy bbu wni burden ita kuma taje gidansu ko?", ya gyaɗa kai yace "Toh shknn our Mami... yaushe zata tafin..?", Mami tace "ko gobe sai a kaita", yace "Toh". Nurain na barin wajen Mami direct ɗakin da Hajar take ya wuce, ta fito daga wanka knn ya shigo, rabonsa da ita tin safe a palour da akay musu hoto da baby dinsu, yace "where is our princess..?", tace "An tafi da ita wajen Hajiya za'a mata wanka", ya sauke ajiyar zuciya yace "yau an bata whala ko..?", Hajar tayi ƴar dariya tace "whala kuma..?", yace "Eh mna, nasan an ta ɗaukarta ne, duk yawan mutanen nan sai suce sai sun ɗauki baby", tace "A'a fa Hajiya ce tasa aka goya ta so duk wnda zai ganta saidai ya ganta a baya", Nurain ya sauke ajiyar zuciya yace "better", ƙarasawa yayi inda take, tayi sauri ta saka kayan baccinta riga da wando, saida ta gama sa kayan snn ya gaya mata mgnar zuwa gidan Umma, sosai yaga farin ciki ya bayyana bisa fuskarta, ya riƙe hannunta gami da sarƙe yatsunta da nasa, ƙoƙarin kwace hannunta ta ringa yi amma yaƙi ya saketa, ta marairaice tace "wani fa zai iya shigowa", yace "wnda ya shigo shi yaga duhu, kowa yasan am with my wife" da haka ya riƙo ƙugunta ya janyota jikinsa ya bata wni kiss a lips, ta zaro ido sai kuma ta fara turasa, ya ɗago hannunta da ya sarƙe da nasa yayi kissing, murya ƙasan maƙoshi yace "i will miss you", suka ringa kallon eye balls din juna, yaja hancinta yace "Silly girl..", ba ta san lokacin da wni murmushi ya kufce mata ba, kawai ta faɗa ƙirjinsa ta kwantar ta kanta gami da lumshe ido tana shaƙar pure scent dinsa. Haka kuwa akay washe gari Anty Zulaihah da Sakeena suka raka Hajar da baby Nanerh har gidan Umma, Umma never expected that don haka a fili ta nuna farin cikinta, Hajar ma dai taji daɗi sosai saidai tasan za tayi kewar mijinta. Duk wadanda basu samu sunje barka da suna ba nan gidan Umma suka biyo Hajar, Sosai Hajar take jin daɗin zama a wajen Ummanta, ga Sabrah anyi ƴa kullum ta goye Nanerh har yarinyar ta saba da baya, gashi mimin Uwa ya amsheta sai narka ƙiba take don yacca tazo ƙatuwa haka ta ɗora, kullum Nurain sai yaxo da yamma ko da daddare, a haka Hajar ta cika sati biyu da a gidan Umma, yau ma dai ta shirya tsaf tana jiran Nurain da yace zaizo, sai ƙarfe 8 na dare ya ƙaraso, ya shigo suka gaisa da Umma kafin ya wuce ɗakin soro wnda yake matsayin sitting room kuma ɗakin Mu'azzam, Hajar ta shiga ɗaki ta amso Nanerh wacca take hannun Sabrah tana mata wasa, Hajar tace "har ynxu dai babyn naki bata isa fara dariya ba ai Anty Sabrah", Sabrah tace "idonta biyu shiyasa nake mata wasa kar tayi kuka", Hajar ta wuce ɗakin soro, shiga tayi tace "Sannu da zuwa My Moon", yace "you're welcome Baby wife", ta ƙarasa ciki, Nurain ya amshi Nanerh yana kallonta, a kullum yarinyar ƙara girma take da kyau, ya jima yana kallonta kafin ya ɗauki wayarsa dake hannun kujera, ya kalli Hajar yace "Come", ta taso ta zauna kusa da shi, kunna wayar yayi snn ya kunna data ya shiga wni page, yayi ƴan danne danne snn ya miƙa mata yace "which one do you like?".......✍️ read 92 and 93... 👇 https://chat.whatsapp.com/HOOyHDJCXyO8Uxz5VFhVSU 💛 HAJAR 💛 {92..} Hajar ta amshi wayar ta kalli screen din, a hankali take scrolling tana duddubawa, bayan ta duba ta ɗan kallesa tace "Moon ai ni duk sun min kyau..", yace "wnda yafi miki kyau zaki nunamin..", ta gyara zama harda harɗe ƙafa tana dubawa, after like 5mins ta haska masa wayar tace "This One..", ya amshi wayar yana kallon wnda ta zaɓa da kyau, ya gyaɗa kai yace "Alright.." sai kuma ya ajiye wayar, Nanerh dake hannunsa wacca take wurwurga idanu ce ta fara kuka, Hajar ta lakace mata hanci tace "Ai daman nasan sai tayi halin", ai kam baby kamar tasan me ake ta sake tsanyarewa da kuka, Nurain ya waro ido yace "Baby wife anya ba kiyi rigima ba kina ƙarama", Hajar ta waro ido tace "A'a fa ni banyi rigima ba, daman da kai take kama har rigiman ma kai kayi", Nurain ya zame hular baby Nanerh ya fara rubbing small head dinta wnda yake cike daff da suma kamar gonar audiga, Hajar kam wayarsa ma ta ɗauka ta fara buga game ta barshi da rigimammiyar ƴarsa yana aikin rarrashi, daga tayi shiru kamar abin arziƙi sai kuma ta sake callarewa da kuka, Nurain ya ɗaga yarinya ya ringa dudduba jikinta wai ko wni gurin ne yake mata ciwo shine take kuka, ya kalli Hajar yace "Baby wife tana kukan dare ne..?", Hajar ta gyaɗa kai tace "Sosaima", ya miƙa mata ita, ta amsheta ta fara feeding dinta, yace "let take her to hospital", Hajar ta ɗaga kanta daga kallon Nanerh ta dubesa tace "Umma tace lfyrta lou fa", ya ɗan shafa kansa yace "Yeah, amma dai muje asibitin taga Dr", murmushi Hajar tayi ta shafa kan Nanerh da take ta aukin cin abincinta tace "Okay, let me inform Umma", yace "Ohk", saida ta gama feeding Nanerh wcca ta koma bacci snn ta basa ita, da haka ta shiga cikin gida, A palour ta tarar da Umma tare da Sabrah suna kallo tinda gidan akwai Solar wcca Mu'azzam ya haɗa 2 months earlier, Hajar ta saukar da murya tace "Umma dman cewa yayi zamu kai Nanerh asibiti sbd kukan daren da take..", Umma tayi murmushin manyan tace "Toh shknn, nasan dai bbu abinda yke damunta", Hajar tayi shiru ba tace komai ba, Umma tace "yanxu asibitin zaku tafi..?", Hajar tace "Eh", Umma tace "Toh sai kun dawo", Hajar ta shiga ɗakin da take kwana ta ɗan kimtsa snn ta fito, ta kalli Umma tace "mun tafi" da haka ta nufi ƙofa ta fita, ɗakin da Nurain yake ta shiga, ya kalleta from head to toe yace "shall we..?", ta gyaɗa kai, yace "Ohk, take her", ta ƙarasa inda yake ta amshi Nanerh, yana biye da ita suka fita ƙofar gida inda yayi parking motarsa, ya buɗe mata front seat ta shiga ta zauna kafin ya rufe ƙofar, driver seat ya shiga, yayi stretching kansa yana sauke ajiyar zuciya, kunna motar yayi snn ya kashe Ac sbd Nanerh, a hankali yke driving suna fira da matarsa har suka isa wni private Pediatric clinic, suna zuwa ya yankar musu card, few minutes after that Hajar ta shiga consultation room din bayan wcca take ciki ta fito, Hajar ta zauna kan kujera tana fuskantar female Pediatrician din dake room din, a hankali Hajar tace "Ina yini", Pediatrician din ta amsa da sakakkiyar fuska, tini ta tmbyi Hajar me yake damun babyn nata, Hajar ta ɗanyi jim kafin tace "tana yin kukan dare snn ma idan idonta biyu tana kuka", Pediatrician din ta gyaɗa kai tace "Tana yin bacci..?", Hajar tace "Eh", Pediatrician din ta amshi Nanerh to check on her, baccinta kawai take abinta, ta ɗaga rigarta pink snn ta ɓalle overall dinta, cibiyarta ta duba tana haskawa da pen torch, ta haska both ears dinta suma, murmushi Likitan tayi snn ta mayar da buttons din overall din ta ɓalle mata, a hankali ta ɗagata ta ringa ɗan jijjigata don so take ta tashi, ita dai Hajar kawai kallon Likitan take, ai kam baby Nanerh ta fara yamutsa fuska sai kuma ta fara wutsil wutsil, lokaci guda small pink lips dinta suka fara karkarwa alamar za tayi halin, tini ta tsanyare da kuka da iya ƙarfinta, Hajar dai da ba don a kan idonta akai komai ba da zata iya cewa mintsilar mata ƴa akay, ƙofar aka buɗe, Nurain ne ya shigo da sauri don zamm ya jiyo kukan babyn tinda tsaye yake jikin ƙofa, ƙarasowa yayi ciki yana kallon Likitan yace "Dr what's wrong with my daughter..?", Likita tayi murmushi tace "Relax your daughter is perfectly fine, bbu abinda yake damunta, lfy ma har yaso ya mata yawa...", Nurain ya sauke wni ajiyar zuciya yace "Toh amma wnn kukan fa", tace "rigimammiya ce kawai amma bbu abinda yake damunta", sosai Nurain da ita kanta Hajar suka ji dadi, Nurain yace "Thank you Dr", Likita tace "you're welcome, kawai dai haƙuri za ayi da kukan nata tinda Arigimatu ce", Nurain ya gyaɗa kai yace "Sure", Hajar ta amshi Nanerh a hannun Likitan snn suka fita, bayan sun bar asibitin ne Hajar tace "Moon ynxu wnn princess din taka ta kyautamin knn..", murmushi yayi ya juyo ya kalleta sai kuma ya ɗauke hannunsa daga jikin steering ya shafa cheek dinta yace "zata dena, i promise you this tinda kema kin rage kukan rigima..", ta turo baki tace "Ah ni kam banyi rigima ba", yayi slight smirk yace "Ni dae kin yi min, da fa kullum sai kin yi min kuka, ko kin manta ne..", ta juya idanunta tace "Alright, amma dai nawa da dalili ita kuma Princess dinka mara dalili take", yayi dariya ya juya ya kalleta yace "kema mara dalilin kike min, shknn ma My Princess avenge that for me", ta sake rumgume Nanerh a jikinta tace "her father's daughter", slowly ya kamo hannun Hajar while still driving yace "Te Amo..", ta ɗan yi still don bata gane me yace ba, ya sake cewa "Te Amo", tace "translate..", ya murza hannunta dake cikin nasa yace "I Love you", tayi murmushi tace "Nado Sarang hae", yayi chuckling yace "translate", tace "I Love you too", sukay dariya a tare, sai tara da minti hamsin suka isa gidan Umma, shi dai bai shiga ba amma saida ya tabbatar Hajar ta shiga gida snn ya koma mota ya tafi. Haka nan rayuwar ta cigaba da mirginawa har Hajar tayi wata guda a gidan Umma, kwana huɗu knn Nurain bai je gurinsu ba sbd aikin da ya saka a gaba yake so ya kammala kar lokaci ya ƙure masa, so yake nan da sati guda a hattama komai, China din ma da yaso zuwa tini ya janye tafiyar ya maida hankalinsa akan abinda yake, tinda bai samu yaje wajensu ba hakan yasa suke yin dogon video call, A tsakanin lokacin nan Anty ta fara yiwa Hajar aike na magunguna masu kyau, Hajar kam ta ringa ɗirke abunta don ynxu tasan amfaninsu, gashi ta siyo babbar robar dilke a wajen Oum Sulthan, sosai gyararriyar fatarta ta sake kyau matuƙa, ga sabbin turarukan da take tsuma jikinta dasu wnda a lokaci guda jikin nata ya ɗau ƙamshi mai sanyaya zuciya. Ranar Wednesday Hajar na zaune a palour suna cin abincin da ta dafa musu, shinkafa da wake wcca ta sha haɗin lettuce salad da soyayyen kifi, da kuma zoɓo mai sanyi, bayan sun gama cin abincin Hajar ta fita da kwanukan ta dawo ta zauna, knocking door akay, Sabrah dake riƙe da Nanerh suna zaune palourn ta tashi ta ajiye Nanerh snn ta fita buɗe gida, Sabrah ta dawo tana cewa "Umma Yaya Nabilah ce", daidai nan Nabilah ta shigo da sallama, Umma tace "Ah a Nabilah ce..?", Nabilah ta zauna kan carpet tace "Eh Umma nice", Umma tace "sannu da zuwa", Nabilah tace "Yauwa Umma ina yini", Umma ta amsa snn ta tmbyeta ya take da mai gidanta, Nabilah tace "lfy alhmdllh" sai kuma ta juya ta kalli Hajar wcca take kallonta da sakakkiyar fuska, gaisawa sukay da Hajar a mutunce, Nabilah tace "ya Nanerh..?", Hajar ta nuna kan kujera tace "gata can", Nabilah ta leƙa fuskar Nanerh tace "bacci ma take kar na ɗauketa ta tashi", Hajar tace "Okay toh ynxu tayi bacci da idonta biyu", Nabilah ta saukar da kai tace "Umma daman zai shigo ne ku gaisa", Umma tace "Mai gidan naki..?", Nabilah ta gyaɗa kai, Umma tace "Bismillah shigo dashi", Nabilah tace "Toh" da haka ta miƙe ta fita, Hajar ta tashi ta shiga ɗaki, Umma ta saka hijab dinta, babu jimawa Nabilah ta shigo tare da mijinta, bayan sun gaisa da Umma Hajar ta fito suka gaisa, bai wni jima ba ya tashi ya tafi ya bar Nabilah a nan, har yamma Nabilah na gidan, Umma dai taji daɗin yacca taga Nabilah, kana ganinta kasan tana jin daɗin gidan mijinta, tayi kyau tayi ƙiba abinta don hankalinta a kwance yake, daidai gwargwado mijinta yana kula da ita da iya ƙarfinsa, Nabilah ta gayawa Umma cewa zasu koma Bichi da zama, Umma ta kalli Nabilah tace "kamar ya Bichi..?", Nabilah tace "Ai daman acan garinsu Bichi yake gini kuma ynxu ginin ya kammala, kuma daman wnn gidan da muke ciki na haya ne..", Hajar tayi shiru tana kallon Nabilah don ba ta so komawarsu Bichi ba, haka zalika Umma ma ba ta so tafiyar Nabilah ba amma kuma gidan kai yafi na haya, Umma tace "kun sa ranar tariyar ne..?", Nabilah tace "Eh nan da sati biyu yace", Umma tace "Toh Allah ya kaimu, Allah ya haɗaki da mutanen kwarai a can din", Nabilah tace "Ameen", Umma tace "kina dai zuwa wajen mahaifiyarki ko..?", Nabilah tayi shiru, Umma tayi ajiyar zuciya tace "ba kya zuwa ko..?", Nabilah tace "Naje dai sau biyu", sosai Umma ta yiwa Nabilah nasiha mai shiga jiki, a take Nabilah taji ta ɗan sauko akan haushin Maama da ƴan uwanta da take, ta ƙudurce a ranta zata gidan kafin su koma Bichi. Washe gari Hajar ta je gidan Anty tare da Sabrah, a nan take jin cewa ashe bikin Hafsah ya matso saura 2months, ita ta sha ma bikin saura 4months ashe ba haka bane. Ranar Saturday ne Hajar zata koma gidanta, jiya da Nurain yaxo Umma tace ranar asabar yaxo ya tafi da matarsa, tin safe Hajar take haɗa kaya, sosai take zumuɗin komawa gidanta, saida Umma ta kamata snn ta nutsu kunya ta rufeta, Umma dai ta rausayar da kai ta fita ta barta, Umma ce ta yiwa Nanerh wanka ta shiryata, Hajar ma ta shirya cikin riga da skirt na atampa mai laushi, sosai tayi kyau ɗaurin ɗan kwalinta ya zauna a kanta das das, Sabrah ganin Hajar na shiri ta fara harhaɗe rai, Hajar tace itama ta shirya su tafi, Umma na jin hka tace A'a bbu inda zata, hka dai Sabrah tayi ta matsar kwalla gashi ta saba sosai da Nanerh, ƙarfe uku Nurain yaxo, ya kira Hajar ya gaya mata cewa yazo, saida ya shiga suka gaisa da Umma, already daman sun fito da kayansu palour don haka ya ɗauka ya fita dasu ya saka a booth, yana tsaye jikin mota Hajar ta fito kanta a ƙasa tana riƙe da Nanerh, saida ta ƙaraso snn ya leƙa fuskarta yaga idanunta sunyi ja, eyelashes dinta a jiƙe, yayi slight smirk yace "Uhmm halin ko", ta juyar da kanta, saida suka shiga mota snn ya amshi Nanerh yayi pecking cheek dinta yace "Hi Princess", after a while ya miƙawa Hajar ita, Hajar ta ɗago ta kallesa don wni mugun kyau ya mata, ta lura ma kayan jikinsa sababbi ne kamar yadda nata suke sababbi, ta ringa kallonsa without blinking, twisting fingers dinsa yayi a saitin fuskarta yace "Where are you..?", ta sauke numfashi tace "here". kai tsaye gidan Mami suka wuce, sosai Mami taji daɗin ganin yacca Nanerh ta canza, yarinyar sai girma take alamar tana samun kulawa, Mami ta kaiwa Abba Nanerh don yana gidan itama Hajar din ta shiga great room dinsa suka gaisa, A nan gidan Mami sukay sallar la'asar, immediately Nurain na dawowa daga mosque yace Hajar ta fito, already a cikin mota ta samesa don haka ta shiga suka bar gidan, suna isa unguwarsu Nurain ya rage gudun motar suka shiga layin gidansu, Hajar ta tattare gira tana kallon gidan da Nurain yake danna horn a gaban gate dinsa, Wnn ai ba gidanta bane, ta cikin mirror ta hango gidan Oum Sulthan opposite to gidan da suke da niyyar shiga, hakan ne ya tabbatar mata da cewa eh wnn position din gidanta ne amma fa an canzasa don wnn yafi nata girma, ta juya ta kallesa taga ashe kallonta yake, murmushi ya sakar mata kafin ya juya ya shigar da motar ciki don mai gadi ya zuge gate, nan ma dai Hajar sake sandarewa tayi, anya wnn gidanta ne, an fa canzasa, canzawar ma zuwa high class, ta dubi makeken compound din da suke wucewa har suka isa tafkeken parking space da ya ninka na da, Nurain yayi parking motar ya juya yana kallonta gami da sauke ajiyar zuciya, Hajar dake leƙen window tana kallon gidan ta juyo ta kallesa with mixed facial expression, da cracking voice tace "Moon nan din kuma ina ne..?", yace "Home sweet slum, welcome to your home Baby wife"........✍️ 💛 HAJAR 💛 {93..} Hajar dai kawai kallonsa take har lokacin da wni irin expression, kashe mata ido ɗaya yayi wnda bai iya ba ya buɗe motar ya fita, zagayawa yayi ya buɗe mata yace "get down Baby", ta gyaɗa kai, Nanerh dake laps dinta ya ɗauka ya sakata a shoulder, Hajar ta fito still tana ƙarewa compound din da ya sha wasu flowers masu kyau da ƙara lfyr ido kallo, rufe motar yayi ya danna lock kafin ya riƙo hannunta suka nufi entrance din gidan wnda a ynxu ya canza position, ita dai kawai binsa take like one living status, gsky tana buƙatar fashin baƙi, suna isa entrance door ya ciro key a pocket ya buɗe snn ya murɗa handle yace "go in Baby", taƙi shiga sai kuma ta ɗaga kai, ta buɗe baki knn za tayi mgana ya dafe bayan Nanerh ya sunkuya yayi kissing karan hancinta lightly yace "No more words just go in", a hankali ta shiga ciki kamar wcca kwai ya fashewa, yabi bayanta ya rufe ƙofa, Hajar ta ringa kallon makeken palourn da aka sauyawa matuƙa, sauyi ma kam mai lasisi wnda ya jirkitasa daga ainahinsa na da, Hajar dai was speechless at that moment, Nurain duk yana lura da ita, ya kamo hannunta suka nufi stairs wnda shima taga kamar an canza masa position, kamar yacca tayi tunanin za taga sauyi a saman hakan ce ta kasance, wata huge door ya buɗe sai gasu a wni palour wnda a da bbu shi, Hajar tayi wni murmushi tace "Woah", ta cire hannunta daga nasa ta fara zaga palourn, ya kwantar da Nanerh kan kujera, yasa trow pillows guda uku ya kareta, wajen Hajar da take aukin santin palourn ya nufa, yace "you like it..?", ta juyo ta kallesa ta gyaɗa kai tace "yess i like it wllh", yayi murmushi yace "more are coming", ta cikin palourn yabi da ita suka shiga wata ƙofa ai kam sai gasu a wni huge bedroom, tsabar girman bedroom din daga can nesa kake hango gado wnda shi kaɗai ne a babban ɗakin sai chest of drawers, yace "This is your room..", a fili take nuna masa farin cikinta, bakinta yaƙi rufuwa tsabar murna, ynxu room dinta ba mai wardrobe bane makekiyar Closet ce da ita wcca ta ƙunshi duk wni kayan shiri da zata buƙata, ta wata glass door zaka wuce ainahin bathroom dinta wnda suka opposite da closet din, daga nan ɓangarensa suka wuce, shi kam dai ba a sauyasa ba amma kuma an canza furniture, sosai ko ina ya tafi da imanin Hajar kuma ta ringa appreciating, saida suka gama da ɓangarensa suka fito snn ya kalleta yace "kin san duk wnn da kika gani ba suyi kyau ba..", ta waro ido tace "says who..?", ya koma ta bayanta ya rufe mata idanu da palms dinsa, tace "but what are you doing Moon..?", yace "yeah... i will lead you to the Empire..", tayi murmushi mai sauti tace "Then", yace "ready..?", ta gyaɗa kai tace "sure", a hankali suka fara tafiya yana leading, ita dai sai wani wawaken iska take da hannu sai kace makauniya, tace "Moon karfa na ƙume da bango", yace "how will that happen remember am your saviour", after walking for a minute taji ya buɗe ƙofa snn suka shiga wni guri, a hankali ya zame hannunsa daga idonta, ta buɗe idonta tana ƙarewa wajen kallon, baby room din da a tv kawai ta taɓa ganin irinsa ta gani, yace "My Princess room", ba karamin kyau baby room din yayi ba, komai na ciki pink and white ne, ga wallpapers da stickers masu kyau anyi design nasu an rubuta Princess, bango guda aka cika da sunan Princess with different wall stickers, ragowar wall din kuma Papa's bunny pet pie da dai sauransu, ga teddy bears nan kaca kaca a ɗakin suma duk pink and white, babu abinda bbu na buƙatar baby a room din, ga crib din mai kyau with soft mattress, baby rocker, bassinet, walker duk akwai, majority ma bata isa amfani dasu ba, shelves and drawers ma na ajiye kaya duk a cike suke damm da kaya, sosai Nursery din yayi kyau, sun jima a nan din kafin suka cigaba da zagayen, palourn da suka bar Nanerh suka koma, Hajar ta leƙa fuskarta taga har lokacin bacci take, ta sauke numfashi tace "better". Da daddare wajen ƙarfe tara da rabi Nurain ya shiga room din Hajar, ƙarewa room din kallo yayi yaga bata nan, can ya hangi Nanerh kwance cikin bassinet dinta tana bacci, closet ya shiga ai kam ya tarar da ita tana shirya kayan da ta dawo dasu, bata ma san ya shigo ba cause tayi backing dinsa, ya ƙarasa inda take yayi hugging dinta ta baya, ƴar ƙara tayi don ta firgita, pure scent dinsa ta shaƙa snn tayi murmushi tace "you scared me", ya fige hular kanta ya cusa kansa cikin sumarta gami da shaƙar ƙamshinta, with a husky voice yace "why..?", ƙoƙarin raba kanta da jikinsa tayi amma ya riƙeta, tace "Ai ban san ka shigo ba", shiru ne ya gifta na almost 1mins snn ya rage murya yace "I missed you", ba ta ankara ba taji ya sauke mata wni combo kiss a wuya, ba shiri ta juyo ta fuskancesa tana turo baki, yayi brushing lips dinsu ya zagaye ƙugunta yace "i missed your cooking sweet pie", tayi ɗage ta zagaye wuyansa tace "then should i cook something for you..?", yace "yeah", tayi pecking karan hancinsa tace "i also missed your coffee", yayi dariya mai sauti itama tana tayasa, tace "give and take", yace "Ohk", slowly ta zame jikinta a nasa ta amshi hularta ta saka, yana biye da ita suka fita bedroom, direct ta nufi door, ya tsaya yace "Princess", ta juyo ta kallesa taga ya nufi bassinet din Nanerh, ta tsaya tana kallonsa, yana zuwa gaban bassinet din ya juyo ya kalli Hajar yace "ita ka ɗai zamu bari a nan..", Hajar ta rumgume hannaye tace "yess tinda ba zamu kitchen da ita ba", ya kalli Nanerh yace "idan kuma ta tashi tayi kuka fa", tace "ba zata tashi ba ai bata tashi a wnn time din sai dare ya raba..", yace "Are you sure", ta gyaɗa kai, ya duƙa yayi pecking cheek din babyn kafin ya bar wajen, Hajar dai kawai kallon mamaki take masa, wnn wane irin so yake yiwa ƴar nan ne, downstairs suka sauka, Hajar ta murɗa handle din door din da take tunanin nan ne kitchen ta shiga, shima dai kitchen din anyi renovating dinsa to the extent din da ya canza kamanni, har expanding dinsa akay alamar an shigo da wni filin cikinsa, saida ta gama santin kitchen din snn ta fara tunanin me zata dafa masa sharp sharp wnda ba zai ɗauki time ba, ta kallese tace "Ohh Allah yasa akwai perishable Stuffs", yace "Ermmm i think there is", tace "Ohk", ta buɗe fridge ai kam taga kayan miya fresh ones kamar ma yau aka siyosu, freezer ta buɗe itama taga nama da chicken da fresh fish, yace "i refilled them today…", tace "Okay", ta durƙusa ta dauko pot ta matsa gaban sink ta fara wankewa, yace "Baby wife me zaki dafa ne..?", ta dakata da abinda take ta juyo ta kallesa tace "spaghetti and sauce", ya ɗage gira, tace "irin wnn fa wcca Aljanu suka cinyemin ka taimaka ka bani milk", ya waro ido yace "You", ta kyalkyale da dariya tace "ka tuna", ya matsa kusa da ita yana murmushi yace "ya bxn tuna ba bayan nine babban Aljanin", a tare suka kwashe da dariya ita kam harda riƙe ciki, ya tsaya yana kallonta tana cigaba da dariyar ita kaɗai, idan da akwai abinda yake bata dariya a dramas dinsu ta baya toh bai wuce case din Aljanu ba, ƙiri ƙiri ya cinye mata abinci sai yaxo yace wai Aljanu ne, saida ta gama dariya snn ta cigaba da abinda take, ta ɗora ruwa taliyar a gas, fridge ta buɗe ta ɗebi Attaruhu da tomatoes, yace "Ohh just come with me", ta ajiye robar da ta zuba vegetables din tabi bayansa suka fita palour, ƙofar fita taga ya nufa, bai buɗe ƙofar ba ya tsaya ta ƙaraso, this time around ma rufe mata ido yayi, tace "Another surprise dear..?", yace "sure", saida numfashin Hajar ya ɗauke na wucin gadi bayan tayi tozali da abinda ta gani a gabanta da ya buɗe mata ido, A car, tsaleliyar mota dunƙulallariya fara tass, ta rufe bakinta da both hands dinta, ta juya ta faɗa ƙirjinsa hawayen farin ciki suka ringa sauko mata, rumgumeta yayi sosai yace "As promised, the gift for giving birth to a Princess and for you being my beloved wife", lokacin da suka koma kitchen kam ruwan taliya ya kusa ƙonewa saida ta ƙara wni. New page New Chapter na sabuwar rayuwa Hajar da Nurain suka buɗe, ga Princess dinsu a gefe wcca ta ƙarawa sabuwar rayuwar tasu armashi, yau sati biyu knn da dawowarsu, a cikin sati biyun nan Nurain ya fara koyawa Hajar driving, a compound yake koya mata snn kuma da tasa motar suke amfani, ai kam tini Hajar ta kwashe don she is a fast learner, sabuwar motarta kam kullum sai ta shiga ta bata wuta snn take jin daɗi. Ranar Monday Nurain ya fita aiki, wajen ƙarfe sha ɗaya Hajar ta sauko downstairs da Nanerh a shoulder dinta, baby rocker dinta ta kunna mata ta sakata a ciki don idonta biyu, kitchen Hajar ta wuce ta fara yin snacks za ta ajiye a fridge tinda na fridge din sun ƙare, a buɗe ta bar kitchen din sbd Nanerh dake palour ita kaɗai, lfyr Allah Hajar ta fara aikinta, Nanerh na cikin rocker dinta wcca take bouncing da ita lightly, sai bin toys din jikin rocker din take da kallo kuma hakan ne yasa ba tayi rigima ba, ƙarar bell Hajar taji, tayi still don ba tayi expecting visitor ba, wanke hannunta da ya ɓaci da flour tayi snn ta fita ta buɗe ƙofa, Oum Sulthan ta gani, tini Hajar ta bata hanya tayi welcoming dinta in, Hajar ta miƙawa Sulthana hannu, yarinyar ta maƙe shoulder don ƙiwa take, Hajar tayi dariya tace "Toh shknn bazan baki sweet dina ba..", nan ma dai Sulthana ta maƙe shoulder, Oum Sulthan ta ɗauki Nanerh dake cikin rocker dinta, Hajar tace "Ina shirin shigowa sai kuma kika rigani", Oum Sulthan na kallon Nanerh tace "ba komai ai", Hajar tace "An dawo lfy, ya ku ka baro mutanen Maiduguri", Oum Sulthan tace "Lfy lou muka barosu", Hajar tace "Alhmdllh, Falmata bata biyoki ba..?", Oum Sulthan tace "Ai makaranta", Hajar tace "hka ne kuma", Hajar ta tashi ta shiga kitchen ta kawowa Oum Sulthan snack da lemo, Oum Sulthan tace "ynxu watan Nanerh nawa..?", Hajar tace "biyu zata shiga na uku", Oum Sulthan tace "Masha Allah wllh kamar ƴar wata biyar", Hajar tayi murmushi, Oum Sulthan tace "kuma kince bata shan madara ko..?", Hajar ta gyaɗa kai tace "Eh", sai sha biyu da rabi Oum Sulthan ta tafi, fira sukay sosai da Hajar. Da yammacin ranar Hajar ta kira Umma suka gaisa don yau bata samu ta kirata da safe ba, suna gama waya da Umma ta kira Nabilah, bayan sun gaisa Hajar tace "ya mganar tafiyar naku..?", Nabilah tace "saura kwana biyu mu tafi", Hajar tace "Okay... Allah ya kaimu, wai ƴar uwa kinada bank kuwa..?", Nabilah tace "Opay ne dani", Hajar tace "Aha, sai anjima", Nabilah tace "mu jima da yawa ngd da kulawa", Hajar tace "ba komai" da haka ta katse kiran, transfer na kuɗi masu ɗan tsoka Hajar ta yiwa Nabilah, ta tura mata text tace ta siyi wni abun ba yawa, after 20mins sai ga Nabilah na kira don taga kuɗin, Nabilah tace kuɗi sunyi yawa Hajar tace ba komai wllh ta riƙe, sosai Nabilah ta ringa surfawa Hajar godiya kamar za tayi kuka, Hajar tace ai yiwa kai ne. Da daddare Hajar ta shiga ɓangaren Nurain da jug din fresh coconut juice, da sallama ta ƙarasa shiga ciki, Nurain na zaune kan carpet da Nanerh gefensa wacca take kwance kan floor mattress dinta yana mata wasa, Hajar ta ajiye jug din kusa da kayan abincin da ta jere a carpet, yace "Baby wife zo ki gani ynxu fa Princess ta gama yimin dariya", Hajar tace "A'a saidai ta ƙuda ai bata isa fara dariya ba", yace "No ynxu fa tayi dariyan", tace "Eh ta ƙuda ba" da haka ta ɗauki cup ta tsiyaya coconut juice din ta miƙa masa, ya ɗago daga wasan da ya cigaba da yiwa Nanerh ya amshi juice din, lafiyayyar sakwara da green veggies soup with fresh offals da smocked fish ta zuba masa, habawa ai yana ganin abincin ya gyara zama, ta ɗan kallesa da wutsiyar ido cause yau favourite dinsa ta dafa, spoon ta miƙa masa ya amsa, ya gutsiri sakwarar ya dangwali miyar ya kai baki, ta riƙe hannunsa tace "Bismillah fa", yace "Ohh Bismillah", ta sakar masa hannu ya fara cin abincin, as usual yau ma santin ya ringa zuba mata, ita dai saidai tace uhmm tana cika masa cup da juice daga zarar ya shanye, bayan ya gama cin abincin ta kwashe kwanukan ta fita dasu, da ta dawo ba ta tarar dashi a palour ba ya shiga ciki, ta ɗauki Nanerh ta wuce da ita ɗakinta ta mata wanka ta saka mata overall dinta, breastfeeding dinta tayi har saida tayi bacci snn ta kwantar da ita a bassinet dinta itama ta shiga wankan, tana fitowa daga wankan ta shiga closet, rubbing lotion tayi kafin ta mulke jikinta da night secret, night secret wata breath taking humra ce mai shegen ƙamshi wcca ta siya wajen Oum Sulthan, hair spray ta fesawa gashinta, da haka ta ɗauki silk nightgown ta saka, ta fito bedroom da shirin kwanciya, dakatawa tayi ganin fitulu a kashe sai iya na bedside ne a kunne, kan gado ta kalla ta gansa zaune ya jingina da allon gadon yana latsa waya, yace "kawomin envelope din da na baki ajiya", tace "Toh" ta juya ta koma Closet, ta ɗakko envelope din da ta ajiye ƙarƙashin kayanta ta fito, ta kai masa ya amsa ya fara buɗewa, zagawa tayi ɗaya side din gadon ta janyo bassinet din Nanerh daf da ita, Addu'a da ta saba yi mata duk dare kafin su kwanta ta mata, bayan ta gama mata addu'ar ta janyo cap din bassinet din ta rufeta, juyawa tayi ta kalli Nurain da yake duba abinda ke cikin envelope din da ta kawo masa, ya ɗaga passport dinta da ya fito 1week earlier, ita dai kawai kallonsa take sai kuma ta ja duvet ta kwanta, ganin ta kwanta yace "Mama bear bacci...?", ta gyaɗa kai tace "Uhmm", ya ja hancinta yace "yau fa ba bacci", ta mirgina da shirin juya masa baya, ya fixgota ta faɗa jikinsa, ya mata raɗa a kunne, tayi lamo tana sauraronsa, lokaci guda ta ɗago tace "really..?", yace "Sure", ta fara shafa thick eyebrows dinsa tace "when..?", yace "ba zai kai nan da 1week ba, i can't leave you and my princess behind, let's go together", ta ɗora forehead dinta saman nasa tace "Together..", ya gyaɗa kai yace "yhap"....….✍️ 💛 HAJAR 💛 {94..} Within 4days Nurain ya gama processing komai na tafiyar tasu, Viser dinsu ma ta fito, har flight ticket ya saya tare da lap baby ticket na Nanerh don nan da 2days ne tafiyar, ya rage kwana ɗaya da zasu wuce Abuja ne ya kaita ta yiwa Umma sallama, har wajen Mami suka je, Mami sai tmbyar Nurain take shin ba a sanyi a inda za sun don idan ana sanyi bbu inda zasu da takwararta saidai su tafi su kaɗai, Nurain yace bbu sanyi ai ynxu summer ce a can, sai a lokacin Mami ta dena surfa masa tmbya. Washe gari da sassafe suka wuce Abuja, Nurain bai kama musu hotel ba gidan Hammad suka wuce cause ƙarfe 12 ne zasu koma airport, Maysha ta tafi da Hajar side dinta bayan ta rumgume Nanerh, breakfast mai rai da lfy Maysha ta jerewa Hajar, Hajar dai tabi kayan abincin da kallo don a ƙoshe take, kafin su baro gida saida ta musu abinci, ganin Hajar ba ta taɓa abincin ba Maysha ta kwantar da Nanerh da take ta riƙo ta fara zuba mata abincin, Hajar tace "Laa Please dama baki zuba ba wllh am full", Maysha tace "please ko kaɗan ne ki ci", Hajar ta ɗauki fork tayi loma biyu ta ajiye ta sha ruwa, Maysha sai ririta Nanerh take tana mata wasa, ji take kamar a bar mata ita, tana azabar son babies. Nurain kam yana tare da Hammad acan sashensa, wani yaro da bazai wuce 8yrs bane ya shigo palourn, yaron fari ne sosai kamar an bursuna masa hoda, gashin kansa baƙi siɗik kuma coily, kana ganinsa dai ka san ba ƴaƴan hausawa bane amma dai yafi kama da ruwa biyu wato halfcast, wajen Hammad ya taho yana murza idonsa, Hammad ya zaunar da shi gefensa yace "Ashraaf", yaron ya ɗaga idanunsa da ƙwayarsu take light ash wacca ta sake bambamcesa da ƴan Nigeria ya kalli Hammad yace "Mommy... Uncle where is my Mommy..?", Hammad ya shafa kan yaron yace "Boy your Mommy will be here soon insha Allah, don't worry uhmm", yaron ya gyaɗa kai, Hammad yace "have you eaten..?", Ashraaf yace "Am not hungry", Hammad yace "No my boy you must eat something if you want your Mommy ta come back", Ashraaf yace "Okay, will i see my Mommy if i eat..?", Hammad yace "Insha Allah..", shi dai Nurain na zaune palourn yana kallonsu, Hammad ya nuna Nurain sai kuma ya kalli Ashraaf yace "show your respect my boy..", Ashraaf yayi taku uku towards Nurain kafin ya tsaya ɗan nesa dashi yace "Good morning", Nurain yace "Good boy... what's your name...?", Ashraaf yace "Ashraaf", Nurain yace "let shake hands boy", walking slowly yaron ya isa gaban Nurain snn ya zura hannunsa cikin na Nurain da already ya miƙa masa, a hankali Nurain yayi shaking hands din nasu, Hammad yace "go to your Aunt", Ashraaf yace "yess" da haka ya nufi door ya fita, Hammad ya bisa da kallo hakama Nurain, Nurain yace "i like the boy, yaron waye..?", Hammad ya sauke ajiyar zuciya yace "he is my son, ɗan ƙanwata Azeeza ne", Nurain ya gyaɗa kai don yasan siblings din Hammad din by name tinda bai taɓa ganinsu ba, Umminsu kawai ya taɓa gani, Hammad ya sauke numfashi yace "something terrible happened, an nemi Azeeza an rasa..", Nurain ya tattare girarsa ya gyara zama yace "An nemeta an rasa... ɓata tayi..?", Hammad yace "sure ɓata tayi tinda duk inda ake tunanin zata je an duba ba'a sameta ba, Yemen Uk zanzibar duk anje nemanta ba a samu ba, her husband General Talba bbu inda bai sa an bincika ba a faɗin Nigeria amma no any trace of her, 3 months knn ana abu ɗaya", Nurain yace "ya subhanallah amma Hammad me yasa baka gayamin ba even a little i can help", Hammad yace "i wasn't my self all through Dr", Nurain yace "Innalillah, Ashraaf shi ka ɗai ne yaronta..?", Hammad ya gyaɗa kai yace "Yeah shi ka ɗai ne, and he is the only male child of General Talba shiyasa ya ɗauki son duniya ya ɗora akan Ashraaf, nima da kyar ya bani yaron na taho dashi sbd yaron ya ringa kuka sai ya biyoni, Ummi ma taso ta amsosa amma uban ya hana wai da mai zai ji da rashin Azeeza ko kuma dauke masa yaro da ake shirin yi, kawai dai wni irin bauɗaɗɗen mutum ne he is rude and arrogant amma kuma yana son Azeeza, son da yake mata ne ma yasa har yau bai haƙura da nemanta ba", Nurain yace "Allah Ubangiji ya bayyanata", Hammad yace "Ameen ya rabbi". Maysha ta ɗaga kanta daga wasan da take yiwa Nanerh ta kalli door jin anata faman murɗa handle, tashi tayi ta buɗe ƙofar, ta kalli Ashraaf dake tsaye bakin ƙofar tace "boy..", ganin Nanerh a hannunta sai ya fara ɗage yana son ya hango fuskarta, Maysha tayi murmushi ta riƙo hannunsa ta shigo dashi ciki snn ta rufe ƙofar, ya nuna Nanerh da finger yace "Baby", Maysha tayi nodding head tace "uhmm Baby", murmushi Ashraaf yayi, Maysha ta shafa kansa tana jin daɗi har cikin ranta, yau kwanan yaron huɗu a gidan amma bai taɓa murmushi kamar wnn ba, zama tayi kan carpet ta ɗora Nanerh a laps dinta, ai tini Ashraaf ya zauna kusa da ita ya ringa kallon Nanerh, cheeks dinta da suke a cike ne suka ja hankalinsa har ya kai farin hannunsa sol ya shafa cheeks din, Maysha tace "you like the baby Ashraaf..?", ya gyaɗa kai yana cigaba da taɓa Nanerh, Maysha ta ɗaga kai ta kalli Hajar dake kallonsu, Hajar tayi murmushi tace "sai a dage a yiwa boy ƙanwa tinda dai yana so", Maysha tayi ƴar dariya tace "A'a mu wnn za'a bar mna", Hajar tayi dariya tace "Toh shknn na bar muku", kamar abin arziƙi ana zaune qlou da Nanerh ba rigima, lokaci guda ta tsanyare da kuka sai kace wcca aka kunna da remote control, Ashraaf ya ringa murza kanta wai nan lallashinta yake har saida hularta ta cire, ganin taƙi shiru Maysha ta tashi ta miƙawa Hajar ita, Ashraaf kuma ya fita da gudu Maysha na tmbyarsa ina zasa, after like 5mins lokacin Nanerh tayi shiru tana hannun Hajar tana feeding dinta Ashraaf ya dawo ɗakin da horse toy a hannunsa, slowly ya nufi Hajar snn ya zauna kusa da ita, Hajar ta ringa kallonsa, ya kamo hannun Nanerh ya saka mata toy din, ai kam toy din ya faɗi ƙasa don Nanerh ba tayi wayon riƙe abu ba, ya sake ɗauka sai kuma ya ɗora a cikinta ya juya ya kalli Maysha yace "Aunt i gave her my toy she will not cry again right...?", Maysha tace "Sure... come here", ya tashi ya tafi wajenta, ta riƙe hannunsa sai kuma ta kalli Hajar tace "ina zuwa please, zan basa abinci ne", Hajar tace "Toh", Maysha na riƙe da hannun Ashraaf wnda yake waiwayen Nanerh dake hannun Hajar suka fita. Before 12noon su Nurain suka isa Airport bayan sun baro gidan Hammad, bayan sun gama bin duk wata procedure suka shiga jirgi, seats din kusa da window suka zauna don dman business class ne, Nurain yasa flight attendant ta kawo musu bassinet sbd Nanerh, ana fara announcement jirgi zai tashi Nurain ya amshi Nanerh, Hajar tayi fastening seat belt dinta gami da runtse ido tana karanto duk addu'ar da tazo mata baki, har yau tana jin tsoron tashi da saukar jirgi, bayan jirgi ya keta hazo ya gama leveling a sararin samaniya Nurain ya kwantar da Nanerh a bassinet din da aka basu, Hajar ta cire seat belt dinta ta gyara zamanta sosai, bbu jimawa bacci ya ɗauketa don dman shi take ji, throughout yester night ba tayi wni baccin kirki ba sbd zumuɗi, a shoulder din Nurain ta kwantar da kanta, shi kam headphone ya saka a kunnensa ya kunna karatun Alkur'ani ya lumshe ido, saida aka fara raba abinci snn Hajar ta farka, ta kalli Nurain dake side dinta, ya cire headphone din yace "kin tashi", ta gyaɗa kai sai kuma ta kalli bassinet din gabansu, wayam ta gani bbu Nanerh, ta zaro manyan idanunta waje ta zaburo sai kace mai shiri miƙewa tsaye tace "My baby", Nurain yayi tapping dinta sai kuma ya nuna mata mutumin da ke gabansu jar fata, a hannun mutumin ta hango Nanerh, saida ta leƙa fuskarsa taga fari ne sosai, ta rage murya tace "kamar ɗan China", Nurain yace "yhap shine". After the journey of 8hours suka isa Hong Kong, lokacin ƙarfe 4 na dare, suna fitowa daga filin jirgi Nurain ya tsare musu Cab, wayarsa ya kunna ya shiga language translator App, da Language translator App din sukay communicating da drivern Cab din tinda shi dai bai iya Chinese ba su kuma basa jin turanci, hotel mai cab din ya kaisu kamar yacca sukay da Nurain, bayan Nurain yyi amfani da currency dinsu da ya taho dasu a hannu ya biya kuɗin transport din suka shiga hotel din, Suit room sukay lodging, wanka Hajar ta shiga bayan ta fito ta yiwa Nanerh ma, daga nan ta jero sallalolin da suka wuceta snn tayi ta asuba da ta ƙarato ynxu, Nurain ya musu order din abinci room service, nan Hajar ta kasa cin abincin, snacks din kawai ta iya ci ta haɗa da drink, bayan sun gama cin abincin Nurain ya fita, Hajar da Nanerh kuma baccinsu sukay sosai, sai sha biyu da wni abun Hajar ta farka, ganin da sauran lokacin sallah bai ƙarato ba ta wuce bathroom ta wanko fuskarta ta fito, a hankali ta isa gaban the wall to wall glass windows that viewed the skyscrapers of Hong Kong city, ɗan buɗa baki tayi in an excited way tana kallonta perfect view din da bata taɓa gani ba a rayuwarta, sosai ta shagala da kallon city din tana jin daɗi, ba ta ma ji ƙarar buɗe ƙofar da akay ba, Nurain ya tsaya yana kallonta ganin duk sallamar da yake batama ji ba, ya ƙarasa inda take yace "me ake gani..?", ta juya ta ɗan kallesa tace "birni nake gani", yace "you like the view from here", tace "Sure.. daman haka China take", yace "All the same amma nan Hong Kong ne", ta tattare gira tace "Ohh", yace "Nanerh ba ta tashi ba..?", tace "Eh", Lunch ma a nan cikin hotel din ya musu order, sai da daddare yasa ta shirya zasu fita yin dinner snn suga gari, tini Hajar ta shirya snn ta shirya Nanerh cikin baby jeans carpenter masu kyau, Hutong restaurant suka je one of the top traditional restaurant in Hong Kong, traditional food and modern one akay seving dinsu, Nurain yasa aka kawo musu seafood, spicy lamb ribs Hajar ta fara taɓawa, bon appetit the food is so yummy saidai seasoning din basu ratsa taste dinta ba, ai kam ta ciro guzirin maggi da tayi ta ringa barbaɗawa tana cin abincin, bayan sun gama yin dinner a Hutong restaurant ba hotel suka koma ba, babban Disneyland of Hong Kong ya kaita, daman wajen yafi daɗin zuwa da daddare, ita Hajar yadda taga mutane garin sunfi hulɗa da daddare ne yafi bata mamaki, sai kace wasu ƙannen aljanu, sosai Hajar taji daɗin Disneyland din, ta zaga ko ina tana shan cotton candy da Nurain ya saya musu, sai 12 na dare da wni abun suka koma hotel. Washe gari kuma da wuri suka fita ya kaita Victoria peak da kuma Ocean park, a Ocean park ne suka hau speed boat suka zaga farkon ruwan wajen, A washe gari kuma bbu inda suka je hutawa akay sai next day suka je Wong Tai Sin, shi kuma wajen kawai natural abubuwa ne suke tsawa and it is a top tourist spot, a ranar nan din kawai suka je sbd wajen nada girma da ɓangarori daban daban, Lantau Island ne ƙarshen wajen da suka je a Hong Kong, daga nan kuma ya kaita malls yace su sayi kayan tsaraba.........✍️ 💛 HAJAR 💛 {95..} Satinsu ɗaya a Hong Kong suka wuce China, A Beijing suka sauka kuma anan ne Nurain ya gabatar da ɗayan shirin nasa na zuwa China, kullum sai ya fita sun haɗu da Mr Lee, idan ya dawo da daddare ko yamma su fita da Hajar, A cikin sati biyu ya gama abinda zai yi, a washe garin da ya gama aikin suka shirya zuwa Shanghai City, Shanghai shima babban birni ne a ƙasar China snn akwai wajajen buɗa ido a garin, by train suka tafi Shanghai din tinda miƙaƙƙiyar tafiya ce daga Beijing, Woah a Shanghai city ma sun zaga ba ƙarya, Hajar ta buɗa ido iya buɗawa, duk wni guri da baƙi suke zuwa saida suka je, Yu Garden suka fara zuwa, anan Hajar taga ƴaƴan itatuwan da bata taɓa gani ba, fruits da vegetables ba a cewa komai, har watermelon mai purple flesh ta gani, da tayi tasting taji zaƙi zau kamar zuma, next inda suka je shine The Bund, shi kuma historical place ne, shima dai wajen ya burge Hajar sosai, da suka bar Bund suka je Museum da daddare, Shanghai Ocean Aquarium ne a ƙarshe a inda suka ziyarta a Shanghai city, kamar Hong Kong a nan din ma one weeks sukai, daga Shanghai next inda suka je shine Guilin, waoh nan din ya share komai da Hajar ta gani cause duk yafi birgeta, Guilin is so natural with breath taking scenery, hotel din da suka sauka ma a garin Guilin na traditional ne, seven places suka ziyarta a Guilin, reed flute cave, Elephant trunk hill, Lijiang, Fubo mountain, Yulong river, Chuanshan park and the last one Li river. Beijing suka koma suka fara shirin komawa Nigeria, ya rage saura kwana biyu su tafi ya kaita taga The great wall of china wnda yake nan garin Beijing, watansu ɗaya da sati biyu knn da baro Nigeria, ranar da zasu tafi Hajar ta shirya snn ta shirya ƴarta Nanerh wcca ta ƙara wayo don ynxu ta cike 3months old har da ɗoriya, Hajar na shiryata tana ɓangala mata dariya don ynxu yarinyar ta koma sarkin dariya, ƙarfe tara na dare suka isa Airport, bayan sun bi duk wata procedure suka shiga jirgi, kamar a zuwa wnn karon ma Hajar bacci tayi, da sassafe suka iso Nigeria Abuja, a take Nurain ya yankar musu flight ticket na zuwa kano, ai kam suka biyo jirgin da zai taho kano, bayan sun fito daga filin jirgi Nurain na riƙe da Nanerh wacca take ɓangalawa duk wnda ta gani dariya, ai kam mutane da yawa sai kaga suna murmushi wasu kam basa iya jurewa sai sun mata wasa. Tinda suka fito ta zuba musu na mujiya, lokaci guda ta miƙe daga kan kujerar da take jira bayan ta tabbatar da fuskar Nurain, har yaxo ya wuceta bai lura da ita ba, Hajar na gefensa sun jera suna tafiyar tare da farin ciki madawwami a fuskokinsu, Ruqayyah ta kasa jurewa ta juya tace "Dr..", at first Nurain bai tsaya ba saida ya sake jin an kira inkiyar tasa a karo na biyu snn ya juyo, Ruqayyah ta ƙaraso inda suke da murmushi kwance fuskarta tace "inata mgana baka ji ba Dr" ta faɗi hakan ne tana kallon Nanerh dake hannunsa wcca ta hau ɓangala mata dariya, Nurain yace "Ohh A Nurse", Hajar ta kalli Ruqayyah da wni irin expression, sosai Ruqayyah ta fahimci cewa wnn yarinyar ta hannun Nurain ƴarsa ce sbd kamarsu da ta ɓaci, Nurain yace "how are you doing A Nurse..?", Ruqayyah tace "great Alhmdllh... long time no see", Nurain ya kalli Hajar snn ya dubi Ruqayyah yace "Meet my beloved wife..", Ruqayyah tayi murmushi tana kallon Hajar tace "sannunki", Hajar da a lokaci guda taji bata son Ruqayyah tace "yawwa sannu", Ruqayyah ta amshi Nanerh tace "your daughter is so cute Dr", Nurain yace "thank you", Hajar ta juyar da kanta tana kallon wni position din, da gefen ido Nurain ya kalleta, Ruqayyah tace "naxo tarbar mai gidana ne", Nurain yace "ohh that's good" da haka ya amshi Nanerh yace "Toh na gaisheki A Nurse byee", da haka sukay sallama a mutunce, Ruqayyah ta koma ta zauna ta cigaba da jiran mai gidan nata Dr Sa'eed, bbu laifi sosai take jin daɗi zama da mijinta don kamar yacca na faɗa a baya ba shida matsala. Kwanan su Hajar 6 da dawowa aka shiga bidirin bikin Hafsah da Ahmad, Samm Nurain ya hana Hajar ta ringa kwana don shi lamarin biki ba burgesa yake ba, hka kurum wasu mazan su kalle masa mata, ai kam hka kullum Hajar take sintirin zuwa gidan biki saidai hakan bai dameta ba don da motarta take tafiya, though har ynxu hannunta bai faɗa ba amma kuma ta iya ba laifi, ansha biki iya biki don an zuba bajinta from both side, outside event biyu akay bayan na gida, ranar Juma'a akay ɗaurin aure, da yammacin ranar dangin ango suka xo tafiya da abarsu, har da Mami cikin wadanda suka zo ɗaukar Amarya don Maman ango close friend dinta ce, su Mami suka ɗauki Hafsah da aka shiryata cikin shigar amare na lafaya, Hajar tabi ƴan kai Amarya ta bar Nanerh a wajen Umma. Gidan Amarya Hafsah saidai muce masha Allah don kwa ya haɗu iya haɗuwa gashi danƙarere, Hajar ta shiga makeken bedroom din da aka ajiye Hafsah bayan rurumar ƴan kawo Amarya sun ragu, friends din Hafsah ne kawai a room din, Hajar ta durƙusa gaban Hafsah ta leƙa fuskarta dake a rufe, Hajar ta kyalkyale da dariya tace "Yau ga Hafsah a gidan Ahmad", Hafsah ta janyo Hajar ta rage murya tace "Na shiga uku na, wllh Allah ni tsoronsa nake ji..", Hajar ta waro ido tace "Mijin naki kike jin tsoro", Hafsah ta gyaɗa kai tace "wllh tsoro yake bani, ni dae gidanmu zan tafi", Hajar tayi dariya tace "A haba dai yarinya tin ynxu za wani kice kina jin tsoronsa, toh ki riƙe tsoronki zuwa nan gaba sai kiyi mai hujja..", Hafsah tayi ƙwal ƙwal da ido lokaci guda hawaye suka taru cikinsu tace "Na shiga uku", Hajar tace "wai ke meye haka", Hafsah ta yarfe hannu tace "ba zaki gane ba Allah kuwa..", Hajar tace "Ni kwa na gane tinda ni nan jiyau ce" ta ƙarashe tana dariya ƙasa ƙasa sai kuma ta zauna gefen gadon, hand bag dinta ta buɗe ta ciro wata leda ta amshi jakar hannun Hafsah ta saka ledar a ciki, Hafsah ta bita da kallo tace "meye wnn..?", Hajar tace "turaren sitz bath ne da musk soap", Hajar ba ta so kaiwa lokacin da Angwaye zasu zo ba amma Hafsah ta riƙeta, ai kam Angwayen na zuwa aka fita da Hafsah palour, sosai Hajar ta sha mamakin jin yadda hannun Hafsah dake cikin nata yana karkarwa, toh wai me yake damun Hafsah, ita bata ma kaita ba aka mata auren, Hajar na shirin zaunar da Hafsah kan kujera bayan sun iso palour Ahmad dake zaune palourn da friends dinsa su biyar ya taso, ba wani wala wala ko wata aba kunya ya taso ya rumgume Hafsah, wni irin zaro ido Hafsah tayi bayan ta shaƙi scent dinsa da ya tabbatar mata shine tinda fuskarta a rufe take, afujajan ta fara turasa, yayi murmushi mai sauti a saitin kunnenta yacca bbu wnda zai ji yace "Halal hug.. welcome home Baby", jikinta yayi lagwas ta dena tura san, Abokan ango suka hau ihu yayinda friends din Amarya suka hau shewa, Hajar kam kamar lips dinta zasu yage sbd murmushi, Finally dai ga Hafsah a gidan Ahmad as his lawful wedded wife. Washe gari da yamma Umma na zaune tare da Anty a palour, Anty ta ringa kallon Umma with a weird facial expression, Umma tayi kicin kicin da fuska tace "A gsky ni barin unguwar ma zanyi, tinda don masifa da bala'i da bita da ƙulli har inda nake ya nemo, wnn wni irin masifa ne da dogon wuya, maza yan bala'i ne ko uban wa yake tantance musu tsakanin mai aure da bazawara", Anty ta kwantar da murya tace "Toh ai mu hka muke so Addah, wnn ai rufin asiri ne babba, Kawu na Yola kawai zansa Iya ta yiwa mgana", Umma ta saki baki ta karkaɗa ƙafa tace "goɗai goɗai dani kike min mganar nan Jamilah, uhmm ai ni kam na gama aure har abada ma kuwa, nayi aure har na samu ribar cikinsa, Allah ya bani ƴaƴa har uku na gari wnda zasu kula dani, na rabu da mijina lfy snn na masa takaba cikin aminci, toh bayan wnn me nake nema a wni aure kuma, ai kawai a cigaba da gurgura rayuwa haka Allah ya bamu sa'a mu koma garesa da imaninmu", Anty ta buɗe baki da nufin convincing Umma, tini Umma ta shata mata layi tace bata son mgnar, hakan yasa Anty tayi gumm da bakinta ba ta sake cewa komai ba. Rayuwa ta cigaba da garawa Hajar cikin kwanciyar hankali da jin daɗi, daga kitchen Hajar ta fito da ƙaramin bowl mai ɗauke da plane Noodles with boiled egg, wajen Nanerh dake wasa cikin keken yaranta ta nufa, Nanerh na ganin Mamanta ta fara miƙa mata hannu tana so ta ɗauketa, Hajar ta ajiye bowl din noodles din kan hannun kujera snn ta durƙusa ta cicciɓo ƙatuwar ƴarta ta, ta zauna kan kujera ta ɗauki bowl din noodles ta fara bawa Nanerh, tini Nanerh ta hau zuƙulƙular noodles, 5months take da shi amma sosai ta kama abinci, bbu abinda bata ci bayan abincinta na gwangwani, daya daga cikin ma'aikatan gidan ce ta fito daga kitchen, ta zuba guiwoyinta gaban Hajar tace "Anty na gama aikin", Hajar tace "Ohk sannu, ina Binta..?", mai aikin tace "tana can ɗakinmu", Hajar tace "Ohk ayi noon duty", mai aikin tace "Toh" da haka ta tashi ta fita ta ƙofar kitchen zuwa backyard din gidan ta wuce boys quarters inda nan ne ɗakinsu, bbu jimawa mai aikin ta dawo tare da ƴar uwarta suka hau aikinsu, within few minutes suka gama gyara ko ina na downstairs din wnda daman a gyare yake, Hajar na zaune tana feeding Nanerh har suka gama, iya kacin aikinsu downstairs don ko hanyar upstairs bbu wnda ya taɓa bi, ita take gyara part dinta dana mijinta, Hajar na gama feeding Nanerh ta haura upstairs da ita, room dinta ta shiga da ita ta mata wanka ta sauya mata kaya, kafin ma ta gama shiryata har ta fara gyangyaɗi hakan yasa ta kwantar da ita ta cigaba da baccin, Hajar ta wuce part dinta tayi wankan itama, turare ta baza as usual ta saka wasu kaya na neman fitina, bom short ne wnda ko rabin cinya baixo ba ta haɗa crop wcca ta bayyana cibiyarta, As usual ta tarbi mijinta, tana riƙe da briefcase dinsa suka haura sama, yace "where is my Princess..?", tace "tayi bacci", saida ya shiga room din Nanerh ya dubata yayi pecking cheeks dinta snn ya wuce part dinsa, a kullum upgrading son da yake yima ƴarsa yake, after yayi refreshing kansa yayi wnka Hajar ta kawo masa abinci, ya zabga uban tagumi yana bin duk wasu moves dinsa, gaba ɗaya yaji ya tsani abincin kawai kallonta yake, walking like a cat ta iso inda yake ta zauna kan cinyarsa ta zagaye wuyansa tace "Cappuccino me zan zuba mka..?", ya haɗe thick eyebrows dinsa yace "No ni ba abinci nake so ba", ta waro ido tana wasa da sajensa tace "Toh me kake so...?", ya zagaye ƙugunta yayi kissing karan hancinta yace "i need you", ta noƙe fuskarta tana murmushi sai kuma ta maƙe shoulder, lokaci guda ta ɗagasa, wayarsa ce tayi ring, ya ɗauka ya kalli sceen din, tini yayi picking don Sakeena ce ke kiranta, ko 2 mins ba suyi suna wayar ba, ya ajiye wayar ya kalli Hajar yace "Noor ce ta haihu", Hajar tace "Masha Allah...", yace "bari naci abinci sai mu tafi ba", ta gyaɗa kai tace "Tom"…..……✍️ 💛 HAJAR 💛 {96..} Hajar na gama zuba masa abincin ta tafi room dinta, closet ta shiga ta sauya kaya, saida ta gama saka kayan snn ta sauka downstairs zuwa kitchen, catfish pepper soup din da tayi ɗaxu ta saka a microwave tayi warming dinsa, with few mins ta jera abincin da zasu kai asibiti a basket, sama ta haura ta shiga room din Nanerh, baccinta take lakadan cikin crib dinta, Baby Carrier Hajar ta ɗaura kafin ta ɗauki Nanerh ta haɗata da chest dinta snn ta ɗaure belts din, ɓangarensa suka wuce, already ma ya gama cin abincin ita yake jira don haka suka fito, bayan sun sauka downstairs Hajar tace "Moon zamu kai musu abinci yana kan Island", yace "Sure.." da haka ya shiga kitchen ya dauko basket din abincin, parking space Nurain ya wuce Hajar kuma ta zaga backyard zuwa boys quarters, masu aikinta su Binta ta gayawa cewa ta fita, Allah ya tsare sukay mata, tace Ameen da haka ta bar wajen, Other car din Nurain suka shiga ba wcca ya dawo da ita ba, ko nisa ba suyi ba suna tafiyar Nanerh ta tashi, ɗago kanta tayi tana kallon Hajar sai kuma ta ɓangala dariya har saida rabbit tooth da both dimples dinta suka fito, Hajar ta fara mata wasa ita kuma ta ringa kyalkyala dariya har da ƙoƙarin shiɗewa, Nurain ya kallesu ya shafa kan Nanerh yace "Princess", shima ta basa nasa kason na dariya sai kuma ta fara miƙa masa hannu wai ya ɗauketa, da taga yaƙi ɗaukarta sai ta fara mimmiƙewa za tayi kuka, Hajar ta ɓalle belt din Carrier ta juyar da Nanerh ta kalli window, hakan yasa ta haƙura da zuwa wajen Abban nata da yake driving ta ringa kallon motoci, Nurain yace "Wifey mene burinki a karatu?", da sauri Hajar ta kallesa don bata taɓa tunanin zai mata mganar cigaba da karatu a yacca yke da mugun kishin nan ba, ya kalleta yace "Uhmmm kinyi shiru baby wife", Nanerh ta fara gantsarewa ta ringa ƙoƙarin juyowa don taji muryan Abbanta, Hajar ta hanata juyowar ai kam ta saka kuka, saida Nurain ya dauketa snn suka samu salama, ɗaukarta da yayi bai hanasa cigaba da tuƙi ba tunda bata takura masa ba, tinda ya ɗauketa daru ya ƙare, sai a snn ya samu chance din cigaba da tmbyar Hajar akan karatunta, tace "dana gama secondary school Nursing school ita nake da burin zuwa, sai dai kuma ban samu na shiga ba..", yace "Nurse kike son zama baby wife...?", ta gyaɗa kai tace "shine babban burina a karatu", yace "Okay... kin taɓa applying ne...?", ta gyaɗa kai, yace "Ohk i see, in dai school of Nursing ta kano state ce nasan ba tada kyau, siyasa kawai suka saka a gaba, basa bada Admission sai kanada hanya idan yarinyar ka ma ta shiga schl din akwai wni exams da suke yi su zubar da yara, ita exams din ba qualifications din yaro suke dubawa ba cause siyanta ake da kuɗi ko kuma hanyar ƴan siyasa..", Hajar ta zuba masa manyan idanunta, yace "I heard that from integrate person wnda ko ban gani ba amma na yarda, So you will not go to that bushy school a bar musu kwalinsu, i will find the best Nursing school for you insha Allah", wni sanyi ne ya ratsa zuciyar Hajar, wai itace zata koma schl abinda bata taɓa kawowa ba, Nurain ya kira Sakeena ta sake tuna masa sunan hospital da Address, gab da magrib suka isa hospital din, bayan Nurain yayi parking ya kalli Nanerh yace "weldon Princess kinga kin sa mun daɗe a kwalta", dariya ta ɓangala masa, ya kashe motar snn ya zare key daga ignition, da zafin nama Nanerh ta kaiwa key din cafka, gamm ta riƙe key din da ƙarfinta taƙi saki, ya bar mata a hannunta ya buɗe motar ya sauka, Hajar ta fito ta ciro basket daga booth suka shiga cikin asibitin, Mami da Sakeena sai Aunties din Abdul mijin Noor biyu suka tarar, Hajar ta ajiye basket din hannunta ta gaida kowa da ladabi, Nurain ya miƙawa Mami Nanerh ya amshi cute baby boy din Noor dake hannun Sakeena, after 3mins ya mayarwa da Sakeena babyn yace zai fita sallah ne tinda magrib yayi, Mami tace "Wnn ba key din motarka bane hannun takwarata..?", yace "Eh shine", Mami tace "Ohk toh amshi abinka kar ta cilla wni gurin da za ayi ta nema", yace "Toh" ya ƙaraso zai amshi key din, ai kam tini Nanerh ta gantsare zata saka kuka, sakar mata yayi ta cigaba da wasanta yace "Ai kuka za tayi ne fa", Mami tace "Au kuka za tayi, shknn idan ta wurgar ai ka yanko wni", ya juya ya fita yana shafa kansa, wato ya yarda ya yanko wni ɗin da Princess dinsa tayi kuka, Hajar dai ta amshi baby ta koma gefen gadon da Noor ke kwance tana bacci ta zauna, tinda ta haihu take bacci don long labor tayi, almost 48hrs tana labor, sai bayan sallar isha'i snn Noor ta farka, Mami tasa Hajar ta haɗa mata shayi mai kauri, Hajar ta miƙawa Noor mug din shayin tace "Sannu", Noor ta numfasa ta amshi mug din, Hajar ta zauna gefenta tace "ynxu kin gane gidan glass din da nake gaya miki..?", Noor ta sauke wni ajiyar zuciya tace "gidan glass ɗaya ma knn, ke nifa nan da kika ganni na buga final insha Allah", Hajar ta guntse dariyar da ta taho mata tace "A haba dai nan da 1yr ki silliɓo wta please", Noor tace "tsakani ga Allah tawa ba irin taku bace Hajar, na samu tear fa sosai", Hajar tace "Ayya sorry, ai kwalliya ta biya kuɗin sabulu your baby is so cute..", Noor tayi murmushi, Sakeena ta kallesu tace "wai ƙus ƙus din me kuke ku ka wni haɗa kai..?", Noor tace "ba komai", Sakeena tace "Toh maza ki shanye tea din". 2weeks Later Hajar na zaune palourn downstairs tare da Sabrah wcca ta ɗakkota shekaran jiya, Sabrah sai wasa take yiwa Nanerh da toys dinta da take zaune baja baja a cikinsu, kayan wasa gareta masu yawo sai kace abinci, a cikin kayan wasan harda horse toy da Ashraaf ya bata, shine ma a hannunta tanata gasa masa cixo da rabbit tooth dinta, Sabrah tace "Addah na ga Yaya Maimuna akan titi tana bara a cikin almajirai", Hajar ta dakata da latsa wayar da take tace "wace Maimunar..?", Sabrah tace "Maimunan Maama ta tsohon gidanmu", Hajar ta tsuke ido tace "Maimunan kika gani tana bara..?", Sabrah ta gyaɗa kai tace "Eh idan zanje schl nke ganinta akan titi", Hajar was very shocked amma kuma bata gamsu ba, Maimunan ce zata fito kan titi tana bara, a haba dai wnn ai impossible ne, Hajar tace "kawo min kayan abincin Nanerh naga kamar cikin yayi ƙasa", Sabrah tace "Toh", gwangwanin cereal food din Nanerh da Vacuum flask Sabrah ta kawo mata, tini Hajar ta damawa babynta cereal food dinta a ƙaramin silicone bowl dinta, Hajar ta ɗauki Nanerh ta fara bata abincin, ana yi ana wasa, don idan ba a wasan nan saita ƙi ci next action kuma kuka ne, bell din door aka danna, Hajar tace "Open the door Sabrah", Sabrah ta tashi da sauri ta buɗe ƙofa, Hajar ta buɗa baki ganin wcca ta shigo, Khausar ta ƙarasa shigowa ciki tare da friends dinta biyu, Hajar ta tarbesu, bayan sun zauna suka gaisa a mutunce, Khausar ta ɗauki Nanerh tana mata wasa, Hajar ta saka Sabrah ta kawo musu ruwa da lemo, Khausar tace "Ohh Hajar ynxu fa zamu wuce", Hajar tace "daga zuwa... ai kwa bari ku huta", Khausar tace "driver na jiranmu ai, daman IV card na kawo mki har gida", ɗaya daga cikin friends din Khausar ta ciro cards daga handbag ta miƙawa Hajar tace "ba ki gane ni ba ko..?", Hajar ta tsuke idonta tana so ta tuna inda ta taɓa ganinta, friend din Khausar tace "Banafsha ce", Hajar ta buɗa baki tace "Na gane... ykk Banafsha..?", Banafsha tace "fine Alhmdllh", su Khausar basu wni jima ba suka yiwa Hajar sallama suka tafi, sai bayan tafiyarsu Hajar ta duba cards din, nan da kwana shida ne bikin, ashe har lokaci ya taho, ranar sunan babyn Noor taji ana mganar bikin Khausar din amma bata yi tunanin yaxo kusa ba, komai mai wucewa ne indai kabi duniya da sauqi wai yau Khausar ce ta tako har gidanta ta kawo mata katin bikinta, baya ga haka ynxu sun ƙulla da Khausar suna zuba friendship dinsu sai kace tin da sun san juna. Daga hka aka shiga bikin Khausar da Farooq, sosai bikin ya zama na musamman don ya haɗa both side, ga ɓangaren Mami ga kuma ɓangaren Abba, bikin Farooq da Khausar yayi armashi ba ƙarya, gashi zumunci ya sake ƙulluwa, daman Mami da Ummin Farooq zaman lfy suke ba wni mganar facalanci shiyasa lokacin da Farooq ya jewa da Umminsa da mganar Khausar kai tsaye tace ta amince, kuma daman tasan wace ce Anty Zulaihah ƙanwar Mami, A ɓangaren Farooq Ango sam bai ɗagawa babban amini ɗan uwansa kuma abokinsa ƙafa ba akan sabgar biki, duk irin noƙewar da Nurain ya ringa yi hka Farooq ya ringa jajiɓosa suna shiga sabga, ɓangaren Hajar da Nurain kam drama aka ringa bugawa a wajen events, shi Nurain ya shige cikin Abokan ango wnda duk ƴan uwa ne, ita kuma hakimar tasa tana daga cikin friends din Amarya, duk inda Hajar tayi Nurain na ankare da ita wai kar wni yayi mata mgana, ita kam shigarta ma was more than decent don ba irin na bride mates bane. Hajjaju Hajiya ma ta baza capacity dinta daidai gwargwado, tace bikin Angonta ake don haka dole ta raƙashe, nan fa jikokinta suka yoh mata caaa da tsokana wai batada kishi za a mata kishiya tana murna, Hajiya kam tace ba komai ai wadata ce tasa yayo mata kishiyar, da za a tafi dauko Amarya Hajiya ce a gaba, daman tace indai tana raye kuma da lfyrta toh duk wata jikarta mace ita zata kaita ɗakin miji, haka zalika idan namiji ne itace zata ɗauko masa matar ta kai masa gidansa, ai kam a hannun Hajiya aka damƙa Khausar, Hajiya ta riƙo hannunta gam zuwa mota tana cewa "Allah yasa ki zama kamar matar Usuman, yarinya ƴar albarka irin albarka, ba sakawa bare aje ga fitarwa, nutsuwa hankali ga kawaici duk ta haɗa, ga uwa uba tarbiyya, Allah yasa kema irinta ce". Hajar dai ana shirin tafiya gidan Amarya ita kuma ta wuce gidanta don a zahirin gsky ta gaji snn kuma ga rigimar da Nanerh take mata itama ta gaji, Sabrah ma har ta gaji da rainon, wajen ƙarfe takwas na dare Hajar tayi wnka, ta lallaɓa Nanerh har tayi bacci, gashi dai bacci take ji amma ta kasa sbd mijinta bai dawo ba, a zabure ta miƙe zaune a kan gadonta ta janyo wayarta ta shiga kiransa, missed call biyu tai masa no response, habawa ai tini ta diro daga gadon ta hau shawagi ta cigaba da doka masa kira, sai a kira na huɗu ya ɗaga, tace "Moon", ƙasa ƙasa taji muryarsa yace "Wifey", daga nan bata sake jin muryarsa ba amma kuma taji alamar kamar driving yake, katse kiran tayi ta sake kiransa, an ɗaga amma kuma sai taji muryar mace, ji tayi tamkar an kwaɗa mata guduma a ka don har wani baƙi ne ya gilma mata.......✍️ 💛 HAJAR 💛 {97..} Sauke wayar Hajar tayi daga kunnenta ta wurgarta kan gado ba tare da tayi ending call din ba, wata irin tafasa zuciyarta ta ringa yi har jiri na neman ɗibanta, ta ja ƙafa ta hau kan gado ta kwanta ta cusa fuskarta a pillow, tunanin zuƙa zuƙan friends din Khausar da suke shige da fice a bikin ta ringa yi, bayan friends dinta ga cousins dinta na ɓangaren uba suma masu yawa kuma kyawawa, Hajar ta suntuma tayi famm saura ƙiris ta fashe, idonta ya soye don duk uban baccin da take ji ya gudu, duk bayan 10 to 15 mins saita ɗaga kai ta kalli agogo, har ƙarfe goma ya wuce Nurain bai dawo ba, ita abinda yafi ƙona mata rai shine da bai sake kiranta ba, tashi tayi ta fita palournta na upstairs, ta kalli Sabrah wacca ta barta tana kallo amma kuma tayi bacci ynxu, daman ita da Nanerh ne suke kwana a bedroom din Hajar ita kuma Hajar ta kwana a turakar mijinta, a yau ba ta jin zata kwana a turakar tasa don wnn fitowar da tayi sbd ta rufe ƙofa ne, tana cikin wnn tunanin aka buɗe ƙofa Nurain ya shigo, ɗaga kai tayi ta kallesa nan ta sake jin wni raɗaɗi a zuciyarta, abinda yasa taji raɗaɗin shine kyan da yayi, lokaci guda pure and breath taking scent dinsa ya cika ɗakin, ya mayar da ƙofa ya kulle yana kallonta yace "Baby wife", ba ta ko kallesa ba ta ƙarasa gaban center table ta ɗauki remote ta kashe kayan kallo, kawai gani tayi har ya matso kusa da ita, da sauri taja da baya ta zille masa, ta juya da gudu ta shiga bedroom dinta, lokaci guda hawaye ya ciko idanunta, ai tini Nurain yabi bayanta, kwance ya sameta kan gado ta rufe da duvet har kai, ya sauke ajiyar zuciya ya ƙarasa gaban gadon ya zauna gefenta, Calmly yace "Baby girl.." sai kuma ya kai hannu ya kwashe duvet din, ta sake janyowa ta rufe kanta, saida sukay haka sau uku, yace "Me nayi kuma Baby wife...?", a ɗan fusace ta miƙe ta zuro ƙafafuwanta ta sauka daga gadon, ganin ta nufi hanyar closet yayi sauri ya tashi ya riƙota don yasan next action din nata, bathroom zata shige kuma duk bala'i ba zata buɗe ba, ƙoƙarin fixge kanta ta ringa yi, ita so take ta gudu taje tayi kukan da take dannewa, ganin yacca ta haƙiƙance ya juyo da ita ya rumgumeta tsam a jikinsa, hakan yasa ta gagara motsi, with cracking voice tace "please let go off me", yace "I will not", fashewa tayi da kuka tace "Ni ka kyaleni ka tafi can wajen sabuwar girlfriend din da kayi", ya waro ido yace "wollah bbu wata girlfriend da nayi Baby wife..", ta fara jan shessheƙa tace "Ai naji muryarta kuma har dasu bata waya tamin mgana", yace "No ba haka bane Baby", turasa tayi ita a dole sai ya saketa, ya kai lips dinsa saitin kunnenta yace "don't cry and listen to me..", yana rumgume da ita ya fara tafiya zuwa gefen gado, ya zaunar da ita snn ya duƙa gabanta gami da riƙo hannayenta cikin nasa, ta saukar da kanta ta wani sha kunu, shiru ne ya ratsa room din, shi kam kawai kallonta yake yana auna salon nata kishin, ta ɗago sukay ido huɗu, ta haɗe gira tace "Toh idan ba girlfriend kayi ba wce ta ɗauki wayar..?", ya sauke numfashi yace "Sumayyah ce fa", ta zuba masa ido tabbas sai ynxu ta ɗan gane muryar Sumayyah taji, ya murza hannunta dake cikin nasa yace "muna tare da Iron Lady xan kaita gida ne kika kira baby wife, Hajiya ta hanani yin wayar wai baxan kifar da ita a mota ba, tace wai ina driving ina waya ai baxai yiwu ba, shine na bawa Sumayyah wayar nace ta miki mgana tinda har da ita zan kai gida tare da Iron Lady...", Hajar tayi ajiyar zuciya a bit relief, yace "ina kaisu gidan zan kiraki Charge dina ya ƙare" da haka ya ciro wayarsa ya nuna mata taga tabbas ta mutu bbu Charge, ta juya lulu eyes dinta gami da turo baki tace "Amma baka dawo da wuri ba", yace "Punk... ya hanani sakat saida muka rakasa gidansa snn na samu na gudo", tayi shiru ba tace komai ba tana jin duk raɗaɗin zuciyarta yana zagwanyewa, yace "Daman nace Princess a wajenki ta koyi rigima...", tace "Ai ni nawa da dalili", ya waro ido yace "Ina dalilin anan, har an kusa bani though punishment daga an kira waya anji muryar mace", ta ɗan hararesa, murmushi mai sauti yayi ya janyota yayi kissing idanunta da suka kumbura yace "My ƴar rigima". Washe gari ƙarfe takwas Hajar ta sauka downstairs da Nanerh a hannunta, kawai ƙamshin turaren wuta da freshener ne yake tashi don masu aikinta har sun gama aikinsu, sosai take jin daɗin zama dasu sbd suna jin mgana snn ga tsafta, idan ta gaya musu abu sau ɗaya shknn, saida ta bawa Nanerh abinci ta sakata a kekenta snn ta shiga kitchen ta hau shirya musu nasu abincin, Sabrah ce ta shigo kitchen din, Hajar tace "kin gama shiryawar?", Sabrah ta gyaɗa kai tace "Eh... Addah me zan kama miki..?", Hajar ta bata cabbage tace "ki yanka sa ƙanana", Sabrah ta amshi cabbage din tace "Toh", Hajar tace "kiyi a hankali karki yanke", Hajar ta buɗe fridge ta ciro marinated chicken ta fara mata yankan tsayi tace "Sabrah ranar nan kina gayamin kinga Maimuna tana bara, kin tabbata ita kika gani..?", Sabrah tayi shiru tana tunani, Hajar tace "ba ita bace ko..?", Sabrah tace "Ni wcca nake gani har fuskarta baƙa ce, ita kuma Maimunan Maama fuskarta fara ce ƙafarta da hannunta baƙaƙe", Hajar ta girgiza kai, wnn bai isa ya zama hujja ba don Maimuna bleaching take ta iya yiwuwa ita Sabrah ta gani, Sabrah tace "kuma har ciwon da Maimuna take dashi a goshi na gani", Hajar ta numfasa ta kawar da zancen, kawai dai sai taji ta kasa samun sukuni ne, bata son ahalin Babanta a irin wnn rayuwar, she wish sauran ƴan uwanta su nutsu su koma kamar Nabilah. ★Da kyar Maimuna take jan ƙafarta da ta mata mugun nauyi sbd cikin jikinta da ya girma, tayi wani mugun baƙi sai kace wacca ta shafa gawayi, wata fatattakakkiyar roba sai kace ta kwasar kashi ce a hannunta, tayi wata iriyar rama sai kace wcca ta shekara goma tana jinya, gida ta shiga wanda a ynxu ya sake ruɓewa, tana shiga soro ta tsaya ta janyo duƙunƙunannen hijab dinta da ya koɗe ta goge hawayen da suke sauko mata, wucewar da za tayi wajen shagon Iliya mai awo aka samu wni mutum ya gwaɓa mata mgana, da haka ta shiga gida tana jan ƙafa, sororo tayi tana kallon Maama dake sanye cikn wasu ruɓaɓɓen kaya duk sun zama tsumma, Maimuna tace "Maama..", Maama ta ɗago ta kalli Maimuna sai kuma ta saukar da kanta, Maimuna tace "Na shiga uku... Maama mai ya faru dake", Maama tace "ciwon Sa'adatu ne ya tashi tayi min duka", Maimuna ta ƙarasa ciki tace "Tana ina..?", Maama tasa haɓar zani ta toshe hancinta da ke yoyon jini tace "da kyar na samu na rufeta a ɗaki", Maimuna ta ajiye mushiyar robar dake hannunta ta matsa gaban windown ɗakin da Maama ta rufe Sa'adatu, malelekuwa kawai Sa'adatu take a ƙasar ɗakin da ko leda babu, gurnani take sai kace mage lokaci guda kuma saita kurma wni uban ihu, Maama ta leƙa robar da Maimuna ta ajiye sai kuma tace "yau baki samo komai a wajen maular ba..?", Maimuna tace "Na samo naira talatin", Maama ta fara matsar kwalla tace "yau ko na kwakin bamu samu ba knn... innalillah wa'inna ilayhirraji'un", rabonsu da abinci tin shekaran jiya kuma shima dai garin kwaki ne suka jiƙa bbu sugar suka ci, su duka ukun rabin gwangwani suka sha sbd shi suka samu, Maimuna ce mai fita tayo bara saita samo musu na kaiwa baki, toh ynxu itama Maimunan idan ta fita ba samo abincin take ba, Sa'adatu kam hauka take tuburan lokaci zuwa lokaci, idan haukan bai motsa ba sai kaga ta zauna waje ɗaya tanata kuka, idan kuma ya motsa saita ringa doke doke, abin nata dai sai kace shafar aljanu, kuma idan ta tashi doke doke akan Maama take durango, tana dukanta tana kuka tana mata Allah ya isa da Allah wadai, Maimuna tace "kin bata ruwan tofin..?", Maama tace "shi naxo bata ta cafkeni ta lakaɗa min na jaki", Maimuna tayi zaman daɓaro a ƙasa ta rasa abinyi, rana zafi inuwa ƙuna, wnn wace irin rayuwa ce suke yi, tinda Allah ya yiwa Baba rasuwa duniya ta juya musu baya, ashe da cikin wadata suke da rufin asiri amma ruɗin zuciya ya hanasu gani, haƙiƙa mahaifiyarsu ta cucesu matuƙa, ta sabauta musu rayuwa, ta musu gurguwar tarbiyya ta hanasu bin ta mahaifinsu ta gsky, Maimuna ta miƙe ta nufi soro, Maama tace "ina zaki..?", Maimuna tace "zanje in nemo abinda zanci ne Maama, wllh yunwa nake ji kamar zan mutu, ƙirjina ma ciwo yake" tana gama fadin haka ta fita, bata bi ta hanyar shagon Iliya mai awo ba ta zaga ta baya, da ƙyar take jan ƙafarta bata ma san inda ta dosa ba, kawai ganin mutum tayi a gabanta, ya busa mata hanyaƙin wiwi da yake sha a fuskarta, Maimuna na ɗaga kai taga Bisi Ƙwale, ja da baya tayi ta zagaye zata wucesa, ya kashe wutar wiwin da yake sha a goshinta snn ya buɗa murya yace "kere na yawo zabo na yawo don haka dole su haɗu, yau bbu abinda zai hanani kakkafaki a nan wajen", Maimuna ta hau sosa goshinta da ya kwaile sbd wutar da Bisi Ƙwale ya manna mata, juyawa yayi ya leƙa kangon da suke zama ya kira Ƙwage, yana juyowa yaga bbu Maimuna a gabansa ta gudu, can ya hangota har ta masa nisa, ai kam tini ya saki iskar wandonsa yabi bayanta, Ƙwage ma da ya fito ya rufa masa, Allah ya taimaki Maimuna ta afka cikin gida, tana ƙoƙarin saka sakata Bisi Ƙwale ya banko ƙofar, ai kam gaba ɗaya ƙofa ta sauka daga jikin gini don ta gama ruɓewa, da gudu Maimuna ta shige cikin gida, Maama na tmbyarta lfy ina ba amsa, Bisi Ƙwale ya ɗauki wni icce da ya gani ya rufesu da duka, Ƙwage ya ɗauki wata murgujejiyar taɓarma, tashin farko ya saukewa Maama ita a cinya, Maama ta zube ƙasa cikin gunjin azaba, Maimuna ta rarrafa banɗaki Bisi Ƙwale ya bita yana sauke mata itace a gadon baya, ihu Maama da Maimuna suke suna neman agaji, Ƙwage yace "tsinanniyar yarinyar nan da tasa aka kaini gidan kaso..", Bisi Ƙwale yace "mu ƙaddamar musu kawai", Sa'adatu da ta ɗan dawo hankalinta ta leƙo ta window, ai kam Ƙwage ya hangota, ya saka taɓarya ya bige ɗan ƙaramin kwaɗon da aka rufe ɗakin ya shiga, saida ya shemar da Sa'adatu snn ya murguza mata tabaryar a baki gaba ɗaya haƙoranta na gaba guda shida suka sabauce, uku suka zube a take ragowar ukun kuma suka shige cikin dadashi, tini Sa'adatu ta sume don haka Ƙwage ya rabu da ita, Bisi Ƙwale ya fito daga banɗaki da ya tarfa Maimuna yana zazzare ido bayan yaga ta dena motsi, Ƙwage ya ɗaga tabarya ya ɓaurawa Maama a goshi, Bisi Ƙwale yace "Zo mu ware", da sauri suka fita daga gidan bayan sun wurgar da makaman da sukay aika aikar............✍️ 💛 HAJAR 💛 {98..} ★Hajar ta fito balcony zata kira Sabrah da ta fito da Nanerh tana mata wasa, a tsakiyar compound ta hangosu suna kallon gate, daga ƙofar gate din kuma Binta ce mai aiki da Inuwa mai gadi, mai gadi yayi kane kane a bakin ƙofa alamar wni ya hana shigowa, Binta tace "ka ga Inuwa don Allah kaɗata wnn wace irin almajira ce mai nacin tsiya", daga waje Maimuna da hannunta ke nannaɗe da tsumma hawaye na bin kuncinta tace "dan girman Allah ku barni na shiga wajen ƴar uwata", Binta ta mata wni kallon tara saura kwata tace "wace ƴar uwar taki", Maimuna tace "wllh ni ƴar uwar matar gidan ce ubanmu ɗaya...", Binta tace "Chasss kuji mahaukaciya ke kin isa ki zama ƴar uwar matar gidan nan, ke asuwa..", Maimuna ta fashe da kuka tace "dan Allah ku bar ni na shiga..", Binta tace "kaga Inuwa bani hanya na koyawa jakar nan hankali", Inuwa yace "A'a bari ni na koya mata, wllh idan bata bar ƙofar gidan nan ynxu ba saina sumar da ita", Binta tace "barni da ita kawai, kar ka taɓata ace ka taɓa mai rai, wnn idan ka taɓata ai sai ka mata mummunar illa", Inuwa ya matsa daga jikin ƙofar, Binta ta maye position dinsa tana kallon Maimuna tace "baiwar Allah tin muna shaida juna ki tafi", Maimuna tace "ku dubi girman Allah...", ko jin sauran maganar Binta ba tayi ba ta zage ta hankaɗata tace "ke kin san girman Allahn da muka haɗaki dashi kika ƙi tafiya", Binta ta banke ƙofar gidan ta bar wajen, cikin gida ta dosa, Hajar dake tsaye balcony bayan ta saka Sabrah sun koma ciki da Nanerh tayi kiranta, da sauri Binta ta tafi wajen Hajar, tana isa gabanta tayi bowing tace "Anty gani..", Hajar tace "me ya faru a bakin gate na ganki a can kuna hayaniya...?", Binta tace "Wata mata ce wai saita shigo, irin Almajiran nan masu kama da tubabbu, wai cewa tayi ke ƴar uwarta ce shine ta bani haushi na kulle ƙofar", Hajar ta kalli gate din sai kuma tace "ta tafi ko tana nan...?", Binta tace "Wllh ba sani ba, amma da kyar idan ta tafi don irin wadan nan mutanen akwai baƙin naci", Hajar ta kunce mayafin doguwar rigarta da tayi ɗan kwali dashi ta yafa a wuyanta, walking a bit fast ta nufi gate, Binta tabi bayanta tace "Anty kar kije wajen wnn matar ba a rasa cuta a jikinta ba", Hajar bata tanka mata ba ta cigaba da tafiyarta har ta isa gate, tana zuwa gate din kam tasa Inuwa da ya koma kan kujera ya buɗe mata, ana buɗe ƙofar Maimuna dake maƙale da gate zaune rashadan a ƙasa ta ɗago kanta tana kallon Hajar, Hajar ma ta ringa kallonta tana ƙanƙance ido don bata ganeta ba, da rarrafen hannu ɗaya Maimuna ta rarrafa ta riƙe ƙafafuwan Hajar tace "ƙoƙon bara da maulata na kawo miki Hajara, dan girman Allah ki temaka min", Hajar ta ɗan ja da baya tana kallon Maimuna, Binta ta ɗauki farar kujerar da mai gadi yake zama ta tura Maimuna da ita tace "ke karki sake taɓata, muka san wace irin cutar ce a jikinki", Maimuna bata haƙura ba ta sake rarrafowa ta riƙe ƙafar Hajar tace "kar ki duba halina Hajara, kar ki duba halin mahaifiyata, kar ki duba halin ƴan uwana, ki duba girman Allah da Manzonsa, dan darajar Allah da ma'aiki ba dan ni ba ki taimaka mna Hajara, duniya ta mana ruku'un dila, masifa da bala'i ta ko ina Kunno mana kai suke, ƴan uwanmu duk sun gujemu, makwabta babu wnda yake jin kukanmu bare ya jiƙanmu, ke kaɗai ce wcca nake tunanin zaki taimaka mna...", Binta ta ɗaga kujera zata mangare Maimuna Hajar tace "rabu da ita Binta", Maimuna ta rushe da kuka tace "ki duba mahaifinmu Hajara", kukan ma da kyar Maimuna take yi sbd galabaita, ko mai cutar kwasheko ya fita kyan gani, Hajar taji wata ball ta tsaya mata a throat, Allah sarki Baba tabbas yaga jarabawa akan Maimuna da Sa'adatu da uwarsu Maama, ya haifi fanɗararrun ƴaƴa da suka zama annoba cikin al'umma, da ɗacin murya Hajar tace "idan tukunya tayi ɓori...", Maimuna tace "haƙiƙa kanta take ɓatawa", Hajar ta dubi Inuwa da Binta tace "ku fitar min da ita", wni azabar haushin Maimuna taji bayan ta tuna yacca suka gallazawa Baba, yadda Baba ya sha wahala akansu, ba ta jin zata iya taimakon su Maimuna bayan abinda suka yiwa Baba, habawa ai tuni Inuwa ya figi Maimuna ya jata ƙiyyy Binta na taimaka masa, Hajar ta juya da nufin komawa ciki amma saita kasa tafiya, tana jin Maimuna nata ihu, katamau Maimuna ta riƙe jikin gate su Binta na janta, Hajar tayi wni tunani saita juya tana kallon Maimuna, ai wni yana cin arzikin wani, Naseer da Huzaifa da Nabilah duk ƴan uwan Maimuna, tsakanin Naseer da Huzaifa bbu wnda ya taɓa mata wulaƙanci duk kallon ƙanwa kuma ƴar uwa suke mata, Nabilah ma a ynxu tana alfahari da ita kuma zata nunata a ko ina a matsayin ƴar uwarta, a da ne suka saɓa amma ynxu komai ya wuce, uwa uba kuma mahaifinsu ɗaya da Maimuna wnda ko taƙi kota so jini guda ne yake gudana a jijiyoyinsu, Hajar tayi ƙarfin halin yin magana ta dakatar dasu Binta, Maimuna ta sake rarrafowa har guiwarta ta dauje fatar wajen ta kwaile tace "ko kuɗin zuwa asibiti ne ki taimaka mna dashi, ga Maama can a gida ƙafarta zata ruɓe, ta karye a cinya har yau ba'a ɗorata ba, Sa'adatu kuma bakinta zai ruɓe haƙoranta duk sun shige dadashi". Can boys quarters Hajar ta kai Maimuna, ta saka Zaituna ɗayar mai aikinta ta kaiwa Maimuna ruwa da abinci, hannu baka hannu ƙwarya Maimuna ta rufa kan abinci, abincin da ta ci ko gardi albarka, Hajar ta ɗauko kaya cikin kayanta da ta fitar na bayarwa ta kaiwa Maimuna tace ta shiga toilet dake nan boys quarters din tayi wanka ta canza kayan jikinta, ko don ɗoyin da take bazata shiga da ita cikin gidanta ba, Maimuna ta shiga wanka Hajar ta fito daga boys quarters din ta shiga main building, a palournta na upstairs taga Sabrah tare da Nanerh da ta baza mata kayan wasanta, Hajar ta wuce bedroom dinta, wayarta ta ɗauka ta shiga kiran Umma, Umma na picking bayan sun gaisa Hajar ta wassafa mata me ya faru, Umma ta jinjina wnn mganar snn tace "ynxu haka ita Maimunan tana nan gidanki..?", Hajar tace "Eh, wai da zuwa anjima saina kaita gida...", Umma ta katseta da faɗin "ki kaita gida sbd ke kika kawota ko...?, karki kuskura ki fita daga gidanki akan wasu can mutanen da mutunci bai ishesu ba, kuma ynxu ba sai anjima ba ta bar miki gida", Hajar tace "Toh Umma, tace Maama da Sa'adatu na kwance ba lfy", Umma tace "Toh Allah ya basu lfy... ynxu ki tashi ki sallameta", Hajar tace "Tom" da haka ta kashe wayar, yadda Umma tace haka Hajar tayi, haka nan ta sallami Maimuna bayan ta bata kuɗi tace ta kai su Sa'adatu asibiti, Maimuna kamar zata haɗiye harshenta wajen yiwa Hajar godiya sai kace wacca ta bata arziƙin duniya. Umma suna gama waya da Hajar bata ajiye wayar ba ta kira Naseer, har ta gama ringing ta katse bai ɗaga ba, tana ƙoƙarin sake kira sai gashi ya kira, da ladabi Naseer ya gaida Umma, ta amsa masa kafin tace "Allah yasa dai baka koma Lagos din ba..?", yace "Ai kam dai ban koma ba gobe ne zan juya", Umma tace "Toh ina son ganinka yau din nan, idan ma zai yiwu ka taho ynxu", yace "Tom Umma". After like 40mins bayan nan Naseer ya iso gidan, da yaji Umma na nemansa urgent shine ya bar abinda yake ya taho, ita kanta Umma saida tayi mamakin yacca ya iso cikin ƙanƙanin lokaci, gaisuwa ya sake tisa mata duk da sun gaisa a waya, Umma tace "ban dai matsaka ba ko Naseer..?", yace "A'a ba damuwa Umma", Mu'azzam ne ya fito daga ɗakin Umma, Umma ta kallesa tace "ka ganshi..?", Mu'azzam yace "Eh" yana gyara agogon hannunsa, Naseer ya kalla yace "Yaya ina wuni", Naseer yace "lfy lou Mu'azzam... ya aiki..?", Mu'azzam yace "wllh Alhmdllh", Naseer yace "Toh yayi kyau Allah ya taimaka", Mu'azzam ya dubi Umma yace "Umma na fita", tace "Toh sai ka dawo Allah ya tsare hanya...", yace "Ameen" da haka ya fita, Umma ta ɗan sauke ajiyar zuciya tana kallon Naseer da kyau tace "ya wajen ƙannenka su Maimuna da Maama kuma..?", ya shafa kansa yace "suna nan lfy", Umma ta girgiza kai tace "A'a ba lfy ba Naseer, Anya kwa kana zuwa inda suke", ya saukar da kansa baice komai ba, Umma tace "baka zuwa knn..?", yayi ajiyar zuciya yace "Ina gudun fushin mahaifiyata ne, Maama ƙoƙarin yimin baki take akan abinda bai taka kara ya karye ba, ina yin iya ƙoƙarina na ganin na sauke haƙƙinsu a kaina amma Maama bata gani, indai naje gidan sai Maama ta faɗi mganar da zata min illa a rayuwa, ita da kanta tace idan na sake zuwa inda take saita tsine min, wnn dalilin ne yasa na jima banje gidan ba..", Umma ta girgiza kai tana auna gidahumanci da jakanci irin na Maama, Umma tace "Naseer ka daure kaje wajen mahaifiyarka, na tabbata ynxu bazata tsine maka ba, wncan karon ma faɗi kawai take amma baza tayi ba, bbu wata uwa da ta tsani ɗan ta har zata tsine masa bayan ya kasance mai mata biyayya", Sosai Umma ta gayawa Naseer mgana mai daɗi wcca tasa ya sauko daga dokin fushin da ya hau, har saida ya mata alƙawarin daga nan zai wuce wajen Maama. Ko da Naseer yaje gidansu wajen Maama kai tsaye taxi ya kirawo aka ɗura su Maama zuwa asibiti, ita kanta Maimuna data ɗan dawo hayyacinta bayan ta dawo daga gidan Hajar asibitin a kai da ita, shi dai Naseer kawai bin Maimuna yake da kallo ganin turtsetsen ciki a jikinta, ana kaisu asibiti aka shiga da Sa'adatu Theater aka ciro haƙoran da suke shige mata dadashi, Maama kam babban aiki aka shirya yi mata sbd karaya biyu ta samu a ƙashin cinya kuma ƙafa ɗaya, in banda kuka babu abinda Maama take tana cewa Naseer ka kiramin Nabilah da Huzaifa na gansu, zuwa washe gari akace za a yiwa Maama aiki a ƙashin cinya, likitoci sunce idan ya wuce gobe to saidai a datse ƙafar, Naseer ya kira Huzaifa yace ya kamo hanya, shi daman Huzaifa dan i don't care ne ga kuma zuciyar tsiya, tintini yayi watsin uwar watsi da lamarin su Sa'adatu da ita kanta Maaman, gashi Naseer ya gaya masa yacca sukay shiyasa ya sake fusata, a daren ranar kuwa Huzaifa ya iso Kano daga Dutse, saida ya fara duba Maama a ward din ƴan karaya snn ya wuce ward din da Sa'adatu take don itama tana jin jiki, Nurse ya tarar tana bata Yoghurt kasancewar bbu mai kula da ita mace, Huzaifa ya ringa kallon Sa'adatu kafin yace "wane ya fille mata kunne ɗaya..?", Nurse tace "A haka muka ganta dashi". Washe gari an shiga da Maama surgery knn saiga Nabilah, Umma ce ta kirata a waya ta sanar da ita abinda yake faruwa, itama Umman Naseer ne ya gaya mata yace duk an kwantar dasu a asibiti, Saida aka yagalgala tsokar Maama snn aka samu yi mata ɗorin ƙashi, wai nan ma don asibiti ne, baiwar Allah Nabilah ita ta ringa ɗawainiya da uwarta da Sa'adatu, Maimuna kuma Huzaifa ya kaɗata gida sbd tsohon cikin da take dashi, daga shi har Naseer sosai wnn cikin nata ya tsaya musu a rai, Maimuna da aka kaɗa gida ce take jagwalgwala abincin da ake kaiwa asibiti...........✍️ 💛 HAJAR 💛 {99..} Kwanansu Maama uku a asibiti aka canza Sa'adatu zuwa na mahaukata, lokaci guda ciwon nata ya tashi ta fara dukan Nurses, allurai aka ringa garƙama mata a asibitin mahaukatan, da aka mata gwajin kwakwalwa Sai aka ga kwakwalwar nata lfy lou bbu cuta, gida aka mayar da ita aka duƙufa neman mgani na Aljanu tinda ana tunanin su suka shafeta, Maama kam satinta biyu a asibiti tana jinya, ranar da ta cika sati biyu da kwana biyu aka sallameta, Naseer Huzaifa da Nabilah ne suke ta tiri tiri da ita. Washe gari Maama na zaune tsakar gida akan tabarma ta miƙe ƙafar data karye, Nabilah ta kawo mata abincin da ta dafa, Maama ta kalli Nabilah da idanunta da suka cika da ƙwalla tace "Allah ya miki albarka Nabilah", Nabilah tace "Ameen", Maama ta janyo ƙasan rigarta ta ringa goge hawayen da suka shiga sakko mata, da yammacin ranar Naseer ya shigo, tabarmar da Maama ke zaune tana jinyar ƙafa ya nufa, ya duƙa gabanta yana tambayarta ya jiki, kawai saita fashe da kuka wiwi, nadama da dana sani ne fal cike da zuciyarta, Naseer yace "Maama ki dena wnn kukan dan Allah..", Maama ta fyace majina tace "dole nayi kuka Nasiru, ban yiwa kaina adalci ba, ban yiwa mahaifinku adalci ba, ban yiwa ƴaƴan da na haifa adalci ba, haka zalika ban yiwa mutanen da na zauna dasu adalci ba, haƙƙin mutane ma kawai ya isheni, da baƙin cikina da na ƴaƴana da na yiwa gurguwar tarbiyya mahaifinku ya rasu, Nasiru dole nayi kuka idan na tuna haukan dana tafka...", dai dai nan Huzaifa ya shigo da ledar fruit da ya siyowa Maama, Huzaifa ya zauna kan dokin ƙofa yayi kiran Maimuna, daga ɗaki ta fito tana jan ƙafa, rama sosai ta ƙara gashi ta wani ɗashe kamar bbu jini a jikinta, ta samu guri ta zauna da kyar tace "Yaya gani", Huzaifa ya kalleta da ɗacin rai sai kuma ya dubi Naseer yace "Yaya ya za muyi da wnn...?", Naseer ya sauke ajiyar zuciya yace "Ai saita faɗi waye ya mata cikin", Huzaifa ya murtuke fuska yana kallon Maimuna yace "Ke..!!", Maimuna ta sunkuyar da kanta, Huzaifa ya daka mata tsawa yace "ba kiji mai akace ba", Maimuna tasa bayan hannu ta shaɓune hawayen dake sakko mata tace "wllh ban sani ba", Huzaifa yace "baki sani ba kamar ya, a ruwa ake sha..?", Maama tace "Maimuna kiyi mgana mna, nan ƴan uwanki da kika gani masu ƙwato miki haƙƙi ne", Maimuna tace "Billahillazi la'ilaha illa huwa ban sani ba, fyaɗe aka min" ta rushe da kuka. Tsakar dare naƙuda ta kama Maimuna, tun tana jurewa ita kaɗai har ta ja jiki ta tashi Nabilah, Nabilah da taga bazata iya da Maimuna ba ta tashi Maama, ga Maama ba ƙafa saidai jan buttocks, Maama tasan naƙuda ce ta tahowa Maimuna, mgana ake ta tsakar dare bbu abin hawa ballantana a kaita asibiti, Naseer da Huzaifa ne suka tafi neman abin hawan, Maama ganin haihuwa ta taho don har Maimuna ta fara nishi kan ɗaya ya taho ta kalli Nabilah tace ta bata reza, Nabilah ta lalubo reza a jakarta wcca ta taɓa amfani da ita sau ɗaya, a duk wnn zazzafar wainar da ake toyawa Sa'adatu bata san anayi ba, kawai bacci take sai kace mushe, cikin azaba Maimuna ta haihu, ta haifi ƴa mace, saidai kuma tana haihuwar jini ya ɓalle kamar an yanka rago, wata mummunar tear ta samu tin daga sama har ƙasa ta yage, Nabilah ta naɗe jaririyar ta ajiyeta a ƙasa, gaba ɗaya sun gigice ganin yacca jini yake malala, cikin azaba da raɗaɗi Maimuna tace "wayyoh Allahna Maama, ƙirjina zai fashe", Nabilah ta rushe da kuka ta fita a guje ba tare da tasan ina ta nufa ba, lokaci guda Maimuna ta fara convulsion idanunta suka ƙaƙƙafe, hakan tasa Maama ta manta da karayar cinyarta ta miƙe a gigice ta nufi ƙofa, da ƙarfi ta taka ƙafar ai kam ɗorin ya goce, ƙashin ya huda tsokarta ya ɓillo waje, azaba tasa Maama ta tafi luuu ta faɗi a ƙasa bayan kanta ya daki dokin ƙofa. Nabilah kam ashe maƙota ta je ta ringa bubbuga ƙofa, cikin sa'a gidan Mukaila suka buɗe ta taho tare da matarsa, suna zuwa suka tarar da Maimuna Allah ya amshi abarsa, Maama kuma ta sume, kukan jaririyar Maimuna ne kawai yake amsa ƙuwwa a gidan. ★Wajen ƙarfe 10 na safe Hajar ta shiga part din Nurain, direct bedroom ta wuce, bata gansa a bedroom din ba don haka ta shiga closet, ta ɗan waro ido ganin kayan da yake sakawa tace "fita za kayi Husband..?", yace "Uhmm", tace "Ohk" sai kuma ta ƙarasa ciki ta tsaya daf dashi tace "fatan dai ba a min nawa aikin ba..?", yayi murmushi yace "yeah", ya miƙa mata links din da yake shirin sakawa, amsa tayi ta maƙala masa snn ta ɓalle masa buttons din riga, tace "Wai ina zaka yau fa Saturday..?", yace "you know Hammad..?", tace "Eh", yace "shine ya kirani ya bani location yace na samesa a wajen, sunxo kano ne sbd sunji labarin wani yaga ƙanwarsa Azeeza da ta ɓata anan garin", tace "Mother din wnn yaron da muka gani a gidansa..?", yace "Ashraaf... Eh Mamansa", tace "Allah ya bayyanata..", yace "Ameen", Hajar kawai Ashraaf take hangowa, har yau horse toy din da ya bawa Nanerh yana nan tana wasanta dashi, tace "breakfast is ready, sai kaci zaka fita ko..?", yace "Eh", tare suka fito, Hajar ta wuce ta sauka downstairs, shi kam room din Nanerh ya buɗe, kan floor mattress dinta mai faɗi ya ganta ga toys nan iri iri zagaye da ita, yayi murmushi yace "Princess", tini Nanerh ta jefar da toy din hannunta ta rarrafo da sauri inda yake tana ɓangala masa dariya, ya sunkuya ya ɗauketa ya ɗan cillata sama, nan ma ta kyalkyale da dariya, pecking cheeks dinta yayi, sai ƙamshin baby colories da perfume take, fess da ita kamar uwarta, an kama mata cikakkiyar sumarta da cotton band, Hajar na tsaye dining section tana serving abinci taji saukowarsu, ta ɗaga kanta ta kalli Nurain da Nanerh take wawurar hancinsa yana kaucar da fuska tace "Ehen ka ɗaukota ta hanamu cin abinci ko bayan ita ta cika stomach dinta", ya ƙarasa dining din ya zauna a kujerarsa sai kuma ya ɗora Nanerh kan table suka cigaba da wasansu, Hajar na gama zuba masu abinci ta shiga wani room dake downstairs, few secs ta fito da keken Nanerh, ta ajiye keken daga gefen kujerarta snn ta amshi Nanerh a hannunsa ta sakata cikin keken, ta ɗago kanta sukay ido huɗu dashi, ta ɗan turo baki tace "wnn uwar hidimar ce zata bar mu muci abinci lfy, ynxu zata baddala table din", da haka suka fara cin abincin, Hajar na bawa Nanerh wnda zata iya ci cikin abincin. Ƙarfe 11 da wni abun Hajar na closet dinta tana sake kimtsata duk da cewa a gyare take, tana aikin tana humming song, bayan ta gama aikin ta fito, wayarta da ta ajiye gefen gado kusa da Nanerh da take bacci ta ɗauka, 5 missed call from Umma, haka kurum taji gabanta ya faɗi, kiran Umma tayi, bayan sun gama wayar Hajar ta zauna gefen gado ta dafe kanta tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un". A ranar Hajar taje gidan rasuwar ta tarar da Umma acan, duk wnda yaji irin mutuwar da Maimuna tayi sai zuciyarsa ta karye, mutuwa ce ta shahada, ƴarta na nan goye a bayan Nabilah, wujijjigar da Maama tayi ba a cewa komai, bayan an kaita an gyara mata ɗorin da ya sake ɓarɓarcewa tace a dawo da ita gida bazata zauna a asibiti ba, sai ranar sadakar uku snn Hajar ta sake zuwa gidan rasuwar, abinci mai kyau ta kai wnda ta saka su Binta sukay, gidan rasuwar a ɗaɗe yake mutane ƙalilan ne suke zuwa, Hajar na zaune can gefe a tabarma ɗaya da Nabilah wacca take bawa ƴar Maimuna madarar da Huzaifa ya siyo mata, Ita Hajar jira take Umma tazo sai su tafi tare, ai kam bbu jimawa Umman tazo tare da Mu'azzam da Sabrah, Umma ta yiwa Maama ta'aziyya, Mu'azzam ma ya mata, Maama saidai ta gyaɗa kai don bata iya mgana tsabar yacca mutuwar ta daketa, Naseer ne ya shigo Umma ta masa ta'aziyya hakama Hajar, ya tashi zai fita Maama tace "Naseer karka fita, ka kirawo Huzaifa ma", Naseer yace "Toh", ya ciro waya ya kira Huzaifa wnda shima yana kusa, bbu jimawa kam ya shigo, Maama ta ɗan yunƙura tana kallon Mu'azzam tace "Mu'azzamu a bakacin Maimuna ni ina nema mata yafiyarka, dan Allah ka yafe mata abinda ta maka", Mu'azzam ya shafa kansa yace "Na yafe mata duniya da lahira", Maama ta kalli Umma tace "Faɗima dan girman ki yafemin abinda na miki, haƙiƙa na cutar dake ban barki kin zauna lfy a gidan mijinki ba, na cutar dake haka zalika na cutar da ƴaƴanki", Umma ta numfasa tace "na yafe miki, Allah ya yafe mana duka", Maama ta share hawayen da suke zubo mata tace "kowa da yake zaune nan nasan bbu wnda bashi da tabona, ku yafemin ba don halina ba", shiru tsakar gidan yayi bbu wnda yace komai, Sa'adatu ce ta fito tana cewa "Maama ni baki nemi gafarata ba bayan kece kika sabautamin rayuwa, duniya ta min ruku'un dila, duniya ta min gwatson kyanwa, duniya ta min juyin kwaɗo, duk kece sanadi Maama, Allah sarki Maimu Allah ya jiƙanta ya gafarta mata, ni bazan ce komai ba akan mummunar laifin dana tafkawa mahaliccina ba saidai zan dawwama yin istigfari har na koma garesa, ina masu hali irin nawa..?, ƴan mata, zawarawa, matan aure wnda suke aikata abinda yafi zina bala'i suke neman jinsinsu, ina kira da masu irin wnn hali nawa dasu tuba tin kafin lokaci ya ƙure musu, duniya ba wajen tabbata bace lokacinta ƙalilan ne, Zeenatu Mabaruka Teema da tsinanniyar shugabarmu mai ƙungiya naga darisa akansu da kuma kaina, bbu wnda acikinmu wnda bai amshi hukunci ba, nima na amshi nawa, ƴar uwa ki tina ba'a nan masifar take ba sai mutuwa ta riski bawa, rayuwar kabari har lokacin da zata tsaya gaban mahaliccinka domin amsar hukunci, Ni Sa'adatu nayi nadama kuma ina kira da masu irin halina su gyara tin kafin lokaci ya ƙure musu....", daidai nan ta zube ƙasa ta fara haukan nata tana kuka, Huzaifa ya jata ɗaki ya kulle tin kafin ta fara doke doke. Mijin Nabilah yayi kawaice sosai don baice ta dawo gida ba har Maama taji sauƙi, toh saidai ace sauƙi amma kuma ba sauƙi ba don ƙafar shanyewa tayi ta warke a haka, Maama bata iya tafiya saidai da sanda ko kuma ta hau keken guragu, ƴar Maimuna da aka mayar mata da sunan uwarta Nabilah ce ke kula da ita, Sa'adatu an ɗan samu waraka ta dalilin rubutun da ake bata. Da Nabilah tazo tafiya tace zata tafi da Maimuna ƙarama, Maama tace A'a ta bar mata ita wnn yarinya a jikinta take ganin kurwar Maimuna kuma gashi tana kama da uwarta, da kyar Maama ta shawo kan Nabilah akan yarinyar tace bata san ya dangin mijinta zasu amshi yarinyar ba snn kuma bata so wni abun ya haɗata da mijinta. Life continues... Naseer da Huzaifa suka haɗa hannu suka canzawa mahaifiyarsu gida ta bar unguwar dala, gwara ta bar unguwar ta koma inda ba a santa ba inda za a santa da sabon kyakkyawan halinta na yanxu, bil ƙalbi warruhi Maama take kula da Maimuna ƙarama da taimakon Sa'adatu wcca taji sauƙi sosai saida ta nakasta ainun don ba tada haƙoran gaba da kunne ɗaya, haka abun yake shegiya dai Maama ta ganta a kanta, yacca take kiran Hajar shegiya a da ynxu itace take rainon shegiya, shegiyar da take masifar mutuwar so. bayan watanni biyar akay auren Naseer inda ya auri ƙawar Hajar wacca sukay Islamiyya tare wato Zainab, idan kaga yacca Umma da Maama suke ynxu kai ka ɗauka basu taɓa zaman hatsaniya ba, sosai Umma ta shiga bikin Naseer akay da ita, Alhmdllh arziƙin Naseer ya ƙara burunƙasa don ynxu ba direba bane, acan dry port ta Lagos da Port Harcourt ya samu babban aiki, murna a wajen Hajar ba a cewa komai da Yayanta ya auri ƙawarta Zainab, Huzaifa ya baro Dutse ya dawo Kano da aikinsa, shima an kai kuɗinsa wajen budurwarsa dake dutse, Mu'azzam kam tukunna dai don tasa wife to be din Insha Allah bata isa aure ba, Anty tace ta basa Humairah, ita kuma Umma tace ta bawa Abdallah Sabrah, hakan zai sa zumunci ya ƙara ƙulluwa snn dangin ya ƙara girma......✍️ 💛 HAJAR 💛 {100..} Hajar ta shirya snn ta shirya Nanerh don yau juma'a ranar Umma zata tare a sabon gidan mijinta, bayan ansha gwagwarmaya Umma ta amince tayi aure, Kawunanta ne suka haska mata hanya yayinda Anty ma ta nusar da ita, tabbas aure shine rufin asirinta da na ƴaƴanta, ba a cewa uwarsu zaman kanta take ba ko kuma a kirasu da ƴaƴan mace, gashi kuma daman ba wni tsufa tayi ba don a shekara arba'in biyar kawai ta ɗora a kai, Babban mutum Umma ta aura wnda ya samu kyakkyawar shaida, danƙareren gida ya mallaka mata wnda anan ne zata zauna a gidan da yake matsayin nata, hakan tasa Umma ta tafi da yaranta biyu da suke gabanta, Mu'azzam da yake wni ɗan noƙewa wai shi babba tini ya saki jikinsa domin kwa a zahirin gsky mijin mahaifiyarsu mutumin kwarai ne kuma har ya fara musu riƙo irin na uba, tin safe sai yamma Hajar ta koma gida bakinta har kunne, ƴan uwanta sai samun cigaba suke a rayuwa, Ummanta ma has move on. Rayuwa mai mugun azabar daɗi da tsafta Hajar da Nurain suke shimfiɗawa, Happy family knn, shekarar Nanerh ɗaya Hajar ta yayeta daga mama, bbu wnda suka gayawa anyi yayen tsakanin Umma da Mami sbd kar wani yace a kaita wajensa, Nurain ne ya kissifa wnn shawarar don baya son a rabasa da Princess dinsa ko da kuwa na kwana ɗaya ne, Hajar ma tayi na'am da hakan don ita bata so a rabata da ƴarta, yarinyar akwai shiga rai da kyau kamar a sace, Hajar ba ta sha wni wahalar yaye Nanerh ba don already yarinyar ta kama abinci, tin kafin ma ta yayeta bata fiya shan mimin ba sai an bata, Nanerh na nan chubby da ita sai ma kyau da ta ƙara bbu wata rama na yaye. A kusan tare Hafsah da Khausar suka haihu, Khausar ce ta fara haihuwa ta haifi baby boy snn Hafsah da itama ta haifi baby boy, Nabilah kuma har yau Allah bai kawo haihuwar ba duk da cewa ta riga Khausar da Hafsah aure, komai iri ɗaya na kayan barka Hajar ta bawa Hafsah da Khausar, Hajar da taje barkar Hafsah sai taji dama ta kwana kawai sbd Nurain baya nan ya tafi Lagos wni workshop, amma dai bata kwanan ba tinda mijinta bai bata wnn damar da zai tafi ba, ranar da zai dawo tin asuba Hajar take shirin tarbonsa, kunshi da kitso daman tin jiya aka mata, favourite dinsa ta dafa iri iri, wajen sha ɗaya ya iso gidan, habawa kaga rige rigen zuwa tarosa tsakanin ƴa da uwa, Nanerh har dasu tuntuɓe, Hajar ta cake taƙi ƙarasawa ta tsaya kallon Nanerh, Nurain ya ɗauketa snn ya cillata sama, dariya kawai Nanerh ke ɓaɓɓaka masa, yayi pecking cheeks dinta yace "Princess", Hajar ta riƙe ƙugu kamar gske tace "wnn yarinyar..", Nurain ya ajiye Nanerh kan kujera ya wuce gurin Hajar ya rumgumeta, tace "Sannu da zuwa My Moon", yayi kissing lips dinta lightly yace "yawwa wifey". Bayan sallar la'asar Nurain yace Hajar ta shirya zata rakasa unguwa, veil da jaka kawai taje ta dauko tinda a shirye take, bata zama a hargitse a gidanta gsky, Nurain har ya ɗauki Nanerh sun fita compound, Hajar na fita compound ta nufi parking space ta buɗe front seat din motar da suka shiga, Hajar ta kalli Nanerh dake zaune a spot din da yake nata tana shan sweet, Hajar tace "ke Papa's bear or Princess kike that's my spot", Nurain ya ɗauke Nanerh daga kan kujerar, Hajar ta shiga ta gyara zamanta ta rufe ƙofa, sai a snn ya miƙa mata Nanerh, saida suka isa gidan Anty Zulaihah snn Hajar ta san nan din zasu ita tasha ma wni gurin ne daban, bayan sun gaisa da Anty Zulaihah wcca ta dauki Nanerh tana mata wasan kakanni Hajar ta tashi ta shiga ɗakin da Khausar take, tare ta ganta da Farooq wnda yake riƙe da babynsa, shima zuwansa knn, ai da tasan tare suke da Farooq da baza ta shigo ba amma kuma tayi knocking door Khausar tace ta shigo, Khausar tace "barka da zuwa Oum Nanerh", Hajar tayi murmushi tace "yawwa Maman boy", Hajar suka gaisa da Farooq ya tmbyi Nanerh, tace masa tana wajen Anty Zulaihah, Nurain ne ya shigo, firr Farooq yace Nurain bazai ɗauki baby ba ai ya makara, Nurain dai baice uffan ba don ya gane rama abinda ya masa yake, Hajar da ta gane itama ta ringa murmushi, basu wani jima ba suka tafi, gidansu Nurain suka wuce don daman yana son zuwa ya gaida parent dinsa tinda yau ne ya dawo daga Lagos, Hajar na zaune a main palour tare da Noor wcca ta kawo ɗanta Anaab wajen Mami yaye, Hajar tace "kai Noor yanxu yaushe Anaab din ya isa yaye, he is too young", Noor tace "na ji da wnda yake womb dina ma", Hajar ta riƙe haɓa sai kuma tayi dariya tace "har kin manta gidan glass din knn..?", Noor tace "ina fa na manta, da planning fa a jikina", Hajar tace "ikon Allah", Noor tace "Ai canza wani zanyi bayan na haihu", Hajar tace "Toh Allah ya raba lfy", Noor tace "Ameen... ya kamata a yiwa Nanerh ƙanwa gsky", Hajar tayi dariya tace "ba gashi nan zaki mata ba, ga Anaab ma already an mata, very soon Anty Sakeena ma zata mata wani", sai after isha'i su Hajar suka bar gidan Mami, Nurain ya rage gundun motar jin wayarsa tayi ring, wayar da bata wuce ta minti biyu ba yayi ya ajiye wayar, Hajar ta ringa kallonsa ganin expression din fuskarsa ya sauya, ta bude baki zata tmbyesa lfy knn yace "ɓatan mutum bbu daɗi wllh, har yau su Hammad basu haƙura da neman ƴar uwarsu ba, wai ynxu ma Kano zasu sake zuwa to check on other places da ake tunanin za a iya samunta...", Hajar tace "kamar ina.?", yace "Psychiatric hospital, Gidan gajiyayyu and Mortuary", tace "Allah ka bayyanata wnn karon", yace "Ameen", Nurain ya sauke ajiyar zuciya yana tuna Ashraaf, may be har yaron ya haƙura da neman mahaifiyarsa, ya kalli Hajar da itama tunanin da take knn yace "ko mu siyo spicy seafood..?", ta gyaɗa kai tace "Sure, i like it", ɗauke kan motar yayi ya canza hanya, bayan sun sayi seafood din suka juya, Hajar ta kalli agogon dashboard taga ƙarfe tara saura, ta kalli hanyar da suke shirin wuceta tace "Dan Allah Moon muje wajen Iron Lady", yace "sai dai next time kinga yanxu dare yayi", tace "Toh Allah ya kaimu", ya kalleta a taƙaice, samm bata masa musu abinda yace tayi shi take yi, kai tsaye bbu musu ta haƙura da zuwa wajen Hajiyar, murmushi Hajar tayi ganin yayi reverse ya shiga layin gidansu Farooq, ta back door inda direct zaiyi leading zuwa ɓangaren Hajiya suka bi bayan sun shiga gidan, Nurain ya saɓa Nanerh da tayi bacci tin a gidan Mami a shoulder, Hajiya na zaune kan darduma dake saman carpet ta mimmiƙe ƙafafuwa, ga nan kayan sa ranar Aysha da aka kawo yau zagaye da ita, Hajiya ta ɗaga kai ta kalli ƙofa jin an shiga, ta saman kantamemen glasses dinta ta ringa kallon su Hajar da suka shigo, Hajiya tace "su waye waɗan nan da tsoho daren nan, duu Allah ku fita ai an gama ganin kayan sai kuma gobe idan Allah ya kaimu, yoh ina dalili tin ido na ganin ido baku zo ba sai yanxu salon ku ƙuma mana sata", Nurain ya haɗe gira ya kalli Hajar yace "kin gani ko, toh gashi nan tana koramu harda sharrin ce mana ɓarayi", Hajar ta ƙarasa ciki ta zauna kusa da Hajiya da ta bita da kallo tace "Hajiya mune fa..", Hajiya ta micincina ido tace "Ah aha ashe su Hajaru ne, ai nayi zaton mutanen unguwa ne magulmata, tinda aka kawo kayan nan suke shige da fice sai kace lefe, kayan sa rana ne fa", Nurain ya ƙaraso ciki, Hajiya tace "Ajiye wnn shagwaɓaɓɓiyar nan kan kujera ka tareta da matashi, Allah yasa kar ta tashi har ku tafi don ƴar nan taku akwai hidima ynxu saita baddala lissafin kayan nan", Hajar tace "ina yini Hajiya..", Hajiya tace "lfy lou ƴar albarka", Nurain yana kwantar da Nanerh ta tashi, ai kam saida ta baddalawa Hajiya palour kafin su tafi wajen ƙarfe tara da rabi, a haka ma Hajiya tace gsky su tafi lada ya isa haka, wnn ƴan tasu ko fura nan ta barta wajen cika ciki. Washe gari Hajar na dusting kayan kallo Nurain ya shigo palourn, ajiye duster din hannunta tayi tana kallonsa ganin ya ɓoye wani abu a bayansa, yace "guess what..", tace "Chocolate", ya girgiza kai yace "No", tace "Sweet", ya sake girgiza kai, tace "Rose", nan ma ya girgiza kai, langwaɓar da kai tayi tace "i can't guess", ya ƙarasa ciki ya ajiye brown envelope din da ya ɓoyo kan doguwar kujera, Hajar tayi kasaƙe tana kallon envelope din, daman wnn shine abinda yake cewa tayi guess, ita ina zata gane wni envelope, kamo hannunta yayi ya zaunar da ita kan kujerar shima ya zauna suna fuskantar juna, envelope din ya buɗe ya ciro papers guda biyu ya ajiye mata akan laps, ta kalli papers din sai kuma ta kallesa, ya mata alamar ta duba, a hankali ta kai hannu ta dauki paper daya ta karanta, tini facial expression dinta ya canza zuwa na annashuwa, har wni rawa hannunta yake ta dauki ɗayar ma ta duba, paper daya ta aikin hajji ce, dayar kuma ta schl wcca har an gama mata komai lectures kawai zata fara shiga, sai sun dawo daga hajj din ne zata fara zuwa schl, ita dai tasan kwanaki ya amshi credentials dinta amma bata san schl yake mata processing ba, tini hawaye ya ciko idanunta, ta rasa wne words za tayi amfani wajen gode masa, zagaye wuyansa tayi da hannayeta ta haɗe forehead dinta da nasa tace "bbu wni words da tayi fitting na mka godiya mijina, Allah ya saka maka da mafificin alkhairy", ya goga karan hancinsa a nata yace "you deserve more than this my wife..", tace "you're the most kind of blessings that happens to me, i cherish every second with you", yayi murmushi mai sauti yace "Hajar i Nurain take you as my wife, Mother of my child and unborns, to have into hold from the day i met you forward, for better for worse", tayi murmushi tace "for richer, for poorer", ya goga karan hancinsa a nata again yace "in sickness and in health", tace "Till death do us apart..", yayi ajiyar zuciya da murmushi a fuskarsa yace "Until death do us apart", sukay dariya a tare snn suka haɗa baki suka ce "Once and for all", ta raba goshinsu a hankali, ta kai hannu ta ringa shafa kwantaccen sajensa, ya haɗe lips dinsu waje ɗaya ya fara kissing dinta passionately, The kiss last for almost a minute, tana kallon cikin idonsa tace "Na gode Allah da ya bani kai matsayin miji", yace "Nima na gode Allah da ya zaɓamin ke as my wife", ta kwantar da kanta a shoulder dinsa...... Nima Feenerh feeche nace Allah na gode maka daka bani dama na sauke wnn Littafi.... Alhamdulillah.. Alhamdulillah.. Alhamdulillah. A nan na ajiye Alƙalamina a cikin wnn littafi mai taken HAJAR, kuskuren dake ciki Allah ka yafemin Ni dana rubuta da ku masu karatu... darussan dake ciki Allah kasa al'umma suyi amfani dashi. As you read the book Hajar kinji daɗi kin samu nishaɗi da annashuwa, Ni Feenerh feeche abu ɗaya nake buƙata a gareki da zaki biyani, dan girman Allah ki karanta suratul Iklas ga Mahaifina, Allah ya kai ladan ƙabarinsa ya gafarta masa....😭 da wnn kaɗai zaki biyani ƴar uwa. My diehard fans gaisuwa ta musamman a gareku da irin ƙwarin guiwar da ku ka bani through the journey of Hajar.... ngd sosai... Hau'wa Yunusa, Nafisa Ummu Readone, Maryam Shehu Usman, Zainab A Aliyu, Khadija A Taheer, Zulaihah Bint Saeed, Maryam Adamu Bappah, Sulaymstiches, Maryama, Aeesha, Saadat Baba duk da dai late comer ce, Hajar namesakes, Nafisa Sasaal partner, da sauran fans da ban jeru sunansu ba da ƴan bayan katanga toh duk ina miƙo gaisuwa. Team Hajar 💛 jinjina ta musamman a gareku wllh ina yinku wujiga wujiga, Team Nurain ❤️ kuma ina yinku ba laifi. Taku har kullum... Nafeesah Yusuf Nagoda (Feenerh feeche...✍️) Mai son complete Document can Ping me Via my WhatsApp digit, but there is payment it is not free.... 👉 08141826023 BISSALAM.... ********************** ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** ************************* ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** **************************