[14/04, 2:02 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ BOOK 2 🅿️➖1️⃣ ______________ *_Assalamualaikum. Barkanku da wannan lokaci, fatan ansha ruwa lafiya? Anyi salla lafiya?. UBANGIJI ya karɓi ibadunmu, ya yafe mana kurakuranmu, yasa muna a cikin ƴantattun bayi. Ina mana Barka da dawowa filin daga, ya rabbi ka bani ikon rubuta abinda bazai cutar dani da ku ba. Ka tsarkake min alƙalamina domin rahamarka. Ka gafarta ma iyayenmu da malamamu damu baki ɗaya. Ka ɗauramu a bisa tafarki madaidaici da bazamuyi dana sani ba. ALLAH ka hanamu cutar da junanmu koda da kalma mara daɗi ce.🙏_* _Ayi mana afuwa da jinkirinmu yau da gobe sai ALLAH 🥰🥰❤️._ *Ƴan ƙungiyar Bati ku matso nan munada meeting 😂. Kun san dai AZUMI aka gama ko, goman ƙarshen nan hummmm 😂 karki yarda ki zama a cikin wanda na ɗaga hannu nace ya ALLAH gasu nan....* _Bazan dai ƙarasa ba amma gaskiya kada ki yarda sister dan in dai an amsa akwai cakwakiya gaskiya 😂😂😂😂🏃_ 500 kacal ne 😘 _____________ ........Sosai ciwon kai yay ma Maanal rijib a wannan yinin isowarsu Abuja, shima kuma AA ɗin zuwa yamma dole aka saka masa drip ma, dan sam baya jin wani ƙarfin jikinsa. Har cikin dare ba'a gama saka masa ruwan ba dan kusan leda uku ne. Dole Fawzan ya kwana tare da shi bisa umarnin Abah. Oum taso yin magana amma tai shiru, dan ita so tai ta kawo Maanal a daren sashen AA ɗin, amma ta fahimci take-taken Abah so yake ya kawo wani sharaɗin hora AA ɗin, dan dama shine ya bata umarnin wucewa da Maanal sashenta sanda suka iso.       Bayan sun baro sashen AA bin bayan Abah tai nasa sashen ta masa magana, amma sai ya nuna mata shi barci yake ji ta barsa dan ALLAH. Haushi ne sosai ya kamata, dan haka fuuu ta baro sashen. Da kallo ya bita ganin yanda ta wuce, sai kuma ya shiga girgiza kansa a fili ya furta, “Fateema son yaranki yayi miki yawa, in dai fushi ne ƙyama sakko dan sai na hora Ajwaad a gidan nan”. Daga haka ya shige toilet yana murmushi... ___________★      Zuciyar Babban Yaya cike da wasi-wasi ya nufi sashen Oum ganin har goma saura na dare yau ma Maanal bata koma sashenta ba, ga AA ɗin kuma ma jikin nasa ya dawo dan yanzu haka wani ƙarin ruwa aka cire masa. Ganin bata a falo ya nufi bedroom ɗinta. Sai da yay sallama ta amsa tare da bashi izinin shiga sannan ya shigan. Yanayin yanda take a zaune da fiskarta dake cike da damuwa yasa gabansa faɗuwa, duk da yasan akwai damuwar yanayin da Auta ke ciki dai.        “Oum baƙya jin daɗi ne?”.    Ya faɗa cike da damuwa matuƙa yana kaiwa kusa da ita zaune. Idanu ta zuba masa kawai, dan duk yanda taso yin murmushi ko sassauta damuwar tata hakan ya gagara sam. Sai ma ƙwalla kaɗan da suka taru mata a idon. Ai sai babban Yaya ya sake rikicewa matuƙa.    Hannunsa ta riƙo tana girgiza masa kai, “Kaga kwantar da hankalinka bafa wani abu bane ba.”         “Haba Oum yazan yarda da hakan, kalla fa yanda damuwa ta bayyana a fuskarki sosai. Dan ALLAH in ma dan ciwon Auta ne ki daina tada hankalinki komai zai wuce kamar ba'ayi ba in sha ALLAHU. Dan yanzu hakama barci yake yi na cire masa drip ɗin dan ya ƙare. Jikinsa sam kuma babu zafi da ganin yanda yake barci ma kasan Alhamdullah babu wani damuwa ba kamar jiya da yinin yau ba. Yanzu haka ma nazo ne akan batun Maanal, nazata zata kwana a can ne yau ai tunda jikin da sauƙin itama?”.           Sosai ɓacin ran Oum ya ƙara bayyana akan fuskarta, ta ce, “Akan hakanne ai Abanku ya ɓata min rai Fadeel, yace wai bazata koma can ba yanzu sai bayan salla ya koyama Ajwaad hankali. Wane hankali kuma ake buƙatar koyama yaron nan bayan wanda ya koya. Kama ajiye batun wahalar ciwo da yasha a shekarun baya, a kwanakin nan kawai kaga hanlin daya shiga fa da wanda yake a ciki yanzu. Kowa fa a rayuwa da irin yanayinsa da kuma ƙaddararsa, amma Abanku ya kasa fahimtar hakan, ya kasa fahimtar Ajwaad nada zurfin ciki ne. Yanda Maanal keda muhimmanci a garesa bana tunanin dole sai ya buɗe baki yace wani abu za'a yarda dashi. Shin so yake na rasa yarona ne saboda wannan tsaurin nasa?”. Ta ƙare maganar muryarta na rawa kamar zata saki kuka.       Cikin sake rikicewa sosai Babban Yaya ya shiga girgiza mata kai nasa idanun na kaɗawa sosai shima. “Dan ALLAH Oum ki kwantar da hankalinki, ni bara naje na samesa yanzu. Ko kuma ki kira Baba ko Abba ki haɗashi da su.....”           “Saboda ban isa da gidana ba kenan ko mai uwa?”. Atare babban Yaya da Oum suka juya da sauri suna kallonsa, ƙarasa shigowa cikin ɗakin Abah yayi, cikin nuna ɓacin rai sosai ya cigaba da faɗin, “Saboda biyan buƙatar taka uwar ni a kira nawa iyayen a haɗani da su. Lallai Fadeel sannu, nace sannu kaji ko!”.        “Kayi haƙuri Abah ni ba haka nake nufi ba, amma Oum fa......”     “Malam tashi ka wuce sai da safe.” Abah ya sake katseshi cikin sake nuna ɓacin rai. Kallon Oum Babban yaya yayi idanunsa na sake kaɗewa, kanta ta jinjina masa alamar yaje ɗin. Dan haka ya miƙe kawai ya nufi ƙofa. Da kallo Abah ya bisa, sai kuma ya girgiza kai a zuciyarsa yana ayyana (su dai akan uwarsu kowa ma ya mutu har liman babu ruwansu). A fili kam dubansa ya maida kan Oum data ɗauke kanta gefe tamkar ma bata san da shi ba a ɗakin. Sai kuma ta yunƙura zata miƙe. Yasan mi zatayi, dan haka cike da bada umarni ya ce, “Koma ki zauna”.        Komawar tayi ta zauna, kafin ta ɗago idanunta da suka sake kaɗewa a karo na farko ta kallesa, aiko ya sake yin kicin-kicin da fuska harda ɗan willa mata hararar data sakata janye idanun nata a kansa sannan ya furta, “Oh ke yanzu saboda na yanke hukuncin daya dace akan ɗanki shine kika ɗauki fushi da ni kin kira babban ɗanki kina sanar masa kuyi min taron dangi saboda ban isa nace ga yanda za'ai ba”.       Idanu Oum ta ɗan rumtse kaɗan, sai kuma ta buɗe a kansa. Baki ta buɗe kamar zatai magana sai kuma ta fasa saboda ƙwallar da suka cika mata idanu. Ɗauke nasa yay dan yasan yanzu sai ta karya masa zuciya, shi kuma a wannan karon ya ɗauka aniyar tauna tsakuwa dan aya taji tsoro, dolene ya hukunta Ajwaad kodan ya sake sanin muhimmancin Maanal. Bazai yiwu ya samu aurenta a ɓagas ba su kuma bashi ita a ɓagas. Ƙoƙarin barin ɗakin yayi, sai Oum kawai ta saki hawayen da take riƙewa cikin muryar kuka ta ce, “So kuke sai kun kashe min shi hankalinku zai kwanta ko Gadanga, yanzu horon da ƙaninka yay masa kawai bai wadatar a yafe masa ba”.          Murmushi Abah daya tsaya cak tun fara maganarta ya saki a hankali, sai kuma ya maida fuskarsa ya haɗe kafin ya juyo yana kallonta daga inda yake tsayen. “Rafeeq bai hora ɗanki ba, takarar nema sukai yay muku adalci ya sadaukar saboda ƙyaƙyƙyawar zuciyarsa, da kuma nasan zai yi hakan sai na hana masa”.  Ya ƙare maganar yana mai juyawa ya fice abinsa. Wani irin ƙululun abu ne ya sake tokare wuyan Oum, har zuciyarta na tunzurata akan takai Maanal sashen Ajwaad koma miza'ayi ayin mana....... ___________★          Alamun shigowarsa ya sata dakatawa daga kai-kawon da takeyi, zama tai kamar ba ita ba ta nutsu a bakin gadonsa tare da ɗaukar littafin addu'oin sa dake a bed side drawer ta fara karantawa. Da farko Abah daya shigo ransa a ɓace sam bai ganta ba. Sai da ta ɗago ta kallesa cikin tausasa harshe matuƙa ta furta, “Sannu da shigowa”. Sannan ya kalleta. Ciki-ciki ya amsa mata, dan haka ta taso da ƴar sassarfa tana faɗin, “Lafiya kuwa? Naga kamar ranka a ɓace?”. Tsaki yaja mai ƙarfi, sai kuma ya wullar da wayarsa a saman gadon nasa shima yana kaiwa zaune hannunsa akan goshinsa yana murzawa. “Fateema ce ke neman ɓatan rai Kamila”.       Ɓoyayyan murmushi Mamy ta saki, a zahiri kam cike da damuwa ta ce, “A haba kodai baka fahimta bane, amma nasan bazata ɓata maka rai da son ranta ba yallanɓai.”          “Mtsoww!! Bazaki gane ba Kamila, ita dai sam bata gajiya da rikici akan ƴaƴanta, dokar dana kafa jiya akan komawar Maanal sashen Ajwaad shine taketa faman fushi, yanzu naje mata sai da safe na samu ta tasa babban ɗanta gaba tana faɗa masa, shiko yana bada shawarar a haɗani da iyayena.”      Sosai Mamy takai zaune yanzu kam, hannunsa ta kamo cikin nata cike da kulawa. “Kayi haƙuri, zan sameta muyi nagana ta yanda zata fahimta. Dan tabbas Ajwaad ya cancanci a fara horashi kafin a bashi yarinyar nan kodan halaccin iyayenta da basu duba abinda ya faru a baya ba suka sake bashi batare da ko tada magana ba. Taurin kan yaron nan ne yayi yawa, ya kamata ya fahimci ba komai akema taurin kai ba a rayuwa....”        “Abinda nake son ta fahimta kenan ai nima Kamila. Amma tamaƙi ta nutsu ta saurareni, ni kuma so nake mu rabashi da halin kodan bambancin dake a tsakanin jiyansa da yau ɗinsa”.        “Karka damu zata fahimta in sha ALLAHU. Ka bata lokaci ta huce yanzu sai mu haɗu muyi magana. Idan ma ta kama Maanal ɗin ta dawo sashena da zama to, dan in ba hakaba bazai damu ba”      Ɗan jim Abah yayi, sai kuma ya jinjina kansa cike da gamsuwa ya ce, “Kumafa kinzo da shawara Kamila, dan in har Maanal na a sashen Fateema ba'a rabu da bukar bane an haifi habu za'ai. Dan ɗan nata dai can zai koma ya tare abinsa, kinga kuwa bazai damu ba.”         “Tabbas hakan ce zata kasance”. Cewar Mamy wani farin ciki na ratsa mata zuciya na nasara. Abah kuwa da bai san dawan garin ba ya sake furta, “To ai zanyi maganin abun, bari dai ya samu lafiya”. “ALLAH ya bada iko, ina goyon bayanka kuma ɗari bisa ɗari a wannan gaɓar. Dan in aka biye ta Mamansu haka za'a mika masa ita kaga ya samu damar cigaba da mana abinda yaso tunda ta shagwaɓa shi daga ita har ƴan uwan nasa. Sun nuna masa komai ya nema sai ya samu komai girman sa”. Sosai kalaman Mamy ke shigar Abah, yana kuma jin gamsuwa da su da tasirinsu ƙwarai da gaske a zuciyarsa fiye da yanda take ma fatan ya fahimta ɗin.........✍️ *(Mamy😏. Mamy☹️. Mamy😮‍💨. Matar nan ko🤔. Hummmm😥.)* _Amin afuwa dan wlhy mura nake mai zafi, idan na samu sauƙi za'afi ganin page ɗin da tsaho..._ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [14/04, 2:02 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣ ______________ ........A safiyar washe gari har kusan sha biyu Abah baiga idon Oum ba a gidan. Dan haka ya fahimci fushin nata fa na gaske ne. Shi dariya ma ta bashi, dan haka shima ya shareta. Har yamma dai bai ganta ɗin ba, ya dai daure har akai sallar magrib da isha'i sannan ya nufi sashenta. Ko'ina tsaff yake da ƙamshi, sai masu aikinta daya samu a falon ƙasa suna hira. Suka gaisheshi da girmamawa ya amsa musu da kulawa ya wuce.        Oum na zaune a doguwar kujera Maanal kwance ta ɗora kanta a cinyarta su duka idanunsu a tv. Sallamar Abahn ta saka Maanal ta shi zaune, kanta a ƙasa tai masa sannu da gaida shi. Shima fuska ɗauke da murmushi ya amsa mata tare da tambayarta ciwon kanta. A tausashe ta ce, “Ya daina Abah Alhamdullah”.      “Masha ALLAH ai haka ake so ɗiyar Abanta ƴar albarka.”     Murmushi Maanal tayi mai faɗi, sai kuma ta miƙe tsam, dining area ta nufa ta ɗakko ruwa a freight tazo ta ajiye gabansa, cike da dabara ta shige bedroom ɗin Oum. Shi ko Abah cike da mamaki sosai ya ke kallon Oum ganin tunda ya shigo falon bata ko ɗaga ido ta kallesa ba. Sai ma wani sake ciccin magani take. Ji yay kamar ya juya ya fita ya bar mata sashen. Har yay kamar zai juyan sai kuma ya dakata, ruwan da Maanal ta ajiye masa ya ɗauka ya sha kafin ya dubeta da ƙyau. A ɗan kausashe yace, “Har yanzu fushin ne kenan? Dan na hana ki bama ɗanki matarsa shine nima kika ɓiye min ganinki yini guda Fateema? Ni kenan ban isa sharɗanta doka a fahimceni ba ashe dai?. Miyasa kike da son kanki da yawa akan ƴaƴanki ne wai?”.       Karo na farko ta ɗago ta kallesa, idannunta cike da hawaye. Muryata na ɗan rawa ta ce, “Miye abun son kai anan Abahn su?. Yaron nan kodan halin daya shiga ai ya cancanci a yafe masa a kuma fahimcesa. Eh naji shi mai kuskure ne, amma koda bai fito yace yana son Maanal ba halin daya shiga kawai amsa ce. Amma sai ace baza'a bashi matarsa ba har sai bayan salla. Haba Gadanga ka fahimta mana, baifa da lafiya, yana buƙatar mai kulawa da shi.....” hawaye suka shiga ziraro mata batare data kai ƙarshen zancen ba. Shi Abah sai abun ma ya fara bashi dariya. Yanzu dan kawai yace Maanal bazata tare ba sai bayan salla shine abin kuskure har ta zauna tana kuka. Oh ya rabba, Fateemansa sarkin daru kenan. Kansa kawai ya girgiza, batare da yace komai ba ya juya zai bar mata ɗakin, dan dole ya turza sosai ta yanda ita da ɗan nata zasu san ba wasa yake akan al'amarin ba. Da sauri ta ce, “Gadanga!”. Tsayawa yay, tare da ɗan waiwayowa ya kalleta. Sai kawai ta sake sakar masa kuka. Da sauri ya fice abinsa, dan in tana irin wannan darun nata yafi buƙatar yin nesa da ita, idan ba haka ba sai ta karya masa zuciya ta sakashi yin abinda bai niyyar ba.        Kai tsaye daga sashen Oum ɗin sashen AA ya nufa, dan son sake duba jikinsa, saboda yau ma a kwance ya yini ko salla bai fita ba sakamakon rashin ƙwarin jiki da yake fama da shi har yanzu. A sashen ya samu babban Yaya da Fawzan a tare da shi, sai dai shi barci ma yake AA ɗin, su kuma suna ƴar hirarsu. Cike da girmamawa suka gaisheshi, ya amsa musu da kulawa yana taɓa goshin AA dake barci. Jikinsa babu zafi kamar jiya, dan da ganin ma yanda yake barcin zaka san Alhmdllh. A hankali ya sauke ajiyar zuciya, sai kuma ya ɗago idonsa akan su Babban Yaya ya ce, “Alhamdullah yanzu kam babu zazzaɓin ai. Ya kamata kuje ku kwanta ku huta kuma ni bara na zauna da shi yau”.            Idanu Fawzan ya ɗan waro waje da faɗin, “Haba Abah da kanka. Ai sai Oum ta zane mu.”     Dariya Abah yayi, hakama babban Yaya ya murmusa tare da faɗin, “A'a Abah mun yafe maka kaje abinka. Dan gaskiyar Fawzan Oum zata iya zane mu ne”.     Nan ma murmushi kawai Abah yayi, sai kuma ya zauna suka ɗan tattauna akan jikin AA ɗin da tun shekaran jiya da suka iso daga Kano sai a hankali, dan duk dauriyarsa sai da ya sake kaiwa kwance. Gashi ya kuma kafe bazai je asibiti ba, sai nan doctor yazo yake duba shi. Bayan Abah ya musu sallama ya fito babban Yaya ya biyosa da sauri. Dakatawa yayi yana kallonsa harya ƙaraso.       “Lafiya dai ko Fadeel?”.    Cike da ladabi babban Yaya ya ce, “Eh Abah, kawai dai akan batun tarewar Maanal ɗin ne dai, dan ALLAH kayi haƙuri a bashi matarsa, ALLAH bana jin daɗin yanda nake ganin Oum a cikin damuwa. Abubuwan sun mata yawa, ga ciwon Ajwaad ɗin ga kuma wannan batun. Abah harfa rama naga tamun yau ALLAH ”. Babban yaya ya ƙare maganar kamar zai yi kuka.       Murmushi Abah yayi, sai kuma ya ɗan furzar da iska tare da faɗin, “Wato Fadeel ya kamata muma kammu adalci muyima yarinyar da iyayenta suma. Dan tabbas da nasan Rafeeq zai zagaye yay wannan aikin sai na hanashi, saboda nifa har yanzu ina akan bakana sai Ajwaad ya sauke kansa ƙasa yazo da bakinsa ya nema na bashi Maanal bayan ya nema afuwarta, idan ma ta kama ya faɗa mana dalilinsa na wannan dagewar”.      Kai sosai Babban Yaya ya jinjina, ya ce, “Na fahimceka Abah, kuma nima ina bayanka. Sai dai hakan bazai hana na baka haƙuri ba na kuma nemawa Auta afuwa. Kasanshi da zurfin ciki, maybe akwai abinda bamu sani ba game da al'amarin, amma wlhy mu shaida ne Ajwaad na son Maanal matuƙa. Kuma sai nake ga mata da miji sai ALLAH, kamar barinsu su kasance a taren zai sa su sasanta kansu kodan soyayyar da suke ma juna su duka”         “Humm wace soyayya kuma Fadeel, yana sonta zai watsar da al'amarinta ya zauna jan jiki a sanda ya sake ganinta, to Miye na girman kan, aure abin wasa ne? Barshi dai a bata tare ɗin ba, zai fi jin zafin wannan bulalar fiye da wadda kake hangen. Ina son hakan ya zama izina a garesa ya canja wannan halin nashi kodan yanzu shi mai iyali ne nanda wani lokaci haihuwa za'a fara masa”.     “Tabbas aure ba abin wasa bane Abah, mu kuma masu biyayya ne ga kowanne irin hukunci daga gareku. Amma idan mukai dubi da halin kawai daya shiga akan tsoron rasata abun muyi nazari ne. Ta wani ɓangaren ina tsoron kar dangin mahaifinta ne fa sukai masa wani abun tun wancan lokaci tunda dama kakarsu ta nuna bata son aurenmu da su Shaheedeh. Abah kasan zata iya bin kowacce hanya domin cin nasara, sannan shi kansa asiri gaskiya ne fa”.      Sosai Abah ke kallon babban Yaya. Zuciyarsa nata faman kai-kawo akan kalamansa. Sai dai kuma baice komai ba akan hakan illa nufar hanyar fita da faɗin, “Zanyi nazari, amma ina akan bakana na bazata tare ba yanzu ku cigaba da jiyyarsa ALLAH ya tashi kafaɗunsa”. Daga haka ya fice abinsa. Da kallo kawai Babban Yaya ya bishi, shi kansa al'amarin Autan nasu na damunsa, da rikita shi, amma dai koma miye ai ta ƙare tunda an ɗaura, komai mizai biyo baya mai sauƙi ne insha ALLAHU......         Murmushi mai faɗi da yalwa Mamy ta saki, dan dukan tattaunawar Abah da su Babban Yaya a cikin kunnenta ta kasance. Tayi matuƙar yin farin cikin yanda shirinta yay tasiri akan Abah cikin sauƙi haka, dan sam batayi zaton zai amshi batun da muhimmanci ba duba da sanda take tsara masa yin hakan yi yay kamar maganar tata bata tasirantu a gareshi ba. Shiyyasa taga ƴar gwal ɗin tashi har yanzu babu fara'a ashe an sake wargaza mata shiri ne. Wani murmushin ta sake saki haƙoranta na bayyana sosai, sai kuma ta gimtse fuska da gyara yanayinta ta ƙarasa shigowa falon sosai tana sallama.         A tare Fawzan da Babban Yaya suka ɗago suna kallonta tare da amsa sallamar. Cikin yanayin da take nuna musu na kawaici ta amsa gaisuwar da suke mata, tare da tambayarsu yaya mai jikin. Suma cikin girmamawar da suke bata suka tabbatar mata da sauƙi, yanama yin barci ne. Kai kawai ta jinjina musu, batare data sake cewa komai ba ta nufi bedroom ɗin AA ɗin. Barcin kuwa yake har yanzu, fuskarsa tayi fayau. Guntun murmushi ta saki a hankali, dan tasan tabbas ƙaunar da takemasa dabance a cikinsu, tun daga ɗaukar cikinsa har haihuwarsa duk da wahalar data sha shi ɗin na musamman ne a gare ta. A karo na biyu ta sake sakin murmushin, sai kuma ta kai zaune kusa da shi gab tare da kai hannun ta shafa yalwatacciyar sumar kansa dake a hargitse. Addu'ar samun lafiya tai masa mai ɗorewa tsahon mintuna kafin ta tashi ta fita....         A hankali AA da tun tsaiwar Mamyn a kansa ya farka ya buɗe idanunsa ya bita da kallo, sai da ta maida ƙofar ta rufe ya sake maidasu ya lumshe luuuu. Ya jima kafin ya sake buɗesu, sai dai sun masa nauyi sosai alamar barci bai gama sakinsa ba. So yake ya tashi zaune, sai dai kansa juya masa yake yi, dan haka dole ya sake maida idanun ya rufe barcin ya ƙara yin awan gaba da shi cike da mafarkin Mamy da haka kawai ganinta a kansa tsaye ya tsaya masa a rai duk da yasan ba wani abu mara ƙyau tazo tayi a garesa ba, amma dai zuciyarsa ta riƙe abun matuƙa..........✍️ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [15/04, 2:42 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣ ______________ ........Mamy kam a inda tabar su Fawzan anan ta samesu, sai dai yanzu Nibras ta ƙaru.       Ɗan tsurama Nibras ɗin datai mata wani iri idanu tayi, sai kuma cikin tausasawa ta furta, “Nibras baki da lafiya ne?”.        Kallon Nibras ɗin Fawzan da Babban Yaya suma duk sukayi saboda jin furicin Mamyn. Cikin damuwa Fawzan ya ce, “Mamy gara kam ki tambayeta ke, dan tun jiya nima nake fama da ita amma sai tace ba komai gajiyar biki ce wai.”            Cikin jinjina kai Mamyn tace, “Itama gajiyar bikin akwaita ɗin ai, dama sai a hankali zata saki kowa duk da ga wani na tunkarowa kuma dai. Kinga kije ki samu ki gasa jikinki da ruwa mai zafi sosai sai kisha pracitemol ki kwanta abinki kiji. ALLAH ya ƙara sauƙi”.       Ji Nibras tai kamar ta zageta, amma sai ta daure ta jinjina mata kai kawai da faɗin, “To Mamy”. Daga haka ta juya ta fita zuciyarta na mata zafi da ƙuna matuƙa. Tazo ne dan taga fuskar AA ko zataji sassaucin abinda ke cizon zuciyarta, amma Mamyn ta wani korota. Ba komai zata dawo ne, dan in har yau Fawzan anan  zai kwana ALLAH sai dai su kwana tare a sashen AA ɗin. Koba komai ta rage raɗaɗin kishin dake dafa mata zuciya. Sau ƙin ma har yanzu ko sau ɗaya bataga Maanal a sashen nashi ba..        Fitar Nibras ya saka Mamy ma yunƙurin tafiya, amma sai Babban Yaya ya dakatar da ita cikin ladabi. Tsayawa tai tana kallonsu su duka. Fawzan ya ce, “Mamy dan ALLAH magana zamuyi ne”.       Wani irin sanyi mai silalar da kuzari ne ya shiga bin jijiyiyin jininta yana gauraye jikin ta. Yayinda wani farin ciki ke cika zuciyarta tamkar kumfar omo a cikin ƙaton bahon wanki. Yau itace yaranta ke faɗa mata suna son yin magana da itane iya su kaɗai babu matar can a tsakkiyarsu. Ya rabba, ita kam mizatace da UBANGIJI yau. A zahiri kam sai ta dake babu wani alamun komai a fiskarta ta dawo ta zauna. Babban Yaya ne ya fuskanceta da ƙyau cikin nutsuwarsa.      “Mamy akan Ajwaad ne dama muke son dan ALLAH kisa baki a tsakanin rikicin Abah da Oum. Dan ALLAH ki taushi Abah akan ya bari Maanal ta tare a ɗakinta gobe idan ALLAH ya kaimu, dan gani yake kamar Oum ta kasa fahimtarsa ne saboda soyayyarmu ta rufe idonta, Auta na buƙatar matarsa a kusa da shi ya fahimci Oum dan ALLAH”.       Sosai kalmar soyayyar nan ta daki zuciyar Mamy, dan saida ta maimaitata a zuciya yafi sau uku. A fili kam sai ta sake raunana fuskar tata ta ce, “Oh dama wani abune ke faruwa? Ai ni na zata dan bashi da lafiya ne kawai bata tare ɗin ba. Yau gajiya tasa sau ɗaya kawai muka haɗu da Oum ɗin. Amma gaskiya ai Abahn naku ya faɗa, Mamanku ta cika rigima akan al'amarinku.....”     Cikin ƴar dariya Fawzan ya ce, “Kai Mamy kema haka zaki ce”.         “Ai gaskiya ne Fawzan, ita idan kaga tana fushi a gidan nan abu ya shafi ɗayanku ne. Karku damu zan sameshi muyi magana in sha ALLAHU. Itama zuwa da safe zan zauna da ita. Ni bara naje na ɗan kwanta nima kamar Nibras ɗin gaɓɓaina duk ciwo suke min”.      Godiya sukai mata da sai da safe. Fitarta babu jimawa Oum ta shigo itama. Su duka miƙewa sukai sukai kanta ganin har yanzu fiskarta a cinkushe, ga idannunta kamar wadda tayi kuka. Take suma duk fuskokinsu suka sauya. Murya a rauanne Babban Yaya ya ce, “Oumna Please ki cire damuwar nan, kin san fa Abah wani lokacin dan kawai ya kunnaki ne bawai abinda ke ransa kenan ba.”        “Amma Fadeel ya tausaya masa mana, kwance fa yake baida lafiya. Shin ALLAH ma ba muna masa laifi ba ya kuma gafarta mana saboda rahamarsa”.     “Hakane Oum shima zai huce”. Cewar Fawzan yana mata murmushi da kama hannunta ya sumbata. Haka sukaita lallashinta har sai da tayi murmushin itama. Kafin su nufi bedroom ɗin AA ɗin. Ganinsa zaune a bakin gado yasa ta ƙarasa shiga ciki da sauri, kusa da shi ta zauna tana mai riƙo hannunsa daya dafe kansa da shi, dan yaji duk zancen Mamy da su Babban Yaya. Mamakin Mamy da halinta ke sake raunana masa zuciya, amma yana mata fatan shiriya kafin lokaci ya ƙure mata. Yasan duk abin nan fa Abah keyi daga cikin shirinta ne, zai kuma bama kowa mamaki in sha ALLAHU cikin sauƙi.           “Auta yaya akayi? Kanne har yanzu dai?”.     Karan farko ya kalla Oum ya sakar mata murmushin ƙarfin hali, sai kuma ya kwantar da kansa a saman kafaɗarta. “Ya daina Oum”.       Ya faɗa acan ƙan maƙoshi.     “To Alhamdullah, ALLAH ya ƙara lafiya baby na kaji, yanzu mi kake son ci?”.        “Oum tea kawai”.    “To ba damuwa bara Fawzan ya haɗa maka”.    Kansa ya jinjina mata, sai kuma ya kalla Babban Yaya da Fawzan. Murmushi yay musu kaɗan, suma dake kallonsa suka maida masa murtani suna tambayarsa yaya jikin nasa. A samman laɓɓa yace da sauƙi. Daga haka Fawzan ya fita haɗa masa shayin. Kallon Oum ya ɗanyi, har ya janye idanun sai kuma ya tsira mata su, kafin tai ƙoƙarin dai-daita fiskarta har ya furta, “Oum kinyi kuka”.      “Kukan lafiya Auta ”. Ta faɗa tana ɗan harararsa cikin yanayin son basarwa. Ina bai gamsu ba, cikin rashin kuzari ya zamo ƙasan lallausan carpet ɗin gaban gadon ya zauna yana mai zuba mata idanunsa dake a shanye. Zatayi magana ya girgiza mata kai, “Oum Please ki daina damuwa, nasan a kaina ne ko? Dan ALLAH ki bari naji sauƙi fa, ki tambayi babban Yaya ma”. Ya ƙare maganar yana kallon babban yaya a raunane.     Cike da tabbatarwa babban Yaya ya jinjina kansa shima yana kaiwa zaune kusa da Oum ɗin, Fawzan ma yazo ya miƙama AA kofin tea ɗin daya haɗa masa suka zagayeta kowa na mata nashi daddaɗan kalamin, idan ka gansu abin sha'awa da birgewa sojojin yaƴanta zagaye da ita, basu barta ba har sai da fiskarta ta washe da fara'a kamar yanda suke so. Shima AA sai ƙoƙarin ƙarfafa kansa yake yanda hankalinta zai ƙara kwanciya. Ganin dare yayi Oum da babban Yaya suka baro sashen suna ƙara tattaunawa aka bar Fawzan da zai kwana da shi. Bayan wucewar tasu ne Fawzan ya zayyanema AA komai dake faruwa ana rikicin da Abah keyi akan tarewar Maanal kamar yanda ta buƙaci ji. Murmushi AA yayi mai faɗin da har ya saka Fawzan zuba masa idanu baki buɗe.           “Oh abin ma kai nishaɗi ya baka kenan?”.    Cewar Fawzan cike da mamaki. Murmushin AA ya sake saki a karo na biyu, sai kuma a hankali ya jingina da fuskar gadon yana kai hannu ya ɗan shafo gashi kumatunsa. “To yaya Fawzan in bai sakani nishaɗi ba kuka kake son nayi, banda ma abin Oum minene abin ɗaga hankali anan, ta bar masa ƴarsa mana”.       Dariya Yaya Fawzan yayi da faɗin, “Oh hakama zakace? ALLAH yasa ya jika, kaga idan sati ɗaya yay niyyar horaka sai ya maida shi wata uku kadai san halin Abah”.       Murmushi kawai AA yayi kaɗan batare daya sake cewa komai ba. Fawzan kuwa ya tasashi gaba da tsogumi... __________★       Washe gari da safe Alhamdullah Oum ta tashi da sauƙin damuwa ba kamar jiya ba. Dan tunda ta kira Mah-mah a ɗazun da asuba ta sanar mata sai Mah-mah ɗin ta tausheta da mata nasiha akan ta sakama Abah ɗin ido, ta bashi damarsa matsayin mahaifi dan ko yaya shima bazai yi abinda zai cutama Ajwaad ɗin ba ai, sannan kuma tunda a gida ɗaya suke ai babu wani abun ɗaga hankali in dai yaran yanzu ne masu ƙarancin kunya, shi da kansa ma zaice ya ɗauki matarsa basai ta ɓatama kanta rai ba. Ji tai zuciyarta ta rage jin haushin Abah ɗin, ta kuma ɗau alwashin daidaita komai a tsakanin AA ɗin da Maanal ta yanda Abahn da kansa zai tattarasu ya kora sashen nasu batare da alwashin nasa ya cika ba.        Yau ɗin yanda Manaal take ta faman sinne-sinnen kai ya saka Oum kamata ta duddungure da faɗin, “Wai Auta ni kike son maidawa surukarki a gidan nan, jiya na saka miki ido ne kawai naga iya gudunki, to kar naji karna gani. Maza tashi muje kitchen ki haɗama mijinki abinci yau kije ki duba jikinsa dai kada mu take doka”.     Murmushi Maanal tayi tana ɓoye fuskarta a jikin Oum ɗin, itako Oum na mata dariya. Atare da Oum suka shirya abinci mai sauƙi ma AA ɗin har kala uku, sai wanda suma zasu ci, dan yauma Abah a sashen Mamy zai karya. Suna kammalawa Oum tace taje tai wanka, yayi da masu aiki keta faman kimtsa sashen kamar yanda suka saba. Ba wata kwalliya Maanal tayi ba, ta dai gyara fuskarta ta ɗan saka kwalli da lipsgloss, sai tai simple ɗaurinta daya zauna mata ɗan kwantaccen gashinta ya ɗan fito ta gaban goshi kaɗan. Tana ƙoƙarin saka turare kiran Amaal ya shigo mata. Ɗagawa tai cike da shagwaɓa dan haushinsu take ji a Kano sunce zasu dawo amma sukai mata wayo. Dariya Amaal ɗin taita mata, sannan ta kwantar mata da hankali akan ai next week in sha ALLAHU suna nan tafe da sauran kayanta, dan Daddy yace sai zuwa ƙarshen sati za'a kai kayan gararsu ita da Huznah. Duk da dai Oum tace a ɗan saurara akwai sauran biki da zasu yi anan Abujan shiyyasa ma bata tare ba. Sosai ita Maanal ma abin ya bata mamaki, yanzu duk wancan kaikawon da akasha na Kano bai kuma isa ba. A fili kam sai suka cigaba da maganar su da Amaal. Tana ajiye wayar mai aikin Oum ta shigo tai kiranta, mayafi ta ɗauka ta sanya, dan haka kawai taji tana jin kunyar fita a haka matuƙa. Tayi ƙyau sosai, duk wanda ya ganta kuma yaga amarya, dan ƙamshinta daban ne, ga ƙunshinta raɗam yanata ɗaukar ido daga baƙin har jan, fatar jikinta kam da tasha gyara ba'a magana, sai wani irin glowing take a idanun mai kallo kamar ka lasheta. Ita kanta Oum kallonta kawai take tana murmushi, ta jima bataga ma'auratan da suka dace da juna ba irin Maanal da Autanta, sai dai ai musu fatan zama lafiya mai ɗorewa kuma. ALLAH ya kawo zuri'a masu albarka..........✍️ 🏃Da suwa zamuje sashen AA ɗin ne?.         *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [15/04, 2:42 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣ ______________ .......Basket ɗin da aka shirya masa kayan abincin Maanal ta ɗauka, kai kace wani anguwa zasu je ba cikin gidan ba. Sun fito gwanin sha'awa daka gansu kaga uwa da ɗiya ba uwar miji da matar ɗa ba. Oum tasan Mamy na sashen Abah dan haka bama tace Maanal taje ta gaida su ba, shiru ma gidan alamar kowa na sashensa, sai ma'aikata dake ta ƙoƙarin kimtsa ko'ina, sunta gaishesu har suka isa sashen AA. Haka kawai Maanal ke jin kamar tace bazataje ba, amma bazata iyama Oum musu ba duk tsanani. Kai tsaye Oum ta shige dan tasan bazasu sami kowa a falon ƙasan ba, Maanal dai  biye da ita zuciyarta na mata wani nauyi. Dan kana shiga da sallamar sabon fenti dana sabbin kaya zaka fara cin karo. Tabbas dole ne mai kallo ya furta Masha ALLAH, dan kuwa dai Daddy yayi matuƙar ƙoƙari, daga Maanal ɗin har Huznah ya zuba musu dukiya. Duk da asace Maanal ke kallon komai sai da taji hawaye sun cika mata ido sosai, wata irin ƙaunar Daddy da Ammie na ratsata, falon ƙasa ma kenan, bata san yaya kitchen yake ba, kuma su Didi sun sanar mata daga saman har ƙasa Daddy ya cika mata su da kaya. Zuciyar Maanal bata ƙarasa fashewa ba sai da suka hawo upstairs ɗin, ya subahannallah komai yaji, a hakan ma nan ba'a kammala aikin ba dan ga manyan kwalaye nan a ajiye gefe an tule, zama sukai a cikin kujerun dan su an riga an shiryasu, dai-dai nan Fawzan ya shigo shima da alama yaje sashensa ne.       Cike da tsokana yace, “Inyee kaga Lilly amaryar Auta”.        Da sauri Maanal ta ɗan waro masa idanu, sai kuma ta ɓata fuska. Dariya Fawzan yake yi, Oum dake tayashi ta ce, “Ni ban taɓa ganin yaya irinka ba Fawzan, anya kuwa bazan turaka hutu Kano ba ka bar min yara su shaƙata”.     Dariya sosai Fawzan yake yi, ya kai zaune kusa da Oum ɗin yana gaisheta, itama Maanal ɗin sai ta gaisheshi. Oum ce kawai ta tambayi yaya jikin Autan nata, Maanal kam kunya ta hanata yin hakan. Fawzan ya ce, “Da sauƙi sosai Oum, dan tare mukaje massallaci ma da asuba yau. Ku shiga mana ai ya tashi”.        Murmushi Oum tai da faɗin, “Alhamdullahi”. Sai kuma ta juya ta kalla Maanal da kanta ke'a ƙasa. Cike da kulawa ta ce, “Auta tashi ki shiga masa da abincin gamu nan zuwa”. Kai kawai Maanal ta iya ɗaga mata, sai dai ji take kamar tace ma Oum ɗin a'a amma babu dama. Haka ta ɗauka basket ɗin kanta a ƙasa, Fawzan ne yay mata nuni da ɗakin yana tsokanarta, ita dai yau babu bakin maida murtani sai Oum ke kare mata. Sai da tai ɗan jimm a tsaye kafin tai knocking da yatsanta ɗaya kamar mai jin tsoro, tabbas badan bazata taɓa iya musu da Oum ba komi za'ai bazata je inda yake ba, duk da kuwa har cikin ranta tana jin damuwa da rashin lafiyar tasa. Jin shiru ta sake yin knocking ɗin, sai kawai jitai daga falo Fawzan nace mata ai ta shiga kawai ba lallai yajita ba. Nan ma jitai kamar ta saki hawaye, amma haka ta danne kamar mai tsoron shiga wuta ta tura ƙofar ɗakin a hankali. Sai da ta ɗan rumtse idannunta taja numfashi kafin ta saka ƙafarta a hankali lips ɗinta na motsawa alamar sallama. Bata kalla cikin ɗakin ba ta maida ƙofar ta rufe, yayinda wani sassanyan ƙamshi ya daki hancinta, ɗan sanyin acn da aka saka kaɗan yay wani shiga jikinta. Sosai ta saki ajiyar zuciya a cikin ƙirjinta. Sai kuma ta shiga bin ɗakin da kallo jin alamar kamar babu mutum, babu kowa kam, sai dai gadon babu gyara alamar yanzu aka tashi a kansa, ɗakin ya tsaru matuƙa, ga komai dai-dai misali babu wani tarkace, duk da safiya ce babu yawan haske a ɗakin, dan labulayen duk a sake suke, fitulun kuma a kashe sai mara haske sosai kalar blue. Hakan ya saka launin ɗakin sake zama mai ɗaukar hankali. Nanma ajiyar zuciya ta sauke, sai kuma ta cigaba da takawa a hankali kamar mai sanɗa da nufin ajiyewa ta fice abinta tunda ALLAH tasota baya ɗakin, sai dai kuma da'alama shirin nata zai bi ruwa, dan tana gab da isa tsakkiyar ƙaton bedroom ɗin ƙofar bathroom dake daga can cikin closet ɗinsa da zaka iya hangowa ta cikin ɗakin ta buɗe, harga ALLAH da farko tsorata tayi dan haka ta kalla wajen, sai dai kuma da gudu ta ɗauke idanun nata zuciyarta na wani kalar bugawa saboda saukarsu a kansa. Ba ƙaramin jin ta gama rikicewa tayi ba, dan daga shi sai ƙaramin towel daya ɗaura a ƙugunsa, buɗaɗɗen jikinsa jiƙe da raɓar ruwa alamar wanka yayi, dan hatta sumar kansa a jiƙe take itama dai da alama wanketan yayi. Shima dai cak ɗin ta tsaya, dan ganin nata ya saka shi jin shock na rashin zato dan tunda suka dawo bai gata ba, duk ciwon nan bata shigo dubashi ba. Kamar zai ɗauke kai dan jin haushi. Sai dai ganin yanda tai tsammm kanta a ƙasa ya sakashi sakin wani shegen murmushin gefen baki yana ɗan yin luuu da idanun nasa kamar zai lumshesu. Ƙaramin towel ya cira dake rataye a jikin wani ƙyaƙyƙyawan hanger dake gab da ƙofar bayin, dan an tsara su ne a wajen kala-kala ta cikin closet ɗin gwanin birgewa. Saman kansa ya kai towel ɗin kafin ya fara takowa harya fito daga closet ɗin gaba ɗaya.         Bedroom slippers ne a ƙafarsa masu taushi, duk da ba ƙara sautin takun nasa ke badawa ba sai take jin sa ita har tsakkiyar kanta, karo na farko a rayuwarta da taji wani mashahurin tsoron kasancewarsu su biyu kacal a waje, da ace zata iya da ɓacewa kawai zatai a ɗakin ta huta. Amma babu damar hakan gareta tunda ita ba aljana bace. Yana isowa gab da ita batama san wani ƙarfi yazo mata ba tai saurin juya masa baya tana sake ƙarfin rumtse idannunta hannayenta biyu data riƙe basket ɗin na ƙara damƙe shi da ƙyau. Cak ya tsaya shima dariya na neman cika masa zuciya, dan yanda ta juya ɗin da saurinta sai ka ɗauka wani kumurcin maciji ta gani ko zaki. Da ƙyar ya iya danne dariyar dake cinsa a rai ya matsa jikinta sosai, tsabar neman magana sai ya zagayo da hannayensa ta gefe da gefenta ya ɗaura akan nata hannayen dake riƙe da basket ɗin, badan ya riƙe hannun nata da ƙyau ba da sai basket ɗin yayi faɗuwar da abincin zai tarwatse a wajen. Yanda ta takure jikinta waje guda ya sake bashi damar manne jikinsa da bayanta sosai tare da duƙo kansa saman kafaɗarta yana busa mata numfashinsa a saman dokin wuya da cikin kunne, sannu a hankali ya sake matsar da fuskarsa jikin tata idanunsa a lumshe, kwantaccen gashin kumatunsa dake da damshin ruwa na gogar gefen fuskar tata. Da sauri ta zame hannunta dake riƙe da basket ya koma nasa hannun gaba ɗaya. Karo na farko ya saki ɗan murmushi mai sautin da har taji, har yanzu kuma idanun nasa a lumshen suke yana shaƙar ni'imtaccen ƙamshinta. Cikin matuƙar raɗar da koda wani ne a kusa da su da wahala yaji miya faɗa a hankali can ƙasan maƙoshi ya furta, “Good morning Bestie”.            Tsabar yanda maganar tashi taima Manaal shigar zuruff bama tasan ta zabura ba tana ƙoƙarin tureshi, dolensa ya bata damar fita a jikin nasa, dan duk ta daburce har tana neman kaɓe basket ɗin abincin hannun nasa. Hanyar fita ta nufa da sassarfa, muryarta na rawa, harshenta na sarƙewa ta furta, “Su Oum na falo”. Kafin yay wani yunƙuri harta fice. Kansa kawai ya girgiza yana mai sakin murmushin da har sai da haƙwaransa suka bayyana, a ransa kam ayyanawa yake (Zamu haɗe ne ai yarinya).        😂Tace maka ita ba yarinya bace yanzu kana sake maidata baya🏃       ★ Sarai Oum ta lura da yanda Manaal ta dawo kamar wadda aka biyo, sai dai batai magana ba har sai da Manaal ɗin ta sanar musu cewar ya tashi. A dai-dai nan ma kiransa ya shigo wayar Oum ɗin. Basu ji abinda ya faɗa ba, Oum tadai miƙe tana murmushi tace su shiga.      Fawzan ne ya fara shiga, Oum biye da shi, itace ƙarshen shiga dan maƙalewa tayi a bayan Oum. Sosai Oum ta nuna farin cikin ganin yanda jikinsa yay sauƙi yau sosai fiye da kullum, shima ganin fara'a a fuskarta sai zuciyarsa ta masa sanyi. Fawzan kam ya tasashi gaba da tsokana shi da Maanal data zauna a cikin yanayin takura, dan tun haɗa idon farko da tayi da AA ta ɗauke kanta bata sake kallon sashen da yake ba. Yanzu ma da Fawzan ɗin ke tsokanarsu kanta a ƙasa sai Oum ke kare musu. A dai-dai nan Saheeba da Nibras sukai sallama. Kafin a basu iznin shigowa Naufal da Anum sun shigo. Kai tsaye yaran inda AA yake suka nufa cike da farin cikin ganinsa a zaune, shima fuskarsa da ɗan sakewa ya ɗaga Anum ya zaunar a jikinsa, Naufal kuma ya zauna a kusa da shi.         Da kai kawai ya amsa gaisuwar da Saheeba da Nibras sukai masa. Ba haka Nibras taso ba, amma har ranta taji daɗin ganin jikinsa da sauƙi sosai yau ɗin. Wani gefe na zuciyarta kuma najin zafin ganin Maanal a tare da shi, gashi data kallesa sai taga idanunsa akan Maanal ɗin suke, ita kuma ƴar ranin hankalin sai wani latse-latsen waya take yi ita adole ga mai aji. Oho ita Maanal bama tasan tanai ba, hasali ma jinta take duk a takure, da Oum zata barta ma da tuni ta wuce abinta ta koma sashenta ita kam..... ________★   A lokacin da anan ahalin gidan ke sashen AA a ɓangaren Mamy tana can tana waya da babbar yayarsu akan batun auren AA ɗin da Nuratu da sukaji su Abah sunyi shiru sunƙi cewa komai ga shi har yau laraba, a yanda tsarin nasu yake kuma daga gobe alhamis ya kamata ace biki ya fara musamman tasu ɓangarensu, amma sunji ɗif babu wani bayani. Shine tai kiran Mamy ɗin dan jin mike faruwa. Bayanin da Mamyn ke mata rai ɓace yasa tace yau zatazo Abujan dan tana Kano. Da wannan sukai sallama.        Zama Mamy tai tana mai dafe kanta. Eh lallai taci nasara akan Abah na hana Maanal tarewa a sashen AA, sai dai tana jin fargaba akan tunkararsa da batun bikin nan kuma. Musamman idan akai dubi da halin da AA ɗin ke'a ciki na ciwo. To amma kuma itama fatanta ai ayi bikin ne. Numfashi mai nauyi ta sauke sosai, tana mai tattara batun gefe ta jingine har isowar yayar tata dai, dan gara su tunkari Abahn tare zatafi samun ƙwarin gwiwa....        Kusan ƙarfe uku na rana kuwa yayar Mamy ta iso gidan. A lokacin kusan kowa yana a sashensa, dan hatta AA yana sashen Oum, daga sallar azhar daya samu iya fita yau shi da sauran yan uwansa suka wuce sashen Oum ɗin. Manaal dai na ɗakin tunda taji motsinsu taƙi fitowa, sai ma tayi kwanciyarta barcin dole, daga baya na gaskiyar ya ɗauketa.       Mamy da kanta ta fito ta tarbi ƴar uwarta, kai tsaye kuma sashenta suka wuce, suna dai-dai gifta window ɗin Oum dake kallon sashen Mamy ɗin sautin dariyar su Fawzan ta shiga kunnunwansu, kasa haƙuri sukai sai da suka leƙa. Aiko idanunsu suka gano musu zaratan mazajen ƴaƴan na Oum zagaye da ita tana bama AA abinci a baki, dai-dai kuma lokacin Babban Yaya shima ya buɗe nasa  baki wai ta bashi, shine suka saka sanya dariya, shima Fawzan yace bazai yarda ba ya je aka bashi. Kai da kaga fuskar Oum kasan cike take da farin ciki, haka suma su babban Yayan, farin cikin Oum ɗinsu ya saka fuskokinsu bayyana murmushi na musamman, musamman ma shi da AA da ba cika son yin dariya sukai ba sai sun so. Fuuuuu Mamy ta wuce sashenta zuciyarta na tafasa. Koda suka shiga ɗaki saita sakar ma yayarta kuka. Ita kanta yayar tata wata irin masifa take ji na tafaso mata daga ƙirjinta, amma dole ta danne ta shiga lallashin Mamyn da nuna mata kuka fa ba shine mafita ba. Dole suzo susan abinyi dan al'amarin na Oum fa na neman zame musu ɗan zane. Dan tabbas ta rigada ta gama mallake zukatan yaran nan da salon makirci (kamar yanda suke fassara soyayyar Oum ɗin akan su AA. Sai dai kuma wannan nasu mummunan zaton ne kawai, dan ita dai baiwar ALLAH Oum har cikin zuciyarta ne, hasalima takan manta da cewar ba itace ta ɗauka cikin su AA tai naƙudarsu ba saboda yanda ta sakankance matuƙa).........✍️ _Dangin Mamy ina gaisuwa 🙄🥱🏃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [16/04, 4:47 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣ ______________ 5 ......Sun tattauna sosai kafin su yanke shawarar yayar ta tunkari Abah da batun bikin cikin hikima. Hakan kuwa sukayi, bayan sallar la'asar Abah ya dawo gida Mamyn tai mata rakkiya har sashensa. Bayan sun gaisa cikin mutunta juna dan akwai ƴar kunyar surukuta a tsakaninsu duk da kuwa Abah ya girmeta sosai, amma yana kawaice mata saboda dattako. Cike da kissa tana murmushi take faɗin, “Kukam kamar a kanku aka fara aurar da auta, yanzu bayan shagalin Kanon bazaku barmu mu huta ba wani satin kunce zakuyi wancan kuma?”.         Cikin danne takaici da ƙyar Mamy ta ƙaƙaro murmushi tana ɗan laɓe baki, “Ai jikinsu ne zai gaya musu dan nikam dai nayi na ALLAH da naje muku Kanon ma. Amma da zaku tausayama kanku da kun barshi ku haɗe duka”.       Cikin rashin damuwa Abah yay ƴar dariya shima da faɗin, “Ai ku kwantar da hankalinku bikin ma Saturday ɗin dama da wahala ya yiwu. Dama yau nake son zama daku akan zancen dan yau da safe Baba ya kirani, ya kuma tabbatar min zuwa gobe shima zai samu mutanen gidan naku dan bammayi zaton Aunty Babba zatazo ɗin ba”. Ya ƙare maganar yana kallon Aunty Babba datai wani irin ɗagowa tana kallonsa.    Wani irin harmutsawa zuciyar Mamy tayi, da ƙyar Aunty Babba ta iya saita yanayinta cike da dakiya ta ce, “Lafiya dai ko Aban Fadeel? (Dan haka take kiransa)”.              “No lafiya Lau, Baba ne yace a ɗan dakata Ajwaad ɗin ya ƙara samun lafiya sosai, dan yaron nan ya bugu sosai dan ma ALLAH ya bashi ƙarfin hali ne. Ga kuma mutane sunyi ƙoƙari na zuwa wancan ɗin, ga azumi yana gabato mu kwana goma sha kawai ya rage, sai yace a bari kawai bayan salla idan muna da rabon kaiwa sai ayi. Amma nima naso ayin kawai a huta, damma uwarsa taƙi bani haɗin kai amma ina son horasa akan yarinyar nan ita kanta, idan son samuna ne kada ta tare yanzu har sai bayan sallar itama da kansa ya magantu ya faɗa mana dalilin ƙin amsar aurenta da yay har yana neman kashe kansa, amma nasan da wahala ta bari duk da dai jiya da yau naga ta daure ana son aga gudun ruwana, kuma zasusha mamaki ita da ɗan nata dan na shirya musu sosai....”     Gaba ɗaya takaici ma ya hana Mamy magana, jitake kamar ta falle fuskar Abah ɗin da mari ta huta daga ita har yayar tata. Amma dai suka danne da ƙyar suna ƙawata fuskarsu da murmushi kaɗan. Da ƙyar Aunty Babba ta ce, “Uhhm kaima kasan dai bazata bari ka horashin ba Aban Fadeel, amma kuma hakan shine dai-dai, ya kamata yasan muhimmancin yarinyar, kar yaga an bashi a ɓagas ya ɗauka arha ya samu ”.       “Ato kema dai ƙya faɗa Aunty, amma bazata yarda ba, shekaran jiya fa kuka ta sanya min ma wai ina son na maida masa ciwo baya. Tunda dai anyi ya wuce a haƙura mana. Kai ban san irin son da Fateema kema yaranta ba wlhy.”      Shiru Aunty Babba tai masa dan maganarsa ta ƙarshe sake sukar mata zuciya take, ita ko Mamy ma sai ta miƙe abinta. Shima kiran wayarsa da akayi ne ya sashi miƙewa ya fita. Da kallo suka bishi, yana fita Mamy ta miƙe a fusace har idannunta na tara ƙwalla tana faɗin, “Ashe da rigima kuwa a gidan nan Aunty......”      Da sauri Aunty Babba ta rufe mata baki, sai kuma ta kama hannunta suka fice ta baya zuwa sashenta..... __________★       Har dare Oum bata san yayar Mamy na gidan ba. Sai kusan takwas su AA sun dawo massallaci, shi kaɗai ya wuce sashen Oum. Babban Yaya da Fawzan kowa sashensa ya wuce. Abah kuwa sun barsa a waje yana gaisawa da maƙwafcinsu. Kai tsaye upstairs AA ya haura, dan ƙasan masu aiki na gyarawa kasancewar anan suka tashi. Shiru falon babu kowa sai ƙamshi mai daɗi na turaren wuta da aka saka ke tashi. Cikin yanayinsa na wanda yasha faman jiyya ya kai kwance a doguwar kujera, a haka ya jawo remote ɗin tv dana ac ya kunna, yana cikin searching channel Oum ta fito daga bedroom. Zama tayi tana ɗan matse fuska da faɗin, “Auta kun dawo?”.        Remote ɗin tvn ya ajiye tare da juyowa ya kalleta. Maganar da yay yinƙurin yi ya haɗiye tare da tashi zaune idanunsa akanta. Fahimtar kamar ya gane yanayin da take ciki ya sata saurin gyara fuskarta, cikin murmushi ta ce, “Lafiya? Ya naga ka tashi?”.            “Oum muje asibiti”. Ya faɗa cikin sanyi da damuwa maimakon amsa tambayar datai masa. Murmushi ta sake saki tana gyara ƙafafunta, “Asibiti kuma? Ni lafiyata ƙalau”.       Idanunsa da suka ɗan kaɗe ya tsurama ƙafafunta, sai kuma ya zamo ƙasan lallausan carpet ɗin falon ya zauna gab da ita. Ƙafafun nata ya kamo ya ɗora a saman jikinsa. Duk sun ɗanyi fushi kuwa, cikin sauri ya ɗago yana kallonta. “Oum dan ALLAH ki tashi muje asibiti, see your leg! fa”.        Murmushi sosai Oum tayi da faɗin, “Oh oh! Look, there's nothing wrong, my dear. I'm okay fa. Kawai dan kwana biyu ban ɗan motsa bane ba. Sannan yau na manta bansha magani na da yamma ba sai yanzu na tuna nasha bayan idar da salla. Ina mai tabbatar maka zata sauka yanzun nan”.       Sam bawai zuciyarsa ta gamsu bane, amma bazai iya jayayya da ita ba. Sai kawai ya shiga mammatsa mata ƙafafun. Idanu kawai Oum ta zuba masa tana murmushi, dan tasan yayi shiru ne kawai badan ya gamsu ba. Cikin son kwaranye masa damuwar data bayyana akan fuskarsa ta ce, “Auta ya kamata kaci abinci fa, sai kasha maganinka, doctor yace 8 amma gashi har ta shige baka nema ba.”        Fuskarsa a narke sosai ya ce, “Oum bana jin cin komai fa, zan sha maganin a haka kawai”.     “A'a bazai yiwu ba, bara na haɗa maka ko tea to.”    Da sauri ya maida ƙafafunta da take neman janyewa a jikinsa. “No Oum zan haɗa da kaina zauna ki huta. Naji sauƙi fa sosai”.           “Haka ake so ai my baby ALLAH ya ƙara afuwa, amma wannan jikin naka da sauran ƙarfinsa. Bara kawai na kira Inte ta haɗa maka”.      Fuska ya yamutsa, dan shi fa baya son masu aiki su masa abinda zaici. Bawai dan basu da tsafta bane ko yana ƙyanƙyamin su, a'a kaf ma'aikatan gidansu da iliminsu da kuma tsaftarsu. Kawai shi abinci idan bana Oum ba baya so sai idan ta ƙure. Dan ko abincin Mamy yakan daɗe baici ba a gidan balle masu aiki, su Saheeba kam ai da wahala su girka abinci ya cisa, shi kallon ma basu iya yake musu ba. Oum data fahimci baya so sai tai murmushi. Dai-dai nan Maanal ta fito daga bedroom ɗin Oum hannunta riƙe da novel, sai waya manne a kunneta tana magana da Didinta Shahidah. Sam hankalinta bai kai kan AA ba sai Oum dake zaune a kujera, sai da tazo gab da su fuskata ƙawace da murmushi daya ƙara mata ƙyawu sosai tana faɗin, “Kai Didi to ga Oum ɗin” sannan idanunta suka sauka akansa, ai da gudun tsiya ta janyesu tana haɗiye murmushin nata. Shima nasa idanun daya ɗan zuba mata ya janye, dai-dai nan Oum takai wayar data amsa a hannunta kunnenta. Ƙoƙarin juyawa tabar falon tayi, Oum ta riƙo hannunta tana mata alamar ta tsaya. Sai kuma ta ɗan janye wayar a kunnenta a hankali tace, “Haɗama mijinki tea”. Maida wayar tai ta cigaba da amsa gaisuwar Shahidah tana murmushi.         Manaal dai ta kasa motsawa, dan haka kawai furicin Oum ɗin ya ratsa mata jiki da ƙyau. Kalmar *Mijinki* ɗin nan da Oum ya ambata sai taji ta mata nauyi sosai a ƙirji. Juyowar da Oum tayi taɗan kalleta ya sata ajiye novel ɗin hannun nata ta nufi hanyar stairs cikin sanyin jiki tamkar wadda aka saluɓema kuzari. Ƙasa-ƙasa ya bita da kallo, sai kuma a hankali ya ɗan lumshe idanun nasa yana mai sakin ajiyar zuciya acan ƙasan maƙoshinsa ya cigaba da matsama Oum ƙafafun nata.       Sarai Oum na lure da su da yanayin da suka shiga. Amma sai ta basar ta cigaba da wayarta da Shahidah...        Kusan mintinan goma sha sai ga Maanal ta dawo. Ta samu har yanzu Oum na waya, yayinda shi kuma ke riƙe da novel ɗinta kansa a ƙafar Oum dai-dai gwiwa ya ɗan kwantar daga zaunen da yake. Murmushi Oum tai mata da nuna mata gaban AA ɗin alamar ta ajiye madaidaicin tiren dake a hannunta anan. Kanta ta gyaɗa, tare da kaiwa duƙe gabansa ta ajiye tray ɗin a hankali. Sai a lokacin ya ɗago idanunsa ya ɗan kalleta. Fuska taɗan ɓata tana kallon littafinta dake hannunsa, sai kuma tai masa yuuu da idanun irin na jin haushin dake nuni da wayace ka ɗauka min novel?. Laɓɓansa da ciwo ya sakasu sake komawa pink sosai ya wani ɗan laɓe mata, tare da ɗage gira kaɗan irin na (An ɗauka ɗin nan) sai hakan ya sake tunzurata ta miƙa hannu zata warce novel ɗin. Janyewa yay yana mai ɗan zaro idanu waje na mamakinta. Harara ta sake dalla masa ta ɗauke kanta.      Shayin ta shiga haɗa masa, tasan baya shan suger sosai tun zamanin ƙuruciya, dan ko sanda yay tashen shan chocolate baya shan mai suger sam dan baya shiri da shi sam. Gwara-gwara ma zuma ita kam yana masifar so, shine ma ya koya mata sonta itama. Amma dan neman magana yanzu saita ɗibo har huɗu kasancewar mai ƴaƴa ne zata afka masa. Ai baima san ya cafke hannunta ba yana ɗan waro idanunsa da faɗin, “Oum kinganta ko? Zata saka min suger”.          Oum data basar da su kamar bata san mima suke yi ba ta kallesu, cikin shagwaɓa Maanal data ƙwace hannunta daga riƙon da yay mata ta ce, “Oum nima fa novel ɗina ya ɗauka min”.       Ita Oum ma sai suka nema sakata dariya, dan idanun Maanal har sun fara ƙyalli alamar taruwar ƙwalla. Ta fahimci sufa idan suna a gabanta mantawa ma suke yanzu bada bane sun girma. Dai-dai nan Mamy da yayarta sukai sallama batare da Oum ta raba faɗan ba. Kusan a tare Oum da Maanal suka amsa sallamar, sai dai ita Maanal a hankali. AA kuwa a maƙoshi ya amsa yana kai tea ɗinsa ɗaya ɗauka baki. Yayinda yaƙi yarda ya kalla su Mamy da tun shigowarsu ita nata idanun ke'a kansu a kaikaice. Dan ba ƙaramin dukan zuciyarta ganinsu a taren yayi ba, ga yanayin zaman nasu kusa-kusa dan tray ɗin nan ne kawai ya rabasu sai ƙafar Oum ɗaya dake kusa da AA gab, ɗayar kuma kusa da Maanal. Manaal ɗin ce ta fara ƙoƙarin gaishesu, yayinda shi kuma ya ɗan basar da farko, sai Oum dake sallama da Ammie. Da ƙyar Mamy ta danne zuciyarta ta amsa gaisuwar Maanal ɗin, yayarta kuwa dan makirci tuni ta washe haƙwara tana tsokanar AA da Maanal. Wai autoci sunzo sun saka babarsu a gaba.       Ƴar dariya Oum tayi da faɗin, “Aunty harda ke kema bazaku bar min yara su huta ba? Saukar yaushe haka babu labari?”.        Kafin Aunty ta bada amsa AA ya gaisheta. Amsawa tai da kulawa tana jajanta masa jiki. Kansa kawai ya jinjina mata yana bin Maanal data miƙe da kallon ƙasan ido. Hakama Mamy da yayarta a kaikaice Maanal ɗin suke kallo, kowa kuma da abinda yake kissimawa zuciyarsa akan yarinyar. Yayinda Oum kam hankalinta ke akan AA ne kawai. Babu jimawa Maanal ta dawo, ƙaramin tray data saka ruwa da lemo da kofi akai ta ajiye a gaban Auntyn Mamy. Itako sai ta shiga saka mata albarka cike d makirci. Harda faɗin, “Eh lallai na ƙara yarda autar Hajiya Fateema ta girma”.        Kunya ce ta kama Maanal, dan haka ta sulale zata bar wajen, yayinda Oum ke dariya Mamy na tayata da murmushin yaƙe. AA kam novel yake karantawa hankali kwance yana shan tea ɗinsa. Oum ce ta tsaida Maanal ganin ta nufi hanyar ɗaki. “Auta dawo kici abinci, nasanki daga wannan shigar zaki iya neman wajen kwanciya”.      Kan Maanal a ƙasa ta ce, “Oum bana jin yunwa ALLAH. Sannan ba kwanciya zanyi ba yanzu zan dawo”.           Kai Oum ta jinjina mata, ita kuma ta shige tana istigafari akan ƙaryar da taima Oum, dan harga ALLAH batai niyyar dawowa ba sam...         Hira ta ɓarke sosai a tsakanin Oum da su Mamy, sai dai ita hankalinta ya rabu biyu da rashin dawowar Maanal falon, sam bata son yarinyar ta takura kanta. Dan ta fahimci har yanzu Maanal ɗin bata gama dawowa Maanal ɗinta ta baya ba. Ba komai ta saki jiki ba kamar yanda suke a da, yanzu ma wata kunya take neman ƙirƙira a tsakaninsu ne, shiyyasa take ta ƙoƙarin ganin ta kauda mata da yanayin. AA ma dai har yanzu yana zaune yana saurarensu, sai dai a zahiri zaka ɗauka gaba ɗaya hankalinsa akan novel ɗin da yama Maanal kwace yake. Sai dai sam ba haka bane ba, mamakin su kawai ke nuƙurƙusar masa zuciya da ruhi, dan su duka biyun ya musu farin sanin da harda wanda basu bayyana a gabansa ba. Haka yake, mutum ne shi mai tsartar tsiya, ALLAH ya azurtashi da saurin gane halayyar mutane a ƙanƙanin lokaci balle su. Kuma wannan halin nasa tun yana yaro yake tare da abinsa, miskilancin sa da rashin yawan magana yasa ba'a fahimtar hakan kai tsaye, sai Oum ɗinsa data gama masa sanin in and out. Duk da hankalinsa nakan su Mamy ya fahimci hankalin Oum kuma a rarrabe yake. Ganin yanda take faman kallon hanyar bedroom ɗinta yasa shi ajiye novel ɗin hannunsa ya ɗauka kofin daya gama shan tea yanzu ya haɗa wani shayin, cike da kulawa ya kalla Oum.          “Oum bara na kai mata wannan naga duk kin damu”.     Murmushi tai masa tana mai jinjina kanta, sai kuma ta shiga sanya masa albarka. Shi dai ya wuce yana amsawa fuskarsa da ɗan murmushi. Daga Mamy har yayarta da kallon takaici kuwa suka bisa, suna ganin Oum ta juyo garesu suka basar.......✍️ _Mun tafi kai tea. Saura kuma aci amanar Abah🙄🏃🏃🤣🤤_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [16/04, 4:47 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣ ______________ .........Babu knocking babu komai ya tura ƙofar ya shiga, tana zaune a gaban mirror tana shafa mai daga ita sai towel. Cikin yanayinta na rashin gaggawa ta juyo duk da kuwa tsoro taji, amma miskilancinta ya ɓoye hakan akan fuskarta. Shima dai saukar idanunsa a kan nata ya saka zuciyarsa motsawa, duk da jarumtar da yake nunawa a kanta da danne yanayinsa da tsiya-tsiya saboda miskilancin nasa shima da iya taku, a yanzu kam zuciyar ƴan maza da gangar jiki duk sai da suka motsa da ƙarfin ikon ALLAH. Da ƙyar ya iya lumshe idanunsa ganin taja hijjab ta saka a yanayin ko'in kula da shi. Busashen yawun daya haɗiya na samun sassauci daga kasalar dake neman zagwanye ɗan ƙarfin daya fara samu a yau ya saka Adam's apple ɗinsa motsawa sosai a cikin wuyansa. Cikin tasa dakiyar da basarwar shima ya cigaba da takowa cikin ɗakin, a gabanta saman mirror ɗin ya ajiye kofin shayin, batare daya sake kallonta ba ya ɗan jingina bayansa a mirror tare da harɗe hannayensa a ƙirjinsa.        “Kinsan bazaki dawo ba miyyasa kikama Oum ƙarya?”.    Shiru tai babu alamar zata tanka masa, hakan ya sashi karkatowa ya kalleta, dan abune daya san tafi kowa sanin ya tsana, wato yin magana a masa banza. A kausashe ganin tana neman miƙewa ma ya ce, “Ni nake miki magana kina min banza?”.        A halayya irin ta AA babu abinda Maanal bata sani ba, kai sai dai ma ta bama wani labari. Dan ko Oum badan ita uwace ba zatace akwai abubuwa da yawa data fita sani game da shi. A yanda yay maganar kawai ta fahimci ya hau zuciyar tasa, dan haka itama a ɗan tunzure ta juyo tana kallonsa cikin ido. Girarta ɗaya a ɗage ta ce, “Kai da ka shigo ka min sallama ne balle neman izini? Ko an gaya maka dabba ce a ɗakin!”. Ta ƙare maganar da balla masa harara ta murguɗa baki. Yanda kasan robbot haka ya tsaya hana kallonta kawai harta ƙarasa cikin closet ɗin Oum. Da wani irin salo ya shiga girgiza kansa irin na ɓacin ran nan yana cizon lips, a ransa kam rayawa yake (Wato yarinyar nan duk randa na tashi gyara mata zama zata banbance akwai tazarar shekaru a tsakaninmu masu yawa ƙwarai da gaske.) a zahiri kam closet ɗin ya nufa shima. Sam Maanal bata san da isowarsa wajen ba hankalinta na'a zaɓar kayan barci da zata saka. Dan tun shekaran jiya Oum ta saka Inte mai aikinta ta shirya kayan Maanal ɗin cikin closet ɗin ta tunda babu ranar komawarta nata sashen. Sama taka kawai taji nutsatstsiyar muryarsa mai cike da zurfi da fitar isa a cikin kunenta.        “Amma kin san zan iya dirje bakinki a ɗakin nan har sai yayi jini batare da sanin kowa ba ko? Bar ganin Abahnki ya tsaya miki tsaf zan koya miki yanda akema miji magana cikin tausasawa da ladabi nabar masa ke na ƙara gaba har sai kin HAIHU zan dawooo....” yanda ya ƙare zancen cikin ƙasan maƙoshi da busa mata numfashinsa akan dokin wuya zuwa cikin kunne ya sata kasa daurewa ta saki kayan a ƙasa tare da juyowa gaba ɗayanta dan sam batayi zaton a kusa yake da ita gab-gab ba. Aiko sai kawai gata a jikinsa gaba ɗayanta. Daburcewa tayi, wajen mutsu-mutsun janyewa ta ruƙunƙumesa gaba ɗaya saboda motsa jikinsa da yayi ya ƙure duk space ɗin dake a tsakaninsu suka mannu da katakon wadrob ɗin bayanta. Bata da zaɓin daya wuce yimasa zobe da hannayenta saboda shiga ɗimuwa. Gashi ta motsa gabas da yamma kudu da arewa babu ko ɗan ɗigon space ɗin barin jikin nasa balle fita. Mayataccen ƙamshin turarensa kam ya gama gauraye ilahirin hijjabin Oum data saka zuwa hancinta har ya ratsa fatar jikinta.         AA kam ɗan duniya, tunda ta shige jikin nashi yay wata kalar tsaiwar sojan badakkare kawai ya lumshe oily idanunsa masu hasken tsiya kamar an watsa madara a ciki ya wani kalar tura lips ɗinsa cikin baki ya matse yana sauke numfashi a hankali. Sai da ya tabbatar ɗumin jikinta ya gama ratsa nasa gangar jikin har ƙofofin gargasar jikinsa na bubbuɗewa, wata ƴar zufa ta taru masa a goshi sannan ya ɗan ja jikinsa baya gudun kar'a tafka abun kunya a ɗakin tsohuwa. Dan yasan kansa ƙwarai-ƙwarai da gaske, ALLAH ya azurtashi da ƙarfin buƙata, sai dai ya masa rahama da jarumta da dauriyar iya shanye yanayinsa koda ta ƙarfi ne. Sam bai shirya yin kowanne kalar yunƙuri a gareta ba a yanzu, ya ɗauka ɗammarar bama Abah damar horashin daya ɗauki alwashin yi, itama zai bata damar manta bayan data riƙe a ranta, itama Mamyn zai bata dama akan nata yunƙurin, daga haka sai ya fara dama tashi damar a yanda yake fata da tsarawa da kansu zasu bashi ita da gudun tsiya.       Tunanin da yay zurfi a ciki yasa bai ankara har Maanal ta surare daga wajen ba, sai da ya motsa ƙafarsa yaji ya taka kayan data yadda sannan ya farga da hakan. Juyawa yay kaɗan ya dubeta, zaune take a bakin gado ta dafe kanta da duka hannayenta. Fuskarta a duƙe take shiyyasa bazai iya sanin a wane hali take ba. (Ga tsiwa ga tsoro) Ya ayyana a ransa yana mai duƙawa ya ɗauka kayan data ciro ɗin, tare da rufe closet ɗin. Inda take ya iso, batare da yace komai ba ya ajiye mata kayan a gefenta ya wuce abinsa. A tunaninsa su Mamy sun jima da barin sashen, amma sai ya samu a yanzu ma harda Abah, da alama kuma magana suke mai muhimmanci. Sai dai fitowarsa ta sakasu ɗagowa duk suka zuba masa ido amma banda Oum. Sosai ya karanci kallon tuhuma da zargi a idanun Abah. Yayinda Mamy da yayarta suke masa na takaici da ɓacin rai. To yaya lafiyar kura... Dama, ai sai ya wani fiske abinsa yama shiga gaida Abahn. Abah yasan wanene ɗan nasa da halayyarsa, dan haka shima sai ya basar ya amsa masa tare da tambayar jikinsa. Ya amsa cewar da sauƙi, daga haka ya nufi hanyar fita abinsa dan fahimtar zaman nasu iya nasu ne...       Sarai Oum ta lura da kallon da Abah yabi AA ɗin, dan haka ta sake cuskule fuska tamau. Murmushi kawai Abah ya saki ya basar shima, a ƙasan ransa mamakin Fatemansa na sake mamayesa. Tama kwantar da hankalinta bazai mata magana ba. Amma yasan matakin da zai ɗauka. Dan yanzu kam ya sake aminta da zancen Kamila ƙwarai da gaske...... ________★          Maanal tana tabbatar ta daina jin motsin su Mamy a falo ta miƙe ta fito ɗaukar ruwan sha. Ganin Oum ta nufi hanyar stairs kamar mai tafiya da ƙyar tai saurin nufarta da faɗin, “Oum!” a raunane. Tsayawa tayi tare da juyowa, ganin Maanal ya sata sakin murmushi. “Oh kinji sun tafi shine kika fito daga ɓuyan? Auta sokike dai ki maidamu surukanki a gidan nan ta ƙarfi da yaji ko?”.     Kai Maanal ta duƙar tana murmushi. “A'a Oum nayi wanka ne, naga kuma zakuyi magana shiyyasa”.        “Za'aima Oum wayo kenan”.   Murmushi Maanal tayi tana rufe fiskarta da tafukan hannayenta. Oum ma dai dariya tayi. Sai kuma ta ce, “Kinga bara na bama su Inte wayar nan su kaima Aunty ta manta da ita”.      Da sauri Maanal tace, “Kawo nakai musu Oum”. Babu musu ta bata, dan itama tasan bazata iya sauka ƙasan ba ƙarfin hali ne kawai irin nata. Gittata da Maanal tayi yasa taji ƙamshin turaren AA sosai a hancinta fiye da sama-sama da take ji. Hakan ya sake tabbatar mata a jikin Maanal ɗin ne. Murmushi tayi sosai, a ranta tace, (Ai nasan za'a rina. Irin hakan nake gudarma Abanku amma ya kasa fahimta). Koda Maanal ta nufi ɗakin masu aiki samu tayi har sun kwanta. Sai kawai ta maida musu ƙofar ta rufe a hankali. Ta kitchen tabi ta fita dan zai fi mata sauri. Gidan fayau yake da haske dan tako ina akwai security light kwanyar, kanta tsaye ta shige sashen Mamyn, babu kowa a ƙasa sai Haule dake a kitchen, jin motsin Maanal ya sata leƙo. Murmushi ta sakarma Maanal, tare da fitowa gaba ɗaya cikin girmamawa ta ce, “Aunty Amarya barka da dare”. Guntun murmushi Maanal tayi mata da miskilar fiskarta dan sunan da Haulen ta kirata da shi ya mata wani iri, musamman daya kasance Haule zata girmeta, dan zasuyi sa'anni da Amaal. Cikin yanayin rashin sakewarta tace, “Mamy fa?”.        Upstairs Haule ta nuna mata. “Suna sama”. Kai kawai Maanal ta jinjina mata ta nufi hanyar, bayan ta buɗe ƙofar ta shiga ta maida ta rufe, dan tsarin sashen irin na Oum ne komai da komai, na AA dai ba haka yake ba, to bata sani ba ko nasu Fawzan ma da nasu tsarin. A hankali take taka stairs ɗin kamar wadda bata so, tana a kusan na biyar ɗin ƙarshe taja ta tsaya cak sakamakon shashshekar kuka, faɗuwa gabanta ya shiga yi, sai dai kafin tayi wani yunƙuri ta tsinkayi muryar Aunty Babba na magana cikin takaici.        “Wai Kamila kina da lafiya kuwa? Tamkar wata ƙaramar yarinya ki zauna kinama kishiya kuka! Ina jarumtar taki ne ta tafi?. Har wacece Fateema yanzu a gareki da zata baki tsoro. Sanda ma take jin kanta a Fateema Darma ɗin kin shigo gidanta kinyi rayuwa da mijinta, kin haihu sai yanzu ne zaki zama sususu akan ƙananun abubuwan nan.....?”              “Bazaki gane ba Aunty, wlhy Matar nan ta wuce dukkan yanda kike zato da tsammani. Ni wlhy a wannan gaɓar ƴaƴana nake buƙata tako wane hali, idan ba hakaba kuwa zan iya kashe Fateema.....”      Kaɗan ya rage Maanal takai ƙasa dan firgita. Dan wata muguwar hajijiya ce taji tana neman zubar da ita. ALLAH dai ya taimaketa ta dafe glass ɗin stairs ɗin da ƙyau. Anya bayan ƙaddarar data faru da ita tsakaninsu abaya akwai wani abu data taɓa jin ya girgiza zuciyarta kamar wannan? Mamy fa? Mamy dai Mamy dai ke furta zata iya kashe Oum. Mamy dai Mamy dai kalamanta ke bayyana akwai ƙullaliya tsakaninta da Oum....  Tunaninta ne ya katse jin abinda Aunty Babba ke faɗa.         “Kamila ki kwantar da hankalinki, na ɗau miki alwashin a wannan gaɓar sai munyi maganin Fateema. Babu maganar kisa a ciki, amma wlhy da ƙafafunta sai tabar miki gidan Aliyun da take taƙamar nata ne, ɗan uwanta ne tare da ƴaƴanki. Dan babu abu mafi ciwo a gareta kamar a shekarun nan ace Aliyu ya saketa, ya kuma rabata da ƴaƴan data gama wahala da su da sakankancewa nata ne....”       “Aunty bana katseki bane, amma tayaya Aliyu zai saki Fateema? Kada ki manta da jininsu ɗaya, iyayensu ɗaya. Zasu yarda ne ya saketa?”.    “Da gudun tsiya ma kuwa. Ko an faɗa miki haka zamu barshi ne? Ai sai mun juya masa kai daga garesu gaba ɗaya, ta yanda su duka babu wanda ya isa sakashi balle hanashi”.          “To ita kuma wannan ƴar iskar yarinyar da aka aurama Ajwaad fa? Kin fa san halin yaron nan da baƙin taurin kan masifa. Yanzu kina ganin tunda yasan a ƙulle nake da shi ko dubashi naje sashen sai ya hau barcin ƙarya. Kuma jira nake ya gama warkewa sai na sillesa tas, kuma ko yaƙi ko yaso sai ya rabu da annobar yarinyar nan. Dan har abada bazan taɓa son abinda ke tare da Fateema ba. Ba kuma zan haɗa jini da Asiya ba dan na mata tsana mai girma itama saboda kusancinta da Fateema”.         “ALLAH na tuba idan mun gama da Fateema wacece ita kuma wannan abar da uwarta. Ai ki fahimta wannan masifaffen son da Ajwaad kema yarinyar nan ba banza ba ne, tun suna yara suka tsafacesa ai. Shiyyasa ta tsara duka yaran su auri nata tsarin wato ƴaƴan munafukarta mai zuwa mata bin bokaye Asiya, kinga ya tabbata ke da su sai dai kallo. Matar nan fa yanda kika san NASARA haka take akan iya tsari, ke kuma sai ki sakankance sai abu na neman kwaɓewa. Yanzu dai ki muje ki kwanta dare yayi, ki ƙara nazari nima zanyi nawa. Amma dole ne Nuratu ta dawo gidan nan tai azumi. Wani ƙaramin wasa nake son a buga tsakaninsu da yarinyar nan, har itama waccan sakaran matar Fawzan dole ta shigo tawagar, facalanci nake so su buga ɗan gaske ta yanda sai ta tsani kanta a gidan nan daga ita har uwar ɗakin nasu. Tarewarta kuma ki riƙe wuta babu ita......”         “Ai ni so nake ma ta dawo nan gabana ta zauna, dan Ajwaad da kike ganin yaron nan hummm. Kuma tsarin nan naki yayi. Ai dama nafi son na fara gasama Fateema aya a hannu sai ta gama firgicewa da ni kafin tabar min gidan”.     “Yauwa ashe kin fahimceni, yanzu dai wayata nacan a sashenta na bari dan ta naɗar min maganganunsu, da safe nasan zamuji abubuwa da yawa”.      Ƴar dariya Mamy tayi da faɗin, “Kai aunty shiyyasa nake sonki”.     Idanu Maanal ta tsirama wayar, sai kuma tai murmushi tana mai kai hannu ta share hawayenta dake rige-rigen sakko mata........✍️ _Tofa yau dai Maanal taji ainahin Mamy, mi kuke tunani?🏃🏃🏃_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [17/04, 4:53 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣ ______________ .......Tsam ta miƙe daga zaunen da take a step ɗin, babu buƙatar ta bada wayar yanzu, dan haka ta fice a sashen. Da alama Haule ma ta shige ta kwanta dan har ta kashe wuta. Maanal taji daɗin samun Oum na wanka, sai kawai ta adana wayar ta kwanta. Koda Oum ta fito likimo tayi kamar mai barci, duk maganar da tayi kuma ta fiske. Hakan yasa Oum ɗin fahimtar tadaiyi barcin.      Shirin barci tayi, dan Abah sai kiran wayarta yake. Babu yanda ta iya dole ta kimtsa ta tafi. Saboda ya tabbatar mata yau idan batazo sashensa ba shi zaizo a gaban Maanal ya ɗauketa. Tasan halin kayanta, dan haka ta haƙura kawai tai shiri ta tafi. Sai da tama Maanal addu'a ta shafeta sannan ta rage mata hasken ɗakin ta daidaita mata ac kamar wata ƴar Baby. Aiko tana fita Maanal ta rushe da kuka. Wani irin tausayin Oum mai tsanani na ratsa mata zuciya matuƙa. Tabbas ta taɓa jin Oum ba ita ta haifi su Babban Yaya ba Mamy ce, amma bata taɓa sake tuna hakan ba ko kallon hakan a zuciya balle a zahiri saboda babu wani alamu dazai nuna hakan koda ga Mamyn ne balle Oum data gama sakankancewa. Itafa ganin komai take tamkar almara ko mafarki. Duk yanda taso yin barci hakan ya gagara, dole ta zauna kawai a zaune tana nazartar abubuwa. Daga ƙarshe ta ɗakko wayar nan ta goge recording ɗin da suka saka, yako naɗa da yawa dan harda maganganun Abah da Oum bayan fitar su Mamyn. Batamayi nisa a ji ba ta goge kawai ta ajiye wayar. Mikewa tai ya shiga bayi ta ɗauro alwala tazo ta shiga miƙama UBANGIJI kukanta. Kusan ma dukkan addu'oin ta akan Oum ne....      WASHE GARI yanda su Mamyn sukazo gaida Oum cike da makirci bakuna a washe sai Maanal ta shagala a kallonsu. A ranta tana jinjina lallai maƙiyin ɓoye shine ainahin maƙiyi, dan zai taima rayuwarka illa batare daka sani ba. Balle ace yana a jikinka, tare da kai matsayin masoyi na zahiri. Gara wanda zai zo ya kalleka ya ce maka wane BANA SONKA BANA ƘAUNARKA. Kasan baya ƙaunar taka zaka kiyaye komai tsakaninka da shi. Koda suka nema waya sai ta basu, da Oum tai magana sai tace ai taje kaima su Inte ɗin ta samu sunyi barci shiyyasa ta dawo da ita.       A cikin zuciyarta kuwa faɗi take (Oum baki san su wanene waɗan nan mutanen ba. Sunfi duk wani abinda kike kallo a matsayin haɗari haɗari. Amma kada ki damu, ba sunce YAƘIN SUNƘURU bane abun, muje zuwa yanzu ne za'ai wasan na gaskiya. KAREN BANA SHINE ZAI MAGANIN ZOMON BANA. Ni Maanal Habib Giro, na ɗauki ɗammara da alwashin sai waɗan nan mutanen sunyi nadamar sake dawowata RAYUWARSU. idan su aya sukai alwashin gasa miki a hannu ni zan gasa musu ƘARFE ne a tsakiyar kawunansu. Sai sun san ZURU BATA CIN ZURU SAI SAI DAI A HAƊU AI ZURU-ZURU. Ƴaƴa kuma tunda ALLAH ya mallaka niki tofa naki ɗin ne. MUJE ZUWA WASA).       🤣🤣Tofa nace ba. Ƴar mutan Giro fa tace muje zuwa wasa, da alama ainahin MAANAL zata dawo🥱. (Maanal dama in an MUTU ana dawowa😜?) 😂😂🏃🏃🏃 ____________★        KANO         Tsaye yay kawai yana kallon ƙofar daya gama mummurɗawa ya ji a rufe. A karo na farko ransa ya fara ɓaci da salon iskancin Huznah. Wai mi take nufi da shine halan? Ɗan iska ta ɗauke shi ko mi? Yau kwana ɗai-ɗai har takwas kenan da kasancewarta a gidan, amma tunda baƙi ƴan biki suka tafi da magriba tayi sai ta shige ɗaki ta kulle kanta. Da rana kuwa ita da kowa dake shigowa faran-faran. Hatta shi da rana tsakaninsu normal ne, da farko ya dauka kunya ce da kawaici irin na yaranmu, duk da baiyi zaton samun hakan daga Huznah ba, musamman idan akai dubi da shekarunta da wayewar zamani.. Wani ɗan murmushi yayi a karo na farko, ya sake sakin murmushin a karo na biyu saboda abinda zuciyarsa ta sake hasko masa. Baice komai ba yau ma ya juya ya koma ɗayan ɗakin dan dama bedrooms ɗin biyu ne a gidan sai falo, kitchen, ƙaramin store. Gini ne dai irin na mai rufin asiri ba irin wanda su Hajiya Basariyya suka jima suna fata ba.      Yana barin wajen Huznah da duk ke ankare da motsinsa ta ballama ƙofar harara. Cike da tsana ta ce, “Maye, in dai nice mu zuba, wannan jikin kuma ƙwalelenka na AA ne. Dan wlhy sai na sameshi, sai na sabauta rayuwar agolar yarinyar can ta yanda bazata taɓa moruwa ba. Idan Ummi tabar uwarta tana yanda taso a gidanmu ni sai na tabbatar mata KAREN BANA SHIKE MAGANIN ZOMON BANA. Daga haka ta koma ta kwanta tana cigaba da charting dinta da take yi daman. A dai-dai nan kira ya shigo wayarta. Zaune ta tashi ganin wanda ke kiran. Sai da ta gyara zama sannan ta ɗaga. Murya ƙasa-ƙasa ta ce, “Sille ya akayi?”.       Daga can wanda ta kira Sille ɗin cikin muryar ƴan daba ya ce, “Normal ne uwar ɗaki. Kawai zance miki Nurry fa babu wani bayani a ƙasa kan bikin nan nata da AA. Dan a majiya mai ƙarfi ance har yanzu bashi da lafiya yana gida yana jiyya sai an kwantar sai an tayar. Babu kuma wani yunƙurin ma za'a sake biki a gidan a wannan satin. Kai ita ma agolar gidan taku tana sashen babarsa bata tare turakarsa ba”.      Sosai hankalinta ya tashi da jin har yanzu AA ba lafiya. Cike da mamaki kuma ta ce, “Amma Sille kai bala'i ne, dan ALLAH ya akai ka samo wannan sirri mai girma haka?”        “Hahaha uwar ɗaki kenan, karki manta a hannun Nurry kika ƙwaceni, amma bari na baki a buɗe, ina da yarinya a gidan dake aiki ta dalilin Nurry.”       “Anya Sille bai kamata na fara tsoronka ba”.    Dariya ya ƙyalƙyale da ita jin abinda Huznah ta faɗa. Kafin ya ce, “Haba uwar ɗaki, ai ke ta dabance. Kin ganni nan duk rintsi bana manta alkairi. Sannan amana ɗaya ce”.    Sosai Huznah ta sauke ajiyar zuciya. Tai masa godiya da tabbatar masa zaiga saƙo ta account ɗinsa daga haka sukai sallama.....      Wayar na yankewa daga can Sille ya ƙyaƙyace da wata muguwar dariya. Sai da yay mai isarsa sannan ya ce, “Yaro bai san wuta ba kenan sai ya taka. Daga ke har Nurry ɗin kune kuke min aiki bani ke muku ba. Ina amfani da kune kawai na samu kuɗaɗe. Kuna nan kuna jira baku ankara ba sai dai kuga gawar shegen AA ɗin naku kwance a gabanku. Wannan alƙawari na ne, sannan gaba ce ta tsawon shekara takwas ni da shi.. kai yama kamata nasan agolar yarinyar nan ta gidan ku da akace ya aura”. Wayarsa ya sake ɗauka ya shiga tafa saƙo. Babu jimawa akai masa flashing. Kiran number ɗin yay black, kafin ma ta gama ringig ɗin farko an ɗaga. Daga can ƙasa-ƙasa muryar mace ta bayyana.         “Baby miya faru ne naga kace na maka flashing idan ni kaɗai ce? Faka-faka kafin wannan ƴar sa idon ta fito wanka”.       “Ke nifa yarinyar nan idan tace zata takura miki a gidan nan ALLAH zan aikata barzahu”.      “A'a ka rufa min asiri babu ruwan ka da ita. Sannan itama tana da nata amfanin da take mana ai. Yanzu dai miya faru?”.     Tsaki yaja mai kauri, kafin ya ce, “Hoton amaryar gidan nan nake so?”.       Hankali a ɗan tashe ta ce, “Wai Matar AA”.    “In ba ita ba akwai wata amarya ne a gidan?”.           A sanyaye ta ce, “A'a. Amma Baby kasan hakan akwai haɗari ko? Taya zan ɗauketa hoto nikam?”.    “Kefa wasu lokutan gaja ce wlhy, kuna gida ɗaya baki san yanda zaki shiga jikinta bane?”.        “Tab wlhy Baby hakan zai yi wahala. Itafa irin miskilayen mutanen nan ne na gaske. Sannan zan iya ƙirga maka ganinta da nai a gidan nan. Koda yaushe tana ɗaki ko falon sama kuma a sashen Oum take bana Mamy ba”.      “K ni hakan bai dameni ba. Kawai hotonta nake buƙata na kuma baki kwana biyu kacal”. Daga haka ya yanke wayar yana huci. Itako daga can sai ta zuba uban tagumi zuciyata na kai-kawo. Sille ya zamewa rayuwarta bala'i, itako miya ja mata shigowa bariki. Ƙiri-ƙiri da uwarta da ubanta a duniya saboda neman duniya su sun kasa tanƙwara rayuwarta ga wani ƙaton banza ɗan daba na juyata yanda yake so kuma dole tabi. Tabbas ta ƙara yarda da kalmar nan ta malam bahaushe dake cewa WANDA BAIYI SHARAR MASSALLACI BA YAYI TA KASUWA. To ita a ganinta ta kasuwar ma ai mai sauƙi ce, TA BARIKI yafi dacewa ace....       __________★ KADUNA        A Kaduna ƙiri-ƙiri Ammie ta hana Daddy sukuni sai rigima take masa akan dawowar su Hajiya Yaya. Shi kuma yayi biris da ita. Da yaga tana neman saka masa rayuwa gaba sai ya shirya yabar mata kasar ma. Wannan abu kuwa ya masifar ƙona mata zuciya. Harda kiran Nene tana kuka. Sai da Nene ta gama saurarenta tsaf sannan ta ce, “Ai ni hakan da yay ya min dai-dai Asiya, tunda nace ki fita a maganar su kin ƙi ko. Su idan sune hakan ta fari dake har fati inaga sai sun shirya bama murna kawai ba. Ba gaban iyayensu suke ba? To ki nutsu idan zaki nutsu kinji na faɗa miki. Kuma nima kada ki sake zuwa min da zancensu. Haka kawai ki dinga ɓatama kanki rai da mijinki akan waɗanda basu ƙi ki faɗi ki mutu ba.... Haka Nene taima Ammie tas sannan ta yanke kiran. Ta kuma tabbatar mata ta kira Daddy ta bashi haƙuri idan ba haka ba zatazo har gidan ta sameta.       Wannan faɗa na Nene shine ya kawo ƙarshen rikicin Daddy da Ammie suka shirya ta waya. Sai dai duk da hakan rashin dawowar matan gidan na damunta kodan yaransu dake zuba mata rashin mutunci. Dan ma bata kulasu bata shiga harkar su. Amrah ce kawai babu ruwanta.... __________★        “Mabera! Wai nikam mike damunka kwana biyun nan? Gaba ɗaya baka da sukuni sai tunani da lissafe-lissafe”.      Numfashi mai nauyi Daddyn Nazeefa ya sauke, kafin ya juya yana kallon abokin nasa shaƙiƙi da shi da shi suka san juna na haƙiƙa dan kar-tasan-kar ce. “Himm Bakori kenan, kaima ai kasan maganar gizo bata wuce ƙoƙi. A lissafin auren Nazeefa da yaron Alhaji Usman Chalawa wata uku kenan yau cir, kasan dai lokaci yayi da aikina zai fara a kansa ai. Wannan shine lissafe-lissafen da nakeyi. Sai kuma baban naman dana hango yanzu ya shigo a tarko”.       “Tofa babban nama kuma? Waye hakan?”.    “Ba yanzu zaka sami ba. Sai na gama da Chalawa tukunna. Jiya nayi waya da Nazeefa tace azumi na goma zasu dawo gida. Dan yace mata zasuyi Umra. Dan haka nake shiri, da sun dawo zata fara min nata aikin”.       Murmushi Bakori dake kallonsa yayi, a ransa yana mamakin hatsabibancin aminin nasa, ta gefe tausayin yarinyarsa da yake son jefawa a ramin zamba cikin amincinsa yake. Shifa duk iskancinsa ALLAH bazai iya hakan ba. Dan iyalansa nada muhimmanci mai girma a wajensa...... (Humm dan baka san iyalin naka tare kuke raba dai-dai da aminin naka bane Alhaji Bakori🏃🏃🏃🏃) _________★         Alhamdullah jikin AA yay sauƙi sosai, koma muce ya warke sai abinda ba'a rasa ba na tsakanin ruhi da gangar jiki. Kamar yanda yay alƙawarin bama Abah dama ya bashi ɗin. Dan ya tattara al'amarin Manaal ya ajiye gefe kamar ba shine yasha ciwo akan rasata da yaga zai yi ba. Gefe kuma baice komai game da batun ɗaga aurensa da Nuratu sai zuwa bayan salla ba. Sai dai yaƙi yarda su zauna da Mamy duk yanda taso. Da zarar ya fahimci zasu keɓe sai ya zille abinsa. Fahimtar akwai gaɓar da za'azo ya nema mafita ya rasa ya sashi shirin komawa kan aiki. Itama kuma Maanal yace ma Oum ya kamata ta koma kan aikinta, dan shi ba ruwansa idan ta taka doka zai bari kamfani ya hukuntata ne. Hutun kwana goma aka bata, gashi yau suna neman sati biyu. Azumi saura kwanaki bakwai a fara shi kacal. Ita Oum ma tsayawa tai kawai tana kallonsa. Yayinda Maanal tai kamar bata falon ma. Dan tunda ya shigo ta gaida shi ta maida hankalinta ga karatunta, sai shi da Oum ke hirar. Yanzu haka take masa, idan dai ya shigo sashen zata gaida shi, daga wannan gaisuwar ko kallon inda yake bata sake yi komai tsahon zaman da zai yi. Ko kuma tana fahimtar lokacin shigowarsa yayi sai ta koma ɗaki abinta. Wannan abun na cimasa zuciya da ƙona masa rai, amma ya share kamar bai fahimceta ba. Dan ya riga ya sakama ransa daga ita har Aban nata zai iya dasu. Shiyyasa da Oum ta nuna damuwa akan rashi bashi Maanal ɗin zai shiga lallashinta da nuna mata shifa babu komai ta kwantar da hankalinta ta bama Abah dama yay yanda yake so. A ransa kuwa shi kaɗai yasan abubuwan da yake shiryawa.........✍️ _😂Dan Oum mi kake shiryawa? Dan bamu musha mana._ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [17/04, 4:53 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖8️⃣ ______________ .......A ɓangaren Mamy kam ranta fes akan hakan. Burinta ɗaya yanzu shine Maanal ta dawo sashenta da zama kamar yanda ta zunguri Abah da zancen. Sai dai kamar ya yarda da farko sai kuma taji bai sake maganar ba. Ta ɗan bashi kwana biyu ne ta sake zuwa masa da zancen, dan idan ta cika matsawa zai harbo jirgin ta ne kasancewarsa mutum mai tsarta. Ajwaad kuwa data fahimci kauce-kaucen sa zata tattarashi ne ta watsar, akwai gaɓar data tanada masa ne. Sun gama tsara Nuratu zatazo nan gidan tai azumi. Acewarsu mamanta zata shirya ta tafi umrah sai ace Nuratun tazo nan ta zauna kafin ta dawo. Gefe kuma cike suke da alwashin bayan salla da sati biyu koda tsiya-tsiya sai an ɗaura auren Nuratu da Ajwaad idan ba haka ba kuma suyi maganin Oum...       Oho ita bama tasan sunai ba. Duk da bata son haɗin auren Nuratu da Autan nata bata taɓa ji a ranta zatai wani yunƙurin hanawa ba. Fatanta ma ALLAH ya daidaita komai ya canja rayuwar Nuratu ɗin su zauna lafiya da Maanal da shi kansa Ajwaad data san baya son haɗin auren nan. Kai ko Mamy gani take bata so dan haka take nuna mata a zahiri. Da yake zuciyar Oum ɗin a tsarkake take kuma sai bata taɓa bin ƙwaƙwƙwafin Mamy akan komai ba sam...     Yau ta kasance lahadi, dan haka Oum ta samu Abah da batun komawar Maanal aiki gobe idan ALLAH ya kaimu. A cewarta da zaman nan gara ta koma aikin sai ta samu nutsuwa sosai. Da farko Abah shiru yayi, dan sai ya dinga hango ai zuwa office ɗin zai saka Ajwaad yaga ya samu wata dama akan Maanal ɗin ne. Shiru ya ɗanyi na wasu sakanni, sai kuma cikin jinjina kai ya ce, “Okay zan yi tunani akan hakan”.       Miƙewa Oum tayi tana masa sallama, dan har yanzu basu koma dai-dai da Abah ɗin ba. Ta dai daina fushin da take yi da shi. Da kallo kawai ya bita yana murmushi da girgiza kansa. A ransa yace (Fatete na rigima kenan) da murmushin Oum ɗin Mamy dake da shi yau ta shigo ta samesa. Koda yake tun ma bikin su AA ɗin Oum tace ta bar mata Abah ɗin har sai Maanal ta tare. Hakan ba sabon abu bane ga Oum. Dan haka kawai idan ta bushi iska sai tace ta barma Mamy Abahn na sati biyu koma na sama da hakan. Wani lokacin Abahn ne ma ke gajiya ya balbaleta da masifa yace shi bai yarda ba kamar dai yanda ya sakata kwana a gunsa dole randa yayar Mamy ta kwana a gidan.       Sosai ran Mamy ya sosu da murmushin nasa, wanda tasan akan Oum ɗin ne tunda sun haɗu a waje. Tarasa ya zata raba wannan shaƙuwa da soyayyar, duk da haihuwar da tayi, da kwantar da kai tana musu bauta su duka biyun har yanzu Oum ta fita matsayi da girman iko a wajen Aliyu. Sam baya iya ɓoye ƙaunar da yake mata koda a gabanta ne ita Kamila. Baya shakkar yabon Oum ko sanya mata albarka ko yin kwatance da ayyukan alkairinta. Hira goma zaka zauna da shi zai ambata maka sunan Fateema so takwas ne kansa tsaye. Cikin takaici ta haɗiye ɓacin ranta ganin ya juyo gareta, a hankali ta maye fuskarta da sassanyan murmushi cike da makirci take tambayar fitar Oum ɗin wai taga ranta a ɓace. Ikon ALLAH sai Abah ɗin yay nauyin baki yau, dan murmushi kawai ya mata baice komai ba. A ƙasan ransa kuwa hankalinsa na'a kan Oum ɗin ne, buƙatarta yake a jikinsa ƙwarai da gaske, yana kewar sassanyan ƙamshinta da kulawarta a garesa. Badan wai Mamyn bata masa ba ita, kawai dai yana jin na Fateema a garesa special ne. ALLAH shine kaɗai yasan irin son da yake ma Fateema da ƙauna a rayuwarsa, shiyyasa yake kallon al'amarin Ajwaad da Maanal tamkar nashi da Fateema ne. Dan soyayyar yaran gaba ɗayanta tamkar gado ne daga tasu soyayyar, abinda kawai ya banbanta shine shi da Fateema jini ɗaya ne...      Haushin ganin ya tafi zurfin tunanin nasa wanda Mamy tai imanin akan Oum ne yasa ta miƙe ta wuce bedroom ɗinsa. Dan tana fara ganin irin wannan signing ɗin a garesa a duk lokacin da Oum ta bar mata shi take fahimtar ya gundura da ita hankalinsa nakan matarsa. Tasha zargin kodai Oum tana musu hakan ne dama dan wani tarko nata ko shiri, amma idan ta nutsa a bincike sai ta gano sam ba hakan bane ba..      Abah ya jima kafin ya dawo daga duniyar tunanin nashi, sai sannan kuma ya farga babu Mamy. Ajiyar zuciya kawai ya sauke ya ɗauka wayarsa ya tashi ya fita domin kiran ɗan uwansa suyi shawara akan batun Oum ɗin na komawar Maanal aiki. Wato Uncle Mahmud..... ____________★       Kuka bana wasa ba Nurry tasha da jin batun ɗaga bikinta dana AA har sai zuwa bayan salla. Wani irin tsanar Oum da Maanal ta ƙara faɗi da kauri a zuciyarta. Nanfa ta shiga ɗaukarma kanta alwashi kala-kala na gasama Oum da Maanal aya a tafin hannunsu. Dan ta tabbatar kamar yanda taji iyayenta na faɗa makircin Oum ne kawai. Bata sami nutsuwa ba har sai da sukai waya da Mamy da Saheeba da suka kwantar mata da hankali da tabbatar mata aure na nan babu fashi. ALLAH dai ya kaimu bayan sallar da sati guda za'ai ma ba biyu ba.. Sannan a gidan zatai azumi kuma...         Hakan ya ɗan sakata jin sanyi da sassauci a cikin ranta. Harta ɗan saki jiki ta cigaba da harkokinta musamman a media. Harda su tsara write-up ta turama ƙawayenta da abokan arziƙinta cewar biki sai bayan sallah saboda har yanzu ango babu lafiya..... ___________★        WASHE GARI.   Safiyar yau Litinin har Oum ta fidda ran Abah zai bar Maanal ɗin ganin tun jiyan baice mata komai ba. Haka shima AA ɗin baima saka ran komawar Maanal ɗin yau ba. Kawai dai ya tashi da nasa shirin ne. Bayan sallar asuba daga massallaci Abah sashen Oum ya nufa. Kasancewar yasan yanzu ita da Maanal ne a ɗakin ba kai tsaye yake shiga ba. Dan haka yay sallama bayan yin knocking a ƙofar bedroom ɗin sannan ya koma falo ya zauna. Babu jimawa kuwa sai ga Oum ta fito daga ɗakin sanye cikin dogon hijjabin sallarta. Tunda ta doso shi ya zuba mata idanunsa da suke a narke. Itako sarai data san halin kayanta da gejin da yake kawai na haƙuri da rashinta a kusa da shi sai ta basar kamar bata fahimci magiyar da yake mata da idanun nasa ba. Ɗan nesa da shi ta zauna, sai kuma ta ɗan zamo a kujerar kaɗan cike da neman magana ta ce, “Yaya Aliy ina kwana” (haka take kiransa lokacin ƙuruciya). Hararta yay da faɗin, “A'a baba Aliy ba yaya ba. Saboda kina son a faranta ran ɗanki zaki ce dani wani yayan gulma”.      Ƙaramar dariya Oum tayi, amma batace komai ba. Shima fuskarsa da murmushi ya ce, “Kun tashi lafiya?”.      “Alhamdullahi”. Ta bashi amsa. Kansa ya jinjina cike da gamsuwa. Kafin ya cigaba da faɗin, “Akan maganar ki ce ta jiya. Na bada dama Maanal ta koma aiki, amma da sharaɗin driver zai dinga kaita ba ɗanki ba. Dan bana son wata alaƙa ta haɗasu. Ki kuma gargaɗesa babu ruwansa da yarinyata a office balle ya takurata, na saka securityn da zan san duk motsinsa akan hakan, idan ya karya min doka kuma zan ƙara yawan kwanakin suspension ɗin”.     Murmushi Oum tayi a karo na farko. Hakama AA da yazo sashen sai dai yana hawowa stairs ɗin yaji muryar Abah dan haka ya dakata. Idanunsa ya lumshe, tare da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Ayya Abah koba security ba. Badai ka yarda taje ba, ai sai abinda ka gani kawai Aban Maanal”. Daga haka ya juya ya koma abinsa domin yin shirin office ɗin....       Oum ma bayan tafiyar Abah ɗaki ta koma tace Maanal tai shirin office Abah ya bari. Duk da zama waje ɗayan dama ya isheta sai taji gabanta ya faɗi. Na farko dai tana jin kunya da tunanin yanda zata kalla ƴan company a yanzu. Dan tasan dai sun gama sanin ita ɗin matar ogansu ce a yanzu. Na biyu yaya rayuwarta a companyn zata kasance a yanzu kuma tsakaninta da mai kamfanin. Tunda a gida ya rasa kowace dama a kanta acan da babu idanun Abah kuma fa?.....        “Ko baki son komawa ne Baby?”. Oum ya katse mata tunani. Ƙasa tai da kan nata tana ƙaƙaro murmushi. Sai kuma ƙasa-ƙasa ta ce, “A'a Oum. Kawai dai ina jin nauyin ƴan kamfani ne”.       Dariya sosai Oum ta sanya da faɗin, “Oh oh! Har yanzu dai Babyna na nan da wautarta. Ina ruwanki da su bayan yanzu ke oga ce. Matar oga ai oga ce ko. Tsakaninki da su sai girmamawa ai. Dan haka ki kwantar da hankalinki ki riƙe girmanki, ki ƙara ƙwazo da himma akan aikinki. Kiyi abinda ya dace na rike martaba da girmanki domin kare mutincinki dana mijinki. ALLAH yay miki albarka”.      Cikin jinjina kai Maanal ta ce, “Amin”...      Wanka ta shiga, Oum kuma ta fita zuwa kitchen haɗa musu breakfast dan tasan Auta baya wasa da fita akan lokaci, duk da Abah ya kafa dokar ba tare zasu tafi ba tana son Maanal ɗin ta koyi yanayin fitar tashi tunda na ɗan lokaci ne zasu koma fita a taren.. Zuwa bakwai ta kammala komai daya kamata. Ta fito fes da ita cikin Abaya maroon color datai mata matuƙar ƙyau da haska chocolate color skin ɗinta data sha gyaran aure ta sake kwanciya luff-luff. Ga wani ni'imtaccen sassanyan ƙamshi dake tashi a jikinta. Sam batayi wani kwalliya ba a fuskar, iya hoda ce sama-sama sai kwalli da ɗan lips-gloss kaɗan. Dan ko taje girarta ma batai ba. A dining ta zauna kamar yanda Oum ta bata umarni, ta ajiye ƙaramar handbag ɗinta saman table ɗin dining ɗin itama. Dai-dai nan shima AA ya shigo, tun kafin su ganshi mayataccen ƙamshinsa daya gama manne jikinsa da komai nasa ya iso hancinansu. Yayi matuƙar ƙyau cikin Maroon suit shima sai long sleeve shirt fara tas. Harga ALLAH sai da zuciyar Maanal ta ɗan motsa. Amma sai ta dake abinta tama fara ƙoƙarin zuba abincin a ranta tana ƙunƙunin (wayace ya sake airin kayanta)        “Auta har an fito?”.    Oum ta faɗa dai-dai isowar AA dining ɗin. Kansa ya jinjina mata, tare da kamo hannunta ya sumbata yana mai ɗan bata side hug. Sai kuma a ƙasa-ƙasa ya furta, “Barka da safiya my everything”.       Murmushi Oum ta sake masa, tana mai amsawa da, “Ka tashi lafiya ya ƙarfin jikin?”.         “Alhamdullahi Oumna, ai ɗanki ya warke sarai in sha ALLAHU ”.     “Masha ALLAH haka muke fata ai Auta”.        A hankali Maanal data ƙi sake kallon inda yake duk da zuciyarta na cike da zumuɗi da maradin hakan ta ce, “Ina kwana”.     Batare daya kalleta ba shima ya ce, “Lafiya”. Daga haka ya kalla Oum a ɗan shagwaɓe ya ce, “Oum yunwa zata cinye hanji na”.       Ƙaramar dariya tayi tana kallon Maanal, itama Maanal ɗin dai-dai ta ɗago ta hararesa. Dan itace ke faɗar haka idan tana jin yunwa. Gira ɗaya ya ɗage mata irin (Ni ɗin kike harara?) sai ta sake murguɗa masa baki sannan ta ɗauke kanta. Ita dai Oum wurin tai ƙoƙarin bar musu tana faɗin, “Bestynka ta zuba maka abincin zanje nayi wanka ne”.           Kamar Maanal zatai kuka tabi Oum da kallo. Sai dai batace komai ba. Sai da ta shige sannan ta ɗauke idanun nata. Tsohon minti ɗaya kafin tace, “Me zaka ci?”.        Shiru kamar bazai amsata ba hankalinsa akan waya. Kamar wadda taji haushi ta ɗago manyan idannunta ta zuba masa. Kaifin idanun nata da tasirinsu a garesa ya sashi kasa jurewa shima ya ɗago lumsassun nasa  ya zubasu cikin natan. Bata iya ta janye nata ba suka shiga ma juna kallo mai taushi da kassarasa kuzarin jiki. Lips ɗinta ta sake motsawa a hankali batare data raba idanun nasu ba ta ce, “Nace mi kake so?”.        Cikin kasala da tausasawa kamar baya so shima ya motsa lips ɗin nasa ƙasa-ƙasa ya furta, “Ke!”...........✍️ _Ehemm-eheem nace ba, 1+1 nawa kenan? An bamu assignment ne a makarantar islamiyyar mu ne ni kuma ban gane lussahin ba😌😣, shine nace bara na tambayeku🫣🏃🏃🏃🏃🏃🏃._ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [18/04, 3:56 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣ ______________ .......Daburcewa taso yi, ta kuma rasa yanda zata fassara amsar ta shi. Cikin suɓutar baki ta ce, “Ban gane ni ba!”.       Wani ɗan iskan gajiyayyen murmushi ya saki a iya lips ɗinsa. Kafin ya sake narke idanunsa dake sarƙafe da nata har yanzu. “Kince mezan ci? Me nake so? Nace KE!”. Ya faɗi (ke) ɗin da wani kalar sanyin murya yana ɗan waro fararen oily idanunsa da ƙyau cikin natan. Ai babu shiri ta janye nata zuciyarta na bugawa da sauri-sauri. Sai taji gaba ɗaya ma jikinta na neman fara rawa. Shi ko tsaf ya fahimci halin data shiga, dan haka ya saki murmushi cike da ƙeta. A ransa kuwa rayawa yake (Ba Abanki yace bazai bani ba sai na horu. Kafin na gama horuwar kema sai kin horu yarinya) a fili kam harɗe hannayensa yay a ƙirji kawai ya zuba mata ido. Ita dai ta miskile tana haɗa masa abincin a gabansa. Can ƙasan ranta luguden daka kawai zuciyarta keyi, jitake kamar ta zura da gudu, amma bazata yarda ta zubar da kanta a garesa ba...         “Ehheem! Ehemm!!”.     Gyaran muryar Fawzan ta maido AA daya zubama Maanal idanu a hayyacinsa. Janye idanun yay luuu ya maida kansa, Fawzan ya ɗage gira yana murmushi. Shima sai AA ɗin ya ɗage masa tasa girar irin (Miye?) ɗin nan. Dariya Fawzan ya sanya, tare da jan kujera kusa da AA ya zauna. Maanal data ɗan rage ɗaure fuskar da tayi ta ce, “Good morning Yaya F”.         “Morning Ƙanwar Yaya F, Baby Oum, Autar Abah, sannan kuma Bastyn Besty”.      Duk yanda taso dannewa bai yiwu gareta ba sai da ta saki murmushi tana turama AA duk abinda ta zuba masa, sai dai bata yarda ta kallesa ba. Sai ma hankalinta data maida kan Fawzan ta ce, “Yaya miza'a zuba maka?”.       “Ai duk abinda kika san yayi daɗi zuba min kawai Lilly.”    Murmushi Maanal ɗin tai tana jinjina kai. Sai da ta kammala zuba masa sannan ta koma cin nata. Suna gab da kammalawa Oum ta fito, duk da Maanal dama ba wani tana ci sosai bane ba. Oum na fitowa ma ta miƙe kamar wadda ke akan ƙaya. Cike da tsokana Fawzan ya hau yima Oum kirari, kafin ya gaidata. Itako tana dariya abinta cike da farin ciki. Sai ga babban yaya da su Naufal dake cikin shirin makaranta. Saheeba biye da su. Suma Oum ɗin suka shiga gaidawa cike da girmamawa, yaran kuma sukaje suka rungumeta. Itama Nibras ta shigo cikin shirin aiki, da alama ta makara ne. Idonta akan AA ta gaida Oum cike da ladabi, hakama babban Yaya sannan ta juya tana gaida AA ɗin daya juya yana magana da Naufal. A taƙaice ya amsa mata batare daya juyo ba. Maanal dake karantar yanayin kowa musamman Saheeba da tunda suka shigo taga ta mata wani irin kallo ta ɗauke kai a taƙaice ta ce, “Auntys barkanku da safiya”.        Babu yanda suka iya daga Saheebar har Nibras ɗin dole suka amsa. Sai dai kowanne da kalar zafin da yake jin Maanal ɗin a ransa. Yayinda shigar tata ta saka zuciyarsu sosuwa. Duk da bawani kwalliya tayi ba, babu kuma wani ƙyale-ƙyale a tare da ita kamar nasu. Amma tayi matuƙar yin ƙyau mai sanyi. Ga ƙamshinta na fita a nutse babu wata hayaniya. Tunda kuma tai musu kallo ɗaya ta watsar da su a tasu fahimtar. Yanzu kuma ta jefesu da gaisuwar raini. Oho ita bama tasan sunayi ba. Tama maida hankalinta ga babban yaya suna magana...      Shigowar Abah ta saka kowa maida hankalinsa kansa. Sai Mamy dake biye da shi riƙe da briefcase ɗinsa. Sosai Abah dake kallon zuria'ar tasa farin cikin ya mamaye ransa. A ransa rayawa yake (Nanfa duk mallakina ne, zuri'ata ce. Idan kuma ALLAH yaba Fawzan haihuwa da Ajwaad shima Fadeel aka ƙaro masa sai mu sake yawa). Mamy kam zuciyarta ce ta sosu da ganin wahalarta zagaye da kishiyarta. Tayi-tayi ta hana wannan zaman safen a sashen Oum tarasa yanda zatayi. Dan ita inma sun shiga gaisheta sama-sama ne, amma Oum kuwa anan ma suke breakfast wasu ranakun koda matansu sun girka sai su ƙi cin nasu sai sun zo nan musamman Fawzan da matarsa ke malalaciya..... Tunaninta ne ya katse saboda gaisuwar da Maanal ke mata. Amsawa tai fiskarta da murmushi, sai kuma ta tsargu da yanayin shigar Maanal ɗin. Ta ɗan saci kallon AA dake tsaye kusa da Maanal gab batare da suma sun farga da yanda suke ba. Dan ya miƙe ne zai amshi number a hannun Babban Yaya, kasancewar Maanal ɗin na tsaye a wajen suna magana da babban Yayan kuma sai tsaiwar tasu ta kasance gab-da-gab. Itama daba kallonsa take ba sam hankalinta bai kai da kasancewar kusancinsu ba duk da mayataccen ƙamshinsa ya addabi hancinta. Hirama Naufal ke mata tanata murmushi. Itama dai Nibras hankalinta akan AA da kasancewar Maanal ɗin a kusa da shi yake. Zuciyarta na mata zafi da jin kishin hakan. Ganin Maanal bata tare a sashenta ba ita kaɗai tasan a farin cikin da take ciki. Dan yanda take farin cikin har sai da Fawzan yay mamaki ma ya tambayeta. Amma sai tace da shi babu komai...       Gaba ɗayansu abin sha'awa a tare suka fito wajen da gwarazan motocin mazajen gidan suke duk a wanke. Dan tun jiya Bola ya wanke su fes kasancewar aikinsa kenan. Yara aka fara sakawa a motar su ta makaranta, sannan Baban yaya ya shiga tasa. Abah ya shiga shima tasa driver a gaba yace Maanal ta shigo kusa da shi. Murmushi AA yay a kaikaice kawai ya shiga shima inda nasa drivern ya buɗe masa. Shima Fawzan ya shige tasa hakama Nibras da taji wani kalar daɗi ganin Maanal tare da Abah zata tafi ba AA ba. Cike da mamaki Mamy take kallon motar Abah, dan bata san da komawar Maanal office ba. Sai da duk motocin suka gama ficewa maigadi ya maida gate ya rufe sannan Mamy ta kalla Oum dake murmushi.          “Wai nikam ƴarki badai aiki aka koma ba?”.      Ƴar dariya Oum tayi, ta ce, “Ai na manta muyi maganar jiya. Da ƙyar muka samu mijinki ya yarda, shine aka kafa mana dokar bazata bi Auta ba nace munji”.        Dariyar yaƙe Mamy tayi, a ƙasan ranta tana faɗin (munafuka abinda kika ƙullo kenan jiya dama. Ba komai zan yi maganinku) a fili kam sai cewa tai, “Ai ina bayansa yay maganinku keda ɗan naki”.        “Oh na manta ƴar adawa ce kefa. Nayi nan”. Cewar Oum tana barin wajen. Dariya Mamy tayi kawai, sai da Oum tai nisa da wajen ta gimtse fuska da rakata da harara. Sai kuma suka kalla juna ita da Saheeba dake cike fam da takaici itama. Dan ita sai yau da taga Maanal da ƙyau fiye da ko yaushe taji zuciyarta ta sake girgizuwa. Maanal ba fara bace ba, amma irin Black beauty ɗin nan ce da ALLAH yayma wani kalar sassanyan ƙyawun fuska dana jiki dana fata. Ga idanu masha ALLAH. Ba namiji ba ko mata da yawa sun sha yaba ƙyawun halittar Maanal, a hakanma tana da ƙoƙarin sututurta jikinta ne. Dan bata shigar banza, ko ɗinki bazaka taɓa ganinta da matsatstse ba sam. Gata ƴar ƙwalisa dan tasan sirrin kula da jiki matuƙa. Rashin yawan fara'arta a yanzu kansa irinsu Saheebar shakkarta, dan sai suga kamar ta cika girman kai ne, ita kuma sam a gareta ba haka bane. Maganar ce kawai yanzu bata cika son yi ba ne..... __________★         ZARIA   “Mom please ki barni naje. ALLAH acan nake son yin azumi nidai”.          Harara Hajiya Majdiya ta wurga mata. “Ni kinji nace karkije ne Najma? Ni nace ki kira Mah-mah ki sanar mata, tunda ita tace kije mata azumi kika kuma amsa. Sai yanzu ne zakice kin fasa Abuja zakije. Kina gani kuma tunda muka dawo Rufaidah kullum cikin kira take akan yaushe zaki koma. Ita kanta Mah-mah ɗin jiya muna waya sai da tace yaushe zaki taho.”         Sosai hawaye suka cika idanun Najma. Haushin kanta ya kamata. Miyasa ma ta amsa ma kakar tata zataje can ne. Wayar da sukai ɗazun da Yaya Fawzan ta sake dawo mata. Yanda yake roƙonta akan tazo Abuja tai azumi inba haka ba kullum zai kasance a hanyar Zaria ne. Kuma tasan sunyi alƙawarin ɓoye komai har sai nan da bayan salla Babba ta kammala exam ɗinta... Kamar wadda tunanin nata ya zaburar da ita tai saurin kallon Mom ɗinta.       “Mom na yarda zan kira Mah-mah ɗin, har ma da Aunty Rufaidah ɗin”.     “Sai ki haɗa da Babanki ma. Tunda shima kin san Kano kika gaya masa, kuma ya tsani magana biyu.”        “Mom dan ALLAH ki taimaka min ke ki sanar masa”.     “Wa? Ni? A'a kema kin san ganganne wlhy. Babu abinda ya shafeni. Kinga tashi ki ƙarasa min aiki malama kafin yarana su dawo school da yunwa”.      Sosai Najma ta zunɓura baki tana miƙewa. Kitchen ta nufa dan ɗaura girki. Tana girkin tana neman mafita. Dan bata san yanda zata tunkari babansu ba kasancewarsa mutum mai zafi. Dama da gyar ta samu ya barta zuwa Kanon dan shi kam bai son yaransa suyi nesa da shi ko yaya. Harta kammala tana faman ƙullawa da kwancenwa. Sai da ta fara zuwa ta sanar da Mom ta gama sannan ta nufi ɗakinsu. Miss call har biyu ta samu daga Ya Fawzan. Ta ɗan waro idannunta waje. Kiransa ta shiga yi, sai dai harta tsinke bai ɗaga ba. Tana ƙoƙarin yin na biyu kiransa ya shigo mata. Cike da shauƙi tai masa sallama. Daga can yay ɗan murmushi da faɗin, “Uhm-uhm wannan ƙanwa tawa dai bata jin magana”.        Sosai ta sake kwantar da murya, “Yaya dan ALLAH kayi haƙuri, ina kitchen ne Mom ta sani girki”.      “Ba damuwa na haƙura ai Mom ce”.      “Yauwa Yayana. Dama fa yanzu zan kiraka. ALLAH akwai matsala......” tsaf ta zayyane masa yanda sukai da mamanta. Murmushi yayi kawai, “Kinga karki damu, ni zan kira Grandma ɗin da kaina. Sannan ki shirya zanzo Zarian na ɗaukeki in sha ALLAHU ”.      Cikin waro idanu kamar yana gabanta ta ce, “Baba fa?”.        “Shima ki barni da shi”.     “Yauwa yaya Fawzan shiyyasa nake sonka”.        “Da gaske?”. Ya faɗa da wani irin shauƙi. Ai da sauri ta yanke kiran fahimtar katoɓarar da tayi. Ita kuma kawai irin tayi maganar normal ne bada wata manufa ba. Duk kiran da yay mata ƙin sake ɗauka tayi kuwa. Shi kuma daga can yayta murmushi. Tabbas kasancewarsa da Najma na bashi farin ciki, duk da kulawar da yake samu a gareta iya ta kalaman baki ce ta ɗara masa Nibras. Shi kaɗai yasan irin haƙurin da yake akan rayuwa da Nibras. Amma yana addu'ar Najma ta zama sanadin sharuwar hawayensa......     Itama dai Najma cike take da wani irin shauƙi, dan har tsakkiyar rai jin son Fawzan take yi. Kafin yanzu soyayya take masa na ƴan uwantaka kawai, amma lokaci ɗaya da bayyana mata manufarsa sai taji al'amarin ya zarce hakan. Yaya Fawzan shine irin mijin da take ma kanta fata. Wato mutum mai sauƙin kai. Gashi ƙyaƙyƙyawa ga nutsuwa da dattako. Sai dai kuma wani gefe na zuciyarta na jin shakkar matarsa. Duk da a zahiri Nibras ɗin ba wata masifaffiya bace, sai dai irin matan nan ne marasa sakewa da mutane.... Shigowar kira a wayarta ne ya katse mata tunani, a zatonta Ya Fawzan ɗin ne ya sake kira, amma sai taga Uncle Rafeeq. Idanu ta waro sosai, tare da ɗagawa da sauri.       “Lah Uncle R kai ne?”.   “A'a bani bane”. Rafeeq ya bata amsa cikin gatse. Da sauri tace, “I'm sorry Uncle mamaki nayi ne. Ina yini? Ya Aunty Nuwaira”.        “Lafiya Lau muke. Miya samu wayar Aunty inata kira a kashe?”. “Nah-nah ce ya shiga da ita bayi ɗazun da safe ta tsunbula a ruwa, shine aka sakata cikin shinkafa”.       “Tofa ALLAH ya kiyaye to, jeki kai mata taki”.    “Okay Uncle. Amma dan ALLAH kafin na kai mata na roƙeka wani abu”.             “Banda kuɗi nayi brock”.        “Kai Uncle nifa ba kuɗi nake nufi ba”.     “To ina jinki”. “Uncle kaga so nake naje Abuja nai azumi, sai aka samu matsala nariga na faɗama Baba Kano zanzo tun kwanaki, yanzu idan nace masa na canja bazai yarda ba, zai ma iya cewa duka a fasa......”.......✍️        _Mu haɗe a Maawad da wanda suka shirya🏃🏃🏃🏃😲_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [18/04, 3:56 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖🔟 ______________ ........“To ke wace gulmar ta saki canjawar, bayan naji Mah-mah da Aunty Rufaidah na maganar zuwan naki ma”.        Baki taɗan tura gaba, sai kuma cike da shagwaɓa ta ce, “Ni Abuja nake so yanzu Uncle please, idan akai salla su kuma basai nazo musu ba. Kaga nayi ma Ya Fa... Uhm uhm Aunty Maanal alƙawari itama”. Tai saurin waskewa jin katoɓarar da ta nema yi. Jimm Rafeeq yayi yana nazarin sunan data so fara ambata. Sai kuma tunaninsa ya ɗan koma baya akan ganinsu daya dinga yi a bikin nan tare da Fawzan. Tabbas ya zargi akwai wani abu kam, sai dai rashin hujja ya sashi sakin zancen tun a lokaci.....       “Uncle Please mana...” Ta katse masa tunani. Ajiyar zuciya ya ɗan sauke. Tare da faɗin, “Ba ruwana, kije ke ki samesa ba babbanki bane”.     Sosai ta sanya masa kukan shagwaɓa. Dan haka yace yaji zai yi tunani ta kaima mamanta wayar....       Badan taso ba ta fita kai wayar, tana addu'a a ranta ALLAH ya ɗaurata akansa, dan tasan yanama Baban nata magana zai amince......     _________★        Kusan a tare motar Abah data AA suka iso MAWAAD COMPANY. Maanal dake murmushin hirar da Abah ke mata tabi ko'ina da kallo. Komai yana a yanda ta sanshi. Sai da Abah ya ƙara mata nasiha na karta sakarma AA fuska da Addu'a sosai sannan ya barta ta fito. Hango AA tsaye jikin motarsa yana waya yasata tsayawa har sai da motar su Abah ta fita. Numfashi ta sauke a hankali, wata irin ƙauna ta ɗa da mahaifi na sake mamaye zuciyarta akan dattijon arziƙi Abah. Tabbas alkairin Abah a gareta mai yawa ne, da baki bazai iya musaltashi ba ma. Jinsa take a ranta shi da Oum matuƙa gaya a matsayin mutane masu muhimmancin gaske. Wani murmushi mai sanyi ya ɗan suɓuce mata hawaye na taruwa mata a cikin ido tunawa da nasihar Oum ita kuma. Ita fa dariya Abah da Oum ɗin ke bata ma a kwana biyun nan, Abah na nuna mata ta hora AA, Oum na lallashinta ta yafe masa komai ya wuce su koma kamar da can baya da suke.....        Tunaninta ne ya katse jin an riƙo hannunta da wani tattausan abu da ta tabbatar hannu ne shima. Sai kuma ƙamshin turarensa yay mata irin shigar zuruff ɗin nan ya wuce har tsakkiyar brain ɗinta yabar maƙaƙinsa a maƙoshinta. Cikin ɗan motsawar zuciya ta waiwayo, sai ko idanunta a cikin nasa daya wani tsatstsareta da su. Ƙwacewa numfashinta ya nema yi, ta fisgoshi da ƙarfi tana mai saurin juyawa ta kalla harabar Companyn. Sosai ma'aikatansu ke shigowa ciki, wasu a abin hawa wasu a ƙafa. Da yawansu idanunsu a kansu suke, duk da dai sai wani sinne kawuna suke wanda ta tabbatar na munafuncine kawai. Ƙoƙarin sake juyawa garesa ta sakeyi, dai-dai ya kawo ɗayan hannunsa zai zare handbag ɗinta a ɗayan hannunta. Hucin numfashinsa ya wani irin sauka mata a fuska. Gaba ɗaya sai tai mutuwar tsaye kawai, harya gama zare handbag ɗin ya koma tsaye sosai hannunsa a cikin nata. Batare daya kalleta ba can ƙasan maƙoshi ya furta, “Let's go”.        Ƙin motsawa tayi, dan haka ya waiwayo yana kallonta. Da wani salon ƙanƙance idanu tamkar ya manta a inda suke tsaye, muryarsa acan ƙurya ya furta, “Ko goyo kike so?”. Yay maganar da ɗan takowa gabanta kamar zai duƙa ɗin ta hau bayansa. Ai a zabure ta riƙo hannunsa jikinta har yana ɗan rawa. Hakama muryarta na rawa ta ce, “Ya ilahi mi kake yi haka?”.           Karo na farko ya saki wani shegen murmushi da ita kanta sai da zuciyarta ta motsa. Girarsa ɗaya a ɗage yana wani wara mata fararen idanunsa masu ƙyalli a cikin nata. Sai taji tsigar jikinta na tashi. Da sauri ta ɗauke kanta. Shima bai sake magana ba yaja hannun nata. Dole ta bishi yanzu kam suka fara tafiyar a jere. A nutse suke ɗaga ƙafafunsu su ajiye kuma a tare. Hakan yasa ƴan gulma sake nutsuwa a kallon nasu, harda masu ɗaukar hoto a kaikaice. Sarai AA na lure da komai, amma da yake gwani ne a iya basarwa da kama kai yayi tamkar ma bai san da wasu halittu a harabar Companyn ba bayan shi da ita. Ita ko kunya da nadamar ƙin saurin shigewarta tuni duk ta baibayeta.          Securitys ɗin ƙofar kansu sunyi kasare suna kallon abin mamaki, yau boss riƙe da handbag ɗin mace. Macen da kowa yake cikin ɗunbin mamakin aurensu. Dan tunda akai bikin a companyn gulmar kenan. Burin kowa wannan ranar da zasu dawo kan aiki, dan kowa jima yake kamar bai taɓa ganin Maanal ɗin ba. Cikin sauri suka shiga miƙa gaisuwa ganin suna neman gota su. Tare da yi ma boss murnar aure da jajanta masa yaya jiki. A mamakinsu ya amsa harda ɗan murmushinsa. Duk da dama can ba wai yana wulaƙanta kowa bane, amma ganin murmushin boss haka arhar banza ai sai mai rabo.      To a cikin ma suna shiga kowa yay tsit, waɗanda ke leƙensu ta windows da musu video duk sun koma mazauninsu da gudu. Gaba ɗaya Maanal ji take kamar ta zura da gudu, dan gaba ɗaya attention ɗin kowa ya dawo kansu ne. Ta gefe ido take kallon ganin yanda duk suka miƙe a tare cike da girmamawa, shima sai yaja ya tsaya. Da ɗaɗɗaya suka shiga miƙo gaisuwa. Hannu ya dinga ɗaga musu fuskarsa da sakewa amma ba murmushi yake ba. A mamakinta sai itama suka shiga gaisheta. Karo na farko ta ɗan ɗago ta dubesu, ba wani yawane da su ba dan ba'a gama zuwa ba. Nan kuma iya waɗanda ke a ƙasa ne, mafi yawansu ma cleaners. Guntun murmushi kawai tai musu.       Fahimtar a takure take yasa AA ɗan kallonta tare da matsa hannunta dake a cikin nashi. Dubansa ta ɗanyi, a saman lips ya furta mata, “Muje”. Yanzu kam bata musaba ta bishi, dan hakan zaifi mata sauƙi ita kam. Duk da dai a ranta bata son binsa office ɗinsa department ɗinsu take son wucewa. Suna shiga elevator ta wani sauke ajiyar zuciya tare da janye hannunta dake a cikin nasa. Dariya ma shi kam ta bashi, dan haka ya taɓe baki da faɗin, “Matsoraciya, nine kika raina kawai”.        Kallonsa tai baki a tunzure ta ce, “Waye matsoraciyan?”.         Kamar wasu masu faɗan yara ya juyo yana riƙe ƙugu idanunsa ware a kanta ya ce, “Ke mana”.           Itama juyowar tai tana matsowa gab da shi idannunta cikin nasa da yanayin harara hannayen nata a ƙugu kamar yanda sukeyi a da in suna faɗa ta ce, “Niba matsoraciya bace sai dai idan kai”.      Matsawa shima yay ƙoƙarin yi gabanta sosai idanunsa a cikin nata. Baya ta shiga ja yana binta har suka dangane da bangon elevator ɗin. Sai da ya tabbatar ya matse mata ko'ina ta yanda ko numfashinta a sarƙe yake fita sannan ya ɗaura hannunsa ɗaya a bangon shima ya sake mata rumfa, still dai idanun nasa na'a cikin nata da take mar-mar da su na alamar tsoro amma a zahiri a dakenta take. Ranƙwafawa yay a kanta da ƙyau tsahonsu ya dai-daita, kafin ya sake matsar da fuskarsa gab-gab da tata tamkar zai haɗe bakinsu waje guda. Gaba ɗaya sai Maanal ta rikice, fuskarta tai ƙoƙarin maidawa gefe cikin in-ina da sarƙewar harshe ta ce, “Wa....w. wai miye haka kake yi?”.           Cikin son ƙoƙarin hanata janye idanunta a cikin nasa tamkar mai raɗa ya furta, “Kulawa da ƴar Abah mana.” ya ƙare maganar yana hura mata iskar bakinsa akan idanu.       Baki ta ɗan tura tana ƙoƙarin tureshi da yin mar-mar da idanun saboda iskar da yake hura musu, “To ni nace maka ina so?”.            “Ai basai kin faɗa ba, Abanki ma haka yake so naga”.        Kasa cemasa komai tayi, ga idanuwanta sun fara tara ƙwalla. Dai-dai nan ƙofar elevator ɗin ta rabe biyu ta buɗe kanta. Daburcewa Manaal tayi ganin mutane har kusan uku tsaye saboda itace ke facing ƙofar, shi kuma ya juya musu baya. Ai babu shiri takai hannu gefen cinyarsa ta mintsina cikin rawar murya da raɗa ta ce, “Mutane fa”.       Idanu ya ɗan lumshe dan har yanzu hannunta na'a jikinsa taƙi sakin mintsinin data masa sai ma sake matsewa take sosai. Kaɗan ya waiwayo kansa ya kalla ƙofar elevator ɗin. Sai kuma yay wani kalan luuu da idanun cike da basarwa ya miƙe tsaye da ƙyau. Maɓallin rigar suit ɗinsa ya shiga sakawa tare da kallon hannunta dake a jikinsa har yanzu. Silently ya ce, “Sai fatan ya cire ne Besty”.       Da sauri ta janye hannun nata, sai kuma ta yunƙura zata fice ya cafko hannunta. Cike da takunsa na nutsuwa da ƙasaita tamkar komai bai faru ba ma ya fito, su HOD dake wajen suka shiga musu barka da dawowa cikin girmamawa. “Thanks you”. Kawai ya faɗa a taƙaice ya jata suka bar wajen kanta a ƙasa ita dai.        Sai da suka ɓace a wajen gaba ɗaya Director Steven ya kalla HOD da CFO fuska da murmushi ya ce, “Uhm dama haka boss yake”.      Dariya HOD ya sanya, tare da faɗin, “Ai irinsu daman yan babu sauƙi ne ina gaya maka. Ai kowa ya shirya, dan sai an mana ƙurmus a companyn nan da soyayya”.       Dariya suka sake sanyawa a karo na biyu, banda CFO da zuciyarta ke mata zafi da raɗaɗi saboda kishi. Tsahon lokaci take jin son AA a ranta duk da ta girmesa a shekaru, sai dai tana matuƙar ƙoƙarin dannewa ta yanda kowa bai taɓa fahimtaba a companyn. Shi kansa ta fahimci kamewarta ya sashi bata amanna kai tsaye, dan duk wadda zata nuna masa tana sonshi in har tana a kusa da shi duk iya aikinta sai ya canja mata waje. Hakan data fahimta yasa ita tazo da sabon tsarin kame kanta. Ita ɗin bazawarace, mijinta rasuwa yayi shekaru biyar kenan, bata taɓa haihuwa ba. Bata sake wani auren ba kuma har yanzu. Tun randa akai musu interview a companyn ta ɗaura idanunta akan CEO taji duk duniya shi kaɗai take so. Ƙyaƙyƙyawace itama ta gaske, gidansu kuma gidan kuɗi ne ƙwarai da gaske, tayi karatu mai zurfi, ko aikin nan tana yinsa ne dan ra'ayi kawai bawai dan buƙatar albashi ba, duk da dai AA mutum ne mai ƙoƙarin kamantawa ma'aikatansa albashi mai tsoka dako gwamnati albarka musamman daya kasance ƙasar tamu zalunci yayi gaba ba'a wadata ma'aikatan da albashi mai ƙyau..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [21/04, 2:25 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣ ______________ ........Cike da farin cikin aikar da Mamy tai mata ta fito, dan dama hanyar da zata fita a gidan take nema sai kuma ga mafita ta samu cikin sauƙi. Abinda ya ƙara mata daɗi da Mamyn tace ta hau taxi tunda drivers ɗin gidan duk sun fita. Ɗaya ya tafi kai yara makaranta, ɗaya ya tafi da Abah ɗayan AA. Ita kuma tana buƙatar akai mata saƙon ne yanzun nan. Ba komai Haule ta fahimta akan Mamy ba, amma ta daɗe da gane wasu abubuwanta a gidan musamman akan fuska biyu ga Oum, kawai dai ba abinda ya shafeta bane shiyyasa bata gaɓa ɗaɗara kanta da ƙasa ba. Sai dai duk wani aiken Mamy ita take sakawa, ta yarda da ita ɗari bisa ɗari. Tasan kuma hakan nada nasaba da kasancewar Maman Nuratu ce ta kawota gidan. Sai dai abinda Mamyn bata sani ba Maman Nuratun ta kawota ne dan tai mata aiki a gidan, yayinda ita kuma Maman Nuratu bata san Sille takema aiki ba a kansu su duka da AA. Can gaban wani tsohon Company Haule tace mai taxi ya sauketa. Ta zaro kuɗinsa ta basa sannan ta tura kai ciki babu ko ɗar. Kai kawai mai taxi ɗin ya girgiza zuciyarsa na sosuwa da ganin yanda yaran mu na hausawa suka lalata kansu. Kowa yasan wajen nan maɓoyar ƴan daba ce da manyan ƙasa  ke amfani da su wajen ta'addanci, shiyyasa ko anzo an kama su basa wuce ranar ake sakinsu su dawo. Ya tabbatar yarinyar nan kodai kayan shaye-shaye zata saya ko kuma mu'amular banza. Shi dai yaja taxi ɗinsa yay gaba.         Tunda Haule ta shigo cikin tsohon companyn sosai yaran Sille dake zaune daba-daba wasu na shaye-shaye, wasu na wanki, kai kowa dai na hidimar gabansa tamkar wanda suka samu gida suketa gaisheta dan kowa a cikinsu yasan yarinyar oga ce. Ita ko cike da jin kai take amsa musu harta dangane da idan ɗakin Sille yake. Bacher ce ta langa-langa, daga ciki kuma katako, sai dai an fenteshi tsaf ta yanda bazaka taɓa yarda katako bane ba. Ɗakin babbane sosai, akwai gado a ciki da kujeru set guda, sai freight da television harda speakers harda AC. Ƙasan ɗakin kuwa tils ne tsaf. Zaune yake a kujera ya wani barbaje gabansa kwalaben giya ne har uku, sai dai ba giyar yake sha ba taba ce a hannunsa kunnesa maƙale da waya alamar magana yake, daka gansa kuwa kaga Sillen na gasken gaske, dan sirrine sosai tamkar zai karye ko in iska mai nauyi zata iya yin gaba da shi. Tunda ta shigo ya zuba mata ido, tana ƙarasowa gabansa yasa ƙafa ya taɗota ta faɗa a kansa, matseta yay a jikinsa tare da manna mata kan tabar hannunsa a damtsen hannunta. Ƴar ƙara tai da ƙanƙame jikinta saboda zafin wuta, sai yay murmushi da yarda tabar a ƙasa ya shiga shafa mata wajen da har ya ɗashe dan ya ƙonata. A haka ya kammala wayar, ana yankewa daga can bai wani tsaya komai ba yay wurgi da ita gefe ya ɗauka Haule cak ya nufi gadon ɗakin da ita.....        Sai da suka gama masha'arsu sannan ta miƙe a ɗan rikice tana faɗin, “Baby bara na wuce. Aikana matar can tayi gidan su Nuratu nakai saƙo”. Ta miƙa masa wayarta tana cigaba fa faɗin, “Gashi na ɗakko maka yau da safe, dan ita da shi duk sun koma aiki”.        Kamar yanda bai tanka mata ba tun ɗazun yanzu ma batare daya ce komai ba ya amsa wayar daga kwancan da yake. A zabure yay wani kalar tashi zaune yana waro idanu waje. Sai kuma ya nufi drawer ɗin dake a ɗakin ƙarama ya buɗe, kayan ciki ya shiga watsowa a ƙasa har ya samu damar ganin abinda yake nema. Ita dai Haule tsoratama tayi da yanayin nashi, da sauri ta miƙe tsaye tana kallonsa. Juyowa yay inda take idonsa akan wani hoto daya ɗakko. “K duba min nan ko idona ne? Data cikin hoton nan da wannan duk mutum ɗaya ne?”. Karo na farko kenan dayay mata magana cikin buɗaɗɗiyar muryarsa mara daɗin saurare da tafi gangar jikinsa girma. Amsar wayar tata tayi da hoton ta zuba musu ido itama. Sai kuma ta ɗago tana kallonsa. “Baby tabbas wannan duk mutum ɗaya ce, kawai dai anan bata ƙarasa kaiwa mace bane ba. Dama kasan matar AA ɗin?”.         Bai tanka mata ba, sai wani irin naushi daya kaima bangon katakon ɗakin yana faɗin, “Yanzu ne yaƙin na gaske zai fara”..      Sakare Haule tai tana kallonsa. Sai dai ko kallon inda take bai sake yi ba ya nufi bayin dake ɗakin ɗan ƙarami na wanka, wanda shima dai ɗin na langa-langa ɗin ne.. Wanka yake yana dariya sosai kamar mahaukaci sabon kamu. Jinsa yake a wani irin nishaɗi mai girman gaske daya daɗe baiji a zuciyarsa ba. Ajwaad ya auri Maanal fa? Eh lallai yanzu ne za'ai wasa mai zafin gaske tsakaninsa da shi. Tabbatacen alwashine wannan a garesa sai ya nakasta Ajwaad da Maanal. Dole ne yayi RAMUWAR GAYYA DA TAFI GAYYA zafi. Shine fa Sillen karan gero mai wuyar tsagewa, idan kai nasarar tsagewar baka yanke ba kai mai nasara ne. Uban daba yake a yanzu mai kujerar ƙarfin iko. Ajwaad! Maanal! Ku jira sakamako....     Ya kwashe da wata shegiyar dariya yana kaiwa bangon langa-langan duka har sai da Haule dake shirin tafiya ma ta firgita. Hakama yaransa dake can ta waje duk sai da suka kallo ɗakin da mamakin minene ya saka ogan nasu nishaɗi haka ne?...      _Tofa, mike faruwa ne? Wanene kuma Sille? Miyake nufi da yanzu ne wasan zai fara? Menene tsakaninsa da AA ko nace Darma Family da har ya shafi Maanal yake ajiyar hotonta?. Hummm kumuje zuwa kudai cakwakiya ce ta gaske fa🏃🏃🏃😀._ ___________★        Suna ƙarasa shiga cikin office ɗin Maanal ta ƙwace hannunta daga cikin na AA. Babu musu shima ya saketa. Bai kuma ce komai ba ya nufi kujerarsa. Ko'ina a tsaftace yake ƙal a office ɗin. Ga wani ƙamshi mai kwantar da zuciya na tashi. Files ɗin dake a table ɗin nashi tule yabi da kallo, sai dai an ajiyesu a tsare dan kowa yasan shi ya tsani ganin waje rakwacam ba tsafta. Hannu ya kai a hankali ya kunna computer ɗin saman desk ɗin, kafin ya ɗago idanunsa ya zuba akan Maanal dake a tsaye har yanzu. Kallonsa take yi itama, sai dai yana ɗagowa ta kauda kanta. Baki yaɗan taɓe, sai kuma ya ɗauka kan waya ya danna 1 tare da kaiwa kunnensa. Dai-dai an ɗauka. A taƙaice ya furta, “Zo ciki”. Bai jira amsa ba ya yanke kiran. Maanal ya kalla fisha ya ɗauke idanunsa, ciki-ciki ya ce, “Malam sit”.      Harararsa ta ɗanyi, sai kuma taje ta zauna dan bata son wanda taji yace yazo ya shigo ya ganta a tsayen kodan nasihar da Oum da Abah sukai mata na darajta kanta ga ma'aikatan companyn. Bawai tazama mai girman kai ko wulakanta kowa ba. A'a ta mutunta kanta da kame kanta yanda ya dace dai matsayinta na matar ogansu. Inba haka ba mutane da yawa zasu fara amfani da ita a yanzu domin cimmasa a ciki da wajen companyn. Hakama mata dake ƙulafucinsa a ciki da waje zasuji shakkar nunata koda da zunɗene balle isa gabanta.       AS ne ya shigo bakinsa da sallama bayan yayi knocking AA ɗin ya bashi damar shigowa ciki. Batare daya kalleta ba saboda girmamawa ya wuce sum-sum kamar munafuki inda boss yake. Hankalin AA a computer shima, batare daya ɗago ba ya ce, “Daban kiraka ba bazakazo kamin bayanin abinda ya dace ba kenan Haneef?”.            “Ayi haƙuri sir, naga kana tare da Auntynmu ne shiyyasa. Amma ai min afuwa”.      Komai AA bai sake cemasa ba. Sai tulin documents ɗin dake zube ya kalla. Matsowa AS yayi kusa da shi domin fahimtar abinda yake nufi. Cike da nutsuwarsa ya shiga masa bayani yanda ya kamata. Shi kuma yayi shiru yana saurarensa. Hakama Maanal dake latse-latse a waya kunnenta na kansu ne tsaf. Fin minti ashirin kafin su gama magana da AS ya fita. Dan haka ta ɗago ta kalla sashen da yake zaune. Ganin zai fara aikinsa kamar ya manta da ita yasa ta miƙe. Wayarta ta saka a handbag ɗinta sannan ta nufesa, batare data ƙarasa inda yake ba ta ce, “Nifa zan tafi”.      Yi yay kamar baijita ba tsawon sakanni kafin ya ɗago ya kalleta. Ganin yanda ya kafeta da idanu yasata ɗauke nata tana sake tsuke fuska. Shima janye nasan yay ya maida ga aikinsa yana faɗin, “Nace miki na gama dake ne?”.          “Amma kasan fa aiki nazo ko. Kuma Abah yace ka fita harkata”.     “Hakane Aunty Maanal yi haƙuri ƴar gidan Abah”. A yanda yay maganar tasa ta ɗan hararesa. Dan irin gatsen da yake mata kenan ko ada can idan tace yay abu kota takura masa idan yace bazaiyi ba sai ya dinga kiranta da Aunty...... Takaici ya saka Maanal ɗauke hankalinta daga gareshi gaba ɗaya. Tsohon mintuna arba'in yanata aikinsa kamar ma ya manta da ita akai knocking ƙofar. Sai da ya kalla sashen da Maanal take sannan ya bada izinin shigowa. AS ne ya shigo yanzun ma. Batare daya kalletaba yanzu ma yay mata sannu. Maimakon amsawa saita samu kanta da harararsa, dan haushin ogansa ya shafe sa shima. Shi dai da yake ba kallonta yake ba baima san tanayi ba. Cikin girmamawa ya ƙarasa gab da AA, murya a ƙasa yake masa bayani like ba'a son taji komai. Sai ta sake tunzura. AA ya jinjinama AS kansa, tare da faɗin, “Shike nan kuje ka kaita, su kuma su bari after break na ɗan rage aiki”.       “Okay sir”. AS ya faɗa yana nufar inda Maanal take. Kansa a ƙasa ya ce, “Aunty bismillah”.        Miƙewa tayi batare da tace komai ba, sai dai ta kalla inda AA yake zaune cikin yanayin harara. Sai ko akai sa'a shima ita ɗin yake kallo. Gira ɗaya ya ɗage mata, sai kuma ya kashe ido ɗaya cike da neman rigima da son tunzurata. Aiko fuska ta yamutse tare da janye nata fuuu tabi bayan AS bayan ta zuba masa harara. Rakata yay da idanu har ta fice gaba ɗaya. Guntun murmushi yayi yana mai lumshe idanunsa ganin yanda take cika da batsewa. A kan lips ya furta, “Ƴar gatan Abanta kenan” yay wani murmushin shaƙiyanci yana datse lip da haƙori.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [21/04, 2:25 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣ ______________ ........ KANO    Ganin yanda ya shareta kwana biyu bai sake gwada son kwana ɗakin ba yasa yau ta saki jiki, balle ma daya shirya ya fita wajen aiki. Su uku ne kawai a gidan, ita sai ƙannensa biyu ƴammata da suka zo mata wai yini. Dan yana fita babu jimawa suka zo. Sune suka mata gyaran gidan tsaf da tsohon kwana biyu bai samu shara ba. Dama dai yaran anguwa dake ɗan shigo mata take ritsawa su mata. Ko kuma baƙin da sukazo ganin gida idan taga ƴan tagajan-tagajan ne sai ta saka su. Wasu ma danginsu ne, amma da yake su dama ƴan gidansu an musu shaidar girman kai da raina mutane bata jin ko nauyi take cewa su mata aiki koda sun girmeta. Su kuma da shegen kwaɗayi da neman gindin zama sai suyi ɗin kuwa.         Ƙannen nasa ma sai faman yamutse-yamutse take musu. Sajeeda sarkin zuciya har tace su tafi kawai, da ƙyar Khadijah ta lallaɓata. Aikin ma kinyi tayi sai Khadijan ce tayi mafi yawa a ciki. Huznah dai ana bedroom an ɓararraje ana barci, dan daga charting ta ɓingire a wajen. Ana idar da sallar Azhar Sageer ya dawo gidan. Yaji daɗin ganin babu kowa sai ƙannensa, ga kuma mutuniyar tasa na sharar barci. Hankalinsa kwance ya kaɗa su Sajeeda gida, yaje kuma ya kulle ƙofar gidan sannan ya koma ciki. Hajiya Huznah anji daɗin fanka barci yay daɗi sai taji hannu na yawo a jikinta. A firgice ta farko sukai ido huɗu kuwa da Sageer. Wani irin ɓacin rai ne ya sata yunƙurawa a masife, sai dai gogan yariga ya mata ɗaurin huhun goro da jikinsa. Ƙarfi kuma ba ɗaya ba, dan ko motsin arziƙi bata iya tayi ba, tana ji tana gani kuma ya shiga yin yanda yaso da ita batare daya nuna damuwa da hawayen da take ba. Cikin sauƙi da nuna mata mazanfa maza ne yay kiɗinsa yay rawarsa tare da more sadakinsa. Itako tana faman kuka da zaginsa, zagi kuma na rashin mutunci. Nunawa yay bai damu ba, dan ta ceci kanta data kawo mutuncinta, harga ALLAH bai kumayi tsammanin hakan ba daga gareta, musamman idan yay dubi da wayewar yan gudansu ta tsiya. Sai dai kuma mahaifinsu mutumin kirki ne, dan tsaye yake akan tarbiyyarsu babu wasa. Hakama Yazeed yana nasa ƙoƙari kasancewarsa babba kuma namiji. Yaso taimaka mata amma taƙi yarda, dan haka yay ficewarsa yabar mata ɗakin ransa fes.          Kuka bana wasa ba Huznah taci, daga ƙarshe tai kiran wayar Hajiya Basariyya. A lokacin Hajiya Basariyya na zaria tare da ƙawarta cikin wani ƙauye wajen wani malaminsu. Sosai gabanta ya faɗi jin yanda Huznah ke kuka. A rikice tace, “Ke dan ubanki minene zakisa zuciyata ta buga”.      Kasa magana Huznah tayi, sai da ta sake jan wani ƙugin kukan sannan ta ce, “Ummy fyaɗe yamin”.        “Fyaɗe kamar ya?”.   “Wlhy Ummy fyaɗe, ina barci a ɗaki kawai yazo ya haike min, nayi duk yanda zanyi na ƙwaci kaina amma na kasa. Kuma da yake shi tsinanne ne ya fita yana min dariya. Wlhy ji nake kamar na kashe shi Ummi, gashi nan ko tashi na kasa yi wata irin azaba nake ji a jikina”.      Jagwab Hajiya Basariyya ta kai zaune, kafin ta ce, “Amma dai wannan yaro anyi matsiyaci ɗan iska. Munafiki sum-sum da shi. Wlhy Huznah kin cucemu kin cuci kanki. Yanzu duk faɗi tashin da nake na ganin kin baro wannan kurkukun gidan kin koma inda daula take ki huta muma ahalinki mu huta shine kikai saken da matsiyacin yaron nan ya ƙwace abinda shine kimar taki. Yanzu ubanmi zaki kaima AA Darma ɗin to?”.      Kuka sosai Huznah ta sake fashewa da shi mai ƙarfi ma kuwa tana faɗin, “Na shiga uku Ummi, wlhy ina sonshi, bazan iya haƙurin rasashi shi ba. Ki taimakeni ALLAH ba laifina bane ba, kullum rufe masa ƙofa nake kamar yanda Aunty tace nayi shine munafikin ya dawo da rana azzalumi dan ya cutar dani. Ummi dan ALLAH ki taimakeni kada na rasashi.....” kuka ya sarƙeta. Kasa magana Hajiya Basariyya tayi, sai Maman Yaseerah ce ta amshi wayar...... _________★             Mamaki ne sosai ya kama Maanal ganin inda AS ya kawota. Wato sabon Office da aka bata kafin tafiyarta hutu, ita sam tama manta da batunsa. Office ne madaidaici da aka ƙawata aka kuma haɗa mata komai daya kamata da zata iya buƙata. Kujerar zamanta da desk mai ɗauke da computer guda ɗaya, sai visitors chairs dake gaban desk ɗin. Ta gefen damarta haɗaɗɗiyar kanta ce ta show glass da aka shirya kayan buƙata irin wanda mai zane zai buƙata...., Hatta da pensul gasu nan tari-tari kamar a shagon sai dawa. Sai daga ɗan gaba yan kujeru guda biyu suma da visitors zasu iya zama ko ita idan tana bukatar hutawa, daga bayansu akwai fright da wata ƴar kanta ƙarama an ajiye dispenser da coffee machine sai kofuna a cikin glass kanta ɗin na shan shayi dana shan ruwa. Office ɗin a cikin jerin officers na Designers Directors yake. Daga floor ɗin nasu kuma sai nasu oga kwata-kwata dake a floor ɗin ƙarshe. A tsakaninsu ma ba sai ka hau lifter ba su steps ne kawai.      Sallama AS yay mata bayan sake tayata murnar sabon office duk da a waccan ranar duk sun mata. Karan farko tai guntun murmushi tare da amsa masa. Yana fita ta sakama ƙofar key, sai kuma ta jingina a jikinta tana murmushi. Wannan fa shine DARE ƊAYA ALLAH KANYI BATURE. Tayi wata biyar kacal matsayin Junior watch designer yau gata a wanan matsayin. ALLAH kaine abin godiya, kai ke maida bawa sarki, kai ke badawa ga wanda kaso a lokacin da kaso. Kai ke sauya al'amura daga wautar tsarinmu zuwa ƙyaƙyƙyawan ikonka. Ya rabbi ka cigaba da jagorantar rayuwata bisa ikonka ba wayona ko dabarata ko tsarina ba...       Takawa ta cigaba da yi cikin office ɗin a nutse har zuwa kujerar zamanta mai laushi da ƙyau tanata sheƙi na sabunta. Sai da tai addu'a sannan ta zauna, ta lumshe idanunta tare da yin wani kalar juyi tana dariya ƙasa-ƙasa. Sai kuma ta tura kujerar jikin desk ɗin sosai ta ɗauka wayarta. Sai da ta duba taga Didi Shahidah da Amaal da Ammie duk a online sannan ta shiga group ɗinsu tai video call. Babu ko ɓata lokaci duk suka shiga yin joining. Sun san da zaman office su duka, amma basu taɓa ganinsa ba. Aiko ta shiga nuna musu komai daki-daki. Sai da aka gama murna sannan Ammie ke tuhumarta miyyasa ta dawo aiki haka da wuri, kwana tara fa kenan.        A shagwaɓe ta ce, “Ammie su Oum ne fa sukace na dawo”.      “Shi Ajwaad ɗin fa?”. Shiru tai ta kasa cewa komai. Ammie ta ce, “Humm. Maanal nidai zan baki shawara kibi mijinki, abinda ya faru ya riga ya faru, kar kiga Aban Fadeel nata baki kariyar nan kice kin samu damar bijirewa kema. Bance kada kibi umarninsa ba, amma ki ƙyautata alaƙarki da mijinki kinji”.      Sosai idanun Maanal suka cika da ƙwalla. Muryarta na rawa ta ce, “Amma Ammie shike nan komai da yay min yasha ruwa? Har yanzu fa babu wata nadama a tattare da shi. Ganin komai yake tamkar ma dolene a tsakanina da shi. Idan shi dake namiji bai sauke girman kansa ba Ammie sai ni na zubar da kaina a garesa?.”        “Ni bance ki zubar da kanki ba. Amma ki kula da duk abinda zai dinga kasancewa a tsakanin ku. Maanal kawai kinƙi yarda ne, amma Ajwaad ya jima da yin nadama, sannan yana sonki fiye da zaton kowa. Bafa dole sai namiji ya buɗe baki yace ma mace yana sonta bane zata yarda. Irin su Ajwaad a aikace suke nunawa musamman idan akai dubi da yanayin shaƙuwarku”.      Baki sosai Maanal ta tura gaba, “Ammie kawai dai baya laifi ne a wajenki”.          “Oh haka kikace? Shike nan nayi shiru. ALLAH ya daidaitaku cikin sauƙi. Ni bara naje gidan Nene zanje ALLAH ya sanya albarka. Sai a sake riƙe gaskiya a kumayi aiki tuƙuru”.      Kai ta jinjina tare da faɗin, “In sha ALLAHU Ammie”.      Ammie na fita Amaal da Shahidah da suke sauraren faɗan Ammie suka shiga tsarama Maanal abubuwa. Dan suma dai suna goyon bayan kada Maanal ta sake tayi sake har sai ya kwantar da nashi kan. A cewarsu ita Ammie bata san halin mazan zamanin nan ba ZUMA NE SAI DA WUTA. Balle ma irin su AA miskilai ga giyar kuɗi na hura su.        Kiran wayar da akai ya saka Maanal tuna a office take, haka suma su Shahidahn duk suna wajen aiki. Ai babu shiri sukai sallama akan idan sun koma gida ayi zaman. Wayar ta ɗaga, Director Mustapha ne. Bayan sun gaisa yake sanar mata akwai meeting nasu na designers zuwa 12 inji HOD. Yanda yake mata magana da girmamawa sai ma abin ya bata dariya. Itafa su rufa mata asiri suna oganninta bai kamata suna mata haka ba. Maganar aiki daban da matsayin da suke kallonta da shi yanzu. Dan haka ta ɗauki aniyar yin maganar a wajen meeting ɗin in sha ALLAHU.        Ganin akwai sauran lokaci ta fara duba ayyukanta na baya, wanda ta fara bata ƙarasa ba da wanda zatama gyara. Sosai take aikinta a nutse, cike kuma da shauƙi. Akwai aikin da suka fara fa Yaqub, basu kuma kammala ba, tana ganin kafin aje wajen meeting ɗin kuma ya kamata su kammala shi. Kan waya ta ɗauka bayan ta duba cote ɗin department ɗinsu tai kira. Bayan an ɗaga tare da gaisheta batare da tasan wanene ba ta buƙaci ganin Yaqub a office ɗinta, ba kuma tare da jiran amsa ba ta ajiye..           Cike da gulma daga can Zaharadeen ya ce, “Matar boss ce fa da kanta.”       Kusan su duka idanu suka waro, Yaqub ne kawai yay kamar ma bai jisu ba. Zaharadeen ya cigaba da faɗin, “Yaqub kai take nema, dan ALLAH idan kaje ka nema mana damar ganinta, dan ya kamata muje mu miƙa gaisuwa mu taya murna muyi ALLAH yasa alkairi ko ALLAH zaisa ta manta da abinda ya faru baya”.      Miƙewa Yaqub yayi yana mai girgiza kansa. A fili ya furta, “Oh ko kunya ku bakuji ba yanzu ko ita da kanta tace kuzo sai kuje dan neman kusanci da ita”.        “Da gudu ma kuwa. Ko tunani ka kai kaɗai zakaci arziƙin?”.    Cewar Ema.. Murmushin takaici Yaqub ya saki, batare da yace komai ba ya nufi hanyar fita abinsa ɗauke da folder ɗin daya haɗa drawing pappers ɗin daya san zata nema a wajensa. Yana gama ficewa Jameel ya ce, “Ɗan baƙin ciki, idan fa bamuyi da gaske ba guy ɗin nan sai ya kankane komai ta yanda ko kallonmu bazata ringa yi ba balle ta tuna munrayi tare anan matsayin abokan aikinta. ALLAH dai yasa ta manta da abinda ya faru baya. Ni damuwata ma randa ta kamamu muna gulmarta ni da Teemo da Hafiz”.        Caaa kowa yay yana faɗar albarkacin bakinsa. Sai dai duk suna cikin fatan ALLAH yasa Maanal ta yafe musu sudai. Daga haka suka ɗora da gulmar ashe Maanal ɗin tasan abinda ta taka akwai alaƙa tsakaninta da boss shiyyasa take musu girman kai. Gashi nan cikin ƙanƙanin lokaci tazo ta samesu ta kuma shallake abinta matsayin ogarsu. Kai kai wannan al'amari da taɓa zuciya yake..........✍️ _😀 ALLAH ya shirya yan gulma a duk inda suke🤣😂_        *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [22/04, 3:30 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣ ______________ ......A office ɗin Maanal kuwa sai da taima Yaqub magana sannan ya ɗan saki jiki suka ƙarasa aikin a ɗan gurguje saboda lokacin meeting ɗinsu yayi. A tare da shi suka fita a office ɗin. Hakan yay dai-dai kuma da sakkowar AA daga sama, da'alama daga office ya fito. Bayansa CFO ce da Bussines Director. Da alama suma wani abun zasuyi mai muhimmanci, dan elevator suke ƙoƙarin nufa. Wani irin zuba musu ido AA yayi ɗan guntun sakewar dake fuskarsa na ɓacewa. A ransa ko ayyanawa yake, (Yarinyar nan bazata fita sabgar yaron nan ba ko?). A zahiri kam yanda ya wani ɗauke kai sai ka rantse baima gansu ba. Amma ita Maanal tana gannin kallon banzar daya watsa mata na fisha ta ƙasan idon. Amma itama sai ta wani basar kamar bata gansu ba ta nufi hanyar conference room tana cigaba da wayarta. Dan magana take da Amrah data kirata suna fitowa.      Shi dai Yaqub ɗan matsawa yay ya gaishesu. CFO ce kawai ta amsa da Bussines Director. Boss yi yay kamar baiji ba ta shige elevator. Kasancewar shi Yaqub ba kallonsu yake ba bai san yaya boss ɗin yake ba. Sai da suka shige ƙofar ta rufe sannan shima ya nufi conference room ɗin.....   _________★        Rafeeq na zaune Nuwaira a jikinsa tana masa hira amma shi hankalinsa na wani tunani daban. Maganar zuwan Najma Abuja ce keta masa kai-kawo a rai. Kodai zai yi amfani da wannan damar ya sata tai masa wani aiki. Wani gefe na zuciyarsa kuma na farin ciki da fatan tabbatuwar abinda yake hasashe a tsakanin Najma ɗin da Fawzan. Dan auren wani ƙarin GARKUWA ne ga aunty Babba bayan na AA da Maanal. Tun jiya yake son yin waya da Maanal, dan yana son su tattauna wasu abubuwa masu muhimmanci sai dai bai san a yanda zata kalli al'amarin ba. Sannan alaƙarsa da ita kafin aure zai iya saka AA yaji wani abu a ransa idan yaga kiran duk da yasan har abada Ajwaad bazai kawo mummunan abu a garesu ba, amma yana da ƙyau ya kiyaye. To amma a yanzu batun Najma sai ya zaburar da shi, a ganinsa hakan wata hanya ce mai sauƙi da saƙon da yake so zai isa ga Maanal ɗin dan ita kawai yake so a wannan gaɓar tasan hakan saboda ya yarda da ita ɗari bisa ɗari, ya kuma gamsu da tarbiyyarta da soyayyar da takema ƴar uwarsa, soyayya ce irin ta ɗa da mahaifi.....        “Babie!”.   Nuwaira ta kirashi a cikin kunne cike da shagwaɓa. Kallonta yay da sauri, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya tare da sakar mata murmushi ya sake jawota jikinsa. Hancinta ya kama ya ɗan ja. “Kefa yarinyar nan shagwaɓaɓɓiya ce. Minene kuma?”.      Baki ta ɗan tura masa. “Bakai ne ka tafi tunani ba inata kiranka bama ka jina. Minene ke damunka wai? Ina lure da kai tun jiya baka da sukuni”.        Sake lakace mata hanci yayi. Tare da faɗin, “Tunaninki nake fa”.    Tai murmushi mai ƙayatarwa. Duk da tasan ba hakan bane cike da farin ciki tace, “Godiya nake Babie. ALLAH ya ƙara mana farin ciki da kwanciyar hankali”.       “Amin my angel, harma da soyayyar juna”. Ya faɗa yana ƙanƙameta a cikin jikinsa. Wata irin soyayyarta na ratsa jini da ɓargonsa. A tabbas har randa aka ɗaura masa aure da ita zuciyarsa Maanal take so, amma ganin halin da suka samu AA ya sake sakashi ɗaukar ɗamarar yaƙi da zuciyarsa akan sadaukarwarsa. Dan ya sake tabbatar da AA ya fisa buƙatar Maanal. Shine kuma ya cancanci samunta ɗin. Koda ya shigo ya samu Nuwaira a ɗakinsa matsayin mallakinsa baiyi wani yunƙuri ko tunanin zasu sami juna ta sauƙi ba, sai dai kuma labarin ya canja saboda karfin tasirin nasihar iyayensu a garesu, gashi shi kuma yana a cikin wani hali na buƙatar abokiyar rayuwa. Cikin ƙudirin samawa kansa sauƙi kawai ya yarda ya tunkareta, sai dai a lokacin da komai ya kankama sai labarin ya canja, dan tamkar ya shiga sabuwar duniya ne da zazzafar soyayyarta. Na biyu haƙurinta da biyayyarta, Nuwaira bata da kwaramniya, ga sauƙin kai da kyakkyawar fahimta. A ɗan kwanakin da suka samu tare ya fahimci hakan sai soyayyarta ta ƙara tasirantuwa a zuciyarsa. Dan haka yake baje kolin amarcinsa yanda ya kamata, itako tana nuna juriya da dattako..      Ɗaukarta yay cak ya nufi bedroom. Zizzilewa ta farayi cikin dariya tana faɗin, “My R please Aunty Rufaidah fa zanje na taya aiki a kitchen”.         “A nan ma ai aikin zakiyi, yama fi na Aunty Rufaidah lada”. Ya faɗa yana tura kai cikin ɗakin da sumbatar goshinta...... __________★        Tattaunawa ce sosai ta kasance a zaman meeting ɗin na su Maanal. Domin abubuwane masu muhimmanci da suke son kawowa na gyara a matsayinsu na artists ɗin companyn. Daga ƙarshe Director Mustapha ya sanar dasu batun da za'aje ƙasar Chaina a kansa. Wadda tun kwanaki CEO ya gabatar, ya kuma bada damar kowanne ɓangare su bada mutane biyu da zasu samu horaswar ta kwanaki goma kacal in sha ALLAHU. To zuwa yanzu kowane department na ƙoƙarin kai nasu, dan haka suma ya kamata sukai nasu ɗin. Dan haka aɗan nazari da su manyan sukayi cikin satin daya gabata, da ayyukan kowa da suka duba da ƙwazonsa sun yanke waɗanda suke ganin sun cancanci zuwa.       Aifa nan kowa ya shiga gyara zama da fatan ya kasance shine. Duk da kuwa wasu a cikinsu an taɓa zuwa dasu wasu ƙasashen akan irin hakan. Dan ba sabon abu bane duk bayan wata shida Company na irin wannan zuwa ƙaro sanin kai da kai ɗin dan ƙaruwar ilimi ga ma'aikatansu. Director Steven ne ya miƙe yay bayanin waɗanda suka samu wannan dama. Wato Maanal Habib Giro da Yaqub Nuhu. Tuni fuskokin su Zaharadeen sun canja, ko tafin da akayi ma da ƙyar suka tafa. Maanal da Yaqub suka nuna farin cikinsu. Duk da ita dai Maanal bata so haka ba. Musamman data tuna maganar da AA ya taɓa mata akan tafiyar. Sai dai tana fatan ALLAH yasa bada shi za'ai ba.      Suna tasowa a meeting ɗin yay dai-dai da lokacin break. Ransu Zaharadeen a ɓace suka wuce. Kowa naji a ransa akwai makirci a wannan tsarin. Dan a ganinsu kawai an zaɓi Maanal ne dan tana matar boss a yanzu, ita kuma ta zaɓi Yaqub saboda suna tare. To aiko lallai zasusha mamaki, dan ko zasuyi amfani da wannan damar akan Yaqub game da alaƙarsa da Maanal ɗin sai yabar Companyn nan da ƙafafunsa. Ai sun san dai boss ba mahaukaci bane ba zuciyarsa ba dutse bace zaiji kishi...        Salla kowa yay ƙoƙarin zuwa gabatarwa. Bayan an idar masu tafiya cin abinci suka tafi, masu komawa office suka koma. Harda Maanal kuwa a masu komawar, duk da yau batazo da abincin nata ba. Hankalinta kwance ta fito daga elevator tana danna waya fuskarta da murmushi dan kuwa charting take da su Aneesa. Dai-dai ta danna zata ma Zeezah vn aka zare wayar a hannunta, da sauri ta ɗago idanunta, sai ko cikin na AA dake kallon wayar alamar karanta charting ɗin yake. Hannu takai zata amshe wayar, ya janye jikinsa batare daya daina karanta hirar tasu ba.      Kamar zata saki kuka ta ce, “Amma dai haka babu ƙyau ALLAH”.    Bai tanka mata ba bai kuma daina karantawar ba, sai ma fara tafiya da yayi, binsa tayi tana jinta duk a ruɗe, dan tsokanarta su Aneesan keyi a kansa. Acewarsu har an gama cin amarcin ne ta dawo aiki. Amasar data tura musu cewar (Ai ba sai an gama a gida ba zasu cigaba da ci a office) yasa suka tasata gaba da shaƙiyanci irin na ƙawaye. Itako tana bama kowa amsa dai-dai shi. Dan tafi sakewa tai musu surutu a charting fiye da zahiri. Son amsar wayar yasa Maanal bata ankara ba har sun shigo office ɗinsa. Sai da yakai zaune a rukunin kujerun ta ƙara kai hannu zata fige wayar batare daya daina abinda yake ba ya saka mata ƙafa ta faɗo jikinsa sannan. Da sauri ta kalla inda take, aiko dai a cinyarsa take ɗare-ɗare babu ƙarya. Miƙewa tai yunƙurin yi, yasa hannunsa ya sake rungumota da ƙyau, tare da saka idanunsa cikin tsakkiyar nata da wani salon ɗage gira sama.         “Bake kika ce za'aci amarcin a office ba! Miye na pretending kuma amarsu ta ango?”. Yanda yay maganar kamar mai raɗa ya saka tsigar jikinta tashi, ga kunya na neman halakata tamkar ba tana tare da Bestyn ta dake goyata a bayansa ba ko bayan kekensa, wanda suke cin abinci a kwano ɗaya. Wanda yasha yimata wanka da mata tsarki, wanda yasha wanke mata underwears harda masu jini a jiki batare da ƙyanƙyami ba. Wanda y.....”       Knocking ƙofar da akai ne ya katse mata tunani, bama tasan ta daka tsalle ta miƙe daga jikin nasa ba gaba ɗaya. Bai hanata ba, amma ya kamo hannunta ya zaunar a gefensa gab, kafin ya danna remote ƙofar ta buɗe a hankali ta hanyar rabewa biyu. Kallo ɗaya AS yay musu ya duƙar da kansa. A haka ya ƙaraso gabansu ya ajiye basket ɗin hannunsa yana faɗin, “Sir gashi in ji driver”. Bai jira amsarsa ba ya juya ya fice, ƙofar ta koma a hankali ta rufe kanta. Ajiyar zuciya Maanal da kanta ke ƙasa ta saki. Kallonta yayi, ganin ta kauda kai gefe ya ɗan laɓe baki, sai kuma ya gyara zama ya fara fiddo kulolin da ke cikin basket ɗin wanda babu tantama yasan na gidansu ne, kuma tabbas daga Oum suke. Sai da ya gama buɗe komai ƙamshin abincin ya bulale office ɗin sannan ya juya yana kallon Maanal dake satar kallon sa shi da abincin ta gefen ido.          “Mrs Darma aikin kine wannan! Tashi ki bani abinci”.       Kallonsa ta juyo tayi, ya ɗage mata gira ɗaya. Cike da neman magana ya furta, “Kin san dai anan babu Aban naki ai balle kice bazaki yi ba”.      Sosai ta tura baki gaba. Batare da tace komai ba ta matsa kaɗan bakin kujerar ta ɗauka plate ta fara haɗa masa abincin. Idanu kawai ya zuba mata, ransa fes da kasancewarsu a hakan. Sai yanayin ke tuna masa wani lokaci acan baya daya shuɗe. Murmushi ne ya shiga ƙawata fuskarsa dan tamkar a yanzu ne komai ke faruwa. Harta kammala bai farga ba, sai da ta ɗan bubbuga spoon a plate ɗin sannan. Cike da basarwa ya haɗiye murmushinsa, batare daya ce komai ba ya gyara zama abinsa ya hau cin abincin bayan ya ɗauka wani spoon ɗin ya ƙara alamar nata.         “Nifa na ƙoshi”.     “Ɗura kike so kenan? Garama kici da arziƙi”. Tasan zai aikata kuwa. Dan haka ta ɗauka spoon ɗin kawai itama. Jujjuya abincin kawai take amma ta gagara kai lauma ko ɗaya, baice mata komai ba, face ɗibowa ya nufi bakinta da shi. Yanda yay wani kicin-kicin da fuska babu alamar wasa yasa ta amsa ɗin.        “Gulmammiya dama abinda kike so kenan”. Ya faɗa yana dungure mata kai tamkar ba shine yay maganar ba.         Ita sai abin ma ya bata dariya, amma bata dara ɗin ba ta dai yi murmushi dan ya tuna mata baya. Idan ya lallaɓata taƙi cin abinci musamman in tana fushi da shi sai ya ɗiba ya bata a baki tare da dungure mata kai sannan yace mata gulmammiya. Murmushin nata ba ƙaramin ɗaukar hankalinsa yay ba, amma yasan yana yin magana zata birkice masa, dan haka yay shiru ya cigaba da cin abinsa yana ɗiba yana bata kuma. A mamakinsu sai gashi su ci sosai abinsu. Sun kammala kenan tana gyara wajen kiran waya ya shigo masa, AS ne ya sanar masa ma'aikata fa sun taru domin masa murnar aure. Amsa ya basa da cewar suna zuwa. Daga haka ya yanke kiran.          “Oya let's go mutane na jiranmu”. Da mamaki Maanal ta bishi da kallo dan ya nufi inda rigar suit ɗinsa take, “Wai mi?”. Ta faɗa cikin sigar tambaya.       Batare daya kalleta ba yace, “Zasu tayamu murnar aure ne”.     Kasa sake cemasa komai tayi, ta ƙarasa tattare komai kawai ta maida a basket ɗin sannan ta miƙe, veil ɗinta ta gyagygyara tare da ɗaukar wayarta a inda ya ajiye sannan ta nufi ƙofa inda yake tsaye yana jiranta.........✍️            *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [22/04, 3:30 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣ ______________ .........HUZNAH         Sosai gaɓɓan jikinta ke mata ciwo, duk yanda take tunanin iya daurewa hakan ya gagara. Kuka kam taci harta godema UBANGIJI. Zagi babu kalar wanda Sageer bai sha ba a wajenta. Gashi bata sake jin motsinsa ba a gidan sai bayan magrib. Tana zaune wujiga-wujiga har yanzu bata gyara jikinta balle sauke nauyin sallolon dake a kanta ya shigo ɗakin. Kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa, batare da damuwa da hararar da take binsa da shi ba ya wuce bathroom ɗin ɗakin. Ruwa mai ɗumi ya tanada sannan ya fito, batare da Huznah data cusa kanta a ƙafafunta tana sabon kuka na takaicin ganinsa ta ankara ba taji kawai an cicciɓeta. Mutsu-mutsu ta farayi na son sauka, amma da yake ƙarfi ba ɗaya ba ko gezau ya shige bayin da ita. Tana kai masa duka da komai da fisge-fisge ya taimaka mata. Sai da ya tabbatar ruwan ya ratsa mata jiki ta samu ƴar nutsuwar da yake buƙatar ganinta a ciki sannan ya fito a binsa muryarsa babu alamar wasa ya bata umarnin yin wanka tare da gargaɗinta mintuna biyar ya bata tazo tai sallolin data tarama kanta. Idan kuma ba hakaba zata sha mamaki.       Haka kawai taji wata masifaffiyar shakkarsa, babu ɓata lokaci ta gabatar da duk abinda ya sanyata ta fito tana ɗingisa ƙafa ɗaure da towel. Duk da ta bashi dariya da tausayi duk sai ya danne, fuskarsa babu fara'a ya miƙa mata riga da hijjab, komai batace ba ta ɗauka ta sanya ta fara gabatar da salla. Sai da yaga har tayi raka'a biyun farko sannan ya fita domin zuwa massallaci shima...... ______★       Ƙarfe biyar Abah ya kirata yace ta fito su wuce. Lokacin tashi yayi, amma akwai aikin da take yi, sai dai bazata iya cema Aban haka ba, sai kawai ta tattara aikin da abinda duk zata buƙata ta tafi da su bayan ta kashe wutar office ɗin ta fice. Kai tsaye inda AS ya nuna mata zata dinga ajiye key dan masu shara da safe su gani ta ajiye. Batare da tabi takan AA ba ta fice abinta ta samu su Abah. Cike da girmamawa ta gaisheshi sannan ta shiga driver ya maida ƙofar da dama shine ya buɗe mata ya rufe. Fuskar Abah da murmushi ya danƙa mata tsarabar da yayo mata, dan shi fa har yanzu kallonta yake tamkar su Naufal a gabansa. Cike da jin daɗi tai godiya ranta fal farin ciki...          Sam AA bai san da tafiyar Maanal ba. Aiki ya masa yawa harya shiga over time ɗin nasa na tsiya. Kiran magrib ya sashi kallon ƙawataccen agogon dake a office ɗin. Ɗan tsai yay cikin tunanin Maanal data faɗo masa a rai. Sai kuma ya ɗauka waya yay kiran AS dan yasan tunda bai shigo masa sallama ba shima yana nan bai wuce ba. Ilai kuwa hakanne. Yana ɗauka daga can AA ɗin ya furta, “Zo mana”. Ya yanke kiran. Babu jimawa sosai AS ya shigo, sai da ya masa sannu da aiki kafin yace, “Gani sir”.       Batare da AA ya ɗago daga abinda yake ba ya ce, “Besty fa?”.     Sam AS bai gane kan zancen ba, dan haka ya ce, “Sir Besty kuma?”. Karan farko AA ya ɗago ido ya kallesa, sai kuma ya dafe goshi ya ɗan murza. Cike da basar da suɓutar bakin nasa ya furta, “Maanal”.          “Oh I'm sorry Sir, ai inaga tun five ta tashi”.     Jimmm AA ɗin yayi, sai kuma ya jinjina kansa batare da ya sake cewa komai ba yay masa nuni yaje. AS na gama fita AA yaja numfashi ya fesar, sai dai a zahiri baice komai ba. Saima miƙewa da yay ya nufi bedroom yay alwala. Koda ya fito tattara dukkan abinda zai buƙata yay a cikin briefcase ɗinsa, dan dolensa yay aiki a gida kam daren yau. Yana fitowa AS ya amshi kayan hannun nasa ya haɗa da nashi shima, a tare suka sauka ƙasa. Sai da suka fara salla a massallaci su ƴan tsiraru dan akwai irinsa ƴan over time sannan suka nufi gida shi da drivern sa, AS ma tashi motar ya shiga ya nufi nasu gidan.....       Lokacin da AA ya isa gida tuni Maanal ta jima da hutawa. Dan har taya Oum girki tayi kasancewar rigimar Abah ta tilasta mata komawa kan duty. Bayan sun kammala ne suka nufi ɗaki yin salla. Ana idarwa tai zaman yin karatun Alkur'ani Oum kuma na lazimi har akai isha'i sannan suka fito. Sashen Abah Oum ta tafi, hakan yasa Maanal zama ta shiga duniyar tunanin nata na fama.         Gaba ɗaya kwanakin nan hankalinta ba'a jikinta yake ba. Dan al'amarin su Mamy yayi matuƙar jijjiga mata zuciya. Dauriya kawai take tana danne komai dan kar kowa ya fahimta musamman AA da Oum. Hatta a office yau dauriya kawai take da ƙarfin hali. Dan tasan idan kowa bai fahimci halin da take ciki ba shi zai fahimta. Shiyyasa ma ta toshe duk wata hanyar kasantuwarsu a waje guda a gidan kafin yau, yayinda shi kuma ta fahimci yana fushi da ita akan hakan duk da dai yanda suka kasance yau a office kamar ya huce...         Bayan wucewar Oum zaman shurun ya isheta, gashi tana son yin waya da Didi Shahidah. Tasan kuma dole ta nemi inda zata kawaice idanun mutane kodan abinda zasu tattauna. Fitar Oum zuwa sashen Abahn ya bata damar ɗaukar novel ɗinta da glasses ta yafa ƙaramin veil a kanta batare data ɗaura ɗan kwalin atafar doguwar rigarta ba ta ɗauka ruwa da popcorn dake ajiye a dining. Compound ta fito, sai da ta gama bin ko'ina dake ƙwanyar da hasken security light da kallo sannan ta nufi hanyar inda AA ya taɓa kaita kwanaki dake da swimming pool, dan tasan can ɗin ma sharr ne da hasken tamkar rana. Shigarta wajen ya sakata lumshe idanu saboda busowar wata ni'imtacciyar iska mai ƙanshin furanni a cikin hancinta, murmushi tayi, zuciyarta na sake zumuɗin ƙarasawa gaban ruwan. Sai dai me tana ɗaga ƙafa dole ta koma ta tsaya cak, sakamakon saukar muryar Mamy cikin kunneta. Magana take a kausashe, cike kuma da bada umarni. Kai kawai Maanal ta girgiza cike da takaici zata juya dan bama ta buƙatar jin baƙaƙen maganganun da Mamyn ke faɗa akan Oum, amma mi sai taji Muryar AA a bazata yana faɗin, “Amma Mamy yanzu baƙya ganin hakan zai zama wani abu daban idan nace yarinyar nan ta dakata da zuwa Company na. A yanzu fa Maanal matata ce, a ganina ta wuce dukkan wata alfarma kuma sai iko ma da take da shi akan komai na. Kema fa gashi faɗa kike kullum akan Abah, dan na tabbata da ace baku haɗa miji da Oum ba amintarku har abada bazata taɓa rawa balle har kukai ga wannan matakin. Duk da dai daga ɓangarenki ne aka samu rashin fahimtar, dan har zuciya wlhy Mamy kina a zuciyar Oum da girma da daraja. Ni dai Mamy bazan gaji da baki haƙuri da faɗa miki gaskiya akan wannan al'amarin ba. Dan ALLAH ki ajiye makamanki akan Oum, bana son lokaci yakai ƙurewar da wani a gidan nan zai ji wani abu akan hakan, musamman sauran ƴan uwana da Abah. Sannan batun aurena da Maanal kiyi haƙuri, hakan wani hukuncine na UBANGIJI dake rubutacce a ƙaddararmu, kodan yanda abubuwa suka faru a baya, da yanda suke a yanzu yakamata mu fahimci al'amarin nan fa mai girma ne.....”          “Hakane ubana”.      Mamy ta faɗa cike da hasala da gatse kuma. Murmushi AA yayi na tsantsar damuwa. Sai kuma ya ɗan kalleta da idanunsa da suka kaɗe sosai. “Kiyi haƙuri idan kalamaina sunyi nauyi da yawa Mamy, har abada ni mai biyayya ne a gareku ku duka ukun nan. Sannan zan bama kowanneku kariya daga cutarwar ɗan uwansa.....”       “Kai ka sani kuma wannan. Na baka kafin nan kafin fara azumi kazo min da cikakken bayani akan ma'anar Maawad kamar yanda na faɗa maka, tare da dukkanin takardun kadarorin ka...”           “Mamy ki gafarceni, wlhy ban san yanda zan iya tunkarar Oum na amshi abubuwan nan a hannunta ba”.       “Okay haka kace? Toni zan tunkareta na amsa tunda ba uwata bace ba ai”.       “Mamy Please....” Ko kallonsa batai ba ta wuce fuuu. Ja baya Maanal tai ta laɓe a ɗan lungun da akai adon wajen. Dan bata buƙatar Mamyn ta ganta. Zuciyarta kuwa wani irin zafi take mata, matuƙar tausayin AA na ratsa mata ɓargon jiki. Kenan shi Mamy ta bayyana masa ainhinta, tana kuma amfani da damar tana tursasa masa yin abubuwa dan tasan yanda Oum keda muhimmanci a garesa. Murmushi ta saki mai matuƙar ciwo, sai kuma da sauri ta share hawayenta ta bar jikin bangon tamkar yanzu ne take shigowa saboda jin ƙarar taku alamar shine zai fito. Bayyanarta ya sashi tsayawa cak, itama sai ta tsaya ɗin tana kallonsa, dan duk yanda taso basarwa ta kasa hakan. Tausayinsa ne ke neman fin ƙarfin zuciyarta.        AA da ganin Maanal ɗin ya sashi jin shock wani irin tsinkewa zuciyarsa tayi, addu'a yake ALLAH yasa yarinyar nan bataji tattaunawarsa da Mamy ba. Dan bazai taɓa son hakan ta kasance ba sam. Cikin son basarwa ya shiga haɗiye nannauyan abinda ke tsaye a maƙoshinsa ya daidaita fuskarsa. Sai kuma ya cigaba da takowa a hankali har zuwa gabanta. Kayan hannunta ya ɗan zubama ido, kafin ya janye ya maida kan fuskarta. Cikin tausasa murya da ƙanƙanceta ya furta, “Daga ina?”.        “Sama”.    Ta bashi amsa. Murmushi yayi a karo na farko, tare da lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kanta. “Bakin nan dai bazai daina ma mutane baƙar magana ba ashe?”.        Samun kanta tai da ɗan sakar masa murmushin itama sai kuma ta kauda kanta gefe tana mai laɓe bakin kaɗan. Shima murmushin ya sake saki dan nata murmushin wani sanyi ya saukar masa a zuciya. A hankali kuwa ya saki ajiyar zuciyar tare da matsowa gab da ita. Matsawa tayi baya tana mai waro masa idanun kaɗan, irin na (lafiya dai?) shima sai ya bita. Danganewa tayi da bango, hakan sai ya bashi damar dafe bangon da hannu ɗaya ya mata rumfa da jikinsa. Gaba ɗaya ta jita kamar a keji, ga wani irin watsal-watsal da zuciyarta ke mata, sassanyan ƙamshin turarensa kuwa na saukar mata da kasalar jiki da gaɓɓai. Shima ɗin wani irin haurawa yaji jininsa nayi a saman kai, a hankali muryarsa cike da taushi da nauyi ya furta, “Bestie, please give me a hug mana”.          Sosai zuciyarta ta harba, duk yanda taso daurewa ta kasa, idannunta ta ɗago slowly ta sauke akansa, shima kallon nata yake, sai taga kamar idanunsa na ƙyallin hawaye, duk da tasan wannan normal ne a garesa, dan in har ma yana cikin farin ciki sosai idanun na fari tas-tas zakaga tamkar kuma an bisu da mai ne. Amma na wannan yanayin babu abinda take hangowa a cikinsu sai tsagwaron damuwa da ɓacin rai........✍️ _To bazawarin Huznah dai kazo da bidia, runguma kuma? Gaskiya wannan salon cin amanar Abah ne kawai 😂_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [23/04, 4:14 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣ ______________ ........Samun kanta tai da sakar masa sassanyan murmushi, tare da buɗe hannayenta a hankali alamar bashi damar daya buƙata.         Idan yace zuciyarsa bata nema tarwatsewa ba a wannan gaɓar yayi ƙarya, amma wannan ba lokacin tunani ko nazari bane. Duk da ya mata tsaho sosai cike da jin illahirin jinin jikinsa na narkewa ya wani irin shigewa jikin nata ya rungumeta tsam har sai da ta ɗan rumtse idannunta. Sosai tausayinsa ya shiga marmashe mata illahirin zuciya, dan kasancewar kanta kwance a ƙirjinsa tana iya jin yanda zuciyarsa ke bugawa da sauri-sauri, ga hucin numfashinsa na sauka a kunnenta da zafi-zafi. Sun kai tsahon mintuna biyar a haka, ita harma ta fara jin ƙafafunta sun mata nauyi. Sai taji shima kamar ya mata nauyin. Muryarta na wani irin komawa sanyi ƙalau ta ce, “You're sleepy?”.          Maimakon bata amsa sai ya girgiza mata kai kawai. Sai kuma ya miƙe tsaye sosai ya ɗagota itama daga ƙirjin nashi ta tsaya da ƙafafunta. Fuskarta ya kafe da sassanyan kallo, ita sai ma ya bata kunya. A hankali ta risinar da idanunta ta koma kallon yatsun ƙafarsa dake fes-fes cikin tattaunsan baƙin takalmin daya sanya. Hannu yasa ya ɗago fuskar tata ta hanyar kamo haɓarta cikin hannunsa. Maimakon ta kallesan kamar yanda yake buƙata sai ta lumshe idanun nata. Murmushi ya saki kaɗan, cike da son tsokanarta ya ɗan ranƙwafo ya dai-daita fuskar tasu numfashinsu na sauka a fuskokin juna. Cike da shauƙin yanayin nasu ya  furta, “Besty!”.           Kasa amsawa tayi, dan gaba ɗaya jinta take kamar ta nutse a cikin ƙasa. Shima fahimtar bazata amsa ɗin ba sai ya sake sakin murmushi irin mai maƙalewa a gefen bakin nan. Cikin maida muryar tasa ƙasa-ƙasa sosai tamkar mai raɗa ya ce, “An bani Hug saura kis....”       Ai baima kai ga ƙarasawa ba ta waro idanunta gaba ɗaya warrr a kansa. Sai dai kasancewarsu gab da juna ya sata maidawa kuma da sauri ta lumshe tare da janye jikinta baya tabar wajen da sauri. Dariya sosai ta bashi, amma sai baiyi ba ya saki ɗan murmushi yana miƙewa tsaye da ƙyau ya zuba duka hannayensa a cikin aljihun farin jeans ɗin wandonsa ya bita da kallo. Sai da ta zauna batare da ko waiwayensa tayi ba ta buɗe novel ɗinta ta sanya eyeglasses a idonta sannan ya shiga takawa a hankali zuwa inda taken..      ★ Ya jima tsaye a inda ta barshi yana kallonta, kafin ya tako shima a inda taken. Kujerar dake facing ɗinta ya zauna, batare da yace mata komai ba ya zuba mata idanunsa kawai hannayensa duka harɗe a ƙirjinsa. Yanda ya zuba mata idanun nasa masu kaifi ya sakata daburcewa ta daina fahimtar abinda ma ta fara karantawa. Amma a zahiri bazaka taɓa tunanin a rikicen take ba dan ta maze ƙwarai da gaske kamar bata san da shi a wajen ba. Dai-dai nan kiran Oum ya shigo wayarsa. Kasancewar ringing ɗinta na musamman ne ya saka shi dakatawa daga faɗar abinda yay niyya ma Maanal. Wayar ya ciro daga aljihu yana gyara zamansa da ƙyau. Sai dai idanun nasa har yanzu a kanta tamkar ya samu television ɗin kallo.     Cike da tsokana ya furta, “Assalamu alaikum uwargidan Abah har a ALJANNA”.      Murmushi Oum tayi daga can. Cike da jin shauƙin ƙaunar Autan nata tace, “ALLAH to ya tabbatar Autan Oum ɗinsa, sannan tare da ku Bestyn bestynsa.”      Murmushi AA yayi mai faɗi, sai kuma ya ɗan saci kallon Maanal a miskilensa ya furta, “Shike nan dai Oumna kin rama 1-1 kawai.”     Dariya sosai Oum tayi, sai kuma ta ce, “Dama zance kazo kaci abinci gamu nan zuwa tare da Abahn ku zaici abincin tare damu”.          “I'm so happy, Oum! gamu nan”. Daga haka ya yanke batare da Oum ta fahimci inda (gamu nan) ɗinsa ta dosa ba. Yana ajiye wayar ya zare book ɗin Maanal tare da ɗaukar kwalin popcorn ɗin nata da goran ruwan ya ce, “Oya let's go Oum na kira”.      Komai bata kawo a ranta ba ta miƙe kawai. A jere suka fito duk da ba wata hira suke ba. Sai da sukazo fitowa ne cike da neman magana ya gwargwaɗa mata magana a kunne. Da sauri tai gaba zata barsa saboda kunya, yayinda murmushi ya ɗan ƙawata fuskarta batare data shirya hakan ba. Shima murmushin yake yi dan haka kawai murmushin nata ya saka shi jin nishaɗi. Ai cak Abah da Oum dake fitowa daga sashensa suka tsaya. Galala Abah ya saki baki yana binsu da kallo, yayinda Oum ta gimtse dariyar dake neman suɓuce mata da ƙyar. Suna tsaye kamar gumaka AA da Maanal suka shige sashen Oum batare da su sun ma farga da su ba. Gyaran murya Oum tayi kaɗan, hakan ne yasa Abah maido da idanunsa kanta, harrarta yayi. Daƙyar ya iya gimtse dariyar tayi gaba tana faɗin, “let's go tunda gasu can.” bata jira cewarsa ba tai gaba tana murmushin data kasa riƙewa. Suna zuwa ƙofar sashen Oum Maanal ta zame tai hanyar baya ta kitchen ita adole bata son a gansu tare da AA. Bata san wanda take gudun su gansun ba sun riga sun gansu. Samun su Inte na haɗa abincin da zasu kai dining sai kawai ta shiga tayasu.          AA kam daya shige shi kaɗai dariya ma ta bashi. A ransa yace (Magulmaciya, kina so kina kaiwa kasuwa). Fawzan kawai ya samu a falon yana kallo. Zama yay kusa da shi. Fawzan ya dubesa da ƙyau, sai kuma ya ɗan matsa da fuskarsa yana shinshina shi. Harararsa AA ɗin yayi, ciki-ciki ya ce, “Miye?”. Da ƙyar Fawzan ya gimtse dariyar dake cinsa, cikin ɗaure fuska shima kamar yanda AA ɗin yayi ya ce, “Yada tsarguwa haka Malam, ka bari na gama tantancewa mana. Naji ne kana ƙamshi kamar na turaren Lilly.”       Irin ɗan waro idon nan AA ɗin yayi, ya ce, “Kai yaya Fawzan ido ka koma samin?”.      “Oh da mikake tunani? Kasan dai bazan bari aci amanar Abah ba. Kuma zanma ƙanwata garkuwa”.     Rasa ma abin cewa AA yay, sai kawai ya zubama Ya Fawzan ɗin ƙasaitattun idanunsa. Sosai Fawzan ya kwashe da dariya, dan yasan ya gama kaishi maƙura kenan. Ai idan kaga Auta ya rasa abin faɗa to yakai maƙura kenan...      A haka Oum da Abah suka shigo suka samesu. Gaishesu sukayi, suka amsa Oum na faɗin, “A'a ina Baby na kuma?”.      Fawzan ne ya bata amsa da, “Ai tunda na shigo ban gantaba Oum, maybe tana sama ko?”.     Kai Oum ta jinjina tana jiran AA ya bada amsa, amma ya basar abinsa tamkarma baijisu ba. Sosai shima Abah ke satar kallon AA ta gefen ido ransa fal mamakin, dai-dai nan Maanal da su Inte suka fito a kitchen. Dariya taso kama Oum, amma ta danne da ƙyar idonta akan Maanal ta ce, “Oh ashe kina kitchen Auta”.       Kai Maanal ɗin ta jinjina tana murmushi da satar kallon AA daketa latsa waya kanshi kwance a kafaɗar Fawzan hankalinsa kwance like baima san mike faruwa ba. Juyawa tai tana gaida Abah dayay Zuru yana kallonsu su duka. A ransa ko faɗi yake (Aiko zakuci ƙaniyarku ku duka) a zahiri kam amsawa yay cike da kulawa. Daga haka suka ɗunguma dining cin abinci.....                A nutse suke cin abincin, yayinda Oum da Abah ke ɗan hira Fawzan kuma da Maanal. AA kam hankalinsa nakan waya komi yake oho masa. Abincin ma bawani ya maida hankali bane a cinsa. Wayar Oum ta zare daga hannun nasa, yako kalleta a shagwaɓe. Harararsa tayi tare da nuna masa abinci tana faɗin, “Ni tunda ka tashi ciwon nan kake neman maida abinci abokin gabarka Auta. Oya maza yanzu naga plate ɗin nan, in ba haka ba ɗura zan maka”.        Dariya Fawzan yayi, Maanal ma ta kasa riƙe nata murmushin saboda ganin yanda AA ɗin yay da fuska. A dai-dai nan Mamy ta shigo sashen da sallama. Gaisheta Fawzan yayi bayan duk sun amsa mata sallama, tare da faɗin, “Naje sashen yaran nan sukace kina wanka”.      Cikin danne takaici Mamy ta ce, “Eh sun faɗa min”. Ledar hannunta ta ajiye a gaban AA da tunda ta shigo ya maida hankalinsa ga cin abincinsa. Maanal kam sai satar kallon Mamyn take bayan ta gaisheta itama. Ajiye ledar ya saka AA ɗagowa ya kalleta a karo na farko, hakama su Abah kallon ledar suke. Murmushi ta ƙawata fuskarta da shi, tare da juyawa tana kallon Oum. “Bara na aiki ɗanki gidan Aunty tunda dai yaji sauƙi, na manta shaf har drivers ɗin gidan sun tafi gashi da sassafe zasu wuce lagos”.        Fuskar Oum babu wani damuwa ta ce, “Eh ya kamata kam a kai mata su a daren nan. Auta sai ka maida hankali ka gama ko kar dare yayi, duk da dai kai ba tsoron fitar daren kake ba”.      Kansa kawai ya jinjina batare da yayi magana ba. Dan shi yasan babu wani saƙo. Mamyn ce ta kafa masa sharaɗin zuwa yaga Nuratu ya kuma bata kayan da zata bashi yace inji shi wai Ramadan basket. Zama Mamyn tayi suka cigaba da hira da Oum da Abah, sai kawai AA ɗin ya miƙe badan ya kammala cin abincin ba, dan zuciyarsa gaba ɗaya jinta yake a ƙuntace, amma miƙewar da zai yi suka haɗa ido da Maanal sai wata dabara ta faɗo masa. Guntun murmushin iya shege yayi, cike da shagwaɓa ya dubi Abah. “Abah dan ALLAH ka bani aron ƴarka ta rakani tsoro nake ji”.       Atare gaba ɗayansu suka ɗago suna kallonsa, ya sake narke fuska kamar zai yi kuka. “ALLAH Abah da gaske nake”. Ai kasa daurewa Fawzan da Oum sukai suka sanya dariya. Abah kansa da ƙyar yake iya danne tasa dake neman kufcewa. Maanal kam baki da hanci tama saki tana kallonsa, yayinda Mamy ta cika tayi fam fa takaici har hakan ya kasa ɓoyuwa a fuskarta. Cikin dariya Oum ta ce, “Please Abansu a taimaka mana, ai bazasu daɗe ba yanzu zasu dawo”. Fawzan ma yace, “Abah ayi haƙuri ta rakashi kada yay mana kuka ko kura ta cinyeshi a hanya dan tsoro. Kasan Besty da Besty duk tsanani tare suke zuwa aika”.      Kai Abah ya girgiza, tare da faɗin, “ALLAH ya shiryeka Ajwaad. Jiba yanda ka wani ɓata fuska like zakama mutane kuka. Shike nan kuje, amma ina nan ina jiran dawowarku, idan kuka daɗe kwanakin zan ƙara”.          “Thanks You sweet Abah”.      AA ya faɗa a hankali. Nan ma kan Aban ya girgiza kawai, yayinda Oum ke faɗin, “Baby tashi ku tafi kinji”. Ji Maanal tayi kamar ta nutse dan kunya. Duk da kuwa a shekarun baya hakan ba komai bane a tsakaninsu. Dan ko tana gidansu aka aikesa zaije yace tazo ta rakashi kida cikin anguwa ne. Haka itama idan aka aiketa ko yana gida agaban su Abah ɗin zatazo tace masa (Besty zoka rakani aika) amma sai yau gashi tana jin hakan kamar sabon abu. Sarai AA na lure da mugun kallon da Mamy ke masa, amma ya fuske abinsa, sai ma nufar sama da yay ganin Maanal na niyyar warware ƙaramin veil ɗin kanta alamar da shi zatama fita take nufi. Da kallo duk suka bisa, Fawzan kuwa na masa tsokanar daya saba da kirari. Babu jimawa ya dawo da mayafin da yafi na kan nata da ke kamar na yara dan na Abaya ne. Wanda ya miƙa mata ɗin ta kalla, sai kuma ta ɗan tura baki gaba. Wancan ta cire ta amshi na hannun nata ta sanya, zata nufi saman itama ta maida Oum tace ta kawo kuje kawai kar dare yayi. Oum ɗin ta ba, shi kuma ya ɗauka ledar Mamy da takaici ke neman bombing mata zuciya suka fice..........✍️ _Abah da kasan kura kaba ajiyar nama da baka bayar ba😂🥱_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [23/04, 4:14 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣ ______________ .......Wata Nurse da Sageer ya kira anan anguwarsu na tsaka da duba Huznah kiran Hajiya Basariyya ya shigo wayarta. Kasancewar yana a kusa da ita shi ya kai hannu ya ɗauka dan ita ana mata ƙarin ruwa ne. Shine ya fara yin sallama, dan haka Hajiya Basariyya tai ɗib daga ƙoƙarin maganar da tai niyyar yi. Da ƙyar ta iya amsa masa gaisuwar da yake mata. Kafin ya ƙara cewa wani abu ta yanke kiran. Murmushi kawai yayi baice komai ba. A ransa kam dariyar ƙeta yake da faɗin (Mama ai sai kuma haƙuri, ƙiyayya ta ƙare tunda ruwa ya gauraya da jini). A zahiri kam murmushi yayi kawai....        Wani irin malolon baƙin ciki ne ya sake tokare zuciyar Hajiya Basariyya. Dan ita kam abin ya zame mata goma da goma. Tana yaƙin ganin ta koma ɗakinta kafin Hajiya Yaya ta koma, Daddy kuma ya saki Asiya a randa ta koma dan alwashine sai tayi maganin Asiya a wannan gaɓar ga kuma batun Huznah da shima suketa faɗi tashin ganin wannan auren ya rabe tazo ta auri AA sun fiddo waccan shegiyar agolan daga ciki mai ƙwacen saurayi. Ita kuma sakaran tayi sakaci wannan matsiyacin ya kwace ɗan mutuncin. Zaune takai a bakin gadon ɗakin da take zaune a gidan yayanta, ɗakin da saida akai uban rikici matansa suka bari ta zauna duk da kuwa ɗakin baƙi ne. Kayayyakin data amso a Zaria tare da Maman Yaseerah take bi da kallo. Haɗi ne sosai tayoma mutane guda biyar. Daddy, Asiya, Hajiya Yaya, sai mijin Huznah da AA. Kuma duk ana son ta aiwatar da su daga nan zuwa gobe, shiyyasa ma tai kiran Huznah dan taji yaya za'ai nata ya iso a goben itama ta aiwatar, ko Sageer na yawo da ubansa ko sai ya saketa da hannunsa. Dan sunan maganin KANWA UWAR GAMI. Amma shine tantirin ya ɗauka mata waya.. Bumm!! Bumm!!! Bumm!!! Bugun ƙofar ɗakin da take aka shiga yi da masifar ƙarfi, a zabure ta miƙe tana yayimar kayan ta tura ƙasan gado, kafin ta mirza idonta ta nufi ƙofa kamar mai barci. Dan bata raba ɗayan biyu yayanta ne matansa sunkai ƙararta saboda yau ta zagesu tas wai suna saka mata nama biyu a abinci, duk naman dake gidan saboda an rainata ace biyu ne kawai kasonta...         Tana gama buɗe ƙofar wani kakkauran mari ya ratsa mata kumatu. Da bala'in sauri da rawar jiki ta dafe fuskar da hannaye biyu gaba ɗaya. Bai dubi girman shekarunta ba ya sake wanketa dana biyu. Shi dama mutum ne mai zafi sosai. Ai yanzu kam ihu ta ƙwala dan azaba ta koma cikin ɗakin a guje. Bayanta yabi, ta maƙure jikin bango tana hawayen azaba a matuƙar gigice. Cikin wata irin tsawa mai kaɗa hanji ya ce, “Ina kukaje yau dan ubanki?”.        Hawaye na ziraro mata ta ce, “Babu inda naje fa yaya, matanka sun haɗani dakai saboda su munafukai ne. Wankin kai da kitso fa naje kuma na gaya maka ka bani kuɗin da kanka”.      “To mara mutunci, aiba maraina wayon naki bane ba ni da idona na ganki tare da Alhaji Usman a Zaria. Ko zakice min kitson acan akeyi?”.      Sosai jikinta ya fara rawa na haƙiƙa kam yanzu, zuciyarta kamar zata faɗo cikin in-ina tace, “Yaya Zaria kuma?..”       “Oh ƙarya nai miki kenan? Wlhy Basariyya ki shiga hankalinki a gidan nan. Wato har yanzu baki daina biye-biyen bokayeba ko? Shike nan karki fasa ki cigaba da yi, ki kuma haɗa inaki-inaki gobe kawu na Katsina zaizo ku tafi tare. Ki koma can wajensa dan ni bazan iya ba...”      Wani irin gigitaccen ihu ta sanya tana roƙonsa ya taimaketa bazata iya zama gidan kawun nasu ba. Ko kallonta baiyi ba ya fice abinsa. Tashin hankali matuƙa Hajiya Basariyya ta shiga a wannan dare. Dan wlhy bazata iya zama gidan kawu Manu ba. A ƙauye yake bama cikin birnin katsinar ba, ita wlhy ko ruwan gidan bata iya sha idan sukaje gaisheshi na yini ɗaya saboda kiwon dabbobinsa na tsiya. Gashi masifaffe hakama matarsa, kuma su duka ƴan uwansu ne dan auren zuminci ne shida matar tasa. Tun babansu na da rai ake fama da shi ya baro ƙauyen amma yaƙi. Mahaifinsu kansa tsoronsa yake ji balle su, dan mutum ne azababbe na bugawa a kalanda, ga tsauri dan komai na gidansa da doka akeyinsa. Kuka sosai taci, daga ƙarshe ta yanke shawarar yin asubanci ta gudu. ALLAH gara ta koma gidan mijinta duk ma bala'in da za'ai ayi bazata fito ba koda Daddy zai daketa kuwa. Kayanta ta shiga haɗawa, tsaf ta kammala ta ajiye komai a ƙofar ɗakin, sauran kuma ta ajiyesu akan daga baya zata turo su Madeena yaranta su ɗaukar mata. Ko barcin kirki kuwa batayi ba, huɗu na bugawa zabar ta miƙe dama ba wani barcin kirki tai ba, a gurguje ta shiga bayi ta kimtsa ta fito, ta saɓi jakarta tana murmushin nasara, sai dai tana murɗa handle ɗin ƙofar taji gam, hakan na nufin an kulleta ta baya kenan. Ai jitai gaba ɗaya ta wani irin gigicewa, bama tasan ta zube a wajen ba ta fashe da kukan takaici, dan ta tabbatar yayanta ne ya rufeta tun fitar jiyan da yayi.......      🤣🥱Ba abun faɗa _________★         Sun fito a jere Maanal na faɗin, “Kai dai ka canja hali ALLAH”. Cikin ƙunƙuni take maganar, amma hakan bai hana AA ɗin jinta ba saboda ƙarfin ji da ALLAH ya bashi. Murmushi yay kawai, sai kuma ƙasa-ƙasa shima yace, “Inba tsoro ba a fito fili a faɗa mana”. Sarai itama Maanal ɗin ta jishi, sai dai bata tanka ba saboda isowarsu wajen motarsa. A dai-dai nan kuma Saheeba ta fito daga sashen Mamy, taje wajenta su Haule suka sanar mata tana sashen Oum. Sai ga Nibras itama ta fito daga sashenta, taci kwalliya abinta sai baza ƙamshi take kamar wadda zata fita. Itama dai sashen Oum zataje, kuma wannan kwalliya duk ta AA ce. A tare duk suka tsaya cak suna binsu da kallo, har Maanal ta shiga mota AA daya buɗe mata ya maida ya rufe sannan ya zaga mazauninsa, sai dai shima kafin ya buɗe da kansa Maanal ta buɗe masa ta ciki kamar yanda suke yi a da. Kallonta yay fuskarsa da murmushi mai sanyi, itama ta masa murmushin tana kauda kanta dan su duka zukatansu suna tariyo musu baya ne. A hankali ya baya mai gadi ya buɗe masa gate suka fice.        Daga zuciyar Nibras har ta Saheeba tamkar zata kama da wuta ne. Cikin takaici da wani irin zazzafan kishi Nibras ta ce, “Wannan mayyar yarinyar sai nayi maganinta”.         “Haɗa dani nan Nibras dan na tsaneta”. Saheeba ta faɗa itama a zafafe. Da sauri Nibras ta kalleta dan ita bata san nata zancen ya fito fili bane ba. Kai Saheeba ta jinjina mata batare da sanin manufar Nibras ɗin na tsanar Maanal ɗin ba. Ita kuma Nibras tasan dalilin Saheeban bazai wuce taya ƙanwarta kishi ba. Amma saboda takaicin da take ciki sai ta cigaba da faɗin, “To wai ina zasuje a wannan daren? Nine fa?”.       Wata ƴar dariyar takaici Saheeba tayi, “Kin san tunda tarewa ta gagareta zatabi duk wata hanya ne yanzu na son ganin taja ra'ayinsa, balle an saba da bin maza a waje”.           “Tabbas kumafa hakane. Shegiya mai zuciyar karnuka, mutum yace baya sonki amma ina, inba shashashar amarya ba mara muhimmanci wa ake kawowa a ajiye sashen surukai gana miji”. Nibras ta faɗa zuciyarta na mata raɗaɗi.      Dariya sosai Saheeba keyi, ranta fes ta ce, “Ai Abah ne maganin ƴar iska, uwarta na murna bokanta ya iya aiki an mannota gidan da tsiya-tsiya shiko ya harba musu tsiya, Kinga ɗan maganin da aka ɗan cuccusa dan matse can duk ya sane. Ai wlhy sai mun dage munci ubanta a gidan nan ta yanda ko ruwa bazata iya sha ba sai a ɓoye, da ƙafafunta zata gudu ne”.          Hannu Nibras ta bama Saheeba suka tafa, dan a ganinta ai gara su haɗa hannu da Saheebar su kori Maanal ɗin ita kuma sai tai yaƙin hana shigowar ƙanwar Saheebar ta bayan fage. Aiko a take ta bada goyon baya ɗari bisa ɗari. Sai da suka gama shirya mugunnyarsu sannan suka nufi sashen Oum ɗin. Acewarsu gara suje su zauna suga dawowarsu...      A hankali AA ke murza steering tamkar baya so, yayinda Maanal tai shiru lafe a cikin kujera. Daga gani kasan duniyar tunani duk suka faɗa. Cikin son kauda yanayin AA yay ɗan gyaran murya. Idannunta dake lumshe ta buɗe ta kallesa, shima ɗan kallon nata yay fisha sai kuma ya maida ga hanya. So yake su dawo kamar da, amma yasan yaƙine babba a gareshi, dan haka maimakon zuwa mata kai tsaye zaibi wasu hanyoyin yin hakan. Muryarsa a tausashe ya furta, “Yaushe kika fara karatun novels? Bayan nasan haushi kike ji idan kikaga inayi ma”.         Ɗan jimm Maanal tayi kamar bata jisa ba, har sai da ya ɗan kalleta. Ƙin kallonsa tayi ita, a taƙaice ta ce, “Kawai na tsinta kaina ne a karatun batare da wani dalili ba”.      Murmushi ne yaso suɓuce masa, amma sai baiyi ba a bayyane ya tsaya masa iyakar cikin ƙirji. Zamansa ya ɗan muskuta da sake damƙe steering da ƙyau ya tsaya a danja data tsaida su, sai kuma ya koma ya jingina bayansa da kujerar ya juya yana kallonta. “Zuwa yanzu books nawa kika karanta?”.          Kaɗan ta ɗan kallesa, cikin yin warrr da idannunta ta ce, “Suna da ɗan yawa fa. Damma Ammie na hanani ne”.      “Ammie bata san karatun novels da daɗi bane shiyyasa. Kinga ni akwai wani book da nake nema saboda labarinsa da aka ɗan fara bani amma har yanzu ban samu ba, koda yake busy na ne ya hanani zuwa manyan books store na duba”.      Yanzu kam muryar Maanal a sake ta kuma juyo tana kallonsa da ƙyau ta ce, “wanne ne?”.     Sai da ya tada motar suka cigaba da tafiya saboda danja ta sake su sannan ya bata amsa. Murmushi tayi mai faɗi sosai har haƙwaranta na bayyana ta ce, “Hum'um kaga nikam na jima da karanta shi, dan tun ina shekarar ƙarshe a makaranta. Ina zaton ma kamar ina da copy ɗinsa yayi daɗi kam ba ƙarya”.       “Woow da gaske Besty?”.    “ALLAH kuwa bari zan duba maka, sai dai inaga yana cikin kayana da za'a kawo daga Kaduna”.          Dai-dai nan yay parking gaban wani baƙin gate madaidaici yana bata amsa, gidan dai daga waje ba wani babba bane, dan kamar gidajen street ɗin ma duk sun fishi girma da ƙyau. Anan wajen gate ɗin ya kashe motar bayan yayi horn, wani ƙyamushashen mutum ya leƙo, alama AA ya masa da hannu na yazo. Bayan ya kunna fitilar cikin motar ta yanda zai ganshi da ƙyau kada ya tsorata. Aiko sai da ya leƙo daga nesa yaga wanene sannan ya ƙaraso yana famar washe baki. Cike da girmamawa ya shiga gaida AA ɗin, amsa masa yay shima da kulawa, kafin yace ya ɗan kira masa yarinyar gidan nan. Nanma da girmamawa mutum ya amsa masa, daga gani dai kasan maigadi ne. Maanal dai na jinsu, dan tunda ta amsa gaisuwar da mutumin yay mata ta ɗauke kanta gefe. Fitilar AA ya kashe, sai kuma ya ɗakko tab.. ɗinsa ya shiga dannawa, miƙama Maanal tab ɗin yay yana faɗin, “Kinga list ɗin novels ɗin da nake nema idan na samu lokaci na karanta su”.     Amsar tab ɗin tayi, ta shiga duba list ɗin, cikin manta dawama take tare ta ɗan karkato tana nuna masa wanda ta karanta a ciki da wanda itama take nema ta karanta. Shima karkarowar yayi sosai har jikinsu na haɗuwa, ta shagala a nuna masa da yimasa bayani har ya ɗaura hannunsa a kafaɗarta ya sake kwantota a jikin nasa da ƙyau batare data farga ba, sai ma sake lafewa tayi sosai abinta tana zuba zance, dama can ta fishi magana, yanayine kawai ya maidata miskilar ƙarfi da yaji. Shi ko idan kaga ya saki jiki kamar haka yana magana to lallai tare yake da ita, dan sai kaga ma kamar ba AA Darma sarkin haɗe fuska da jefa magana ɗaɗɗaya ba da ƙyar. Sun shagala a hirarsu dake fita ƙasa-ƙasa dan ko ita Maanal ɗin da maganarta tafi yawa bawani tanayi zuuu bane ba, koda a cikin motar kake ma ba lallai ace ka jisu yanda ya kamata ba. Balle shi dake bata amsa kamar mai raɗa. Glass ɗin motar tinted ne, dan haka Nuratu data fito cikin matsananciyar kwalliya tana zuba wani shegen ƙamshin mayataccen turaren magani da babarta ta zazzage mata kanta tsaye ta nufi gefen mai zaman banzar fiskarta kamar ta yage dan murmushi. Wai itace yau Ya AA yazo wajenta hira, kai ita kam tafi kowa sa'a a duniya yau ɗin nan. Ta tabbata harta mutu bazata manta da wannan rana ba a tarihin rayuwarta. Sai da taja numfashi ta fesar tare da sake dai-daita kanta da ƙyau, dan babarta taja mata kunne matuƙa akan ta nutsu kada taje tana wannan rawan kan tunda tasan halinsa dai sarai. Sai da ta tabbatar ta samu irin nutsuwar da take buƙata kafin ta ɗaura hannunta a handle ɗin motar ta buɗe tana faɗin, “Assalamu aikum Yayan....” sauran maganar ya maƙale a maƙoshinta sakamakon saukar idannunta akan Maanal dake kwance a kafaɗar AA suna kallon abu a tab...........✍️ _😂😂Ni dai Nurry ƙawata ce bani da damar cewa wani abu anan🥱🤣🤣🏃🏃🏃_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [24/04, 5:24 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣7️⃣ ______________ ........Nurry tamkar wadda ta suma haka ta kasance, yayinda AA da maaanal suka ɗago idanu a tare suna kallonta kawai. Ta kuma ƙi tashi daga jikinsa sai ma ƙara gyara kanta da tayi. Jitai zuciyarta ta mata wani irin nauyi da ganin Nurry ɗin, dan tabbas da tasan gidan su yarinyar nan zasu zo da bazata biyo shi ba. Amma a zahiri babu ko ɗigon damuwa a fuskar tata, sai ma wani irin murmushi data sakarma Nuratun a karo na farko ta furta, “Hy” a hankali.        Sai a lokacin Nuratu ta farfaɗo, a hankali ta zame hannunta dake ɗan rawa daga jikin murfin ta miƙe tsaye gaba ɗaya. Cikin kaushin murya AA ya ce, “K! Baki iya gaisuwa bane?”. Sosai muryar tasa ta ratsa mata zuciya, sanin halinsa na rashin ɗaukar raini ya sakata sake duƙowa dole batare data yarda ta sake kallonsu ba muryarta na ɗan rawa kamar mai shirin fashewa da kuka saboda kishi ta furta, “Kayi hari Yaya ina yini”. Maimakon amsawa sai yaja siririn tsaki kawai. Maanal dai tama maida hankalinta ga tab ɗin gaba ɗaya tamkar bata san mi sukeyi ba. Maanal ɗin ya nuna mata, cikin harara ya ce, “Ita kin gaisheta ne”. Sosai hawayen baƙin ciki suka ciko idanun Nuratu, cikin matuƙar raɗaɗi da jin ƙunar zuciya ta ɗan kalla Maanal ɗin ta ce, “Ina yini”.        Tsabar wulaƙanci yatsu biyu Maanal ta ɗaga mata, batare data kalleta ba ta ce, “Kina lafiya?”. Wata shegiyar ashariya Nuratu ta shiga mulmulawa Maanal ɗin a zuciya, a zahiri kam dole ta amsa. AA da bai sake ko kallonta ba juyawa yay sit ɗin baya ya ɗakko ledar da Mamy ta bashi. Ɗan kwantowa yay ta jikin Maanal sosai ya mika mata ledar yana faɗin, “Kiba mamanku inji Mamy”.       Sake sumewar takaici Nuratu tayi yanzu ma, har sai da AA ɗin ya mata ƴar tsawa da faɗin, “Wai tunanin uwar mi kike”. Firgigit ta amshi ledar zuciyarta na hautsinawa. Da kansa ya jawo murfin ƙofar kamar a fusace ya rufe. Dole taja da baya da sauri gudun bugeta da murfin. Shi ko ko'a kwalar rigarsa yayma motar key yay reverse batare daya ko sake kallon inda take ba ya bar wajen...       Gaba ɗaya Nuratu ta zube a wajen ita da ledar, wani irin kukan baƙin ciki irin mai babbake zuciyar nan a lokaci guda ta saki da iya ƙarfinta. Aiko da gudu mai gadinsu dana maƙwaftansu suka fito suna tambayarta lafiya. Amma bata ko kallesu ba. Maigadin maƙwaftansu yace, “Kodai mugu ne yazo wajenta a sanar da securitys ɗin shigowa?”. Kai maigadinsu ya girgiza masa, “A'a nasanshi, ɗan uwansu ne ma sai dai idan wani abunne ya faru. Kaga tsaya min a wajenta bara na sanarma su Hajiya.” baima jira amsar shi ba ya shige gidan. Babu jimawa kuwa suka dawo da Hajiya, basu kowa bane face Maman Nuratun da mariƙiyarta, dan jiya Maman nasu tazo daga Kano batare da ko sanin Mamyn ba. Rufuwa sukai a kanta da tambaya cikin tashin hankali. Ganin bazata basu amsa ba suka kamata zuwa ciki, maigadi ya bisu da ledar (Ramadan basket🤣).       Tambayar duniya su Hajiya Turai sunma Nuratu dake kuka kamar wadda ake yankawa amma taƙi basu amsa. Sai da mamanta ta balbaleta da masifa sannan cikin kuka ta sanar musu komai. Suma duk shiru sukayi cikin tsananin ɓacin rai. Musamman ma mamansu. Hajiya Turai ta ce, “Amma dai Kamila bata ƙyauta ba, ni da mukai waya kinga ai tace min zaizo ne wajen Nuratun su ɗan zanta ya kuma bata hasaffin azumi da samari ke ɗan bama ƴammata a yanzu. Shine zasu bari ya taho da wata kuma?”.       Ɓacin rai ya hana Maman su Nuratun iya cewa komai. Cikin fushi ta fisga waya da nufin kiran Mamyn Hajiya Turai ta riƙe mata hannu. “Mi zakiyi?”.        Rai ɓace ta ce, “Kiranta mana yaya Turai, banda rainin hankali tasan har yanzu bata da power ɗin tanƙwasa ɗanta zata saka mutane yin asara a banza yazo yana wulaƙanta mana yarinya”.           “Toke banda abinki keda bata san kina garin ba kuma. Ki barni kawai da ita. Dan ni ba Kamila zanmawa yarinyar zan wulaƙanta. Sai na sakata nadamar dawowa rayuwar ahalin Darma. Shi kansa Ajwaad ɗin zan koya masa hankali, dan banga mai taɓa min Nurry yay barci lafiya ba koda kece da kika haifeta. Dan ni ba yayar uba bace kawai uwa ce”.      Sosai zuciyar Maman su Nuratu tai mata sanyi, shiyyasa take matuƙar son Hajiya Turai. Dan akwai mutunci da ƙaunar juna sosai a tsakaninsu tamkar ba yayar mijinta ba. Kai a kaf dangin uban su Saheeban da Hajiya Turai kawai suke ɗasawa, ba kuma komai ya kawo hakan ba sai halinsu ne da yazo ɗaya. Sannan Nuratun tun daga yaye Hajiya Turai ta ɗauketa ta riƙe kasancewar ita har yanzu ALLAH bai bata haihuwa ba, mijin ma ya jima da rasuwa shiyyasa suka baro Lagos inda suke zaune da suka dawo nan Abuja. Sai dai da yake tana bussines koda yaushe ƙafarta na hanyar lagos ɗin da Dubai da Chaina. Shiyyasa Nuratun ke zuba tsiyarta yanda take so a garin na Abuja, dan ƙazamin gata Hajiya Turai ke mata, sannan duk abinda ta nema saita mata shi. Wannan yasa take jinta a babbar yarinya ɗiyar manyan mata masu kuɗin Abuja. Dan ubansu dai bawani kuɗin arziƙi ne da shi ba, hasalima da bazar Hajiya Turai ɗin yake rawa shima....          Hajiya Turai data raka Nuratu ɗaki tace ta kwanta tana fitowa ta tashi, wayarta ta ɗauka tai kiran Sille. Bugu biyu kuwa ya ɗauka. Kamar yanda ya saba cike da yaudara ya shiga yimata kirari da fasa mata kai. “Kaga Sille yanzu ba lokacin kirari bane ba tsaya kaji”. Nuratu ta faɗa muryarta a shaƙe. Ɗan ɓoyayyen murmushi yayi daga can, a zahiri kam murya a dake kamar bai san komai ba ya ce, “Ina jinki uwar ɗakina mike faruwa? Waya taɓa min ke yaga fushin maza dan walle ina iya tada Abuja harda fadar shugaban ƙasa”.      Murmushi tayi a karo na farko, shi yasa take matuƙar ji da Sille a rayuwarta, take kuma taɓa duk wanda taso hankalinta kwance dan shine garkuwar ta. Tasha sakashi ya nakasta mata duk wanda ya nuna mata yatsa a garin Abuja wallau namiji ko mace. Numfashi ta fesar mai raɗaɗi, kafin ta shiga faɗin, “Aiki nake so ai min akan jakar yarinyar can da tama AA ɗina asiri ta auresa”.      “Angama uwar ɗaki. Ƙafafu za'a cire mata ko hannaye ko fuskar za'aima ɓalli-ɓalli irin wanda kikama Huznah take kowama”.       Dariya Nuratu ta kwashe da shi, dan fuskar Huznah ɗin ce ta faɗo mata arai. Ta ce, “Kai Sille kai duniya ne, daɗina dakai baka da mantuwa sam. Ita wannan ai ta wuce ɓalli-ɓallin yarbawa, dan zunubinta mai yawan gaske ne. Zan turo maka abinda nake so ai mata. Kuma a satin bikina bayan salla zaka mata hakan, dan ina son aci shagalin bikina tana asibiti kwance rai a hannun ALLAH dan uban ubanta”.        “An gama babbar yarinya, kune Abuja kune kuma masu riƙe da ƙasar gaba ɗaya, dan masu mulkinta a tafin hannunku suke tunda kullum tsaye suke a gabanku haihuwar tsoffinsu”.      Sosai Nuratu ta sanya dariya harda kwanciya, cike da jin takaicinta ya ragu ta ce, “Zakaga saƙo a lalitarka Sille”. Daga haka sukai sallama ta yanke kiran.....      Daga can dariya Sille ya kece da ita, sai kuma ya ƙara gudun motarsa mara fasali ya cigaba da bin bayan su AA dake tafiya a hankali kamar wanda baya son isa gida. Tun fitowar su AA daga gida yake biye da su har nan gidan su Nuratu, akan idonsa komai ya faru sai dai baya jinsu kasancewar can nesa yay parking dan kar AA ya lura da shi. Dan tun Mamy na waya da Hajiya Turai cewar ga AA ɗin nan zuwa wajen Nuratu Haule ta tura masa saƙo, shine yazo ƙofa gidan ya tsaya, a zatonsa AA ɗin ne kawai zai fito, amma sai yaga kamar shi da wani ne a motar, shiyyasa ya fasa aikata abinda yay niyya ya shiga binsa a baya har kofar gidan su Nuratun dan yana son ganin shi da wanene. Bai samu ganin ba tunda basu fita a motar ba, sai yanzu da Nuratun ke sanar masa. Dan haka yaji wani kalar karsashin abinda yake shiryama ransa. Yau fa in har bai kashe AA da Maanal ba to sai ya raunata musu wani sashe na jikinsu kuwa....     Tofa munga idi🏃😳.    Sannu a hankali AA ya gangara gefen hanya yay parking, dan tunda suka baro gidan su Nuratu Maanal tai masa ɗif, tama ajiye tab ɗin ta kauda kanta gefe fiskarta a haɗe. Hannunta ɗaya dake ajiye a saman cinyarta ya kamo cikin nashi, ɗayan kuwa ta tallafe haɓarta tana kallon waje. Yanzu ɗin ma batako motsa ba balle ta juyo ta kallesa, hakan ya sake tabbatar masa fushi take yi. Lips ɗinsa ya ɗan ciza kaɗan, sai kuma ya matso kusa da ita gab yana sake rumtse hannun nata cikin hannayensa biyu gaba ɗaya. Da wata irin murya mai taushi da fitar sauti can ƙasan maƙoshi ya furta, “Besty!”.       Ƙin amsawa tai yanzu ma, sai ya sake matso jikinta sosai, har buɗaɗɗen ƙirjinsa na kwanciya a kafaɗarta. Hannunsa ɗaya yasa ya kamo furkarta da shi, yana ƙoƙarin juyota inda yake. Amma sai ƙoƙarin hana hakan takeyi ita kuma. Bai barta ba har sai da ya juyo da itan a yanda yake so. Sai ta lumshe idanunta kawai. Guntun murmushin da ya tsaya masa a iya lips ya ɗan saki. Cikin sake sanyaya sauti yace, “Kin gaji?”.        Juyar da fiskarta tai ƙoƙarin sake yi, ya riƙe da ƙyau. Tare da sake faɗin, “Barci ne?”. Shiru tayi nan ma. Ya ce, “Ni ne?”. Yanzu ma shiru.     Yace “Oh kishi ne?”. Yanzu kam sai ta buɗe idannunta da suka ƙanƙance ta zabga masa harara. Sosai ya saki wani irin sassanyan murmushi daya daki zuciyarta. Babu shiri tai ƙasa da idanun nata tana tura baki. Murmushin ya sake saki, batare daya sake cewa komai ba ya jawota gaba ɗayanta ya rungume a jikinsa. Atare suka sauke ajiyar zuciya mai nauyin gaske, yayinda zukatan ke wani irin bugawa da sauri-sauri a tare. Sake ƙanƙameta yay, yana jin tamkar ya shigar da ita cikin jikin nasa ta narke kawai ta zama jininsa. Ita ɗin ta dabance a rayuwarsa, irin daban ɗin da baki yayi kaɗan a furtawa. Ya rayu da itane a irin rayuwar da baiyi da kowa ba, ya kusantu da ita a irin kusancin da bai samu da kowa ba. Ya shaƙu da ita a irin shaƙuwar da baiyi da kowa ba. Ita ɗin tamkar half ɗinsa ce a rayuwa. Itace abokiyarsa, abotar da bai taɓa yi da ɗan uwansa namiji ba. Dan zai iya cewa sai da suka rabu sannan yasan ya zauna tare da ɗan uwansa namiji har suyi mu'amula irin ta abota. A hakan ma kuma bai taɓa iya sakin jiki da kowa ba koda rabin kwatar yanda suka kasance shi da ita ne. Har garama Rafeeq, shima kuma dan ya kasance ɗan uwansa ne jininsa. Tsitstsinkewar da jinin jikinsa keyi sakamakon jin saukar ɗumin hawayenta a cikin ƙirjinsa ya sashi ɗagota daga jikin nasa, ƙoƙarin hana hakan takeyi, amma sai da yay nasarar ganin hawayen kuwa...      “Besty kuka” ya faɗa zuciyarsa na wani kalar hanƙoro, kauda kanta tai yunƙurin yi, da ɗan hanzari ya riƙo fiskarta tata, bai wata-wata ba a karo na farko na rayuwarsa ya manna tausasan lips ɗinsa kan nata............✍️    _Wayyo ana cin amanar Abah. Jama'a kukawo ɗauki daga bashi aro yin rakkiya zai ci amanar Abah a titin gwamnati🤣🤣🤣🥱🏃🏃_                *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [24/04, 5:24 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣8️⃣ ______________ .......Sosai jinin jikinsa ya shiga wani irin harmutsawa har cikin brain ɗinsa, illahirin ƙofofin gashinsa suka shiga bubbuɗewa. Domin al'amarin yazo masa da wani irin girma na gaske sakamakon abinda ya ɗauki tsawon shekaru yana dannewa da tsiya-tsiya. Tsaf ya kanainaye Hajiya Maanalu ta yanda bata da damar yin wani yinƙuri koda na motsa kanta ne. Sumbatarta yake cikin rikicewar yanayi da birkicewar tunani, sai dai hakan bai sakashi kasancewa a rashin nutsuwar da ALLAH ya azurtashi da ita ba. Akowane irin yanayi AA nutsatstsen mutum ne mai cike da kamala da dattako, nutsuwa akan komai halittar AA ce, sannan a cikin jinin jikinsa take. Matuƙar nisan kiwo ƙwaƙwalwarsa da zuciyarsa suka tafi ya manta da inda suke, dan kuwa tuni ya fara ƙoƙarin warware mata veil ɗin jikinta da take ta ƙoƙarin ganin ta riƙe ta hanashi hakan, amma yanda ya matseta a cikin kujerar hakan ya gagara, har ALLAH ya bashi nasarar yakicesa ya tura hannunsa a bayanta ya fara kici-kicin sauke zip ɗin bayan rigarta. Zuwa yanzu kam matuƙar ƙololuwar tashin hankali da birkicewar zuciya Maanal ta shiga. Dan tsabar tsoro da firgici zuciyarta neman buɗewa take gida biyu. Abu biyu ne ke maimaita kansu a ƙwaƙwalwarta a wannan gaɓar. Tsoro mai tsananin gaske, da flash back na wasu shekaru da suka shuɗe a rayuwarsu, sai dai tarihin irin wannan gaɓar bazai taɓa gogewa ba har abada dan tabone da ya riga yay tammbari a RAYUWARSU na har abada. A hankali ta saki masa wani irin kuka da kaima bayansa duka dan ta fahimci kamar ya manta itace fa Bestyn sa. Sai dai babu alamar yasan tanayi dan har yayi nasarar sauke zip ɗin yakai ga hook ɗin b ɗinta yana kici-kicin ciresu suma... A dai-dai nan kira ya shigo cikin wayarsa, kiran daya saka komai tsayawa cak harda fitar numfashinsu. Bawai kiran ne yay tasiri ba ga AA, a'a sautin dake tabbatar masa da kiran daga waye ne ya tasirantu a garesa matuƙa. Yafi sakan goma bai iya ya motsa ba balle janye jikinsa kafin ya zare lips ɗinsa akan nata a hankali, sai dai ya kasa raba jikinsa a nata saima sake ƙanƙameta da yay na fin sakan ashirin. A lokacin daya ja jikin nasa baya ya koma a nasa mazaunin jagwab ne ya bama Maanal damar cusa kanta a cikin ƙafafunta ta ƙanƙame jikinta waje guda gaba ɗaya. Jikin nata kuma sai wani kalar rawa yake na tsorata da shiga firgici ga kunya mai tsananin gaske da bata taɓa shiga tsakaninta da shi ba a rayuwarta. Zuciyarta kuwa babu abinda take sai rabewa da komawa ta tsuke kanta da kanta....      Kiran Abah daya sake shigo masa ne ya sashi ɗaukar ruwan dake gefen sa ya ɓalle murfin ya shiga kwankwaɗa duk da uban zafin da yake da shi. Shi kansa ma bai san tun yaushe ruwan yake a motar ba. Sai da yasha kusan rabi ya kife kansa a steering yana maida numfashi, a karo na uku kiran Abahn ya sake shigowa. Sai yanzu ne ya sami damar dai-daita kansa da ƙyar ya ɗaga wayar.       “Ajwaad! Kana kallon ƙarfe nawa kuwa? Sai ɗaya tayi zaku dawo?”. Nutsatstsiyar muryar Abah ta daki cikin kunnensa. Idanunsa ya sake lumshewa ya buɗe da ƙyar, cikin ƙoƙarin ganin muryarsa ta kuma samun nutsuwa yay ɗan gyaran maƙoshi kafin ƙasa-ƙasa ya ce, “Gamu nan in sha ALLAHU Abah”.      Shiru Abah yay sautin shaƙaƙƙiyar muryar ta AA na dakar masa zuciya. Dan duk wanda ya sanshi ya jisa a yanzu zai fahimci akwai lauje cikin naɗi. Amma kasancewarsa dattijon arziƙi sai cewa yay, “Okay kuyi sauri Oum ɗinku nason kwanciya” daga haka ya yanke kiran. Idanu AA ya sake lumshewa ya buɗe a karo na barkatai, shi kansa ganin ƙarfe nawa sai da yaji zuciyarsa ta girgiza. Harga ALLAH bai san sun jima haka ba, dan sai yake ganin ma kamar basu wuce minti talatin da fitowar ba. A karo na farko ya maida birkitattun idanunsa kan Maanal dake a duƙufe har yanzu. Lallausar fatar bayanta da hasken fitilar titin ta hasko ya zubama idanu, sai farar b ɗin jikinta datai matuƙar dacewa da fatar gata fes babu wani alamar datti a tare da ita. Numfashi ya sake ja a fisge, kafin cike da kasala ya kai hannu kan zip ɗin zai ja mata shi saman. Zaram ta miƙe zaune sosai idanunta share-share da hawaye. Shi dariya ma taso bashi ganin yanda ta wani zazzaro masa idanun alamar gargaɗi. Ƙasan zuciyarsa kuwa sai yaji kamar yana jin nauyinta shima musamman da wani gefe na zuciyar keta maimaita masa kalmar (Bestynka ce fa! Amma ka rufe ido ka aikata mata wannan abin kunyar har kana neman sakin layi) kauda tunanin yay gefe murmushin gefen baki na neman suɓuce masa. Amma sai ya daure a tausashe ya ce, “Yi haƙuri zip ɗin zan rufe miki, idan kuma kina son Abanki ya gane to a barshi a hakan kawai kinga na huta sai yace mu wuce sashen mu kawai ya salllama”. Ai da gudun tsiya ta duƙe alamar ya rufe matan. Yanzu kam saida ya murmusa kaɗan, kafin ya kai hannun yaja zip ɗin, yazo dai-dai jikin b ɗin ta ya dakata, hook ɗin yay ƙoƙarin maida mata dan duk ya ciresu saura ɗaya jal ya rage masa. Rumtse idanu kawai Maanal tayi da ƙarfin tsiya harya kammala ya ƙarasa ja mata zip ɗin.      “Oya wanke fuska mu wuce, idan kuma a samu hotel anan kusa muƙarasa to”.     A baima gama rufe baki ba ta ɓalle murfin motar, batare data kallesa ba ta warce goran ruwan hannunsa ta juya ta fara wanke fuskanta. Murmushi ya saki, tare da kai hannu ya shafa lallausar sumar kansa dake lashe kuɗaɗe da shima bai san adadi ba. Koda ta gama bata kallesa ba, ta yarda goran a ƙasa ta maida murfin ta rufo, sai kuma ta matsa jikin murfin ta maƙure. Komai baice mata ba, sai handkacheff ɗinsa mai ƙamshi ya miƙa mata kawai. Ɗan kallonsa tayi, suka ko haɗa ido. Da sauri ta janye nata tana fisgar handky ɗin kawai. Nanma murmushi yay yayima motar key suka cigaba da tafiya. Sai dai yanzu gudu yake sosai saɓanin ɗazun. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa sai gasu a gaban ƙaton gate ɗin gidansu...               Koda suka nufi sashen Oum salaf-salaf Maanal ke tafiya kamar wadda ƙwai ya fashewa a ciki. Gani take kamar tana shiga kowa zai gane abinda ya faru a tsakaninsu. Musamman ma Abah da Oum. Ɗan tsayawa AA yayi, ita kuma kanta a ƙasa tunanin da take yi ya ɗauke dukkan hankalinta har tazo gab da shi bata sani ba. Sai da ta bugu da bayansa sannan ta ɗago da sauri, tayi baya kuma zata faɗi. Saurin juyowa yay tare da riƙota a lokaci guda, cike da kulawa ya jinginata da jikin bango. Muryarsa a sanyaye saboda halin da yake ciki ya riƙe fuskarta, ɗayan hannunta kuma a cikin nashi yana kallon fuskar ya ce, “Tunanin mi kikeyi ne haka?”.        Wata irin kunyarsa take ji shima, dan haka tana ɗan ɗago idonta ta kallai ta maida su ta risinar, shiko nashi yawo kawai suke akan ƙyaƙyƙyawar fiskarta. Kanta kawai ta girgiza masa tana ƙoƙarin janye hannunta dake a cikin nasa yaƙi bata damar hakan. Hawayen da take riƙewane suka ziraro, ya waro lumsassun nasa sosai. “Ya arrahaman, miye abin kukan kuma?”.       Cikin rawar murya ta ce, “Yanzu idan Oum da Abah suka gane fa”.      Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke, a ransa yana faɗin, (Ashefa na manta yarinyar nan ɗanya ce, rinton aji yasata gama makaranta da wuri) a fili kam sai ya shafa fiskarta tare da faɗin, “Sai dai in kece kika so su gane”.     Kallonsa ta ɗago tayi sosai a karo na farko, ya jinjina mata kansa yana ɗan laɓe baki da murmushin gefen baki a tare. Sai kuma ya shafa kanta cike da lallashi da tsokana ya rankwafa yana mai kai bakinsa saitin kunnenta da raɗa ya ce, “To ko mu tafi sashen mu kawai ki kwana acan, da asuba na miki alƙawarinkin rakoki da wuri kafin kowa ya tashi”.      Tamkar wadda ya zaburar, ta sa hannayenta duka biyu a ƙitjinsa ta tura shi baya. Matsawar yayi yana dariya, ita ko ta kwasa da ɗan gudu cikin sashen Oum. Ko ganin Abah dake bayansu ma batayi ba sam. A falon kuwa akwai Oum, Mamy, Nibras, Saheeba da Fawzan harda babban Yaya a yanzu na zaune suna hira sai kawai ganinta sukai kamar walƙiya ta wuce hanyar upstairs. Da sauri Oum ta ce, “Munga idi Baby waya biyoki haka?”.      “Oum fitsari-fitsari” ta faɗa batare data waiwayo ba. Dan tasan wannan dabararce kawai zata rabata da jin kunya. Saboda babu wanda zai kalleta bai fahimci wani abu ba a fuskar ta da lips ɗinta da yasha wahala a hannun wancan mutumin. Dariya Fawzan da Babban Yaya suka saki a lokaci guda, dan abinda Maanal ɗin tayi ya tuna musu da baya ne. Haka take yi idan suka dawo makaranta, sai ta riƙe fitsari tun daga can, mota na tsayawa ta fita a guje zuwa ciki tana faɗin, “Fitsari-fitsari”. Sai da Ammie ta zaneta wataran aka samu lafiya ta daina abin nan. Oum ma dai dariyar tayi, dan itama dai abinda yazo mata a rai kenan. Mamy da su Saheeba kam wani irin takaici ne ya ƙullesu, da kallon abinda Maanal ɗin tayi matsayin wani sabon bariki.... A waje kam, AA na gama dariyarsa dake fita a hankali ya juyo da nufin shigewa shima sukai ido huɗu da Abah daya harɗe hannaye a ƙirji ya tsaresa da idanu. Da sauri AA ya juya yana rumtse idanu da kai hannu ya shafa kansa, haƙoransa damtse da lips ɗinsa. A zuciyarsa faɗi yake (Ajwaad kaga takanka, tsohon nan ba raga maka zai yi ba....) katsewa zancen zucin nasa yay saboda taɓashi da akayi, juyowa yay kansa a ƙasa hannunsa a cikin sumar kansa, sai kuma ya ɗan buɗe ido ɗaya ya ɗan kalla Abahn. Abah da dariya ke cinsa a rai ya gimtse da ƙyar ya wani sake tsatsatsaresa da idanun. Sai AA ɗin cayay, “La Abah kai ne?”.      “A'a bani bane aljani ne”. Abah ya bashi amsa cike da gatse. Bayansa AA ya koma ya tungumesa, ya tabbatar hakan shine rufun asirinsa dan wlhy tsaf Abah zai gane halin da yake ciki, musamman idanunsa da suka kaɗe. Cike da shagwaɓa ya kwantar da kansa a kafaɗar Aban yana faɗin, “Kaga ko Abah ALLAH ban lura time ya tafi haka ba. Na tuba! Na tuba! Na tuba!!”.     Yanzu kam kasa daurewa Abah yay saida ya murmusa. Amma kasancewar AA na bayansa ba gani yay ba. Fuskar ya maida ya himtse a dake ya ce, “Ai na faɗa maka daman saina ƙara kwanakin suspension idan ka daɗe min da yarinya”.          A sanyaye AA ya ce, “Abah holdup ne fa a hanyar”.     “Na aljanu ko? Yo in ba na aljanu ba a daren nan wane huldup ne zai taru. Kaji tsoron ALLAH Ajwaad”.        Ƙaramar dariya yanzu kam AA ɗin yayi da faɗin, “To Abah kawai abar kaza mana cikin gashinta. Kawai kayi murna mun dawo bamu ɓata ba ma”.      Rankwashi Abah ya kai masa bisa kai, da sauri ya sakesa ya shige sashen Oum yana dariya. Shima Aban dariya yake yi da girgiza kansa. Wani irin farin ciki na ratsa masa zuciya. Rabon da yaga Ajwaad a irin wannan yanayin na farin cikin da har zai dinga wasa da dariya kai tsaye an ɗauki shekaru masu yawa. Ko tsokanarsa sukai sai dai yay guntun murmushi kawai yay shiru. Amma yau jiba yanda yake zuba masa surutu da shagwaɓa kai tsaye. Ya ɗan sauke ajiyar zuciya, sai kuma ya nufi sashensa yana mai jerama UBANGIJI kirari da godiya.........✍️ _Abah namu, anya! Anya kuwa🥱. Bara dai nayi shiru😂👍_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [25/04, 5:11 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣9️⃣ ______________ *_LADIES COLLECTION AND MORE_* 08169307477 SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai? To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS COLLECTION AND MORE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S COLLECTION AND MORE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Less Hijabs Supplements Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko 08169307477 Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 *********** ________________ ......Su babban Yaya na dariyar Maanal AA ya shigo. Duk kallonsa sukai, musamman Mamy dake masa kallon ƙurulla, hakama Nibras ji take kamar taje ta rungumeshi ta fashe da kuka saboda kishin Maanal dake ruruwa a zuciyarta. Gashi yanda lips ɗinsa suka wani ƙara zama pink duk sai taji ta tsargu, zuciyarta ta shiga wassafa mata abinda ya faru. Cike da basarwa AA ya kai zaune. A nutsensa kamar bashi ya gama yima Abah shagwaɓa ba ya ce, “Ikon rabbu, miya saku nishaɗi haka?”.       “Bestynka mana” cewar Fawzan, sai kuma ya shiga bashi labarin abinda tayi. Wani ɗan murmushi ya saki tare da girgiza kansa. Ba ƙaramin dukan zuciyar Mamy da Nibras murmushin nasa yayi ba. Amma sai ya katse yanayin nasu da faɗin, “Mamy mun kai”. Batare daya kalleta ba. Dan yasan tana nan tana tuhumarsa da ido.          Kafin ta amsa masa Fawzan ya dawo kusa da shi neman tsokana, sai dai yana zama ƙamshin sassanyan turaren Maanal daya manne a jikin AA ya shiga hancinsa, idanu ya waro tare da sake matsawa yana shinshina shi. Cike da raɗa Fawzan ya ce, “Ehem-ehem malam yau dai babu zancen dojewa ALLAH ƙamshin turaren Lilly kake yi?”.      Harararsa AA yayi, shima ƙasa-ƙasa ya ce, “Yaya Fawzan ka rage gulma wlhy, mutum da matarsa dan anji ƙamshinta a jikinsa sai mi?”.     Sosai Fawzan ya saki baki da hanci yana kallonsa, shima AA ɗin kallon nasa yake da wani irin salon ɗage gira sama irin na (Eh ɗin nan). Jinjina kai Fawzan yayi, a hankali yace, “Ashe za'a bajeta a gaban Abah gobe. Dole a ƙara maka kwanaki sai after babbar salla”.        Yanzun ma ƙasa-ƙasa shima AA ya ce, “Yo a bajetan mana, zuwa babbar sallar kun fara jiyyarta dan ta fara laulayi kuwa, kunga sai ku bari sai ta haihu ku bani”. Daga haka ya miƙe cike da basarwa tamkar bashi ya faɗa ba. Fawzan daya saki baki yana kallonsa ya kwashe da dariya da faɗin, “Kai wannan yaro tantiri ne kai, ALLAH sai na tona”.     Gwalo AA daya nufi hanyar fita ya juyo yayma Fawzan, kafin yace, “Oum! Mamy! Babban yaya good night”. Ya fice a binsa. Cikin ɗaga murya Fawzan yace, “Muma da bakace mana good night ɗin ba lafiya lau zamu kwana, kuma gobe sai na fasa ƙwai a gaban Abah”.       Wani kalar ƙululun takaici ne ya kume Mamy, dan kallon da takema Fawzan da AA ta gefen ido tsaf ta fahimci abinda suke tattaunawa da juna ta hanyar motsin bakinsu. Gittawar AA a yanzu kuma sarai ta ji ƙamshin turaren Maanal itama. Hakama Nibras data sanya musu ido. Saheeba dai tsarguwa kawai tayi, shiko babban yaya da Oum dariya ma suke musu dan Fawzan da Ajwaad tamkar tom and jarry haka suke. Komansu irin na asalin sako-da-sako ne basa ragama juna. Ta wani gefen kuma kamar wasu abokai.. Fitar AA ɗin ta saka hirar tashi gaba ɗaya, dan dama dai rashin dawowarsu yasa hirar tsaho haka da sha biyu ta wuce...        Lokacin da Oum ta shiga ɗaki samu tai Maanal harta kwanta. Murmushi kawai tayi itama ta shiga kimtsawa domin tafiya wajen mijinta. Taje zuba kayanta a laundry basket taji ƙamshin turaren AA matuƙa a wajen, kayan cikin basket ɗin ta kalla, kayan Maanal ne data cire yanzu. Kasa daurewa Oum tai ta ɗakko doguwar rigar takai hancinta. Itace kuwa ke ƙamshin na gasken gaske. Kai Oum ta girgiza dariya na suɓuce mata, sai yanzu ta fahimci dalilin gudun Maanal da ƙin tsayawa a wajensu da wannan kwanciyar saurin. Ƙasa-ƙasa ta ce, (Wannan nake jiye maka Abansu, karka bashi matarsa dai a juri zuwa rafi) daga haka ta ajiye rigar ta ƙarasa shirinta ta tafi wajen mijinta... _________★   Sille ya jima akan titin bayan wucewar motar AA. Dan abinda ya gani na faruwa daga nesan da bayansu da yake kasancewar gilashin motar a sauke yake kaɗan ya sashi canja shawara. Waya ya fiddo ya shiga yi musu video. Dan wata shegiyar waya ce dashi mai ƙarfin camara ta yanda yake iya zooming abu mai nisa sosai. Yako yi nasarar ɗaukar komai yanda ya kamata, daga ƙarshe ya adana videon a wayar tasa yana murmushin cin nasara. Dan yaci alwashin sai videon nan ya zame masa kadarar tatsar mutane da yawa kuɗaɗe kafin yasa ai masa editing ɗinsa ya bazashi a media ta yanda sai ya kunyata rayuwar AA da Maanal dan zai canjama al'amarin siga ne ta koma matsayin kafin aurensu ne hakan ta faru. Sauran alwashinsa kuma zai biyo baya dan baya yafiya ba kuma ya canja tsarinsa akan maida murtani saboda sabon idea.....      Hummm wannan Sille! Wannan Sille wai mike damunka ne🙄🥺. ________★      Murmushin da Oum keta faman yi ne ya saka Abah dake binta da kallo faɗin, “Wai shi wannan murmushin na miye?”.         “To Gadanga miye a murmushi ko dai ka tsargu ne?”.   “Tsarguwar ma sai nayi, dan nasan halinki sarai”.    Dariya Oum ta sakeyi, sai kuma takai zaune a kusa da shi tana faɗin, “Abansu ka fahimci a yanayin da Ajwaad da Maanal suka shigo kuwa?”.      Kansa ya girgiza alamar (a'a) Cikin ɗan waro idanu Oum tace, “Gadanga kaji tsoron ALLAH”.      Murmushi kawai yayi baice komai ba. Oum ta ɓata fuska. “To ALLAH ina gaya maka idan baka bama Auta matarsa ba za'a haifi ɗa mara ido, kadai gani da idonka sau biyu”.            “A haifi ma mara kunne, ai nasan dai duk rashin kunyarsa bazaiyi abinda kike tsoron ba. Fateema da kike ganina sarai nasan abinda nake yi, dan haka ki daina damun kanki ina kan ra'ayina. Saboda ni nasan dalilina nayin komai”.     Shiru kawai Oum tai tana kallonsa, sai kuma ta kai kwance cike da haushi. Baki kawai Abah ya taɓe ya cigaba da duba littafin hannunsa daya kasance na addu'oi....       ★Washe gari Abah ya tashi da uzirin fita da wuri, dan haka ya bada umarnin driver yakai Maanal wajen aiki. Yauma kamar jiya bayan sun kammala breakfast da Maanal bataci ba tace azumi take kowa ya shiga motarsa. Driver ya buɗema Maanal mota itama. Oum batace komai ba dan a gabanta Abah ya sanarma driver ɗin. AA ma yi yay kamar baiga komai ba ya shiga tashi motar nasa drivern ya jasa. Sai da suka fito ko street ɗin basu gama bari ba ya saka drivern sa tsaida na Abah. Fitowa drivern yay yazo saitin inda AA ɗin yake zaune yana faman duba wasu takardu. Batare daya kalla drivern ba sai gilashin daya ɗan sauke a dakensa ya ce, “Buɗe mata ta dawo nan”.     Daburcewa sosai drivern yayi, dan ba ƙaramin gargaɗi Abah ya masa ba akan hakan kasancewar yasan AA ɗin zai iya aikatawa. Cikin tashin hankali driver yace, “Ranka ya daɗe Alhaji fa yace...”      Wani banzan kallo da AA ɗin ya ɗago ya watsa masa ya saka shi kasa ƙarasa faɗa, sai ma duƙar da kansa da yay ƙasa da sauri. Shi kam dai sun sakashi a tsaka mi wuya. Kusan minti ɗaya AA ya ajiye takardun hannun nasa ya ɓalle murfin motar ya fito. Yayi ƙyau matuƙa cikin baby pink color ɗin suit, fuskar nan babu walwala sai kwarjinin kamala dana ibada ke fita. Maanal da haushin tsayawar tasu ya kumeta taja tsaki tana ƙoƙarin ƙarasa abinda take a laptop ta fito kawai taji an buɗe side ɗin da taken, ɗagowa tai cike da masifa dan son ganin wanene suka haɗa ido da AA da yay kicin-kicin da fuska. Itama dai tayi ƙyau sosai cikin lass da akaima doguwar riga, ta kafa ɗaurin zarah buhari sai veil ɗinta da yay dai-dai da tsarin shigar tata. Tana ƙoƙarin rufe laptop ɗin kawai ya duƙo cikin motar a kanta, kafin ta samu damar magana ya ɗagata cak ya fito da ita. Idan tace al'amarin AA bai fara girgiza tunaninta ba ma ai tayi ƙarya, yanzu banda ikkanci a titin ALLAH zai ɗakkota a mota da safen nan mutane nata kai-kawo. Koma tace a anguwarsu data tabbatar ko wani bai sanshi ba wani ya sanshi duk da ana rayuwa ne irinta ba ruwan wani da wani ɗin nan a anguwar. Da sauri kuwa nasa drivern ya fito ya buɗe masa ɗayan side ɗin da yaga ya zagaya, a ransa kuwa dariyar halin ogan nasa yake, yayinda suka matuƙar birgesa duk da yanata wani sinne kai. Ajiyeta AA ɗin yayi ya gyara mata rigarta ya rufe ƙofar, ita kam ai tamayi sumar zaune ne ko mi zatace oho. Dan sam tama kasa masa magana dan al'ajabi. Shigowarsa wajen da yake zaune hannunsa riƙe da tarkacenta da drivern Abah ya kwaso mata ya sata kallonsa ta gefen ido, sai wani ɓaɓɓata fuska yake kamar ba shine daren jiya ya gama aikata mata abin kunya ba. Aikinsa ya cigaba da yi batare daya sake kallonta ba yana cema drivern sa, “Muje” a daƙile.      Yanda ya basar ya cigaba da aikinsa itama sai ta basar ta cigaba da nata aikin. Har suka iso Company wani magana bai shiga tsakaninsu ba. Kai babu ma wanda ya kula ɗan uwansa. Koda motar ta tsaya kuma kasancewar tana tattara kayanta shine ya fara fita. Tayi zaton zai yi tafiyarsa ne. Amma sai a mamakinta ya zagayo ta inda take ya buɗe mata. Koda ta fito kuma sai ya saka hannu ya amshi kayan hannunta harda handbag ɗin kamar jiya. Ya kuma kama hannunta da ɗayan hannunnsa. Nashi kayan kuwa sai drivern sa daya bisu da kallo yana murmushi ne ya tattara yabi bayansa da su.      Yau ma cike da gulma wanda suka iso ke binsu da kallo suna kuma gaishesu da girmamawa. Yayinda wasu ke gwada son amsar kayan hannun AA ɗin amma sai ya girgiza kai kawai alamar (a'a). Kamar dai jiya harda masu leƙensu ta windows dan gulma. Suna shigowa kuma kowa ya nutsu aka shiga miƙa musu gaisuwa... Yau dai kai tsaye office ɗinta suka nufa. An gyara komai fes an saka air freshener masu daɗi, shine ya kunna wutar office ɗin dake a kashe, har saman desk ɗinta kuma yaje ya ajiye kayan hannun nasa batare daya kalleta ba ya nufi hanyar fita, ita dai tana tsaye tana kallon ikon ALLAH. Har yaje ƙofar sai kuma ya dawo gabanta yaja ya tsaya. Cike da gargaɗi fuskarsa a tamke murya a dake ya ce, “Daga yau wannan ya zama first and last da zaki bishi in har ba tare da Abah ba. Azumin mi kikeyi kuma”.      Yanzun kam kallonsa tai cike da mamaki, sai kuma ta tura baki gaba ta ce, “Na nafila mana”.         “To sai kisan yanda zakiyi da shi tunda baki sanar min ba.” ya ƙare maganar da dalla mata harara ya juya zai fita..........✍️ _Oh oh AA rigima azumin ne kuma sai an sanar maka munga idi🏃🏃🤣_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [25/04, 5:11 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣0️⃣ ______________ *_LADIES COLLECTION AND MORE_* 08169307477 SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai? To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS COLLECTION AND MORE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S COLLECTION AND MORE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Less Hijabs Supplements Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko 08169307477 Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 *********** _______________ 20 WANNAN SAƘONKU NE😊 LA'ILAHA ILLA-ANTA SUBAHANAKA INNI KUNTU MINAZZALUMIN!! ......A tunzure Maanal data cika tai fam da wannan mulkin mallaka ta ce, “Kamar ya nasan yanda zanyi da shi? Yanzu ibadar ce kuma dan zan yi sai na sanar maka?”.         Sai da ya buɗe ƙofar sannan ya waiwayo ya kalleta, cike da izza ya furta, “Ya rage naki”. Daga haka yay ficewarsa. Harara ta rakashi da ita. Sai kuma tama ƙofar gwalo dan shi dai ai ya riga ya fice abinsa. Kujerar zamanta ta nufa ta zauna tana ƴar dariyar ƙeta. Dama babu wani azumi da takeyi, tayi hakan ne dan gujema halinsa na salon tattaɓata daya ɗauka. Handbag ɗinta ta buɗe ta ciro ƙyaƙyawan bottle mai kama da cup ɗin nan na zamani dake cike da tea, sai gasashshen bread a ƴar bowl data sanyo batare da ko sanin Oum ba. Dan Inte tasa ta haɗa mata su. Hankalinta kwance ta fara aikinta tana karyawa. Sai zabga murmushi take da bata san na miye ba itama. Kawai dai ta tsinta kanta a cikin nishaɗin yin hakanne....      Kusan ƙarfe goma takarda ta iso mata daga office ɗin HOD. Bata komai bace sai ta tafiyarsu. Komai an kammala, sannan iya su da zasuyi tafiyar an basu hutun zuwa aiki gobe, idan ma daga yau mutum zai wuce gidan duk an basu dama amma sai zuwa break bayan anyi zama da su, suyi shiri kawai dan jibi in sha ALLAHU ƙarfe biyar na yamma jirginsu zai ɗaga. Ajiyar zuciya kawai ta sauke a hankali, zata ƙarasa ayyukanta kawai yau ɗin ita kam bazata tafi yau ba. Ƙarfe sha biyu suka shiga meeting. Sai a lokacin taga sauran wanda zasu yi tafiyar da su. Ashe harda cikin manyan ma. Dan akwai CFO, sai CMO, WCD da sauransu..... Sunyi nisa a meeting ɗin kafin CEO ya shigo shida Assistant ɗinsa. Bayan sun zauna ya nema afuwar jikinrinsa, acewarsa yana da baƙi ne. Maanal na ɗagowa suka haɗa ido. Da sauri ta janye nata. AS ne yay musu bayanin abinda zasuje yi, dan kowa da fanin sa, tare da karanto musu dokokin tafiyar. Zasu yi kwana goma ne, kenan zasu dawo azumi nada kwanaki takwas, dan yau saura kwana huɗu a fara. Daga ƙarshe yace kowa zaiga alert na kuɗi a cikin account ɗinsa domin shirin tafiyar. Bayan komawa ya zauna AA ya dubesu a dakensa, idonsa ne ya sauka akan Maanal a karo na barkatai, sai dai yanzu ita ba kallonsa take ba, tana magana ne da Yaqub ƙasa-ƙasa, da'alana akwai bayanin da yake mata da bata gane ba a maganar AS. Shima janye nasan yayi yanayinsa na canjawa sannan ya fara musu nasa jawabin mai cike da gargaɗin daya saka Maanal ɗagowa ta dubesa, harara ya sakar mata a kaikaice, wani gefen kuma nasiha ce. Ya rufe da addu'a daga haka meeting ɗin ya tashi. A tare Maanal da Yaqub dake mata sallama suka fito, sai kawai jitai an riƙo hannunta, juyowa tai da sauri, sukayi ido huɗu kuwa da mai gayya da aiki. Wani banzan kallo yay mata, sannan ya zubama Yaqub wani kallon gargaɗi daya sakashi barin wajen da sauri....... __________★ اَللَّهُمَّ اكْفِنِيهِمْ بِمَا شِئْتَ. Allahummak finihim bima shi'ita. _Ya ALLAH! Ka isar mini su da abin da Ka so._ _________★ AIRPORT           Cike da farin cikin dawowarsa ƙasar haihuwarsa bayan dogon hutun daya sha na watanni uku yake fitowa a jirgin. Yayi fresh da shi dan ma tsufa ya cinye komai. Ƙarfarsa na gama sauka bisa ƙasa idonsa ya sauka kan amaryarsa, gefe kaɗan Oler ne da Rabilu sai sauran yaransa dai na siyasa. Sen... Bukar Kaugama yay wani murmushin jin daɗi mai cike da ma'anoni. Dan kuwa abu biyu ke ɗawainiya da shi, farin cikin dawowa ƙasarsa a gaɓar da zai mallaki ƴar shilar amaryarsa Maanal, da kuma kewar ƙasarsa ta haihuwa. Babu kunya amaryarsa tazo ta rungumesa tana masa barka da dawowa cike da farin ciki.       Cikin irin nasu salon na manyan ƙasa ya wani ɗan bubbuga bayanta da ɗan mata ƙaramin kiss a gefen fuska sannan ya janyeta daga jikin nasa ya riƙe mata hannu. Sai lokacin su Rabilu sukayo wajensa suma. Fuskokinsu da farin ciki suke masa barka da zuwa. Shi ko yana amsa musu da kulawa. Basu wani ɓata lokaci ba suka ɗunguma inda jerarrun motocin da sukazo tarbarsa suke. Aka buɗe masa wadda tafi kowacce daukar ido shi da amaryarsa suka shige. Motocin na fitowa a airport ɗin tawagar uwargidansa na isowa itama tarbar tasa. Sunata sauri ganin sun makara, sai dai kuma basu dace ɗin ba. Drivern ta daya lura da motocin ne ya ce, “Ranki ya daɗe ai kamar ha Excellency ɗin ma can fa har sun fito”. Da sauri ta kalla motocin itama, tabbas kuwa motocin gidansu ne, sai dai motar da ta tabbatar yana a ciki tasan tana a gidan amaryarsa ne ajiye. A take ranta ya ɓaci matuƙa. Cikin fushi da jin zafin kishi tace, “Mubi bayansu”.      Babu musu yay reverse, hakama drivern daya ɗakko yaranta shima, sai ma'aikatan gidanta, motar ƙawayenta ce ƙarshe, dan kuwa shiri tai na musamman akan dawowar tasa yau tare da shirya masa wani ƙwarya-ƙwaryar liyafa dan ranar tayi dai-dai fa Anaversary ɗin aurensu. Motocin su amarya na gama shiga maigadi zai maida gate ya rufe na uwargida suka iso. Dole ya dakata dan aguje suke. Fuskar Sen... Bukar da murmushi ya fito a motar, dan amaryar tasa ce ke zuba masa iskanci a motar, shiko ya narke mata. Da ƙyar ma ta bari suka fito. Sai dai me yana gama fitowa Uwargida ran gida na tsayawa a gabansa kamar wadda aka jeho. Hamshaƙiyar mace data amsa mace, dan kuwa sune manyan mata. Amma (iyayi na mutum nan yace bai son ƙiba🙄, shima kuma fa ƙaton gaske ne🥱). Yanda uwargidan ke kallonsa cikin ido dole ya ƙaƙaro murmushi tare da ɗan rungumota yana faɗin, “A'a ku kuma maimakon airport nan kuka yo?”.        Itama a maimakon bashi amsa ɗagowa kawai tayi daga jikinsa, sai kuma ta kama hannunsa a dake ta ce, “Muje ko! Ga mutane a waje na jiranmu”.      Gaba ɗaya daburcewa sen.. Bukar ya nema yi, dan kowaccensu da shirinta take an kai sunansa wajen teacher na zaure, ya kalla amarya ya kalla uwargida. Kowacce ta haɗe fuska abinta kamar dai a film. A ransa faɗi yake (wadda duk zata ɗaukeni gaba ɗaya daga hannunku ta kusa zuwa ai tula-tulan banza). Amaryar ƴar tsiyace ya sani, ita kuma uwargidan bata da yawan magana amma itama fa ba daga baya ba tasan ta inda take dafa shi duk rashin mutuncin da yake musu musamman ma ita da babu kalar da bata gani ba. Fuuu amaryar ta shige ciki ita mai zuciya, a zatonta ai zai biyota kamar yanda yake mata idan su kaɗai ne musamman ludayinta na akan dawo, (bata san yanzu akwai Manaal ba😂), wannan ya bama uwargida dama ta jashi suka wuce...... _________★ اَللَّهُمَّ مُنْزِلَ الْكِتَابِ، سَرِيعَ الْحِسَابِ، اهْزِمِ اْلأَحْزَابَ، اَللَّهُمَّ اهْزِمْهُمْ وَزَلْزِلَهُمْ. Allahumma! Munzila-l-kitabi, sar'a-l-hisabi! Ihzimi-l-ahzaba. Allahumma ihzimhum wa alzihlum. _Ya ALLAH! Mai saukar da littafi, Mai gaggawan sakamako! Ka karya kungiyoyin abokan gaba. Ya ALLAH! Ka karya su, ka girgiza su._ ________★      Idan Maanal tace yanda taga fuskar AA hankalinta bai tashi ba ƙarya tayi, ita shaida ce tun suna ƙanana ya tsani yaga tana kula wani, ko ƴan uwansa su Fawzan dan baida yanda zai yi ne kawai. Addu'a ta shiga karantowa a zuciyarta ita dai, dan yanda ya damƙi hannun nata ma ji take kamar ta fasa kuka. Suna shiga office ɗinsa a kusan tsakkiya ya sakar mata hannu, batare dako kallonta ya sakeyi ba ya wuce kujerarsa ya zauna. Aikinsa ya cigaba da yi tamkar yama manta da ita. Itama tun tana basarwar harta koma satar kallonsa, tama kai ta zuba masa idanun kai tsaye. Kusan mintuna ashirin taji ƙafafunta na neman sagewa, zuciyarta kuma nata angizata akan taje kawai ta bashi haƙuri, dan itama abinda yay ɗin ya sake fargar da ita alaƙarta da Yaqub fa dole ne ta tsaya a iya matsayin daya dace, ba kamar ada da suka ɗan fara ba kodan darajar aure da kare mutuncin wanda yake a matsayin mijin nata kuma ogansu a ma'aikatar gaba ɗaya. Sai kuma nasihar Ammie da Nene da ma Oum take mata faman kai-kawo a rai, basuce ta wulaƙanta kanta ba, amma sun gargaɗeta ta sauke nauyin dake kanta musamman a gaɓar data san abu kuskurenta ne. Gyarawar tata shima zaisaka ya gyara nasa kura-kuran su gina ƙyaƙyƙyawar rayuwar aure mai nagarta, dan ita wannan rayuwar tasu ta yanzu tana da banbanci da wadda sukai a baya ta ƙuruciya musamman ga ita dake ƙarama sosai, tunda ko acan bayan tasan nagaba yay gaba, kawai dai ita dashi haɗuwar jini ce bawai abotar kai da kai ba. A hankali ta fara takawa zuwa inda yake tamkar mai koyan tafiya, maimakon zama a visitors chair kai tsaye inda yake zaune ta zagaya. Kusa da shi kaɗan taja ta tsaya, hakan datai ya saka ziciyar AA ƙara gudu a ƙirjinsa, dama can bawani aiki yake yi ba, dan ji yay bama ya fahimtar komai. A yasan shima yana da kishi mai karfi a kanta, dan haka yake so ta gane kuma ta kiyaye, duk da kuwa sanin hakan a gareta game da shi ba sabon abu bane ba ai, amma ya fahimci kamar ta manta ne....        “AA!”.   Ta kirashi da sunan da abakinta ya fara jinsa, ga shi nan kuma ya bisa dan wasu da yawa a yanzu bama su iya tantance ainahin sunansa sai AA Darma kawai. Duk da harbawar da zuciyarsa ta shiga yi a ƙirjinsa saboda tasirin kiran sunan nasa da tai bai kalleta ba, aikinsa kawai yake kamar gaske.           “Besty fushi fa ba ƙyau!”.     Ta faɗa tana leƙa fuskarsa cike da shagwaɓa. Nan ma tamkar dutse haka yay mata shiru. To itama fa zuciyar tata ta fara hawa, dan haka tai shiru kawai tana kallonsa. Tsahon mintuna uku taga ba kulatan zai yi ba kawai saita nufi barin wajen. Karan farko ya ɗago ido ya bita da kallo, itako ta wuce fuuuu alamar dai itama ta hau sama. Shima ai yasan yanda ya tsani yay magana ai masa shiru haka itama ta tsani ɗabi'ar. Har ita zai nunama zuciya da kishi, ita jiya ba ɗaukarta yay ya kaita wajen budurwarsa ba dan wulaƙanci, amma mitace masa, sai shi dan kawai ya ganta da abokin aikinta, to shike nan kuma bazata dinga mutunci da mutane ba'a Companyn?.       Tana gama fita yay wani irin watsar da file ɗin hannunsa akan desk ɗin, sai kuma ya buga shi ya juya kujerar ya kalla bangon wajen daya kasance glass....     Manaal na shiga office ɗinta kayanta ta tattara tsaf tai fitowar ta. Duk inda ta gitta gaisheta akeyi, ita sai suka ma ƙara bata haushi. ALLAH ya sota sanda ta fito harabar kamfanin duk ana ciki, sai securitys ne kawai ke ɗan kai-kawo. Suma duk wanda ta gitta sai ya gaisheta, drivern AA dake cikinsu yana hira yana hangota ya taso da sauri, gaisheta yay, tare da faɗin bara ya ɗakko mota. Amma sai sai tace da fa shi karya damu su Abah na jiranta a waje. Jin tace Abah ya sashi dakatawa, haka ta fita a ƙafa a kamfanin.         Tun fitiwarta harabar kamfanin sosai idon AA ya sauka a kanta, har maganarta da drivern sa da gaisuwar da securitys suke mata duk ya gani, kawai dai baya jin mi suke faɗa ne. Ji yay zuciyarsa ta ƙara hasala. Da ga zaunen da yake bazai iya ganinta ba yanzu saboda ta fita a kamfanin, dan haka ya miƙe tare da matsawa jikin gilashin. Sai ko ya hangota ta tsaida wata taxi ta shiga. Idan AA yace zuwa yanzu zuciyarsa batai kumburar da take neman fashewa ba yayi ƙarya. Shi yarinyar nan zata wulaƙanta da mutuncinsa a garin nan tana matarsa ta shiga taxi, shi zatama laifi ta fishi zuciya kuma. (Amma ai ta zo lallashinka kaƙi kulata) Wani sashe na zuciyarsa ta faɗa. Ji yay kamar ya kaima zuciyar naushi, amma dai ya daure, wajen ya bari gaba ɗaya, sai ma ya koma rukunin kujeru ya zauna, dan yasan ko aikin yace zai cigaba shirme kawai zaita tafkawa.........✍️ حَسْبُنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ. Hasbunal-lahu wani'mal-wakeel. _ALLAH ne mai isar mana, kuma madalla da shi abin dogaro._ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [25/04, 5:11 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣1️⃣ ______________ .........Maanal dai ta isa gida lafiya abinta, ALLAH ya sota a wallet ɗinta akwai kuɗi, haka ta cire ta biya shi tai ciki. A ƙasan maƙoshi AA dake bibiyarta ta hanyar GPS tracker ya sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ya kife wayar a saman desk ya kwantar da kansa da bayansa jikin kujerar da yake ya lumshe idanunsa. Maanal na shiga Nuratu da Hajiya Turai na fitowa a mota, da alama zuwansu kenan. Idon Maanal ne ya sauka akan ƙaton akwatin da Bola ke fitarwa a booth. Tayi niyyar wucewarta, sai zuciyarta ta gargaɗeta da hakan kodan Hajiya Turai dake babbar mace. Dan zata iya sa'a da Ammiensu koma ta girmeta. Duk da ta lura da kallon banzar da Nuratu ke mata saita watsar da ita, kaɗan taɗan matsa kusa da su ta gaida Hajiya Turai dake kallonta itama irin kallon ƙasan idon nan na ƙurulla. Bata kuma jira jin a yanda ta amsa mata ba tai gaba abinta. Daga Nuratun har Hajiya Turai binta sukai da kallo, tsakin da Nurry taja yasa Hajiya Turai faɗin, “Ko itace Maanal ɗin?”.      Baki Nurry ta taɓe, a gadarance ta ce, “Waifa Momy itace, shegiya baƙar banza, tana tafiya tana murguɗama mutane ɗuwawu dan asan tana da su ko”.        Hajiya Turai dake bin Maanal ɗin da kallo har yanzu ta ce, “Yoni Baby yarinyar nan ma nada muhimmanci kuwa a gidan nan? Kamar fa daga wajen aiki take a ƙafa alamar taxi ce ta ajiye ta, ace duk motocin gidan Darma ace surukar gidan na hawa taxi kuma matar AA duk dukiyarsa”.        “To Momy dama ba aikin asiri bane yasa ta shigo gidan, tunda ya riga ya gama da ita tun a titi wace soyayya zata gani kuma. Ba dai na shigo gidan ba, sauran asirin ma dan ubansa zan ƙarasa karyashi ne. Ana gama bikinmu zata ware dan sai ta sha ƙi baƙin cikin shagalin da za'a sha kafin na sa ya saketa.”      Sosai Hajiya Turai ta sanya dariya. Tamkar wasu ƙawaye ta bata hannu suka tafa. Daga hakan suma suka nufi sashen Mamy cike da nishaɗi...   Oho Maanal ma bata san sunai ba, tana shiga sashen Oum sama ta wuce abinta. Ta samu Oum da baƙuwa. Maanal ta gaishe da matar ƙyaƙyƙyawa da ita. Itako cike da kulawa take tambayar Oum, “Hajiya Fateema ko ɗiyar tamu ce?”.     Murmushi Oum tayi, ta ce, “Itace Hajiya Shuwa”.       “Kai Masha ALLAH, yarinya dirarriya ƙyaƙyƙyawa haka ga nutsuwa. A ruwan idon autanki bai tafi a banza ba ashe, ashe yasan miya taka, ɗaya yake son tsamowa a cikin dubu, to ALLAH ya sanya albarka a cikin auren nasu”.      Oum dake ta murmushi ta ce, “Amin ya rabbi”. Sai kuma ta kalla Maanal dake nufar hanyar bedroom. “Baby wai har kun tashi ne? Ina Bestyn naki?”.       Cikin danne komai Maanal taima Oum bayanin su an basu damar zuwa suyi shiri ne saboda tafiyar jibi. Oum ta ce, “Tofa tafiyar ta tashi ke kenan?”.     Manaal ta ce, “Eh Oum.” daga haka ta shige ta barsu. Hajiya Shuwa da gaba ɗaya Maanal ɗin ta ƙara birgeta ta ce, “Kai masha ALLAH, jiba yanda ta saki jiki dake kamar ba surukai ba, haka naso mu rayu da Amisha amma ƙawayen banza sukai mata huɗubar tsiya. Shiyasa yanzu nace masa aure zai ƙara, dan na gaji da ɓacin rai wlhy Hajiya Fateema. Wani lokacin idan aka juya min kan yaron nan ko kallo ban isheshi ba, shiyyasa kikaga nai tafiyar nan marocco ko sallama ban miki ba. Shi ma kansa bai san na tafi ba sai bayan kwana uku”.       “Kiyi haƙuri Hajiya Shuwa jarabawa ce, kowa da irin tasa kuma. Amma Amisha ta bama kowa mamaki, dan nidai ina ganinta shiru-shirun nan banyi zaton haka a gareta ba. Ni kaina yanzu saboda tasan yanda muke dake bata shigowa gidan nan, har mukaci bikin nan muka tsare bata leƙo ba, shima Ameer ɗin Fawzan yace baije mana ɗaurin aure ba, shine ma ya haɗasu faɗa shine yake cemasa ai dama Amisha tace ba sonsu muke ba, nice ke zugaki kina wulaƙanta masa mata. Nace ma Fawzan ya barsa baya cikin hayyacinsa ne kawai”.        Kwafa Hajiya Shuwa tayi, ranta na sake mata zafi da halin da ɗan nata yake ɗaya tilo namiji. Su Hajiya Shuwa sune makwaftan su Oum ta hannun damar su, asalinta ƴar marocco ce girman Libya, daga can mijinta Alhaji Mubarak KT ya aurota, yara biyu suka haifa kacal a duniya, Ameer shine babba, bayan haihwarsa ma ta jima bata sake ba harta haƙura ma sai ga ciki. Sunyi farin ciki sosai ita da mijinta, ALLAH ya sauketa lafiya ta haifi mace ƙyaƙyƙyawa itama suka saka mata Ameerah, bayan haihuwar Ameera bata sake ba kuma, yarinyar nada shekara goma a duniya ALLAH yayma Alhaji Mubarak rasuwa sakamakon bugawar zuciya na dare ɗaya daya samu. Shi ɗin babban ɗan gwagwarmaya ne kuma ɗan siyasa ta wani gefen, duk da dai bai saki jiki a siyasar ba gaba ɗaya. Yana kuma kasuwanci sosai. Ya tafi ya barta da yaran su biyu, ita ga cigaba da kulawa da rayuwarsu har girma, duk da dai sanda ma ya rasu Ameer har ya shiga University yana first year ɗinsa. Ameera ce ke primary 4. Tasha wahala da dangin mijinta dan dukiyar ƴaƴanta komawa tai tsole musu ido, acewarsu ai ɗan uwansu ne ya tara, bazai yiwu ya aurota daga wata ƙasa ba daga sama tazo ta mamaye komai, aiko suka ƙulla mata akan ta basu yara su cigaba da riƙewa da dukiyar ita kuma ta koma ƙasar ta. Hankalinta ya tashi, dan babu wanda take tausayi irin Ameera. Nanfa ta shiga faɗi tashin ganin hakan bata kasance ba, tana neman taimakon abokan mijinta, amma mi, kowa sai ya nuna sai in ga amince zata auresa zai yi hakan, wasu ma da iskanci suke zuwa mata. A cikin wannan kai-kawon nata ne suka haɗu da Ambassador Aliyu Darma, ta dalilin nashi abokin shima da ya kasance abokin mijin Hajiya Shuwa. Shima dai yayi mata maganar banza ne, ta fito ranta a ɓace shine sukaci karo da Abah da yaji komai dan yay ƙoƙarin shiga office ɗin ne yaji kalaman abokin nasa sai ya tsaya, amsar da Hajiya Shuwa ta bashi yay matuƙar birgesa, data fito kuma ya ganta mace mai kamala da nutsuwa. Baice mata komai ba a lokacin ta wuce ya shige, bai kuma nunama abokin nashi yasan komai ba shima. Sai da ya dawo gida ya sanarma Oum komai, hankalinta ya tashi baiwar ALLAH harda kukanta. Itace ta ƙarfafa Abah suka shirya taimakon Hajiya Shuwa, washe gari taje har gida ta sameta, zuwa ranar kuma Hajiya Shuwa ta sallama ma dan Oum ta sameta tana haɗa kayanta, tana shirya nasu Ameera domin danƙama dangin uban nasu kamar yanda suka buƙata. “ALLAH sarki na ALLAH baya ƙarewa duk rintsi”____wannan itace kalmar da Hajiya Shuwa ta faɗa bayan Oum ta gama mata bayanin abinda ya kawota, daga haka ta rungume Oum tana kuka...      Wannan shine sanadin tarayyar su, Abah ya tsaya mata akan komai har sai da aka mata tsakani da dangin Alhaji Mubarak, aiko sai akaita gulma ai sonta Abahn keyi, dan har Mamy ma ba sonta take ba ta kuma tsargu da hakan, musamman data roƙa Abah ya sayi filinsu dake a kusa da su dan lokacin su suna a zone 4 ne. Da farko Aban yaƙi, gudun kar ace ta basu ne shiyyasa suka taimaketa, sai da taita roƙonsa da tabbatar musu zamansu a kusa zai zamar mata garkuwane sannan ya amince. Ƙaton filine amma sai da Abah ya ƙara da wani a bayansu shine ya gina wannan babban gidan suka zama makwaftan juna. Anta jira aga Abah ya aure Hajiya Shuwa amma akaji tsit har ma shekaru suka ja. Ameera ita ta ɗan ragema Oum kewar Maanal a lokacin, har ALLAH yasa ta wuce karatu waje ita, yanzu haka tana can, amma tana gab da dawowa ƙasar haihuwarsa. Amisha ƴar ƙanwar Hajiya Shuwa ce, auren zuminci ne ita da Ameer, duk da kuwa su sukaga juna suka gina soyayyar su ba iyayen suka haɗasu ba. Farkon auren kowa nata yabon Amisha musamman data kasance da suffar mutane masu shiru-shiru da haƙuri, sai da tafiya tai tafiya sai komai ya canja, yanzu Amisha aya take gasama Hajiya Shuwa a hannu, har takai wataran idan ta juye kan Ameer ɗin sai ya manta da Hajiya Shuwa na a gidan ma tare da su gaba ɗaya. Sai ta dage da addu'a sai abin ya sassauta. Watanni kusan bakwai kenan abubuwa suka rikice a tsakaninsu shine kawai ta tattara ta wuce marocco sai jiya ne take dawowa, bata nan akai bikin su AA ɗin, sai bayan wucewarsu aiki ta shigo shine suketa hira da Oum ɗin dan ƙawaye ne sosai...       Baƙi da aka kira Hajiya Shuwa a waya cewar tayi ya sata tafiya gida, sai lokacin Maanal ta fito falon, tayi wanka abinta fes sai ƙamshi take. Takardar da aka basu a wajen aiki ta bama Oum ɗin, tare da zama gefenta ta ɗaura kanta a kafaɗarta. Shafa kan nata Oum tayi tana murmushi, cike da kulawa ta ce, “Ko azumin ya fara duka?”.       Shaf Maanal ta manta da ƙaryar azuminta, ta kalla Oum tana dariya. “Lah Oum ƙarya fa nayi dama babu wani azumi ɗazun ban son karyawa ne kawai”.        Idanu Oum ta zaro waje, sai kuma ta dungure kan Maanal ɗin tana dariya itama. “ALLAH ya shirya kin Baby na to da har yanzu bata canja hali ba”. Dariya itama Maanal tayi, tare da ɓoye fiskarta a jikin Oum ɗin. Itama Oum na cigaba da dariyarta ta ce, “To aiko tare zamu shiga kitchen yanzun nan idan munyi sallar zuhur”.          Haka ɗin kuwa akai, bayan Oum ta kammala duba takardun ta riƙe a hannunta akan zata nunama Abah, duk da dama ta masa bayani akan tafiyar amma bai ce mata komai ba. Salla suka je sukayi, koda suka fito kai tsaye kitchen suka nufa, sun fara aikin kenan Mamy da Hajiya Turai da Nurry suka shigo sashen. Oum ce kawai ta fita suka gaisa, basu wani jima ba Hajiya Turai tace bara ta wuce tunda taga Oum ɗin aiki suke itama zataje wani waje ne. Godiya Oum tai mata, sunzo zasu fita Maanal ta fito ta gaishesu. Tana kallon hararrata da Nurry take bata kula ba ta koma kitchen ɗin abunta. Sai da zasu fita Mamy ke faɗin, “Lafiya ƴarki ta dawo aiki da wuri haka yau?”.       “Lafiya Lau, daga office ɗin ne aka basu damar zuwa suyi shirin tafiya ne”.       Sai Mamy ta rasa ina zata kamo zancen tafiya kuma. Amma bata nema ba'asi ba dan tana son su fita su ƙarasa zancensu da suke da Hajiya Turai. Ba kuma tason ma Hajiya Turai ta fahimci bata san da zancen da Oum ɗin keyi ba dan yanzu ta gama cika mata baki akan batun dawowar Maanal a taxi. Ta nuna itace ta kafa sharaɗin sai dai Maanal ta hau taxi amma ba motocin gidan ba, shiyyasa sukaga hakan. (Mamy an iya ƙayya🤣🙏)     Tsulum Nuratu taja ta tsaya tana faɗin, “Momy bye nima zan zauna taya Oum girki, bara naje wajen sis.. Manaal ɗin”. Daga haka ta juya ciki ta nufi kitchen tabar su Oum na murmushi. Duk da dai abinda Nuratun tayi ya bama Mamy takaici, amma sai ta danne... Maanal na cikin aikinta ita da su Inte dake musu ƴan yanke-yanke a work table Nurry ɗin ta shigo. Ko kallon inda take Maanal batai ba, sai su Inte ne ke gaisheta a girmamame, itako tana amsa musu a yamutse. Sun riga sun san halinta shiyyasa basu wani damu ba. Dai-dai nan Oum ta dawo, dan haka Nuratu ta nufi wajen Maanal cike da makirci tana faɗin, “Sis.. Maanal mizan tayaki da shi?”.         Wani shegen murmushi kawai Maanal ta saki tana kallon Nurry ɗin a tsakkiyar ido, a zuciyarta faɗi take, (Yarinya ai indai makirci ne baki yar a ƙasa ba, idan kuma kikace ni dake ta haka zamu buga wasan ƙasa zaki sha kuwa a hannuna). A fili kam maimakon bata amsa fruits da za'a gyara ta nuna mata da hannu fiskarta da murmushin har yanzu. Oum data ƙaraso inda Maanal ɗin take ta ce, “Yauwa gyara su kam Nuratu, sai a gama da wuri dan yau nasan Auta a jigace zai dawo gidan nan ba'a aika abincin rana ba hira da Hajiya Shuwa ta ɗauke min hankali”.........✍️        _Hhhhh gaskiya Maanal baki ƙyauta ba, ya zaki bama Nurry ɗinmu gyaran fruits 🤣🤣_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [25/04, 5:11 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣2️⃣ ______________ ........Matuƙar tiƙe Nuratu takaici yayi, amma bata da damar cewa bazatai ba tunda itace ta kawo kanta. Sannan duk iskancin nan nata mugun shakkar Oum take ji, sosai matar na mata bala'in kwarjini, ga son da kowa yasan AA na mata tana son tai kamun ƙafa da ita. Kai bama ita ba, ko iyayen nata kan faɗi irin cika musu idon da Oum ɗin keyi, dan duk yanda suka shirya tunkararta da rashin mutunci suna yin arba da ita komai ke ƙwace musu. Cike da son ƙular da Nurry Maanal ta shiga yima Oum hira suna dariya. Aiki sosai Nuratu ta shaƙa, dan ji ta dingayi kamar ta juya ta caka ma Maanal wuƙar hannun nata.        Sunata aikinsu da hira, dan Maanal ma dai ke girkin Oum hira kawai take tayata, Nurry kuma anata aikin gyara fruits da take yi cikin takaici shiyyasa bata wani sauri, koda yake ba aikin ta iya ba dan bayi take ba sam. A gida komai masu aiki ne ke mata shi, idan iskancinta na ka ma hatta underwears ɗinta basu take su wanke sai tace matching baya wankewa da ƙyau. Su Inte dai sun gama sun gyara wajen sun fita suna gyaran falo da saka ƙamshi. Dai-dai nan AA ya shigo da sallama. Da sauri Nurry ta juya har tana neman yankewa da wuƙa, sai Oum da itama ta juya tana masa murmushi. Maanal kam tamkar batana san mike faruwa ba aikinta kawai take yi.         “Lallai yau Auta ne da tashi a office ko five baiyi ba ma?”. Oum ta faɗa tana miƙa masa ruwan data tsiyaya masa a cup. Amsar ruwan yayi, tare da jan kujerar work table ɗaya ya zauna. A kasalance ya janye idanunsa dake akan ƙullin da Maanal tai ta bayanta na rigar girki dake jikinta. Kamar wanda baya so ya ce, “Oum na gaji ne ALLAH shiyyasa na gudo”.        Murmushi kawai Oum ɗin tayi, dan tasan ba hakan bane ba, ta tabbata dan Maanal ta dawo ne. Cike da ɗan rawar murya Nuratu data tsaresa da kallo ta shiga gaisheshi. Ikon ALLAH, to shifa sai yanzu ma yasan akwai wani a kitchen ɗin bayan Oum ɗinsa da Maanal. Waiwayowa yay ya kalleta, sai kuma ya ɗauke idanun a taƙaice ya amsa, cikin kuma halin ko'in kular nan nasa kai kace baima gane Nuratun ba. Oum da bataji daɗin yanda yayma Nuratun ba tace, “Nuratu ce fa baka ganeta ba ne Auta?”.       “Na ganeta mana Oum! Nifa yunwa nake ji”.   Sarai Oum ta fahimci zancen Nuratun yake so a kawar, dan haka ta girgiza kai kawai da juyawa ta kalla Maanal dake ta aikinta. Juyowa tai ta kalla AA kuma, sai taga ya zubama Maanal ɗin ido ne a kaikaice. A take Oum ta fahimci akwai abinda ke faruwa a tsakaninsu, dan da wuri take gane idan sunyi faɗan nasu. Nan ma kanta ta ɗan girgiza, batare da tace komai ba ta buɗe ƙaton freight ɗin kitchen ɗin ta fiddo kwalin fresh milk, a gabansa ta ajiye tana faɗin, “Fara da wannan ga Baby nan na mana girki an kusa kamallawa”.         Idanu ya waro waje, “Kai Oum ana dai mana jagwalgwalo, miyasa baki mana da kanki ba?”.      Dariya Oum tayi, ta nufi hanyar fita tana ƙoƙarin ɗaga wayarta dake ring, ta ce, “Oh jagwalgwalo ko? Babyn ce ke jagwalgwalo! ALLAH yasa ta hanaka abincin nan mu gani”. Ta fice batare data jira mizai ce ba. Shima bai ce komai ba, sai ma ajiye kofin fresh milk ɗin daya ɗauka zai fara sha yay ya miƙe. Nuratu da gaba ɗaya jikinta ke wani irin tsuma, tana jin kamar ta daka tsalle ta rungumesa take ji ta bisa da kallo, duk da tun kwalliyar safe ce a jikinsa yama cire jacket ɗin samna suit ɗin sai fara tas ɗin long sleeve shirt dinsa dake clean harda karin gugarta kamar yanzu ya sakata wani irin ƙyau yay mata, ga ƙamshinsa mai saka kasala na tashi kamar a yanzu ne ya saka turaren.       AA kam ko kallon inda take baiyi ba, hankalinsa kwance, kansa kuma tsaye ya ƙarasa inda Maanal take ya tsaya dab da ita. Ita ko da yake ta juya masa baya bama tasan da zuwansa wajen ba, tadai ji yawaitar ƙamshin turarensa sosai. Hannayensa duka biyu ya zagaya a saman cikinta ya rungumota, tare da ɗora kansa a wuyanta duk a lokaci guda. Harga ALLAH tsorata tayi, dan haka tai wata ƴar zabura tana ƙoƙarin juyowa. Amma sai ya sake riƙeta da ƙyau ta yanda hakan ya gaggareta.         “Ni kika wulaƙanta kika tawo a taxi ko? Ki saurari hukuncina dan sai na saɓa miki”. Ya faɗa a cikin kunnenta cike da isa babu alamar wasa a furucinsa. Amma irinsu Nuratu dake a gefe sai su ɗauka wata maganar soyayya yay mata a kunnen, dan daya gama faɗa harda su manna mata ƙaramar sumba a kan wuya ya ƙara faɗin, “Ai dama kinfi kama da Kukun”. Haushi ya saka Maanal ɗaga ludayin hannunta kamar zata ƙwala masa saboda yace tafi kama da kuku. Sakinta yay yaja baya yana murmushin ƙeta na cin nasarar ƙular da ita, dai-dai ta juyo gaba ɗaya yay mata gwalo kuwa, zaburowa tai kansa da ludayin. Aiko da ɗan gudu ya ɗauka fresh milk ɗinsa ya fice a kitchen ɗin yana dariyar data saka Nurry yin sumar tsaye dan mamakinsa da al'ajabi da yanda dariyar tasa tai bala'i bala'in tafiya da imaninta. Dan zata iya rantsewa bata taɓa ganin yana dariya kamar haka ba a rayuwar sanin datai masa kaf. Bawai yana ƙyaƙyalƙyalawa bane sosai a yanzun ma, amma illahirin haƙwaransa sun bayyana a waje. Oum dake shigowa itama tana dariyar yanda AA ɗin ya fito a kitchen ɗin da ɗan gudu ce ta riƙe ludayin Maanal, tana dariya ta ce, “Amasa haƙuri babyna bazai ƙara ba”.      Cike da shagwaɓa Maanal ta ce, “Oum gwalo fa ya min, yace nafi dacewa da kuku, kinga yana sake yimin gwalon ko”. Tai maganar tana nuna bayan Oum da AA yake tsaye daga can waje. Juyowa Oum tai ta kallesa itama, sai ya haɗe fuskar kamar bashi ke yin tsokanar ba. Oum data tabbatar yayi ɗin ta ce, “Okay na bari ta kwale ka ko”.         “Tadai fasan kai Oum, kuma dan ALLAH kinga na kulata tunda na shigo?”.      “To ya zan sani tunda fita nayi, sai dai a tambayi Nuratu.” Oum ta faɗa. Maanal ce ta amshe da faɗin, “ALLAH Oum yayi, kuma a tambayi Nuratun ma ai tana ganinsa”.      Ai kafin ma Nuratu da takaici ya kume tsigar jikinta har wani tashi take yi tayi magana ya sake ma Maanal gwalo yabar wajen. Karaf kuwa a idon Oum. Salati Oum ta ɗauka da faɗin, “ALLAH ya shiryaka Auta ka daina tsokalar min yarinya kaikuwa. Sai kuma ta kama hannun Maanal, kinga manta da shi zaki rama ne, badai zai dawo cin abinci ba taron dangi zamu masa harda Fawzan in ya dawo”. Daga haka suka koma Oum ta tayata suka ƙarasa girkin aka bar Nuratu da takaici. Gashi babu damar barin kitchen ɗin kuma. Dole ta haƙura suka kammala ikin duka suka shirya a dining sannan suka tafi salla. Sanin AA nan zai dawo yasa ta maƙale abinta, acewarta sai ta sake ɗaura ɗammara na maganin Maanal ɗin, hakan kuma bazai faru ba sai ta nutsu ta fahimceta....     ________★       Shagali sosai aka sha a gidan Sen.. Bukar, sai dai shi gaba ɗaya hankalinsa nakan Rabilu ne dan ya fahimci akwai magana a bakinsa. Duk kuma yanda yaso su kebe da Rabilun hakan ya gagara, dan uwargida yau tayi masa kane-kane. Kuma tsaf ta fahimci inda hankalin nasa yake dan haka taita dariya a ranta. Zuwa yanzu babu abinda bata sani ba game da Maanal. Tun sanda mijin nata ya kawo mata batun ƙara auren nasa ta shiga bincike da bibiyarsa har sai da ta gano akan wadda yake rawar ƙafar. Da farko ta shirya tsaf domin nakasa rayuwar Maanal ɗin, dan ta ɗaukama kanta alwashi wata bazata sake shigo mata gidan miji ba, wanda suke a cikin ma tana shirin ficewarsu ne. Sai kuma UBANGIJI mai hikima ya nuna mata ikonsa rana tsaka ta samu labarin auren Maanal ɗin da AA Darma, yaron data taɓa ji a bakin mijin nata yana aibantawa da ɗaukar alwashin wulakanta rayuwarsa saboda yafi su kusanci da shugaba ƙasan. Dariya sosai sukaci ita da ƙawayenta masu ɗaurata a hanya, dan ita babu abinda ya dame ta da wata matsalar mijinta da AA Darma, ita AA Darma ma ya biyata a yanzu tunda ya ɗauke Maanal. Farin cikin wannan aure yasa ta shirya wannan liyafar ta Anaversary ɗinsu, abinda bata taɓa yi ba kuwa. Shi kansa Sen yayi mamaki, amma sai shanye a ransa yana faɗin (Hakan dai bazai hana ƴar shilata Maanal shigowa ba).       Bayan an gama shagali yanda ta kanainaye shi dole ya haƙura, dan ya ma nema Rabilu ya rasa. Bai san ita ta kora Rabilun ba dan dama ta mugun tsanarsa saboda tasan shine mai nema masa matan auren kuma kawalinsa na matan banza. Ta jima da son rabasu sai dai hakan ya gagara....       “Sen... Namu”. (ALLAH sarki Uncle ɗina KA BARI YA HUCE MAI RABON YA ƊAUKE🤣)           __________★       Daga sashen Oum AA sashen Mamy ya nufa domin gaisheta, dan ƙa'idarsa ce yin haka daga shi har ƴan uwansa. Da safe zasu shiga su gaisheta, hakama idan sun dawo aiki, sai dai da wahala kaga sunyi zaman mintina ashirin a wajen nata. Saboda tun farko bata jasu a jikinta ba, ita a dole tanama Oum kawaici. Wanda sai daga baya AA ɗin ya fahimci ba hakan bane ba...       Zaune ya sameta a falo Haule na gyara mata ƙumba suna kallo, glass bowl ne a gabanta tana shan fruits da aka yanka ƙanana a ciki. Cike take taf da haushin zaman Nuratu a sashen Oum. Da sauri Haule ta shiga gaisheshi. Batare daya kalleta ba ya amsa ciki-ciki yana kaiwa zaune a kujerar kusa da Mamyn, ganin yanda taketa faman ɓata fuska ya sashi yin murmushi a zuciyarsa. Shi wlhy wani lokacin yanda ta saka kanta a ƙunci babu gaira babu sabar tausayi take bashi. Da ace zata ajiye makanamta dai zata kasance cikin farin ciki ne da nishaɗi ta kuma samesu fiye da yanda take so su da take faɗan a kansu. A hankali ya matsar da jikinsa kusa da ita gab, batare da yayi magana ba ta zare spoon ɗin dake hannun nata ya ɗauka yanka ɗaya na apple ya kai mata baki. Ƙuri tai tana kallonsa kamar wadda ta suma. Domin abune da bai taɓa kwatanta yimata ba sai dai taga yanama Oum. Shi kuma ya ɗauka aniyane a ransa na canja salon mu'amularsu ko hakan zai sassauta zuciyarta ta ajiye makaman yaƙinta akan Oum, dan baya fatan wani a gidan ya fahimci halayyar nan ta Mamy. Ganin yanda take kallon nasa tamkar hawaye na son taruwa mata a ido ya sashi jinjina mata nasa kan tare da sakar mata murmushi mai sanyi, sai kuma ya ɗan buɗe bakinsa alamar (haa). Kamar sakarai a hankali ta buɗe lips ɗinta kuwa ya saka mata yankam apple ɗin, ta shiga taunawa tana kallon nashi. Sai ta samu kanta itama da amsar spoon ɗin ta ɗauka kankana ta bashi. Babu musu ya amsa yana mata murmushi, kafin ƙasa-ƙasa ya furta,.....✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [28/04, 3:28 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣3️⃣ ______________ .........“Jazakhallahu khairan Amaryar Abah, aminiyar Oum, Maman Fadeel da Fawzan da Auta Ajwaad”. Yanda ya jero kalaman nasa masu kama da kirari ya sata sakin murmushi a bazata, sai kuma a hankali takai hannunta ta shafa kwantaccen gashin fuska tana sakin murmushi mai haɗe da ƴar dariya. Samun kansa yay shima da yin dariya, ya kama hannun nata ya sumbata. Ji Mamy tai tamkar zuciyarta na ɓaɓɓarewa gida biyu, cike da shauƙi mai girma ta sake kai hannun nata saman sumar kansa ta barbaza. Nan ma dariyar yay mata. Tare da faɗin, “Thanks you Mamy. Dan ALLAH ki daina damuwa akan komai, nafi son kullum nazo naga fuskarki cikin farin ciki. Na tabbata kuma idan kika ajiye komai zaki samu fiye da haka. Bakiga Oum ba, koda yaushe tana cikin farin ciki, saboda tana da ƙoƙarin ɗaukar jarabawa da sauƙi. Mamy muna sanki kamar yanda muke son Oum, yanda kuke treating ɗin rayuwarmu ne ya banbanta. Dan ALLAH ki ajiye komai kinji Mamyna”.         Kanta kawai ta jinjina masa, duk da kalamansa sun mata daɗi matuƙa a zuciya wani yanki na cikinsu sun mata zafi da ɗaci, ba komai ya kawo hakan ba kuwa sai jingina Oum da yayi a ciki har yana nuna mata yin koyi da ita. Cikin basar da komai ta ce, “ALLAH ya shige mana gaba Ajwaad! Kaga Nuratu?”.       “Amin ya rabbi, na ganta tana sashenmu”. Ya bata amsa a tausashe cikin danne komai, dan harga ALLAH ko sunan yarinyar nan baya son yaji ta ambata masa. Cikin tausasawa Mamyn ta katse masa tunani da faɗin, “Ajwaad kaga dai komai kace zan yisa domin samun farin cikinka, kaima ina son ka kula da Nuratu domin samun farin ciki na a ɗan zaman nan da zatayi da mu na azumi, Hajiya Turai ce zata umrah shiyyasa ta dawo nan ta zauna. Idan ka kwantar da hankalinka zaku fahimci juna a ɗan zaman nan da zatayi kafin bikinku. Ajwaad Nuratu na sonka sosai, irin son da duk yanda ka taƙwanrata zata maka biyayya, bar ganinta haka a tsaitsaye tana da hankali, gata ne kawai da Hajiya Turai ke mata na tsiya ya mata yawa. Amma nasan kai ɗin jarumi ne, zaka gyarata a yanda kake so yarona”.      Kansa kawai ya jinjina mata, dan baya son raunana mata zuciya, sannan yana son binta da wannan salon ko ALLAH zai taimakesa ta canja. Itama dai kusan tunani iri ɗaya sukeyi, dan tana ganin AA ɗin ya amshi batun nata da muhimmanci a yau, dan haka zuciyarta gaya mata take lallai tana da buƙatar canjawa, canjawa irin wadda Ajwaad ɗin keso kodan samun nasara a kansa, dan ta ƙarfin tsiya tabbas bazata taɓa samunsa ba, tunda ta gwada hakan tsahon shekaru kenan babu wani canji saima caɓulewar abubuwa. Ita dama bata jin su Fadeel, a ganinta duk a tafin hannunta suke. Ajwaad shine uban taurin kai da kafiya, sannan shine baisha nn ɗinta ba, zaifi mata wahalar janyewa fiye da su Fawzan da suka sha daga jikinta bayan dakon ɗaukar ciki dana haihuwa. Dan bazatace raino ba wannan kam Fateema tayi tare da cin kashinsu da fitsari. Dan in har batai ƙarya ba zata iya irga adadin wanke musu koda kashi da fitsari ne, shima sai in Oum ta fita wani uzirin ne ma.        AA nason tashi ya tafi sashensa ya watsa ruwa amma hirar da Mamy ke jansa da ita cike da farin ciki yasa ya haƙura ya zauna har akai kiran magrib, ƙarshe alwala ma catai yaje ɗakinta yayi. Haka kuwa ya haura saman yayo duk dan sanyata a farin ciki. Daya fito taita sanya masa albarka jitake kamar kada ta barshi ya tafi, sai dai hakan ya zama tilas babu yanda ta iya. Bayan fitarsa da wannan farin cikin ta kasance, tana idar da salla kuwa ta kira Maman Saheeba ta sanar mata komai. Suna yanke wayar daga can Maman Saheeba tace “Ina yaya Kamila bazai yiwuba, lokacin samun irin wannan farin cikin naki baiyi ba, ai idan har na bari kikai nasarar jawo Ajwaad jikinki to tabbas aurenshi da Nuratu bamai yiwu bane ba, nasan halin MAKIRIN yaron nan, tsaf zai juya miki tunani da hatsabibancin sa, dan yafi sauran ƴaƴanki taƙadaranci kema kina faɗar hakan da kanki. Kansa a buɗe yake matuƙa da sanin duniya, in har ba a yanayin da kuke ciki a baya ba lallai zai botsare ne”. Nanfa ta shiga kai-kawo na neman mafitar hanyar ɓata komai....      ★Ana idar da salla AA dole gida ya dawo domin yin wanka kafin isha'i, tunda Mamy ta cinye masa wancan lokacin. A tare suka shigo da Ya Fawzan, babban yaya bai dawo gidan ba har yanzu. Sashen Mamy Fawzan ya nufa domin gisheta, shi kuma AA ya nufi nasa sashen dan yin wanka.        Bayan Fawzan ya gaida Mamy zai tashi sai ta ɗakko masa hira, mamaki ne ya kama shi, dan sam babu hakan a tsakaninsu tun suna yara. Tsakaninsu da Mamy umarnine nayi ko bari kawai sai gaisuwa. Amma batun shaƙuwa ko hira ko wasa da dariya Oum ce kawai ke musu da Abah. Daurewa yay yana amsa mata sama-sama, tsulum sai ga Saheeba da yara, da yake fita tayi Mamy bata kawo komai a ranta ba. Dan sai yanzun ne suke dawowa, zama Anum tai a jikin Fawzan tana masa labarin inda zukaje, yayinda Naufal ya nufi Mamy, a mamakin Mamyn sai Saheeba ta nema wajen zama tana faɗin, “Washa Mamy na gaji”.      Murmushin yaƙe Mamyn tai mata kawai da sannu a taƙaice dan harga ALLAH batayi murna da zaman Saheeba ɗin ba, dan zuwanta ya katse mata kasancewa da Fawzan. Kiran sallar isha'i ya saka Fawzan miƙewa ya ajiye Anum data fara barci saman gadon Mamy, cike da kulawa yace ma Naufal, “Tashi muje massallaci my boy”.       Da kallo Mamy da Saheeba suka bisu, suna gama fita Saheeba ta saci kallon Mamy ta gefen ido. Baki ta taɓe kaɗan, sai kuma ta ƙawata fiskarta da murmushi dan kaf MAKIRCIN Mamyn ta iya itama. “Lah Mamy wai ina ƴar hutun taki? Banji motsimta ba”. Ta faɗa baki a washe.      Miƙewa Mamyn tayi, sai kuma a ɗan yanayin jin haushi ta furta, “Tana sashen ƙanwar uwarta Fateema”.     Cike da mamaki Saheeba tace, “Tomi ya kaita can Oum?”.       “Oho mata”.    Mamyn ta faɗa cike da takaici tana kabbara sallarta. Harara Saheeba ta dalla mata cike da jin haushi ta fice a ɗakin zuwa nata sashen....      ★Nuratu dai tunda aka idar da sallar magrib ake dakon dawowar AA sashen, sai dai kuma taji tsitt. Sai faman hararar Maanal dake karatun Alkur'ani takeyi, itako bama tasan tanai ba. Lokacin isha'i yayi suka gabatar, suna idarwa Maanal ta shiga bayi da nufin yin wanka. Hakan da Nurry ta gani itama sai ta fito ta nufi sashen Mamy. Oum ca take ta tafi kenan, sai take cemata ya zata tafi bataci abinci ba. Batare data tsaya ba tace, “Oum ina zuwa yanzu zan dawo”. Daga haka ta ƙarasa ficewa da sauri. Sanda Nuratu ta koma sashen Mamy bata sani ba, sai da ta fito cikin kwalliya da uban ƙamshi daga ɗakin data sauka sannan Mamy ta ganta. Harara ta zuba mata, zata fara mata faɗa tai saurin rungumeta tana faɗin, “Mamy ki fahimceni, na zauna ne dan nayi maganin shegiyar can, kin san kuma Ya AA ma acan yake, dole na nema mana kusanci ai. Yanzu ma komawa zanyi. Sai na dawo”. Daga haka bata jira cewar Mamy ba ta fice a sashen. Sai Mamy ta samu kanta da sauke ajiyar zuciya kawai, ita kanta rawar kan da Nuratu keyi akan Ajwaad na damunta, dan tasan halinsa baya son mace a haka...        A falo Nuratu ta sami su Oum, Maanal na zaune a ƙasa ta baje takardu da laptop tana aiki, sanye take da simple riga mara nauyi tashan iska milk color, sai veil ɗin rigar siriri data naɗa a kanta, ɗan zamawar da yay baya ya bama kwantaccen gashin goshinta damar fitowa. Sam babu ɗigon kwalliya a fuskarta, babu alamar ma ta shafa mai dan fuskar tai irin fayau ɗin nan. Hatta lips ɗinta a ɗan bushe suke kaɗan. Sai ƙamshi mai sanyi dake fita ƙasa-ƙasa. Gaba ɗaya sai Nurry tai sororo tana kallon ta, dan tayi tsammanin zata dawo taga Maanal ɗin ta caɓa kwalliya ne kamar mai shirin fita waje. Amma sai ga akasin hakan.         Itako Maanal ɗin ma kallo ɗaya datai ma Nurry ɗin sai ta bata dariya. Kwalliya fa ta ciwo sosai abinta. Anci uban shadda da yaji aikin stones sai ƙyalli suke. Kwalliya sosai a fiskarta harda lipstick ja da brawn sama gira tasha jagira, gashi ido a tsaitsaye an baza masa maskara a hakan ma na ƙari ne dan sunyi dogaye sosai. Anci ɗaurin ture kaga tsiya harda ɗan karkatashi gefe akai. Ƙamshi kam ba'a magana duk ta bulbule falon. Ita Maanal ma sai ta bata dariya, a zuciyarta tace (Aiki ja) a fili kam murmushi ta saki mai sanyi hankalinta a aikinta bazaka taɓa cewa da Nuratun take ba.        A haka babban Yaya da sai yanzu ya shigo gidan ya samesu. Shi kansu sai da ya kalla Nuratun da ƙyau, ganin kallon da yake mata ta shiga gaisheshi. Amsa mata yay da kulawa tare da tambayarta mutanen gida. Dan shi a zatonsa ma yanzu ne tazo shiyyasa. Sannu da zuwa Maanal tai masa, tare da gaisheshi. Itama ya amsa mata da kulawa yana tsokanarta da cewar “Lilly yau kuma aikin office ɗin ne har a gida haka?”.     Fuskar Maanal da murmushi ta ce, “Yaya ina ragewa ne, saboda yau na taso aiki da wuri”.        “Masha ALLAH haka ake so, ai gara kada ki koya over time ɗin tsiya ɗin nan na Auta”.        Sosai Maanal tai ƴar dariya tana nufar freight ɗin dining da faɗin, “Ai bazan koyaba Babban Yaya”. Dai-dai nan Oum ta fito daga hanyar upstairs. Itama dai kallon Nuratun tayi da ƙyau sai kuma ta janye ta maida kan babban yaya tana murmushi irin na manya. Ruwa Maanal ta miƙama Babban Yaya ya amsa yana sanya mata albarka, cike da farin ciki ta gyaɗa masa kai ta koma wajen zamanta ta cigaba da aikinta. Shi kuma suka fara gaisawa da Oum. A haka AA da Fawzan suka shigo sashen. Zama duk sukayi, cike da iyayi Nuratu tai musu sannu, sai kuma ta miƙe ta nufi freight kamar yanda taga Maanal tama babban Yaya suma ta ɗakko musu ruwan. Fawzan ne kawai yace mata “thanks”, shima kuma rabin hankalinsa naga duba takardun Maanal datai zane daya ɗiba yana kallo. AA kam ko kallon ma inda take baiyi ba, magana suke da babban Yaya ƙasa-ƙasa. Koda Babban Yaya ya miƙe Oum tace ya bari suci abinci tukkunna tunda Saheeba sai daren nan ma ta dawo gidan shi kuma yace ya gaji kwanciya zaije yayi yau bazai dawo hira ba AA bai tashi ba har sai da su dukansu suka isa dining ɗin. Maanal ma dai tana haɗa takardunta ne. Ita bama tasan AA ɗin bai tashi ba, sai da ta yunƙura zata miƙe suka haɗa idanu. Harrarta yay ita kuma ta taɓe baki. Dan tasan bawai ya daina jin haushin nata bane daman, ko ɗazun saboda ganin Oum ne.      Bata sake kallon inda yake ba ta nufi dining ɗin, sai lokacin shima ya miƙe. Kujerar kusa da Maanal ɗin yaja ya zauna, Fawzan dake kallonsa cike da neman tsokana ya wani ɗage masa gira ɗaya. Harararsa AA ɗin yayi ya ɗauke kai. Shima Fawzan ɗin sai yay gyaran murya, kallonsa duk sukai, sai kawai ya basar. Babban Yaya daya san halin tom and jarry ɗin ƙannen nasa kansa kawai ya girgiza, dan ya tabbatar da AA Fawzan ɗin yake. Kowa zai fara ƙoƙarin zuba abinci karaf Nuratu ta miƙe acewarta bari ta saka musu. Babu wanda ya hanata, dan haka ta fara zubama Oum, sai babban yaya da Fawzan, gaban AA ta dawo har tana ɗan duƙo masa wai zata ɗauki plate. Wani irin zafi ne ya turniƙe zuciyar Maanal, shiko AA ɗin ma hankalinsa ba'a nan take ba, waya yake latsawa, tabbas yana jin ƙamshin turare mai ƙarfi a kusa da shi, amma baima san na wanene ba duk da ya fahimci baƙon ƙamshi ne bai taɓa jinsa a wajen kowa ba a gidan. Nibras ce ta shigo da sallama a cikin tata kwalliyar.........✍️ _Maanal tamu kenan, gaki kuma a tsakiyar kuraye😂, bari muga yaya wasan zai kaya🏃🏃🤣_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [28/04, 3:28 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣4️⃣ ______________ ........Cikin ladabin son birge AA ta shiga gaida Oum, da kulawa Oum ɗin kuwa ta amsa mata tana tambayarta yaya aikin?      “Alhamdullah Oum, tumma ɗazun na tashi na biya ta gida ne ganin Mom da tace ƙafanta na ciwo”.     “Wayyo ashsha ALLAH ya bata lafiya, yaya jikin nata?”.     “A Alhamdullah da sauƙi sosai, bama a kwance take ba”. Ta faɗa tana harrar Nuratu dake zubama AA abinci, tunda ta shigo akanta idannunta suka fara sauka, ji tai kamar ta shaƙo shegiya, dan tayi ma mamaki ubanmi ya kawota gidan. Maanal da itama dai ta shaƙa ɗin da iskancin Nuratu amma ta fiske babu wani alamar komai a fuskarta atare ita da babban yaya suka jajantama Nibras ɗin batun jikin mamanta. Sai Nuratun itama tayi mata jajen. AA dai kamar ma bai jisu ba sai da Oum ta kallesa, a taƙaice batare daya ɗago ba ya ce, “Sorry ALLAH ya bata lafiya”. Cike da sanyaya lafazi Nibras ta amsa, kallonta Maanal tayi ta gefen ido, dan bata sani ba ko ita kaɗaice ta fahimci Nibras ɗin ta canja murya wajen amsa AA ɗin. Sai ko amamakinta taga hankalin Nibras gaba ɗaya akan AA yake. (ikon ALLAH) Ta faɗa a ranta, a zahiri kam kamar ma bata san mike faruwa ba a wajen. Sai ma Nuratu data kawo hannu zata zuba mata itama, fuskarta da murmushi ta girgizama Nuratun kai murya ƙasa-ƙasa ta ce, “No barshi ma na Besty zai ishemu”. Tai maganar tana ɗaukar spoon ɗin da Nurry ta sakama AA, ita kuma ta ɗauka wani ta saka masa.      Idan Nuratu tace bataji kamar ta shaƙo wuyan Maanal ba tayi ƙarya, dan tuni annurin daya cika fuskarta sanda take zubama AA ɗin abinci a yanzu ya ɓace ɓat. Ɗauke kai Maanal tayi kamar bata ganta ba, sai ma kai hannu da tayi ta zare wayar AA ɗin ta ajiye a gefenta. Ɗagowa yay ya kalleta, itama kallon nasa take, dan haka suka ɗan zubama juna idanu har sai da Fawzan yay gyaran murya. Maanal ce ta fara janye nata cike da basarwa ta ɗauka spoon ɗin ta fara cin abincin, shiko yaƙi daina kallon nata. Fiiiyyy Nuratu tabar wajen ta koma wajen zamanta, Nibras ma sai da taji ƙwalla sun cika mata idanu. Zuciyarta raya mata take anya bazata kashe Maanal ba a gidan nan wataran. Dan sam idanun AA basa iya ɓoye abinda ke cikin zuciyarsa game da ita. Jitai gaba ɗaya abincin ya fitar mata a rai, amma tasan tana ƙin ci Oum zata dameta da tambaya ita da Fawzan.        Duk abinda kowa keyi Oum na karance da shi. Oum ta jima tana auna abubuwan da Nibras kema AA, musamman idan ta shagaltu da kallonsa ko idan tana masa magana. Sai dai duk da abinda zuciyarta ke fassara mata takan ture hakan a ranta. Amma a kwanakin nan sai irin kallon da take jifan Maanal da shi ke tsaya mata a rai, dan kallon yana kama da irin kallon kishi da jin zafi. A ganinta ko kishi ne irin na facalanci bai kamata a yakasance haka ba, dan kishin facalanci ga wanda ya saka kansa kusan na hassadar mijinki yafi mijina ne, ko mijinki yafi miki hidima fiye da nawa. Abu na ƙarshe yanda sam Nibras bata acting irin na matar gida ga mijinta a wajen Fawzan. Fawzan kullum a nan sashenta yake cin abinci safe da yamma, weekend harda na rana, itama kuma nan ɗin take zuwa taci. Sannan ko zaman cin abincin akai bazata tashi ta zuma Fawzan ba, sai dai ya zuba da kansa. Kai zasu iya zaman awa biyu a sashen ma bakaga sunyi magana da juna ba, amma idan AA na nan da yayi magana ko bada ita yake ba zata saka baki. Idan kuma har AA baya sashen ko yay tafiya to bazaka ƙara ganin Nibras a sashen ba. (Ya ilahil alamin, ALLAH kada kasa abinda nake hasashe akan yarinyar nan hakane. Lallai data cika mara hankali kuwa, da auren Fawzan a kanta ta ringa jin son wani namiji, namijin ma ɗan uwansa. Kai kai wannan kwamacala basa fatanta kuwa koda a mafarki).. shigowar Saheeba da yara ya katse Oum daga tunani, fuska cike da murmushi ta kamo su Naufal jikinta, Saheeba kuma ta zauna tana gaisheta. Itama dai abincin ta zuba, Oum ta girgiza kai kawai. Wannan lalace na surukansu na bata mamaki, matsayinsu na tsoffi su basu dafa sun kawo musu ba, sai dai kullum suzo sashensu su ci. Koda yake nan ɗin ma dai ne suke zuwa, dan ita Mamy bata ɗauka ma kanta hakan ba. Hasalima faɗa take akan ya kamata Oum ɗin ta taka musu birki. Itako sai dai tayi dariya kawai dan bazata iya ba, koba komai da yaranta su wahala da rashin abinci daga matansu gara suzo nan su ci ɗin hankalinta zai fi kwanciya.      Kowa nata cin abincinsa hankali kwance, sai dai hankalin Saheeba, Nibras, Nuratu, duk akan AA da Maanal ne, yayinda su kuma hankalin baya kan kowa, abincin su suke ci kawai a plate ɗaya, ƙasa-ƙasa AA na takalarta wai abincin babu wani daɗi. Itako tana harararsa ƙasa-ƙasa batare data tanka masa ba. Sai da ya isheta ne takai hannu ta ƙasan table ɗin ta mintsinesa. Idanu ya ɗan rumtse tare da cije lips dan yaji zafi, kafin yasa shima nashi hannun ta ƙasan table ɗin ya riƙe natan dake mintsininsa, tayi-tayi ta kwace yaƙi saki, dole ta haƙura. Shi ko ya cigaba da murza hannun dan wani irin laushi da santsi yake masa. Yanda yake mirza hannun sosai tsigar jikin Maanal ke tashi, amma ta dake abinta..         Abinda Maanal bata sani ba tuni ƴan sa'idonsu sun fassara abinda hannayensu keyi a ƙasan table, musamman daya kasance lokacin da Maanal ta mintsini AA ya lumshe ido da cije baki. Itama kuma yanayinta ya canja da ya kama hannunta yana murzawa. Su duka ukun zukatansu yi suke kamar zasu babbake. Yayinda sam babban Yaya da Fawzan da Oum su basu san ma mike faruwa ba. Hasalima hirarsu sukeyi. Rashin saka bakin AA a hirar kuma sun san wannan normal ne daga halinsa. Ba kowace hira bace zakaji bakinsa sai idan yaso tankawa, balle ma su Saheeba na wajen, kowa yasan baya hira da su, daga gaisuwa babu abinda ke sake shiga tsakaninsa da su..         AA neman harmutsama Maanal jiki yake, dan haka babu shiri ta miƙe tana fisge hannunta wai ta ƙoshi. Kallonta Oum, Babban Yaya da Fawzan sukai, yayinda AA yay wani shegen murmushi yana cigaba da cin abincin sa. Murmushin nasa ya ƙara tabbatar ma da ƴan saka ido abinda suke hasashe, ta wani gefen kuma ya motsa zukatan Nuratu da Nibras dan abune da basu saba gani ba. Lallashin Maanal Oum keyi akan ta ƙara ko kaɗan. Cike da shagwaɓa tace, “ALLAH Oum da gaske na ƙoshi zan yi amai idan na ƙara”.        A mamakin kowa sai ji sukai AA yayi ƴar dariya. Shagala matan sukai a kallonsa, dan har Saheeba ma dai mamaki ne ya dabaibayeta wai AA da dariya. Babban Yaya kam murmushi yayi, zuciyarsa fes da ganin farin cikin Autansu nata dawowa. Fawzan kuwa tsokanar tasa daya saba yayi. Yayinda Maanal ke kallon Oum kamar zatai kuka.         “Oum kin ganshi yana mun dariya ko”.     Kallonta AA ɗin yayi, “Kefa matsalata dake sharri Besty, shike nan bazanyi dariya ba, to inba tsargar kai ba mi kikayi da zan miki dariya?”.      Harararsa tayi, fuuu tabar wajen. Dariyar ya ƙara sanyawa, cikin ɗan ɗaga murya yace, “ALLAH ya raka taki gona”.       “Amma fasa tafiyar to”. Manaal ɗin ta faɗa tana dawowa. Sai dai kujerar gefen Oum ta jawo ta zauna yanzu. Hatta Oum dariya takeyi, hakama Babban Yaya da Fawzan. Su dai matan da alama abin haushi ma ya basu, dan kowacce ta ɗauke kai. Cike da lallashi Oum tace, “Kinga ƙyaleshi Babyna, ya kamata zuwa yanzu ki saba da halin Auta, dan yaga ma kina fushi shiyyasa yake tsokalarki. Kin bari yaga lagonki ne, amma ki bari muma zamu gane nasa ai”.         Gwalo Manaal ta masa tare da kashe ido ɗaya. Sai ya haɗe fuska yana harrarta. Akan lips ya furta, “Zan kama ki ne ALLAH ya kaimu Chaina”.       Tsaf taga abinda ya faɗa, dan wannan sigace da sukema juna magana a baya idan basa son wanda ke kusa da su ya fahimta. Sosai taji gabanta na faɗuwa. Ita dai wannan Chaina da tana da yanda zatai sai ta cire kanta a ciki ALLAH. Gashi taga Abah baida niyyar hanawa..     Babban Yaya ne ya fara barin sashen, dan yace ya gaji barci yake son yi. Sai Oum ta kora Saheeba ta bisa. Maanal ma bata zauna ba ta tattare kayanta ta wuce ɗaki, acewarta aiki zatayi. AA ne ya zama na huɗu, acewarsa shima zaije yay aiki ne. To dama dai Nibras da Nurry dan shi suke zaune, sai dai da kunya ai su ce suma zasu wucen. Dan haka suka ɗan daure suna taya Oum hira. Dan AA yaja hannun Fawzan sun fice tare kamar zasuyi magana ne ya dawo shima dai shiru. Dole suma cikin dabara sukama Oum sallama suka gudu. Da kallo kawai Oum ɗin ta bisu, sai ma duk taji sun fara bata tausayi musamman ma Nibras, zata cigaba da mata addu'a ALLAH ya cire mata shaiɗancin nan a zuciyarta, za kuma ta dinga bata shawara a cikin hikima ko ALLAH zai sa ta gane ta tsaida hankalinta waje guda ga mijinta.....   _________★         Matuƙar zafi rayuwa tama Hajiya Basariyya. Dan tana dira gidan Kawu Manu dake wani ƙauye a ingawa local government ya ƙwace wayoyinta duka. Ya kuma shimfiɗa mata sharuɗan zaman gidansa. Zata hau yimasa magiya daban haƙuri yace baya buƙata. Lokacin da suka iso dambun tsakin masara sukai mai daɗi, yaji zogale da gyaɗa abinsa kuwa ga man ƙuli mai ƙamshi ɗan asali. Amma ita ƴar rainin wayo sai cewa tai bazata ci ba. Babu wanda ya kulata kuwa. Da dare akai tuwo na dawa mai daɗi nan ma. Harda naman zabuwa a miyar, dan duk da Kawu Manu na ƙauye miyar gidansa kullum da nama. Kiwo yake sosai na dabbobi kala-kala. Nan ma ƙin ci tayi, taci biscuits ɗin data ɓoyo a kaya da drinks. Duk bawai ya isheta bane ta dai daure. Washe gari da safe ana idar da sallar asuba da kansa ya kwankwasa mata ɗaki, yanda ta fito ya fahimci bama tayi salla ba. Aiko ya balbaleta da masifa, ya kuma tabbar mata shi ba'a masa lallaci a gida musamman na ibada. Dan haka ta tattara ta koma ɗakin Iya matarsa. Sosai hankalinta ya tashi da jin hakan, amma babu yanda ta iya. Haka taje tai salla, tana idarwa yace ta fito, tsintsiyar kwakwa ya jefa mata ya nuna mata tsakar gidan alamar shara, ya koma kan ɗan dutsen da yake zama a tsakar gidan daga can gefe ya zauna. Ba ƙaramar raunana zuciyarta tayi ba, dan tasan babu abinda ya damu Kawu Manu da shekarunta horata zai yi yanda ya kamata. Shiyaysa taso ta gudu gidan mijinta. Babban tashin hankalinta kayayyakin da suka amso da Maman Yaseerah suna can ta baro a Kaduna gidan yayanta, ga Huznah bata san a halin da take ciki ba a yanzu. Haka dai tai sharar s jigace saboda abune da ita kanta basan adadin shekarun data ɗauka batayi ba, ga tsakar gidan ƙaton gaske kun san dai gidan ƙauye akwai yalwar albarka. A gidanta komai yan aiki ke mata. Wataran ma suyi tace baiyi ba sai sun maimaita. Tana gama share ƙaton tsakar gidan yace ta shiga turken dabbobinsa dake zagaye da danni na itace. Wani irin amai ta dinga ji na masifa na taso mata, dan sunyi ɗanyen kashi ya haɗe da fitsari abin ba'a magana. Sai kawai taji hawaye sun ciko mata ido. Haka ta duƙa tayi sharar, da ƙyar ta gama, sai da ta koma tayi amai sosai. Yi kawu Manu yay tamkar bai jiyota ba, balle kuma Iya daketa hada-hadar ɗora wainarta ta sayarwa ta safe da take yi. Gefe kuma ta dama koko ta ɗaura ɗumamen tuwo na gida.       Hajiya Basariyya na kammala sharan Kawu ya shigo turken, ɗakin dake a gefen wajen ya nuna mata, yace ta fiddo abinci ta raba musu, ta kuma wanke manyan kwatanniyar dake wajen guda biyar ta haɗa musu ruwan dusa a ciki. Daga haka yay ficewarsa ya barta..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [29/04, 4:21 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣5️⃣ ______________ 25 .......Sosai Rabilu ya gigice da tsawar da Sen.. Bukar ya buga masa. Shi ko cikin matuƙar rufewar idanu da shiga tashin hankali mara misaltawa ya cigaba da faɗin, “Kai wawan inane da bazaka kirani ka sanar min ba tun a lokacin Rabilu, sai yanzu zakazo kana gaya min wannan shashashar maganar. Aiko wlhy ko ɗan uban wanene wanda ya auretan sai ya saketa, dan ban taɓa san wata mace kwatankwacin yanda nake son yarinyar nan ba”.        Cikin girgiza kai Rabilu ya ce, “Ranka ya daɗe kayi haƙuri, nima na rasa ta yanda zan isar maka da saƙon nan ne wlhy, tunda kaga tunda ka tafi bamuyi waya ba balle na samu lambar. Amma ka gafarceni. Auren yarinyar kuma yazo da ƙura, dan in har akace za'a ƙwatota akwai rikici. Saboda AA Darma ta aura”.      “AA what?!!”. Sen.. ya faɗa cikin matuƙar zabura jijiyiyin jikinsa na mimmiƙewa. Dan baya jin a kusan nan an taɓa faɗa masa abinda ya girgiza masa zuciya kamar wannan da yaji a yanzu. AA Darma ne ya aura ƴar shularsa fa. Eh lallai akwai yaƙi kenan a Abuja. Tsabar yanda Rabilu ya sake firgicewa da yanayin ogan nasa shi kansa jikinsa rawa yake yi. Sai da yaji dana sanin ma sanar masa zancen. To amma yasan dole ne ya sanar masan, kodan yanda tun jiya ya fahimci yanda ya matsu da jin wani abu a bakinsa game da Maanal ɗin. Yau kuma yana fitowa a gida shi ya fara nema yace yazo office ya samesa. A ɗarare kuwa yazo amma bashi da damar zillewa dole ya faɗa.       “Munafuki tashi ka fitar min a office. Kuma karna sake ganin fuskarsa sai na nemeka”.     A rikice Rabilu ya fara bama Sen.. haƙuri, amma bai sauraresa ba, sai ma cewa yay idan bazai fitan ba zai sa security suzo su fidda shi. Yasan zai iya, dan Sen.. bashi da kirki, shi kansa alaƙarsu tayi tsaho ne saboda yana samo masa irin matan da yake so ne a kuma duk lokacin da yake buƙata.  Haka ya tashi ya fito jikinsa a sanyaye. Dan wannan hanya dai shi kam itace hanyar cin abincinsa. Gashi tafiyar Sen... Ɗin wata da watanni ta sashi a halin rashin kuɗi, ya dawo da tunanin yanzu zai jiƙe ga kuma wannan akasi ya shigo. Amma ba komai zaije yay tunanin hanya mai bullewa, yasan wutar da zai kunno ta yanda dole Sen... zai nemosa da wuri-wiri...... _______★         Washe gari kasancewar Maanal tasan ba fita aiki zatai ba tana idar da sallar asuba ta sake komawa barci bayan taba Oum saƙon wani document taba AA. Oum bata hanata kwanciyar ba, dan taga raba dare tai jiya tana aiki, sai da ma tace ta kwanta sannan tace to. Amma badan haka ba ai bazata barta kwanciyar nan ba. Dan ta ɗauki ɗamarar hana Maanal zama irin su Nibras a gidan, tana son babynta ta horu da kula da mijinta, duk da tasan Ammie ma ba wasa bace wajen tarbiyyar yara, hakan ma a bayyane yake ga Maanal ɗin.         Yau Oum ita kaɗai ta haɗa breakfast ɗin da taimakon su Inte. Bayan ta kammala ta bar musu su shirya a dining ita kuma ta nufi yin wanka, dan tasan itama Abah na hanyar dawowa tunda yace shigar safe zaiyi. Har yanzu Maanal na ƙudundune a duvet tana barcinta hankali kwance...      Bayan kammala wankan Oum ta shiryawa ta samu Fawzan kawai a falon yay zaman karyawa, dan yana son fita da wuri-wiri ne acewarsa. Gaishe da Oum yayi, ta amsa masa da kulawa tana tambayarsa iyali. Shima ya tambayeta Maanal tace tana barci.         “Oh na manta Oum tace yau bazata aiki ba tana hutu”.      “Eh, ai kasan saboda tafiyarsu gobe ne”.    “Wai Chaina ɗin dai?”. “Eh, duk da bamu da matsaya dan Abanku baice komai ba har yanzu”.   “A Oum karki damu zaima barta, ai aiki ne”.        “To ALLAH yasa Fawzan Abanku ne rikicinsa yawa garesa”.     Ƴar dariya Ya Fawzan yayi, dai-dai lokacin kuma AA ya shigo da sallama. Yau dai normal shiga akai ta yadi ruwan toka mai duhu sosai. Kai daka kallesa kasan an sayesa da kuɗaɗe masu tsada, dan ya kwanta luff-luff kamar ajiyayyar ƙanƙara. Rigar ba wata mai tsaho bace, hakama hannunta gajere ne ko gwiwa bai kai ba. Babu dai hula amma yayi ƙyau sosai. Briefcase ɗinsa ya ajiye a saman kujera kusa da wadda ya ja zai zauna cikin muryar nan tasa mara hayaniyar sauti ya ce, “Good morning Oum, Ya Fawzan morning”.       A tare suka amsa masa, Ya Fawzan ya ce, “Ya dai Autan Oum naga kanata kunbura?”.           Ƙin kulashi AA yayi, sai ma jan flaks ɗin gabansa da yay ya buɗe dan yasan maybe kunu ne. Sai Oum ce ta bama Fawzan ɗin amsa da, “Fawzan kadai sakama autana ido a gidan nan”.         Da ƴar dariya Fawzan yace, “Oum babu wani sa ido, shi ɗin ne sai a hankali, yanzu haka fushin nan dan Lilly bazata aiki bane yau.”            “Oum ALLAH zan bar masa wajen”.    AA ya faɗa cike da shagwaɓa. Dariya Oum ta danne ta ce, “Kaga manta da shi my baby, ci abincin ka. Ni zan maka maganinsa. Dan kawai mutun ya tashi da ɗan rashin son maganarsa sai kuma a fassara shi”.      Dariya sosai Fawzan yake yi, sai ma ya miƙe abinsa dan ya kammala karyawa, duƙowa yay saitin kunnen AA ɗin cike da raɗa ya ce, “Saboda kai kwar-kwar ne shine ka tsara su Oum da sunan aiki kai da Lilly a Chaina ko, to ka turan hundred k kona tonaka cewar honeymoon zakaje ehe”. Yana gama faɗa yay gaba, sai da ya je ƙofa sannan ya juyo, kamar yanda yay zato kam harararsa AA ɗin keyi.           “Harareni da ƙyau nidai inji alert, idan ba haka ba zakaga tone-tone yau”. Yay ficewarsa. Karan farko AA ya saki murmushi tare da girgiza kansa. Har cikin ransa yana ƙaunar ya Fawzan ɗinsa. Dan soyayyar ƴan uwansa ta musamman ce a garesa. Abincinsa ya cigaba da ci suna ƴar hira da Oum, shigowar Nuratu ya sashi yin shiru. Sosai ƙamshin turaren data bulbula ya fara hawa masa kai, dan ko kaɗan bai kalla ma inda yasan take ba. Gaisheshi ma da tayi hannu kawai ta ɗaga mata. Tabbas yana son ƙamshi, amma ba irin wannan mai hawa kan ba na mahaukata, balle ma ga mace, shiyaysa kaf turaren da Maanal ke amfani dasu suna masa daɗi da saukar masa nutsuwa, musamman ma traditional. Sallamar Nibras itama da nata salon gayun yasa shi miƙewa badan ya kammala cin abincin ba, matsawa yay inda Oum take ya kama hannunta ta sumbata. “Oum yimin addu'a”.     Addu'ar ta masa harma da sauran ƴan uwansa sannan ya mata sallamar tafiya. Har ya nufi ƙofa ta ce, “Af Auta na manta. Akwai takardu da Baby ta ajiye na baka, suna nan a side drawer na manta na fito da su. Kansa kawai ya jinjina mata, a ransa kuwa faɗi yake, (Lallai ƴar Oum ta gama rainani, ina boss ɗinta a wajen aiki amma ni zata aika na kai mata aikinta. Ba komai zamu haɗe ne). Da wannan tunanin ya shiga bedroom ɗin Oum. Saukar idanunsa a kanta ya sashi sauke ajiyar zuciya duk da bawai yana ganin fuskarta bane. Sai kuma ya shiga takawa a hankali har zuwa gaban gadon. Dai-dai fuskata ta ya tsaya cak, samun kansa yay da zubama ƙyaƙyƙyawar fuskarta datai wani fresh fararen idanunsa. Yanda ta ɗan tura baki gaba baima san ya saki murmushi ba. Sai kuma ya kai duƙe gaban gadon a saitin fuskar tata. Yatsarsa manuniya ya ɗaura a saman lips ɗin da suka ɗan bushe suka sake takurewa waje guda ya shiga shafawa, kafin ya janye ya maida saman goshinta ya gyara mata gashinta da suka ɗan barbaje har saman idonta. Duk yanda yaso daurewa ya kasa, sai da ya kai nasa lips ɗin a slowly ya sumbaci natan. Sai ko kamar tasan mike faruwa ta motsa, idanunsa ya ɗan rumtse dan sam baya son ta farka ta ganshi. Sai kuma ALLAH ya taƙaita abun kwanciya aka gyara. Shima miƙewa yay ganin ta cigaba da barcin, inda Oum tace file ɗin yake ya ƙarasa ya ɗauka. Daga haka ya fito. Oum kawai ya cema “bye”. yay ficewarsa ko kallo Nurry da Nibras basu ishesa ba. Da baya ya dawo, hakan yasa su duka sake kallonsa. Ya ce, “Oum idan Besty ta tashi Please ta min shara. Sashen yayi daty”.         “A'a bola fa? Yanzu ya daina gyarawa?”.      “No Oum na dakatar da shi, saboda akwai banbancin da da yanzu ai ko”.    “Eh gaskiya hakane kuma Auta na. Babu damuwa zata share in sha ALLAHU. ALLAH ya bada sa'a”.         Da “Amin” ya amsa yana wucewa. Oum ma sai ta miƙe tabar Nibras da Nurry dake ta faman ƴar hararrar juna..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [29/04, 4:21 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣6️⃣ ______________ ........Manaal bata gashi ba kuwa sai 11, wanka ta fara yi sannan ta fito. Babu kowa a sashen sai motsin su Inte a kitchen. Kitchen ɗin ta nufa, suka shiga gaisheta da girmamawa duk da kuwa ta tabbatar zasu girmeta. Amsa musu tayi da tambayar ina Oum.          “Tana sashen Abah daya dawo babu jimawa”. Cewar Joy.    Maanal tace, “Oh Abah ya dawo, bara na gaisheshi to”. Daga haka ta fice. Hijjab taje ta ɗauka sannan ta nufi sashen Abah ɗin. Bayan tayi knocking tai sallama, sai da aka bata izini sannan ta shiga. Yana zaune da matansa, tunda ta shigo yake mata murmushi, itako cike da jin kunya ta zauna a ƙasa kusa da ƙafafun Oum ta shiga gaisheshi. Amsa mata yay da kulawa sosai, kafin ya ɗora da faɗin, “Yau ana hutu ko ƴar Abah, shiyyasa na shiga sashen Mamanku kinata barci”.         Murmushi Maanal tayi cike da jin kunya, sai kuma ta juya ta gaida Mamy data cika tai fam. Ko'a kwalar rigar Maanal dan ita a yanzu kallonta kawai take yi. Da ƙarfin hali Mamyn ta amsa mata, dan cike take taf da takaicin maganar tafiyar ta da Oum ke tuntuɓar Abah yanzu. Kuma Aban baiyi wani jayayya ba yay addu'a da fatan alkairi. Ita kanta Oum tayi mamakin sallamawar tasa kai tsaye, balle Mamy da sai yanzu ne take sanin fa tafiyar. Ita dai Maanal sallama tai musu ta koma sashen Oum. Bayan ta zauna ta gama breakfast kitchen ta nufa domin shirya lunch. Wayarta dake kashe ta kunna, sai ko sakwanni suka fara rige-rigen shigowa. YouTube take ƙoƙarin shiga domin duba girki ko zataga wani tai sha'awa, sai kawai taci karo da numbern AA ta notification alamar ya tura mata saƙo. Duk yanda taso ta share hakan ta gagara, dole ta shiga WhatsApp ɗin domin duba saƙonsa.       “Your hand is soft😋, and it reminded me why you're the one I want to hold on to forever”. Iya abinda ya tura kenan da emojin lasar baki. Da alama kuma tun daren jiya ya tura saƙon. Bayan gama cin abincinsu kenan koma tace bayan tashin ta. Samun kanta tayi da sakin murmushi, batare da bashi amsa ba ta fito abinta ta shiga YouTube ɗin datai niyya. Girki tayi masu daɗi, tana ƙoƙarin kammalawa Oum ta shigo. Tako ji daɗin ganin Maanal ɗin a kitchen. Albarka ta sanya mata, sannan tace ta haɗa wanda za'a kaima AA office ya kirata zai aiko driver shiyyasa ma ta taso nema masa abincin, ashema Maanal ɗin ta hutacceta. Da to Maanal ta amsa mata, ta shiga haɗawa kuma komai yanda ya kamata cike da tsari. Har zata rufe ƙular saita tsaya, cokali ta ɗauka ta rubuta (ACICI) a kan abincin sannan ta rufe..      Bayan an wuce da abincin tai salla ta nufi sashen nashi tare da su Inte domin su tayata gyaran da Oum tace taje tayi masa...   ________★        Yau ɗin nan sosai aiki yay masa yawa, sai dai hakan bi hanashi yawan duba wayarsa ba kuma WhatsApp, shi kansa ya kasa fahimtar abinda yake jiran gani, sai dai wani sashi na zuciyarsa na tabbatar masa reply ɗin Maanal yake jira. Kuma yaga ta buɗe saƙon awa biyu data shige amma babu amsa. Haka dole ya haƙura lokacin sallah ya wuce massallaci. Bayan ya koma office babu jimawa drivernsa yazo masa da abincin da yay kiran Oum. Zama sosai ya gyara domin cin abincin dan yunwa yake ji. Yana buɗe kula ta biyu yaci karo da rubutun da tayi, shi da farko ma baiyi zaton abu aka rubuta a kan abincin ba ta hanyar zanawa sai da ya saka ido sosai da tunanin ko wani ne ya saka hannu ya jagwalgwala masa. Sai kawai yaci karo da (ACI-CI). Shiru kawai yayi yana kallon rubutun, zuciyarsa na faman masa kai-kawo. Shi dai yayi imani wannan ba aikin Oum bane ai. Amma duk da haka sai ya ɗaga waya yay kiran Oun ɗin. Sannu da aiki yay mata kamar yanda ya saba a duk lokacin data aiko masa da abincin.      Daga can tace, “Ai Bestyn ka ce ma ta girka bani ba. Sanda ka kira waya naje dan nema maka na samu harta kammala girkin”.       Godiyar dai ya sake ma Oum sukai sallama. Yana ajiye wayar ya sauke ajiyar zuciya, sai kuma yayi murmushi mai sanyi. Samun kansa yay da tsayawa yana kallon rubutun kawai, daga ƙarshe ya ɗauka wayarsa yay hoto sannan ya fara zubawa. Sai da ya gama haɗa komai sannan ya sake ɗaukar wayar, hoton ya tura mata, a kasanshi ya rubuta.      “Meaning”. Kawai.... Maanal na zaune a bakin kadon ɗakinsa data gyara tsaf bayan ta canja bedsheet dan ita kaɗai ta shigo nan su Inte na ƙasa suna gyarawa waya a hannunta suna charting da Waleed saƙon ya shigo. Yanzu kam bata buɗe ba, ta notification ɗin taga abinda ya turo da wanda ya rubuta. Murmushi kawai tayi tana sake maimaita kalmar (meaning) ɗin daya turo a zuciyarta. Daga haka ta cigaba da hirarta da Waleed ɗin kawai. Tabar AA acan da kallon waya. Dan ko da ya kammala cin abinci ya koma kan kujerar aikinsa kaɗan-kaɗan sai ya dauka wayar ya duba kamar ɗazun. Amma har lokacin bata buɗe ba kuma tana a online. Ransa ya sosu amma ya danne, daga ƙarshe ma ya kashe wayar ya ajiye tunda dama iyakar mutanensa ne masu muhimmanci koma yace family ɗinsu kawai keda no ɗin...      Da yamma koda ya dawo gidan ya samu sun fita ita fa Oum. Bai san ina sukaje ba bai kuma tambaya ba. Dan sashen Mamy ma ƙin shiga yayi kasancewar yasan tana tare da Abah daya yini a gida. Sai da Fawzan ya dawo sannan suka nufi sashen Oum ɗin a tare. Sai dai kuma Nuratun da yake gudun su haɗu a sashen Mamy sai suka sameta a sashen Oum ɗin kwance tana kallo. Yi yay kamar ya fasa zaman, sai kuma akai sa'a su Oum suka shigo.       Tunda ya kalla Maanal sau ɗaya ya fahimci gyaran kai sukaje, dan idanun mutuniyar sunyi ja alamar tayi kuka. Kansa kawai ya girgiza yana kallon Oum. Sai kuma yakai zaune a kusa da ita murya a ƙasa ya ce, “Oum daga ina haka?”..             “Wankin kai nakai Baby dan nasan sanda zaka dawo ka gaji balle ka kaita. Aiko ansha daru, ashe har yanzu bata daina kukan wanke kai da kitso ba. Tamaƙi yarda ayi kitson sam”.        Lumsassun idanunsa ya zubama Maanal daketa ɓata fuska, itako taƙi yarda ta kalla kowa sai ma Fawzan dake lallashinta ta kula. Idanun ya ɗauke a hankali. “Ai inaga sai randa aljanun kan nata suka barta zata daina wannan halin”. Yaba ma Oum amsa cikin sanyin yanayi. Murmushi Oum ɗin tayi, yayinda Maanal da taji abinda ya faɗa ta dallo masa harara. Sai kuma ta miƙe fuuu tai ɗaki.     Oum tace, “Kaga ka Koreta auta”.   “Oum dama mai son yin kuka ne aka jefesa da kashin awaki kawai”. Daga haka ya maida kansa ya kwantar a kujerar. Iya wuya Nuratu takai da iskancin Maanal a gidan, shegiyar yarinya gansamemiya ta zauna tana ma mutane taɓara su kuma suna biye mata kamar wasu makafi. Amma ai ta iya zura hannu a ƙasan table tana taɓa maza ko. Ita kaɗai take surutanta a zuciya, fuskarta kuma na bayyana halin da take ciki...       Da wuri Maanal tayi barci dan kanta ciwo yake mata. Tunda Oum ta bata magani tasha sai barci. Ita dama ƙarshen taɓa mata kai kenan ai. Musamman idan bata so kamar mai aljanun dai tabakin AA ɗin. Washe gari ta kama ranar tafiya, shima AA baije office ba. Amma zuwa goma ya fita a gidan. Bai dawoba sai azhar. Ya samu Maanal harta haɗa kayanta, sai kuma a lokacin ne su Nuratu suka san da tafiyar da Saheeba. Nibras ko dake wajen aiki bata sani ba. Kai tsaye AA daya shigo sashen Oum ya nufa. Daga ita sai Maanal a falon sama. Bayan ya gaida Oum Maanal ta gaisheshi batare data kallesa ba. Shima kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa. Dan wani irin ƙyau yaga ta masa a bayyane, bai san tun daren jiya Oum kema yarinyar tata gyaran jiki da kayan haɗi na musamman da Hajiya Shuwa ta kawo ba, ta kuma bata abubuwa tasha, ita dai Maanal ta tsargu da abinda Oum ɗin ke bata, dan tasha gani a wajen su Didinta suna sha. Amma sai bata nuna ba ta dake kamar bata gane komai ba.        “Kaya nawa kika ɗiba?”. AA yay maganar idonsa akan Maanal muryarsa a dake dan ransa a ɓace yake, rashin walwalarsa yau a bayyane take. Mamy ce kuma ta haddasa hakan a gareshi, dan kaca-kaca yau tai masa akan wannan tafiya tasu da Maanal, harda cewa ma da sai dai a fasa da Maanal ɗin ko shi ɗin ya fasa, sai da ya mata alƙawari akan Nuratu data kafa masa sharaɗin kiranta kullum sannan kuma tai masa ALLAH ya isa idan ya mu'amalanci Maanal a shimfiɗa..... Tunanin nasa ya kauda gefe, ya sake maimaita maganar ga Maanal datai kamar bata jisa ba cikin yanayin ɗan tunzura.       Kallonsa Maanal tayi dan harga ALLAH sai yanzu taji abinda yace, da farko hankalinta nakan charting da take da su Didinta ne, ganin yanda ya tsatstsareta da nashi kaifafan idanun a gaban Oum kuma ko kunya babu sai ta ɗauke nata da sauri. A sanyaye ta ce, “goma”. Komai bai sake cewa ba, sai miƙewa da yay ya fita. Da kallo duk suka bishi, Oum kuma ta fahimci ransa a ɓace yake, amma sai tai tunanin ko daga waje aka tunzuro shin.       Babu jimawa ya dawo da madaidaicin traveling bag na trolling mai shegen ƙyau. Baice komai ba ya wuce ɗakin Oum da shi, fin mintuna goma sai gashi ya sake fitowa da shi. A falon ya ajiye sannan ya ɗan kalla Maanal ɗin ya ɗauke ido yana ƙoƙarin ficewa. Ciki-ciki ya furta, “Ki bar wancan”. Daga haka yay ficewarsa. Kallon juna Oum da Maanal sukai. Fuskar Oum da damuwa ta ce, “Akwai abinda ke damunsa”.      Ƙasa Maanal tai da kanta, dan ita kam bata san mi zatace ba. Itama ta fahimci akwai damuwa a tare da shi, duk da tasan wannan normal ne a halinsa, dama idan kaga sakewa a tare da shi to lallai suna tare ne, dan ita sam bata son yanayin baƙin miskilancin nashi, shiyyasa duk yanda zata sakashi magana ta sani. _________★ 4:30pm       Su AS suka iso domin ɗaukarsu. Shine ya fara fitowa daga sashensa. Sanye yake cikin ƙananun kaya normal wandon jeans black da t-shirt black data kwanta masa a jiki sosai, dan irin mai santsin nan ce da laushi jiki. Yaci zanzaro brawn belt daya fidda ainahinsa na dogon mutum dake tsaye sosai a suffarsa ta zakin. Sai jacket da itama ta kasance brawn color a hannunsa ya saƙale batare daya saka ba. Sosai fuskarsa data sha gyara gashin sajensa ya kwanta luff-luff ke'a ɗaure, kamar ko yaushe idanunsa manne da sirrin fari tas ɗin gilashinsa dake sake ƙawata shi. Tafiya yake ɗai-ɗai a kuma nutse cike da ƙasaita yana ɗaura agogo a tsintsiyar hannunsa takalmansa masu matuƙar ƙyawu sau ciki na bada ƙarar sauti kaɗan-kaɗan.        Sosai Nuratu ta shagaltu da kallonsa, ji take kamar ta haɗiyesa ta huta. Dan daya ɗan gittata zuwa gaban Mamy mayataccen ƙamshinsa ya daki hancinta jitai illahirin jikinta na rawa. AA da bai san ma tana yi ba dan shi ko lura da ita baiyi ba a wajen ya ɗan zubama Mamy ido kafin ya risinar cike da girmamawa ya furta, “Zamu wuce Mamy”.         Ƙin yarda Mamyn tai ta kallesa, kasancewar su Oum a wajen kuma yasa tai masa addu'a cike da nuna rashin kulawa kamar yanda take musu. Muryarsa a sauƙaƙe ya furta, “Thanks you” a hankali. Sai kuma ya matsa gaban Abah. Murmushi Abah yay masa, tare da ɗaura hannunsa a kafaɗarsa. Sai kuma ya matsar da bakinsa kusa da kunnen AA ɗin ƙasa-ƙasa ya furta, “A rufan asiri a dawo min da yarinyata lafiya Oum's boy, kaga dai gudun rigimar uwar taka yasa na baka salin-alin”.         Idanu AA ya lumshe tare da sakin guntun murmushi kansa a duƙe. Batare da ya yarda ya kalla Aban ba ya gyaɗa masa kai, muryarsa a sanyaye yace, “In sha ALLAHU Abah zan cika alƙawari”.     “ALLAH yay muku albarka”. Abah ya faɗa yana murmushi da ɗan bubbuga kafaɗar tasa. Gaban Oum AA ya ƙarasa..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [30/04, 4:46 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣7️⃣ ______________ ........Gaban Oum AA ya ƙarasa, Maanal na gefenta sanye cikin Abaya red color datai mata matuƙar ƙyau, tai rolling kanta da mayafin, sai mitsitsiyar handbag a hannunta. Suna haɗa ido ta kauda nata, shima nashin ya maida akan Oum, cike da kulawa ya rungumeta, “Oumna zan yi missing ɗinki”.          Ya faɗa cikin maƙoshi. Murmushi Oum tayi, tare da ɗan bubbuga bayansa. Sai kuma ta ɗagoshi cike da kulawa fiskarta da murmushi ta shafa fuskarsa. “Nima haka Auta, amma karka damu kamar yau ne ai zaku dawo. Ga Baby na nan zata kula min da kai”. Tai maganar tana juyawa ta kamo hannun Maanal. A cikin nashi ta sanya, a tare suka saki ɓoyayyar ajiyar zuciya kuwa. Sai dai a zahiri kowa a dake yake, dan Maanal ma kanta a aƙasa yake, shine ma dai ke kallonta ƙasa-ƙasa. Addu'a sosai Oum tai musu, tare da damƙa ma junansu amanar kansu. Daga haka tace suje lokaci na ƙurewa. Gashi jirginsu 5:20 zai tashi.        Sai yanzu ne Saheeba ta buɗe baki da ƙyar tai musu addu'ar dawowa lafiya, hakan ne ya zaburar da Nuratu, itama ta ce, “Ya AA ALLAH ya tsare”.      Hannu kawai ya ɗaga musu, tare da kai ɗayan hannunsa ya amshi trolling ɗinsu da Maanal ta kama zata ja. Ɗan ɗagowa tai ta kallesa, suna haɗa ido ta janye tare da sakar masa akwatin. Shima bai ce komai ba ya turashi yay gaba, ita ko Maanal sai da ta sake rungume Oum sannan ta wuce idannunta cike da hawaye. Ji take kamar zasuyi tafiya ne mai jimawa.        Da sauri AS ya zaburo ya amshi akwatin hannun AA ɗin domin sakawa a booth dake buɗe. Shi ko jikin motar ya nufa ya tsaya har Maanal ta iso, ganinsa tsaye ya sata fahimtar ita yake jira ta shiga. Dan haka ta nufi shigar, hannu yasa ya tare mata saman kai dan karta buge, sai kuma akai rashin sa'a abayarta ta nema taɗeta. Riƙota yay da hannunsa ɗaya bayanta ya jinginu da jikinsa. Muryarsa a ƙasan maƙoshi can ƙasa sosai ya ce, “Are you okay?”.     Kanta ta jinjina masa tana ɗan sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta matsa daga jikinsa ganin su Oum duk suna kallonsu har tana iya hango yanda fuskar Mamy, Nuratu da Saheeba ta canja, shiga tayi sai dai tana ɗan yamutsa fuska dan ƙafarta na ɗan mata zafi. Lurar da AA yayi saboda idonsa a kanta yake ya sashi kaiwa tsugunne irin na yanayin maza ya ɗaga Abayar kaɗan ya kamo ƙafar dake a cikin ƙyaƙyƙyawan baƙin takalmi fes-fes da ita. Takalmin ya zare ya ajiye, batare da damuwa ba ya ɗaura ƙafar a saman jikinsa. Ji Maanal tai kamar tayi kuka dan nauyin Abah da Oum. Amma yaya zatai tunda tasan ba fasawa zai yi ba. Duk da haka sai da tai magana a sanyaye ta ce, “Bafa da yawa bane”.      Bai kulata ba, sai ƙoƙarin ɗan jajjan ƙafar kawai yake yi, sai da yay kusan na minti biyu sannan ya maida mata takalmin ya gyara mata ƙafar a cikin motar tare da rigarta ya miƙe. Da kansa ya rufe mata murfin sannan ya juya ya kalla su Oum dake kallonsu cike da jin daɗi, sai dai banda su Mamy. Dan ji tai wani irin ƙududu ya riƙe mata zuciya katamaumau. Nuratu kam ƙwalla ne suka cika mata ido ma. Hannu ya sake ɗaga ma iyayen nasa sannan ya zagaya ɗayan side ɗin da AS ya buɗe masa ya shiga ya zauna. Suma su AS sukai sallama da su Oum ɗin suka shiga motar ta fice.      Sannu a hankali Maanal ta lumshe idanunta da hawaye suka ciko. Jin suna neman zubo mata ta buɗesu tare da kai yatsarta ta ɗauke su tana kallon waje. Sarai AA na hankalce da ita, dan haka ya kai tattausan hannunsa ya kamo nata dake ajiye a kan cinyarta, saman tashi ƙafar ya dawo dashi yana mai harɗe yatsunsu waje guda. Ta gefen ido ta ɗan dubesa, ganin ba ita yake kallo ba ta shagala sosai a kallon nashi, dan harga ALLAH idan tace bai yi mata ƙyau ba ma tayi ƙarya. Ta shagala sosai a bazata ya waiwayo suka haɗa ido, cike da borin kunya ta kauda nata gefe tana ɓata fuska. Shi dai baice mata komai ba, kuma bai daina kallon nata ba har sai da wayarsa ta motsa alamar shigowar kira. Ɗauka yay ya duba, babban yaya ne. Dan haka ya ɗaga tare da kai yatsansa ya gyara zaman bluetooth ɗin kunnesa baƙi, cikin yanayinsa na rashin son ɗaga sauti yay sallama... Tsabar yanda yake magana can ƙasa su kansu su AS dake a gaba ba jinsa suke ba. Ita kanta Maanal dan kawai ta nutsu ne ta maida hankali a kansa duk da ba kallonsa take ba. A haka suka iso airport dan gudu sosai sukayi.      Bai motsa domin fita ba, ita kuma ya riƙe hannunta bai bata damar ta fitan ba. Magana suke da AS. Ita Maanal ma tayi zaton bada shi za'a ba. Sunja kusan mintuna biyu a haka sannan aka buɗe musu. Juyawa yay ya ɗan kalleta, kafin ya saki yatsun hannunta dake sarƙale da nashi a hankali sannan ya yunƙura ya fita yanzu ma jacket ɗinsa da bai saka ba har yanzu a hannu. Itama ɗin fitar tayi, dai-dai driver na rufe side ɗin data fito ɗin AA ke isowa wajenta. Yayinda AS daya fiddo akwatinsu da wani da bata san na waye ba ya tura su yay gaba. Shi kuma da yake binta da wani kallon ƙasa-ƙasa hannunsa ya miƙa mata. Hannun ta zubama ido, sai kuma ta ɗan ɗago ta kallesa. Ita ɗin dai yake kallo idanunsa na komawa ƙanana. Yau dai ta fahimci kurumtar ce ta motsa ta miskilanci, dan haka ta ɗaura hannun nata a hankali saman nashi, shiko ya haɗesu da ƙyau sannan suka fara takawa a tare.       Dole duk wanda ya kallesu su burgesa, dan kallo guda zai tabbatar maka da su ɗin ma'aurata ne. Sun matuƙar dacewa da juna kuma, duk da ita ɗin ƴar ƙarama ce a gabansa, dan koda take da tsaho tsahon nata gaba ɗaya bai wuce kafaɗarsa ba. Arba da ma'aikatansu su Yaqub ya sakata jin nauyi da kasancewar a yanda suke. Shi ko ko'a kwalar rigarsa. Sai ma amsa musu gaisuwar da suke masa yake ta hannyar jinjina kai. Itace ke amsawa cike da jin nauyin da su kuma suke fassarawa da jan ajinta. Dai-dai nan kuma aka fara shelar neman matafiyan da zasu tashi a jirginsu zuwa Qatar. Gaba yay riƙe da hannun nata su AS da su Yaqub da yaƙi yarda ya kalla ko inda Maanal take biye da su. Sai da sukai ƴan abubuwan da suka kamata kafin wucewa inda jirginsu yake. A haka yana riƙen da ita suka shiga, su sun wuce vip ne.        Ganin hakan sai da yasa Maanal sauke ajiyar zuciya a ɓoye. Duk da ya jita bai nuna yaji ba, sai ma taimaka mata da yaya ta zauna a nata sit ɗin kafin shima ya zauna a nasa dake kusa da ita. Ta inda suken keɓantaccen waje ne madaidaici zaman mutum biyu tamkar wani falo ko ɗan ɗaki, zaka iya maida kujerun gado idan kaso. Ga television da kayan dai ƙawa yanda ya kamata. Tuni Maanal ta zama baƙauya, dan ita kam bata san akwai hakan a jirgi ba. Kai masu kuɗu na sha'aninsu. Bata tsinke da al'amarin ba sai da AA ya danna wani ɗan bottom ta gefen kujerar belt ya saka kansa da kansa a jikinsu. Dai-dai jirgin na tashi zuwa sama dole ta lalubo hannunsa a cikin nata. Kallonta yayi, sai kuma ya buɗe tafin nasa ya maida natan a ciki ya sargafe yatsunsu cikin na juna. Sosai ta sake ƙanƙame masa hannun har tana kafa masa ƙubunanta da ba wani tsahone da su ba dan bata wasa da yankewa a kan fatarsa. Aiko sai da ta fasa masa fata abinka da ba'asan wahala ba. Bata fargaba kuma sai da jirgin ya gama dai-daita ta buɗe idanun, hannun nasu ta ɗan kalla tana sauke ajiyar zuciya, har zata janye sai kuma tai saurin sake kallo. Sosai taji gabanta ya faɗi, babu shiri ta juyo da shi ganin yana ƙoƙarin juyarwa dan karta gani. A sanyaye cike da damuwa ta ce, “Ya ALLAH na ji maka ciwo”.      Komai bai ce ba, ya dai ɗan kalli hannun ya kauda kansa. Yayinda ita kuma ta buɗe yatsun nata tana matso da hannun saitin bakinta ta shiga wura masa iska da baki kamar wanda ya kone. Ai ba ƙaramin ratsa jijiya da jinin AA hura hannun nan yay ba, a take ƙofofin gashinsa suka shiga bubbuɗewa. Dole yay ƙoƙarin janyewa yana faɗin, “It's okay”.          Kanta ta jinjina masa idannunta na cika da ƙwalla, sai kuma taja tissue ɗaya dake ajiye a kwalinsa ta shiga goge jinin daba wani zuba yake ba ya dai nuna alamar fita ne kawai. Dai-dai nan ma'aijaciyar jirgin ta shigo bayan tai ɗan knocking, tray ɗin hannunta mai ɗauke da coffee ta ajiye, sai kuma ta dubesu domin jin ko suna buƙatar wani abu ne. Cikin harshen turanci Maanal tace suna buƙatar First aid box.          “No...”     AA ya faɗa yana ƙoƙarin dakatar da ita, amma sai maanal ɗin tace taje ta kawo. Itama ganin jinin yasata fita, babu jimawa ta dawo da wata matashiya kamarta da first aid ket ɗin a hannu. Kai tsaye inda suke tayo, ta ajiye box ɗin tana ma AA sorry. Shi ko kallonsu ma baiyi ba. Maanal ɗin da duk ta rikice kawai yake kallo ƙasa-ƙasa. Mata ta kawo hannu zata kama hannunsa Maanal tai mata tsawa batare da ita kanta tasan mi tayin ba. Cike da masifa tace ta bata zata masa. Karo na farko AA yay wani ɗin killer smile na gefen baki ya lumshe idanunsa kawai. Sai dai yana kallon yanda take goge masa jinin a ɗofane tana kuma hurawa da baki wai kar yaji zafin spirit. Sai yaji kawai abin ya masa suger. Ƙoƙarin tsokanarta yay, dan haka ya ɗan ja hannun baya kamar wanda yaji zafin.      Ai da sauri Maanal ta kallesa a raunane ta ce, “Da zafi ko, I'm sorry”. Yanda tayi kamar zatai kuka yasa shi ƙara girman idanun nasa a kanta yana kallonta ciki-ciki. Kansa ya girgiza mata ganin yanda ta zuba masa idanun dake tara ƙwalla. Kan nasa ya girgiza mata kaɗan, sai kuma ya juya nasa hannun nata ya koma sama, ya matso da shi tare da ɗan duƙowa ya sumbata. A hankali ta lumshe nata idanun tare da jan ajiyar zuciya.       Su dai ma'aikatan jirgi sun shagala suna kallon ikon rabbu, wannan al'amari kamar a film, dama a baƙaƙenmu akwai masu irin wannan shagaltacciyar ƙaunar, dan wannan ta wuce soyayya sai tsantsar ƙauna mai zafin gaske da sam bata ɓoyuwa a idanun masoyan. Da ƙyar ɗaya tai ƙarfin halin miƙama Manaal plaster ɗin data yanko tare da ƴar audiga. Maanal ɗin ta amsa ta sanya masa sannan tasa plaster ɗin a sama. Tattarwa sukai suka wuce suna waigensu..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [30/04, 4:46 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣8️⃣ ______________ .......Matuƙar saka rayuwar Huznah gaba Sageer yayi a wannan tsakanin da buƙatunsa. Tabi kowacce irin hanya na bijirewa amma ya nuna mata namiji yake. Sai dai taci kukanta da zaginsa a zuciya dan tsoronsa ALLAH ya dasa mata. Ko fita yay da zarar taji motsin dawowarsa zuciyarta ke fara dukan uku-uku. Gashi yanzu ya hana kowa shigowa gidan dan kullesu yake ta ciki, mutum ya ƙaraci bugunsa dole ya haƙura. Wayarta ya amshe ya kashe tun ranar da sukai waya da Hajiya Basariyya. Girki kam tunda tayi sau ɗaya ta ƙwaɓa musu hauka ya koma yi da kansa. A rana ta uku yasata shiga kitchen ɗin ya fara koya mata. Dan ya tabbatar mata yana da mata bazai dinga zuwa gidansu cin abinci ko saye ba. Idan zata zage ta zage babu abinda za'a fasa. Tako tabbatar da babu abinda za'a fasa ɗin kuwa. Dan tako ina baya raga mata yanzu. Hatta da gyaran gidan tsaye yake mata akai sai tayi komai yanda yake so.          Sau biyu tana satar wayarsa ta gwada kiran Hajiya Basariyya sai taji tata wayar a kashe itama. Ba ƙaramin tashi hankalinta yay ba da rashin jin uwar tata. Shiko sarai yana sane da ita, abinda bata sani ba yaji komai akan abinda ya faru da Hajiya Basariyyar a kwanakin nan Daddynsu na faɗa ma Babanshi saboda haƙurin daya bashi akan ya barsu su koma ɗakinsu suyi azumi. Shine yake sanar masa abinda Hajiya Basariyya ta aikata, da idonsa ya ganta shi da ƴaƴanta a wani ƙauye bin malamai, su kuma sunje cinikin gona ne a kusa da ƙauyen. Amma yay masa alƙawarin maida Hajiya Yaya idan tayi azumi koda goma ne a gidansu.         Sosai Huznah tai ramar dole a wannan gaɓar, ga shi kota kulle ƙofar ɗakin ma yanzu a banza ama wofi zai buɗe da wani key ɗin ne. Gida kuma in zai fita ta baya yake kulleta. Tun tana masa girman kai harta fara tunanin saukewa ta bashi haƙuri kozai taimaka ya bincika mata Umminta, dan tana son sanin wane hali take. Kamar kullum yau ƙarfe biyar ya dawo kasuwa. Tana falo zaune idonta a tv sai dai bata fahimtar komai kallon kawai take yi. Shigowarsa ta sata zabura tana masa sannu da zuwa. Sosai ya zuba mata ido dan mamaki. Amma sai baice komai ba ya gyaɗa mata kai kawai. Kitchen tai saurin nufa, a wani mamakin nasa bata jimaba sai gata ta fito da ruwa ta ajiye gabansa. Badan ruwan leda bane ALLAH sai ya tsargu wani abun mutuwar ta zuba masa. Amma yasan bazai yiwu ba tunda fure water ne....        “A kawo abinci?”. Ta faɗa cikin katse masa tunani. Sai ya samu kansa da sakin murmushi. “Kina lafiya kuwa Huznah?”. Ya faɗa yana tsatstsareta da idanu. Kanta ta jinjina masa alamar eh. Iska ya ɗan furzar, sai kuma ya gyaɗa kansa da miƙewa yana faɗin, “Okay bara na watsa ruwa to, kibar abincin sai nayi sallar magrib tukkunna.”           Murya a ƙasa ta ce, “To”.    Nan ma sai da ya sake kallonta kafin ya wuce ciki abinsa yana kwasar dariya a zuciyarsa.....       Ni kaina dai abin ya bani dariyar Man Sageer 🤣😜 _________★         Gaba ɗaya Oum kewar yaranta take ji, dan ma babban Yaya da Fawzan sun ɗauke mata kewarsu. Nibras ma da farko ta shigo, amma jin hirar da su Fawzan keyi akan tafiyar su AA ɗin saita miƙe tsam kamar ma wadda jikinta ke rawa. Sallama tai musu cikin danne kukan dake neman zuwa mata tace zataje ta kwanta ta gaji. Da kallo kawai Oum ta bita. Hakama babban Yaya da tuni shima ya fahimci take-takenta. Amma a mamakinsu shi Fawzan ɗin da suka ji tausayinsa ya kama su shi hankalinsa ma nakan waya abinsa sai zabga murmushi yake dan charting yake da Najma.      Sai sukai tunanin ai bai fahimci matar tasa bane saboda sonta ya rufe idonsa. Sai dai abinda basu sani ba Fawzan ya riga kowa fara fahimtar matar tasa da inda haukanta ke ɗawainiya wajen kaita. Ya barta ne kawai bisa wasu dalilai dan yasan wane Autansu. Sannan yafi son kowa ta fahimta da kansa musamman Mamy data haɗa auren nasu. Dan yayi alƙawarin in sha ALLAHU da bakinsa dai bazai cema kowa a gidan ga halin da yake zaune da Nibras ba, har sai idan sune suka gani sukai magana....     Kuka sosai Nibras ta shiga yi a sashenta, ba komai ya kawo hakan ba sai jin matsanancin kishin AA akan Maanal. Yanzu ita har rashin muhimmancinta a gidan nan yakai AA ya shirya tafiya da wannan ƴar iskar yarinyar amma bata sani ba har sai bayan tafiyarsu. AA ɗinta, sanyin idaniyarta. Aiko har abada bazata yafe ma Maanal ɗin wannan tafiyar ba, sai ta mata hukunci dai-dai da hakan....       A ɓangaren Mamy ma dai ranta a jagule yake ita da muƙarrabanta su Nuratu. Dan Nuratu ma tun bayan tafiyar su Maanal data shige bedroom bata sake fitowa ba. Ita kanta Mamy sai da Abah ya fahimci bata cikin walwalarta. Koda ya tambayeta sai ta nuna masa kawai yanayi ne sannan kamar kanta zai mata ciwo take ji tasan kuma zafin gari ne dake sirkawa.      Sannu yay mata tare da bata magani yace tasha ta kwanta yau yama yafe mata zuwa sashen nasa kawai. Aiko wannan freedom ɗin data samu kusan raba dare sukai suna waya da yayarta da maman su Saheeba. Sun tsara yanda zasu tarwatsa Oum da Maanal sosai a gidan. Daga ƙarshe suka birkice zuciyar Mamy musamman akan AA. Tare da tunzurata akan batun ƙara auren Fawzan wai dan a tantance waye baya haihuwa shi da matar tasa tunda idan sunje asibiti sai ace musu duk ƙalau suke lokacine kawai baiyi ba. Su dai sam basu aminta da hakan ba dole akwai lauje cikin naɗi.      Tsaf kuwa zuciyar Mamy duk ta hau akan shawarwarin nasu. Duk da ita dai Aunty Babba har cikin ranta tana yaƙine da kishin ƴar uwarta wato Mamy, yayinda Maman Saheeba ke komai da zuciya biyu, dan itafa fatanta ƴaƴanta su kasance a gidan su mamaye komai na dukiyar su Babban Yaya ta hanyar baza ƴaƴa. Kunga ko komai ai ya dawo tafin hannunsu. Dan ita kanta Saheebar ido a rufe maganin haihuwa ake neman mata tunda tun daga cikin Anum shiru kake ji bata sake ko ɓatan wata ba ga Anum na neman cika 5years.      Ita ko Mamy ɗauka take duk sonta suke yi musamman ma Maman Saheeba, dan wasu lokutan ita Aunty Babba kan ɗan faɗa mata gaskiya shiyyasa tasu bata tsaho a tare..... _________★         Bayan sallar magriba da isha'i da su Maanal suka gabatar ita da AA da har yanzu bai sake ba wajen zamansu suka koma. Ganin ya buɗe laptop itama sai ta ciro novel a bag ɗinta kawai ta hau karatu. Koda aka kawo musu abinci daga ita har shi babu wanda yabi takai duk da shine da kansa ya bada umarnin a kawo ɗin. Ɗan ɗagowa yay ya kalla Maanal jin kamar ta daina motse-motse, aiko dai gyangyaɗi take. Shi sai ma taso bashi dariya, yo tun ba'aje ko ina da tafiya ba, Chaina fa suka nufa tafiya mai nisan awanni.        Wani ɗan bottom ya danna a gefen kujerar a take ta wani kalar buɗewa ta zama gado, abinda ya raba tsakkiyarsu mai kama da hannun kujera ya naɗe kansa wajen shima ya zama flat. Laptop ɗin ya matsar gefe ya kwantota a jikinsa tare da zare novel ɗin hannun nata ya ajiye. Fuskarta data fito so cute a zagayen rolling ɗin veil ɗinta ya zubama ido, sai kuma ya janye cikin lumshewa ya kuma buɗe a lokaci guda. Veil ɗin ya shiga warware mata a hankali bayan ta cire pin ɗin data riƙe da shi. Yana ko gamawa ta gyara kwanciya tana sauke ajiyar zuciya. Shima sai ya samu kansa da sauke ajiyar zuciyar acan ƙasan maƙoshi. Ɗan takurewar da tai waje guda ya sashi ɗaukar lallausan farin mayafin dake gefensu kaɗan ya lulluɓa mata har a kafaɗa, sai kuma ya zare ribbons ɗin data kama kanta da su a tsakkiya gashinta ya tarwatse masa a hannu, kamawa yay ya tattaresa cikin hannun nasa ya shiga tufkewa a hankali ta yanda bai tsamke tushen ba balle taji zafi. Veil ɗin ya ɗauka ya ɗaura mata a kan kamar ɗan kwali cike da dabara, daga haka ya ɗan ranƙwafa ya sumbaci kan nata sannan ya ɗauka laptop ɗinsa ya cigaba da aiki duk da kuwa wani ɓangare na jikinta yana a jikinsa ne...         Sosai ya raba hankalinsa biyu a kallon fiskarta da aikin, dan yanda ta ɗam tsuke baki zaka fahimci kamar tayi barcin ne da faɗa a zuciyarta. Yasan halin mutuniyar tasa ba rabo take da masifa ba har a cikin barci tanayi faɗa. Kawai dai kura ce tai lafiyar dole. Eh lafiyar dole mana tunda dai risinar ta dole ce ai....          ★Barci sosai Maanal tasha, dan bata tashi farkawa ba sai kusan 9:30, zuwa sannan awa ɗaya da rabi ce ta rage musu su sauka cikin ƙasar Qatar domin yin canjin jirgi. A hankali ta shiga motsawa, sai kuma tai juyin daya bata damar komawa tana fuskantar lafefen cikin AA, rashin nauyin rigarsa da yanda ta kwanta masa a jiki har yana jin saukar nunfashinta a kan fatar cikin nasa. Sosai tsigar jikinsa ta fara tashi. Cikin wani irin motsawar zuciya ya lumshe idanunsa a slowly sakamakon sake motsawa da tai ta kife ƙirjinta da ƙyau a cikin nasa tare da zagayo hannayenta ta bayansa. Daga ganin yanda tai ɗin ka tabbatar ta ɗauka filo ne ta rungume. Cigaba da saukar numfashin nata mai ɗumi a jikinsa ya sashi jin ina bafa zai iya ba. Da ƙyar ya iya jawo busashen yawun da ke neman suɓucemasa a baki ya haɗiye, maƙoshinsa yay wani irin yin sama da ƙasa a lokaci guda cikin wuyansa. Idanun da yake faman rumtsewa ya buɗe, sai kuma a hankali ya ture laptop ɗinsa gefe can ƙuryar maƙoshi ya shiga kiran sunanta cikin taushi da sauƙin sauti dake fita cike da kasala da ƙyar..........✍️         *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [30/04, 4:46 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣9️⃣ ______________ .......Tun Maanal najin tamkar ana kiran sunan nata a nesa ko cikin barci harta fara jin saukar sautin a cikin kunnenta. Numfashi irin na mai ƙoƙarin farkawa ta sake tare da fara buɗe idannunta a hankali. Tun tana ɗan jansu luuu ta maida kuma ta lumshe harta buɗe gaba ɗaya a kan fuskarsa daya ɗan duƙo yana kallonta shima. Sake maida idanun tai ta lumshe, sai kuma ta buɗesu da ƙyau, cikin sa'a kuwa suka shige cikin nashi dake a kaɗe daya zuba mata. Itama nata ɗin sun kaɗe tare da ƙara girma sun ɗan kumburo ta fatar saboda barci. Samun kansu sukai da kallon juna, kallo irin mai shiga jikin nan da tsinka jini. A tare yanayin jikinsu ya fara canjawa, cikin ƙarfin hali AA ya motsa nashi lips ɗin can ƙasan maƙoshi da sauti na mai raɗa girarsa ɗaya a ɗan ɗage ya furta, “You still pretending to be sleep?”.        Baki ta ɗan tura tana lumshe idannunta, sai kuma ta ɗan kifa kanta a jikinsa tamkar wadda taji kunya ƙasa-ƙasa da murya irin ta wanda ta tashi a barci ta ce, “Uhm… sorry. Ban san na kwanta haka ba.”           Gefen lips ɗinsa ne ya motsa kaɗan alamar son yin murmushi, sai dai baiyi ba, Da wani irin sake sauƙaƙa murya ya ce, “Hmm kinji na tambayeki yanda kika kwanta ne?. Barci yay daɗi kin haye VIP jiki.”      A yanda yay maganar ya sata ɗan ɗagowa ta ɗan kalle shi da ido ɗaya, cikin ɗan waro masa idanun da shagwaɓe fuska ta ce, “Na haye? Ni wlhy sharri kamun”.       Ɗan sunkuyowa yay fuskarsa gab da tata yana kallon cikin idonta a hankali, cikin zolaya ya furta, “To ko jikina ya janyo ki ne? Dan da alama yana da ɗumi sosai tunda har kika zaɓeshi fiye da bargo.”         Idanunta ta janye daga cikin nasa tana mai kai hannu ta sosa goshi dan kunya, sai kuma ta ɗan juya gefe tana jin kamar ta saki kuka dan kunya ciki-ciki ta ce, “Ni dai sharri aka mun tunda ban hau ba, ƙilama bugar dani akai dan a ɗaura ni”.            Yanzu kam sai da ya ɗan murmusa tare da lumshe ido, yana jin daɗin yadda take jin kunya. Cikin sake sauke murya ya ce, “Shiyyasa naga an kanannaɗe ni ai ko Madam pretender! Maimakon ki ce (thank you for being so comfortable Besty) ki bani sumba mai zafi na godiya”.       Hannunta dake jikinsa tai saurin warwarewa, sai kuma ta yunƙura zata tashi. Maidata yay ya hanata hakan, cikin son ɓoye fuskarta ta ce, “ALLAH ni ka daina kana bani kunya”.          Cike da basarwa cikin magana ɗaɗɗaya kamar ba daga bakinsa take fitowa ba ya ce, “Kunya mai ƙyau ce musamman idan tana zuwa daga fuskar da na fi son gani.”        Yanzu kam kasa jurewa tai sai da ta kallesa, shima kallon nata yake, suna haɗa ido ya wani ɗage mata gira ɗaya sama. Ai babu shiri ta ture hannunsa dake riƙe da kafaɗarta ta tashi zaune. Komai bai sake ce mata ba, sai ma laptop ɗinsa daya ɗauka ya cigaba da aikinsa jijiyiyin jikinsa na wani mimmiƙewa. Amma ya danne komai da tsiya-tsiya kamar ba shine ya gama zuba zance ba. Itama tashi tai ta shiga toilet batare data yarda ta sake kallon ko sashen da yake ba. Ta jima a bayin kafin ta fito. Batare data yarda ta kallesan ba ma yanzu ta ɗauka book ɗinta ta zauna ɗan nesa da shi.         Ganin yanda tai kamar bataga abincin ba ya sashi yin ƴar gyaran murya, ƙasa-ƙasa yana kallonta da idon daya san sirrin zuciyarta. Cikin yanayin rashin walwalar da har yanzu ke mamaye da fuskarsa ya furta, “To Madam barci, za ki ci abincinki ne ko har yanzu jikina ya fisa daɗi?”        Baki ta ɗan tura gaba tana kallon shiryayyen abincin, “Wannan abincin ai ya huce tuni fa. Kawai bana ma jin ci”.        Idanunsa da ke lausashe da wani yanayi mai wahalar fassara ya zuba mata, sai kuma ya janye su a slowly ya maida ga screen ɗin laptop ɗin yana kai hannu ya gyara zaman glashinsa. “Na tashe ki kice na miki rowar lallausan jiki bayan na sanki da mita”. Yay maganar cike da basarwa. Koda ta ɗago ido ta kallesa yama fiske abinsa sai ka rantse ba shine ya faɗa maganar ba. Jitai bazata iya barmasa ba itama, cikin nata yanayin basarwar ta ce, “Humm sai cika baki, kana jin kamar jikin naka wani katifa ne”.       Kaɗan ya taɓe baki batare daya bar aikin da yake ba ya ce, “Ai ni sai dai ma nakira kaina 'His Royal Mattress'.”         Rasama abin cewa Maanal tayi, sai kawai ta zaɓi yi masa shiru. Shima bai sake tankawar ba, sai danna abu da yay a hankali table ɗin da aka shirya abincin ya matsa gabanta zuu. Kallonsa tayi, shima dai-dai ya ɗago ya kalleta bayan ya kalla agogon dake ɗaure a hannunsa. “1:7min ya rage mana sauka Doha”.            Kanta kawai ta ɗan jinjina, sai kuma ta ajiye book ɗin ta fara bubbuɗe abincin. Tana cin abincin kaɗan-kaɗan shi yana aikinsa da kallonta lokaci-lokaci batare da yayi magana ba. A haka ta tsakuri abincin ta ajiye dan sam jitai ma bai mata wani daɗi ba ita kam. Ganin lokaci ya gabato shima ya tattare aikin ya ajiye tare da maida komai inda yake. Itama veil ɗinta ta ɗauka ta naɗa bayan ta maida ribbon ɗinta. Dai-dai nan aka sanar da isowarsu ƙasar Qatar. Sun sauka a Hamad international airport dage birnin Doha. Babu wani zaman jira da zasu yi, dan daga jirgin ma wani jirgin suka shiga da in sha ALLAHU shine har ƙasar Chaina. Nan ɗin ma dai vip section ne ita da shi, sai dai na wannan jirgin ma yafi wancan matuƙa, dan harda gadon barci da yaji shimfiɗu na alfarma. Sai Maanal taji duk ta samu kanta da tsarguwa. Amma a zahiri ta wani dake abinta sai gajiya da jikinta ya fara nunawa na zama waje ɗaya.       Sosai Doha ta birge Maanal, duk da bazata iya ƙarar da komai na cikinta ba daga jirgi ma take kallonta, gashi dare ne sai dai tako ina akwai haske fayau kamar ka yarda allura ka ɗauka abarka. A wannan tafiyar an samu canjin yanayi, domin kuwa AA ne yay barci a yanzu, yayinda Maanal tai zaman kallon wani american film da yay mata daɗi sosai, daga ƙarshe itama dai ta sake ɓingirewa barcin a kujerar da take. Tafiya ce ta awanni takwas daga Doha zuwa Shanghai da zasu sauka ta ƙasar Chaina. Dan haka AA ya samu barci isasshe, dan sai asuba ya farka, ganin itama Maanal barcin take sai ya samu kansa da zuba mata ido. Ya jima yana kallonta kafin ya miƙe domin gabatar da alwala. Koda ya fito itama tashinta yayi tayo alwalar, duk da inda son samu ne zataso yin wanka ma, amma a wannan jirgin babu alamar akwai wannan damar, dan haka ta ɗan gyagygyara inda zata iya sannan ta fito. Salla suka gabatar, bayan sun idar kamar yanda ta saba ta ciro Alkur'ani dake a handbag ɗinta ta fara karatu, idanu kawai ya lumshe yana sauraren daddaɗan sautinta dake fidda ƙira'a dalla-dalla. A haka lokaci yayi, aka fara sanar da saukarsu nan da awa ɗaya kacal. Addu'a tayi tare da azkar suka kimtsa komansu duk da ba wani tarkace bane ba iya na hannu ne bag ɗinsu na ƙasa....            ★An buɗe ƙofar jirgi da sanyi mai ɗauke da iska mai ɗan zafin canjin yanayi na sabon gari ya bugi fuskarta. Ita tana kallon komai da yanayin sabo, mamakin ganin rana ce yanzu anan Chaina , mutanen da ke tafiya da sauri, harshen da ba ta fahimta ba, da kuma sautin rayuwar da bata saba da shi ba. Shi kuwa gogan naku, ya sauka kamar wanda yazo gida – a yanayi na izza mai nutsuwa, cikin shigar da ba ta da yawa amma tana da nauyin kamanni. Ba ya magana da yawa, amma idanunsa na bin komai cikin salo. A tare su Yaqub suka iso inda suke suna gaishesu cike da girmamawa. Ita dai kanta a ƙasa, dan girmamawar da suke bata kunya take bata musamman su CMO. CFO dai taƙi yarda ta kalla inda suke, dan ba ƙaramin danne zuciyarta take ba akan wannan ƴar tatsitsiyar yarinyar dake neman ɓata mata aiki. Sai dai a zahiri bazaka taɓa fahimtar yanayinta ba dan mace ce wayayya mai kuma wayo da iya taku.       Taji matuƙar daɗi data fahimci a hotel ɗaya zasu zauna su dukansu. Manaal tayi mamakin motar da tazo ɗaukarsu, ƙyaƙyƙyawar gaske baƙa wulik mai aiki da caji ba fetur ba. Kasare tai tana kallon chainawan da suka fito su biyu suna gaishe da AA cike da girmamawa. Shi ko ya amsa musu cikin yanayinsa na riƙe girma, sai kuma ya ɗan kalla Maanal dake gefensa da harshen Chaines da Maanal bata san ya iya ba sai yau ɗin nan ya sanar musu ga matarsa. Sosai farin cikinsu ya sake bayypana, suka juya suna gaishe da Maanal cikin harshen turanci da girmamawa. Ita kam da ƙyar ma ta iya fahimtar turancin nasu, ta amsa musu a taƙaice sai dai da kulawa. Sake maida hankalinsu sukai ga AA, cikin yaren da ba fahimta take ba sukai masa magana. A mamakinta sai taga yay ɗan guntun murmushi kawai. Samun kanta tai da ɗan shagala a kallonsa, yana yin kamar zai juyo ta kauda kanta gefe.      A mamakinta daga ita sai shi ne suka shiga motar, sauran kuwa bata san yanda suka kare ba..... Sannu a hankali motar ke tafiya bisa lafiyayyen titin mai faɗin gaske da yalwa ta yanda motoci keta kai kawonsu cike da watayawa. Motar tayi shiru. Hankalin AA naga tab ɗin da ɗaya a ƴan cainar suka bashi, Maanal kam ta maida nata hankalin ga waje tana kallon gine-gine masu ban mamaki da ƙawa. Eh lallai ga inda gini ke amsa sunan gini, duk da kuwa Abuja ba daga baya ba a ƙyaun gine-gine da tsarin anguwanni sai taga can ya koma mata local. Duk yanda taso danne shauƙinta hakan ya gaggara, a bazata batare da tasan da matsowar AA gab da ita ba da murya mai laushi, amma cike da basarwa ta tsinkaye sa a cikin kunenta yana faɗin, “Kar kiyi kamar zaki ɓata mana. Ina nan a kusa dake, ki tuna.”      A hankali ta ɗan murmusa a ƙasan maƙoshi. Sai kuma ta ɗan juyo ta kallesa cikin ido tana mai ɗan ɗage gira sama ta ce, “Lah nazata ai a Nigeria na baroka ma ni, kasan abinka da baƙauye yazo birni.” Yatsa ya kai zai ɗalli hancinta, tai saurin juya fuskarta gefe ta hanashi damar hakan. Lips ya ɗan cije, sai kuma ya koma ya zauna da ƙyau cike da basarwa.        Sai da suka iso hotel ɗin taga su Yaqub, sai dai basu tsaya a inda suke ba su sukai ciki bisa jagorancin yan chaina ɗin nan. A jere ita da shi suke tafiya a dogon corridor ɗin dake shiru babu hayaniyar komai, sai dai komai a tsaftace yake ƙal kamar kaci abinci a ƙasa. Card ɗaya ya miƙa masa yana nuna masa ƙofar ɗakin da suka tsaya cikin yaren su. Shi kuma ya gyaɗa kai kawai yana amsa batare da yace komai ba. Hannu suka ɗaga mata alamar bye suka wuce. Ita kuma tai ɗan murmushi da jinjina kanta kawai a taƙaice.        Matsawa AA yay jikin ƙofar ya saka card ɗin. Ita kuma ta ɗan tsaya sororo.........✍️ _To mun ido Chaina kuma, bari nima na shiga nawa ɗakin na watsa ruwa sai mu ɗora labari 🏃🏃, karku damu ɗakina kusa dana su Maanal ne komai zan jiyo muku 😂._ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [30/04, 4:46 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣0️⃣ ______________ .......Cikin mamaki da ɗan daburcewa ta ce, “Wai ɗaki ɗaya?” ta tambaya fuskarta cike da rauni.      Juyowa yay yana kallonta kai tsaye, sai kuma ya basar cikin zurfin furuci ya ce, “Basai kin damu ba, sunansa ɗakin barci kawai, ba ɗakin yin wani abu ba.”      Baki ta tura gaba tana ɗan kau da idanunta, shima sai ya tura ƙofar kawai ya shiga, ɗan juyowa yayi, ganin tana tsaye cikin yanayin ƙaulani har yanzu, “Ko ɗauka kike so?”         “Ni ban ce ba”.     Ta bashi amsa idonta a ƙasa, sai kuma ta motsa a hankali zuwa gaban ƙofar, jatai ta sake tsayawa, batare data kallesa ba ta ce, “Amma ba gado ɗaya ba?”.        Yanzu kam kansa ya ɗan girgiza yana kallonta da ƙyau, sai kuma ya ɗauke idanun ya ɗan kalli gefe. Da alamun ƙosawa ya ce, “You can sleep on your pride if the bed makes you nervous”. Daga haka ya matsa mata alamar ta shiga. Haka kawai ta samu kanta da sanyi jiki. Cikin ɗari-ɗari ta shiga, numfashinta na sizen, zuciyarta kam rawa take a hankali kamar wadda ke jira ace mata ar ta feta a guje. Tana jin ya maida ƙofar ya rufe ta wani lumshe idanunta. Sai kuma ta samu kanta da matsawa jikin window ko zata samu iska ta bugeta abinda ya tokare mata nunfashi ya narke. Shiru tai tana kallon hasken rana daya fara buɗewa dan yanzu ana nufar kusan ɗaya na rana ne a ƙasar.        Cike da takunsa na ƙasaita da izza ya ƙaraso inda take, tsaye yay kawai a bayan ta yana cire agogon hannunsa kamar wanda ba ya cikin gaggawa. Shima dai idanunsa na kallon garin ne zuciyarsa cike da wadatuwa da iskar dake buso su. Shiru ne ya mamaye ɗakin, ba motsi, ba rikici, sai shauƙi da tambayoyi dake cike taf a zuciyar Maanal marasa ma'ana da shiga ƙaulanin furta wa a bayyane.       Tamkar mai raɗa muryarsa a ƙurya cikin kalamin dake fita ɗai-ɗai ya furta, “Hum! K! A komai sai kin yi kamar za ki gudu ne?”.    Baki ta ɗan taɓe batare data juyo ba ta ce, “Kai kuma kullum sai ka dinga yi kamar kana son a biyo ka ba”.       Yanzu kam murmusawa yay, sai kuma ya laɓe baki kaɗan, da murya ƙasa sosai ya ce, “Ba kullum ba ne. Amma a wannan gaɓar ya kasance tare da ke watakila.”     Da sauri ta juyo tana kallonsa. Sai kuma kamar a tsorace ta ce, “Wai me kake nufi?”.        Gira ya ɗage sama yana wani ƙanƙance ido ya bata amsa da, “Duk abinda zuciyarki ta baki. Dan anan babu Aban naki dai kin sani. Garama ki lallaɓa a rabu lafiya in ba haka ba kuma jiki magayi”. Yana gama faɗa ya wuce yana wani shegen makirin murmushi irin mai saka kaɗuwar hanjin wanda ya tsargun nan...... __________★        Cikin ƴan kwanaki kaɗan Hajiya Basariyya tai wata irin rama da baƙi, ba komai ya jawo mata hakan ba sai zafin rana da uban aikin da take lafta a gidan kawu Manu. Dan takai yanzu har gona idan zaije tasa ƙeyarta yake su tafi tana taya shi da ƙananun ayyuka. Taƙi sakin jiki taci abincin gidan, ga biscuits ɗin nata sun ƙare. Sarai iya na lure da ita, amma tai kamar bata ganin ba dan itama ba shiga dabgarta take ba, ai yunwa ba ƙanwar uban wani nace ba, magana ma sai ta zama dole yake haɗa su. Tun Hajiya Basariyya na dauriya da tunanin ai kawun zai barta koda a sati guda ne harta fara gazawa. Hankalinta a tashe yake sosai da ganin ana niyyar ma ɗaukar azumi a jibi idan ALLAH ya kaimu. Ita ko tasan idan aka ce a gidan nan zatai azumi ai tagama mutuwa....        Da daddare ta yanke shawarar samun Kawu Manu ta bashi haƙuri ta tabbatar masa tayi nadama kuma ta amshi laifinta. Haka ɗin kuwa akayi, bayan sallar isha'i yana zaune yana cin tuwonsa suna ƴar hida da iya dake gefe ta fito daga ɗakin iyan. Su duka kallonta sukayi, kafin Iya ta janye nata cikin taɓe baki. Shima Kawu Manun janye nasa yay ya koma ga cin abincinsa. Sum-sum tazo ta tsugunna a gabansu kamar wata munafuka, yi yay kamar bai ganta ba, dan haka ta fara magana cike da rawar muryar son yin kuka.       “Kawu dan ALLAH kayi haƙuri na tuba. Wlhy nabi ALLAH na biku bazan sake ba. Na maka alƙawarin zan zauna lafiya a ɗakina. Ba kuma zan sake biyema wata ƙawa ta kaini wajen kowa ba. Wlhy Kawu wasu abubuwan dole ce ke sani aikatawa. Tunda Daddyn Huznah ya auro amaryarsa gaba ɗaya baya mana adalci, ya tattare komansa ya tare gareta. Agololin ƴaƴanta sune kawai ƴaƴa a gidan. Koda kwatance baya yima ƴaƴanmu irin gatan da yake musu. Ni babu kamar ma nawa, dan ita Hajiya Sadiya yana tsoron mahaifinta tunda tana goranta masa sune tushen arziƙinsa. Sannan ɗanta shine akan komai na dukiyarsa, nidai nice a baya ga komai na gidan kamar mara gata. Yanzu kaga akan auren nan nasu Huznah, ƙiri-ƙiri ya ɗauka wanda zata aura ya bama agola dan ya birgesu. Ya haɗa Huznah da ɗan Sani bayan ko ku Kawu kun san Sani ba ƙaunata yake ba, tun ma kafin a auro ni ya nuna adawarsa, dana shiga gidan kuma suka haɗe kai da Hajiya Sadiya suka dinga cin mutunci na sai da na zama jaruma. Kawu ya ake so nayi, Huznah fa ita na fara gani a duniya matsayin gudan jini, bazan so ganinta a damuwa ba tunda na san bata son ɗan Sani, kuma kowa shaida ne a kan hakan tunda tun a shekarun baya bama ta gama Secondary ba yace yana sonta tace a'a nima kuma nace a'a....”       Cikin katseta Kawu Manu daya gama wanke hannu yace, “To yanzu ya kike so ayi?”.        “Ayi haƙuri Kawu a barni na koma ɗakina naje na rungumi ƴaƴana, sannan dan ALLAH kasa baki a raba auren nan na Huznah ALLAH nasan bata jin daɗin zaman nan”.     “Ita da kanta tace miki bata jin daɗin zaman? Duka yaushe ma aka kaita gidan auren da zata fara banbance daɗinsa da akasinsa? In ce gaba ɗaya yau sati na huɗu muke, koma wata guda ba'a ƙulla ba cif. Basariyya ki kiyayeni, ki kuma fita idona, niba dattijon banza bane. Ai dama tunda Mairo (Iya) ta dawo daga bikin ta sanar min iya shegen da kike zubawa nasan kin shirya sheɗanci a zuciyarki, to ni bazan hanaki kashe auren ƴarki ba, amma ki sani, ana sakota ta koma gidan ubanta kema zan kira Usman ya sakeki ki dawo nan, kuma wlhy anan ƙauyen zaki samu miji na aurar dake. Komawa kuma ba yanzu ba dan har yanzu bakiyi hankali ba, karma ki sake samuna da wata magana anan zakiyi azumi tashi ki ban waje shashasha da bata da wani girma sai na jiki. Shekaru na nuna kansu a jikinki har kin aurar da ƴa amma hankali sam babu a tattare dake sai shaiɗanci fal a zuciya. Da kike cewa shi Alhaji Usman ɗin yana fifita amaryarsa fiye daku tafi ƙyautata masa ne shiyyasa, ku kuma kun zauna baƙin kishi, har kuna wani gorantawa yara da kiransu agololi, su waɗannan agololin zata iya yiwu ma sune zasu tallafi rayuwarku ta gaba kosu taimaki ƴaƴanku, dan ka kiyayi ɗaukakar wanda mutane suke son ƙasƙantarwa jahilcin banza da wofi kawai....        Hawaye sosai Hajiya Basariyya ta miƙe tanayi, zuciyarta kuwa tamkar zata kama da wuta saboda zagin ƙare dangin da Kawun yay mata. A ranta kuwa alwashi take ɗauka ko guduwa ne sai tayi wlhy. Dan bazatai azumi a wannan garin ba ta mutu a banza.... __________★       CHAINA (Shanghai)    Sosai zuciyar Maanal ta shiga kai kawai. Kalamansa ta shiga son fassarawa, (Hum! K! A komai sai kin yi kamar za ki gudu ne?. Ba kullum ba ne. Amma a wannan gaɓar maybe ya kasance tare da ke watakila) jitai kamar zuciyarta zata ɓare dan tsoro, sai kuma ta shiga ƙalubalantar kanta aka amsar data bashi. Wayyo ita kam taga takanta, mi mutumin nan ke son maida ita ne, yama barta da gajiyar tafiyar nan ta awanni mana, amma sai ya takaleta da rigima. Waiwayawa tai ta ɗan kallesa, dai-dai yana zare shirt ɗin jikinsa, ay da sauri ta juya zuciyarta na bugawa, sai kuma ta rumtse idanunta da ƙarfi dan ingarman jikinsa yaƙi barin cikinsu. Eh sunyi wata rayuwa a baya a bigiren ƙuruciya, duk da ba sa'anta bane ko a wancan lokacin amma dai yaron ne shima. A lokacin da ƙaddarar rabuwa tazo musu yana a gaɓar kammaluwar zama cikakken namiji ne, kuma sam baya tu'ammali da gym a wancan lokacin, sannan bai taɓa yarda ya zauna a gabanta koda da dogon wando da singlet bane ba. Dan zata iya rantsewa bata taɓa ganinsa ba kaya jikinsa ba, sanin ma tana shigar musu ɗaki a wasu lokutan kafin ma Oum ta hanata idan zaiyi wanka sai ya kulle ƙofa, ko yace mata zaiyi wanka karta sake ta biyoshi, itama kuma data fara mallakar hankalinta ta fahimci mi yake nufi tuni ma irin waɗan nan yanayin take zille masa....... “Tunanin mi kike yi?”.      A ɗan zabure Maanal ta juyo gareshi, dan a bazata taji saukar muryar tasa a cikin kunnenta. Babu shiri kuma ta sake juyawa tare da matsawa a kusa da shi ta koma jikin window ɗin sosai. Muryarta har ɗan rawa-rawa take wajen faɗin, “Wai dan ALLAH mi kake son maida kanka ne? Hakan fa baida ƙyau kana zuwa gabana babu kaya kai ko kunya ma baka ji”.      A hankali AA ya kai hannunsa kan gashin gemunsa daya zagaye har zuwa kumatunsa yana ɗan jansa kaɗan-kaɗan, yayinda ya zuba mata idanu a wani irin yanayi. Jin shiru yasa ta ɗan sake juyowa a tunaninta ya bar wajen, sai suka sake haɗa ido, ai a sukwane ta sake juyar da kanta. Ji take kamar ta saki kuka, ALLAH kunyarsa take ji, haba jama'a Bestyn ta fa, wlhy al'amarin ya mata girma. Sai kawai taji hawaye na cika mata idanu ma, dan harga ALLAH ita dai wannan zuwa Chaina ya zame mata alaƙaƙai.          Shi ko AA a wannan gaɓar dariya ma ta soma bashi, amma dai baiyi ba, fuskar tasa ma babu walwala kamar dai yanda ta kasance take tun barowarsu gida. Sai in yaso yin murmushin ne yake yin taƙaitacce. Barin wajen yayi yana ƙarasa kunce belt ɗinsa, dan shi da dogon wandon kawai suka rage sai na ciki. Belt ɗin kawai ya cire ya nufi bayi da dogon wandonsa, ƙarar rufe glass door ɗin ya saka Maanal da komai ke neman ƙwacewa sakin nannauyan numfashi. Magana ta ALLAH bazata iya zaman nan ba, wlhy a takure take matuƙar takura, ita dai bara ya fito, zata roƙesa ya barta ta koma wani ɗakin kawai, dan zamansu tare anan zai iya sakawa zuciyarta ta buga ne, sannan zai iya karya mata lago da shawarar su Didi. Jin ƙafafunta sun fara sagewa cike da sanyin jiki ta baro wajen window ɗin, a ɗaya daga cikin sofas ɗin ɗakin dake tsare matuƙa takai zaune, sai ta juya ma ta inda zai fito baya, wayarta ta ciro ta fara game, duk da ba fahimtarsa take ba gara tayi dai. Ƙarƙashin zuciyarta kuwa kewa take ji, kewar su Oum da Ammien ta. Ashe sanda tana Abuja dan suna waya ne da Ammien a koda yaushe shiyyasa take jin damuwar rashinta a kusa da ita kaɗan-kaɗan, yanzu kam sunyi nisa da juna, ta yanda bama tasan yaya zasuyi koda waya ba tunda ba layin ƙasar ne da ita ba..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [01/05, 2:51 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣1️⃣ ______________ .......Maanal ta matuƙar shagala a tunaninta AA ya fito a bayin, sanye yake da bathrobe golden yellow, gaba ɗaya ƙamshin sabulunsa na shower gel ya mamaye ɗakin, ɗan kallon Maanal data juya baya yayi ya ɗan taɓe baki yana cigaba da goge kansa da ƙaramin towel. Hankalinsa kwance yaje inda take ya zauna a wata kujerar daban. A dakensa ya furta, “Ki tashi kije kiyi wanka dan zamu fita shopping ɗin abubuwan buƙata”.         Batare data yarda ta kalleshi ba ta girgiza kanta. Sai kuma muryarta ƙasa-ƙasa kamar zatai kuka ta ce, “Ni ba sai nayi wankan ba, dan ALLAH mizai hana na koma wani ɗakin koda na kusa da kai ne, kaga zamanmu anan kai zan takura maka ai....”       “Ni nace miki na takura?”. Shiru tayi dan yanda yay maganar miryarsa da ɗan tsauri sai taji wani kalar shakkarsa.    “Dake nake fa! Kuma nasan kin jini”.       Yanzu kam kanta dake duƙe ta girgiza masa, dan taƙi yarda ta ɗago ta kalla koda sashen da yake ma. Ciki-ciki shima yaja tsuki da yazo masa a bazata, kafin a daƙile ya ce, “In kuma kina da kuɗi sai kije ki kama wani ƙofa a buɗe take”. Daga haka ya miƙe ya bar mata wajen. A bakin gado ya zauna ya shiga gyara jikinsa zuciyarsa na zafi, haka kawai yaji haushin maganarta, wai miyasa bazata sassauta ma zuciyarta ba, miyasa bazata fahimcesa, abubuwa sun masa yawa matuƙa, yana son raba koda wani yankin ne na damuwarsa da ita amma taƙi bashi fuska, bai gajiya ba yana cigaba da binta dan yasan shi mai laifi ne a gareta, amma koyaya bazata tausaya masa ta sassauta masa ba ne.         Maanal da tunda ya maka mata baƙar maganar in tana da kuɗi taje ta kama ɗaki taji hawaye sun cika mata ido, sai kuma suka gangaro a hankali. Veil ɗinta tasa ta ɗauke su, sai kuma ta ajiye wayar ta miƙe, bayin ta nufa. Ya ɗan bita da kallon ƙasan ido harta shige. Tana maida ƙofar ta rufe ya janye idanunsa yana sauke ajiyar zuciya...       Kafin ta fito ya shirya abinsa tsaf cikin ƙannan kaya. Dogon wando ruwan ƙasa ya saka t-shirt mai v neck mara nauyi data kwanta a jikinsa matuƙa ta fiddosa a ingarmansa. Turare ya saka sannan ya shiga ɗan gyara sumarsa sama-sama da kwantaccen gashin kumatunsa. Ficewa yay a ɗakin bayan yayi sallar azhar dan ya tabbatar bazata fito ba in har yana ciki tunda har yanzu tana a ciki a maƙale, samun kanshi yay da girgiza kai kawai. Wai yau shine Maanal ke jin kunya, yarinyar da a gabansa ta fara dukkan abinda take ɓoye masan a yanzu. Yarinyar da yasha yima tsarki. Yarinyar da yasha wanke ma underwear. Yarinyar da yasha goyawa a bayansa. Oh-oh duniya-duniya, Maanal ɗinsa, Bestyn sa na jin kunyarsa. Koda yake shi hakan ya masa, yana son mace mai kunya, dan wannan noƙe-noƙen da take masa ƙara daraja take a idanunsa, irin wannan hallayar tatace tayi ƙaranci a tattare da ƴammatan yanzu shiyyasa ya tsani mafi yawancin su. Kaga yara ƙanana tun basu tafasa ba suna neman ƙonewa, masu ɗan ƙoƙarin ne suke gama Secondary da wannan yanayin, ana shiga jami'a sai a fifirce su wayayyu. Humm mutane da shirme, rawar kai da rashin kamun kai ne wayewa wai. Wannan abu na ƙona masa zuciya. Ai a baka yarinya a ɗanyarta bata san komai ba na rayu, koda ta sani ɗin wannan kunyar ta hanata iya bayyanawa a gabanka shine ka more alaji. Amma ka aureta kafin ka kai mata kiss ta miƙo maka baki, kafin ka kai hannu jikinta ta sallama maka jikin kaico. Ai yarinya ta dinga jin kamar zata nutse a waje idan kuna tare, koda ta san mi kake nufi ta nuna bata sani ba, duk iliminta duk wayewar zurfin karatunta a gabanka ta maida kanta bata san komai ba shine zaka dinga jinka a wani shauƙi da ƙasaitar cikakken namiji. Ka dinga kallonta tamkar wata baby doll a gabanka, ka koya mata karatunka idan akazo gaɓar da zata goge sai akai matsayar da ita zatai maka bita. Amma an kawo maka yarinya tana nuna maka ita tasan komai idonta a buɗe suke ai akwai matsala, idan kai wasa ma wata sai ta maka fyaɗe, ko kuma kaita zargin kanka da ita kodai tama taɓa yi ne a waje kafin kai. Dan ko ta kawo maka mutuncinta zuciyarka zatai ta tunanin an ɗan sha minti gaskiya.....        Ƴar karar Maanal ta maidosa hayyacinsa daga dogon tunanin da ya tafi, ƙofar ya kalla, sai kuma ya murɗa handle ɗin a hankali ya tura ya shiga. Daga bakin ƙofar ya hango yanda take kici-kici da riga alamar zip ne ya sarƙafe mata a gashi. Numfashi ya ɗan furzan, sai kuma ya shiga takawa a hankali har inda take, hakan yay dai-dai da tuntuɓe da tai da bakin lallausan carpet ɗin gaban gadon saboda yawon da take ɗanyi a wajen na kici-kici. Riƙota yay jikin nasa, yay mata zobe da hannunsa ɗaya a kan ciki, ɗayan yana ƙoƙarin kaishi ya riƙe hannunta da take kici-kici cire rigar.        A ɗan rikice ta ce, “Na banu waye?”. Sai kuma tai ƙoƙarin sunkuyawa, hakan ya bama ƙirjinta damar kwanciya a tsintsiyar hannunsa dake a saman cikinta. Harga ALLAH ji yay yana neman daburcewa, amma sai ya danne da ƙyar, cikin cije lips da ƙanƙancewar murya ya furta, “Mijinki”.          Dama zuwa yanzu ta nutsu, dan ƙamshin turarensa ya isar mata shi ɗin ne tun kafin ya faɗa. Miƙewa tai tsaye sosai ta tsaya da ƙafafunta. Shima sai ya sauke numfashi a rarrabe ya kamata ya zaunar a bakin gadon shima ya zauna. A mayuƙar kasalance ya shiga zare gashin a zip ɗin. Ajiyar zuciya sosai Maanal ta sauke lokacin da ya gama zarewa rigar ta sauka. Suna haɗa ido ta kauda kai da sauri, ƙasa-ƙasa ta ce, “Thanks you”.      Miƙewa kawai yayi batare da yace komai ba ya ɗauka jacket ɗinsa mara nauyi  da scarf dan yasan zuwa anjima kaɗan zasu iya jin sanyi duk da garin Shanghai ba gari bane mai yawan sanyi ya nufi ƙofa. Sai da ya buɗe zai fita sannan ya furta, “Jiranki nake”. Daga haka ya maida mata ƙofar ya rufe. Duk ji Maanal tai babu daɗi, dan ta fahimci kamar a cikin fushi yake har yanzu, bayan kuma ya fara sakkowa lokacin suna a jirgin Nigeria zuwa Qatar, bata san kuma miya ƙara ɓata masa rai ba tunda suka iso. Jikinta dai duk a sanyaye ta ƙarasa shiryawa, dan sam bata son a dalilinta taga wani a ƙunci, kodan ta ɗanɗana zafin hakan taji a shekarun baya oho, tayi ƙyau sosai cikin doguwar rigar atamfar, daka ganta kaga cikakkiyar ba'afirikiya. Bayan tai ɗaurin zarah buhari ta yana gyalenta sannan ta ɗauka handbag ɗinta ta fito. A bakin ƙofa ta ganshi tsaye, ya jingina jikinsa da bango tare da ƙafarsa ɗaya, ɗayarce kawai a ƙasa, sai hannunsa ɗaya jacket ɗinsa ce a saƙale, ɗayar kuma yana latsa waya.        “Na gama”.   Ta faɗa cikin ƙaramin sauti ganin baiko motsa ba duk da tasan yaji fitowarta. Kaɗan ya waiwayo kansa ya kalleta, sai kuma ya ɗauke yana mikewa tsaye sosai ya zura wayarsa a aljihu. Tafiya suka fara yi a nutse, kowa zuciyarsa na tunani daban, har suka gama shanye rabin corridor ɗin sannan suka iso ga elevator. Shine ya danna ya fara shiga, kafin tabi bayansa sannan ya sake dannawa ƙofar ta rufe. Cikin abinda baifi minti ɗaya ba suka iso, ƙofar na buɗewa ta yunƙura zata fita ta tsinkayi shigar lallausan tafin hannunsa a cikin nata. Ciki-ciki kowa ya sauke ajiyar zuciya, sai kuma suka kalla juna a lokaci guda. Fin seconds goma suna kallon junan cikin ido, motsin masu jiran su fito suma su shiga ne ya maido su hayyacinsu, itace ta fara janye nata, kafin shima a slowly ya maida ga mutane biyu dake a ƙofar. Ƴammata ne su biyu, suka wani bishi da kallon ƙurulla, hannun Maanal ɗin ya sake damƙewa suka fice. Dai-dai suna barin wajen ɗaya a cikin ƴammatan ɗaya takai bakinta wajen kunnen ƴar uwarta tai mata gwargwaɗe daya sakasu yin ƴar dariyar shaƙiyanci daya tabbatar da maganar tasu akwai iskanci a ciki. Basu ƙarasa jin abinda suke faɗan ba dan sunyi nisa. Maanal dai jitai zuciyarta ta ƙuntata da dariyar yaran, dan ita yara zata kirasu duk da ta tabbatar bazasu girmeta ba dan suma dai bazasu wuce 20+ ɗin ba kamar ita.      Ganin sun fito a hotel ɗin gaba ɗaya a ƙafa har sun fara tafiya a titi Maanal ta dakata. Shima tsayawa yay sai kuma ya ɗan kalleta. Cike da shagwaɓar da ta saka tsigar jikinsa tashi ta ce, “Wai babu a bin hawa?”.      Idanunsa masu laushi ya zuba mata, cikin wani irin kallo dake mata tasiri a cikin jiki, ganin bashi da niyyar tanka mata sai ta sake narke fuska. Kamar zatai kuka ta ce, “Wai mi akai maka kaketa fushi ne tun a gida?”.         Sosai yanzu kam ya lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kanta, batare daya amsa maganar ƙarshe ba ya ce, “A ƙafa zamuje dan jikinmu ya warware da zaman jirgi”. Yana gama faɗa yaja hannunta kawai suka cigaba da tafiya. Harga ALLAH jitai zuciyarta ta raunana. Sam bata son ganinsa a damuwa. Hankalinta tashi yake. Musamman yanzu data fahimci irin wannan yanayin yana samosa ne daga Mamy. Dan lokacin da zasu taho ta lura da kallon gargaɗin da Mamy ke masa, wanda ta tabbatar ko rantsuwa tayi babu kaffara akanta ne game da wannan tafiyar da babu yanda zatai ta ya hana yinta da ita. Cike da son lallashinsa ta matsa jikin hannun nasa sosai ta kwantar da kanta. Cak ya tsaya yana kallonta, itama kallon nashi takeyi idanunta na ɗan tara ƙwalla. Kamar mai raɗa cikin motsa lips ɗinta a hankali ta ce, “Baka ƙyau idan kana fushi, Please kayi murmushi”.         Idanunsa dake wani kalar raunana a cikin nata ya janye slowly, sai kuma yay ɗan murmushin gefen baki a taƙaice. Murmushin itama tayi, tare da faɗin, “Thanks”. Komai bai ce mata ba suka cigaba da tafiya. Duk inda suka gitta binsu ake da kallo musamman saboda shigar jikinta da ta zamewa wasunsu baƙon abu. Kai da abu yakai ya kawo ma har tsaidasu ake dan ayi hoto. Sai dai AA yaƙi bada haɗin kai dan sai yay kicin-kicin da fuska, ko kuma ya hana a tsaya ta gefen Maanal ɗin.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [01/05, 2:51 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣2️⃣ ______________ ........Sunzo dai-dai gidan wani abinci ya tsaya, kallonta yay murya a ƙurya ya furta, “Kina jin yunwa?”.         Dan kawai kar yaga ta gwalesa ta jinjina masa kai, dan bata wani jin yunwa ita kam. Ciki suka shiga, Maanal tabi wajen da kallo tana jinjina tsaruwarsa da ƙawatuwarsa. Sun kuma samu tarba ta mutuntawa da akema kowanne customer. Wajen zaman daya dace dasu aka basu, tare da takardar da tsare-tsaren abincin ke ciki. Shine ya amsa yana dubawa, dan su dai komai nasu da yarensu suke rubutawa. Hajjaju Maanal kuma ba'a iya Chaines ba. Shi kansa mamakin sanda ya iya yaren takeyi, duk da dai bata da tabbacin ko ya iya sosai-sosai ko sama-sama ne. Tana nan ta shagala a tunani har aka fara kawo abubuwa ana jera musu. Ganin yanda take bin komai da kallo sai a sannan AA yay magana. A taƙaice ya ce, “Komai dake anan Halal ne”. Ajiyar zuciya ta sauke kamar dama abinda takema waswasin kenan. Sai kuma ta ce, “Amma to musulmai ne masu wajen?”.        Kansa ya jinjina mata, dai-dai waiter ɗinsu na sanar masa an kammala. Ya jinjina mata kai cikin harshen Chaines yace, “Thanks you”. Sai da tabar wajen sannan ya maida hankalinsa ga Maanal yana ƙoƙarin tura mata abinda yasan zata iya ci a gabanta. Tare da cigaba da amsa mata maganarta. “Musulmai ne ita da mijinta dake da wajen”.       Kai Maanal ta jinjina, sai kuma ta saki murmushin daya sashi tsayawa yana kallonta. Tana ɗagowa suka haɗa ido tai masa alamar (miye) da ido tana ɗaure fuskar. Kansa kawai ya ɗauke ya fara cin abincin a nutse. Itama fara ci tayi, ba laifi da daɗi, sai dai test ɗin akwai banbanci mai nisa tsakaninsa da namu na gida. Haka dai ta daure taci batare da yin ƙorafi ba. Shi ko jira yake tai ƙorafin dan yasan zatayi, da batayin ba kuma yayi mamaki amma bai ce komai ba. Sun ɗan jima a gidan abincin kafin su fito, yanzun ma a ƙafa suka cigaba da tafiya, sai dai tafiyan bai nisa ba suka isa wani ƙaton Mall mai ƙyawu sosai. Dan bayan wajen shopping akwai wajen wasan yara, da ɓangaren games na manya, akwai wajen hutawa na masoya, kai da abubuwa daban-daban. Sudai wajen kasuwar suka nufa, ɓangaren tufafi ma. Anan ɗin ma sun sha kallo, dan Maanal har sai da taji kallon ya fara mata yawa ita kam. Dan haka ta ƙara maƙurewa jikin AA. Shi da kansa ya shiga zaɓa musu kayan daya kamata, na fita da na shan iska da sai dai a saka a cikin ɗaki. Sai jackets musamman ita duk da yasan ba garin sanyi bane sosai sai irin yamma haka da safiya, a yanzu haka ma yayi mamaki da batai ƙorafi ba, koda yake ƴammar bata gama yi ba rana ce da ɗan sauran zafi kaɗan. Hannunta yaja ɓangaren underwear. Maanal tai tsuru-tsuru kunya duk ta baibayeta. Cike da neman magana ya ce, “Anan aikinki ne ke zaki zaɓa mana Besty”.         Cikin ɗan waro idanun ta ce, “Mi ɗin?”.     Da ido yay mata nuni da underwear ɗin. Ai ba shiri ta juya baya tana faɗin, “Ni ALLAH ka daina min irin haka baida ƙyau”.         Ɗan murmushi ya samu kansa da yi, sai kuma ya ɗan leƙa fuskarta. Da sauri taja mayafinta ta rufe fuskar. Abinm ma sai ya bashi dariya. Amma dai bai dara ɗin ba ya barta yaje yana zaɓa musu. Nashi ya fara zaɓa a ɓangaren maza. Sai kuma ya koma na matan. Dan tsabar son ƙureta parckeg na b&p ya ɗakko yazo gabanta, kamar ba daga bakinsa maganar ta fito ba ya ce, “Besty wane size?”.      Ya subahannallah, mutum nan dai so yake ya kasheta kafin su bar ƙasar mutane, ai da gudu-gudu ta nema barin wajen amma ya riƙoto, hannun daya riƙetan ta kama ta ɗan ciza. Babu shiri ya saketa yana faɗin, “Ouch! Ke dai muguwa ce”.      Gwalo ta masa tabar wajen. Cikin ɗan ɗaga murya kaɗan yace, “Zamu koma masauki ai zaki biya diyya yarinya”.      Cak ta tsaya, shi kuma ya juya abinsa yana murmushi ya zaɓa mata wanda ya tabbatar zasu mata duk da dai ƙiyasi yayi da zuciya......      _________★         Yau RK ya kamo hanyar Abuja domin dawowa kan aikinsa. Kasancewar yana son ɗaukar Najma a Zaria ta mota ya biyo. Aiko bai ɓata lokaci a Zaria ɗin ba dan itama Najma ɗin a shirye take tsaf shi kawai take jira. Alhamdullah ƙarfe biyar a ƙofar gidan su AA tai musu. Lokacin da motar RK ke shigowa babban harabar gidan Saheeba da Nuratu da Mamy na zaune suna shan iska. Sai su Naufal dake yawo a motocinsu ƙanana shi da Anum. Oum bata nan tana maƙota gidan Hajiya Shuwa. Dan tunda ta dawo bata shiga ba sai yau. Nibras da babban yaya da Fawzan kam basu dawo aiki ba. RK na kallon irin kallon ƙurullar da suke bin motar tashi da shi, dan basu santa ba sabuwa ce dal daya ɓare saboda angwanci. Tinted glass ne shiyyasa basa iya ganin kowaye. Najma ce ta fara buɗewa ta fita, cike da ɗoki ta ƙwala kiran sunan Naufal da Anum. Atare yaran suka juyo motocin nasu kowa na rige-rigen isowa saboda ganin Aunty Najman Zaria. Suna isowa kowa ya fito suka rungumeta. RK na fitowa sukai arba da shi suka saketa sukai kansa, gaba ɗayansu ya ɗaga a tare yana dariya. Dai-dai nan motar Fawzan ta shigo gidan, kamar haɗin baki babban Yaya biye da shi. Sai a lokacin Saheeba da Nuratu suka taso suna faman taɓe baki dan Mamy ce tace suje kar ace basu tarbesu ba.      Wani sassanyan kallo Najma da Fawzan sukama juna, duk da kuwa tare yake da Nibras a motar. Koda suka fito cikin ƴar basarwa ya ɗaga Anum dake masa oyoyo yana kallon Najma ƙasa-ƙasa yace, “Ba gaisuwa love?”.          Da sauri ta kalla gefensu tana fatan kada wani yaji, sai taga hankalin kowa nakan Uncle Rafeeq. Maimakon ta fara gaida Fawzan sai ta fara gaishe da babban yaya. Cike da kulawa da ƙauna irin na ƴan uwantaka da aka san duk wani jinin Darma da ita yake amsa mata yana tambayar Mamanta da sauran ƙannenta. Ta ce, “Duk kowa lafiya yake suna gaishe ku yaya”.       “Muna amsawa. Amma nan za'a mana azumi ba?”.       Kanta ta jinjina masa tana murmushi. Shima murmushin yayi da sanya mata albarka, sannan ya maida hankalinsa ga RK da suke gaisawa da Fawzan. Itama sai lokacin Najma ɗin ta gaida Fawzan ɗin. Amsa mata yay normal kamar yanda ya saba a baya. Ta juya ta gaida Saheeba. Tasan Nuratu, sai dai basa shiri, dan Nuratu fa ita bata cika zaman lafiya da mutane ba musamman idan ta fahimci ka fita to in sha ALLAHU kai ka zama abokin gabarta. Ƙin gaida Nuratun tayi ta juya ga gaida Nibras. A daƙile ta amsa mata, wannan ita kuma halinta ne, dan haka Najma bata kawo komai a ranta ba.        Inda Mamy ke zaune suka nufa, fuskar RK da murmushi yake gaisheta, yayinda Najma taje ta rungumeta tana faɗin, “Oyoyo Hajiya Mamyn mu”.     Da ƙyar Mamy ta haɗiye abinda ta tokare mata zuciya, dan ranta a ɓace yake tun tafiyar su AA ta jiya. Gashi har yanzu basu kirasu ba balle ta tusa masa gargaɗin dake a ranta. Sun gaisa cike da mutunta juna ita da RK, kafin ta maida hankali akan Najma. A kuma lokacin ne Oum ke shigowa gidan. Wayyo tuni Najma ta saki Mamy ta sheƙa da gudu ita da su Naufal wajen Oum ɗin. Suma su Babban Yaya da Fawzan da RK ɗin duk wajen Oum ɗin sukayi. Haka suke mata ko yaya ta fita data dawo duk su zagayeta kamar wasu yara. Da mamaki Oum dake shafa kan Najma tana rungume dasu Naufal tace, “Lallai yau ango ne a Abuja? Ai mun zata kayi ƙaura ka koma Kano”.      Dariya RK yayi da faɗin, “Dafa za'ace nai hakan ai da kun min gata Aunty”.      Dariya Babban Yaya da Fawzan suka sanya, yayinda Oum ta riƙe baki. Babban Yaya yace, “Uncle ai babu damuwa barinka zamuyi ka koma abinka”.         RK yace, “Yauwa Son kuyi taimako, ni dama za'a saya min ticket zuwa bayan isha'i ina Kanon dabo abina ai da yafi”.     Da wannan dariya suka shige sashen Oum. Bayan su Mamy sun mata sannu da dawowa. Sai dai su basu bisu ba, sai ma takaici ne daya saka Mamyn wucewa sashenta tabar Nuratu da Saheeba anan suna gulma. Nibras kuwa tayi sashensu dan yanzu ba zuwa sashen Oum ɗin take ba tunda su AA suka bar ƙasar.....        Najma na baza idon son ganin Maanal Oum ta sanar mata ai basa ƙasar, jiya suka wuce Chaina amma kwana goma zasuyi zuwa sati biyu su dawo. Sam Najma bata so hakan ba. Amma ta musu addu'ar dawowa lafiya.         Shi ko RK dariya yay da faɗin, “Ɗanki ya samu lafiya dai, harda tafiya honeymoon”.       Itama dariyar tayi, ta ce, “Aiki fa sukaje Rafeeq. Honeymoon ɗin nan ko za'aje shi sai dai bayan salla in sha ALLAHU. Ni nazata da Nuwaira zaku taho nan ɗin”.      “Wlhy naso hakan Mah-mah ce ta hana, wai na bar mata yarinyarta sai bayan salla tunda bata jin daɗi”.         Oum tace ALLAH ya bata lafiya. Fawzan cike da tsokana yace, “ALLAH ya raba lafiya Uncle”.    Filo RK ya ɗauka ya jefa ma Fawzan, ya miƙe ya fice yana dariya. Shima RK da Babban Yaya miƙewa sukai suna dariyar suka fita dan lokacin sallah yayi. Oum dai nata murmushi, dan ita kanta da RK ɗin yace Nuwaira bata jin daɗin abinda zuciyarta ta kawo mata kenan har an samu ciki. Addu'a tai musu tare da miƙewa ita da Najma sukai ciki domin yin sallar magrib tana addu'ar ALLAH ya kaita randa zataga na AA da Fawzan haka..        Bayan sallar isha'i sukai zaman cin abinci, anata hira cike da farin ciki dan harda Abah duk da a sashen Mamy yake yau. Amma ganin ɗan uwansa yace anan zaici abinci shima. Saheeba da Nuratu dai suna sashen Saheeba ɗin sun ƙulle suna tsogume-tsogume, dan tunda AA ya wuce ko sashen Mamyn ma Nuratu ba son zama take ba, koda yaushe tana nane da ƴar uwarta ne. Itako Nibras tana sashenta, abin duniya ya isheta. Tun juya take dakon jiran jin AA ya kira waya amma shiru kake ji. Har gwada number sa da yake amfani da shi in yaje Chaina ɗin tayi amma bata shiga ba. Dama ta sata ne a wayar Fawzan, ta adana da wata ɓoyayyar number ɗinta data tanada dan AA amma tunda ta sai layin ta kasa kiransa balle masa ko text ne saboda tsoro. Ana cikin hirar Fawzan da Najma suka saci jiki kitchen kamar masu tattare kaya, anan sukai ɗan sabuwar gaisuwa da hira sama-sama. Gudun kada a gane su suka dawo. Shi dai RK ma dariya suke bashi, dan yanzu kam ya sake tabbatar da abinda yake hasashen..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [02/05, 6:15 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣3️⃣ ______________ ......Sai da AA ya tabbatar ya tura dukkan siyayyar tasu masaukinsu sannan. Maimakon wucewa gida wani garden ya kaita. Wajen ya matuƙar birge Maanal. Anan sukai salloli suka huta har zuwa duhun dare kafin suka fito. Ganin yanda take naɗe hannaye a gyale saboda sanyi ya sashi cire jacket ɗinsa. Gabanta ya dawo ya tsaya, hakan yasata ɗago idanunta ta kallesa. Shima kallon nata yake. Cikin sanyin murya idanunsa a cikin nata ya ce, “Sanyi?”.     Kanta ta jinjina masa tana ɗan lumshe nata idanun dan bazata iya jurar kallon nan nasa ba. Shima nasan ya lumshe ya kuma buɗe a hankali. Sai kuma ya dafa kafaɗarta ya matsota jikinsa sosai. Harta gama sallamawa rungumeta zai yi sai taji saɓanin hakan. Jacket ɗin tashi ya rufo mata ta baya, sannan ya ɗan matsa ya gyara mata ita a kafaɗinta sai ta rufeta ruf. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali, sai kuma ta ɗan kallesa ta kauda idanun ta ce, “Kaifa? Riganka fa baida wani kauri”.          “Karki damu bana jin sanyi”.      Ya faɗa ƙasa-ƙasa yana kama hannunta suka cigaba da tafiya. Yanzun ma a ƙafa suka nufi hanyar gida, yasan ta gaji, amma gara suyi hakan dan in sun kwanta su samu damar yin barci da ƙyau. Sosai birnin Shanghai ya ƙara burge Maanal. Tana mamaki da jinjina fasahar mutanen nan wajen iya tsara gine-gine dogayen gaske. Ga wutar lantarki da ba'a maganar ɗaukewarta ma. Akan titi fa suke amma haske tako ina abin zabbirgewa. Suna isowa hotel ɗinsu taji zuciyarta ta fara rawa. Amma sai ta dake tana mai roƙon UBANGIJI hana tabbatuwar abinda take ma tsoron. Sosai tayi mamakin ganin dukkan shopping ɗinsu a ƙofar ɗakinsu. Card ɗin ƙofar yasa ya buɗe, kafin yakai duƙe ya ɗiba kayan duka ya shiga da su, ita kuma tabi bayansa. A hankali ta zare rigar tasa daga jikinta kamar bata so, dan wani irin nutsuwa da sanyin zuciya ƙamshinsa ke sakata. Zama tayi akan kujera, shi kuma ya shiga ƙoƙarin rage kayan jikinsa. Sai kawai ta duƙar da kai ƙasa. Yana lure da ita, sai dai baice komai ba ya gama ya wuce bayi. Ya ɗan jima kafin ya fito, nan ma bata kallesa ba. Tadai fahimci wanka yayo kodan mayataccen ƙamshin shower gel daya cika ɗakin. Shi ko hankalinsa kwance yay shirin barcinsa da ɗaya daga cikin kayan da sukai shopping dan harda na barci. Cike da godiyar UBANGIJI yakai zaune a bakin gadon yana ɓalle murfin robar ruwa yakai bakinsa. Sai da yasha kusan rabi sannan ya dubi Maanal dake zaune kamar wata marainiya. Kansa ya ɗan girgiza, kafin ya ajiye ruwan babu wasa a muryarsa ya ce, “A zaune zaki kwana kenan?”.      Kanta ta girgiza, sai kuma ta mike batare data kalla inda yake ba. Wajen kayan shopping ɗin nasu ta nufa, tunda a gabanta ya ɗauka kayan barcin, a kayansu kuma ɗazun taga bai ɗakko mata nataba dan iya kaya kawai ya zubo mata kala shida. Sai b&p ɗinta ƙwara ɗaɗɗaya datai amfani da su ɗin nan da zasu fita. Cike da nuƙu-nuƙu ta ɗauka duk abinda take buƙata, ta wuce bayin sum-sum kamar za'ace ar ta fece. Shi dai ta ƙasan ido kawai yake kallonta, a ransa ko dariya yake da mamakin mutuwar bakin tsiwa. Ta jima a bayin dan shi har ma barci ya ɗaukesa sannan ta fito, dama kuma tayi zamanta ne dan har yay barcin. Daɗi kuwa taji sosai maganin yayi ɗin, kayan data cire ɗin ta ajiye, sannan ta zare ribbon ɗin kanta ta tifke gashin, veil ɗinta na abaya ta ɗauka ta ɗaura a kan, sannan ta juya tana kallon ɗakin. Bayan gadon babu wani abu da zata iya kwantawa akai, dan su kansu kujerun bazasuyi wani daɗin kwanciya ba. Sai dai carpet ɗin dake a ƙasa. Shi kuma tana tsoron sanyi, dole dai yau ko taƙi ko taso a gado ɗaya zasu kwanta kenan. Karan farko ta ɗan kai dubanta a gadon. Ba wani babba bane can, kamar dai 6-by-6, yanda ya kwanta a gefe ta sake fahimtar ya bar mata ɗayan wajen ne ta kwanta. Batace komai ba cike da kasalar jiki data gaɓɓai ta nufi gadon, kamar mai ɗofanuwa akan wuta ta zauna kaɗan a baki-baki, sai kuma ta zubama bayansa daya juya mata ido, shima dai wando ne da riga a jikin nasa masu taushi kalar blue. Sun masa ƙyau, sai ƙamshin turarensa ke bugunta. Numfashi ta sauke ƙasa-ƙasa, sai kuma takai hannu tana jawo pillows ɗin gadon dake da yawa ta shiga jerawa a tsakkiyarsu. Ɗaya daya rage ta ajiye shi saitin ƙafafunsa sannan ta kwanta suka kasance a kwanciyar kai da ƙafa kenan. Duvet ɗin ta ɗan ɗaga ta shiga ciki, ta lulluɓe har zuwa wuyanta saɓanin shi da iya ƙafafu kawai ya rufa. A haka tai addu'ar barci, tun zuciyarta na ɗar-ɗar har barcin dai na gaske yay awan gaba da ita.          Zuwa can AA ya juya, yana kai hannunsa zai gyara duvet yaji ya tokari abu, idanun nasa ya buɗe dake cike da barci, ya ɗan zubama pillows ɗin data jera ido, sai ita kuma dake can ƙarshen gado kamar zata faɗa, dan ya tabbatar in har tai ƙwaƙwƙwaran juyi babu abinda zai hanata wantsalawa ƙasan. Kansa kawai ya ɗan girgiza, a ransa yana faɗin (yarinya idan nayi niyyar yin wani abu ba pillows ba ko block kika jera ai sai nayi) ya taɓe baki tare da maida idanunsa ya lumshe....... _________★      GIRO   A fusace ta bankaɗe labulen ɗakinta ta fito har zanen jikinta na neman taɗeta, shi kuma ya nema kwancewa a jikin nata tai saurin yayumoshi ta soke. Cikin rawar murya data jiki ta ce, “Sailuba uban waye ya shigar min ɗakin yanzu dana fita?”.        Da farko kamar Sailuba batama jita ba, tanata tankaɗen garin tuwo da zata ɗora, sai da ta shaƙi iska dan kanta ta ce, “To Gwaggo nikam ina zan sani, nima yanzu nake dawowa sashen ina ɓangaren su Zainaba ina jiran Audu ya kawo min niƙa, wani abu akai miki a ɗakin ne?”.            A harzuƙe Gwaggo tace, “In ba wani abu akai min ba zakiga na fito ina tambaya ne. To wlhy bazan yarda ba, yanzu ƴan sauran kuɗin nan da suka rage mana ƙarshe da za'ai noma akeje aka lalube, kuma kema kin san ɗayan biyu ne, a cikin ƴaƴanki ko Haƙilah ko Sule, tunda ALLAH ya basu dogon hannu da bai iya zama waje guda sai sunyi ƴan ɗauke-ɗauke......”     “A'a Gwaggo ya zakice haka, naga ɗauke-ɗauken nan kowa ya samu dama yi yake yi, sannan yaran wasu sashen ma bazasu iya zuwa su ɗauka bane. To Haƙilah ma bata kwana a gidan nan ba tana gidanmu ne balle ace itace, shi ko Sule tun safe yace min zai tafi Suru sayen kayan sana'arsa.....”          “Siyen kayan sana'a ko sayen kayan shaye-shaye da yake koyama ƴaƴan mutane. Tunda kince basa nan sai ke ki fito da kuɗin tunda kema in kika faki ido ɗauke-ɗauken kikeyi shiyyasa gashi nan duk kin tsiyata min yaro. Lokacin da Habibu ke tare da Asiya arziƙi har zuba yake, amma ke da yake mai farar ƙafa ce bayan talauci da kika saka masa harda ciwo..”     Cikin matuƙar ɓacin rai Sailuba ta miƙe tana nuna Gwaggo. “K! Tsohuwar banza ya isheki, kodan kinga kwana biyu na ɗaga miki ƙafa ne a gidan nan shiyyasa kike tunanin dawo da tujarar taki. To bari kiji Sailu na nan da kika sani ban canja ba. Kuɗinki ɗin banza da zanje na ɗauka, kuɗin ma da wani ne ya bayar ba guminki ba, sai dai idan ɗan naki ne ya ɗauka ko shi Baban tunda shima ɗan hauma-haumar ne ai”.         Kafin kace mi rigima ta kacame tsakanin Gwaggo da surukarta Sailu. Hakan ba sabon abu bane a gidan, dan sau karo biyu Sailu na lakaɗawa Gwaggo duka. Ƴaƴanta kuwa idan kaji zagin ƙare dangi da sukema Gwaggo bazaka taɓa yarda kakarsu data haifi ubansu bace ba. Sosai sashen ya cika da matan gidan, maƙota ma na leƙe ta katanga. Abin zai baka mamaki yanda kowa Sailu kawai yake bawa haƙuri, duk da kuwa zagin da take surfama Gwaggo a gaban kowa. Kuka Gwaggon ta sanya yuuu-yuuu tana rantsuwar yau sai Habibu ya saki Sailu a gidan, idan ba haka ba sai ta tsine masa.         Sailu dake ɗura mata zagi ta ce, “A hayye nanaye koba saki ba. To maza sakashi ya sake nin kiga idan zai iya. Ko an gaya miki ni Asiya ce kukarki mai daɗin hawa. Iyayenta sun muku bauta sun gina ɗanki kunci amanar zuminci, to wlhy Talle ni nafi ƙarfinki, ke wanda ma ya fiki nafi ƙarfinsa. Tsohuwar banza da bata iya komai ba sai sa ido, ɗanki na kwanciyar aure dani kina leƙenmu ta taga saboda ke kwartuwa ce....”       Ai gaba ɗaya gida ya ɗauki salati da sallalami, yayinda Gwaggo ta fashe da kuka tana rantsuwa sharri Sailu take mata. Amma ina kowa yaƙi saurarenta sai aibantata akeyi akan wannan al'amari, saboda kowa dai ya tabbatar Gwaggo zatayi abinda yafi hakan. Ana cikin hakan wani matashi ya shigo, agaba ɗaya shekarunsa basu wuce goma sha ba. Amma abin tausayi da mamaki a kallo ɗaya zaka gane shaye-shaye ya gama kassara rayuwarsa. Ga raunuka a jikinsa na tabbacin wuƙace da sauransu. Sule kenan, da ake kira da AUTAN MASHAYA a garin na giro. Wasu kuma suke ƘARAMINSU BABBANSU. Dan kuwa Sule hatsabibin yaro ne na gaske, baya ji ƙwarai da gaske, ga sata ko ɓera albarka, dan duk iya tattalinka da kayanka idan Autan mashaya ya ƙyalla ido a kansu sun zama ba naka ba. Baya tsoron kowa a garin baya shakkar kowa. Idan ma ka cika takura masa koda da kallo ne kaɗan daga aikinsa ya maka zanen yarbawa a fuska koya tsiyayar maka da idanun. A ƙarancin shekarun nan nasa ƙaramin dila ne na kayan shaye-shaye anan cikin ƙauyen har ma da ƙauyukan kusa da su, babban tashin hankalin da ƴan garin suke ciki yanzu yanda yake koyama yaransu ƙanana masu tasowa shaye-shaye, a yanzu haka bawai ya gama kaiwa cikakkun shekarun balaga bane, amma yasan yanda zai tarfa mata a lungu ya mammatse koda kuwa matan aure ne, kai koda tsoffi ne. Dan ita kanta Gwaggon ya taɓa matseta a cikin ɗaki wataran taita ihu tana neman taimako, kafin wani ya shigo ya ware ta taga, daya faɗa uwarsa ta ƙaryata.      “Wai lafiya naga an tarar mana a part ɗinmu ne?, kufa wannan zuri'ar na fahimci kun fara zama ƴan tsugudidi”.       Sule ne ke maganar cikin yanayinsa na ƴan daba........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [02/05, 6:15 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣4️⃣ ______________ .......Cikin ƙanƙanin lokaci taron ya fara watsewa, dan tsoronsa kowa keji kamar mutuwa, tsabar makirci sai lokacin Sailu ta ɗaura hannu aka ta ƙwallara kuka. Cikin wani irin zaro idanu Sule ya ce, “Kai! Ikon wahabu, k! Tsohuwa ince dai lafiya kike irin wannan tsuwwar haka. Shin ko dai Baba ya wulla ne na fara shirya bikin fatin cin gado?”.        Kukan Sailu ta sake fashewa da shi, sai kuma ta nuna Gwaggo da tun shigowar Sule tai lakur na tsoro. “Ba kakarku bace tace wai ka shiga ɗakinta ka saci kuɗi, shine ta tara mutanen gida tanata zagina, harda cewa sai ka shiga wuta kai da Haƙila da ni, wai mun zame mata jaraba babanku ya talauce sanda Asiya na tare da shi kuɗi har zuba suke a ƙasa..”       “Kan uban can kai.. ke tsohuwar nan ko, to wai ma tsaya Babanmu, da take faɗar haka ita ma ai wutar zataje, bakiga fuskarta ba tafi kama data ƴan wuta. K! Wlhy Talle idan baki daina sanya mana ido a gidan nan ba sai na miki sabuwar kaciya da gatarina, shegiya mai suffar kwaɗi. Kuɗi kuma na ɗauka zan ƙara jari ne, idan kin isa ki ƙara magana ALLAH kinji na rantse ko sai na juya fuskarki daga gaba ta koma baya. Dalla shige daga ciki zanyi lissafi....”        Ai da gudu Gwaggo ta afka ɗaki ta danno ƙofa, jikinta sai rawa yake kar-kar harda ɗan fitsarinta a cikin zani. A waje ko tuni sule yaja tabarma ya baje kayansa dake cikin jakar daya ratayo. Ba komai bane sai ƙwayoyi da ganyen tabar wiwi. Ko'a jikin Sailu ta koma ta zauna ta cigaba da tankaɗenta tana kallonsa. Idan ma taga wata tabar tafi wata da yake ƙullawa sai ta ce, “Waccan kamar tafi sauran yawa ɗan baba. Kodai wani ɗan ludayina ƙarami zan baka yanda zaka dinga gane gwajin?”.       “Eh to kema kinzo da shawara kawo, idan naga kuɗin ya fita ribar da ɗan auki zan baki ƙulli ɗaya ki busa”.     Dariya Sailu tai tana miƙewa. “A'a ɗan baba rabani da busawar nan. Wannan ai sai ku ƴan zamani, mukam tafi ƙarfin mu”.      Dariya ya ƙyalƙyale da ita da faɗin, “Babanmu kefa dama tuni na fahimci kanki ƙarami ne, tun randa na baki zoɓon nan nawa da zaƙami a ciki kika baje kikaita barci har kwana uku nace tabb Babanmu fa ta bazu da yawa”.      Nan ma dariyar takeyi daga ɗaki. A haka ta fiddo masa da ɗan ludayi na cikin madarar jarirai ta miƙa masa. Ya ce, “Yauwa uwa maba da mama, kinga ko gashi ɗan kif-kif abinsa. Zako kici burodi anjima da shayi da ƙwan wajen kalla”.      Daɗi sosai Sailu taji, ta shiga sanya masa albarka. Duk abin nan da akeyi fa Babu na gidan, a kwance yake baida isasshen lafiya, dan ranar ma daga gona sai ɗakkosa akayi. Hawaye ne suka shiga gangaro masa, rayuwarsa da Ammie da ƴan ƴaƴansu uku ta faɗo masa a rai....... Hummmm, kowa ya tuba dan wuya ba lada😮‍💨😮‍💨🥱 ____________★          Alarm ɗin daya saita musu domin tashi sallar asuba ne ya farkar da su. Cikin kasala irin na mai barci ya buɗe idanunsa da sukai masa nauyi sosai. Fin minti biyu kafin ya yinƙura ya tashi zaune bakinsa na ambaton sunan ALLAH. Hannu ya kai ya kunna lamp dake a bed side drawer. Hasken ya bashi damar sauke idanunsa akan fuskar Maanal dake facing inda yake. Samun kansa yay da zuba mata idanun, fin mintuna biyu kafin ya matsa sosai, kishingiɗa yay akan hannunsa daya tokare kansa da shi yana facing ɗinta sosai fuskokinsu dab-da-dab dan sai da ya janye filon wajen. Yatsarsa ya kai saman tsukakkun lips ɗinta ya shiga zagayawa, yaja fin minti ɗaya yanayi kafin ta fara motsawa kaɗan-kaɗan, sai kuma idannunta suka fara rawa, da ƙyar ta shiga ɗagasu sama a hankali tana buɗewa. Da farko shaaa take iya ganinsa, sai kuma sannu a hankali idon ya washe ta ganshi da ƙyau. Cike da wani irin kasala da shauƙi ta zuba masa idanun nata da suka sake shanyewa saboda sanyi, shima dai kallon nata yake da nasa dake a raunane kamar wanda yasha kafso yay marisa. Wani irin kallo sukema juna mai kassara garkuwar jiki dana ɓargo, mai saukar da kasala da tsitstsinka jini. Illahirin gaɓoɓin jikinsu na sakewa a lokaci guda.         Cikin wani irin motsa lips kaɗan ya furta, “Amarya mai rowa”.      Sosai taji ƙirjinta ya buga sakamakon yin maganar tasa, babu shiri ta waro idanun gaba ɗaya domin tabbatarwa bafa a wancan yanayin bane, domin kuwa mafarkinsa take yi a like yanda yake a kusa da itan nan sai kuma gashi ɗin reality. Yanda ta waro idanun shima sai ya ɗage mata gira ɗaya sama yana mata irin kallon (Miye kike kallona ba haka bane?) ɗin nan. Hakan da yay ya sake tabbatar mata reality ɗin ne fa ba a mafarkin ba, ai da sauri tai yunƙurin juyawa zuciyarta na dumm-dumm.         Hannunsa ya ɗaura akan jikinta ya taro fuskar tata ya hanata juyawa, jitai gaba ɗaya tama gama daburcewa, ga wani yanayi na saukar mata a cikin jiki. Wannan yanayin ta jima tana fuskartarsa a tare da ita musamman lokacin gabatowar asubahi har zuwa safiya. Wani lokacin takanji kamar tayi kuka saboda yanda take shiga matsuwa da son kasancewa kusa da abokin halittarta. Tsaf AA yake wani binta da kallo daki-daki, dan ya fahimci halin da take a ciki itama sarai a idanunta. Samun kansa yay da ɗan murmusawa kaɗan, sai kuma ya sake matsar da fuskar tasa gab da tata suna busama juna numfashi. Rawa jikin Maanal ya nema farawa, hakan ya bashi damar janye filon dake ta wajen cikinsu ya matsota jikinsa kawai ya rungumeta, bai wani jira maida ba'asi ba ko bata dama ya manne lips ɗinsu waje guda. Da wani kalar sanyi jiki da na yanayin asuba yake sumbatarta, yanyinda itama yanayin da take a ciki ya sata shagaltuwa ta fara ƙoƙarin miƙa masa wuya. Sai kawai yaji ya ƙara rikicewa...      Tafiya tayi tafiya ya fara ƙoƙarin kai hari wani sashin daban, a lokacin ne ta nema dawowa a hanyyacinta, sai dai duk yanda taso janye jikinta hakan ya gagara. Kanta ta shiga girgiza masa tana ƙoƙarin ture masa hannu, sai ga hawaye sharrr-sharrr na sauka har a fuskarsa. Jikinta kuwa rawa yake na tsoro, dan brain ɗinta ƙoƙarin dawo mata da wani abu daya shuɗe a shekarun baya take yi. Sosai yanzu ta fara kicin-kici, a wannan yanayin ta buge masa ƙasan ciki da gwiwar ƙafarta batare da ta fargaba itama, dan da gaske AA tunaninsa yayi nisa da duniyar da take ciki.         Babu shiri kuwa ya saketa, saboda wata azaba data ratsa masa jiki har zuwa tsakkiyar ƙwaƙwalwa. Jikinsa ya dunƙule a waje ɗaya ya riƙe cikin da duka hannaye biyu ya rumtse ido da matuƙar karfi. Dan tabbas badan ya kasance jarumin gaske ba babu abinda zai hana ya fasa ihu. Amma ina jikinsa ne kawai ke ɗanyi kamar yana rawa... Maanal kam data samu ta kuɓuta tsoro ne ya sakata direwa a gadon, cikin sauri ta wuce bayi. Tana maida ƙofar ta rufe ta jingina a jiki jikinta na karkarwar tsoro hawaye na bin fuskarta. Ji take kamar zai biyota, dan bata taɓa ganin AA a irin wannan mugun yanayin ba, tru-tru fa ya fita a yaccinsa ƙoƙarin isa inda zuciyarsa ke raya masa kawai yake yi. Ina bata shirya hakan ba, wlhy bata shirya ba, da gaske tsoro take ji, matuƙar tsoro. Duk yanda jikinta ke nuna mata buƙatuwa da irin wannan yanayin ko'a film in tana kallo taga kiss ya fara wuce na hankali sai kaga jikinta ya fara rawa tsoro ya kamata, dan wancan abun daya faru a waccan ranar ne yake dinga dawo mata, wani lokacin sai take jin ma kamar zata suma dan tsoro. Shiyyasa bata iya sakin jiki ta kalla film ɗin turawa musamman na soyayya. Gara na faɗa yafi bata kwanciyar hankali. Kai ko'a karance-larance novels ɗinta bata taɓa karanta irin wannan wajejen. Idan kuma ta fahimci book yayi shaiɗanci da yawa gara ta haƙura dan English novels ba komai zaka samu ana ɓoye ba...         Ita kanta bata san adadin lokacin data ɗauka a wajen ba, dan ƙafafunta har sun fara sagewa. Sauran guntun hawayenta ta share, kafin cikin ƙarfin hali ta ƙarasa shigewa bayin. Dole cikin gilashin da ake wanka ta shiga, ta sakarma kanta ruwa kawai batare data iya cire kayan barcin ba. Ratsatan da ruwan keyi yasa ta fara sakin ajiyar zuciya a jajjere, wani irin tausayin duk yarinyar da akama fyaɗe na sake raunana mata zuciya, dan wanda ya fuskanci ƙalubalen kawai yasan mi ake ji koda gwada yimasa akai ba'ayi ba kuwa. Ta jima ruwan na dukanta, sai da taji nutsuwa matuƙa sannan tai wanka sosai ta kuma tsarkake jikinta dan dole tai hakan, bathrobe ta ɗauka ta sanya, ta ɗaure igiyar da ƙyau, taji daɗin yanda ya saukar mata ƙasa sosai. Sai kuma taja towel ta naɗe kanta sannan ta fito a ɗakin cikin ɗari-ɗarin zuciya.       Sai da ta ɗan kalla cikin ɗakin taga babu alamar shi sannan ta fito gaba ɗaya, tayi ta wajen gado kaɗan dan ɗaukar kaya ta koma bayin ta sanya a mamakinta sai ta gansa duƙunƙune a yanda ya barsa, gashi babu alamar ma yana motsi. Gabata ne ya faɗi, cikin tsoro-tsoro ta shiga matsawa da sanɗa, har tazo jikin gadon bai motsa ba, ta ɗan duƙo ta leƙa fuskarsa, idanunsa a kulle suke, kuma sai taga kamar baya numfashi da gaske. Kamar mai tsoron taɓa wani mugun abu haka takai yatsarta saitin hancinsa a slowly. Tai ɗan jimm tana saurare, sai taji da gaske fa baya numfashi sam.       “Na shiga uku ni Maanal”. Ta faɗa a gigice tana hayewa a gadon. Tsabar yanda jikinta ke rawa bama tasan ta kamo kansa ta ɗaura a cinyarta ba, ta riƙe fuskar da tafukan hannayenta biyu tana girgiza shi da kiran sunansa.      “AA! Besty! AA! Ajwaad! Ajwaad!! Na shiga uku ni Maanal Ajwaad please ka tashi, miya faru? Ajwaad dan ALLAH ka taimakeni ka tashi”.      Ina, AA baima san tanayi ba. Wani irin kuka ta saki ta kife kanta tanayi akan tashi fuskar.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [02/05, 6:15 pm] Leematu: *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣5️⃣ ______________ .........Hawayenta da damshin ruwan jikinta na wanka suka shiga sauka masa akan fuska. A hankali cikin ikon ALLAH ya shiga motsawa, sai kuma numfashinsa ya fisga alamar farfaɗowa. A yanda ya fisgi nunfashin ne ya sakata ɗagowa da sauri. Ga hawaye na cigaba da tarara akan fuskarta. Idanunsa ya ɗaga da ƙyar ya kalleta, ya zuba mata su kamar mai son ganeta, sai dai kuma kukan nata ne ke wani kalar tsinka masa zuciya, tausayinta yake ji matuƙa.        “Dan ALLAH kayi haƙuri”.    Ta faɗa hawaye na sake ɓalle mata. Duk da azabar da yake ji a nashi jikin dan kawai ta kwantar da hankalinta sai ya saki mata wani sassanyan murmushi yana ɗan lumshe idanunsa da sake buɗewa a lokaci guda. Cike da dauriya da jarumta ya motsa lips ɗinsa a hakali. “Taimaka min na tashi”.     Kanta ta shiga jinjina masa tana share hawayen dake cigaba da gangaro mata. Duk da ya mata matuƙar nauyi da ƙyar ta iya kamashin ya haɗa da nasa ƙarfin halin ya tashi zaune. Yasan bazai iya zama a wannan halin ba, sannan kuma bazai iya cigaba da kwanciya baiyi salla ba, dan tabbas AA mutum ne mai kiyaye ibadarsa, duk runtsu bai yarda yin wasa da lokacin salla ba. Sannan ita kanta baya son cigaba da ɗaga mata hankali. Wannan wani irin yanayi ne daya ɗauka tsahon shekaru a cikinsa, haka kuma zakaga ya gama jigatarsa batare da kowa ya sani ba har ALLAH yasa ya samu sauƙi ya miƙe. Har gara ma sau biyu Fawzan ya taɓa riskarsa a halin, yayta masa faɗa tare da bashi taimako, daga nan ya sake kasancewa a takatsantsan ɗin kiyayewar hana kowa sanin a halin da yake ciki, kawai yayi imanin komai yana da lokacinsa, kowa kuma da irin jarabawarsa.. Duk da bawani iya riƙesan da ƙyau Maanal tai ba saboda ya mata nauyi haka ta lallaɓa sukaje har zuwa bayi ko miƙewa da ƙyau bai iyayi. Suna isa ƙofa ya dafe bango yace taje tai sallarta zai iya. Hawaye ta sake sharewa, ta juya kanta a ƙasa. Binta yay da kallo, sai kuma ƙasa-ƙasa ya furta, “Kina da alwala ko?”.       Tsayawa tai cak, sai kuma ta jinjina masa kanta batare da ta juyo ba. Dan hawaye ne ke ta gudu sosai a fiskarta, saboda sarai ta fahimci minene matsalarsa. Ita kuma harga ALLAH tana jin tsoro, matuƙar tsoro ta yanda bata san ya zata iya miƙa wuya domin taimaka masa ba. Dan tasan hakan ne kawai samun lafiyarsa yanda ya kamata. Har ta kimtsa tai sallar asuba bai fito ba, tashi tai taje ƙofar bayin, tai shiru tana tunanin yanda zatayi, sai kuma ta kai hannu da niyyar ƙwanƙwasawa dai-dai nan ƙofar ta zuge ya bayyana. Baya ta ɗan ja kaɗan, ta sauke kanta ƙasa ganin daga shi sai towel, sai wani ƙarami dake a hannunsa. Sosai ya zuba mata idanunsa, sai kuma ya janye a hankali ya ƙarasa fitowa a ɗan duƙe dan bai iya miƙewa da ƙyau. Da ƙyar ya iya kaiwa cikin sofa yana cigaba da naɗe ruwan kansa batare daya sake kallonta ba ya ce, “Bani dogon riga”.       Da sauri ta nufi akwatinsu, dan anan taga jallabiyu har biyu daya sanyo, ta ɗakko ta saman kawai ta iso inda yake. Amsa yay ya sanya kafin ya kunce towel ɗin a zaunen sannan ya miƙe. Kamar dai a yanda ya zauna a haka ya lallaɓa kan sallayar datai salla yayi shima. Tana zaune a bakin gado tana kallonsa cike da damuwa, hawaye kam har yanzu lokaci-lokaci sharesu takeyi. Yana idarwa baima iya yayi ko azkar ba ya lallaɓa ya dawo saman gadon ya kwanta, a waje guda ya dunƙule kamar ɗazun, kafin a hankali ya kalla Maanal dake kallonsa. Murya a shaƙe ya ce, “Zoki kwanta mana”.      Kanta ta girgiza masa. Sai ya lumshe idanu ya sake buɗewa. Muryarsa na sake komawa can ciki ya ce, “Miyasa?”.       Tata muryar na rawa ta ce, “Ban jin barci”.      “Zoki tayani to”. Yay maganar da ƙyar yanzu kam. Kallonsa tayi, ganin haka ya sashi basarwa. Itama sai a hankalin takai kwance nesa da shi, sai dai suna facing juna sannan yanzu ba kai da ƙafa ta kwanta ba. Idanu kuwa suka zubama juna, tsahon lokaci kafin sannu a hankali nasa su lumshe, itama tun tana kallonsa har barcin ta kwasheta. Batayi wani barcin kirki ba ta farka, dan mafarki tai AA ɗin a cikin mummunan yanayi. A zabure kuwa ta tashi, sai idannunta suka sauka a kansa. Yanda ya sake dunƙule jikinsa waje guda ya sake tabbatar mata da mafarkinta. Jikinta har rawa yake ta matsa kusa da shi, tana kai hannu kansa taji wani irin masifaffen zafin da har sai da ta rumtse idannunta da ƙarfi.. gaba ɗaya sai taji tama rikice, ita ko ina zata kama a ƙasar mutane, gashi bata san inda sauran abokan tafiyarsu suke ba. Dabarar kiran wayar hotel ɗin ce tazo mata, duk da bata jin yarensu sai tai tunanin yin turanci. Haka kuwa akayi, ta sanar musu tana buƙatar wani a ɗakin da suke ta faɗi number ɗakin, bata jira amsa ba ta yanke wayar saboda yanda taga AA na yamutsa fuska da sake dunƙule jikinsa. ALLAH ko ya taimaketa sai gashi anzo anyi knocking ƙofar, babu shiri ta miƙe tana gyara veil ɗinta taje ta buɗe. Ma'aikacinsu ne namiji, bayan sun gaisa ta sanar masa mijinta ne baida lafiya ko suna da doctor dazai duba shi?. Da sauri ya ƙarasa shigowa ɗakin ganin yanda take magana a ruɗe, yana ganin a yanayin da AA ɗin yake ciki bai wani sake tambayarta ba'asi ba ya zaro waya a jikinsa yay kira. A mamakinta ko minti biyar ba'a cika ba wasu suka shigo sanye da kayan asibiti da ɗan abun ɗaukar mara lafiya. Gaba ɗaya suka ɗaga AA zuwa kan abun, shi kuma ma'aikacin yace ta ɗakko jacket ta taho dan akwai sanyi yauvkaɗan gashi safiya ce. Tashi ta jiya kawai ta yayuma ta biyo su, a tare suka shiga elevator, minti ɗaya da sakanni ta kawosu ƙasa harabar hotel ɗin, amamakinta ambulance ma na jiransu. Ciki aka saka AA itama akace ta shiga, sai ma'aikatan asibitin. Shi kuma ma'aikacin hotel ɗin da driver na gaba. Cikin sharara gudu na masifa suka iso wani ƙaton gini, da yarensu akai rubutu dan haka Maanal bata fahimci komai ba, amma dai ta tabbatar asibiti ne dan ga ambulance nan da yawa tako ina. Bata da lokacin tunani dan fitowa sukai aka shiga da AA ciki. Sai faman share hawaye take, ma'aikacin hotel ɗin nan na lallashinta da turancinsa mai fita da harshen Chaines.       Sunyi zama yakai na mintuna talatin kafin cikin ma'aikatan asibitin wani ya fito. Da Chaines yayma ma'aikacin hotel ɗin magana, sai shi kuma ya juya yana kallon Maanal da turanci yace ga matarsa nan. Kallon Maanal ma'aikacin yayi, shima da turancin ya bata takardar hannunsa yace tai signing. Bata san mi aka rubuta ba tunda Chaines ne a jiki, dan haka tai tambayar ta miye? Dan bata iya yaren ba. Su duka biyun sun fahimci tasan abinda take yi, dan haka ma'aikacin hotel ɗin ya amsa ya ciro wayarsa yayma takardar hoto, miƙa mata wayar yayi ya nuna mata inda zatai translate ya koma mata da duk yaren da take so. Godiya tai masa tayi duk yanda ya nuna mata, sai ko gashi ya koma mata da turanci. Sai da ta kammala karantawa ta fahimci komai sannan ta amsa pen tai signing ɗin ma'aikacin ya koma ciki. Bayan kamar mintina ashirin ya sake fitowa yace zata iya shiga wajensa.      Wata nannauyan ajiyar zuciya ta sauke tare da masa godiya. Ma'aikacin hotel ɗin yace mata zai koma bakin aikinsa shima. Idan suna buƙatarsa tai magana ga ma'aikatan asibitin zasu kira hotel ɗinsu zai zo. Godiya tai masa sosai shima sannan ta nufi ciki shi kuma ya juya ya tafi..... ___________★       Siyayya ce sosai yayo ta azumi, sai dai samun gidan shiru ya fahimtar da shi matar gidan barci take yi. Bai tasheta ba dan yasan wahalar data sha a hannunsa daren jiya. Sai kawai ya shigar da komai kitchen ya juya ya fita, dan yana son zuwa ya amso nama da kifi na gidansu da ya sayama iyayensa na azumi kamar yanda yay musu siyayya da kuma nasu na nan gidan. Kusan awa ɗaya da rabi ya sake ɗauka sannan ya dawo. Mamaki ya kamashi ganin har yanzu bata tashin ba kuwa. Ledojin hannunsa ya kai kitchen, sai kuma ya nufi ɗakin barcinsu. Barcin kuwa take a ƙasan tils, yay ɗin jim yana kallonta, kafin ya matsa ya ɗan taɓata yana kiran sunanta.       “Huznah! K Huznah!!”.    Motsawa tai, tare da buɗe ido sai kuma tai miƙa tana kallonsa. Zaram ta miƙe kamar wadda ta tsorata da ganinsa, sarai ya fahimceta amma sai ya fuske. Cike da kulawa yace, “Wannan wane irin barci ne? Da alama ma ko girki baki yi ba ko?”.       Fuska ta ɗan yamutsa sai kuma ta jinjina kai alamar eh.   “Okay, ki tashi kiyi salla ga nama can na kawo da kayayyaki ki adana su. Ni naje massallaci zan taho mana da abinda zamuci”.     Bai jira amsarta ba ya fice. Da kallo ta bisa, sai kuma hawaye sharrr suka shiga rige-rigen sakko mata. Wlhy bata son mutumin nan, ko kallon fuskarsa bata sanyi. Tasan in har AA na wannan duniyar bazata taɓa son kowa ba. Ita kaɗai tasan a irin ƙuncin zuciyar da take kwana, ga Sageer ya maidata kamar jaka. Sam baya raga mata, safe da dare wani lokacin har da rana idan ya dawo gidan sai ya nemeta. In ma ta masa gardama ya murɗeta yay abinda zai yi ya ƙara gaba. Ya kwace mata waya ta rasa ta ina zataji Umminta, ta ina zataji labarin AA a bakin Sille. Ji take kamar ta kashe Sageer ta hutama ranta. Sanin halinsa na tasan inya dawo baiga ta yi abinda yace ba yasa ta miƙe. Sam bata jin daɗi, kwanciyar ƙasan tils ɗin nan ce kawai ke mata daɗi, kuma babu inda ke mata ciwo a jikinta. Wanka ta farayi tai salla. Sannan ta nufi kitchen ɗin, ta jima tana kallon kayan daya jibge mata kafin ta fara ɗaukewa cikin ɓacin rai zuwa store ɗinsu. Sannan tazo ta buɗe ledar naman. Rasama yaya zatai da shi tayi, dan aikin nan dai ba sabawa tai da yi ba a gida sai masu aiki, a yanzu ma sakata gaban da Sageer ɗin yayi ne aka ɗan samu canji. Ledan kifin itama ta buɗe, ai kamar jira ƙarnin na bugar hancinta ta wani rikice, a guje ta buɗe ƙofar baya ta fita ta fara sharara amai a ciki filawoyin wajen. Sageer dake shigowa ciki kakarin aman nata ya sashi nufo bayan cike da mamaki. Shi sai ma ya tsaya kawai yana kallonta. Sai da ta gama tai lagab a ƙasa sannan ya ƙaraso wajen, da yake akwai rijiya ata bayan ruwa ya jawo ya zuba a boket dake ajiye ya kawo mata yana mata sannu. Kanta ta jinjina masa ta ɗauka ruwan ta wanke bakinta da fiskarta, ta zuba akan filawoyin data ɓata sannan ta miƙe da ƙyar. Taimaka mata yay suka shiga, suna shiga kitchen ɗin tasa hannu ta toshe hancinta. Kitchen ɗin yabi da kallo, sai kuma baice komai ba ya shige da ita cikin falo. A kujera ta zaunar da ita, sai dai bata iya zama ba ta zamo ƙasa ta kwanta. Muryarta har rawa yake tace, “Bana son ƙarnin kifin can, dan ALLAH ka fita da shi”.      Sosai yake kallonta da mamaki, dan shi dai yasan a zuwanta gidan nan yasha sayo kifi ya kawo suci har ɗanye suyi abinci balle yace bata ci tun fil azal. “Yau kuma kifin ne zaki ce baƙya so Huznah?”.      Hawaye ya cika mata ido ta ce, “Wlhy bana so, dan ALLAH ka taimakeni ka fita da shi. In ba haka ba zan sake yin amai”.      Shike nan ba damuwa zan fita da shi tashi kici abinci”. Yay maganar yana ajiye mata ledar takeaway daya yi musu. Shi kuma ya nufi kitchen ɗin ya shiga gyara kifin da naman dan a tunaninsa sabon iskanci ne dan kar ta gyara, tunda sarai yasan halinta dan ma baya mata da wasa ne. Tsaf ya gyara komai ya zuba su a freezer ɗinsu sannan ya koma falon shima.......✍️      Hajiya Huznaty😂🤣🤣bara dai nayi shiru. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*