🌼 🌹 🌹 🌼 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 BA NI DA GATA*🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌼. 🌼 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 *ᴘᴀɪᴅ ʙᴏᴏᴋ* *STORY & WRITTEN BY* *ZULFA'U SA'EED IBRAHIM* ( *_MATAR SAYYADEE_*) ☀️ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION*☀️ ( *Home of quality and trusted writer's of the nation*)💪🏻 *𝐃𝐄𝐃𝐈𝐂𝐀𝐓𝐄𝐃 𝐓𝐎 𝐓𝐇𝐄 𝐌𝐎𝐒𝐓 𝐁𝐄𝐀𝐔𝐓𝐈𝐅𝐔𝐋 𝐖𝐎𝐌𝐀𝐍 𝐈𝐍 𝐓𝐇𝐄 𝐖𝐇𝐎𝐋𝐄 𝐖𝐎𝐑𝐋𝐃 (𝐌𝐘 𝐌𝐎𝐓𝐇𝐄𝐑)*. *𝐀𝐋𝐋𝐀𝐇 𝐘𝐀 𝐉𝐈𝐊'𝐀𝐍 𝐊𝐈 𝐃𝐀 ℝ𝔸ℍ𝔸𝕄𝔸* *___________________* *𝔽ℝ𝔼𝔼 ℙ𝔸𝔾𝔼 1&2* *___________________* ...........Garin ya yi luf-luf cike da ni'ima. Ga wani 'dan sanyi-sanyi da ke busowa gami da k'amshin k'asa sakamakon hadarin da ya ha'du sosai, ko wani irin lokaci ruwa zai iya tsugewa. Gefe guda kusa da wani tarin bola da ta yi tsini, wata kyakkyawar yarinya ce da bazata wuce ten years ba du'ke a wajan sai rawar d'ari ta ke yi sakamakon wannan hadari da ya taho da iska da kuma sanyin da ke biyo iskan. Gashi ba wani kayan arziki ba ne a jikin wannan yarinya da ko 'dan kwali babu a kanta sai uban tulun gashin da ya zubo har kafa'dunta. 'Yar 'karamar shimi (vest) ne a jikin ta, sai wani kod'ad'd'an wando da ya yayyage ta wajan d'uwawunta da kuma guiwar wandon. Shi kan shi wandon iya k'aurin ta ya tsaya. Ha'koranta har ha'duwa su ke da juna saboda tsabar sanyin da ta ke ji, gashi kuma da ma da d'an zazzab'i a jikin ta. Ruwa ne ya kece kamar da bakin kwarya. Cikin abunda bai fi minti 'daya ba wannan yarinya ta ji'ke sharkaf. Da gudu ta mi'ke ta yi bayan wannan tulin bolan da ke cikin wani rusassan kangon da kad'an ya ke jira ya gama zubewa sakamakon wannan uban bola da ake zubawa a wajan. Inda baiwar Allahn nan ta koma bai hana ruwa dukanta ba, domin babu wajan da za ta gujewa ruwan a wajan. Haka nan ta cigaba da tsugunno a wajan kusan kimanin awa biyu kamin ruwan nan ya tsagaita. A wannan lokacin kuwa har kakkafewa take yi saboda tsabar sanyi. Gashi magriba ta gabato. Ta na nan kwance a wajan ta soma jin takun tafiyan mutane ga dukkan alamu masallaci za su je. 'Dan le'ko da kanta ta yi ta wani 'dan huji ta na kallon mutanen da suke wucewa ta na addu'ar Allah ya sa ta ga Hamdan. Addu'an ta ya kar'bu, sai dai kash! tare su ke da ankul ( uncle) Saban (Sauban) kamar yadda ta ji Hamdan 'din na kiran shi. Ajiyar zuciya ta yi tare da komawa ta lafe a wajan kasancewar ta riga da ta ha'kura da abincin yau. Wasu siraran hawaye ne su ka Shiga zirarowa daga idanunta. Bayan hannunta ta saka ta share tare da fa'din, "Allah ni ba ka bani mama da baba ba kamar kowa. Ni bola ce ta haife ni. Kuma bola ba ta ba ni abinci mai kyau, ba ta kai ni makaranta, ba ta saya min kaya masu kyau, kuma bata wanke min jiki na. Mutane ba sa sona. To meyasa ni ma ban zama bola ba kamar yar da mama na ta ke? Mutane haka suke kira na 'yar bola, kuma wai *BA NI DA GATA*, Allah ni ma ka mayar da ni bola kamar yadda mamata take ni ma nai ta girma kamar ta. Kowa ba ya sona, Hadaan (Hamdan) ne kawai ke so na. Shike sammin abinci daga gidan su. Shi ya kawo min wannan kayan ma da ke jiki na. Allah ni ma ka mayar da ni bola kamar mama saboda mutane su dai na gudu na". Ta fa'di hakane ta na kuka, domin a nata wautan bolan da ke wajan ita ta haifeta, ita ce uwarta, ita ce ubanta. Saboda kuma jama'a na kiran ta *Y'AR BOLA* sai ta ke 'dauka ai bolan ce mahaifiyar ta. Ita kullum burinta, ta zama bola don ta yi magana da mahaifiyar ta suma su koma gidan su. Har an idar da sallah, kasancewar had'a sallah aka yi, tunda kowa ya shige gida sai garin yai tsit. Gashi dama ruwan ba d'aukewa ya yi gaba d'aya ba. Har yanzu ana yayyafi kuma alamar ruwan sake tsugewa zai yi. Don irin ruwan nan ne da ake kwana ana tsugashi. Tun ta na ri'ke ciki ta na kukan yunwa, har bacci yai gaba da ita anan wajan sauro na zu'kan jinin ta. Can cikin baccin ta taji ana dukan k'afafunta a hankali tare da kiran sunan ta, wanda Hamdan ne ya ra'da mata sunan wato binty (beauty). Beautyn ne ba ta iya kira ba ta ke cewa binty. A da idan wani ya tambaye ta miye sunanta, cewa ta ke yi *Y'AR BOLA* kamar yadda ta ji mutane su na fa'di. Idan aka ce mata *Y'AR BOLA* ba su na ba ne. Sai ta ce Binty (beauty) a hankali ku ma sunan na ta ya koma Binty, wasu kuma su ce Binty *Y'AR BOLA*. A hankali ta ke bu'de idanuwanta har ta bu'de shi tas a kansa. Duk da akwai duhu ta shaida shi, domin karfe tara ta wuce na dare. Hannu ta kai ta shafi fuskan shi tare da fa'din, "Hadaan (Hamdan), ina ta jiran ka yunwa na ke ji. Na gan ka za ka sallah kai da ankul Saban, har na cire rai zaka kawo min abinci". "Beauty ni ma hankalina na kan ki, ina ta so na fito, amma Mummy ta ki barin sitting room balle in samu in fito in kawo miki food ki ci, now wash your hands with this detergent and water before eaten, it's a very good hygiene. Understand?". Fa'din wani kyakkyawan farin yaro da ba zai wuce 13years ba. Ita dai Binty (Beauty) ba ta san mai ya ke cewa ba, 'ko'karin ta kawai ta 'karbi take awayn dake hannun sa. Shikuma yak'i ba ta wannan damar. "Hey! Easy mana beauty. Zan ba ki, amma firstly sai kin fara wanke hannun ki saboda gudun cuta. Our teacher always tells us to wash our hands before and after every meal. Saboda haka, ga ruwa da detergent nan, ki wanke hannun ki sai in baki Irish and plantain 'din ki ci". Ya fa'di hakane tare da jawo hannun ta ya zazzaga mata detergent 'din tare da ruwa. Sai da ya sata ta wanke hannun sau bakwai, ka na ya mi'ka mata takeaway 'din tare da fork na roba. Cikin sauri ta kar'ba ta soma cikin. Shida-shida ta ke ta ha'dawa har ta cinye tas. Ka na ta yar da cokalin tare da saka hannu ta su'de robar tas, sannan ta yar tare da sakin k'atuwar gyasa ta koma ta kwanta a nan 'kasan wajan ta na mayar da numfashi. "Imaging! How can a human being live and survive here, Allah na gode maka da ni'imar da kai min". Hamdan ya fa'di hakan ya na mai 'karewa beauty kallo cike da tausayi da har bacci ya soma 'daukar. "She's very beautiful with long hair. Who must be her parent? Why is she all alone in this garbage? Da ni babba ne da na ne mo mata iyayan ta ita ma ta rayu da su kamar ni da Mummy da Appa". Hamdan ya sake fad'i ya na shafa dogon gashin da ke kanta da ya yi dak'an-dak'an har cukurku'dewa ya yi ya na so ya koma dada. Ganin da yai ta yi bacci sosai, sai ya fiddo bedsheet a cikin ledan da ya zo da shi ya rufa mata tare da kunna mata maganin sauro da lighter, duk da yasan babu abunda maganin zai kare mata, don ko kamfanin *SUPER KILL* aka saka a wajan ba zai hana sauro cizon ta ba. Don sauran zamanin yanzu, ka na jan bargo suna ja.🤣🤣 Kamar zai yi hawaye ya mi'ke tare da barin wajan ya lallab'a ya tura get ya shiga gidan da san'da har ya shige 'dakin sa tare da hawa gado ka na ya saki ajiyar zuciya tare da fa'din, "Thank God, nobody saw me". *𝕎𝔸𝕊ℍ𝔸 𝔾𝔸ℝ𝕀* Sai da rana ta fito sannan Binty ta farka tare da sakin mi'ka gami da doguwar hamma. Gashin da ya barbazo ya rufe mata fuska ta mayar da shi baya tare da janye zanin gadon da Hamdan ya lullub'eta da shi ka na ta mi'ke tsaye. Idanuwan ta ne ya sauka akan pure wata guda uku da brush da maclean a kan wani bulo. Wajan ta nufa domin ta san Hamdan ne ya aje mata su a wajan, domin ya ce a kullum ta tashi da safe ta ri'ka alwala tare da wanke bakin ta da brush, don har koya mata yadda ake brush 'din sai da ya yi. Brush 'din ta fara yi ka na ta yi alwala ko in ce shirme. Domin ko alwalar ba ta iya ba, balle a kai ga zancan sallah. Bayan ta gama alwalar da brush 'din, ta zo ta hau kan wannan zanin gadon ta soma sallah haka nan ko 'dan kwali babu a kan ta sai buyagin gashin ta. Dunguran-dunguran banza tai ta yi. Domin sallar daga sujada aka fara, sannan aka d'ago a kai ruku'u ka na aka k'ara tafiya sujada. Haka tai ta dungurawa har ta kammala kusan raka'a goma. Fitowa tai tare da hawa kan bolan nan tare da fa'din, "To mama, zan tafi in nai mi abincin da zan 'karya da shi tunda dai bakya sona. Na san Hadaan ya tafi makaranta, ankul Saban ba zai barshi ya kawo min abinci ba. Zan je na nai mo da kai na". Ta na gama fa'din haka ta soma saukowa daga can saman bolan. Kallon gyefan daman ta ta yi, idanuwan ta suka sauka akan wani tsoho tukuf, gashin sa fari fat har kafa'da, hannun shi ri'ke da sandar da ya ke dogarawa, ya na mata murmushi. Cikin sauri da wani irin zumu'di ta 'karisa wajan shi tare da fa'dawa jikin sa ta ruk'unk'ume shi tare da fa'din, "Kaka!" Sai kuma ta fashe da kuka tare da 'kara rungume shi. Shafa kanta wannan tsohon ya yi yana murmushi tare da fa'din, "Haba Bintyn Hadaan! Mi ye na kukan? Ba ga ni na dawo ba". "Guduwa zakayi ka sake bari na a nan, babu wanda ke sona. Yara su na tsokana ta, ba na samun abinci, Hadaan ya je makaranta. Yanzu ma ban karya ba". Fa'din Binty. "Ki yi ha'kuri Binty, ko mai ya yi tsanani ya na tare da sau'ki. Wannan waje da ki ke, shine kad'ai mafita a gare ki. Yanzu duk bayanin da zan miki, ba za ki ta'ba ganewa ba don kwakwalwar ki ba za ta 'dauka ba. Amma ki yi hak'uri. Ina mai tabbatar miki maki'yan ki sai sun rusuna a gaban ki. Sai kin zama filita mai haskakawa. Ki yi hak'uri ki daure ki ci jarabawar ki. Tun da har Allah ya raya ki a cikin bola tun ki na 'kan'kanuwar ki har izuwa yanzu, to lallai Allah ya na so ya nunawa magauta ishara da Isar sa ne. Lallai ubangiji shine ke rayawa da kashewa". Sam Binty ba ta fahimci ko kalma 'daya daga cikin maganganun kakan na ta ba. Sai ma jefa masa tambaya da ta yi. "Kaka yaushe zan zama bola irin mamana kowa ya dai na tsana ta?". Murmushi wannan tsoho ya yi tare da fa'din "Binty na, ba za ki zama bola ba, sai dai in sha Allah za ki zama abun kwatance a cikin al'umma, tabbas sai ma'kiyan ki sun duk'a a gaban ki. Tabbas idan rana ta fito tafin hannu ba zai ta'ba iya kare ta ba Binty na". "To kaka yaushe ne ranar zata fito? Kuma yaushe ne zan zama abun kwatance?". Binty ta kuma jefa masa tambaya. "Ranar na nan zuwa Binty na. Ki je Allah ya albarkaci rayuwar ki. So na ke ki yi gwagwarmaya, ta yadda nan gaba ko mai zai zo miki da sau'ki". Fa'din Kaka. "To kaka, bari na je na yi bara na samu abinci yunwa na ke ji". "To Binty na, Allah ya sa a da ce". Ya na gama fa'din haka Binty ta bar jikin shi tare da gangarowa daga kan bolan. Sai da ta sauko gaba 'daya ta 'daga kanta sama, wayam ta ga ni a wajan. Ko alamar kaka ba ta gani ba. Murmushi ta yi tare da fa'din, "Kaka ya 'kara guduwa ya bar ni". *ASSALAMU ALAIKUM READERS, GA NI NA ZO MA KU DA SABON LITTAFI NA MAI SUNA A SAMA, WANDA YA ZO DA ZAFI-ZAFIN SA, KUMA NA TABBATA ZA KU JI DAD'IN SA. BA ZAN CI KA KU DA SURUTU BA, KAWAI KU BI NI A FREE PAGES, KU DA KAN KU ZA KU GA NE BOOK D'IN NA DABAN NE. KAWAI KU NU NA MIN ONE LOVE WAJAN SIYAN BOOK D'IN AKAN FARASHI AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA:* *Normal group shine mutum zai bi ya 500 idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300.* *VIP kuma 1000 ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700.* *MUTANAN NIGER KUMA ZA SU BI YA KAMAR HAKA*: *Normal group shine mutum zai bi ya 500F idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300F.* *VIP kuma 1000F ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700F.* *ʜᴀʙɪʙᴀᴛɪᴇꜱ ᴅᴀɴ ɢɪʀᴍᴀɴ ᴀʟʟᴀʜ ᴋᴜ ɴᴜ ɴᴀ ᴍɪɴ ʟᴏᴠᴇ ᴡᴀᴊᴀɴ ꜱʜᴀʀɪɴɢ* 🌼 🌹 🌹 🌼 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹*BA NI DA GATA*🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌼. 🌼 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 *ᴘᴀɪᴅ ʙᴏᴏᴋ* *STORY & WRITTEN BY* *ZULFA'U SA'EED IBRAHIM* ( *_MATAR SAYYADEE_*) ☀️ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION*☀️💪 ( *Home of quality and trusted writer's of the nation*)💪🏻 *DEDICATED TO THE MOST BEAUTIFUL WOMAN IN THE WHOLE WORLD (MY MOTHER). ALLAH YA JIK'AN KI DA ℝ𝔸ℍ𝔸𝕄𝔸* *________________* *FREE PAGE 3&4* *________________* .............Juyawa ta yi ta soma tafiya ta na 'dan tsalle-tsalle gashin kanta na sama na 'kasa. Wasu 'dandazon almajirai ta gani sun yi layi suna karb'an sadaka. K'arasa ta yi ita ma tai layin. Sun rage saura su hu'du, abun sadakar ya k'are. B'ata fuska ta yi ta na kallon sauran ukun da su ma ba su samu sadakar ba. D'aya daga cikin su mai dogon goshi ya kwad'a mata d'an chinan hannun sa tare da fa'din, "Shegiya y'ar bola mai bak'in jini. Ke ce kika sa ba mu samu sadaka ba. Bar nan ko in zane ki". Yaron ya fa'da tare da yo wa kan ta kamar zai mazge ta. Da sauri Binty ta ja baya tare da barin wajan. Idan da sabo Binty ta saba da hantarar mutane. Wajan wani mai shayi ta 'karisa tare da rakub'ewa ta na kallon jama'ar da ke wajan su na shan shayi. Wani 'dan tsamurarran gaye ne ya kai shayi bakinsa idanuwan sa suka sauka akan Binty dak'an-dak'an ta na had'iyar yawu. Aiko ya fesar da shayin bakinsa tare da fa'din, "D'an Liti wannan wani irin iskanci ne za ka ri'ka bari irin wad'annan yaran suna tsayawa gaban mutane idan su na cin abinci. Wannan ai iskanci ne. Yanzu haka ji na ke kamar na amayar da hanjin ciki na wallahi". D'an Litin ne ya zagayo tare da kama kunnan Binty ya murd'a da k'arfi tare da fad'in, "Dan iyayan ki mata ba na hanaki zuwa wajan nan ba. Shegiya yarinyar kawai mai d'an banzan nacin tsiya. Ni anya ma yarinyar nan ba aljana ba ce? Shegiyar yarinya tun ta na da shekara uku ta ke rayuwa ita kad'ai a saman bola kuma ta rayu har izuwa yanzu. Ni wallahi tsoro ma ta ke ba ni yarinyar. Sai shegen kyau kamar ita tai kanta". "Kai kuwa d'an Liti ai Allah shi ke rayawa kuma shi ke kashewa. Ba abun mamaki ba ne dan ta rayu ita kad'ai a saman bola. Kai dai idan zaka taimaketa ka ba ta buredi da shayi ka ba ta, ba ka tsaya kana wani surutan banza a wajan ba". Fa'din wani mutum da ke cin taliyar 'yan yara (Indomie). "To bazan ba da ba. Idan kuma kai ka basheni jalin, sai ka d'iba ka bata". Fa'din D'an Liti. "Yo to ai abunda za ka ce kenan. Ke yarinya zo ungo wannan sauran taliyar ki cinye duk da dai kad'an ya rage". Fa'din mutumin nan. "Idan wanga d'iya ta ci taliyar nan a cikin robata Allah gwada maka yai. Sai dai ka juye mata a cikin leda". Fa'din d'an Liti. "Haka ka ce d'an Liti?". Fa'din bawan Allah nan. "Awo wallah". D'an Liti ya fa'da ya na buga cinya irin na y'an daudu. Girgiza kai bawan Allah ya yi tare da d'aukar ledar da aka b'are indomie ya juye mata a ciki tare da mik'a mata. Da uban sauri Binty ta karb'i ledan. Nan wajan a tsaye tai loma biyu ta cinye tass tare da zubawa wannan bawan Allah idanu alamar nai man k'ari. Da gudu 'dan Liti ya biyo ta tare da fa'din, "Bar nan ko in halako ki walleh". Gudu ta yi sosai, duk da D'an Liti ya dai na bin ta ba ta zai na gudu ba. Sai da ta ga ta yi nisa sosai sannan ta tsaya ta na mai da numfashi. Haka tai ta gararanba a cikin anguwanni. Duk in da ta je kyamatar ta ake yi. Musamman wajan ma su sai da abinci. Idan Allah ya ba ta sa'a wani ya ci ya rage tai wuf da shi ta cinye. Idan kuma aka kamata ta sha kirb'a. Haka tai ta yawo ga rana kuma ba takalmi da d'ankwali a kan ta. Hatta kayan da ke jikin ta ma ba na kirki ba ne. Sai da rana ta fa'di ka na Binty ta dawo wajan bolan nan ta zauna ta na sauke numfashi. Bakin ta duk ya bushe. Sosai ta ke jin k'ishirwan ruwa. Kallon himilin bolan nan ta yi tare da fad'in, "Mama yau ban samu abinci sosai ba. Yunwa na ke ji. Ina jin k'ishi sosai". Daga bayan ta taji an saka hannu an rufe mata idanu. Wani farin ciki ne ya lullub'e ta tare da fad'in, "Hadaan, kai ne ko? Nasan kai ne. Ai kai kad'ai ne kawai ke zuwa waje na". Zagayowa yai ta tare da fad'in, "Yau ma kin je yawo ko? Ai tun d'azu na ke ta nai man ki, na kawo miki abinci ki ci ban gan ki ba na bawa kare ya cinye". Kwal-kwal ta yi da idanu tare da fad'in, "Hadaan yunwa na ke ji, dan Allah ka ba ni abinci, yau na yi bara ban sa mu ba. Ina jin k'ishi sosai zan mutu". Sosai tausayin ta ya kamashi, ji ya ke dama zai iya convincing mummy ta yadda Beauty ta dawo gidan su da zama. Amma ya san ko mutuwa zai yi hakan ba zai faru ba. Juyawa ya yi tare da d'auko wani d'an basket da ya zo da shi sai ya boye a bayan wani bulo tare da ajewa a tsakiyar ta. Cikin sauri ta soma kiciniyar bu'de abunda ke cikin basket 'din. Rik'e hannun ta ya yi tare da girgiza kan sa ya na fad'in, "You've already know the rules. Wash your hands before eating". A cikin maganganun sa, kalmar wash kawai ta rik'e, shiyasa da ya yi dogon turancin sa idan ta ji the word `wash` ta san mai ya ke nufi. Wato ta wanke hannun ta. Mi'ka masa hannuwan ta yi alamar ya zuba mata abunda ya saba zuba matan idan zata wanke hannunta. Zazzaga mata detergent ya yi tare da ruwa sannan ta soma mitstsike hannun. Sai da ta wanke sau goma. Har ta k'osa ka na ya fiddo plate tare da bu'de kula ya zuba mata lafiyayyan fried rice da ya ji kayan lambu ga mi da hanta. Aikuwa ko kallon cokalin da ya ke mik'a mata ba tai ba ta zunduma hannu ta soma ci. Kasancewar shi ko da cokali za ta ci abinci ba ruwan shi sai ta wanke hannun ta. Cikin abunda bai fi mintuna uku ba har ta lamushe ta na kuma buk'atar k'ari. Sauran na cikin kulan ya juye mata tare da cinyar kaza da baya. Aikuwa ta cinye tas har da tauna k'ashi murus ta kuma d'ad'd'ake goran ruwan faro ta saki gyatsa tare da jingina da bangon kangon ta na mayar da numfashi. Shikuwa Hamdam tun ya na jin mamakin irin cin abincin da Binty ke yi har ya dai na. Don shi ko kashe shi za'ayi ba zai iya cin ko kwata ba. Wani wawan mari yaji an sauke masa a kan fuskan sa wanda k'arar marin ya saka Binty firgita daga baccin da ya soma d'aukar ta. Don ita haka take da cikin ta ya d'auka za ta soma gyangyad'i. "D'an uban baban ka ba na hanaka zuwa wajan nan ba? D'an iskan yaro ya na so ya jawo mana fitina. Wani d'an iskan ne ka ga ya na zuwa inda ta ke idan ba kai ba. To yau sai na ci uban ka, kuma wallahi dole ba bi su kulsum ku wuce Abuja. Bazan iya da iskancin ka ba. Ke kuma idan ma wani abun ki ka wa d'ana aniyar ki ta bi ki, ba bu abunda zan miki balle anjima da daddare a turo min bak'ak'en aljanu su ga baya na. D'ana kuma daga yau ba za ki k'ara ganin sa ba. Shegiya". Hajiya Saratu mahaifiyar Hamdan ke fad'in haka tare da jan hannunsa, 'dayan hannun ta kuma na kan hancin ta. Uncle Sauban da ke can gyefe tsaye sai aikawa Binty da harara ya ke yi. Shi kuwa Hamdan sai ihu ya ke ya na fad'in shi bazai koma abuja ba. Daga nan wajan bolan mota aka jefa Hamdan 'din, dama already an saka kayan sa cikin mota. Binty fitowa tai da gudu ta na kallon abunda ke faruwa ta na kuka. Ta na hango Hamdan daga cikin mota ya na dukan glass ya na kallon ta ya na hawaye. Da gudu ta shiga bin motar ta na kuka ta na 'daga masa hannu, shi ma kuma ya na kallonta ta glass 'din baya yana mata waving. Ba ta dai na bin motar da gudu ba sai da motar ya b'ace mata da gani. Haka ta dawo cikin kangon bolan nan ta na kuka sosai. *ᗩᗷᑌᒍᗩ* Wata kyakkyawar yarinya ce da ba za ta wuce ten years ba, sanye da wando pencil sai wata riga mai matu'kar kyau iya guiwarta. Gashinta tai parking d'in shi a tsakiyar kan ta wanda ya kasance jajaja, maroon-maroon. Kyakkyawa ce sosai kuma fara ce. Fuskan nan na ta ya ci make-up kamar wata babbar budurwa. Hannun ta kuwa tasha zanan lalli. Kallon wata kyakkyar mace ta yi da ke zaune akan 1sitter ta na yanke farcenta. Kallon ta yi ta re da fa'din, "First love ya ki na ganin?". Wacce ta kira da first love 'din ko kallon ta ba ta yi ba, a yadda kanta ke k'asa ta ce, "Looking good!". Sautin kuka yarinyar ta ji ya kara'de d'akin. Cikin sauri matar ta d'ago ta kalle ta tare da fad'in, "Sabrin mai ya same ki?". Sosai Sabrin ke kuka tare da fad'in, "Mom ko kallo na fa ba ki yi ba balle ki ce na yi kyau kuma na fi kowacce mace kyau a duniyar nan. Sai cewa kawai ki ka yi Wai looking good". Baki bu'de Hajiya Sakna ke kallon autar tata tare da fad'in, "Me ke damun ki ne Sabrin? Ta yaya zan miki k'arya in ce kin fi kowace mace kyau a duniya. Ke ma kin san k'arya ki ke yi. Ki na da kyau Sabrin sosai, amma ba ki fi kowa kyau ba. Akwai wanda su ka fiki sosai". "No way! Everyone in school said that I'm the Queen of the country. We have wealth, Education, beauty and rest. And I am also the Queen of our school. Duk makarantar mu ba bu Wanda ya kai ni kyau, duk ajin mu na fi kowa k'ok'ari. Daddy na ya fi daddyn kowa kud'i a makarantar. Ba na son kowa ya fi ni, ina so in ga na iya komai ta yadda babu kamar ni in the whole world". "Sabrin, whole word?". Mom ta fa'da cike da tashin hankali da mamaki. Domin kuwa sosai halin Sabrin ke ba ta tsoro. Ta na da wani irn kishi da ya wuce misali. Ita burinta ta kasance ta fi kowa, babu Wanda zai fita. Idan kuwa ko cikin k'awayanta ta ga wa ta ta fi ta da wani abu, to fa zaman lafiya da kwanciyar hankali ya k'are har sai ta fi wannan da ta fita za ta sa mu natsuwa. Sosai Sabrin ke da mugun hali. Hatta mom d'in ta kishi ta ke da ita. Ko wani abu daddyn ta ya siyawa mom in dai ya fi abubda aka sai mata to babu zaman lafiya sai ita ma an sayo mata. Kuma daddyn ta ya d'aure mata gindi wanda hakan na matu'kar k'ona ran mom don ta tabbata idan Sabrin ta ta shi da wannan halin zata sha wuya a rayuwa don gidan wani zata. "Of course mom. Babu wanda zai fi ni a cikin duniyar na. Ko mai nawa ne ni kad'ai. Nagode miki da kika haife ni mai kyau.". Mom ta kasa cewa komai, don har ga Allah sosai lamarin Sabrin ke ba ta tsoro. Juyawa Sabrin 'din ta yi tare da fad'in bari na je side d'in aunty, nasan ita za ta min maganar da zan ji da'di. Ta fi ki sona". Ta na gama fad'in haka tai side 'din kishiyar mahaifiyar ta da ke k'ara dulmiyar da ita. *ASSALAMU ALAIKUM READERS, GA NI NA ZO MA KU DA SABON LITTAFI NA MAI SUNA A SAMA, WANDA YA ZO DA ZAFI-ZAFIN SA, KUMA NA TABBATA ZA KU JI DAD'IN SA. BA ZAN CI KA KU DA SURUTU BA, KAWAI KU BI NI A FREE PAGES, KU DA KAN KU ZA KU GA NE BOOK D'IN NA DABAN NE. KAWAI KU NU NA MIN ONE LOVE WAJAN SIYAN BOOK D'IN AKAN FARASHI AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA:* *Normal group shine mutum zai bi ya 500 idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300.* *VIP kuma 1000 ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700.* *MUTANAN NIGER KUMA ZA SU BI YA KAMAR HAKA*: *Normal group shine mutum zai bi ya 500F idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300F.* *VIP kuma 1000F ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700F.* *ʜᴀʙɪʙᴀᴛɪᴇꜱ ᴅᴀɴ ɢɪʀᴍᴀɴ ᴀʟʟᴀʜ ᴋᴜ ɴᴜ ɴᴀ ᴍɪɴ ʟᴏᴠᴇ ᴡᴀᴊᴀɴ ꜱʜᴀʀɪɴɢ* 🌼 🌹 🌹 🌼 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *BA NI DA GATA*🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌼. 🌼 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 *ᴘᴀɪᴅ ʙᴏᴏᴋ* *NARRATED & WRITTEN BY* *ZULFA'U SA'EED IBRAHIM* ( *_MATAR SAYYADEE_*) ☀️ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION*☀️💪 ( *Home of quality and trusted writer's of the nation*)💪🏻 *DEDICATED TO THE MOST BEAUTIFUL WOMAN IN THE WHOLE WORLD (MY MOTHER). ALLAH YA JIK'AN KI DA ℝ𝔸ℍ𝔸𝕄𝔸* *________________* *FREE PAGE 5&6* *________________* .............."Ohhh my gosh! Queen kin ganki kuwa? Looking more and more beautiful dear. Wa ne Barbie. Ai ko ita ta gan ki sai 'kishi ya kama ta. Daughter zan fa ci kud'i a nan. Gaskiya wanda za ki aura sai ya kasance classic guy ne. Irin kyakkyawan nan, mai kud'i na nunawa sa'a. Amma fa duk kyan shi ba zai kai ki had'uwa ba domin daga ke aka rufe babin kyawawan mata". Fa'din aunty Junaina, kishiya a wajan mahaifiyar Sabrin. Da ita da Alhaji Saifullahi su ne musabbabin k'ara tab'arb'arewar Sabrin d'in. Domin duk abunda ta yi nuna mata suke ta na kan gaskiya. Rungumeta Sabrin ta yi tare da fad'in, "Ohh sweet aunty. That why I love you soon much. Dan Allah aunty kullum ki ri'ka fad'amin irin wannan maganar. Allah ji na ke kai na na k'ara girma". "Do you know what dear? I'm not saying all this to impress you, I'm saying the fact. You're soo adorable my Queen". Wani irin duk'awa Sabrin ta yi tare da kamo hannun aunty Junainan irin yadda akewa princess ko Queen idan ana son rawa da su. Ta ce, "I love you soo much my aunty. Me kike so in yi miki?". "Abu d'aya kawai na ke so ki yi min. Kawai ki yi ta kyau ki na k'ara kyau a cikin kyau". Fad'in aunty Junaina. "Ohhh ba ki da wannan matsalar. Yau na ji gidan shuru, ina sauran y'an matan gidan su ke?". Sosai dariya ya kusa kufcewa aunty Junainan. Wai y'an mata. Duk sa'o'in ta ne y'an shekaru goma. Aunty Junaina na da 'yan mata guda biyu Wanda su ka kasance 'yan biyu kuma lokaci guda aka haife su da Sabrin, sai dai ta girme su da sati biyu. Wannan dalilin ne ya sa ta ke d'aga masu kai. A cewar ta, ta fisu kyau da komai ma. Kamar yadda ta ke auta, suma autan ne a wajan aunty Junaina. "Sun je wanke kai kin san gobe Monday". Fa'din aunty Junaina. Ta'be ba ki ta yi tare da fa'din, "Ni ba ko wa ni beauty saloon na ke zuwa ba. Sai after zuhur prayer zan sa driver ya kai ni. Don ba ni son rana". Yadda Sabrin ta ke wasu manyancan, wallahi za ka d'auka wata k'atuwar budurwa ce. *BINTY* Gaba 'daya duniyar ji ta ke tai mata zafi. Ko kyankyaso ta ga ni ya wuce, sai ta ce dama Allah ya mai da ni kyankyaso in huta. Ranar da daddare ko nai man abinci ba tai ba. Ita ce har sha biyu idanunta biyu ta kasa bacci. Wasu samari ne guda biyu a bige su ka zo wucewa ta wannan bolar da ko da kud'i aka had'a ka bazaka zauna a wajan da rana ba balle da daddare. Haskata su kai da torch light. D'ayan da bai bugu sosai ba ya ta'ba d'an uwansa tare da fa'din, "Babaa! Ni fa wancan yarinyar da ke rayuwar bolan can zan rufar mata in rage yawa. Dan naga ehh, ba yawa ta na da garin jiki, zan yi maleji a hakan. Dan ka fa san ehhh, kwana biyu Safara yawa ta ke min don ban da kud'i. Kawai dan rannan na d'an yi ehhh, ban ba ta ko sisi ba shine ta dai na duba min. Kawai zan farwa yarinyar can in rage yawa. Ni wallahi babaa idan har tai min ma zan iya d'auke ta in raine ta tunda dai ba ta da ehhh, ina nufin iyaye". Ya na maganar ne irin yadda y'an daba su ke yi d'in nan. "Sata kawai babaa, zan jira ka a nan. Idan ka gama kai min fito ni ma inzo inyi ehhh, irin in samu nawa share d'in nan". "Ba ka da case ba ri na je". Ya na gama fad'in haka yai wajan kangon da Binty ta ke. Ita kuwa Binty ta kasa bacci, ta na nan zaune ta ha'da kai da guiwa ta na kuka. Sai ji muryan mutum a tsawace tai a kan ta ya ce, "Ke mik'e!". Sosai ta firgita tare da mik'ewa ta na raba idanuwa. Shikuwa d'an iskan sai lashe baki ya ke yi kamar yaga cikakkiyar budurwa. Hannu ya kai ya fincikota tare da matseta a jikinsa sosai. Ita kuma Binty duk ta gama rikicewa jikinta sai rawa ya ke yi. Wannan ce rana ta farko da wani namiji ya mata haka idan aka cire kaka. Matsar da ita gyefe ya yi tare zuge zip 'din wandon sa ya sauka a kan k'afafunsa. "Ke dan uban ki kama min nan. Matsa min maza ko in yanka wuyarki ki mutu, da safe sai dai aga gawarki". 'Dan iskan nan ya fad'a. Ita kuwa Binty ta k'i yin yadda ya ce sai gwalalo idanuwa ta ke yi a cikin duhu. Ji ya yi an cafke masa mazantakarsa da k'arfi kamar za'a cire. Wani irin ihu ya yi tare da fad'in, "Ke dan uwar uban ki ba da k'arfi ba a hankali za ki yi. Sa ke min abu na ko in ci uwarki ana wajan". Ya fad'a cike da wahala don har ya soma hawaye. Ita kuwa Binty da ke gaban shi a tsaye sai mamaki ya kama ta. Don ita dai ta san ba ta kama masa komai ba amma yake ta ihu wai ta sakar masa abunsa. Ko mi ye abun nasa oho". Wani gigitaccan mari yaji an sakar masa hagu da dama a fuskar sa wanda ya saka sai da ya yi k'undun bala akan bolan da ke zubowa k'asa. A matu'kar hargitse ya mik'e ya na waige-waige. Binty dai na nan tsaye ko motsawa ba ta yi ba. Tu ni tsoro ya dabaibaye shi, hankalin shi ya ta shi. Wani duka yaji an kai masa a k'eyarsa sai da ya yi taga taga zai fa'di. Saurin juyawa yai bai ga kowa ba. Can kuma sai ya soma jin k'arar kofato ya na yowa in da ya ke a tsaye. Ai bai san sadda ya cire wadon da ya ke hard'e shi a k'afa ba, ga shi ko boxer ba mu a jikinsa, yai wurgi da shi ya soma gudu ya na fad'in, "Marados ka gudu wallahi mun shigo sansanin aljanai. Wallahi maganar da mutane su ke fad'i akan yar bolan ce gaskiya ne. Tabbas aljana ce. Ka gudu ka ceci kan ka". Ya na fa'din haka ne ya na falla gudu gashi babu wando Allah ya so shi dare ne. Shi kuwa wanda a ka kira Marados da ya soma 'dan gyangyad'awa a firgice ya mik'e shi ma ya shiga gudu. Gaba d'ayan su kuma su na jin takun kofaton nan kamar ana tseran doki. Marados ne yaji an d'aga shi cak, aikuwa ya shiga sakin fitsari tare da fad'in "Wa innahu min sulaiman, wa'innahu bismillahi rahmanir rahim. Ku kuke ganin mu ba mu muke ganin ku ba. Bawan Allah aljani, dan rahamar ubangiji kai min rai. Wallahi ko ta layin nan idan na k'ara bi ka kashe ni. Dan girman Allah yallab'ai aljani". Shikuwa d'ayan da akai nasarar cafko shi, zawo ya yi ta saki kamar farar kura. Daga sama suka ji an ha'dasu waje d'aya ka na aka sake su timmm a k'asa. Sannan su ka ji wata murya abun tsoratarwa ya na fad'in, "Duk ranar da na sake ganin ku wajan bolan nan, kashe ku zan yi. Kuma ko ba binty ba, ku ka k'ara k'ok'arin yi wa wata yarinyar fyad'e to sai na kashe ku. Daga yau na fara bibiyar al'amuran ku kenan. Ku bar nan ko kuma in yanke mazantakar ku". Ai a sittin suka arce. Ba su suka tsaya ba sai da su ka isa rumfar fale falen da su ke kwana su na ta sakin ajiyar zuciya. *ᴡᴀꜱʜᴀ ɢᴀʀɪ* Binty haka ta ta shi sukuku. Gaba d'aya kewar Hadaan ta ke yi. Musamman da ba ta ga pure water da MacLean da brush d'in da ya saba ajiye mata ba. Hawaye ta ji su na sauko mata daga idanunta. "Kaka, ka na ina". Binty ta fa'da can cikin zuciyar ta. Mi'kewa ta yi ta haye can saman bolan. Bolan na da tsini sosai, domin bene ya yi, amma sam bai mata wuyan hawa. Sai da ta kai k'arshe ka na ta duk'a a kan gwiwowinta ta na hawaye ta re da fad'in, "Ni ma zan tafi wata duniyar daban ba nan ba. Babu abunda na ke samu a nan. Nan ba duniya ta ba ce. Wanda ya ke so na d'in ma ya tafi ya barni. Ni ma zan tafi. Ba zan sake dawowa ba. Idan kin ki kewa ta ki ne me ni a wata bolar na wani duniya da ban". Binty na kuka ta ke fad'in hakan. Mik'ewa ta yi tare da soma saukowa. Sai da ta sauko gaba d'aya ka na ta d'aga kanta ta kalli bolan ko za ta ga kaka, sai dai wayam babu kowa a wajan. Share hawayanta ta yi ta soma tafiya ta na waigen bolan. Tafiya ta yi mai tsayi har ta shigo wani unguwa. Unguwan tsit ya ke, irin unguwan nin masu kud'in nan. Zama ta yi a dandamalin wani tanfatsetsan gida tare da tsinko wasu furannin da aka shuka a k'ofar gidan ta na gutsirawa tare da jefawa a cikin kwata. Wata jibgegiyar mota ce tai parking dab da gidan. Wani jibgegen mutum ne a cikin motar. Tumbinsa har tab'a steering ya ke yi. Bak'i ne sosai har wani shinning ya ke yi. Akwai hak'orin maka golden colour a bakin sa. Wayar sa da ke ringing ya 'dauka a gefan sa tare da kara wayar a kunnensa. Ka min yai magana Wanda ya kira shin ya soma fad'in, "Sammani ka na wasa da k'ungiya wallahi. Saboda kai sabon shiga ne shi ya sa har su ke d'aga maka k'afa. Yau kimanin shekaru biyu ke nan ana fama da kai ka samo yarinya yar shekaru goma ka sadaukar da budurcinta da jininta wa dodon tsafi amma sai wasa da hankalin su ka ke. To ka bud'e kunnan ka ka ji da kyau. Saboda yadda mu ke da kai ne shi ya sa ma zan fad'a maka. Wallahi kwana uku aka ba ka idan baka kawo abunda aka buk'ace ka da shi ba, Durdus da kan shi zai aika Dobak'o ya d'auko masa matarka da babban d'anka a yanka su a kuma shanye jinin su a gaban ka kuma harda kai, idan kuma kak'i sha kai ma a sha jinin ka. Saboda haka ya rage gareka. Kuma ka da ka manta akwai meeting yau k'arfe biyu zuwa asuba, ka da ka sake kai fashi. Don Durdus na nan ya na k'irga fashin ka". Kamin sammani yai magana idanuwansa su ka sauka akan Binty da ke wasa da flower. Wani farin cikin ne ya lullub'eshi tare da fad'in, "Mai nasara yau zan kawo yarinyar nan ba sai jibi ba. Yanzu haka ma ga ta a gaba na". "Na ta ya ka murna. Kuma ka rufawa kan ka asiri". Fad'in Mai nasara tare da yanke waya. Shikuwa Alhaji Sammani bud'e murfin mota ya yi tare da fitowa ya nufi in da Binty ta ke a zaune. *𝘼𝙎𝙎𝘼𝙇𝘼𝙈𝙐 𝘼𝙇𝘼𝙄𝙆𝙐𝙈 𝙍𝙀𝘼𝘿𝙀𝙍S, 𝙂𝘼 𝙉𝙄 𝙉𝘼 𝙕𝙊 𝙈𝘼 𝙆𝙐 𝘿𝘼 𝙎𝘼𝘽𝙊𝙉 𝙇𝙄𝙏𝙏𝘼𝙁𝙄 𝙉𝘼 𝙈𝘼𝙄 𝙎𝙐𝙉𝘼 𝘼 *ASSALAMU ALAIKUM READERS, GA NI NA ZO MA KU DA SABON LITTAFI NA MAI SUNA A SAMA, WANDA YA ZO DA ZAFI-ZAFIN SA, KUMA NA TABBATA ZA KU JI DAD'IN SA. BA ZAN CI KA KU DA SURUTU BA, KAWAI KU BI NI A FREE PAGES, KU DA KAN KU ZA KU GA NE BOOK D'IN NA DABAN NE. KAWAI KU NU NA MIN ONE LOVE WAJAN SIYAN BOOK D'IN AKAN FARASHI AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA:* *Normal group shine mutum zai bi ya 500 idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300.* *VIP kuma 1000 ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700.* *MUTANAN NIGER KUMA ZA SU BI YA KAMAR HAKA*: *Normal group shine mutum zai bi ya 500F idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300F.* *VIP kuma 1000F ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700F.* 🌼 🌹 🌹 🌼 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 BA NI DA GATA*🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌼. 🌼 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 *ᴘᴀɪᴅ ʙᴏᴏᴋ* *NARRATED & WRITTEN BY* *ZULFA'U SA'EED IBRAHIM* ( *_MATAR SAYYADEE_*) ☀️ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION*☀️💪 ( *Home of quality and trusted writer's of the nation*)💪🏻 *DEDICATED TO THE MOST BEAUTIFUL WOMAN IN THE WHOLE WORLD (MY MOTHER). ALLAH YA JIK'AN KI DA ℝ𝔸ℍ𝔸𝕄𝔸* *________________* *FREE PAGE 7&8* *________________* ............"Yarinya ya sunan ki? Alhaji Sammani ya fad'a yayin da ya ke tsaye a gaban ta yana mata murmushi. D'agowa ta yi tare da zuba masa idanuwanta da suke kamar madara tare da fad'in, "Sunana Binty. Binty y'ar bola". Ta fad'a tare da cigaba da jefe flowers a cikin kwata. "Binty 'yar bola kuma? To ina iyayen ki su ke? Ina ne gidan ku?". Alhaji Sammani ya fad'a ta re da zama kusa da ita. "Ni ba mu da gida. A bola mu ke zama. Kuma mamana ce bolan, ita ta haife ni. A can na tashi". Wani farin ciki ya dabaibaye zuciyar Alhaji Sammani, domin ya ga ne d'aukar Binty ba zai masa wuya ba. "To yanzu me ki ke yi a nan wajen ke d'aya?". Alhaji Sammani ya sa ke jeho mata tambaya. "Ni ma ban sa ni ba, amma bazan sa ke ko ma wa bolan mu ba. Ban san wancan duniyar, kowa bai so na a can. Ina so in je duniyar da kowa zai so ni, kuma in rik'a samun abinci ina ci sau uku a rana. Ni ba dole sai na yi wanka ba. Amma ina son in canza wannan wandon na jiki na. Kalla duk ya yage. Ka san wa ya ba ni? Wallahi Hadaan ne ya kawo min, kuma maman shi ta d'auke min shi ta kai shi wani waje mai ni sa". Ta fad'i haka ne hawaye na zubowa daga idanunta. "Ayyaah kin ban tausayi. Amma ki kwantar da hankalin ki, zan kai ki in da za ki samu duk abunda ki ke so, za ki je duniyar da kowa zai k'aunace ki kin ji y'ar yarinya". Alhaji Sammani ya fad'a ta re da rik'o hannunta. "Dagaske? Har wajan Hadaan d'ina za ka kai ni?". Binty ta fad'a out of excited. "Sosai ma kuwa, muje ga motata can ki shiga mu tafi". Alhaji Sammani ya fad'a tare da kama hannunta su ka yi wajan mota. D'aga kan da Binty za ta yi ta hango Kaka a kan wani katanga ya na girgiza mata kai sannan kuma ya na maganar da ita kad'ai ke jin abunda ya ke fad'i. "Ka da ki bi shi Binty. Za ki halaka idan ki ka bi shi. Ki dawo ki koma ki zauna a in da ki ke. Shine alkhairi a gare ki. Za ki fad'a wani hannu daban da zaki sha wahalar rayuwa. Za ki kira k'addarar ki da kan ki Binty". Girgiza kai Binty ta yi ta re da fad'in, "Ni sai na bi shi, bayan wajan Hadaan zai kai ni. Ni ba ruwa na da kai, ai kai ma guduwa ka ke yi ka na bari na babu abunci". Binty ta fad'a ta na murgud'a baki. Kasancewar Alhaji Sammani ya d'an yi gaba kad'an shiyasa bai ji abunda Binty ke fad'i ba. "Binty kar ki bi sa". Kaka ya sa ke fad'i ya na girgiza kan shi. "Sai na je". Binty ta fa'da ta re da isa wajan motar. "Ke da wa ki ke magana Binty?" Alhaji Sammani ya fad'a ya na mai waiwaigawa don ganin da wa Binty ke magana. Ita kuwa Binty ba ta ba shi amsa ba ta shiga k'ok'arin shiga gaban motar da ya sha tinted, amma ta ka sa saboda ya mata tsayi. 'Dagata Alhaji Sammani ya yi ta re da d'aura ta a kan kujera shi kuma ya zagaya ya shiga mazaunin driver ta re da yin reverse ya ko ma ya hau highway zuwa garin Abuja babban birni, don a can ne su ke gudanar da tsafin su. A cikin wani katafaren hotel Alhaji Sammani ya yi parking tare da fita ya kulle Binty a ciki da ke ta bacci. Domin tunda aka haife ta bata tab'a irin wannan doguwar tafiya haka ba. In fact in her whole life ba ta tab'a shiga mota ba sai yau. Reception ya shiga tare da biyan kud'in d'aki na kwana d'aya kawai. Ka na ya karb'i key ta re da fitowa ya dawo cikin mota ya kunna ya yi reverse ya bar cikin hotel 'din. A wani katafaran saloon ya tsaya ta re da bubbuga Binty da ke bacci ta na mafarkin kaka na mata kashedi akan ta gudu ka da ta bi wannan mutumin da ta ke ta re da shi. Farkawa ta yi ta re da fa'din, "Ni sai na bi shi, bazan gudu ba kaka. Ka dai na tab'a ni. Shi ba mugu ba ne. Ya saya min kayan dad'i a hanya. Kuma wajan Hadaan d'ina zai kai ni". Idanuwa Alhaji Sammani ya zuba mata, Can kuma ya k'ara bugunta a hankali. Wannan karan gaba d'aya ta bu'de idanunta ta zuba masa ta re da fad'in, "Mun kawo in da za ka kai ni wajan Hadaan d'ina ne?" "A'a beauty ba mu kawo ba, nan mun zo in da za'a gyara ki ne ai miki wanka a gyara miki gashin ki, saboda in da zan kai ki ba su son k'azamin mutum, kuma ba za su yarda ki ga Hadaan d'in ki ba a haka". "Kai kai kai.. Hadaan ne ya fad'a maka yadda ya ke kiran suna na? Allah ni ban san wanka, amma tunda za ka kai ni wajan Hadaan zan yarda a min wankan". Binty ta fad'a cike da farin ciki a fuskan ta. "Yauwa to jira ni a cikin mota ina zuwa". Alhaji Sammani ya fad'a ta re da fita ya shiga cikin wannan dank'areran Saloon 'din. Mintuna goma su ka fito shi da wata kyakkyawan siririyar mata su na dariya ita da Alhaji Sammani. Wajan motar su ka yo, Alhaji Sammani ya bud'e ta re da sauko da Binty daga cikin mota ka na ya kalli wannan kyakkyawar matar da ta saki hanci da baki ta na kallon tsananin kyawun Binty. "Precious Lord in heaven! What a beautiful girl. Alhaji ina ka samo wannan kyakkyawar yarinya haka? Oh my God, dan Allah ka ba ni ita mana". "A'a ni ba za a ba ki ni ba, wajan Hadaan d'ina zai kai ni". Binty ta fad'a ta re da mak'e kafad'ar ta, ta kuma koma bayan alhaji Sammani ta b'uya. Kaka ta ga ni a bayan wannan kyakkyawar matar ya na girgiza ma ta kai ta re da fad'in, "Binty ki bi ta, idan ki ka bi ta ba za ki halaka ba. In har ki na son k'ara ganin Hadaan ki bi ta". Ita kad'ai ta ji maganar. Zaro idanuwa ta yi ta re da fad'in "Kaka nan ma sai da ka bi yo ni? Ni Allah ba zan bi ta ba. Wannan zan bi ya kai ni wajan Hadaan d'ina". Gaba d'aya daga alhaji Sammani har wannan matar kallon Binty su ka yi ci ke da mamaki ta re da kuma waigawa don su ga dawa ta ke magana, amma wayam su ka ga ni sai mutanan da su ke wuce wa d'aya-d'aya su na shiga Saloon d'in. "Binty dawa kike magana?" Alhaji Sammani ya fad'a ya na kallon ta at the same time kuma ya na kallon gefe da kuma bayan shi. Kasancewar gaba d'ayan su kallonta su ke yi. "Kaka ma na, sai cewa ya ke yi wai ka da na bi ka, na bi wannan". Ta fad'i maganar ne ta na nu na wannan matar. "Tun a in da ka d'auko ni ya ke ce wa wai ka da na bi ka. Yanzu kuma ya ce na bi wannan". Zaro idanuwa Alhaji sammani ya yi jikinsa har ya soma b'ari. "Ka da dai a ce aljana na 'dauko. Na shiga uku ni sammani". Ya fad'a cikin zuciyar sa. Can kuma wani zuciyar ta ce masa, kai Sammani kawai ka kai ta, idan ya so ko aljanar ce su su ka san yadda za su yi da ita. Kai dai ba ka kai ta ka fita ba. "Ke Mss Raliya kwantar da hankalin ki, haka ta ke. Ta na da 'dan matsala a kwakwalwarta ne kad'an. Wani lokacin haka ta ke behaving". Fad'in Alhaji Sammani da turanci ta re da murmushi ya na shafa kan Binty. Ajiyar zuciya Raliya ta saki ta re da fad'in, "Allah sarki, I pity her. Allah ya ba ta lafiya. Muje ko beauty". Ta fad'i hakanne ta re da kama hannun Binty su kai gaba. Ita kuwa Binty dad'i ne ya kashe ta kasancewar ta ji su na kiran ta da sunan da Hadaan ya ke kiran ta da shi. Ciki su ka shiga, shi kuma Alhaji Sammani ya zauna a cikin mota ya na jiran su. Binty baki da hanci ta saki ta na kallon cikin katafaran Saloon d'in nan. Wani 'katon d'aki su ka shiga mai wahalar fasaltawa saboda tsaruwarsa. "Zauna a nan ki jira ni". Raliya ta nuna mata wani kujera ta re da yin gaba ta shiga wani 'dan corridor da ke 'dauke da bathroom a ciki. Bayan minti biyar ta fito ta re da kiran Bintyn. Bintin ta tashi ta re da bin bayan ta. Cikin bathroom d'in su ka shiga. Raliya ta riga da ta had'a ruwan wanka da sai fitar da k'amshi ya ke. Ga sabon sponge nan da kuma toothpaste da brush a gefe. Cire mata kayan jikin ta ta yi tare da saka ta ta shiga cikin wani baf na wanka mai circle. Kai ta fara wanke mata wanda sai a wankewa na goma ya soma kumfa, don da sai wani irin coffee brown 'din datti ke fita da wani irin yauk'i yauk'i abun kyamma da k'azanta. A tak'aice dai sai da Raliya ta wanke kan nan sau goma sha bakwai ka na ya fita k'al k'al gashi bak'ik'k'irin da shi mai cika da tsayi har tsakiyar bayanta. "Subhanallah! Masha Allah!". Raliya ta fad'i domin tun da ta ke aikin saloon ba ta tab'a ganin yarinyar k'arama mai irin wannan uban gashin ba. Wai a hakan ma don ba'a ja shi da hand drayer ba. Wanka kuwa sai da farin sosan nan ya koma ruwan k'asa saboda dattin da ke fita daga jikin Binty. Sai da Raliya ta ga ta yi k'al jikin ta na sulb'i ka na ta na'dota cikin towel su ka dawo wani d'akin mai k'aton madubi gaba da baya. Ga kaya gyaran kai da su attachment nan kala-kala da su relaxer da sauran su a ciki. Wani man shafawa Raliya ta d'auko mai k'amshi ta shafe jikin Binty da shi ka na ta d'aurata akan wani dogon kujera. Wani irin juyowa Binty ta yi ta kalli Raliya ta re da fad'in, "Ni ce wannan a cikin wannan abun? A she ina da kyau. Kalli gashi na ya canza kala. Mai ki ka min na koma haka?". Binty ta fad'a kasancewar ta na da shegen surutu. Kuma duk lokacin Allah ya sa ta ga fuskan ta cikin madubin mota ko kuma irin shagunan nan ma su slide, dak'an-dak'an ta ke ganin ta, kuma wancan lokacin gashin ya rine da kalar k'asa da kuma bola a jiki. "Ke ce mana. Ai ke kyakkyawa ce. Ga ki da dimple da gashi mai kyau". Fad'in Raliya. "Da ki ka min wanka sai naji jikina ya min iska da dad'i. Wai ke ya sunan ki". Binty ta fad'a ta na k'ara kallon kan ta cikin madubi. "Sunana Raliya, amma ke ki kira ni da aunty Raliya kin ji?". Aunty Raliya ta fa'da ta na warware gashin kan Bintyn da ya zuba har bayan ta. Hand drayer ta kunna ta kai shi saitin kan Bintyn za ta fara busar mata da shi. Wani irin ihu Binty ta kwala ta re da wurgi da towel d'in jikin tai ta yi hanyar wa je da gudu. Da kyar Raliya ta ka mo ta. Amma fir tak'i tsayawa a busar da gashin nan, don bak'aramin tsoransa ta ke ji ba. Sai da Raliya ta ga dagaske fa Binty ba za ta tsaya ba sannan ta kashe hand drayan ta re da fita ta kirawo wasu mata guda uku su ka ri'ke mata Bintyn ta na ihu ka na aka jaa gashin nan da yai wani irn masifar tsawo da kyau sai kyalli ya ke yi. *ASSALAMU ALAIKUM READERS, GA NI NA ZO MA KU DA SABON LITTAFI NA MAI SUNA A SAMA, WANDA YA ZO DA ZAFI-ZAFIN SA, KUMA NA TABBATA ZA KU JI DAD'IN SA. BA ZAN CI KA KU DA SURUTU BA, KAWAI KU BI NI A FREE PAGES, KU DA KAN KU ZA KU GA NE BOOK D'IN NA DABAN NE. KAWAI KU NU NA MIN ONE LOVE WAJAN SIYAN BOOK D'IN AKAN FARASHI AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA:* *Normal group shine mutum zai bi ya 500 idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300.* *VIP kuma 1000 ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700.* *MUTANAN NIGER KUMA ZA SU BI YA KAMAR HAKA*: *Normal group shine mutum zai bi ya 500F idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300F.* *VIP kuma 1000F ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700F.* *ʜᴀʙɪʙᴀᴛɪᴇꜱ ᴅᴀɴ ɢɪʀᴍᴀɴ ᴀʟʟᴀʜ ᴋᴜ ɴᴜ ɴᴀ ᴍɪɴ ʟᴏᴠᴇ ᴡᴀᴊᴀɴ ꜱʜᴀʀɪɴɢ* 🌼 🌹 🌹 🌼 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *BA NI DA GATA*🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌼. 🌼 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 *ᴘᴀɪᴅ ʙᴏᴏᴋ* *NARRATED & WRITTEN BY* *ZULFA'U SA'EED IBRAHIM* ( *_MATAR SAYYADEE_*) ☀️ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION*☀️💪 ( *Home of quality and trusted writer's of the nation*)💪🏻 *DEDICATED TO THE MOST BEAUTIFUL WOMAN IN THE WHOLE WORLD (MY MOTHER). ALLAH YA JIK'AN KI DA ℝ𝔸ℍ𝔸𝕄𝔸* *__________________* *FREE PAGE 9&10* *__________________* ..............Bayan an gama busar da kan, aunty Raliya ta mai da ta kan kujeran ta re da k'ara gyara kan tai parking d'insa a tsakiya ta re da yi mata donut, sannan kuma ta saki jelar har tsakiyar bayan ta da shi ma ya sha stones ma su kyau, ta kuma sa ka mata wani kwalliya ma su kyalli da ya k'ara k'awata gashin na ta akan donut d'in. Wad'annan matan da su ka rik'e Binty a kai mata gyaran kai kuwa bakin su ya k'i rufuwa sai adoring gashin su ke yi. Wata doguwar gown kalar pink Raliya ta fito da shi a cikin wani kwali da fad'ar tsaruwar shi b'ata ba ki ne. Pant ta fa ra saka mata fari k'al da shi ka na ta saka mata wannan had'ad'd'an gown d'in. Powder kawai ta shafa mata ta re da lipstick. "Wow!". Fad'in Raliya sai k'ara kallon Bintyn ta ke yi kamar ta lashe ta. Domin fad'in irin kyawun da Binty ta yi b'ata baki ne. Za ka rantse y'ar shugaban k'asa ce ko kuma 'dan majalisa. Hannunta Raliya ta ka ma su ka fito daga cikin wannan d'akin. Duk in da su ka wuce sai ido ya koma kan su ta re da gabon kyawun da Bintyn ta yi. Wasu ma har hoto su ke mata. Ita kan ta aunty Raliyar ta ma ta hoto ya kai kala ashirin. Akwai wanda su ka yi su biyu da kuma wanda ta yi ma ta ita kad'ai. Ko da su ka zo wajan motar Alhaji Sammani, bai ga ne Binty ba, sai ce wa ya yi, "Raliya kun dad'e fa, ina ita yarinyar ta ke?". Nu na Binty ta yi ta na murmushi tare da fad'in, "Alhaji ba ga tanan ba. Ka ga ta canza ko?". Waro idanuwa Alhaji Sammani ya yi tare da fad'in, "Haba dai? Wannan ita ce yarinyar da na zo da ita. Kai ina there must be mistake somewhere, wannan ba yarinyar da na kawo ba ce". Fad'in Alhaji Sammani ya na k'ara gwale idanuwa ya na kallon Bintyn da ke ta zuba masa murmushi kumatukanta na lob'awa. "Wallahi sir itace, ita ce, ni kai na da na gyara ta ba k'aramin mamaki na ke da kyawun da Allah ya ni'imtata da shi. Don Allah Alhaji kar ka ce na cika tambaya, ya ka ke da ita?". Shan mur Alhaji Sammani ya yi ta re da fad'in, "Wannan ba matsalar ki ba ce, forward your account details in tura ma ki kud'in ki tun da kin ga ma aikin ki". Tsuke baki Raliya ta yi ta re da daddanna wayarta. Cikin abunda bai fi minti biyu ba, har Alhaji Sammani ya turawa Raliya dubu d'ari biyu. "Thank you Sir". Raliya ta fad'a ta re da shafa kan Binty ta ce, "To Beauty sai mun sa ke had'uwa. Ki kula da kan ki kin ji?". "To" shi ne kawai abunda Binty ta fad'a. Shi kuwa Alhaji Sammani ce wa ya yi cikin zuciyar sa, "Shegiya sai dai a lahira, don wallahi na tabbata yau na kai wannan kyakkyawar yarinya k'ungiya, sai an ba ni muk'ami na musamman". Ya na gama fad'in hakan ya ka ma Binty ya d'aga ta ta re da sa ka ta gaban mota, ka na ya zagaya ya shiga mazaunin driver ya yi wa motar key ta re da reverse ya bar Saloon d'in ya nu fi wa ni eatery da ita domin ta ci abincin, don har an yi kiran sallar magriba. Waitress ce ta zo ta ka wo ma sa menu ya zab'i abunda za'a kawo ma su. Shi bai yi ordering ko mai ba, Binty ka wai ya sa a ka kawo wa pounded yam da miyan egusi da yaji stockfish da ganda a ciki. Ko da Binty ta ga abincin sai ta dinga bin abincin da idanuwa domin bata tab'a ganin irin wannan abincin ba a rayuwar ta. "Ci mana Binty, ki yi sauri mu ta fi dare na yi". Fad'in Alhaji Sammani. "Ni ban san abincin ba, ya ake yin sa? Ban tab'a ganin sa ba". Binty ta fad'a. "Zan ci uwar yarinyar nan wallahi". Alhaji Sammani ya fad'a cikin zuciyar sa. Amma a zahiri sai ce wa ya yi, "Ki gutsiri wannan, sai ki sa ka a cikin miyar ki sa ka a bakin ki, akwai dad'i". Ya fad'i hakane ya na mata demonstrating. Kamar yadda ya gwada ma ta haka ta yi, aikuwa ta wa ni lumshe ido tare da fad'in, "Kaiiiii wallahi akwai dad'iiiiiiii, kamar in ta ci kar ya k'are". "Duk lokacin da ki ke so ki min magana zan kawo ki nan sai ki k'ara ci". Fad'in Alhaji Sammani ci ke da k'osawa. Ba ta sa ke cewa ko mai ba, sai faman loma ta ke yi ta na jujjuya kai ta re da k'anana-k'ananan wak'a. Miyan kuma duk ya b'ata gaban pink 'din rigarta. Sai da ta ci sakwara biyar duk da cewar k'anana ne sai da Alhaji Sammani ya saki baki ya na kallon ta ci ke da mamaki cin abincin ta. "Tun da kin gama tashi mu tafi kar mu yi dare". Binty da ke lashe hannunta ta mik'e tare da share sauran miyan a jikin rigarta ka na ta d'au goran ruwan dake wajan ta yi gaba. Alhaji Sammani kuwa kiran waitress d'in ya yi ta re da bi yan kud'in ka na ya bi yo bayan Binty da ke tafiya ta na kwankwad'ar ruwan gora. Bu'de mota ya yi ta re da sa ka taa ciki shikuma ya juya ya koma mazaunin driver. Hotel d'in da ya sauka can ya nufa ta re da ruk'o hannun Bintyn ka har d'akin da ya ka ma. Makeken d'aki ne mai d'auke da royal bed da kuma wani rantsantsan Chinese carpet mai d'ankaran laushi. Ga kuma makeken gado samfarin italy. Gaba d'aya Binty rud'ewa ta yi da ganin wannan d'akin, sai kalle-kalle ta ke yi ta re da k'if-k'if da idanuwa. K'afarta ta d'aga ta re da saukewa a kan wannan Chinese carpet d'in mai laushi. Wani ihu ta kwandara da ya firgita Alhaji Sammani, duk a tunanin sa ta hango abunda ke cikin jakar da ya shigo da ita ne. Domin ta kulle idanunta ne ta re da k'ank'ame jikinta. "Ke lafiyan ki?" Alhaji Sammani ya fa'da ya na matsowa in da ta ke. "Sansanin macijai na fad'a. Ka taimaka ka ciro min k'afata ka min na mutu. Na d'aura k'afata a kan maciji mai taushi". Dariya ce ta sub'ucewa Alhaji Sammani, aiko ya kyakyata har da rik'e ciki ka na ya ce, "Kwantar da hankalin ki Binty. Ba'a kan maciji ki ke ba, akan carpet ki ke mai laushi. Ba bu maciji a ciki n hotel d'in nan". Fad'in Alhaji Sammani ya na murmushi. Sai a lokacin Binty ta soma bud'e idanunta kwara d'aya, ka na shi ma d'ayan ta bu'de sa. Doguwar ajiyar zuciya ta yi ta re da fad'in "Kaiii amma Allah na gode ma ka. Na d'auka mutuwa zan yi ai. Yanzu wanna shi ne kapur? To menene kapur 'din? Me ya sa ake saka sa a nan d'in?". Binty ta fad'a ta re da duk'awa ta na shafa carpet d'in ta na dariya. "Kapur d'in akwai d'an ban zan laushi. Hannuna lumewa ya ke yi a ciki. Kalla fa?". Binty ta sa ke fad'i ta na k'ara cusa hannunta a ciki n carpet d'in. "Ammafin shi ke nan ai kwalliyar d'aki da shi". Fad'in Alhaji Sammani ta re da wucewa toilet ya bar ta a wajan sai zuba k'auyanci ta ke yi. Hatta bedside lamp sai da ta shafa ta na mamakin wannan miye. Har Alhaji Sammani ya ga ma abunda zai yi ya fito daga toilet Binty na nan ta shafa wannan, ta shafa wancan. "Ki kwanta a kan fado ki bacci, gobe da sassafe zan kai ki wajan Hadaan d'in ki, kin ji?". Ci ke da farin ciki Binty ta kalli Alhaji Sammani ta re da fad'in, "A wannan abun mai kyau zan kwanta? Kai amma na ji dad'i". Binty ta fad'a ta re da hawa kan gadon. Wani ihu ta sa ki ta re da mik'ewa ta zauna a tsakiyan gadon ta kuma gantsaro ba yan ta ta re da fad'in, "Wayyoo Allah bola uwata ba ya na zai karye." Alhaji Sammani tsaye ya yi ya na kallon ta, har ga Allah ya so kungiya ba ta buk'aci ya kai yarinyar k'arama kuma virgin ba, da ba bu abunda zai ha na shi d'aukar yarinyar nan ya kai ta gidan shi ko dan ya rik'a shan dariya da irin shirman ta. Ita kuwa Binty da ba ta ta'ba kwanciya ko a kan kara ba shiyasa yau da ta kwanta a katifa autopadic ta ji kamar ba yan ta zai b'alle don katifar gand'and'an haka ta ke. Irin na ma su ciwon ba ya ne. "Ni wallahi ban kwanciya a nan, k'asa zan kwanta idan ba haka ba ba ya na karyewa zai yi." Binty ta fad'a ta re da saukowa daga kan gadon ta ko ma kan centre carpet d'in nan ta kwanta ta re da fad'in, "Yauwa ai gwara nan. Ga laushi ga dad'i. Wallahi nan zan yi kwanciya ta. Kai ka yi ta kwanciyar ka a kan dutsen can, amma ni nan zan kwana". Alhaji Sammani bai ce ma ta k'ala ba, ya kashe wuta ya hau gado ya kwanta ya na jiran lokacin zuwa meeting ya yi. ..........."Dadddd!" Sabrin ta kwala kiran sunan daddyn na ta kamar ta na kiran sunan sa'an ta. Abunda zai ba ku mamaki daddyn na ta na kusa da ita. "Wallahi ba za su shiga makarantar nan ba, idan kuma za su shi ga sai dai ni a cire ni a mai da ni *lead British*, kai daddy ni yanzu ma ban san *Hampos Academy* d'in, su a sa ka su, ni kuma a kai ni *Lead British*, amma ba zan shiga makarantar da su ke ba, kuma su ma ba za su shi ga in da na ke ba. That's the final decision. I'm clear dad?" Wani irin mik'ewa haijya Sakna ta yi ta re da isa wajan da Sabrin d'in ta ke ta d'aga hannu za ta sauke mata lafiyayyan mari a kan kuncin ta, Alhaji Saifullahi ya yi saurin ta re hannun Hajiya Sakna ta re da fad'in, "Ahir d'in ki da tab'a fuskan y'ata. Mai ta yi ma ki? Ni fa ba na son irin wannan abun da ki ke yi fa Sakina. Yarinyar nan kin san yarinya ce, a hankali ya ka ma ta a rik'a bin ta. Kin fi kowa sanin yarinyar nan ba ta da isasshen lafiya. Da ciwon zuciya a ki ka haife ta. So ki ke ki kashe min 'ya Sakna?". "Yanzu Alhaji ka na ga nin wannan hanya bai b'ullewa ce? Yarinyar fa k'ara lalacewa ta ke yi. Kar ka manta wata rana gidan wani za ta. Wallahi ba bu wanda zai d'auki wannan iskancin na ta. A ce yarinyar k'ank'anuwa da ita amma bak'in ciki da hassada ya mamace zuciyar ta. Hatta ni d'in nan mahaifiyar ta kishi ta ke yi dani. Ka duba ka ga ni, wad'annan gaba d'aya y'an uwan ta ne, amma ta ke ik'irarin ba za ta yi karatu a makaranta d'aya da su ba. Ka san saboda mai ya sa ta ce haka? To saboda aji su na bearing the same surname da su ne. Ita a rayuwarta ba ta k'aunar wa ni yai abu iri d'aya da ita ko kuma ya fi ta a wani abu. Sabrin ba ta k'i a ce daga ita ni da kai da Junaina ba mu sa ke haihuwa ba don ta kasance ita ce d'aya d'iyar mu. Ku ma wallahi ku ne ma su k'ara dulmiyar da ita wajan nu na mata abubda ta ke yi dai-dai ne. Kuma wallahi Alhaji ba'a saka 'yan biyu a makarantar da su ke so ba to kuwa ba ai ma su adalci ba. Ko da ya ke, adalci ka ke yi ma. Ko mai fa idan za ka sayawa wad'annan y'ay'a to fa na Sabrin sai ya fi kyau da tsada saboda ita d'in ta daban ce a wajan ka. Kuma wallahi yaran nan su na ganin ko mai. Wa ni abu ka ke da sa ma su a cikin zuciyar su wan da wallahi nan ga ba za kai nadama. Ku ma idan har ni mahaifiyar Sabrin ce, ban yadda a raba masu makaranta da y'an biyu ba. Idan *Lead British* za ta ko ma, to su koma ta re. Idan ku ma Hampos 'din za ta cigaba da zuwa, to su cigaba da zuwa ta re. Ai su ma y'ay'an ka ne kamar yadda ta ke y'ar ka. Matsayinsu d'aya". "Never! Matsayin mu ba d'aya ba ne wallahi mom". Fad'in Sabrin ta na turo ba ki gaba. Wawan mari Hajiya Sakna ta sakarwa Sabrin sai da ta gigice ta kifa k'asa. Alhaji ya harzuk'a shi ma ya d'aga hannu ya daddage ya wanke fuskan Hajiya Sakna da mari sai da ta yi taga-taga za ta fad'i. Aunty Junaina kuwa wani irin murmushi ta sak'i wanda ba bu wanda ya lura da ita sai d'aya daga cikin y'an biyu mai su na Amrah. *ASSALAMU ALAIKUM READERS, GA NI NA ZO MA KU DA SABON LITTAFI NA MAI SUNA A SAMA, WANDA YA ZO DA ZAFI-ZAFIN SA, KUMA NA TABBATA ZA KU JI DAD'IN SA. BA ZAN CI KA KU DA SURUTU BA, KAWAI KU BI NI A FREE PAGES, KU DA KAN KU ZA KU GA NE BOOK D'IN NA DABAN NE. KAWAI KU NU NA MIN ONE LOVE WAJAN SIYAN BOOK D'IN AKAN FARASHI AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA:* *Normal group shine mutum zai bi ya 500 idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300.* *VIP kuma 1000 ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700.* *MUTANAN NIGER KUMA ZA SU BI YA KAMAR HAKA*: *Normal group shine mutum zai bi ya 500F idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300F.* *VIP kuma 1000F ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700F.* *EVIDENCE OF PAYMENT 08128755583* *MATAR SAYYADEE CE* SHARE AND COMMENT PLEASE 🌼 🌹 🌹 🌼 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *BA NI DA GATA*🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌼. 🌼 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 *PAID BOOK* *NARRATED & WRITTEN BY* *ZULFA'U SA'EED IBRAHIM* ( *_MATAR SAYYADEE_*) ☀️ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION*☀️💪 ( *Home of quality and trusted writer's of the nation*)💪🏻 *DEDICATED TO THE MOST BEAUTIFUL WOMAN IN THE WHOLE WORLD (MY MOTHER). ALLAH YA JIK'AN KI DA RAHAMA* *KU HANZAR TO KU HWARA PAYMENT, KA DA KU BA RI A BA KU LABARI. NORMAL GROUP, D'ARIN KI BIYAR #500 KACAL ZAI BI YA MI KI BUK'ATA, SHI MA IDAN KATI ZA KI TURO, IDAN KUMA TA ACCOUNT NE, D'ARIN KI UKU #300 YA ISHE KI. VIP KUMA #1000 IDAN KATI NE, IDAN KUMA TA ACCOUNT NE D'ARIN KI BAKWAI #700 ZAI BI YA MI KI BUK'ATAR KI. KI HAN ZAR TA KAR A BA KI LABARI. 0592412800, SAI KI TURO DA SHAIDAN BIYAN KI A WANNAN NUMBER 08128755583. SAYAN NA GARI, MAI DA KUD'I GIDA* *____________________* *FREE PAGE 11&12* *____________________* ............."Alhaji ni ka mara saboda ina ko ya wa y'ata tarbiya?". Fad'in Hajiya Sakna rik'e da kunci ta na kallon Alhaji Saifullahi. "An mareki d'in, ki yi abunda za ki yi. Wannan ba tarbiya ce, kawai ba ki son ta ne shiyasa ki ke ga na mata azaba. Kuma idan har NI ne mahaifin su, kuma ni ke biyan kud'in makarantar, Sai in da Sabrin ta zab'a za ta shiga. Kuma kamar yadda ta ce ba za ta yi karatun a makaranta d'aya da su y'an biyu ba, hakan zan yi. Za ta ko ma *LEAD BRITISH* kamar yadda ta buk'ata, su kuma twince su ta fi *HAMPOS* d'in. That's my final decision". Alhaji Saifullahi ya fad'i a tsawace. Aunty Junaina kuwa, cike da mak'irci da mubafunci ta kalli Hajiya Sakna ta re da fad'in, "Mummyn Zaid, ki yi hak'uri ta je makaranta da ta ke so, ai ba bu komai, su kan su y'an uwan na ta ai sun san halin da ta ke ciki. Su kan su su na supporting ai ma ta abunda ta ke so saboda lalurar ta. Ni na san ba sa jin komai a hakan haka. Ko ba haka ba Amrah". Aunty Junaina ta k'arishe maganar ta na kallon fuskan Amrah da tai kicin-kicin da rai. "Bar ta kawai Junaina, tun ba yau ba na fahimci Sakna kishi ta ke yi da Sabrin kamar ba d'iyarta ba. Ta fi k'aunar sha-sha-shan can Zaid da babu abubda ya sa ni Sai fad'i da rashin jin magana. Ku ma wallahi ni babu wanda ya isa ya raba min kan y'ay'a". Alhaji Saifullahi ya fad'a ya na buga babbar rigar shi cike da masifa. Sabrin kuwa sai murmushin jin dad'i ta ke yi saboda yadda daddyn ta a ko'ina ya ke nuna ita d'in ta musamman ce a wajan shi. Hakan na matuk'ar burgeta. Duk da ta mi wani iri kad'an da daddyn na ta ya wanke fuskan mahaifiyar na ta da mari. Hanan tagwainiyar Amrah kuwa ji ta ke kamar tai bindiga saboda tsabar b'acin rai da yadda daddyn na su ke nuna banbanci b'aro-b'aro a tsakanin su da y'ar uwar ta su. Hakan ya jefa masu mugun tsanar Sabrin d'in a cikin zuciyar su wanda ko k'aunar ganin ta ba sa yi. Hajiya Sakna da ke tsaye dafe da kuncinta ta na hawayen bak'in ciki saboda lallata mata y'a da Junaina da daddynta su ke yi wanda tun tuni ta ga ne Junaina ba k'aunar Sabrin d'in ta ke yi ba. Kawai so ta ke ta lalace, don ita kan ta kishi ta ke da abubda mahaifin na su ya ke wa Sabrin d'in kamar ita ce kad'ai y'arsa don bai had'a Sabrin d'in da kowa ba. Ju ya wa ta yi a fusace ta ha ye sama da sassarfa ta shige d'akinta ta re da turo k'ofa ta fad'a kan gado ta saki kuka mai d'an sauti. Alhaji Saifullahi kuwa, kama hannun Sabrin ya yi ta re sa fad'in, "Sorry my Queen, mu je in d'an yawata da ke a gari hankalin ki ya kwanta kin ji daughter. Don't mind your mother". "Daddy zan je ni ma". Fad'in Hanan". Fad'in Hanan. Wawan mintsili mahaifiyarta ta kai mata a kan cinyarta ta re da antaya mata harara. Hakan ya yi dai-dai da lokacin da Sabrin ita ma ta sauke mata wani irin kallo mai cike da gargad'i ta re da harara. Mahaifin na su kuwa cewa ya yi, "No Hanan, wannan fitar ta queen ce. Ku je ku ta ya mom d'in ku da aiki ka min mu dawo. And make sure you cook her favourite before we come back". Ya k'arisa maganar ne ya na kallon aunty Junaina kasancewar ita ke da girki. "In sha Allah". Fad'in aunty Junaina murmushi kwance a fuskan ta, yayin da zuciyar ta ke wani irin gurnanin wuta mai ci ke da tsantsar tsanar Sabrin d'in. *HOTEL* K'arfe d'aya da minti hamsin da biyar ya farka, da ma baccin na shi sama-sama ya ke. Sauko wa ya yi daga kan gado ta re da kunna hasken torchlight d'in wayar sa ta re da jawo wata jaka mai kama da briefcase ya fiddo wani d'an karamin gunkin da gaba d'aya jikinsa allurai ne aka caccaka har ta tsakiyar kan gunkin nan. Ajiye gunkin ya yi a kan gado a hankali ka na ya fiddo da wani bak'in wando ya saka ta re da wata doguwar jan riga har k'aurin sa, ka na ya zaro wani bak'in d'an kwali ya d'aura a kan sa ya ku ma saka wani jan abu tun daga kan karan hancinsa har goshinsa. Wannan gunkin ya d'auko ta re da d'aga shi sama ya soma wasu surutai da wasu yare. Cikin minti d'aya kan wannan gunkin ya soma fitar da wani irin wuta kamar an watsa petur. Jinginar da gunkin ya yi a jikin bango, ka na yai masa sujada sau goma sha bakwai. Bakin gunkin ne ya bu'de, wani jan mayafi ya fad'o daga ba kin shi. 'D'aukar mayafin Alhaji Sammani ya yi ta re da fad'in, "Karbut-karbut, zundun-zundun, zundubutt". Ya na ga ma fad'in haka ta ke gunkin ya b'ace b'at. Shi kuma Alhaji Sammani ya koma in da Binty ta ke a kwance ya kwanta a gyefanta flat ta re da rufa masu wannan kyallan. Cikin second biyar su ka b'ace b'at gaba d'ayan su. A tsakiyar k'urgumin daji su ka tsinci kan su. Alhaji Sammani ya sab'a Binty a kafad'a ta re da kutsa kai cikin dajin nan. Bai yi tafiyar minti biyar ba, ya isa gaban wani wawakeken fili. Wa ni irn kyafkyafta idanuwa ya so ma yi ta re da yin wasu surutai kamar haka, "Talshibtulyii massburut mulmulgab pucapuca hardurdus birit hadar darrrr". Ya na ga ma fad'in haka wani irin k'ofa ya soma b'ullowa daga cikin k'asa. Sai da ya kwashi mintuna biyar ka min k'ofar ta ga ma bayyana gaba d'aya kuma zagaye da katanga. A gaban k'ofar kan wani ru sheshen kwarangwal ne idanuwan sa na zubda jini. Alhaji Sammani ya shimfid'ar da Binty ta re da isa gaban k'ofar nan ya kalli kwarangwal d'in nan ta re da ma sa sujada guda biyar. Kwarangwal d'in nan ya feso masa jini a fuskan shi, ka na k'ofar ta bud'e. Juya wa Alhaji Sammani ya yi ta re da sab'o Binty a kafad'a da ke bacci kamar ta mutu su ka shiga cikin k'ofar nan. Sai da su ka wuce k'ofofi takwas, duk k'ofa d'aya akwai bak'ak'en dakaru guda d'ari, fuskan su kawai idan mutum ya kalla zai iya mutuwa sabada tsabar firgita da irin halittan su. Wata k'ofa mai ruwan gold wanda ita ce k'ofa ta k'arshe da za ta sadaka da ainahin fad'ar tsafin. Nan ma sai da Alhaji Sammani ya sauke Binty ta re da yin surutai kamar na farko, sannan ku ma yai wa wani gunki sujada ka na k'ofar ta bud'e ya k'ara sab'a Binty a kafad'a su ka shige. Fad'in girman wannan fad'ar b'ata baki ne, amma wannan fada zata iya d'auke mutane dubu hamsin a cikin ta. Gaba d'aya layi su ka yi ko wannan su a kwai wani d'an kwarya a hannunsa mai d'auke da jini a ciki wanda d'aya daga cikin su yai sacrificing wani abun. Alhaji Sammani shimfid'ar da Binty ya yi a tsakiyar wad'annan mutane kanta na fuskanta wani k'atotan dodon tsafin da girman kawai ya cika bango d'aya na hall d'in. Amma kan shi d'an k'arami ne. Sujada Alhaji Sammani ya yi wa wannan gunkin, ka na ya d'ago ta re da nufar wata wawakeken rijiya da ke cikin fadar nan, ya d'auki kwarya ta re da d'ebo jini yq dawo ya fuskanci dodon tsafin nan ta re da nuna masa kwaryan, ka na ya yi kurb'a biyar ta re da ko ma wa layi shi ma ya tsaya rik'e da kwaryan a hannun sa. Wani garjejan mutum ne mai d'auke da tambarin sarauta a kan shi da wani sanda a hannunsa, gaba d'aya tun daga saman shi har k'asan shi bak'ak'en ka ya ne mai santsi da shining a jikinsa. Kallon Alhaji Sammani ya yi wanda ya duk'ar da kan shi jikinsa na rawa. D'an yatsar shi ya d'aga ta re da nu na Alhaji Sammani. Sai ga Alhaji Sammani ya taho kamar iska ya tsaya a gaban shi. Jikin Alhaji Sammani na rawa ya zube tare da yin sujada a kan k'afar wannan mutumin ya na fad'in "Tuba na ke mai girma Durdus, a gafarce ni. Yau na taho da abunda ka buk'ace da na kawo, ku ma nasan za ka ji dad'i da farin ciki idan har ka duba abunda na kawo d'in". Alhaji Sammani ya fad'a kamar zai saki zawo don tsoro. "Na rantse da dodon tsafin Kalhark'o wannan karan idan har ka sab'a mana sai na yi maka hukunci mummuna. Ka dad'e ka na sab'awa umarnin Kalhark'o, kai ba ka san ka na san ya mu a cikin fushinsa ba ne. To da ka. Jawo ma na tab'ewa da tsinuwar Dodo Kalhark'o gwara mu tsone jinin ka ta re da taune k'ashin ka kowa ya hutu. Alhaji Sammani har ya so ma sakin fitsarin tsoro, ya sake sujada a kan k'afafun Durdus ta re da fad'in, "Tuba na ke shugaba, da izinin Dodo Ka Kalhark'o za ka ji dad'in kyautar da na kawo yau". Durdus yatsarsa ya k'ara d'agawa ya nu na Alhaji Sammani da shi, sai ga Alhaji Sammani na ta shi kamar iska ta baya, ya koma matsayarsa. Yatsar ya k'ara d'agawa ta re da d'ago Binty da ke shimfid'e a k'asa. Mik'ewa ta yi k'ek'am ku ma still bacci ta ke yi ko motsi ba ta yi ba. Taho da yatsarsa ya ke yi, ita ma Binty ta na k'ara matsowa ku sa da shi. Sai da ta zo daf da shi ya tsayar da ita cak ta re da yin sama da yatsar shi. Ta ke fuskanka ta d'ago, shi ku ma ya sa ka idanunsa a kan na ta da ke rufe ta na bacci. Shafa idanuwan ta ya yi. Wani irin firgita ta yi ta re da bud'e idanuwanta ta sauke a kan Durdus. *KU HANZAR TA FA, FREE PAGES 'DAYA YA RAGE. KUMA DAGA GOBE NE FA! KA KI JIRA NA SATA Y'AR UWA. D'ARI BIYAR D'IN KI ZAI BI YA MIKI BUK'ATA, SHI MA IDAN KATI NE ZA KI TURO. IDAN KUMA TA ACCOUNT NE. D'ARIN KI UKU YA ISHE KI* Wani irin haske Durdus ya ga ni a cikin kwayar idanun Binty. Ja da baya Durdus ya yi wanda hakan ya firgita hancin gaba d'aya jama'ar wajan. Don yau ne rana ta farko da wani abu ya kid'ima Durdus har ya bayyana a jiki da fuskansa. Shi kuwa Alhaji Sammani zawo ne ya nai mi kwace masa. Hanjinsa kuwa kamar za su tsintsinke. "Ka ji tsoro ne bak'in arne?". Binty ta fad'a da wani razananniyar muryan tsohuwa wacce za ta iya kaiwa shekaru saba'in a duniya. "Wa cece ke? Mai ki ke buk'ata anan? Ni ban gayyace ki ba, ki fita a jikin wannan yarinyar jinin ta za mu sha kuma mu sadaukar da budurcinta ga Dodan tsafi. "Karyan ka!". Fad'in Binty cikin muryan tsohuwan nan ta na wani irin mik'ewa ta na k'ara tsaho har sai da kan ta ya tab'o silin d'in k'aton hall d'in nan. Faratunan hannunta ya k'ara wani irin tsawo daga tsayan nan na ta har ya na tab'a k'asan d'akin taron nan. Wani irin ihu Binty ta yi wanda ya saka ga ba d'aya kayan jikin mutanan wajan fita daga jikinsu har da shugaba Durdus. Wani ihun ta k'ara yi da ya kifo da Dodon tsafi nan da girman sa ya cika bango d'aya. Da ba din tashi saman da Durdus ya yi da sauri ba, sai Dodon na ya kashe shi. Duk da haka ma sai da ya kashe mutane saba'in. Fa'duwa gabanta Durdus ya yi ta re da fad'in, "Tuba na ke sarauniyar aljanu, ki min aikin gafara. Ku d'auki yarinyar nan ki tafi da ita ka da ki halakar da mu". Gaba d'aya sauran mutanan su ma su ka kwanta flat su na rok'an Binty. Shi kuwa Alhaji Sammani ya san ta shi ta k'are. Don ya tabbata mutawa zai yi. A hankali Binty ta so ma rage tsawonta har ta dawo dai dai tsayin ta ta re da fad'in, "Ku azzalumai ku saurare ni, ban ga ma da ku ba, zan dawo a cikin shiri domin in ga ma da ku. Ba za Ku k'ara cutar da wa ni d'an Adam ba. Ku ma zan ta tafi, amma ta rezan ta fi da wannan azzalumin, da kai na na ke son in hukunta shi". Alhaji Sammani kuwa da jin abunda Binty ta fad'a ya sa ki zawo ba adadi. K'arasa Binty ta yi ta re da dafa Alhaji Sammani su ka b'ace ta re. *ASSALAMU ALAIKUM READERS, GA NI NA ZO MA KU DA SABON LITTAFI NA MAI SUNA A SAMA, WANDA YA ZO DA ZAFI-ZAFIN SA, KUMA NA TABBATA ZA KU JI DAD'IN SA. BA ZAN CI KA KU DA SURUTU BA, KAWAI KU BI NI A FREE PAGES, KU DA KAN KU ZA KU GA NE BOOK D'IN NA DABAN NE. KAWAI KU NU NA MIN ONE LOVE WAJAN SIYAN BOOK D'IN AKAN FARASHI AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA:* *Normal group shine mutum zai bi ya 500 idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300.* *VIP kuma 1000 ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700.* *MUTANAN NIGER KUMA ZA SU BI YA KAMAR HAKA*: *Normal group shine mutum zai bi ya 500F idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300F.* *VIP kuma 1000F ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700F.* *EVIDENCE OF PAYMENT 08128755583*🌼 🌹 🌹 🌼 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *BA NI DA GATA*🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌼. 🌼 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 *PAID BOOK* *NARRATED & WRITTEN BY* *ZULFA'U SA'EED IBRAHIM* ( *_MATAR SAYYADEE_*) ☀️ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION*☀️💪 ( *Home of quality and trusted writer's of the nation*)💪🏻 *DEDICATED TO THE MOST BEAUTIFUL WOMAN IN THE WHOLE WORLD (MY MOTHER). ALLAH YA JIK'AN KI DA RAHAMA* *KU HANZAR TO KU HWARA PAYMENT, KA DA KU BA RI A BA KU LABARI. NORMAL GROUP, D'ARIN KI BIYAR #500 KACAL ZAI BI YA MI KI BUK'ATA, SHI MA IDAN KATI ZA KI TURO, IDAN KUMA TA ACCOUNT NE, D'ARIN KI UKU #300 YA ISHE KI. VIP KUMA #1000 IDAN KATI NE, IDAN KUMA TA ACCOUNT NE D'ARIN KI BAKWAI #700 ZAI BI YA MI KI BUK'ATAR KI. KI HAN ZAR TA KAR A BA KI LABARI. 0592412800, SAI KI TURO DA SHAIDAN BIYAN KI A WANNAN NUMBER 08128755583. SAYAN NA GARI, MAI DA KUD'I GIDA* *____________________* *FREE PAGE 11&12* *____________________* ............."Alhaji ni ka mara saboda ina ko ya wa y'ata tarbiya?". Fad'in Hajiya Sakna rik'e da kunci ta na kallon Alhaji Saifullahi. "An mareki d'in, ki yi abunda za ki yi. Wannan ba tarbiya ce, kawai ba ki son ta ne shiyasa ki ke ga na mata azaba. Kuma idan har NI ne mahaifin su, kuma ni ke biyan kud'in makarantar, Sai in da Sabrin ta zab'a za ta shiga. Kuma kamar yadda ta ce ba za ta yi karatun a makaranta d'aya da su y'an biyu ba, hakan zan yi. Za ta ko ma *LEAD BRITISH* kamar yadda ta buk'ata, su kuma twince su ta fi *HAMPOS* d'in. That's my final decision". Alhaji Saifullahi ya fad'i a tsawace. Aunty Junaina kuwa, cike da mak'irci da mubafunci ta kalli Hajiya Sakna ta re da fad'in, "Mummyn Zaid, ki yi hak'uri ta je makaranta da ta ke so, ai ba bu komai, su kan su y'an uwan na ta ai sun san halin da ta ke ciki. Su kan su su na supporting ai ma ta abunda ta ke so saboda lalurar ta. Ni na san ba sa jin komai a hakan haka. Ko ba haka ba Amrah". Aunty Junaina ta k'arishe maganar ta na kallon fuskan Amrah da tai kicin-kicin da rai. "Bar ta kawai Junaina, tun ba yau ba na fahimci Sakna kishi ta ke yi da Sabrin kamar ba d'iyarta ba. Ta fi k'aunar sha-sha-shan can Zaid da babu abubda ya sa ni Sai fad'i da rashin jin magana. Ku ma wallahi ni babu wanda ya isa ya raba min kan y'ay'a". Alhaji Saifullahi ya fad'a ya na buga babbar rigar shi cike da masifa. Sabrin kuwa sai murmushin jin dad'i ta ke yi saboda yadda daddyn ta a ko'ina ya ke nuna ita d'in ta musamman ce a wajan shi. Hakan na matuk'ar burgeta. Duk da ta mi wani iri kad'an da daddyn na ta ya wanke fuskan mahaifiyar na ta da mari. Hanan tagwainiyar Amrah kuwa ji ta ke kamar tai bindiga saboda tsabar b'acin rai da yadda daddyn na su ke nuna banbanci b'aro-b'aro a tsakanin su da y'ar uwar ta su. Hakan ya jefa masu mugun tsanar Sabrin d'in a cikin zuciyar su wanda ko k'aunar ganin ta ba sa yi. Hajiya Sakna da ke tsaye dafe da kuncinta ta na hawayen bak'in ciki saboda lallata mata y'a da Junaina da daddynta su ke yi wanda tun tuni ta ga ne Junaina ba k'aunar Sabrin d'in ta ke yi ba. Kawai so ta ke ta lalace, don ita kan ta kishi ta ke da abubda mahaifin na su ya ke wa Sabrin d'in kamar ita ce kad'ai y'arsa don bai had'a Sabrin d'in da kowa ba. Ju ya wa ta yi a fusace ta ha ye sama da sassarfa ta shige d'akinta ta re da turo k'ofa ta fad'a kan gado ta saki kuka mai d'an sauti. Alhaji Saifullahi kuwa, kama hannun Sabrin ya yi ta re sa fad'in, "Sorry my Queen, mu je in d'an yawata da ke a gari hankalin ki ya kwanta kin ji daughter. Don't mind your mother". "Daddy zan je ni ma". Fad'in Hanan". Fad'in Hanan. Wawan mintsili mahaifiyarta ta kai mata a kan cinyarta ta re da antaya mata harara. Hakan ya yi dai-dai da lokacin da Sabrin ita ma ta sauke mata wani irin kallo mai cike da gargad'i ta re da harara. Mahaifin na su kuwa cewa ya yi, "No Hanan, wannan fitar ta queen ce. Ku je ku ta ya mom d'in ku da aiki ka min mu dawo. And make sure you cook her favourite before we come back". Ya k'arisa maganar ne ya na kallon aunty Junaina kasancewar ita ke da girki. "In sha Allah". Fad'in aunty Junaina murmushi kwance a fuskan ta, yayin da zuciyar ta ke wani irin gurnanin wuta mai ci ke da tsantsar tsanar Sabrin d'in. *HOTEL* K'arfe d'aya da minti hamsin da biyar ya farka, da ma baccin na shi sama-sama ya ke. Sauko wa ya yi daga kan gado ta re da kunna hasken torchlight d'in wayar sa ta re da jawo wata jaka mai kama da briefcase ya fiddo wani d'an karamin gunkin da gaba d'aya jikinsa allurai ne aka caccaka har ta tsakiyar kan gunkin nan. Ajiye gunkin ya yi a kan gado a hankali ka na ya fiddo da wani bak'in wando ya saka ta re da wata doguwar jan riga har k'aurin sa, ka na ya zaro wani bak'in d'an kwali ya d'aura a kan sa ya ku ma saka wani jan abu tun daga kan karan hancinsa har goshinsa. Wannan gunkin ya d'auko ta re da d'aga shi sama ya soma wasu surutai da wasu yare. Cikin minti d'aya kan wannan gunkin ya soma fitar da wani irin wuta kamar an watsa petur. Jinginar da gunkin ya yi a jikin bango, ka na yai masa sujada sau goma sha bakwai. Bakin gunkin ne ya bu'de, wani jan mayafi ya fad'o daga ba kin shi. 'D'aukar mayafin Alhaji Sammani ya yi ta re da fad'in, "Karbut-karbut, zundun-zundun, zundubutt". Ya na ga ma fad'in haka ta ke gunkin ya b'ace b'at. Shi kuma Alhaji Sammani ya koma in da Binty ta ke a kwance ya kwanta a gyefanta flat ta re da rufa masu wannan kyallan. Cikin second biyar su ka b'ace b'at gaba d'ayan su. A tsakiyar k'urgumin daji su ka tsinci kan su. Alhaji Sammani ya sab'a Binty a kafad'a ta re da kutsa kai cikin dajin nan. Bai yi tafiyar minti biyar ba, ya isa gaban wani wawakeken fili. Wa ni irn kyafkyafta idanuwa ya so ma yi ta re da yin wasu surutai kamar haka, "Talshibtulyii massburut mulmulgab pucapuca hardurdus birit hadar darrrr". Ya na ga ma fad'in haka wani irin k'ofa ya soma b'ullowa daga cikin k'asa. Sai da ya kwashi mintuna biyar ka min k'ofar ta ga ma bayyana gaba d'aya kuma zagaye da katanga. A gaban k'ofar kan wani ru sheshen kwarangwal ne idanuwan sa na zubda jini. Alhaji Sammani ya shimfid'ar da Binty ta re da isa gaban k'ofar nan ya kalli kwarangwal d'in nan ta re da ma sa sujada guda biyar. Kwarangwal d'in nan ya feso masa jini a fuskan shi, ka na k'ofar ta bud'e. Juya wa Alhaji Sammani ya yi ta re da sab'o Binty a kafad'a da ke bacci kamar ta mutu su ka shiga cikin k'ofar nan. Sai da su ka wuce k'ofofi takwas, duk k'ofa d'aya akwai bak'ak'en dakaru guda d'ari, fuskan su kawai idan mutum ya kalla zai iya mutuwa sabada tsabar firgita da irin halittan su. Wata k'ofa mai ruwan gold wanda ita ce k'ofa ta k'arshe da za ta sadaka da ainahin fad'ar tsafin. Nan ma sai da Alhaji Sammani ya sauke Binty ta re da yin surutai kamar na farko, sannan ku ma yai wa wani gunki sujada ka na k'ofar ta bud'e ya k'ara sab'a Binty a kafad'a su ka shige. Fad'in girman wannan fad'ar b'ata baki ne, amma wannan fada zata iya d'auke mutane dubu hamsin a cikin ta. Gaba d'aya layi su ka yi ko wannan su a kwai wani d'an kwarya a hannunsa mai d'auke da jini a ciki wanda d'aya daga cikin su yai sacrificing wani abun. Alhaji Sammani shimfid'ar da Binty ya yi a tsakiyar wad'annan mutane kanta na fuskanta wani k'atotan dodon tsafin da girman kawai ya cika bango d'aya na hall d'in. Amma kan shi d'an k'arami ne. Sujada Alhaji Sammani ya yi wa wannan gunkin, ka na ya d'ago ta re da nufar wata wawakeken rijiya da ke cikin fadar nan, ya d'auki kwarya ta re da d'ebo jini yq dawo ya fuskanci dodon tsafin nan ta re da nuna masa kwaryan, ka na ya yi kurb'a biyar ta re da ko ma wa layi shi ma ya tsaya rik'e da kwaryan a hannun sa. Wani garjejan mutum ne mai d'auke da tambarin sarauta a kan shi da wani sanda a hannunsa, gaba d'aya tun daga saman shi har k'asan shi bak'ak'en ka ya ne mai santsi da shining a jikinsa. Kallon Alhaji Sammani ya yi wanda ya duk'ar da kan shi jikinsa na rawa. D'an yatsar shi ya d'aga ta re da nu na Alhaji Sammani. Sai ga Alhaji Sammani ya taho kamar iska ya tsaya a gaban shi. Jikin Alhaji Sammani na rawa ya zube tare da yin sujada a kan k'afar wannan mutumin ya na fad'in "Tuba na ke mai girma Durdus, a gafarce ni. Yau na taho da abunda ka buk'ace da na kawo, ku ma nasan za ka ji dad'i da farin ciki idan har ka duba abunda na kawo d'in". Alhaji Sammani ya fad'a kamar zai saki zawo don tsoro. "Na rantse da dodon tsafin Kalhark'o wannan karan idan har ka sab'a mana sai na yi maka hukunci mummuna. Ka dad'e ka na sab'awa umarnin Kalhark'o, kai ba ka san ka na san ya mu a cikin fushinsa ba ne. To da ka. Jawo ma na tab'ewa da tsinuwar Dodo Kalhark'o gwara mu tsone jinin ka ta re da taune k'ashin ka kowa ya hutu. Alhaji Sammani har ya so ma sakin fitsarin tsoro, ya sake sujada a kan k'afafun Durdus ta re da fad'in, "Tuba na ke shugaba, da izinin Dodo Ka Kalhark'o za ka ji dad'in kyautar da na kawo yau". Durdus yatsarsa ya k'ara d'agawa ya nu na Alhaji Sammani da shi, sai ga Alhaji Sammani na ta shi kamar iska ta baya, ya koma matsayarsa. Yatsar ya k'ara d'agawa ta re da d'ago Binty da ke shimfid'e a k'asa. Mik'ewa ta yi k'ek'am ku ma still bacci ta ke yi ko motsi ba ta yi ba. Taho da yatsarsa ya ke yi, ita ma Binty ta na k'ara matsowa ku sa da shi. Sai da ta zo daf da shi ya tsayar da ita cak ta re da yin sama da yatsar shi. Ta ke fuskanka ta d'ago, shi ku ma ya sa ka idanunsa a kan na ta da ke rufe ta na bacci. Shafa idanuwan ta ya yi. Wani irin firgita ta yi ta re da bud'e idanuwanta ta sauke a kan Durdus. *KU HANZAR TA FA, FREE PAGES 'DAYA YA RAGE. KUMA DAGA GOBE NE FA! KA KI JIRA NA SATA Y'AR UWA. D'ARI BIYAR D'IN KI ZAI BI YA MIKI BUK'ATA, SHI MA IDAN KATI NE ZA KI TURO. IDAN KUMA TA ACCOUNT NE. D'ARIN KI UKU YA ISHE KI* Wani irin haske Durdus ya ga ni a cikin kwayar idanun Binty. Ja da baya Durdus ya yi wanda hakan ya firgita hancin gaba d'aya jama'ar wajan. Don yau ne rana ta farko da wani abu ya kid'ima Durdus har ya bayyana a jiki da fuskansa. Shi kuwa Alhaji Sammani zawo ne ya nai mi kwace masa. Hanjinsa kuwa kamar za su tsintsinke. "Ka ji tsoro ne bak'in arne?". Binty ta fad'a da wani razananniyar muryan tsohuwa wacce za ta iya kaiwa shekaru saba'in a duniya. "Wa cece ke? Mai ki ke buk'ata anan? Ni ban gayyace ki ba, ki fita a jikin wannan yarinyar jinin ta za mu sha kuma mu sadaukar da budurcinta ga Dodan tsafi. "Karyan ka!". Fad'in Binty cikin muryan tsohuwan nan ta na wani irin mik'ewa ta na k'ara tsaho har sai da kan ta ya tab'o silin d'in k'aton hall d'in nan. Faratunan hannunta ya k'ara wani irin tsawo daga tsayan nan na ta har ya na tab'a k'asan d'akin taron nan. Wani irin ihu Binty ta yi wanda ya saka ga ba d'aya kayan jikin mutanan wajan fita daga jikinsu har da shugaba Durdus. Wani ihun ta k'ara yi da ya kifo da Dodon tsafi nan da girman sa ya cika bango d'aya. Da ba din tashi saman da Durdus ya yi da sauri ba, sai Dodon na ya kashe shi. Duk da haka ma sai da ya kashe mutane saba'in. Fa'duwa gabanta Durdus ya yi ta re da fad'in, "Tuba na ke sarauniyar aljanu, ki min aikin gafara. Ku d'auki yarinyar nan ki tafi da ita ka da ki halakar da mu". Gaba d'aya sauran mutanan su ma su ka kwanta flat su na rok'an Binty. Shi kuwa Alhaji Sammani ya san ta shi ta k'are. Don ya tabbata mutawa zai yi. A hankali Binty ta so ma rage tsawonta har ta dawo dai dai tsayin ta ta re da fad'in, "Ku azzalumai ku saurare ni, ban ga ma da ku ba, zan dawo a cikin shiri domin in ga ma da ku. Ba za Ku k'ara cutar da wa ni d'an Adam ba. Ku ma zan ta tafi, amma ta rezan ta fi da wannan azzalumin, da kai na na ke son in hukunta shi". Alhaji Sammani kuwa da jin abunda Binty ta fad'a ya sa ki zawo ba adadi. K'arasa Binty ta yi ta re da dafa Alhaji Sammani su ka b'ace ta re. *ASSALAMU ALAIKUM READERS, GA NI NA ZO MA KU DA SABON LITTAFI NA MAI SUNA A SAMA, WANDA YA ZO DA ZAFI-ZAFIN SA, KUMA NA TABBATA ZA KU JI DAD'IN SA. BA ZAN CI KA KU DA SURUTU BA, KAWAI KU BI NI A FREE PAGES, KU DA KAN KU ZA KU GA NE BOOK D'IN NA DABAN NE. KAWAI KU NU NA MIN ONE LOVE WAJAN SIYAN BOOK D'IN AKAN FARASHI AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA:* *Normal group shine mutum zai bi ya 500 idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300.* *VIP kuma 1000 ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700.* *MUTANAN NIGER KUMA ZA SU BI YA KAMAR HAKA*: *Normal group shine mutum zai bi ya 500F idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300F.* *VIP kuma 1000F ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700F.* *EVIDENCE OF PAYMENT 08128755583* 🌼 🌹 🌹 🌼 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *BA NI DA GATA*🌹 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌼. 🌼 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 *PAID BOOK* *NARRATED & WRITTEN BY* *ZULFA'U SA'EED IBRAHIM* ( *_MATAR SAYYADEE_*) ☀️ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION*☀️💪 ( *Home of quality and trusted writer's of the nation*)💪🏻 *DEDICATED TO THE MOST BEAUTIFUL WOMAN IN THE WHOLE WORLD (MY MOTHER). ALLAH YA JIK'AN KI DA RAHAMA* *KU HANZAR TO KU HWARA PAYMENT, KA DA KU BA RI A BA KU LABARI. NORMAL GROUP, D'ARIN KI BIYAR #500 KACAL ZAI BI YA MI KI BUK'ATA, SHI MA IDAN KATI ZA KI TURO, IDAN KUMA TA ACCOUNT NE, D'ARIN KI UKU #300 YA ISHE KI. VIP KUMA #1000 IDAN KATI NE, IDAN KUMA TA ACCOUNT NE D'ARIN KI BAKWAI #700 ZAI BI YA MI KI BUK'ATAR KI. KI HAN ZAR TA KAR A BA KI LABARI. 0592412800, SAI KI TURO DA SHAIDAN BIYAN KI A WANNAN NUMBER 08128755583. SAYAN NA GARI, MAI DA KUD'I GIDA* *____________________* *FREE PAGE 13&14* *LAST FREE PAGE* *____________________* .............Ko da Binty ta farka, gyefan wa ni unguwan ta tsin ce ta ya she a k'asa jikinta duk k'asa. Gashin nan da ya sha gyara duk ya b'aci da datti duk da dai bai kai ko kwatan lokacin da ta ke rayuwa a kan bola ba. Dube-dube ta fa ra yi, can Kuma ta mik'e ta re da fad'in, "Ina ya ke kuma? Mai ya sa ya kawo ni nan? Shi ma ya gudu ya bar ni bai kai ni wajan Hadaan d'ina ba. Da ma na sa ni babu wanda ke so na". Ta fad'i maganar ne ta re da fashewa da ku ka sosai. Daga can gyefe kuma wata mata ce ta ci ado sanye da atampa wacce ake kira da matso kalar maroon, sai gyalanta irin tsohon yayin nan mai sun tissue, kalar pink da takalminta flat shoe na roba kalar bak'i sai wata k'atuwar jaka da kafatin k'auyan su ba mai irin sa. Wata yarinya ce ke matsar kwalla a gyefanta. Ita kuwa matar nan sai faman fad'a ta ke yi kamar ta ari ba ki. "Shegiya gantalalla y'ar Abun kwari, wacce ba ta san arziki ba. Yanzu ban da ke dak'ik'iya ce, wacece za ta yarda ta shiga gidan Alhaji Usman mai rabo a matsayin y'ar aikin su amma tai wa kanta sagegeduwa. Shegiya kawai kin cuceni kin cuci kan ki. Mu je wajan uwar ta ki, ita ma sai na mata ruwan rashin mutunci, kuma wallahi sai ta ba ni dubu goma na wahalar jigilar da nai ta yi da ke. Shegiya mai fuskan samudawa. Da na sani Bashira na d'auko ba ke lalatacciya ba. To in ban da lalaci ya za'ai in tura ki aiki ki je ki saki leb'e ki na bacci har d'an mai gidan ya buk'aci wani abu ai ta kiran ki shuru saboda ki na baccin asara. Wallahi sai na ci jakar Ubangi, y'ar k'undun uba kawai. Ga shi yau a kawai aka ba ni in samo wata y'ar aikin. Ni da garin mu ya ke Saminaka, Yaushe har na je yau na dawo. Ke dai wallahi anyi tsinanniyar y'a wallahi. Yanzu haka wata za su kira ta sa mo masu wata y'arkin, kin ga ni na rasa y'an karansin (currency) kenan. Wallahi Allah ya isa tsakanina da ke Basira". Kandala ta fad'i ta re da tura k'eyar y'ar yarinyar da ba za ta wuce shekara goma zuwa sha d'aya ba. Yarinyar na hawaye ta kalli Kandala ta re da fad'in, "Baaba Kande wallahi yaron gidan ne d'an iska. Kullum na je kai masa abunci sai ya rik'a tattab'a ni. Har wando ya ke cire min". "Lahaula walak'uwata! Jama'a ku ji min y'ar iskar yarinya da sharri. Dan uwar ki duk y'an matan da ya ga ni a k'asar waje da kuma irin y'an matan da su ke bin sa, ya rasa wacce zai yi lalata da ita sai ke y'ar tatsitsiya da ke? Yau na batsula na ga sharri ganin idona. Shiyasa ke nan ki ka dai na kai masa abincin har cikin d'aki sai dai ki aje a kwar d'aki kamar kin ajewa kare ko mage. Shegiya mai zubin aladun zamanin da. Yanzu ke Basira ko da zan can da ki ka fad'a gaskiya ne, ai arziki ne ki bin ki amma da ya ke she d'in y'ar Abun kwari ce, sai ki ka k'i yarda ko? Wallahi na san da kin aminci a cikin wata d'ayan nan da ki ka yi, sai kin ta ra kud'i ya kai kusan rabin million d'an ba gidan matsiyata ki ke ba. Amma kin cuci kan ki Basira, yanzu ai a kawo wacce za ta amince ta ci arziki ta Kuma bar arziki a in da ya ke. Ni dai ga dukkan alamu watan rashin rabo na ne ya tsaya shiyasa na d'auko ki. Shegiyar yarinya mai k'ashin tsiya". Kandala ta fad'a ta na matsar hawayen asarar da Basira ta jawo mata. Basira kuwa bata k'ara cewa ko mai ba, domin farin cikin da ta ke yi na barin ta gidan Alhaji Usman mai rabo. Don ita kad'ai ta san abunda ta ke ga ni na tantagaryar iskanci a wajan d'an sa na wajan matar gidan ta tsakiya. Don har sanin ta a matsayin y'a mace ya yi. Shiyasa yanzu ta ke jin dad'i da ta bar gidan. Ita kuwa Kandala tsayawa ta yi cak lokacin da idanuwan ta su ka sauka akan Binty da ke kuka ta na waige-waige. "Ki tsaya a nan ki jira ni ina zuwa". Fad'in Kandala ta re da nufar in da Binty ke a tsaye ta na kuka. "Yarinya lafiya? B'ata ki ka yi ne? Ina iyayen ki su ke". Kandala ta jeho mata wad'annan tambayoyin ta re da zuba ma ta idanuwa. "Ban gan shi ba, ya ce min zai kai ni wajan Hadaan d'i na kuma ya ka wo ni nan ya gudu ya bar ni". Binty ta fad'a ta na k'ara b'arkewa da kuka. "Waye shi d'in wanda ya gudu ya bar ki d'in? Kuma ina ne gidan ku". Kandala ta sa ke watso mata tambaya. "Ni ma ban san shi ba, amma ya min alk'awari zai kai ni wajan Hadaan, har kaya mai kyau ya siya min, ya kuma kai ni aka gyara min gashi na". Fad'in Binty ta na shashshek'ar kuka. "To wai ke ina iyayen ki su ke?". Kandala ta sa ke tambayanta cike da k'osawa. "Mamana ta na kan bola, ita ce ma bolan. Ba ni da kowa sai ita. Na gaji da zama a kan bolan ne saboda kowa bai so na shi ne na bar wajan don in koma wani wajan da kowa zai so ni. Shi ne wannan mutum d'in ya gan ni ya saka ni a motar shi ya ce min zai kai ni wajan Hadaan shi ne ya gudu ya bar ni ana". Binty ta fad'a ta na share kwallar da ke zubo mata. Kallon ta Kandala ta yi daga sama har k'asa, ta na son ta tabbatarwa kan ta shin mahaukaciya ce a gaban ta ko kuwa. Ga yarinya dai kyakkyawa da ita. "Ke nan ba ki da iyaye?". Kandala ta sa ke tambaya. "Ni ba ni da kowa sai bola ta. Akan bola na ke rayuwa. Hadaan d'ina ke kawo min abincin da kaya. Shi ne maman shi ta d'auke min shi ta kai shi wani waje a mota. Wajan shi na ke so a kai ni amma babu wanda ya ke son kai ni". Ta k'arisa maganar ta re da fashewa da kuka. "Alhamdulillah! Kandala a she ki na da rabo a duniya. Lallai idan na kai wannan zuk'ek'iyar yarinyar nan gidan Mai rabo na san sai sun ninka min kud'in da su ka saba ba ni. Kai Allah nagode maka". Fad'in Kandala a bayyane. "Yarinya ki na ji na? ki kwantar da hankalin ki, ni nan Kandala shugabar dinlalan Saminaka zan kai ki wajan Hadin d'in ki". "Ni ba Hadin na ce mi ki ba, Hadaan sunan sa. Kuma dagaske ki ke za ki kai ni wajan sa?". "Eh kwarai dagaske. Na san shi ai, d'an makwafciya ta ce ai. Amma yanzu bai k'asar, ya je karatu wani k'asa. Idan har za ki yi duk abunda na ce ki yi, zan kai ki wajan shi da kai na". "Zan yi, Allah zan yi. Mai zan yi? Mai ki ke so in yi yanzu?". Fad'in Binty. "Zan kai ki wani gida, gidan da za ki huta. Ki ci abunci mai kyau sannan Ku ma a ba ki kud'i mai yawa ki sa yi duk abunda ki ke so". Zaro idanuwa Binty ta yi ta re da fad'in, "Dagaske? Zan bi ki Allah in dai za'a rik'a ba ni abincin sau uku kuma mai dad'i". "Ai ko za'a ba ki, amma fa za ki rik'a masu aiki irin su wanke-wanke da gyaran d'aki". "To ai ni ban iya ba". Fad'in Binty. "Kar ki damu, za'a ko ya miki. Yanzu dai zo mu tafi ka da a kai wato". Kandala ta fad'a ta re da kamo hannun Binty su ka koma in da Basira ta ke tsaye. "To annamimiya, ta Allah ba taki ba, ga shi na sa mo yarinyar da za ta maye gurbin ki. Mu je na aje ki gidan Datu na kai y'ar albarkan nan gidan Alhaji Usman Mai Rabo tun da ke ba ki san alkhairi ba. Shegiya mai kan kwankwalati". Kandala ta fad'a ta na tura k'eyar Basira gaba. Cak Binty ta tsaya ta na kallon Kaka da ke gaban su shi ma ya na kallon cikin idanunta wanda ke cike da hawaye. "Binty dan Allah! Dan Allah ka da ki bi ta, yanzu ba ni da ikon taimakon ki, Iyayah mahaifiya gare ni ta gina wa ni katanga tsakanin mu. Ba ni da ikon taimakon ki yanzu. Dan Allah ka da ki bi su ki bi yo ni na mai da asalin in da ki ka fara rayuwa wa to kan bola. Dan Allah Binty kar ki ce a'a". Kaka ya fad'i haka hawaye na ziraro masa. Hakana Binty ta ji ita ma hawayan na zirarowa daga idanunta. Shafa fuskan kaka ta yi ta re da goge hawayan da ke zubowa daga idanun na sa ta ce, "Ka yi hak'uri kaka, amma ba zan bi ka ba. Ban san ko ma wa wannan duniyar. Dan Allah kaka ka bar ni na bi ta. Ba na so na bi ka". "Ba zan miki tilas ba Binty, amma idan so samu ne ki bi ni in kai ki wani duniyar da ban. Mutane ba su da tausayi, ba sa jin k'an way'anda su ke k'ark'ashin su. Maciya amana ne su. Dan ki yarda da wannan tsohon da ke gaban ki". "A'a ni bazan bi ka ba, dan Allah ka matsa min a hanya. Zan bi ta, ita na ke son bi". Binty ta fad'a ta na kuka. Kandala tsaye ta yi ta na kallon Binty ci ke da mamaki. Domin ba kin ta ne kawai ke motsi sai kuma hawayan da ke zubowa daga idanunta. "Lafiya ke kuwa ki kai tsaye ki na ta kuka haka? Ko kin fasa bi na ne in kai ki wajan Hadin d'in na ki da ki ke son ga ni?". "A'a ban fasa ba". Binty tai saurin fad'a ta re da yin ga ba ta wuce kaka da ke kallon ta ya na girgiza mata kai. Juyowa ta yi ta na kallon kakan. Wani irin zaro idanuwa ta yi sakamakon ganin Kandala da Basira sun bi ta jikin Kaka sun wuce. Za ta yi magana ta ji Ba kin ta ya mata nauyi. Kaka kuwa cewa ya yi, "Shikenan Binty, sai wani jik'on. Allah ya tsare ki da tsarewar sa". Ya na ga ma fad'in haka b'at ya b'ace. Sosai Binty ta ke son ta yi magana, amma ba kin ta ya mata nauyi. Sosai ta ke jin ba dad'i ta re da kewar Kaka. Haka ta yi ta bin Kandala zugui-zugui har su ka samu taxi su ka hau. Tafiya su kai sosai kafin su ka zo wani unguwan marasa k'arfi. Domin kuwa in da su ka b'aro unguwa ce na masu hannu da shuni. Wannan unguwa Ku ma da su ka zo yanzu, unguwar ya Ku bayi ne. Wa ni madaidaicin gida su ka shiga mai d'auke da d'akuna guda shidda ciki da parlour-parlour. Datu ce ta fito hannunta d'auke da tsintsiyar kwa-kwa ta na mitar ba ta dad'e da sharar tsakar gidan ba har an b'ata. D'ago kan da za ta yi ta sauke idanuwan ta a kan Kandala. "In ce dai lafiya Kandala na gan ki tafe da Basira da Kuma wanna kyakkyawar y'a haka? Ina ki ka sa mo ta?". Fad'in Datu wacce ta yar da tsintsiyar hannunta ta na k'ara k'arewa Binty kallo. "Hmm Datu ke dai bari. Wannan magana ce mai tsayi. Yanzu dai na kawo ma ki Basira ta zauna a nan don yanzu ko ma wa zan yi na kai wannan kyakkyawar yarinya gidan Alhaji Usman Mai Rabo, ita za ta mate gurbin Basirar. Sauran labarin sai na dawo ka da wata ta riga ni. Amma kin ga wannan y'ar iskan, ta so tai mana asara babba wallahi. Ba ri dai in je in dawo za ki sha labari". Fad'in Kandala ta re da aikawa Basira da harara har da rankwashi a tsakiyar ka sai da Basiran ta da fe kan ta. "Kash! Kin san hali na Kandala wajan san labari. Dan Allah ki d'an so ma fesa min ka min ki dawo". Fad'in Datu. "Kai, ai kin ga matsalata da ke kenan. Na ce mi ki sauri na ke yi, sai ka ce zan gudu. Ke dai bari na je na dawo". Fad'in Kandala ta re da ka ma hannun Binty su ka juya. "Dan Allah kar ki wani wajan, don wallahi ko fitan da nai niyya na fasa, ina nan ina jiran ki". "Ba matsala sai na dawo". Fad'in Kandala ta re da barin gidan. Tafiya su kai kusan na kimanin mintuna talatin ka na su ka iso wani katafaran unguwa da ke da gidaje iri d'aya. Fenti ne kawai ya ban-banta. Fad'in tsaruwar yanayin unguwar da gidan wajan b'ata ba ki ne. Daga gyefan dama zuwa na hagu, duk tsarin ginin gidajan iri d'aya ne. Gida na tsakiya da ke gyefan hagu su ka nufa. Kwankwasawa Kandala ta yi ta re da d'an ja da baya. Wani soja ne ya bud'e k'aramar k'ofar k'atuwar gate d'in ta re da fad'in, "Who's that? Who are u looking for? Who u wan see?". Cike da muzurai sojan ya fad'a kamar wanda ya ga suspect. "N...na mie who de bring people for Alhaji wife to wash da kuma sauran gyaran gida to her". Da kyar Kandala ta iya had'a broken d'in, shi zaman bariki ne ya sa har ta iya shi. Kasancewar Kandala ta yi sana'a Kala-kala har da su sai da abincin a tasha. Ku ma ta yi zaman tafa. K'awarta da ta kwaso k'anjamau ne ya tsorata ta dai na wannan harkan ta koma d'auko y'ay'an mutane daga k'auye ta na kawo su aikatau. Sojan nan ya shiga k'are ma ta kallo, duk da kuwa ya san ta, kasancewar ba yau ba ne rana ta farko ko na biyu ba da zuwan ta gidan. Mai da kallon sa ya yi zuwa ga Binty da ke tsaya ta na cin k'unban hannunta. "Don't tell me say u bring this pretty girl to come and work here?". Fad'in wannan sojan ya na kallon Binty da ta zuba masu idanu domin Sam ba ta jin abunda su ke fad'i. "Na madam se me ka bring her to do work for her pikin". Fad'in Kandala. "Her pikin? Are you mad. You no say da guy na ashawo. Hin dey spoil peoples daughter. And na you dey bring them. God go punish you and madam pikin. God they see everything. If na your pikin will you allow her to come and work here? You'r selfish woman. God go punish you. And lemi warn you, if you tell hajiya watin a say, wallahi a go remove one of your leg that you uzam bring peoples daughters. Enter before I shoot you u with my gun". Da sauri Kandala ta ka ma hannun Binty su ka shige cikin gidan. Ban da gate d'in farko sun wuce gate kusan biyar ka min su isa ainahin gate d'in da zai sadaka da cikin gidan. Hanci, baki, ido Binty ta saki ta na k'arewa wannan makeken gida da su ka shigo cike da k'auyan ci. Ga ma'aikata nan ta ko ina. Masu gyaran fulawa daban, masu bai wa fulawan daban. Masu kula da tantabaru daban, mata y'an aiki kuwa sun kai goma. Ka'totan gida mai d'auke da part part kusan goma. A gate na shida ne ma'aikatan gidan maza su ke da quarter d'in su. Su kuma mata quarter d'in su ya na cikin asalin gidan. Hakan tsarin mai gidan ne wato Alhaji Usman Mai Rabo. Wani shashi su ka fara nufa wanda shine shashin uwargidan Alhaji Usman Mai Nasara, auran saurayi da budurwa kenan tun bai da ko sisi. Zaune ta ke a kan d'aya daga cikin tantsama tantsaman kujerun d'akin. Sanye ta ke cikin wata doguwar rigar shadda wanda ya amshi jikinta. A k'allah za ta kai shekaru amsin a duniya, amma sam jikinta bai nuna hakan ba saboda kyawun jikinta da kuma hutu da gyara da jikin ke samu. Kyakykyawa ce sosai kuma fara tas. A ba kin ta akwai hak'orin maka har guda biyu gyefe da gyefe kalar golden wanda ke k'ara haskaka fararan hak'oran ta. Waya ce a hannunta ta na karanta Alqur'ani mai girma a cikin wayar. Sallama su ka yi, sai da Hajiya Na'ima ta kai aya sannan ta rufe wayar ta re da amsa sallamar ta na mai kallon bakin k'ofar. Shigowa Kandala ta yi ta re da zubewa a k'asa ta na gaida uwargida a wajan Alhaji Usman. Gyefe guda kuma ta na tsungulin k'afar Binty a kan ita ma ta gaida hajiyan, amma inaa Binty ba ta san ma ta na yi ba. Domin ta shagala da kallon tsararran d'akin da ya kusa tsayar da numfashin ta. "Kandala ya gida? D'azu kuwa idan ba kunne na ba ne, na ji kamar Fasila ta na fad'a min kin zo d'azu gaishe ni, ni kuma ina sallah". "Eh kwarai ni ce Hajiya. Na zo ki na sallah shi ya sa na tafi". Fad'in Kandala. Jinjina kai Hajiya Na'ima ta yi ta re da mai da kallon ta izuwa ga Binty da a kallon farko ta ji ta shiga ran ta, ta ce, "Kandala wannan kyakkyawar yarinya fa?". K'ara gyara zama Kandala ta yi ta re da fad'in, "Hajiya Mansura ce ta ce na kawo mata wata y'ar aikin wacce na kawo watan ba ya ba ta yin abunda ya da ce, shi ne na kawo wannan d'in". "Ita d'in wannan y'ar wacece? Kuma ki na da tabbacin za ta iya abunda wancan d'in ta kasa?". Hajiya Na'ima ta jeho mata tambaya ta re da tsare ta da idanuwa. "Em..ehyyy.. Ita d'in yar k'ani na ce a can Saminaka". Fad'in Kandala ci ke da in'ina. Haka nan Hajiya Na'ima ta ji ba ta gam su da zan can da Kandala ta fad'i ba. Musamman da ta ji ta na in'ina. "Me ye sunan ta?". Hajiya ta sa ke tambayan ta ta na mai tsare ta da idanuwa. A nan ne kuma gaban Kandala ya fad'i, domin Sam ba ta san sunan yarinyar ba. Ta man ta shaf ta tambaye ta. Tab'o Binty ta yi ta re da fad'in, "Ke wai ba ki iya gaisuwa ba ne? Ki gaishe da Hajiya mana". Sai a lokacin hankalin Binty ya dawo. Hajiya ta kalla ta re da fad'in, "Ina wuni?". Da ma Hamdan ya ko ya mata yadda ake gaisuwa. "Lafiya k'alau Beauty, ki zauna mana". Binty kuwa wani dad'i ne ya kusan sumar da ita saboda sunan da Hajiyan ta ki ra ta da shi. Kallon Kandala ta yi ta re da fad'in, "Kin ga ni, ita ma ta san Hadaan. Ga shi ta ki da ni da irin sunan da ya ke kira na da shi". Murmushi Hajiya Na'ima ta yi ta re da fad'in, "Yaya sunan ki y'an mata?". "Binty y'ar bola". Binty ta fad'a ta na murmushi. Kallon Kandala Hajiya ta yi, ka na ta mai da kallon ta izuwa ga Bintyn ta re da fad'in, "Binty 'yar bola kuma?". Kamin Binty tai k'arin bayani caraf Kandala ta amshe ta re da fad'in, "Binty ai a kwai shirme. A can garin mu ne fa ake kiran ta da haka kasancewar ba ta k'aunar wanka kullum dak'an-dak'an za ki ganta. Shi ne yara su ke kiran ta da Binty y'ar bola. Shine fa duk wanda ya tambayeta sunan ta sai ta ce Binty y'ar bola. Amma Sunan ta Binty ne". Dariya Hajiya Na'ima ta yi ta re da fad'in, "Duk yarinta ne za ta bari, wata rana ma idan aka ce tai kwana d'aya ba wanka ba za ta iya ba. Amma fa ni da ba din kin ce Mansura ta ce ki kai mata ita ba, ai da na ce ki bar min ita a waje na". "Ai ba matsala Hajiya, idan ki na son ta ki karb'e ta, idan ya so na kawo mata wata. Ai duk d'aya ne da ke da ita". Fad'in Kandala kamar mutuniyar kirki. "A'a ba za ai haka ba. Ai tun da ta riga da ta mi ki magana, ki kai mata ita kawai. Ni da ma ba y'an aiki na ke nai ma ba. Kawai yarinyar ce ta shiga rai na". Fad'in Hajiya Na'ima. "Wallahi Hajiya ba matsala ki d'auke ta kawai". Shuru Hajiya ta yi ta na wani tunani. Tabbas idan har ta ba ri Hajiya Mansura ta karb'i wannan yarinya to ba bu makawa d'an ta Suhail sai ya lalata ta kamar yarda ya saba lalata y'ay'an jama'a uwar sa ba d'aure masa gindi. "To ki bar min ita". Fad'in Hajiya Na'ima. Hankad'a labulan d'akin ta yi ta re da fad'in, "Wannan k'aya ne wallahi. Yarinya ni na saka a kawo min ita, kuma babu wacce ta isa ta karb'e ta idan ba ni ba". *HMMM AKWAI FA CAKWAKIYA.* *ASSALAMU ALAIKUM READERS, GA NI NA ZO MA KU DA SABON LITTAFI NA MAI SUNA A SAMA, WANDA YA ZO DA ZAFI-ZAFIN SA, KUMA NA TABBATA ZA KU JI DAD'IN SA. BA ZAN CI KA KU DA SURUTU BA, KAWAI KU BI NI A FREE PAGES, KU DA KAN KU ZA KU GA NE BOOK D'IN NA DABAN NE. KAWAI KU NU NA MIN ONE LOVE WAJAN SIYAN BOOK D'IN AKAN FARASHI AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA:* *FREE PAGES SUN K'ARE* *Normal group shine mutum zai bi ya 500 idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300.* *VIP kuma 1000 ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700.* *MUTANAN NIGER KUMA ZA SU BI YA KAMAR HAKA*: *Normal group shine mutum zai bi ya 500F idan ka ti ne, idan kuma ta account ne 300F.* *VIP kuma 1000F ne idan kati ne. Idan kuma ta account ne 700F.* *EVIDENCE OF PAYMENT 08128755583* *IDAN HAR BA KI KARANTA BOOK D'IN NAN BA WALLAHI KIN YI MISSING.* *DAN GIRMAN UBAN GIJIN HALITTA IDAN HAR KIN SAN ZA KI FITAR MIN DA BOOK, KA DA KI SA YA, WALLAHI BA NA BUK'ATAR KUD'IN KI. KI TAIMAKA DAN ALLAH* *MATAR SAYYADEE* 🌹 *15-16*🌹 Wani kanne ido d'aya Hajiya Na'ima ta yi ta na kallon Hajiya Mansura wacce ita ce matar Alhaji Usman Mai Rabo ta uku, wa to ta tsakiya. "Ya ki ke haushi ke ba kare ba Mansura?". Hajiya Na'ima ta fad'i ta na sakin wani shu'umin murmushi. Hajiya Mansura kuwa kallon Hajiya Na'ima ta yi, ta kuma mai da du ban ta ga Kandala da tu ni ta jik'e da zufa sai sa ka hannunta ta ke ta na sharewa. Sa ke mai da du ban ta tai izuwa Hajiya Na'ima ta re da fad'in, "Ni ki ke dangantawa da kare a gaban wad'an nan fak'iran". "You made me sai that. Ba yan kin fi kowa sanin yadda na tsani ihu a kai na. Ku ma na sha mi ki warning a kan shigo min d'aki ba bu sallama. Yarinya ku ma na hana, ba zan ba ki ita ba. Ta sa mo mi ki wata. Wannan ta wa ce". Fad'in Hajiya Na'ima ta na kallon cikin idanun Hajiya Mansura da ke jin kamar tai bindiga. "Mu zu ba mu gani". Fad'in Hajiya Mansura ta re da watsawa Kandala wa ni mummunar kallo ka na ta nufi k'ofa. Sai da ta kai ba kin k'ofa ka na ta ce juyo ta kalli Kandala ta re da fad'in, "Ki sa me ni yanzu a sashe na". Ta na gama fad'in haka ta wuce fuuu. Kallon ta Hajiya Na'ima ta yi ta re da mik'ewa daga kan kujeran da ta ke ta ce, "Ki jira ni yanzu ina zuwa". Ta na gama fad'in haka tai hanyar stairs. In ten minutes ta dawo parlourn hannun ta rik'e da wani babban ledan AYK da ke d'auke da tambarin fiffiken d'awisu a jiki. Atampopi ne guda uku masu tsada da kuma turare da kuma duba d'ari a ciki ta mik'awa Kandala ta re da fad'in, "Za ki iya tafiya yanzu". K'ara tankwashe k'afa ta yi za ta fara koro godiya Hajiya Na'ima ta d'aga mata hannu ta re da fad'in, "Ba na son jin komai, kawai ta shi ki tafi, idan ina buk'atar ki zan nai me ki". Mik'ewa Kandala ta yi ta re da nufar k'ofa. Da sauri Binty da tun d'azu sai k'ara k'arewa D'akin kallo ta ke yi ta bi ba yan ta ta re da fad'in, "Ina za ki ta fi ki bar ni kuma? Ina Hadaan d'in?". Kallon Kandala Hajiya Na'ima ta yi ta re da fad'in, "Zan haura sama, idan kun ga ma, ki turo min ita sama". "To Hajiya in sha Allah, Allah ya k'ara girma". Cikin zuciya Hajiya Na'ima ta furta ameen ta re da hayewa sama. Kallon ta Binty Kandala ta yi ta re da b'ata rai sosai ka na ta ce, "Kin man ta abunda na ce mi ki kenan? Ba na ce mi ki Hadaan ya je k'asar waje karatu ba. Kin yi alk'awari za ki yi duk abunda na ce ki yi. Hakan shi zai sa na kawo mi ki Hadin d'in ki. Amma idan har za ki rik'a bijirewa umarni na, to wallahi ba zan ka ko mi ki Hadin d'in ba. Ku ma daga yau duk wanda ya tambayi sunan ki, ka da ki sa ke ki k'ara ce wa Binty y'ar bola. Sunan ki Binty kawai. Kuma idan a ka tambaye ki ni wacece a wajan ki, ki ce ni baabar ki ce. Idan kuma a ka tambaye ki sunan garin ku ki ce Saminaka, sunan mahaifin ki kuma ki ce Hashimu mai goro, kin ji abunda na fad'a miki?". Kandala ta fad'i ta re da rik'e kunnanta. Gyad'a kai Binty ta yi ta re da fad'in, "Ke baaba ta ce, kuma sunan garin mu Saminaka, sannan sunan babana Hashimu mai goro. Na rik'e ai". Binty ta fad'i ta na murmushi. "Yauwa y'ar albarka. Haka za ki rik'a cewa duk a ka tambaye ki. Idan ki kai haka zan kai ki wajan Hadin cikin k'ank'anin lokaci" "To Baaba. Yan zu yau she za ki dawo?". Fad'in Binty. "Ba zan jima ba kin ji, ki yi duk abunda aka umarce ki da ki yi ban da shirme da wasa kin ji?". "To baaba zan yi duk abunda aka ce in yi tun da za ki kai ni wajan Hadaan". "Yauwa to yanzu abunda na ke so da ke shi ne ki bi can, in da ki ka ga Hajiya ta bi, za ta fad'a ma ki duk abubuwan da za ki rik'a yi a gidan nan kin ji?". Fad'in Kandala. Kallan stairs d'in Binty ta yi ka na ta mai da duban ta ga Kandala ta re da fad'in, "Yanzu can zan hau?". Ta fad'i hakan ne ta na nu na stairs d'in da hannunta. "Eh. Maza ki je ka da ta ga kin dad'e. Sai na da ke dawowa". Fad'in Kandala ta re da nufa hanyar waje ko waiwaye ba ta sa ke ba ta fice daga sasan gaba d'aya. Binty kuwa ajiyar zuciya ta sauke ta re da nufar stairs d'in da ke da zigzag kamar maciji. K'afarta ta fara d'aurawa guda d'aya, ka na ta d'ago d'ayan da k'er k'afafuwan na ta na wani irin rawa kamar za su tsinke. A step na biyu Binty ta kakare jikinta na b'ari. K'arshe dai crawling ta ko ma yi kamar yarinyar da ke koyan rarrafe. Ta na yi ta na hawaye. Fasila ce ta fito daga d'akin Hajiya Na'ima hannunta d'auke da kwandon kayan wanki za ta kai washing room, turus ta tsaya ta na kallon Binty da ke rarrafe ta re da hawaye shab'e-shab'e ta na hawowa sama. Dariya ce ta kufcewa Fasilan har laundry basket d'in hannunta ya kusa kufcewa ya fad'i tai saurin taro sa. "Lafiya ki ke rarrafe haka? Ba ki tab'a hawa irin wannan ba ne?". Fasila ta tambaya ta na dariya har da rik'e ciki. "Ni ban tab'a ganin irin wannan ba, wanda na tab'a ga ni bai da kwana-kwana haka, kuma ko shi d'in ma ban tab'a hawa ba". Fad'in Binty ta na hawaye. "Ta shi ki yi tafiya da k'afafun ki, ba bu abunda zai sa me ki, kin ji?". "Na k'i ban ta shi Allah! Salan in zurma na fad'a na mutu. Ni tsoro ma na ke ka da k'afata ta zurma ciki". Dariya Fasila ta k'ara bushewa da shi ta re da fad'in, "Ko irin ki da wad'anda su ka fi ki guda hamsin su ka ba za su zurma ba ba re Ku ma ke y'ar tatsitsiya da ke. Dallah ta shi ki yi tafiya da k'afafun ki ka da ki ba da mu". Fad'in Fasila. "Mai ke faruwa a wajan Fasila?". Hajiya Na'ima da fitowar ta kenan daga d'aki ta ji muryan Fasilan ta na b'ab'b'aka dariya. Saurin natsuwa Fasila ta yi ta re da sunkuyar da kan ta, ka na ta ce, "Wannan yarinyar ce ke rarrafe, wai tsoran ta ka wa ta ke yi". Kallon Binty da ke tsugunne a k'asa Hajiya Na'ima ta yi ta re da k'arisawa in da ta ke ta ka mo ta su ka k'arisa hayewa. "Har baabar ta ki ta wuce?". Hajiya ta fad'a ta na k'arewa Binty kallon. Ga dai rigar jikinta mai kyau da tsada sai dai duk ya yi butu-buti har da miya-miya a gaban rigar. "Eh yan zun nan ta wuce ai". Binty ta fa'da ta re da ju ya wa ta na kallon stairs d'in da ta hauro. "To mu je ki huta ki ci abinci, anjima zan fad'a mi ki abubuwan da za ki ri'ka yi". "To. Da ma yunwa na ke ji sosai". Fad'in Binty. Gaba Hajiya Na'ima ta yi, Binty na bi ye da ita a ba ya har zuwa wani tsararran k'aton parlourn da ke sama. "Zauna a nan, ina zuwa". Hajiya Na'ima ta fad'a ta re da bin wani corridorn da zai sa da ta da bedroom d'in ta. Za ma Binty ta yi a kan tamfatsetsan kujeran mai d'an karan laushi. Can ku ma ta mik'e ta na ta isa wajan labule ta na kallon su ta re da sha fa su. "Ke Fasila shafa min dan Allah. Na ga wannan kyakkyawar yarinya da Kandala ta ka wo nan wajan Hajiya Babba ta bar ta. Ina ce Hajiyan tsakiya ce ta sa a can zo ta da Basira?". Fad'in Jummalo da ke ciro kaya a cikin washing machine. "To uwar gulma, ni ma ban sa ni ba. Ki je ki tambaye ta mana, ai kin san hanyar d'akin nata ai". Fad'in Fasila ta re da maka mata harara. Dafe k'irji Jummalo ta yi ta re da fad'in, "In mutu maza su kai ni ba mata ba. Ko ke sai da ki ka kwashi shekaru bakwai ka min Hajiya Babba ta fara ba ri ki ka fara haurawa sama, shi ma iya kacin ki d'akin aje kayan wanki ki fito da su ki kawo su nan a wanke, balle ni da zuwan jiya-jiya. Ko fa shekara ban yi ba a gidan nan. Satin gaba dai zan cike shekara guda. "Hmm to ai kuwa wannan kyakkyawar yarinya dai da sa'a ta zo, domin kuwa har babban parlourta ta shiga da ita. Zo ki ga yadda mamaki ya kusa kashe ni". Fad'in Fasila ta na kallon Jummalo da ta saki baki da hanci ta na kallon ta. "Haba dai Fasila? Hajiyan ce ta kai ta har parlourn ta wanda daga Alhaji sai y'ay'anta ke shiga?". "Yadda ki ka ji". Fad'in Fasila ta re da ficewa daga washing room d'in. "Kan bura uban caaaan! Lallai wannan yarinya kin zo da sa'a, duk da ya ke Hajiya ta kirki ce, sai dai ta na da mugun rashin yarda ne. Ko in ce duka matan Alhaji ha ka su ke. To wai ma ni ina ruwa na". Fad'in Jummalo ta re da cigaba da kwashe kayan cikin washing machine d'in. "Oga Solomon, watin happen? You no dey talk since dat fat human wey hold that pretty girl hand pass here.". "Mtsww! Baba Haruna, Na something wey they kill me in this house. The thing way Alhaji son de so is no good, and his mother no everything way him de do. Yesternight if you see how he come back from club, ibi like say he wan kill me with his car. He horn like he wan remove my ear. He's drunk and na his baby who de drive the car. Mtsw no be that one de worry sef. Na that pretty girl who that stupid woman bring earlier, and she tell me say na madam se make she bring her to do work for that stupid child of her. I pitty for that cikili girl. I know that stupid he goat go spoil her, da boy na real ashawo. Every day him de bring three to four women to sleep with him. Imaging, this cikili pikin that is not up to twenty years. Chaiii! God they see everything". Oga Solomon ya fad'a cike da tausayi da jimami. "Huh! Mtsw. No be only you that thing they worry. Even me sef, I they pity for that girl. I cannot count the maids who that stupid little brat rape in this house. Even the girl that was fire, what's that her name? I can't remember". Baban Haruna ya fad'a ya na kallon Oga Solomon. "Sekina. Ohhh da girl is very cam". Oga Solomon ya fad'a. "Yauwa, dat her name, Sakina. He impregnate her, thats the reason why Hajiya Mansura fired her". "What? When did that happen". Oga Solomon ya fad'a da k'arfi. "Hey, ni fa matsala ta da kai kenan. Ba ka iya magana a hankali ba, yanzu idan wa ni yaji fa? Ku ma kasan dai akwai munafukai y'an kai report". Ajiyar zuciya Oga Solomon ya yi ta re da fad'in, "Mtsw, I'm sorry baba Haruna, I was shoked that's why. But the thing way Hajiya Mansora de do is not fair atol. Alhaji no nothing about this". Zaro idanuwa Baban Haruna ya yi ta re da fad'in, "I swear him no no everything about this. Alhaji na goodman. I swear if he no wating his wife and his son de do him go furnish them, he will send Hajiya Mansura to her parent house". "I pray may him come know everything way they happen in this house. I pray may hin send that old bitch to her parent house". Tab'a shi da k'afa Baban Haruna ya yi ta re da nu na masa D'an kwairo da ke ta ho wa wajan su. "An zauna ana sana'ar da aka saba kenan". Fad'in d'an kwairo ya na hararar su. Ba bu wanda ya kula su a cikin su. Oga Solomon ne ya bud'e masa k'aramar k'ofa kasancewar fi ta zai yi". "This dan kwero na original amebo". Fad'in Oga Solomon cikin rad'a. "I never see amebo before like him". Fad'in Baban Haruna ya na dariya ta re da mik'awa Oga Solomon hannu su ka tafa. Bubu abunda ka ke ga ni a d'akin sai hayak'in shi-sha da ya turnik'e d'akin kamar d'akin boko. Sai k'arar kid'an da ke ta shi kamar gidan casu. Zuk'ar shi-shan ya ke yi cike da kwarewa ya na fesar da hayak'i. Y'an mata ne guda hud'u. D'aya ta na wajan kan sa ta na masa massage a kansa. D'aya kuma ta na shashshafa jikinsa. D'aya kuma ta na mammatsa masa k'afarsa. D'ayar ta karshe kuma ta na jujjuya jikinta a gaban sa. Gyefe guda kuma cuncurundon abokansa ne su takwas ko wanne da shi-sha port da ya ji mix da kayan ma ye a ciki. Biyu daga cikin abokan sa kuma su na cikin d'aki d'aya da y'an matansu su na amfani da su. "Hey Suhail, har yanzu fa ba'a kawo ma na abinci ba, ko y'an aikin gidan ku sun k'are ne?". Wani bu'de idanu Suhail ya yi ta re da kulle su, ka na ya lallubi wayarsa da ke kan center table d'in gyefar kujeran da ya ke kai. Dialing Sweet mom ya yi ta re da karawa a kunnan sa. "Ke saboda ke bak'ar annamimiya ce, munafuka shi ne ki ka kai mata y'ar aikin da na ce ki ka wo min ko? To ko ki je duk yadda za ki yi ki maido ta waje na, ko kuma wallahi zaman abuja ya ga gare ki wallahi". Fad'in Hajiya Mansura kamar za ta kwad'awa Kandala ma ri. "Hajiya ki min rai dan girman uban giji, wallahi ke nai niyyar ka wo ma wa ita shine ta ce na bar mata ita ke kuma na sa mo ma ki wata. Dan Allah ki yi hak'uri ki ba no zuwa jibi wallahi zan sa mo mi ki wacce ta fi wannan girma da ko mai, wacce za ta iya duk ayyukan da za ki saka ta". Fad'in Kandala. "Za ki rufan ba ki ko sai na kwad'a mi ki mari. Ita wancan yarinyar na ke so. Duk yadda za ki yi, ke ki ka sani". Ka min Kandala ta k'ara magana, wayar Hajiya Mansura yai k'ara. D'aukar wayar ta yi a kan kujera, ganin mai kiran wayar ne ya sa Hajiya Mansura ta sallami Kandala da hannu ta re da d'aga kiran ta ce, "Son ya aka yi? Wani abu ka ke buk'ata?". Kasancewar Suhail ya tsumu da shaye-shaye, muryan sa har fashewa ta yi, idan yai magana za ka d'auka gardi ne d'an shekaru talatin, nan kuwa ko shekaru ashirin bai yi ba. "Mom, we need food right now. Amma kar ki turo min wannan y'ar iskan yarinyar". "Ka da ka damu son, ai tuni na kore ta yau d'in nan. Har na sa an kawo maka wata ma. Kyakkyawa da ita, wacce za ta iya duk aikin da ka saka ta. Ba ma za ta wuce shekaru goma ba. Sai dai fa wancan matar ta yi ma na overtaking". Yamutsa fuska ya yi ta re da fad'in, "Wacece wannan a cikin gidan nan da za ta mi ki overtaking ki na kallon ta kuma". "Wacece kuwa ban da matar uban ka mai isa wai ita jinin sarauta". "To ina ruwa na da jinin sarautar ta. Ko da a ce sarkin ne uban ta, ya min ba kyale shi zan ba. Don haka a karb'o yarinyar nan ko ta halin k'ak'a, ku ma a kawo min abinci in five minutes". Suhail na ga ma fad'in haka ya datse kiran ta re da kwantar da kan shi a jikin kujera. Don har hankalin shi ya tashi da ya ji an samu yarinyar y'ar shekaru goma. Lallai ashe zai more. **********Hannun ta d'auke da faranti ta dawo parlourn. Murmushi ta yi saboda ganin Binty da ke wajan labule sai shafawa ta ke yi. Aje farantin ta yi a kan center carpet d'in da ke shimfid'e a parlour. K'arar ajiye farantin ne ya dawo da hankalin Binty wajan Hajiya Na'ima da ke tsaye ta na kallon ta. "Dawo nan ki zauna kici abinci". Fad'in Hajiya Na'ima ta re da nu na mata abincin. K'arasowa ta yi ta re da zama a k'asa ka na ta bud'e plate d'in saman da aka rufe abincin. Zaro idanuwa Binty ta yi ta na kallon farfesun kaza da ya sha kayan lambu harda irish poteto a ciki ta re da fad'in, "Duka wannan nawa ne?". Ta fad'i haka ne ta na kallon Hajiya Na'ima da ita ma kallon na ta ta ke yi. "Eh duk na ki ne ke d'aya. Ciki sai ya ishe ki, idan ba ki k'oshi ba ki yi min magana zan k'aro mi ki". Fad'in Hajiya Na'ima. "Kai amma nagode mi ki sosai. Gaskiya garin nan Ku na da kirki, ku na ba wa mutane abincin ma su dad'i sosai". Ta fad'i hakane ta re da d'aukar tsokar cinyar kaza ta yaga". "Wayyiwooooo dad'i kashe ni. Wannan na ma da dad'i ya ke. Dan Allah ki rik'a ba ni kullum zan rik'a miki duk abunda ki ke so". Binty ta fad'a ta na karkad'a kan ta. Girgiza kai Hajiya Na'ima ta yi ta re da murmushi ta yi hanyar da zai sa da ta da bedroom d'in ta. Sai da Binty ta cinye farfesun rabin kazan nan da Irish d'in nan tas. Ka na ta kafa kai ta shanye roman ta re da sud'e hannunta ta d'auki goran ruwa ta kafa baki ta sha fiye da rabi, ka na ta ajiye ta re da sakin gyatsa ta jingina da kujeran. Cikin k'ank'anin lokaci bacci ya yi awon gaba da ita. *DAN GIRMAN UBANGIJI KA DA KI FITAR MIN DA BOOK. IDAN KIN SAN ZA KI FITAR DAN ALLAH KI MIN MAGANA NA MAYAR MI KI DA KUD'IN KI* *DAN ALLAH IDAN KIN GA NI BA KI SIYA BA KA DA KI KARANTA KU MA KAR KI YI SHARING, KI NAI MI NUMBER 08128755583 KI SI YA SABODA KI KARANTA DA GUMIN KI BA NA SATA BA*. *_BA NA TYPING SATURDAY AND SUNDAY_* *MATAR SAYYADEE* 🌹 *17-18*🌹 K'arfe biyu da rabi na rana wata y'ar budurwa wacce ba za ta wuce 13-14 years ba ta shigo d'akin sanye da uniform dark purple suit da skirt shi ma dark blue. Sai rigar ciki da ta kasance light purple. A jikin gaban suit d'in akwai logo na makaranta mai d'auke da tambarin makarantar da kuma logon su. Sai baby hijjab dai-dai wuyanta shi ma da ya kasance dark purple. Jakarta fashion mai kyau shi ma dark sagale a kafad'ar ta. Ba k'aramin kyau kayan su ka mata ba. Tsaye ta yi a kan Binty da ke ta sharar bacci gaban rigar nan ya yi biji-biji da roman farfesun kazan da ta gama shi. "What a beautiful creature!". Fad'in Fanan da ta d'an duk'o ta na shafa gashin kan Binty don ta tabbar shin na ta ne ko kuwa attachment a ka sa ka mata. Murmushi Binty sabod mafarkin da ta ke yi ta re da mirginawa k'afarta ya sauka akan plate d'in da ta gama cin abincin. Ita kuwa Fanan mutuwar tsaye ta yi saboda wa ni mugun kyau da murmushi nan ya k'ara fad'ad'a kyawun fuskanta sakamakon dimples d'in ta da ya lob'a. Ko ma wa side d'in da ta juya Fanan ta yi ta re da tsugunnawa ta na kallon fuskan Binty. "Ke kyakkyawa ce". Fanan d'in ta fad'a ta na tab'a kumatun ta in da ya lob'a. "Idan kin ga ma k'are mata kallon, sai ki wuce ki je ki cire uniform ki yi wanka ki zo ki ci abinci". Fad'in Hajiya Na'ima da ta fito hannunta rik'e da waya ta na dannawa. Ta shi Fanan ta yi ta re da isa wajan mahaifiyarta ta re da rungume ta ta ce, "Anna I'm home". Fanan ta fad'a ta re da sakin Hajiya Na'ima ta mai da kallon ta izuwa ga Binty da har yanzu ke bacci ta ce, "`D'un `b'ingum umoy'e? (Wa cece wancan?)". "O inkesse mu'aiki. Unangai taimakima I aaki. (Sabuwar y'ar aiki ce, za ta rik'a taimaka maki da aiki.)". "B'ingil gehil igillab'i. (Yarinyar kyakkyawa ce) muheb'b'i higo munangaimi labari imakko. (Na samu k'awar da za mu rik'a labari da ita). Anna gad'amu tu makaranta amin. Muhwalloimu to makaranta amil onni. (Anna ki saka ta a makarantar mu. Zan nu na wa y'an makarantar mu ita.)". Fad'in Fanan da harcan fulatanci. "Ta wan nu muwad'aimu tu makaranta d'um, yahu itta ka ya ma d'a gara nyama abinci. (Kar ki da mu, zan sa ta a makaranta. Je ki can za ka ya ki zo ki ci abinci)". Fad'in Hajiya Na'ima da harshan fulatanci. "Migodeki Anna imiyid'd'uma. (Nagode Anna ina son ki)". "Mimma imiyid'd'uma Fanan. (Ni ma ina son ki Fanan)". Fad'in Hajiya Na'ima ta na murmushi ta re da jin k'aunar y'ar autar ta ta. Ita kuma Fanan ta bi corridor ta wuce d'akin ta ta na jin dad'in sabuwar k'awa da aka kawo mata. K'arisawa wajan da ta ke kwance Hajiya Na'ima ta yi ta re bubbuga k'afarta a hankali. "Hadaan kai ne?". Binty ta fad'a ta re da bud'e idanuwanta a kan Hajiya Na'ima. "Au ke ce? Ashe mafarki na ke yi". Fad'in Binty ta na mitsike idanuwan ta. "Ki kira ni da Anna ba ke ba, kin ji?". Fad'in Hajiya Na'ima ta re da d'ago Bintyn ta tashi zaune. "Anna fitsari na ke ji". Binty ta fad'a ta kamar za ta yi kuka. "To ta shi mu je in kai ki d'akin Fanan sai ki yi a can har da wanka ta re da alwalama sai ki yi sallah kin ji". Hajiya Na'ima ta fad'i ta re da ruk'o hannun Binty su kai hanyar d'akin Fanan d'in. Knocking Hajiya ta yi ta re da tura k'ofar ta shiga. Babu kowa a d'akin dai k'arar ruwa da ta ke ji daga bayin. Haka ne ya tabbar ma ta da Fanan d'in ta na ci ki ta fara wanka. Binty kuwa sai bin d'akin ta ke da kallo da komai ya kasance baby pink. Ga hotunan Barbie nan a jikin bango da kuma manya manyan teddies nan a kan gad'on da shi kan shi pink colour ne har da zanin gad'on. "Zauna a nan ki jira ta fito, sai ke ma ki Shiga ki yi wankan". Fad'in Hajiya Na'ima. Ka min Binty ta ce wa ni abu Fanan ta bud'e k'ofar ta fito d'aure da towel a jikin ta. Zaro idanuwa Fanan ta yi cike da murna ta re da fad'in, "Beauty kin tashi?". Ta fad'i hakane ta re da ka mo hannun Bintyn ta zaunar da ita a ba kin gado. Binty kuwa mamaki ne ya kashe ta yadda kowa a nan garin ya san sunan ta. "Hammu d'oho kullamu nu'uwatta amfani i`bayi, sai kukkama dirkaya ma d'a uwad'a. (Ga tanan ki koya mata yadda za ta yi amfani da ba yi. Sai ki ba ta daga cikin ka yan ki ta saka). Da ra mu had'a na mu gite o`juli. (Ki sa ka ma ta idanu tai sallah)". Fad'in Hajiya Na'ima cikin harshan fullanci. "To Anna. Dussu du a`han, hunanga taka waliki? (D'aki na za ta rik'a kwana?)". Fanan ta fad'a ta na kallon Anna. "Eh, d'an nangutun kawaliki tugu`u. (Eh a nan za ku rik'a kwana ta re)". Fad'in Hajiya Na'ima. "Yauwa Anna, mihiggimmi. (Yauwa Anna haka na ke so)". Fad'in Fanan. Har Hajiya Na'ima ta kai bakin k'ofa Fanan d'in ta sa ke cewa, "Anna daga k'auye gard'a d'o? (Anna daga k'auye ta zo?)". "Eh". Shi abunda Anna ta ce ta re da ficewa daga d'akin. Ka mo hannun Binty Fanan ta yi ta re da fad'in, "Menene sunan ki? Ni suna na Fanan Usman Mai Rabo. Ke fa?". "Suna na Binty ummmm, ummm Binty.... Binty.... Yauwa, Binty Hashimu mai goro". Binty ta fad'a ta na mai jin dad'in tuno sunan da Kandala ta fad'a mata a kan duk wanda ya tambaye ta sunan mahaifin ta. "Nice name. Amma sunan ki kenan Binty ko kuwa Nick name d'in ki ne?". Fad'in Fanan. "Nee name? Menene nee name kuma?". Dariya ce ta zo wa Fanan d'in, ai kuwa ta sake shi har towel d'in jikin ya kusan za me wa. "Ba ki tab'a zuwa boko ba ne?". Fad'in Fanan. "Ni ban tab'a zuwa ba. Hadaan ne kawai ke zuwa". Fad'in Binty. "Wa ye kuma Hadaan?". Fanan ta tambaya. "Ba ki san shi ba". Binty ta ba ta amsa ta re da sa ke fad'in, "Fitsari na ke ji sosai". "Oh sorry, ta so mu je in nu na mi ki yadda za ki yi amfani da bayin". Fanan ta fad'a ta re da nufar bayin Binty na bin ta a ba ya. Kai hannu Fanan ta yi kan wani kyakkyawan panfo sai ga ruwa shaaa. Wani irin tsalle Binty ta yi ta re da ficewa daga bayin da gudu jikinta na rawa. Da gudu ita ma Fanan ta bi bayanta ta re da fad'in, "Lafiya Binty? Mai ya faru?'. "Hannu na ga kin kai a jikin irin wannan abun mai kama da panfo kawai sai na ga ruwa ya zubo. To Allah akwai dodo a cikin bayin nan". Dariya Fanan ta yi ta re da ka ma hannun Bintyn su ka ko ma ba yin. "Ki kwantar da hankalin ki babu wani dodo a cikin ba yi. Zan ko ya miki yadda a ke amfani da komai a cikin nan wajan". Sai da Fanan ta ko ya mata yadda ake amfani da komai, kasancewar Binty ta na da saurin fahimta da d'auke abu a kai, ta fahimci yadda ake amfani da bayin. Don Fanan ba ta fita ba sai da Binty ta gwada amfani da wa su abun tukun ta fita. Ko da Binty ta fito tu ni har Fanan ta gama shiryawa cikin wando pink da riga white, sai tai parking gashin ta a gyefe da pink d'in ribom, kasancewar ita d'in y'ar kwalliya ce kuma ita ma ta na da gashi ba laifi don ya zubo a kafad'arta. "Yauwa kin yi alwala?". Fanan ta tambayi Binty. "A'a ban yi ba". Binty ta ba ta amsa. "To ko ma ki je ki yi, lokacin sallah na ta wuce wa. Ba kyau wasa da sallah". Fad'in Fanan. Komawa cikin bayin ta yi ta re da d'auro alwala ko in ce shirme ka na ta dawo da'kin. Tu ni har Fanan ta fiddo ma ta da wani riga da skirt y'an kanti kalar pink da ratsin purple a jiki. Don Fanan gaba d'aya kayanta da wuya ka ga babu pink colour a jiki. Don ko a school sunan ta pinky. "Na yi alwalar". Binty ta fad'a. "Yauwa goge jikin ki sai ki shafa wannan mai d'in ki saka wad'annan kayan ki sai ki sallah ga praying mat nan na shimfid'a miki". Kallon mai d'in ta din ga yi ta re da fad'in, "To Fanan ya ake shafawa? Ban iya ba". Cike da mamaki Fanan d'in ke kallonta ta re da fad'in, "Na tab'a so d'aya, amma ba ni na shafa ba, wata ce ta shafa min". "Lord in heaven". Fad'in Fanan ta re da rik'e goshin ta. "Mai ki ka ce?". Binty ta fad'a ta na kallon Fanan d'in. "Ohhh nothing. Ban ce komai ba. Yanzu dai kalli ki ga yadda ake shafawa". Fanan ta fad'a ta re da matso lotion d'in ta shafa a jikin. Ita ma Binty ta yi kamar yadda ta ga Fanan d'in ta yi. Powders Fanan ta d'auko ta shafa mata ta re da taje mata gashin kan ta da ya zubo har tsakiyar bayanta ta kuma ka ma mata shi da ribom ta bar jelar ba ta re da ta nad'e ba. "Ki na da gashi Binty". Fad'in Fanan d'in. "Ke ma ki na da shi Fanan. Na ki ba b'aki ba ne irin na wa, ya fi na wa kyau". "Ke! Allah na ki ya fi kyau, du ba fa, ga cika da tsawo ga shi bak'i sosai. Yanzu dai ta shi ki yi sallah sai mu je parlour". Fad'in Fanan ta re da mik'a mata hijjab. Kayan da Fanan d'in ta fito mata da shi ta saka ta re da hijjab d'in ka na ta hau kan darduman. Kai tsaye ba wani tada ik'ama bare a kai ga karatun sallah ta tafi sujada. Waro idanuwa Fanan ta yi ta na kallon Bintyn ci ke da tsoro da kuma tsan-tsan mamaki. Ita kuwa Binty bayan ta d'ago daga Sujadar sai ta yi ruku'u ta kuma k'ara yin sujadar. Ha ka ta din ga yi har sai da ta yi raka'a takwas ka na ta ce, "Assalammaa alaiku". sau biyar ta re da mik'ewa ta kalli Fanan ta re da fad'in, "Fanan na gama". Ba ki sake Fanan ta ce, "Yanzu wannan sallah ce ki ka yi? Haka ake sallan?". "Eh haka naga a na yi a garin mu". "Lallai! Wallahi to duk y'an garin ku ba su iya sallah ba. Ku ma muje wajan Anna ki je". Fad'in Fanan ta re da yin hanyar parlour Bintyn na bi ye da ita a baya. A parlour su ka samu Anna d'in ta na kallan tashar Arewa 24 su na haska shirin mata a yau. "Anna, wallahi i`matsala. Onni owawa julde. Owi b'e gari rimab'b'e, nihib'b'e julirta. (Anna akwai matsala. Wannan yarinya ba ta iya sallah ba. Kuma ta ce y'an garin su duk haka su ke sallar)". Kallon ta Anna ta yi ta re da fad'in, "Innoye ojulurta? (Yaya ta ke salar)". "Daga sujjada ohud'd'i julde. Ko jande julde uwatta. (Daga sujada ta ke fara sallar. Ko karatun sallah ba ta yi)". "Gaskiya i`matsala. Unangai yaki jande to modibbo mud'un ware. (Gaskiya akwai matsala. Za ku rik'a zuwa karatu ta re idan malamin ku ya zo). Amma nan ga ka, ekki tukimo i hankali. (Ke ma ki rik'a koya mata a hankali)". "To Anna, mi'ekki taimu jande". Fad'in Fanan. "To yahun yama abinci". Fad'in Anna ta re da mai da duban ta ga TV, amma sam hankalin ta ya bar TVn ya ko ma tunanin Binty gaba d'aya. "Lallai yarinyar nan ta na buk'atar taimako". Fad'in Anna cikin zuciyar ta. Fanan kuwa Dining d'in da ke parlourn ta nu fa ta re da zama ta zuba farfesun Kaza da kuma sinasir, ka na ta zuba wa Bintyn. Da kyar Fanan ta iya cinye rabin sinasir ta re da cinyar kaza ta tura plate d'in gaba. Ita ma Bintyn kasancewar ta k'oshi rabin sinasir d'in taci. Kazan ne dai ta k'ara cin cinya da wani tsokar nama har ta lalata gaban rigar ta da roman farfesun Kazan nan. "Oh my God! Du bi yadda ki ka lalata gaban rigar ki, ga shi malam ya ku sa zuwa ku ma ta re za mu je mu ko yi karatu a wajan shi. Mu je in ba ki wata rigar ki canza". Fad'in Fanan ta re da mik'ewa. Ita ma Bintyn mik'ewa ta yi ta re da bin bayan Fanan zuwa d'akin ta. *_________* Tsaye ya ke gaban katotan plasma da ke manne a jikin bango d'akin. Hanu ya kai ta re da k'aro volume d'in home theatern, ka na ya canza music ta cikin wayar da ke hannun sa kasancewar da AUX ya ke amfani. Wakar D'banj ya saka fall in love ya shi ga bin wak'ar kamar haka. 🎻 _I'm D'banj or skibanj like my Jamaica friends call me_ _When the koko master fall in love_ _You know say water water don pass garri_ _Hmmmmn_ _I'm in love, are you in love?_ _Omo you don make me fall in love (you don make me)_ _Fall in love oh, fall in love(you don make me)_ _We suppose marry, 'cause you don make me fall in love (you don make me)_ _Fall in love (you don make me)_ _Fall in love_ (you don make me) _My sweet potato_ _I wanna tell you my mind, wanna tell you my mind oh_ _I no understand oh_ _'Cause I dey see well-well but them say love is blind oh_ _You see as you dey so_ _you are the love of my life, you are the love of my life oh_ _I cannot deny woo_ _I wanna make you my wife, make you my wife ohh_ _see, I never though that I'll find someone like you_ _That will capture my heart, and there's nothing I can do_ _But since I set my eyes on you_ _Omo you don make me fall in love(you don make me)_ _Fall in love(you don make me)_ _Fall in love(you don make me)_ _We suppose marry, 'cause yo don make me fall in love oh (you don make me)_ _Fall in love(you don make me)_ _Fall in love(you don make me)_ _Fall in love oh_ 🎻 A matuk'ar fusace ta banko k'ofar ta re da shigowa tta kashe home theater ta re da buga wayar da bango ka na ta juyo ta kalle shi idanuwan sun kad'a saboda b'acin rai ta ce, "Abu Sufyan ba za ku kashe ni ba wallahi sai lokaci na ya yi. Yanzu da girman ka saboda kai sha-sha-sha ne ba ka san in da ke ma ka ciwo za ka cika min part d'ina da hayaniyar wak'e wak'en banzan ka. To wallahi ka ki ya ye ni. Da ku manya zan ji ko kuma da k'anwar ku Sabrin da ke nai man saka min hawan jini mahaifin ku na d'aure mata gindi? Ko rantsuwa na yi ba zan yi kaffara ba, Abu Sufyan ba kai sallar asubha ba. Mai makon ku da Ku ke maza ku ma manya ku tsaya min a kan k'anwar ku da ke nai man fin k'arfi na, amma ku kan ku nai ma Ku ke ku hauka ta ni. Haba Abu, kun yi min adalci kenan? Ana zuga ku kuna k'ara tab'arb'arewa ku a naku tunanin k'aunar ku a ke yi ko? To wallahi idan za ka natsu, ka natsu. Shekara uku kamar yau ne a wajan ubangiji. Ai Babban wan na Ku zai dawo". Hajiya Sakna na gama fad'in hakan ta juya ta fice ta na jin wani k'una a k'asa zuciyar ta. Ta na fita Abu Sufyan ya ta'be baki ta re da fad'in, "Mom wallahi ki na da matsala. Dad'in aunty Junaina ke nan, ba ruwan ta da sakawa mutum idanu". Ya fad'i hakane ta re da kunna home theatern ya rage volume d'in ta re da cigaba da miming ya na rawa. "Ya Allah ka na kallon komai. Ka taimaka min ga me da lamarin y'ay'ana". "Sannu wacce duk duniyar nan ita d'aya ke da y'ay'a. Ni fa wallahi akan takurawa y'ay'ana wallahi za mu samu mugun sab'ani da ke Sakina. Ke ba za ki koyi da Junaina ba? Ba ki ganin yadda ta ke yi da y'ay'an ta har da ma na ki y'ay'an kamar k'awayan ta. Ta na barin su suyi duk abunda su ke so in dai ba zai cutar da su ba". "Cutarwa ke ce Alhaji? Cutarwa ku ma na nawa? Ai Junaina da kai kun dad'e ku na cutar min da y'ay'a wajan d'aura su a hanya mara b'illewa barin ma Sabrin da Ku ka riga ku ka halakar da ita. Kuma wallahi tallahi sai Allah ya tambaye ku a kan hakan da Ku ke yi. Kun sa Sabrin ta fi k'arfi na. Yanzu haka ka duba agogo almost to 4 amma yarinyar nan ba ta dawo daga makaranta ba bayan an tashi tun 2:00pm. Kuma na aika driver ya ce makarantar a kulle ba ta can. Na ma ka magana ka ce min ai tasan garin ba b'acewa za ta yi ba. Haba! Haba!! Haba!!! Alhaji. Kai ka na ganin hakan dai dai ne? Ina ta ke zuwa? Da izinin wa ta ke fita? Yadda yanzu kidnapping ya yi yawa a gari. Idan aka sace ta fa?". Duk maganganun da Hajiya Sakna ta yi bai shige sa ba, sai maganar sace Sabrin d'in da ta yi ne ya girgiza shi. Wayar sa ya zaro daga cikin aljihu ta re da fita da sauri ya yi wajan mota ya na kwalawa driver kira. Da gudu driver ya zo ta re da duk'awa a gaban Alhaji Saifullahi. Wawan mari Alhaji Saifullahi ya d'auke Shafi'u driver da shi sai da ya kifa k'asa. Ka na ya nu na masa hannu ta re da fad'in, "Wallahi duk ranar da ka k'ara shigowa gidan nan ba ta re da Sabrin ba, a bakin aikin ka kuma sai mun yi shari'a da kai. Kai wallahi ba zai yuwu ba. Bodyguard zan d'auko wa y'a ta". Kamar mahaukaci haka Alhaji Saifullahi ya bangaje Shafi'u ta re da shiga mota ya ja a guje ya bar gidan da tuni mai gadi ya bud'e don ya na ganin duk abunda ke faruwa ka da shi ma ya samu ba shi rabon. Ta re su ka fito Binty na bi ye da ita a baya sanye da hijjab. Wani waje da aka zagaye da fararan kujeru su ka nufa in da Malam Abdulrazaq ya ke zaune ya na jiran su k'araso. Sallama su ka yi ta re da zama ka na su ka gaishe sa. Amsawa ya yi ya na kallon Binty kasancewar Hajiya Na'ima (Anna) ta kira sa ta masa bayani a kan Bintyn, ta kuma ce masa ya taimaka ya lura da ita ta iya duk abubuwan da ya kamata. Kuma ya yi mata alk'awarin in sha Allah zai yi hakan. "Mai nene sunan sabuwar d'alibar tawa?". Malam ya fad'a ya na mai kallon Bintyn. "Suna na Binty Hashimu Mai goro". Fad'in Binty. "Masha Allah. Da fatan za ki natsu ki kuma ba ni hankalin ki saboda ki koya ta re da fahintar abunda zan koya miki?". "Eh zan yi Malam". Fad'in Binty. Kasancewar sai da Anna tai ma ta fad'a sosai akan duk abunda Malam ya koya mata ta tabbatar ta iya shi. Domin idan har ba ta iya ba sai ta Zane mata jikinta. "To Alhamdulillah, yanzu za mu fara da ummul kitab wato fatiha. Bud'e Qur'anin ki". Malam ya fad'a. Upside down ta rik'e Qur'anin. Don iya tsayin rayuwar ta ma ba ta tab'a ganin shi ba. Karb'a Fanan ta yi ta re da nuna mata yadda ake rik'e Qur'anin. Tun a wajan bismillah Malam ya san akwai babbar matsala. Domin ba ta iya ba. Sai dai in da hankalin shi ya kwanta, yadda Bintyn ta ke da saurin d'auke abu a kwakwalwarta. Sanye ya ke da three quarter da riga armless, sai wani shegen glass da ya kwama a fuska. Hannun shi rik'e da goran fanta da yaji kayan maye a ciki. Zugan abokan sa da kuma 'yan matansa da na abokan ba shi a bayan shi cikin shiga na rashin d'a'a. Cak ya tsaya ya na k'arewa wajan da su Binty su ke zaune malam na ko ya masu karatu. Takawa ya yi har in da su ke ta re da k'urawa Binty idanuwa ko kyaftawa ba ya yi. Ita kuwa Fanan ganin wan na ta ya nufi wajan da su, tu ni jikinta ya d'au rawa. Don mawiyacin abu ne su had'u bai mata mummunar duka ba. "Zo nan dan uwar kiii" *_MATAR SAYYADEE_* 🌹 *19-20*🌹 Jikin Fanan na wani irin rawa ta mik'e ta soma takawa a hankali ta na tsoran irin dukan da zai yi mata. Shi kuwa malam zubawa sarautar Allah idanu ya yi, domin ba wannan ba ce rana ta farko da Suhail d'in ya ke hakan idan su na karatu ba. "Dan kutumar uwar ki, in ta tsayuwa ina jiran ki? Kin tsaya ki na wani tafiya simi-simi kamar macijiya. Wallahi na k'irga uku ba ki k'araso nan ba, sai na karya k'ashin k'afar ki". Fad'in Suhail ya na wani muzurai. Da gudu-gudu Fanan ta k'arasa wajan sa ta re da fad'in, "Ya Suhail ga ni. Wa ni abun zan yi maka". Ta fad'i hakan ne bakinta na rawa kamar wacce tai k'arya. Sai da ya k'ara kallon in da Binty ta ke, ka na ya dawo da duban sa izuwa ga Fanan d'in ta re da fad'in, "Wa cece wancan yarinyar?". Suhail ya fad'a ya na wani yamutsa fuskan shi. Kallon Bintyn ta yi, ka na ta mai da du ban ta ga Suhail ta re da fad'in, "Anna ta ce min y'ar aiki ce, za ta rik'a ta ya ni ayyukan gida". "Y'ar aiki". Suhail ya maimaita cikin zuciyar sa ta re da k'ara mai da du ban sa ga Bintyn da ta mai da hankalin ta gaba ga karatun suratul Fatihan da malam ke koya mata. "Kai! Malam ka ke ko malum-malum, sako yarinyar nan ta zo nan". Fad'in Suhail ya na wa malam d'in wani kallon k'ask'an ci. Kamar malam zai ce wani abu, sai kuma ya kalli Binty ta re da fad'in, "Je ki ana kiran ki". Ya fad'i hakan ne ta re da mai da duban sa a kan Qur'anin sa. Binty kuwa mik'ewa ta yi ta re da nufo in da Fanan da ya Suhail su ke a tsaye. Ta na zuwa wajan ta tsaya k'ak'am ta na kallon fuskan Suhail da ke kallon ta from head to toes. "Fanan mai ya sa ki ka tsaya a nan bayan malam na jiran mu zai mana karatu? Har na fara iyawa Allah. Malam ya ce zan yi k'ok'ari sosai". "Ke biyo ni". Fad'in Suhail ta re da wucewa gaba. Ita kuwa Binty ba ta san ma da ita ya ke yi ba. Ganin ya yi gaba ita ma ta juya za ta koma wajan malam domin ya cigaba da koya mata karatu. Ruk'o hannunta Fanan ta yi ta re da fad'in, "Binty Yaya Suhail fa da ke ya ke magana. Ya ce ki bishi. Kuma idan ya juyo ya ga ba ki bi sa ba, zan karya miki k'afa da duka wallahi". Zaro idanuwa Binty ta yi ta re da fad'in, "Da ni ya ke yi? Ai na d'auka da ke ya ke yi. To mai zan masa?". "Oho ni ma ban sani ba, dan Allah ki je ka da ya juyo ya ga bai gan ki a bayan sa ba. Ku ma ya fara miki nisa fa". Fad'in Fanan. Ai da gudu Binty ta bi bayan Suhail d'in har ta isa inda ta ke ta na haki don ya mata nisa. Ga gidan da shegen fad'i da tsayi. "Ga ni Yaya, Fanan ta ce wai ka na kira na". Fad'in Binty ta na haki. Juyowa ya yi ya kalle ta ta re da fad'in, "Shiga mota". Ya fad'i hakane ta re da bud'e gaban mota, shikuma ya zagaya ya shiga mazaunin driver. Ya yin da uku daga cikin y'an matan shi su ka shiga gidan baya. Sauran abokan sa kuma su ka shiga na su motocin kasancewar sun zo da ita. Har lokacin Binty na tsaye a wajan ba ta da niyyar shiga cikin mota. "Ke dan uwar ki zan ta tsayawa ne ina jiran ki ba za ki shiga mota ba?". Suhail ya fad'a ya na zazzaro mata idanuwan sa da suka juye irin na masu shaye-shaye. Saboda yadda ya yi maganar da k'arfi Binty ba ta san sadda ta shige gaban motan ba ta na zazzaro idanuwa. Mik'owa hannunsa ya yi ta re da rufe motar ka na ya yi mata key ta re da reverse ka na ya fito daga parking load d'in. Fanan kuwa wani ajiyar zuciya ta sauke ta re da nufar wajan malam. Shi kuwa Malam tun sanda Binty ta ruga ta bi bayan Suhail gabansa ke bugawa don sarai ya san halin Suhail d'in ciki da bai. Yaron da a k'asar waje ya yi primary da secondary d'in sa. Lalacewar da ya so ma yi ne ya sa Alhaji Usman da kan shi ya dawo da shi gida Nigeria a wani zuwan bazata da ya yi masa ya tarar da abun asshan da ya ke yi da mata da kuma abokan sa turawa su ke yi. Babu irin kwayar da Suhail bai sha. Har safarar cocaine ya na yi ba ta re da sanin iyayansa ba. Mutum uku ya ke shakka a rayuwarsa, wato mahaifinsa da Hajiya Na'ima uwargidan mahaifin na sa. Duk rashin kunyar sa bai iya yin ta a gaban ta, sai kuma babba d'a ga Alhaji Usman da hajiya Na'ima, wato Julaibib Usman Mai rabo, wanda a yanzu haka ya na US ya na Masters degree d'in sa. Malam ya kalli Fanan da ta zauna akan kujera ta na sakin ajiyar zuciya ta re da fad'in, "Ina ki ka baro Bintyn?". Ya fad'i haka ne ya na kallon cikin idanuwan ta gaban sa na fad'uwa ka da Suhail d'in ya lalata y'ar mutane. "Ya Suhail ya ce ta bi shi". Fad'in Fanan in I don't care manner, don ita Sam ba ta d'auka wani abun zai ma ta na cutarwa ba. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Maza Fanan je ki fad'a Hajiya da sauri". Fad'in Malam. "Malam mai ya faru?" Fad'in Fanan zuciyar ta na bugawa saboda yadda malam ya yi magana. "Kar ki yi tambaya Fanan, ke dai yi sauri je ki fad'awa Hajiya Suhail ya ta fi da Binty". Fad'in malam. Da sauri Binty ta mik'e ta re da yin part d'in Anna da gudu don zuwa fad'in abunda malam ya aiketa ta fad'i. Kusada gate d'in k'arshe, wato gate d'in da Oga Solomon ke gadi Suhail ya rage gudun mota ta re da ciro sigari a cikin aljihun wandon sa ya saka a baki. "Baba Haruna, see that stupid boy. He finish chop the girls, now he wan return them back to their houses". Fad'in Oga Solomon ya na tab'a k'afar Baban Haruna. "Mtsww, I pray for da boy may him get HIV, may be he will stop following womens. Mtsee very bad pikin". Fad'in Baban Haruna. Wani irin horn Suhail ke dannawa kamar zai cire kunnuwan Oga Solomon da Baban Haruna. Da gudu Oga Solomon d'in ya ta shi ta re da wangale gate d'in gidan. Sai da Suhail ya zo gab da Oga Solomon d'in ka na ya sauke glass d'in motar ta re da turo kan sa waje ya saka sigari a baki ya na kallon Oga Solomon. Oga Solomon ya soma lalube-lalube a jikin wandon shi ya Ciro lighter ta re da kunnawa Suhail d'in sigarin. Idanuwan sa ne su ka sauka a kan Binty da ke ta zare idanuwa. Gaban Oga Solomon ne ya buga da k'arfi ta re da fad'i cikin zuciyar sa, "This girl don finish. Jesus helf her". Da mugun gudu ya ja motar ta re da barin gidan. Oga Solomon kuwa cikin hanzari ya kulle gate d'in ta re da dawowa wajan da Baban Haruna ya ke zaune ta re da fad'in, "Heeeyyy! Baba Haruna dis girl don finish wallahe". "Which girl?". Fad'in Baban Haruna ya na kallon Oga Solomon d'in. "Da pretty girl way dat stupid old bitch bring dis money". "Watin come happing to her?". Baban Haruna ya fad'a a firgice. "I saw her with my eyes open in dat stupid boy car. I known he will go and rape that girl. Chaii! I pity for her". Oga Solomon ya fad'a kamar zai yi kuka. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Allah dai ya tsinewa yaron nan. How did she even follow him? Kai Allah ya cece ki yarinya". Fad'in Baban Haruna ci ke da jimamai. "Anna! Anna!! Anna!!! Ki na ina?". Fanan ta fad'a tun ta na hawa sama har ta k'arisa shiga parlourn saman. Kicib'is su ka yi da Anna da ta fito a gigice. "Lafiya Fanan ki ke min irin wannan kiran? Ina Binty?". Anna ta fad'a ta re da rik'o kafad'un ta. "Yaya Suhail ya tafi da ita a mota". Fad'in Fanan. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un3×". Hajiya Na'ima ta fad'a ta re da d'aukar wayar ta akan center table ta nufo stairs don saukowa parlourn k'asa Fanan bi ye da ita. Wasu numbobi ta danna a wayarta ta re da kara wayar a kunnanta. Ringi d'aya cikin ba biyu wanda ta kira ya d'aga ta re da fad'in, "Assalamu alaikum Anna....." Katse shi ta yi ta re da fad'in, "Wa'alaikumussalam. Fu'ad zo gida yanzu ina nai man ka. Ko kuma ka da ka zo gida, duk in da Suhail ya ke ka naimo shi ka dawo min da yarinyar da ya fita da ita. Za ka gan ta ba ta wuce Fanan ba. Dan Allah ka hanzarta yanzu ka naimo shi tun kamin ya lalata amanar da aka bar min". "Yanzun nan kuwa Anna". Fad'in barrister Fu'ad ta re da katse wayar. Wa ni number ya yi dialing bugu d'aya aka d'aga, ta re da fad'in, "Sai Oga, da girman kujeran Barrister". "Ka na ji na ko kacha, yanzan nan na ba ka minti biyar ka binciko min in da Suhail ya ke ka kira ni ka fad'a". "An gama Barrister". Fad'in kacha ta re da katse kiran. Barrister Fu'ad kuwa mik'ewa ya yi ta re da tattara files d'in da ke gaban shi ya jawo drawer ya saka ta re da d'aukar key d'in motar shi ya fito ya kulle office d'in shi ya fito zuwa wajan da motar shi ta ke ya shiga ta re da mata key ya bar High court d'in don cika umarnin mahaifiyar sa. Cikin wani k'aton gidan gona ya yi parking. Makekan gidan gona ne in da ake kiwo kala-kala. Gyefe guda kuma wani rantsatstsan two bedroom ne. Shi kad'ai ya zo sai Binty da ke gaban mota ta yi tsamo-tsamo. Duk ya sallami sauran abokan sa da y'an matan sa da duk sun girme sa don gaba d'aya shekarunsa sha takwas ne, girman jiki ne Allah ya ba shi irin na mahaifiyar sa. Bud'e motar ya yi ta re da fitowa ka na ya zagaya ya bud'ewa Binty k'ofa ta re da murtuke fuska ya ce, "Sauko ki fito". Ya fad'a hakan da kausasshan muryan shi da shaye-shaye ya fasa. Binty jiki na rawa ta fito daga motar nan ta re da rukub'ewa a jikin k'ofa ta na kallon sa da idanuwan ta da har ya cicciko da hawaye. "Idan ki ka sa ke ki ka min kuka, kin ga dai girman gidan gonan nan ko, to daga ni sai ke ce a ciki. Zan iya yanka ki in bizne ki babu wanda ya sani, don haka kar ki sake ki min kuka. Duk abunda na ce ki yi kawai ki yi. Kin ji abunda na ce miki?". Jijjiga kai Binty ta yi jikinta na k'ara tsuma musamman da ta ji maganar yanka da biznewa. "Oya wuce muje". Fad'in Suhail ya na nuna mata hanya da hannun sa. Simi-simi ta yi gaba k'afarta na hard'ewa. Tawowa ya yi ya wuce ta ta re da isa wajan k'ofar ya bud'e ka na ya nuna mata cikin d'akin da hannu. Kallon shi ta yi idanuwan sun yi jazurr, hatta leb'anta rawa su ke yi kamar mai jin sanyi saboda tsabar yarda ta firgice. Shiga ta yi hawaye na zubowa daga idanunta tai saurin saka bayan hannunta ta goge. "Oya cire wannan hijjab d'in". Suhail ya fad'a ya na tsare ta da idanuwa. Hijjab d'in ta cire ta re da rik'e shi a hannun ta. Domin gaba d'aya ya firgitata, musamman muryan shi da ya ke kama da na rik'ak'k'un garada. "Ke ban san iskanci. Aje hijjab d'in nan ko in zo wajan nan in taka miki wuya". Suhail ya fad'a ya na zazzaro mata idanuwan shi. Saboda tsabar rud'ewan da ta yi, jifa ta yi da hijjab d'in a kan fridge d'in da ke d'akin ba ta re da ta sani ba. Kallon ta ya shiga yi from head to toes ta re da fad'in, "D'anya ce shataf, amma haka nan zan yi manaji a haka za ta girma musamman idan ta na jin taki". Zame wandon jeans d'in jikinsa ya yi, ya rage da ga shi sai boxer. Rigar jikin shi da singlet ya cire ta re da zama a kan three sitter ka na ya ce, "Zo nan". Ya fad'i hakan ne ya na shafa cikin sa. Binty kuwa tsaye ta ke a wajan ta ki zuwan sai kallon shi da ta ke yi. "Ba da ke na ke yi ba". Ya fad'a da k'arfi sai da ta firgita wanda ba ta san lokacin da ta isa gare shi ba. Jawo ta ya yi ta re sa da zaunar da ita a saman cinyar sa ka na ya zame hulan da ke kan ta. Kyakkyawan gashin kan ta bayyana. Yayin da jelar gashin ke tab'a masa gwiwar k'afarsa. "Wow!". Suhail ya fad'a ya na shafa kan tun daga tsakiyar kanta har k'arshan bindin gashin. Hancinsa ya kai wuyarta ya na sunsuna ta re da lumshe idanu saboda daddad'an kamshin man shafawan Fanan da Bintyn ta shafa. Ga wani fitinannan k'amshi da gashin kan na ta ke yi saboda gyaran da mai saloon d'in nan ta ma ta da kuma wanda Fanan ta ma ta d'azu. B'alle buturan rigar jikinta ya yi ta re da wurgi da rigar a kan tiles. Hannu ya kai ya na shafa ko ina a jikinta kamar ya na shafa jikin budurwa. Ita kuwa Binty ji ta yi kamar ana watsa mata ruwan zafi mai mugun zafi a jikinta. Mik'ewa ta yi a razane ta na susan jikinta don wani irin rad'ad'i da ta ke ji. "Ke ina wasa da ke ne? Waya ba ki izinin ta shi a kan jikina? Dawo ki zauna kuma duk abunda na mi ki ke ma ki min". Suhail ya fad'i ya na gwalalo mata idanuwa. K'in zuwa Binty ta yi ta na soshe-soshen jiki ta re da hawaye. Mik'ewa ya yi a zafafe ya d'auke ta da mari ta re hankad'ata ta fad'i k'asa. Cire belt d'n wandon da ya yi ta re da zame shi ya fad'i k'asa ka na ya damk'o gashin kan ta har sai da ta saki ihu. Ka yan jikinta ya cire kaf ka na ya kwantar da ita flat a kan 3three sitter ya Shiga k'ok'arin cire boxer d'in jikinsa. Dai dai lokacin Barrister Fu'ad ya banko k'ofar d'akin ya shigo. Idanuwan sa ya sauka akan Suhail da ke nai man afkawa yarinya. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Suhail kai wani irin d'an akuya ne? Dan uban ka wannan y'ar k'ank'anuwar yarinyar za kai rapping?" Barrister Fu'ad ya fad'a ta re da k'arasawa kusa da shi ya d'auke shi da maruka hagu da dama. Shi kuwa Suhail jan boxer d'in sa da ya fara cirewa ya yi ta re da jaa baya ya na fad'in, "Ni ai ba tilas nai ma ta ba, ita ta biyo ni". 'Kara d'auke shi da mari Barrister ya yi ta re da fad'in, "Uban ka na ce, Suhail. Wannan yarinyar mai ta sani da Har za ta bi yo ka? Yarinya k'ank'anuwa da ko balaga ba ta yi ba, ita ka ke so ka b'ata. Yanzu idan Fanan ko Sunaina a kai wa haka za ka ji dad'i!". "Oho! Idan su su ka kai kan su, to ni in ruwa na. Yanzu fa kowa fa abunda ya ga dama ya ke yi. Wa ya san kai me ka ke aikatawa". Suhail ya fad'a ya na wani ciccijewa kamar d'an daba. Wanka masa mari ya sa ke yi ta re da nu na shi da yatsa ya ce, "Dole ka ce oho tunda ba uwa d'aya ta haife ku da wad'anda na lissafo ba. Ku ma da ka ke cewa wa yasan abunda ni na ke aikatawa, an fad'a maka kowa d'an iska ne irin ka? To ba ri ka ji, wallahi, tallahi, duk ranar da ka sake attempting yi wa wata yarinya fyad'e, na rantse da girman Allah wannan a wannan karan ba zan saurari Anna da ta ke hanani ba. Ni ka d'ai na san hukuncin da zan d'auka. Ban key d'in gidan nan". Barrister Fu'ad ya fad'a ta re da mik'a masa hannun sa alamar ya sa ka masa key d'in a hannun sa. Suhail sai wa ni cicciza ya ke yi kamar ba zai ba da key d'in ba. Can kuma ya mik'a masa. Barrister ya kalli in da Binty ta ke jikin ta sai rawa ya ke yi ta re da fad'in, "Sauko ki d'auko kayan ki kisa mu tafi wajan Anna". Jikinta na rawa ta sauko daga kan kujerar ta re da d'aukar kayanta da ke yashe a k'asa. Saboda yadda jikinta ke rawa, sai ta kasa saka kayan. Barrister Fu'ad ya karb'i kayan ta re da saka mata, ka na ya kama hannunta ta re da kallon Suhail d'in ya ce, "Fita ka d'au motarka, zan kulle gidan". Barrister Fu'ad ya fad'a ya na antaya masa harara. Wa ni dogon tsaki ya ja ta re da fad'in, "Kill joy". Kamar zai bangaje sa ya fice daga d'akin. Barrister Fu'ad ma tsakin yaja ta re da yin kwafa ya ce, "Zan yi maganin ka soon. D'an iskan yaro kawai". Ya fad'i hakan ne ta re fitowa hannun shi rik'e da hannun Binty. Kulle k'ofar ya yi lokacin tuni Suhail ya ja mota da uban k'arfi ya bar gidan. Kasancewar mota Barrister na k'ofar gate. Kai tsaye fita su kai ya kulle gate d'in da key ya kuma saka kwad'o ta re da yin wajan mota ya bud'e gaban Binty ta shiga, shikuma ya zagaya ta re da shiga mazaunin driver ya kunna motar ta re da reverse. Sai da su ka hau hanya, sannan Barrister Fu'ad ya juyo ya kalli Binty wacce har a lokacin gaban ta bai dai na fad'uwa ba. "Me ya sa ki ka biyo sa". Barrister ya fad' ta re da mai da duban sa ga titi. "Shi ya ce dole sai na shiga mota. Shine ya kawo ni nan". Fad'in Binty muryanta na rawa. Don har yanzu ba ta dai na jin jikinta kamar ana yayyafa mata ruwan zafi ba. Don har turiri-turiri ta ke ji jikin na mata. "Daga yau ko ya kira ki ka da ki je. Ka da ma ki rik'a zuwa in da zai gan ki. Idan kuma kun had'u bi sa kuskure, ki yi gudo ki koma wajan Anna kin ji?". Barrister ya fad'a ya na kallon kyakkyawar fuskan da tsoran da ta ke ji ya k'ara bayyanar da kyawun fuskan ta. "Yauwa Malam ne ke mana karatu, shine ya kira ni. Kuma Fanan ce ta ce idan ban je ba karya ni zai yi". "Idan kuma ki ka je ya tab'a jikin ki, mutuwa za ki yi". Fad'in Barrister Fu'ad ya na kallon idanunta saboda ya ga reaction d'in ta. Aikuwa ta zaro idanuwa ta re da fad'in "Ba na so na mutu, Allah zan gudu idan na gan shi. Wajan Malam ma bazan k'ara zuwa ba". Fad'in Binty hawaye na silalo mata. "Oho ni dai na fad'a miki, ba shi kad'ai ba ma, duk namijin da ki ka sa ke ji ka yadda ya na wasa da jikin ki, ko ya na tab'a miki jikin ki, ko ya ke ji tab'a na da jikin, to mutuwa za ki yi murus, saboda haka ba ruwan ki da wasa da maza, kin ji". "Na ji, ba zan yi wasa da maza ba. Fanan kawai zan yi wasa da ita". "Good girl. Menene sunan ki?". Barrister ya fad'a. "Suna na Binty Hashimu mai goro. Kai kuma fa?". Binty ta fad'a ta na kallon shi. "Yaya Fu'ad, ko ki ce Yaya Barrister. Sannan daga yau ba Binty Hashimu sunan ki. Tsoffi ke cewa Hashimu. Daga yau duk wanda ya tambayi sunan ki, ki ce Binty Hisham mai goro kin ji?". "Binty Hisham mai goro". Binty ta maimaita ta na kallon shi. "Eh daga yau haka za ki rik'a fad'i". Fad'in Barrister Fu'ad. Hakanan ya ji y'ar k'aramar yarinyar da nai san alak'ar sa da ita ba ta shiga ran sa. *DAN GIRMAN ALLAH KA DA KI KARANTA IDAN BA KI SIYA BA, BI YA #500 KI KARANTA NA HALAS D'IN KI BA NA SATA BA ZUWA WANNAN ACCOUNT D'IN 0592412800 ZULFAU SA'ID GTBANK. SAI KI TURO DA SHAIDAN BIYAN KI TA WANNAN NUNBER 08128755583* *MATAR SAYYADEE*✍🏻 🌹 *21-22*🌹 Direct gida su ka yo. Horn Barrister Fu'ad ya yi. Oga Solomon ya ta shi da sauri ya bud'e masa gate. Kasancewar motar ta shi ba tinted, hakan ya ba shi damar ganin Binty da ke zaune a gaban mota. Wani dad'i ne ya mamaye zuciyar Oga Solomon ta re da sarawa Barrister Fu'ad ya na fad'in, "Welcome home Sir". Sauke glass d'in motar Barrister Fu'ad ya yi ta re da fad'in, "Solo, Solo. Solomon how you dey?". Ya fad'i hakan ne ya na dariya. "Ahh, Oga I dey fine wooo, ibi like say I wan dance in from you. I fell happy wallahe". Fad'in Oga Solomon ta re da k'ara gyarawa bindigarsa zama a kafad'arsa. Murmushi Barrister Fu'ad ya yi ba ta re da ya tambaye farin cikin mai ya ke yi ba. Don bai son surutu so kawai ya ke ya aje Binty ya koma wajan aiki don akwai case d'in da zai yi anjima kuma saura rabin awa. Gashi Solomon akwai d'an bura uban surutu kamar uban aku. Jan motarsa ya yi ta re da nufar second gate. Parking ya yi a farfajiyar gidan saboda ba dad'ewa zai yi ba shi yasa bai kai motar parking space ba. Fanan da ke gaban part d'in su, ta na hango Binty a gaban motar wan na ta ta yi wajan da gudu. Domin y'an awannin da su kai da. Bintyn ta mugun shiga ran ta har ta ke jin kamar sun shekara. Kuka kuwa ta yi shi ba bu adadi domin idanuwan ta sun kad'a sun yi jazurr, duk a tunanin ta yaya Suhail d'in ya ta fi karya Binty ne ko ma ya kashe ta. Don ita kan ta akwai wani duka da ya mata sai da ta kwanta a asibiti, sai daddy ya ma sa kaca-kaca akan dukanta ne ya d'an sarara kasancewar ya na shakkar sa. Annah kuwa ko k'ala ba ta cewa, a cewar ta, wai sun fi kusa ai y'ar uwarsa ce ya ma kashe ta. Rungume ta Fanan ta yi ta re da fad'in, "Alhamdulillah you're home sister. I'm so sorry for allowing you to follow him, I won't do that again. Please pardon me sister. But did he hurt you?". Fanan ta k'arisa ta na dudduba jikin ta domin ta ga ko akwai in da Suhail d'in ya ji mata ciwo da dukan. Sam ta manta ma idan za ta shekara ta na turanci Bintyn ba za ta San abunda ta ke ce wa ba. "Dalla matsa ko in bige ki a nan wajan. Da ma ke ki ka ce mata ta je wajan shi ko?". Fad'in Barrister Fu'ad ya na hararar Fanan d'in. "Ohhh brother lemme explain". Fad'in Fanan a marairaice. "Heey! Not a word. I don't need your explanation. Talkative". Fad'in Barrister ta re da matsar da Fanan ya ruk'o hannun Binty su kai part d'in Anna (Hajiya Na'ima). "Ohhh please bro, won't you hold my too?". Fanan ta sha gaban su ta re da mik'a hannunta. Girgiza kai Barrister ya yi ta re da rik'e hannunta ita ma. A parlourn k'asa su ka taras da Annah sai sama da marwa ta ke yi. Ka na ganin ta kasan hank'alinta a tashe ya ke. "Anna she's back. Bro Fu'ad brought her back. Look at her here". Da sauri Anna ta juyo ta re da sauke idanuwan ta a kan Binty. Wani sanyayyar ajiyar zuciya ta sauke ta re da k'arisawa in da su ke ta rungume Bintyn. "Wannan beauty d'in fa za ta kwace miki autahood d'in ki". Barrister Fu'ad ya fad'awa Fanan a kunne at the same time kuma ya na mata dariya da gwalo. "Brooooo". Fanan cike da shagwab'a. Zaro mata idanuwa ya yi ta re da karyar da wuyarsa ka na ya ce, "Yessss. How may I help you?". Turo ba ki ta yi ta re da ita wajan su Anna da ke rungume da Binty ta ce, "Anna me too". Ta fad'i hakanne ta re da ware hannunta cike da shagwab'a. Murmushi Anna ta yi ta re da had'a su duka ta rungume su ta na kissing forehead d'in su. Mai da du ban ta ta yi ga Barrister ta yi ta re da fad'in, "Fu'ad, I hope he didn't do anything to this little girl? Cus wallahi this time I can't hold it". Ajiyar zuciya Barrister ya sauke ta re da fad'in, "He's about to, sai Allah ya kawo ni da sauri. Maganar gaskiya Anna ki bar ni in d'au mataki a kan wannan d'an iskan yaro da ya ke nai ma ya lalata mana sunan gida kuma uwar sa na sane ba za ta iya d'aukan mataki ba. Wallahi jiya sai da wani abokin aiki na ya min magana akan in rik'a kula da shi saboda last 3 days gasa su kai a kan kwayar doki, kuma shi ya ci gasar. Yaro duk ya bi ya lalata kan shi, k'arami da shi. Ko nineteen years fa bai yi ba. He's just eighteen. Haba Anna, dan Allah ki bar ni na d'au mataki. Ki na ganin da ya Julaibib ya na nan zai kyale shi ya yi duk abunda ya ga da ma ne. Wallahi duk ranar da yaya zai sauke k'asar nan ya ji labarin abunda Suhail ya ke yi, to wallahi sai ya karya shi. Ke Anna ai kin fi kowa sanin halin sa. Dan Allah ki bar ni in gyarawa yaran nan zama tun kamin yaya ya dawo ni ma ya had'a da ni. Don cewa zai yi ina kallo ya lalace". "Enough barrister! You can go back to your work. Ku ba ku san abunda na sa ni ba. Duk abunda na ke yi ina da dalili na. Suhail d'an uwan ku ne, ni kuma d'an mijina ne da na ke ma sa kallon d'an ciki na kamar kai da ka ke ga ba na. So just do as I say". "As you wish Anna". Fad'in Barrister in a cool way. Cus har ga Allah ya na son d'auka mataki kwakkwara akan d'an uwan na sa. Domin idan ya lalace kamar shi ne ko Zaid k'anin sa ne ya lalace. "Anna I'm going". Barrister Fu'ad ya sa ke fad'i ya na kallon Binty da ita ma shi ta ke kallo. Kuma Sam ta ka sa fahimtar mai su ke cewa kasancewar su na had'a turanci a cikin maganganun su. "OK". Anna ta fad'a a tak'aice ta re da rik'e hannun Fanan da Binty su ka nufi stairs. "Anna, why not malamin ya rik'a shigowa har parlourn nan k'asa ya na masu karatun? Cus zaman su a waje is not safe for the little girl". Ba ta re da Anna ta juyo ba ta ce, "Zan masa magana, ni ma hakan na tsara". Ta fad'i hakane su na hayewa steps d'in. Ajiyar zuciya Barrister Fu'ad ya sa ki, ya na son tambayar Anna wacece Binty, amma yadda ya ga Anna ta yi kicin-kicin da fuska sai ya had'iye tambayar sa ya fi ce don ka da ya yi latti. Shiga mota ya yi ta re da reverse ya fi ce. Ya kai gate d'in k'arshe wato gate d'in su Oga Solomon ya sauke glass ta re da yafito Solomon d'in da ke rik'e da gate d'in da ya bud'e masa. Da sauri Oga Solomon ya isa wajan motar tare da sarawa Barrister. "I need to talk to you, but leter in the night when I come back". Fad'in Barrister Fu'ad. "OK sir". Oga Solomon ya fad'a ta re da k'ara sarawa Barrister Fu'ad. Mai da glass d'in sama ya yi ta re da ficewa daga gidan. Shi kuma Solomon ya rufe gate d'in ta re da dawowa wajan zaman shi ya soma wak'an yaran su. .........."Kar ko da wasa wanda ya fita da ke yau ya sa ke kiran ki, ki bishi. Kin ji abunda na ce miki?". Anna ta fad'a ta re da rik'e kunnanta d'aya. "Eh Anna na ji. Yaya Fu'ad ma ya ce min haka. Wai idan na saki wani namiji ya tab'a ni, zan mutu. Ya ce ka na yi wasa da maza idan ba haka ba zan mutu". "Abunda ya fad'a gaskiya ne. Ba ke kad'ai ba, dukkan ku har da ke Fanan". Fad'in Anna ta re da mai da dubanta ga Fanan d'in da ke kwalalo idanuwa. "Now go and perform ablution and pray. And don't forget to teach her how to pray". Fad'in Anna saboda kiran sallar la'asar d'in da ake yi. Fanan ce ta soma mik'ewa saboda Binty ba ta san mai Anna ta ce ba kasancewar da turanci tai maganar. Hannun Binty ta rik'e ta re da fad'in, "Mu je mu yi sallah sis". "A'a ni bazan yi ba, ke ki je ki yi. Ni na gaji yau bazan yi ba sai gobe da safe. Dama ni sau d'aya kawai na ke yi. Shi ma Hadaan ne ya ce na rik'a yi idan ba haka ba Allah zai saka ni a wuta". Fad'in Binty ta re da zame Hannunta ta kwanta a kan carpet. Zaro idanuwa Anna ta yi ta re da fad'in, "Binty ai duk wanda bai sallah wuta zai shiga. Banbancin mu da arna kenan ai. Dole ne ki yi duka salloli guda biyar a kowace rana". "Anna menene arna? su waye arna? Su ma mutane ne?". Kallonta Anna ta yi cike da tausayi da kuma mamakin daga wani k'auye ta fito da ba su san addini ba haka. "Binty ina ne k'auyan ku?". Fad'in Anna ta na kallon ta. Shuru Binty ta yi ta na tunanin sunan da Kandala ta fad'a mata idan an tambaye ta garin su. Can ta ce, "Can k'auyan Saminaka". Fad'in Binty ci ke da jin dad'in tuno sunan da ta yi. Jinjina kai Annah ta yi ta re da fad'in, "Binty Arna su ne wad'anda ba su bin duk abunda Allah ya ce ayi. Ba sa sallah, Ku ma ba su yadda da fiyayyan halitta Annabi Muhammad SAW ba, sanna ba su yadda Annabi Isa ba Allah ba ne". Fad'in Anna. "Annah wanene Annabi Muhammad, kuma wanene Annabi Isah?" Fad'in Binty ita ma ta na kallon Anna. "Ohhh may God! Binty ba ki san su ba? Amma dai ba kya zuwa islamiya ko? Ai duk musulmi ya san tarihin su. Kuma yasan su Annabawa ne da Allah ya aikowa mutane". "Quiet please". Anna ta fad'a ta re da kallon Fanan d'in. "Annabi Muhammad SWA shine manzo na k'arshe da Allah ya turo. Allah ya turo shi ne domin ya wa'azantar da al'ummar sa domin su bi hanya na gaskiya. Haka shi ma Annabi Isa". "Menene wa'azi Anna? Kuma su waye su ke bin hanyar dai-dai, kuma suwa su ke bin wanda ba dai-dai ba?". Binty ta sake fad'i. Ajiyar zuciya Anna ta sauke ta re fad'in, "Binty ku je ku yi sallah, a hankali za ki ga ne komai idan har za ki nutsu wajan malam. Zai koya miki komai. Kuma ki masa duk tambayar da ki ke son yi kin ji? Kuma ka da ki sake cewa ba za ki sallah ba. Sallah wajibi ne akan kowani musulmi". "To Anna. Daga yau kullum zan rik'a sallah". "Good girl. Allah ya mu ku albarka. Ku je ku yi sallah". Fad'in Anna. Mik'ewa Binty ta yi, Fanan ta ka ma hannunta su ka wuce d'akin Fanan d'in don gabatar da alwala da kuma sallah. Sosai hankalin Anna ya ta shi da irin jahilcin da Binty da kuma jama'ar k'auyan su ke fama da shi. Yanzu kenan duk kallan da su ke wa Kandala ita d'in jahila ce. "Wannan yarinya Sam ba da aikatau ta da ce ba, da makaranta ta da ce. Ga kyau iya kyau amma kwakwalwa cushe ya ke da kashin kafinta. Dole na yi tsaye a kan yarinyar nan ta yi makaranta kamar yadda zan yi a kan Fanna. Wannan yarinya na zama uwarta da ubanta. Babu wanda ya isa ya karb'e ta a hannu na. Zan tsaya iya tsayin daka naga ta samu ingattaccan ilimi da izinin Allah. Ta yadda za ta ceto k'auyan su daga halakar da su ke ciki. Ya Allah ka taimaka min a kan haka". Fad'in Anna ta re da d'aga hannu sama ta na rok'an Allah. *8:15pm* Wasu had'ad'd'un motoci guda tara ne su ka danno cikin layin. Hu'du a gaba, hu'du a baya. Sai guda d'aya a tsakiya wanda Alhaji Usman Mai rabo ya ke ciki ya na duba sak'on email a wayarsa. Horn su ka danna. Oga Solomon da ke magana k'asa-k'asa da Baban Haruna ya zabura ya mik'e ta re da fad'in, "Baban Haruna, Alhaji is back". Ya fad'i hakane ta re da sauri isa ya wangale gate d'in. Takwas d'in farkon nan su ka shiga ciki ka na motar da Alhaji Usman ke ciki ya danno kai. Tsayawa driver ya yi, domin ya san Alhaji a nan ya ke sauka domin ya duba ma'aikatan sa. Duk nisan da ke tsakanin gate d'in farko da kuma ainahin cikin gida, haka ya ke tafiya a k'afa don kaf sai ya ji lafiyar ma'aika da kuma idan su na buk'atar wani abun ka min ya k'arasa wajan iyalansa. Aje tsaleliyar wayarsa ya yi a kan briefcase d'in sa. D'aya daga cikin bodyguard d'in sa ya fito da sauri ya bud'e masa murfin mota. Kyakkyawan k'afarsa ya fara fito da shi, ka na ya fito da gangan jikinsa. Saboda yadda gaba d'aya gidan ta ko'ina akwai globes farare, dai gidan yai haske kamar ba dare ba. Ko babu wutan nepa su na da k'aton jen *MIKANO* standby a gidan. Babu yadda za'ayi kazo gidan ka ga ba wuta. Gaba d'aya ma'aikata da su ke wajan su ka k'araso su na kwasar gaisuwa. Shi kuwa dattijo cike da fara'a da kamala ya ke amsa masu kamar ba ma'aikatan sa ba. Babu wani d'auke kai ko nuna isa irin na ubangida da bawan sa. "Baban Haruna, Soloman, D'an kwairo, Tanimu, ina fatan dai babu wata matsala ko?". Fad'in Alhaji Usman fuskan shi fad'ad'e da fara'a. "Yallab'ai babu matsalar komai wallahi". Gaba d'ayansu su ka amsa". Cike da farin ciki Alhaji Usman ya jinjina kai. Kallon Solomon ya yi, duk da yasan ya na jin wani hausan, sai dai mayarwan ne ke masa wuya. Don fita hak'k'i sai ya ce, "Is there any problem Solomon? If there's, fell free to say it". "No, no sir. There's no problem sir". Fad'in Solomon ya na girgiza kan sa. "OK. But have you eaten?". Alhaji Usman ya sa ke tambayan sa. "Yes sir. We are full". Jinjina kai ya sake yi ta re da mai da duban sa izuwa ga su Baban Haruna ya ce, "Ina fatan duk kun yi sallah, kuma kun ci abincin". "Eh yallab'ai. Mun yi sallah kuma mun ci abincin". Fad'in su Baban Haruna. "Alhamdulillah! Ba ri na k'arisa ciki". Fad'in Alhaji Usman ta re da yin gaba don duba sauran ma'aikata. Dama tuni motocin da su ka kawo shi sun yi ciki don sun riga da sun san da k'afa zai k'ariso. Sai ya duba ma'aikata sa kaf ya tabbatar da lafiyan su ya ke shiga ya ci abinci ya yi bacci. Yauwa sai da ya kwashi kimanin mintuna arba'in ya duba ma'aikatansa, sannan ya shiga main part d'in gidan. Da part d'in Hajiya Mansura matar shi ta biyu ya soma. Part d'in wacce ya ke d'akinta ne na k'arshe haka k'a'idar sa ya ke. Kullum sai ya duba lafiyar matan shi da y'ay'an shi kamin ya kwanta. Sallama ya yi ta re da murza key ta re da tura k'ofar ya shiga. Babu kowa a parlour kamar yadda ya yi tsammani. Sama ya hau. Ana ne ya d'an ji motsi a d'akin Hajiya Mansuran. Kwankwasawa ya yi ya d'an jira domin ta zo ta bud'e masa k'ofa. K'ofar aka bud'e, Wasila y'ar aikin Hajiya Mansura ta fito kanta a k'asa ta re da fad'in "Sannu da zuwa yallab'ai. Ina wuni?". Kallon ta ya yi daga sama har k'asa ka na ya girgiza kai ta re da fad'in, "Lafiya k'alau". Ya fad'i hakane ta re da shigewa d'akin Mansuran. Kwance ya same ta lullub'e da bargo har wuyanta. Zama ya yi a bakin gadon ta re da fad'in, "Mansura lafiya dai ko? Na ga ba sanyi ake ba amma kin lullub'e kan ki. In ce dai lafiya". Ya fad'i hakan ya na kallon ta. "Mtsw". Hajiya Mansura ta d'an ja tsaki ta re da fad'in, "Sannu da zuwa. Kai na ne ke d'an sara min, ga d'an zazzab'i da ke son kama ni". "Tashi maza muje asibiti". Fad'in Alhaji Usman ta re da mik'ewa. "A'a ba sai munje ba. Ba ka ga fitan Wasila ba, ai yanzu nasa ta ba ni magani da ruwa na sha. In sha Allah ka min safe zan warware". Fad'in Mansura. "Kin tabbata?". Fad'in Alhaji Usman ya na tab'a goshinta da ke sanyi k'alau ba alamar zazzab'i. Jinjina masa kai ta yi ta na k'ara jan bargo. K'ara gyara mata bargon ya yi ta re da manna mata kiss a goshi, ka na ya ce, "Ki yi addu'a ka min ki yi bacci. Allah ya k'ara ma ki lafiya. Sai da safe. Amma dan Allah ki rage saka Wasila aiki da daddare haka. Ai dare mahutan bawa ne. Kusan kullum fa da daddare sai na ganta a side d'in nan. Har tausayi ta ke ba ni wallahi".. "In sha Allah zan kiya ye. Allah ya ta she mu lafiya". Ta fad'i in a cool voice. Sai da ya kashe mata wutan d'akin ka na ya fito ta re da kulle mata k'ofa. Ya na fita ta saki ajiyar zuciya ta re da yaye bargon. Daga ita sai pant. Da sand'a ta fito ta re da bud'e k'ofar a hankali don ganin ko ya fice daga part d'in ta gaba d'aya. Shurun da ta ji ne ya sa ta koma d'aki ta re da d'aukar wayarta ta danna numbern Wasila da ke can d'akin ma'aikata mata. Wasila na d'aga wayar Hajiya Mansura ta ce, "Dawo maza-maza ya fice, kuma kar ki bari a gan ki". Ta na gama fad'in haka ta yanke wayar. Daga nan d'akin matar shi ta biyu ya nufa, wato Hajiya Huriya (Business woman kenan). Ita a parlourn k'asa ya same ta da uban kaya a gaban ta, gyefe guda kuma kud'ad'e ne sai uban lissafi ta ke yi. Ga uban y'an aiki a gabanta sai had'a mata kaya su ke yi su na saka wa a cikin wani kwali su na manne kwalin da salatep. Alhaji Usman na sallama, gaba d'aya y'an aikin nan su ka mik'e su na kwasan gaisuwa ta re da k'ok'ak'in barin parlourn. Dakatar da su ya yi ta re da fad'in ku yi zaman ku. Ni ma wuce wa zan yi yanzu". Komawa su kai su ka zauna su na kallon Hajiya Huriya da ko kallon Alhaji Usman d'in ba ta yi ba, sai faman lissafi ta ke yi. Murmushi Alhaji Usman d'in ya yi ta re da fad'in, "Barka hajiya y'ar kasuwa". Sai a lokacin ta d'ago da kan ta ta re da fad'in, "Ohhh sorry Alhaji, na bar ka tsaye ina ta faman lissafi. Kaya ne nai ordern su, shi ne su ka iso yau na ke dubawa". "Masha Allah! Allah ya kawo kasuwa. Babu wani matsala ko?". Fad'in Alhaji Usman d'in. "Babu". Ta fad'i ba ta re da ta kalle shi ba. "To sai da safe. Amma dan Allah ki d'an sallami bayin Allahn nan su ma su samu su huta. Dare mahutan bawa. Tun safe su ke aiki". "In sha Allah yanzu za mu gama su tafi su kwanta". Fad'in Hajiya Huriya. "Mu kwana lafiya". Fad'in Alhaji Usman ta re da ficewa daga d'akin ya nufi part d'in Suhail. Sallah ya tarar da shi ya na yi. Ja masa k'ofar ya yi ta re da furta Alhamdulillah cikin zuciyar sa. Daga nan kuma ya nufi in da ya ke wato d'akin Hajiya Na'ima. Ya na tura k'ofar wani k'amshi ya daki hancinsa sai da ya lumshe idanunsa. "Alhamdulillah, masha Allah". Fad'in Alhaji Usman ta re da k'ara bud'e k'ofofin hanci ya na shak'ar daddad'an k'amshin da ke fesowa daga cikin d'akin. Tsit d'akin ya ke. Babu kowa a parlourn k'asa. Kasancewar tu ni Hajiya Na'ima ta sallami y'an aikin ta. Saboda ba komai ta ke bari su ke mata ba. Musamman girki, har yanzu ita ta ke abunta da kan ta. Kuma babu girkin da ba ta iya ba. Daga na zamani har na gargajiyan. Sama ya nufa, nan ma sai da ya lumshe idanunsa saboda k'amshin ya fi wanda yaji a parlourn k'asa. Kallon dining ya yi da ke jere da kulolin abunci da kuma fruit. "Ke ta musamman ce Na'ima". Fad'in Alhaji Usman ya na nufar dining d'in. *BA NI DA GATA ISN'T FREE, PAY #500 THROUGH THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800, SAID ZULFAU GTBANK. SCREENSHOT YOUR EVIDENCE AND SEND IT TO THIS NUMBER 08128755583👆* *MRS SAYYADEE*✍🏻 🌹 *23-24*🌹 Bud'e kular farko ya yi, ya yi arba da favourite d'insa wato mashed potato da ya ji bushashshan kifi sai zuba k'amshi ya ke yi. Duk da daddare abinci light ya ke ci, sai da miyan shi ya tsinke da ganin mashed potato d'in nan. D'ayan kulan kuma zallar bushashshan kifin ne ta masa farfesun sa. Ko kad'an ba k'arni kasancewar gona ce wajan gyara kifi. Ga yankakkun fruits nan a k'aton tire dangin su apple, banana, pineapple, watermelon, grapes da sauran su. Grapes d'in ya d'auka ta re da sakawa a bakin sa ta re da lumshe idanuwa. Dai-dai lokacin Hajiya Na'ima ta fito daga d'akin su Fanan domin du ba su. Da murmushi ta k'ariso wajan ta re da fad'in, "Barka da dawowa Abu Julaibib. Ya gajiyan hanya?". Hajiya Na'ima ta fad'a ta re da k'ariso ta tsiyayi ruwa a dispensers ta mik'a masa har da d'an duk'awa. Karb'a ya yi ta re da fad'in, "Alhamdulillah Ummu Julaibib. Allah ya sa ka miki da alkhairi ya k'ara shirya miki zuri'ar ki baki d'aya". "Ameen". Ta fad'a ta re da jawo masa kujera ya zauna, ka na ita ma ta ja ta zauna ta re da soma serving d'in shi. Favourite d'in sa ta zuba masa ta re da mik'ewa ta kai har gabansa, ka na ta dawo wajan zamanta ta na kallon sa. Aje cup d'in ruwan da ke hannunsa ya yi, ta re jan kujera baya ya mik'ewa. Kallon shi ta yi ta re da fad'in, "Abu Julaibib lafiya ka tashi?". "Zan je na wanke hannu na ne. I preferred using my hand than spoon. Abunci ma ya fi dad'i wallahi". Alhaji Usman ya fad'a. "Please come back and sit. Ba ri na kawo maka bowl ka wanke hannun a ciki". Fad'in Hajiya Na'ima ta re da mik'ewa. Dawowa ya yi ta re da zama kamar yadda ta buk'ata. Ita kuma ta kawo masa bowl d'in ya wanke hannunsa ta re da yin bismillah ya soma ci. Ko loma hud'u bai ba, Barrister Fu'ad ya yi sallama a k'ofar parlour. Sai da Anna ta ba shi izinin shigowa ka na ya shigo shi ma ya ja kujera ya zauna ta re da fad'in, "Dad ina wuni? Ka dawo lafiya?". "Lafiya k'alau Barrister. Ya aikin?". Fad'in Alhaji Usman. "Alhamdulillah daddy. Anna ina wuni?". Fu'ad ya fad'a ta re da mai da duban sa ga Anna. "Lafiya k'alau. Have eating?". Hajiya Na'ima ta amsa ta re da tambayan sa. Shafa cikin sa ya yi ta re da fad'in, "I eat nothing since afternoon". Dariya Alhaji Usman ya yi ta re fad'in, "You better find a wife before your momma stop giving you her food". "Ohooooo, you better tell him". Fad'in Anna ta na dariya. "Hmm! Anna, I don't wanna rush my self. Women, now adays. Hmm sai dai alhamdulillah". "Son pray, in Allah, Allah will here you and give you a better one". Fad'in Alhaji Usman. "Ameen". Fad'in Fu'ad ta re da jawo plate ya zuba mashed potato ta re da bismillah ya soma ci. "Hmm, ana maganar Fu'ad, to ina ki ka bar shugaban gwagwaran Africa? Baban boko. Boko mu ka zo yi duniya. Muna nan da ke, ya na dawo wa, zai kuma cewa wani degree d'in zai sa ke yi a wani fannin daban. Degree biyar fa gare shi". Fad'in Alhaji Usman ya na kai farfesun kishi baki. "Hmmm, I'm tired of that boy, ina ga auran dole zan mishi. Tun da na ke ban tab'a ji ko a mafarki an ce ga budurwansa ba. Ina ga hatta Zaid da Suhail sai sun riga shi aure. Sai an Kai hotunan sa masallaci ka min ya samu matar aure. Don ma ya ci sa'a bai da jiki da fuskan tsufa ko kad'an. Wasu ma cewa su ke Fu'ad ne yaya". "Anna na gan ku a rana ke da Yaya bibi. Ke da ki ke backing d'in sa amma yau har da ke ake masa haka". Fad'in Fu'ad. "Na yi d'in. In dai a kan aure ne, mun dunga kenan. Mutun sai k'ara shekaru ya ke yi, amma ya zauna sai ya ga k'arshan biro. Mongol pack ma dai ya mutu ya bar boko, shi da ya k'irk'iri dictionary". Daga Alhaji Usman har Fu'ad dariya su ka saka. "Yauwa Anna, dan wannan y'ar kyakkyawar yarinya ta d'azu, d'iyar wacece?". "Y'ar aiki ce. Kandala ta ka wo ta d'azu da safe". Fad'in Anna. Shak'ewa Fu'ad ya yi ta re da jero tarurruka sai da Alhaji Usman ya ba shi ruwa ya sha. Tuni har idanuwan sa sun kad'a sun yi jazur saboda shak'ewar da ya yi. "Anna, y'ar aiki fa ki ka ce? Wannan y'ar yarinyar kuma wani aiki za a kawo ta yi? Ai kamata ya yi ta na gaban iyayanta ta na karatu. Wai meyasa wasu mutanan dai kamar dabbobi su ke ne? Dan Allah Anna ku dai na k'arban k'ananan yara idan an kawo maku su a matsayin y'an aiki. Wallahi wannan child abuse ne. Idan human right su ka ji wannan, Allah abun kai k'ara kotu ne a nai mo mata hakkin ta a wajan wad'and'a su ke kawo su. Kuma wallahi wasun su mostly iyayan su ba su sani ba". Fad'in Barrister Fu'ad kamar zai yi kuka. "Hmm, maganar da na ke son in yi da mahaifin ka kenan. Na yanke shawarar yarinyar za ta zauna da ni har ta kammala karatun ta ba bu wani maganar aiki. Domin akwai ciwon jahilci a kwakwalwar yarinyar da ma k'auyan su baki d'aya. Domin da kana nan d'azu ta ke min wasu irin tambayoyi, wallahi sai ka yi kuka. Sam ba su san addini ba, balle akai ga zancan boko. Alhaji idan ka amince min, zan yi magana da baabar ta wacce ta kawo ta aiki, a tambayan min iyayanta idan sun yarda zan rik'e ta har ta samu miji ta yi aure bayan ta yi karatu. Don wallahi yarinyar ta shiga rai na ba kad'an ba". Fad'in Anna ta na kallon Alhaji Usman. "In dai wannan ne ai ba matsala Na'ima. Haka nake so in ga kuna taimakon mabuk'ata. Allah dai ya sa ka mi ki da alkhairi. Ni kuma idan har iyayanta sun amince, zan biya duk wani abunda za ta yi har tai aure. Ita ma ta zama d'aya daga cikin family na ba y'ar aikin gida na ba". Fad'in Alhaji Usman. "Allah ya saka da alkhairi ya k'ara bud'i". Fad'in Anna da Fu'ad. "Ameen". Ya fad'a ta re da goge bakinsa da hannun sa da tissue ka na ya wanke hannun ya wuce bedroom d'in sa. "Idan ka gama ka tabbatar ka rufe min k'ofa". Fad'in Anna ta re da mik'ewa ta yi hanyar bedroom d'in ta domin ta kimtsa ta je wajan mijin ta. Bayan mahaifiyar sa na sa ya yi da idanuwa ya na jin wani soyayyarta na k'ara huda zuciyar sa. "Mummy like no other" Fu'ad ya fad'a ta re da goge hannunsa da tissue ya bud'e goran ruwa ya sha ta re da fita daga parlourn ya kullo k'ofar, haka ma main parlour ka na yai part d'in sa da ke gaban na Suhail. Sai da ya fara lek'a d'akin Suhail d'in ta window. Duk da ya kashe wuta, amma haske waje da ya haska windown sa, sai da ya sa ya gane shaye-shaye ya ke yi saboda hayak'in da ke fitowa. Girgiza kai ya yi ta re da shigewa side d'in sa ya kullo k'ofa. Wanka ya yi ta re da gabatar da shafa'i da wuturi, ka na ya hau gado ta re da kunna data ya hau WhatsApp ya d'an yi chatting kad'an saboda baccin da yaji ya soma cika masa idanuwa. Addu'a ya yi tare da kwanciya ya ja bargo. *WASHA GARI* Da asubar fari Anna ta je ta ta so su Fanan da Binty ta re da umartar su da su yi wanka ta re da d'aura alwala su gabatar da sallah. Binty kuwa a tsayin rayuwarta bata tab'a baccin mai dad'i irin wannan da ta yi ba a katifa mai laushi ga sanyin AC har yawo yaso ya mata don sai da ta ja bargo har kanta. Fanan d'in ce ta soma wanka ta re da d'auro alwala, ka na Binty ita ma ta je ta yi. Ta re su kai sallar, duk abunda Fanan ta yi, haka Binty ke yin. Sai wannan karan, wus wus wus, ta ke ta fad'i kasancewar ta ji sautin fitar karatun Fanan d'in sai ta yi tunanin haka ake cewa. Bayan sun idar, Fanan ta d'auko su ka shafa. Ka na Fanan d'in ta d'auko gogaggun uniform d'in ta, ta saka. Skirts d'in ta saka, ka na ta saka vest sannan ta saka rigar sama mai dogon hannu. Ka na ta d'aura suite d'in a sama ta re da b'ame botur. Ba k'aramin kyau kayan su ke ma jikinta ba. Ta je gashinta ta yi ta re parking d'in sa a tsakiya kamar yadda ta saba idan za ta school, ka na ta saka hula ta re da baby hijjab. "Fanan kin yi kyau a cikin wannan kayan". Binty ta fad'a ta na k'ara kallon kayan jikinta. "Ke ma kin kusa sa ka su very soon". Fad'in Fanan ta na saka white socks a k'afarta. "Dan Allah dagaske ni ma zan sa ka? Zan rik'a zuwa makarantar ku?". Fad'in Binty out of exited. "Sosai ma kuwa. Na yi wa Anna magana kuma ta ce za ta saka ki". Fad'in Fanan d'in ta na saka workbook d'in da ta yi assignment jiya a cikin Jakarta. "Na ji dad'i sosai. Ni ma zan shiga makaranta in rik'a yaren da ku ke yi da Anna". "Ke wannan yaran Anna ne ai. Fulatanci ne. Ku ma ke ma idan mu na yi a gaban ki a hankali za ki iya". "To ku rik'a yi dan Allah, ni ma na koya. Ko kuma idan za mu yi bacci, ki rik'a ko ya min". Fad'in Binty. "To shikenan, za mu fara daga yau idan na dawo school. Yanzu tashi mu je mu gaida Anna da Daddy". Fad'in Fanan ta re da yin hanyar k'ofa Binty ta mara ma ra baya. Part d'in daddy da ke sama su ka nufa. Kusan zan iya cewa parlourn sa ya fi duka parlourn da ke part d'in kyau da kuma tsaruwa. Zaune ya ke akan 1sitter ya na kallon BBC news, hannun shi rik'e d'an karamin cup irin na buzaye, amma na shi na glass ne mai kyau ya na sipping shayin da ya ji kayan k'amshi. A gaban shi a kan centre table flasks ne mai d'auke da shayi a ciki. Sai kwalin sugar cube a gyefe. Sallama su ka yi ta re da tsayawa a ba su izini tukun. Don k'a'idar Alhaji Usman ne sai ya ba ka izini ka min na shigo masa d'aki. Amsa sallamar ya yi ta re da ba su izinin shigowa. Fanan ta kama hannun Binty su ka shiga. Duk'awa Fanan ta yi, Bintyn ma ta duk'a kamar yadda Fanan d'in ta yi a gaban daddy da ke kallon su ya na murmushi. "Ina kwana dad?". Binty ma ta kalli daddyn ta re da fad'in abunda Fanan ta ce. Kallon Bintyn ya yi, domin yana nazartar ta. Domin jiya kusan raba dare su kai shi da Hajiya Na'ima su na magana a kan ta. "Lafiya k'alau daughters. Har kin yi shirin makaranta Fanan?". "Eh dad. Da 7:00am ya yi zan wuce. Breakfast kawai zan yi". "Masha Allah!". Daddy ya fad'a ta re da mai da kallon sa izuwa ga Binty ya ce, "Binty ya sabon waje? Hope kin ji dad'in zuwan ki gidan nan?". Kasancewar sauran maganar da Hausa ya yi, shiyasa ta fahimci mai ya ke nufi. Ta ba shi amsa da, "Eh dard (Dad). Na ji dad'i sosai. Mutanan gidan su na da kirki. Har da ya Fu'ad ba". Fad'in Binty ci ke da farin ciki. "In sha Allah za mu yi magana da wacce ta kawo ki nan, ta yi wa iyayanki magana KI dawo nan gaba d'aya da zama sai mu saki a makaranta ke ma ki yi karatu kamar yadda kowace yarinya mai gata ta ke yi. Ke ma ki samu wannan gatan. Kin ji". "Nagode dard (dad)". Fad'in Binty kamar ta taka rawa. Fanan kuwa sai k'umshe dariyar ta ke yi saboda yadda Binty ke pronouncing dad. "Ku ta shi ku je ku karya ka da ki yi latti. Seven d'in ta kusa". Fad'in dad ta re da sipping tea d'in shi. Tashi su kai yi ta re da fita su kai part d'in Anna. Gadon ta su ka taras ta na gyarawa. Don ita sam ba ta yadda y'ar aiki ta gyara mata d'aki ba. Babu y'ar aikin ma da za ta iya cewa ta san kalar d'akin. Da kan ta ta ke gyara d'akin ta. Sai idan weekend ne sai ta saka Fanan d'in ta wanke mata bayi da kuma gyara d'akin. Duk da kuwa kasancewar Hajiya Na'ima d'iyar k'anin Sarkin Gombe. Hakan bai sa ta d'auki d'abi'ar nan na komai baiwa ta yi maka ba. Kuma hakan koyarwa mahaifiyar su ce. Lokacin auran ta ma sai da aka gad'o ta da kuyangu kusan bakwai, amma ta ce ita ba ta so, bautan ubangiji ta zo ba zama a mata hidima ba. "Anna sannu da aiki. Ba ri na k'arisa gyaran gadon". Fad'in Fanan ta na k'arisawa wajan Annan d'in. "No bar shi ai na gama". Anna ta fad'a ta na shimfid'a bargo a gyefan gado. "Ina kwana Anna?". Fanan ta fad'a. Ka min Anna ta amsa, Binty ma ta ce, "Anna ina kwana?". "Lafiya k'alau yara na. Kun dai yi sallah ko?". "Tun da ki ka tashe mu ai ba mu ko ma ba. Mun yi sallah. Kuma yau ta re mu ka yi. Duk abunda na yi, shi ta yi ita ma. Yau ba daga sujada ta fara sallah ba". "Alhamdulillah! Ki yi ko ya mata, za ta iya a hankali. Yanzu mu je ku yi breakfast ki wuce makaranta, kar ki yi latti". "To Anna". Fad'in Fanan. "Anna dan Allah wanene kwana da yinin da kullum safe da rana sai in ji mutane da yawa su na nai man shi?". Fad'in Binty ta na kallon Anna. "Ban ga ne ba Binty, a ina ki ka ji a na nai man na su?". Fad'in Anna ta na kallon Bintyn. "To Anna d'azu munje wajan dard mun ce masa ina kwana. Yanzu ma mun zo mun ce miki. Kuma duk lafiya ku ke cewa. To shi kwanan ya na ina? Ba'a ganin shi sai dai ai ta nai man shi". Dariya ce ta kufcewa Anna da Fanan suka kuwa da ra sosai. Anna ta ce, "Rai dai Binty. In sha Allah idan Allah ya ara mana rai wata rana sai na tsokane ki da wannan tambaya ta ki. Yanzu ku je ku karya kun ji. Komai ya na nan shirye a dinning". Da to su ka amsa mata ta re da fita daga d'akin su kai wajan dinning da ke nan sama. Fanan ce ta had'a ma su tea d'in a cup ta turawa Binty na ta a gabanta ta re da chips. Sosai ta zuba mata chips d'in don ta ga ba laifi a kwai ta da ci. Bayan sun gaba me, Fanan ta goge bakin ta da tissue ta re da mik'ewa ta d'auko jakarta a d'aki. Wajan Anna ta koma ta re da mata sallama ka na ta dawo parlour ta sa mi Binty a kan 3sitter har ta yi bacci. Ficewa ta yi daga parlour ta sauka k'asa. Fasila ta ga ni rik'e da k'aton plate shak'e da abincin ta nufi hanyar fita daga parlour za ta koma side d'in su na maids. Fasila na jin takun tafiya duk ta daburce. Juyowa ta yi, idanuwan ta su ka sauka a kan Fanan ta na kallon ta. Guilty ya ka ma ta, ta ka sa magana sai yak'e ta ke yi. Fanan kuwa k'arasow ta yi ta gitta ta ta re da ficewa daga d'akin don ba yau ba ne na farko da ta kama Fasilan na ma su satan abinci, duk da kuwa ta san idan ta tambaya ba hana ta za'ayi ba. Driver ta sa mu a gaban side d'in su kad'an ya na jiran ta. Hango Suhail da ta yi ya na tahowa ya sa ta ari na kare ta re da saurin shiga mota ta na cewa driver, "Muje, muje please ka min ya iske mu ya kashe ni da safan nan". Jazuli driver kuwa ya yi wa mota key da sauri ta re da reverse ya nu fi gate. Hankalin Fanan bai kwanta ba, sai da ta ga sun fita daga gate d'in k'arshe (gate d'in Solomon) sun d'au hanyar school d'in su. Dogon ajiyar zuciya ta sa ki ta re da kwantar da kanta a jikin motar. *LEAD BRITISH INTERNATIONAL ACADEMY ABUJA* Tun daga tsarin gate d'in makarantar kawai mutum zai kalla zai tabbatar wa kan sa makaranta ce irin na y'ay'an ma su fad'a aji. Kyawawa kuma masu tsadar motoci ne ke parking a harabar makarantar su na sauke d'alibai wannan na wane wannan. Domin duk yarinyar da ka ga ni cikin makarantar to hak'ik'a ubanta wani. Registration d'in makarantar kawai 1m ne. Du term kuma 700 thousands. Cikin makarantar kuwa, tsaruwar ta ya fi gaban kwatance. Za ki rantse da Allah a k'asar waje ki ke ba Nigeria ba. Fanan da ce ta nuna IDcard d'in ta ka na ta shiga makarantar ita da k'awayanta su hud'u. Jamila Muhammad Giwa, Asiya Abdulwahab Girai, Rukayyah Adam Saje, da Salima Mustapha Yawale. Sai it's cikon na biyar d'in Fanan Usman Mai rabo. "Pinky, jiya an yi show a capteria lokacin ki na library. Na so na ba ki labari sai drivern ki ya zo da wuri". Fad'in Asiya Abdulwahab Girai. Wacce su ke kira da Girai to make the name short. "Mai ya faru? Na san ba zai wuce akan Cinderella ba. What did she do again?". Fad'in Fanan still tafiya su ke yi don zuwa assembly. "She slapped Fayrouz in the present of everybody". "What? Do you mean slap?". Fanan ta fad'a ta na shafa fuskan ta. "You de hell did she think is she. Wallahi a hate that girl with passion. She's so proud, just because she's beautiful". Fad'in Salima wacce su ke kira da yawale. Wa ni killer smile Binty ta sa ki ta re da fad'in, "Cool down babes, ba dai tak'amar ta kyau ba? Wallahi cikin Month d'in nan ko kuma next term sai na bata mamaki. Sai na kawar da taurarin ta da ke haske a makarantar nan". Fad'in Fanan ta na murmushi. "Wait Fanan? What are you planning for her. Dan Allah ka da ki watsa mata acid". Fad'in Ruk'ayya wacce su ke kira da Saje. "Allah ya kiyaye. Ban tab'a wannan tunanin ba. Amma dai just wait and see". Fad'in Fanan dai-dai lokacin da su ka is a assembly ground da kallon shi kad'ai ma ya isa ya rikita mutum. *BA NI DA GATA ISN'T FREE, IDAN KIN GA YA NA YAWO A GROUPS KUAM BA KI SIYA BA, DAN ALLAH KAR KI KARANTA. CONTACT THIS NUMBER 08128755583* 🌹 *25-26*🌹 *Bonus ✋🏻😂* *Naji k'orafe-k'orafen ku, to k'orafi ya karb'u. Na mai da Normal group #300, VIP kuma #500. Sai ki hanzarta ki bi ya ta wannan account numbern, 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK. Sai ki tura evidence d'in ki zuwa ga wannan number 08128755583* Sanye ta ke cikin suit kalar dark purple, sai na cikin shi kuma light purple, coat d'in rik'e a hannunta wanda ya kasance shi ma dark purple. Sai baby hijjab d'in da ke jikinta shi ma dark purple. Skirt d'in dai-dai gwiwarta. Sai fara k'al d'in safa da da ya wuce wuyan sahunta. Takalmin k'afarta mai bala'in kyau kalar dark purple. Jakarta light purple sagale a kafad'arta. Yadda ta ke wani shan k'amshi da wasu abubuwa, za ka rantse budurwa ce. Nan kuwa shekararta goma cikin na sha d'aya. Gaba d'aya k'awayan ta y'an koranta suna kusa da ita. Su su ke k'ara fasa mata kanta ta ke jin duk duniya ta fi kowa. "Cinderella, kalli can, yarinyar can Pinky ta zo. Kalli sai wani shan k'amshi ta ke yi". Wani d'ago idanuwan ta yi ta kalli pinkyn da ta ke jin k'ololuwar tsanarta duk fad'in school d'in nan na su. Ji ta ke da a ce Allah zai ce ta kashe mutum d'aya a duniya kuma ba ta da laifi, to tabbas za ta kashe Fanan. Kasancewar mahaifin Fanan d'in ya fi mahaifin ta kud'i. Da kaf school d'in mahaifin Sabrin ya fi kowa kud'i. Lokaci guda Fanan ta shigo makarantar. Kuma tun daga teachers d'in har students, shakkarta su ke yi saboda kud'in mahaifin ta da yadda ya yi su na a garin Abuja da ma wasu garuruwan. D'auke kai ta yi daga kallonta ta re da jan tsaki a bayyane ka na ta ce, "Don't ever show her face to me again. If not, you're out of this team". Fad'in Sabrin ci ke da gadara. "As you wish Ella". Fad'in k'awarta Saudat Lere. Bayan sun gama gabatar da assembly kowa ya tafi zuwa various classes d'in sa. Ajujuwan su kawai abun kallo ne. Ko wani d'alibi akwai laptop a gabansa da ke kan wani table. Ya yin da malami ke can sama shi ma da nashi laptop d'in a gaban sa. A haka ake masu karatun. Duk da akwai k'aton White board a class. Sai lokaci bayan lokaci ake masu amfani dashi. Musamma calculation subjects. Irin su maths da quantitative. ............Hajiya Nai'ma zaune da waya a hannunta ta na lalubo number Kandala. Da kyar ta iya gano numbern ta re da danna mata kira. Kandala da ke can kwance a kan k'atuwar katifat Datu k'awarta sai gwarti ta ke saki. K'arar wayarta ya dawo da ita duniyar mutane. A firgice ta farka ta re da laluban wayar ta danna madannin d'auka ta re da kara wayar a kunne ta ce, "Hallo". Cike da muryan bacci ta fad' hakan. "Assalamu alaikum". Fad'in Anna daga d'ayan b'angaran. "Ameen". Kandala ta amsa ta re da ware daga baccin da ta ke yi. Don ta ji muryan wacce ta kira ta bai mata kama da gajojin murya ba. Addu'a ta ke Allah ya sa samu ne. Don ba ta da number Anna. Annan ma ba ta tab'a kiran ta ba. "Ina magana da Kandala ne?". Fad'in Anna ta na k'ara gyara zaman ta. "Eh ita ce. Allah ya sa dai lafiya". "Lafiya k'alau ki kwantar da hankalin ki. Ki na magana da Hajiya Na'ima matar Alhaji Usman ne". Wani irin wuntsulowa ta yi daga kan katifar. Hantar cikinta ya wani irin murd'ewa waje d'aya saboda tsabar gigicewan da ta yi. Don duk a zaton ta asirin ta ne ya tonu. Su Hajiya Na'iman sun ga no ba ta da alak'a da Bintyn. "Na shiga uku ni Kande. Azabar son kud'i ne yau ya jawo min hukuncin kisan kai". Fad'in Kandala cikin zuciyar ta. Tuni har zufa ya jik'a ta. "Hello Kandala ki na ji na kuwa?". Fad'in Anna. "Hajiya dan darajar Allah wani laifin na yi? Ko kuma ita yarinyar ce ta mi ki wani abun?". Fad'in Kandala jiki na rawa. "Kandala na ce ki kwantar da hankalin ki. Ba ki yi komai ba. Asalima alkhairi ne. Idan ba damuwa ki zo yanzu ina nai man ki". Fad'in Anna ta re da katse wayar. D'aura hannu Kandala ta yi a kai ta re da rusa kuka kamar wacce aka ce mata uwarta ta mutu. Da gudu Datu ta shigo d'akin ta re da fad'in, "Ke Kandala lafiya ki ke kuka haka kamar an aiko miki Lami (Mahaifiyar Kandala) ta mutu?". "Ai idan Lamin ce ma ta mutu da sauk'i Datu. Kuka ne zan yi na kwana uku da jimami ya wuce da a ce gidan Alhaji Usman Mai rabo na tuhuma ta da sato y'ar mutane. Na shiga uku yai ni Kande. Yau zan had'u baba Shitu mahaifi gare ni ban gama jin dad'in duniyar ba". Fad'in Kandala ta na kuka har da fyace majina. "Ke ni fa wallahi wani lokaci haushi ki ke ba ni kamar na hau ki da duka. Ki min bayani dan Allah". Fad'in Datu da ke tsaye kan Kandala. Sai da ta k'ara fyace majina da bakin zaninta, ka na ta ce, "Datu, yanzu Hajiya Na'ima uwargidan Alhaji Usman Mai rabo ta kira ni akan in zo yanzu ta na nai ma ne. Duk da dai ta ce min in kwantar da hankali na ba matsala ba ce, wallahi hankali na bai kwanta ba. Sai na ke jin kamar k'ullalliya aka had'a min". "Mtswww! Wallahi ke sakaryace Kande. Ki ka sani alheri ne ke kiran ki tsiya na hana ki. To ni dai wallahi a nau shawarar ki je. Don irin wad'annan mutane ba k'ananan mutane ba ne. Ki cire tsoro kije wallahi ba bu komai. Amma fa idan kin ji. Idan kuma ba ki yadda ba, kar ki je ki yi wa kan ki". Fad'in Datu. "Ni gaskiya wallahi tsoro na ke ji, amma tunda kin ce haka, za ni. Amma dan Allah mu je ki raka ni". Fad'in Kandala. "Wa? Ni? Allah ya sauwak'e. Kin manta wani zuwa da ki ka yi da ni ke nan. Ai ban manta karo na da wanna shegen k'aton arnen da ke gadin k'ofar farko ba. Mai ya ke da suna, salaman ne ko Salemon? Oho. Wallahi ban zuwa. Kare fa ya sako mana. Uhmm wallahi a'a kam ba bu inda zani. Ke dai sai kin dawo". Fad'in Datu ta re da ficewa daga d'akin ta na k'ara maimai ta "Inahh". Fita Kandala ta yi ta je ba yi ta re da buga kwaskwarima ka na ta dawo ta d'auko bio-clear d'in ta ta mutstsika a jikinta da fuskanta. Sannan aka d'auko hota aka ranbad'a ta re da jan gira da kwalli. Fuskan nan ta fito ranba'dau kamar an shafawa jaki powder. Ka na ta bud'e ghana must go d'in ta ta fiddo brezia irin mai tsinin nan ta saka ta re da saka wata doguwar rigar atampa robber cotten irin na fita anguwan nan. Ta d'auko gyalan nan na ta tissue ta saka ta re flat shoe na roba da kuma latest jakarta ta rataya ta fito. Da ma tuni Datu ta bar gidan ta yi mak'ota don shan sigari kasancewar mai gidan ya hana shan sigari a gidan sa. Jawo k'ofar ta yi ta re da ficewa daga gidan. Sai da ta yi d'an tafiya sannan ta samu taxi. Nan ma sai da su ka kwashi kimanin mintuna talatin ka min su ka iso layin su Alhaji Usman. Gaban gate d'in ta nu fa gaban ta na fad'uwa don ba ta san abubda za ta taras ba a gidan. Kwankwasa gate d'in ta yi hannunta har ya na rawa. "Who be that?". Oga Solomon ya fad'a sai da gaban ta ya fad'i. "Na me Kandala". Fad'in Kandala bakinta har rawa ya ke. "U mean dat stupid old bitch way they bring small pikin to work here?". Fad'in Solomon. "Yes na me". Fad'in Kandala. Tsaki Solomon ya yi ta re da bud'e k'aramin gate d'in ya na kallon ta from head to toes. "Enter abeg. Use less human. God go punish you". Fad'in Solomon ta re da matsa mata ya na kuma fatan Allah ya sa kiran ta a ka yi domin ta mai da yarinya gaban iyayan ta saboda abunda ya faru jiya-jiya daga zuwan ta gidan. Sum-sum Kandala ta shige ta na hararar gaban ta ala dole da Solomon d'in ta ke da bai ma San ta na yi ba sai antaya mata zagi ya ke da yaran Ibgo ta re da d'ebe mata albarka. Side d'in Hajiya Na'ima ta nu fa ta na mai addu'ar Allah ya sa ka da d'aya daga cikin y'an aikin Hajiya Mansura su gan ta su je su shaida mata. Don kan ta ba zai iya d'auka matsalar ba. Sallama ta yi a parlour. Fasila da ke mopping ta amsa mata ta re da ce mata ta shigo. Shigowa ta yi ta re da zama a kan lallausar center carpet d'in d'akin har da tankwashe k'afa. Fasila kuwa, cigaba ta yi da goge-gogen ta. Don ba ta da damar haurawa sama idan ba izinin aka ba ta ba ta je ta d'auko wanki ta kai washing room. Shuru-shurun da Kandala ta ji ne, ya sa ta fiddo wayar wacce ake kira da sha k'idan ka bak'auye ta danna number Hajiya Na'ima kasancewar shine last call d'in da ta yi receiving. Sai da wayar ta kusa tsinkewa ka na Hajiya ta d'aga. Cikin sauri Kandala ta ce, "Barka Hajiya. Tun d'azu ina parlour". Fad'in Kandala har da rusunawa kamar Hajiya Na'iman na ganin ta. "Ok. Jira ni ga ni nan zuwa". Hajiya Na'ima ta fad'a ta re da katse wayar. Mintuna goma ta fito cikin kyakkyawan shiga. Sanye ta ke cikin doguwar rigar shadda d'in kin y'an Senegal da ya amshi jikin ta. Babu yadda za'ayi ka kalle ta ka ce ta kusa hamsin saboda sam kyawun jikinta da yadda ta ke gyara kan ta ya b'oye tsufan ta. "Yi hak'uri Kandala na barki ki na ta jira. Ba ri na sa a kawo miki abun tab'awa". Fad'in Anna ta re da kiran Fasila da ke kitchen. Cikin sauri Fasila ta k'ariso ta re da duk'awa ta ce, "Hajiya ga ni". "Had'o mata abinci da lemu ki kawo mata". Anna ta fad'a ta re da mai da duban ta ga Kandalan. "Ina kwana Hajiya?". Fad'in Kandala ta na wani russunar da kai k'asa kamar ta kirki. "Lafiya k'alau. Idan kin ga ma cin abincin ki min magana ta waya. Zan sauko sai mu yi maganar". Fad'in Anna ta re da mik'ewa daga kan kujera ta yi hanyar upstairs. Ajiyar zuciya Kandala ta saki dai-dai lokacin da Fasila ke ajiye mata yam bones da tea a gaban ta. Da ma ci ke ta ke da yunwa. Aikuwa ta cinye tas ta re da shanye tea d'in ka na ta d'auki wayarta ta re da danna numbern Hajiya Na'ima ta shaida mata ta ga ma. Minti biyar Hajiya Na'ima ta sauko hannunta d'auke da wayarta a kunnanta ta na waya. Har ta k'araso ta zauna ba ta gama wayar ba. Ta kusa minti goma ka min ta gama waya da babban d'an na ta Julaibib. "Yi hak'uri Kande, na barki ki na ta jira na". Fad'in Anna. "Ahh wallahiba komai Hajiya". Kandala ta fad'a ta na sunkuyar da kai gabanta ba fad'uwa. Don ta k'osa ta ji abunda ya faru Hajiyan ta kira ta. "Kandala ba komai ya sa na kira ki ba sai akan d'iyar ki Binty". Ta ke cikin Kandala ya ba da sautin k'ulululu. Ta kalli Hajiya ta re da fad'in, "Allah ya sa ba wa ni laifin ta miki ba". Fad'in Kandala a marairaice. "Babu abunda ta yi Kandala. Sai dai ni ne ke da wani buk'ata idan har iyayanta za su amince". Fad'in Anna ta na kallon idanun Kandala da ya yi fik'i-fik'i. "Hajiya faf'i buk'atar ki idan bai fi k'arfi na ba mai zai ha na in miki. Ai kin wuce haka a waje na". Kandala ta fad'a. "Kandala so na ke in rik'e Binty a waje na har in aurar da ita kuma ba matsayin y'ar aiki ba idan har iyayanta za su yarda. Kuma ka da su da mu, nasan kud'i su ka turo ta ta nai ma. Ni na yi alk'awarin duk wata zan rik'a ba ku dubu hamsin ku yi hidiman ku. Ni Binty kawai na ke so in rik'e in saka ta a makaranta domin ba aiki ba ne ya kama ce ta, karatu ne ya da ce da ita. Amma fa idan kun amince". Fad'in Anna. Hawaye Kandala ta so na yi tare da sharewa da k'asan rigarta ta na fad'in, "Hajiya Allah ya sa ka miki da alkhairi. Wallahi ban da bakin da zan iya miki godiya. Wannan yarinya da ki ke ga ni. Ni ce komai na ta, ni ce uwarta ni ce ubanta. Marainiya ce gaba da bayanta, k'ani na uwa d'aya uba d'aya ya haife ta. Tun ta na ciki yan bindiga dad'i su ka shiga k'auyan mu su kai kashe-kashe, a ciki har da mahaifinta da sauran y'an uwa na. Mahaifiyar ta kuma ta na haihuwarta Allah ya amshi abunsa. Tun daga lokacin ta ke waje na. Ni kai na a wannan kashe-kashen a ka kashe nawa mijin ga ni da marayu har shidda, idan kin ha'da Binty sun ka ma bakwai. Wannan dalilin ne ya sa mu ke yawon aikatau birni don mu samu muci abinci. Binty ce kawai ban tab'a kaiwa aikatau ba. Amma saura y'ay'a na mata hud'u duk su na aikatau. Mazan ne k'anana ke gaba na su ma kuma duk na saka su sana'a. Ita ma Binty ganin ta kawo girma ne, nan da shekaru biyu za ki ha manema sun fito. Shiyasa na turo ta nan domin ta yi aiki mu samu mu tattala kud'in ai mata kayan d'aki da su. Wayyo Binty marainiyar Allah". Kandala ta k'arisa maganar ta re da rushewa da kuka. Sosai Hajiya Na'ima ta ji tausayi ya ka ma ta. Yanzu "Kenan yanzu wannan yarinya ba dan Allah ya turo ta nan ba, da yanzu nan da wasu shekaru biyu masu zuwa aure za'a mata kenan da duhun jahilci a kan ta. Gaskiya dole ma yarinyar nan ta dawo waje na". Fad'in Anna cikin zuciyar ta, a zahiri kuma ce wa ta yi, "Allah sarki! Allah ya jik'an mahaifan ta da kuma mijin ki. Allah ya k'ara maku hak'urin rashi. Amma tabbas ku abin tausayi ne. Idan har za ki amince min, ina son Binty ta kasance a waje na. Sannan saboda marayun da ke gaban ki, na k'ara miki hamsin akan kud'in da zan ba ki duk wata sun zama dubu d'ari sai ki kula da sauran marayun da ke gaban ki, ki kuma sa ka su a makarantar islamiya da na boko. Don zama da jahilci bai yi ba". "Wallahi Hajiya in dai Binty ce na bar miki ita halak, malak. Wallahi na ba ki. Ai nasan gidan mutunci na kawo ta. Hajiya nagode, nagode Allah ya sa ka miki da alkhairi ya k'ara girma". "Ba bu komai Kandala, ai yi wa kai ne. Sannan duk wani abu da ki ke buk'ata ki min magana ka da ki ji kunya. Yanzu idan za ki tafi, zan had'a ki da kayan abinci, sai driver ya kai ki. Bintyn bacci ta ke yi, shiyasa ba ta zo kun gaisa ba". "Ai babu komai Hajiya, idan na sa ke zuwa ma gaisa ai". Fad'in Kandala cike da farin cikin riba biyu da ta sa mu. Kamar yarda Hajiya ta ma ta alk'awari, da za ta tafi ta had'a ta da babban buhun shinkafa foreign buhu hud'u, buhun semo guda hud'u, couscous katon biyu, taliya da macaroni katan uku-uku. Baban gwangwanin madara guda hudu, suger loka ashirin, mangyad'a rabin abod, manja ma haka. Sai maggi star katon biyu ta re da k'arin dubu d'ari. Haka aka loda mata a mota. Sosai Kandala ta b'arke da kuka harda fyace-fyacen majina. Ba kukan komai ta ke yi ba face na dad'i. Ta tabbatar wa kanta Binty sa'ar da alkhairin ta ce. "Dan Allah ki bar kukan nan Kandala. Duk wani abunda ki ke buk'ata ki ma ni magana". Fad'in Anna. "Nagode sosai Hajiya. Allah k'ara girma". Fad'in Kandala ta re da shiga mota driver ya ja ta re da kai ta har k'ofar gidan Datu aminiyarta. Ganin irin uban kayan abincin da ake ta shigowa da shi ne ya sa Datu fitowa k'ofar gidan don ganin waye zai bud'e shago sai idanuwan ta ya sauka akan Kandala ta na baiwa yaran da ke shigar mata da kaya umarni. Ai k'arisa fitowa Datu aka cigaba da shigar da kaya ta re da ita. Sai bayan sun shigar da komai d'akin Datun ka na Datun ta kalli Kandala ta re da fad'in, "K'awas ya na gan ki da sha tara haka?". "K'awa ai ni kaka ta ta yanke sak'a wallahi". Tu ni Kandala ta zayyane wa Datu duk yadda su kai da Hajiya Na'ima da kuma irin k'aryar da ta shatata wa Hajiyan. Sai dai ba ta fad'a ma ta ainahin yawan kud'in da Hajiya Na'ima ta ce za ta rik'a ba ta duk wata ba. "Kin ga abunda na ke fad'a miki ko? Da kin ma kan kin salalar tsiya wallahi. Ah gaskiya Kande kin shigo Habuja da k'afar da ma. Yanzun ya za ki yi da wad'annan uban kayan abincin?". Fad'in Datu. "Sayar da su zan yi, amma zan aje mana wanda za mu rik'a ci ai". Fad'in Kandala. "To ni kuma miye nawa kason a cikin dubu arba'in d'in da za ki rik'a karb'a duk wata?". Datu ta fad'a. "Zan rik'a ba ki dubu goma duk wata. Sannan zan rik'a ajiye dubu biyar duk wata na haya. Daga yanzu na d'auke miki biyan kud'in haya". Kandala ta fad'a. "Kai shiyasa na ke k'aunar ki k'awata. Hanzarta maza in raka ki ki sai do da kayan, kin san na fi ki sanin kan kasuwa. Kin san ni ai". Fad'in Datu. "Aiko dai bari in ta shi". Kandala ta fad'a. ..........Bayan Alhaji Usman ya dawo da daddare, Hajiya Na'ima ta shaida masa duk yadda su ka yi da Kandala. Shi kan shi sai da ya tausaya masu, kuma ya umarci Hajiya Na'ima akan duk wata idan ta zo karb'an kud'i, to a had'a mata har da kayan abinci ma'ishi. Sosai hakan ya yi wa Hajiya Na'ima dad'i. Tun daga wannan ranar Anna ta d'auki d'ammarar kula da Binty. Da kan ta ta ke koya ma ta wasu abubuwa na addini. Idan malam ya d'aura mata karatu, kullum Anna sai ta tsare ta ta yi ma ta karatun da malam d'in ya masu. Gyefe guda kuma, kullum da daddare dai sun yi bitan yaran fulatanci ita da Fanan. Kuma da ya ke Allah ya mata kwakwalwa, nan da nan ta ke d'auke abun. Gaba d'aya satin ta d'aya da zuwa, amma ta haddace suratul fatiha kuma babu kuskure. Ga ta da zak'in murya. Anna kuwa ko k'ofar parlour ba ta ba ri ta je balle ta fita waje Suhaila ko mahaifiyar sa su gan ta. Maganar boko kuwa, Anna ta ce sai first term, shekara mai zuwa kenan. Don so ta ke ta d'auko lesson teachern da zai koya mata karatu kwakwalwar ta ya bud'e tukun. Fanan ba ta ji dad'in haka ba, amma haka nan ta hak'ura. Anna ba'a nan ta tsaya ba, kasancewar gwana ce wajan girki, duk lokacin da za ta had'awa Alhaji Usman girki, da Binty ta ke zuwa ta yi ko mai a gabanta duk da dai ba ta tab'a ba ta wani abun ta yi ba. Don ranar da ta fara shiga kitchen da ita ta kunna gas. Binty rud'ewa ta yi ta re da fasa ihuu ta fita daga kitchen d'in da gudun. Ba k'aramin tsoro gas d'in ya ba ta ba. Da kyar ta yadda ta soma tsayawa a gaban gas d'in amma ta na d'ari-d'ari. Kasancewar ta na da tambaya, duk abunda ta ga Anna ta yi sai ta yi tambaya a kai, hakan ya sa ta ke sanin wasu abubuwa sosai ga me da girki. Don ko ruwa Anna ta k'ara a girki ko ta saka ingredients sai Binty ta tambaye ta miye dalili. Anna kuwa ba ta gajiya da ba ta amsa. Tuni har Anna ta samo mata lesson teacher mai su na Mashkur. Daga k'arfe 10-12 su ke karatun boko. Na islamiya kuwa k'arfe uku don sai Fanan ta dawo daga school saboda ta re ake ma su karatun kuma ana parlourn k'asa. Tuni Binty ta sa ki jikin ta kamar dama y'ar gidan ce. Fasila kuwa duk duniya ji ta ke babu wacce ta tsana kamar Bintyn. Don gani ta ke ita da ta d'au shekaru a gidan ba'a mata irin wannan gatan ba sai ita da ta zo jiya-jiya. Wannan dalilin ne ya sa ta ke jin haushin ta. ..........Zaune su ke a parlourn k'asa akan center carpet, Fanan na koya mata letter sound. Kasancewar tu ni ta iya ABCD har zuwa Z, yanzu letter sound ake koya mata. Sun kai letter p, sai dai Bintyn ba ta bambamce P sound da F sound. Fanan ta ce "Look Binty, kalli bakina, ki kalli yadda zan yi da ba ki ne. Shi F sound haka za ki yi ffffff kamar ki na hura abinci idan akwai zafi. Yanzu ki yi imaging, ina nufin ki d'auka kamar abinci ne a hannun ki, kuma akwai zafi, to hura abinci mu gani". Fad'in Fanan ta na kallon bakin Bintyn. Binty ta yi kamar yadda ta ce ta re da fitar da sautin, "Ffffffffff!". Ta na kallon Fanan d'in ko ta yi dai-dai. "Great! Haka ake fitar da sound d'in F. Kamar idan za ki ce flower, wanna sound d'in za ki sa a farko ba na P ba. Fffflower. Kin ga ne?". Fanan ta fad'a ta re da jann harafin F d'in "Fflower. Hakane ko?". Binty ta fad'a. "Yauwa Binty na. Haka ne. Sai kuma P sound. Shi kuma kamar za ki hure candle haka za ki yi, 'puff' haka. Kin ga ne. Ba ri na ba ki misali da pencil. Pa fencil ake cewa ba, pp pencil. Yan zu kin ga ne bambamcin?". "Eh nagane Fanan. P, pencil, sai Ffff flower". Fad'in Binty. Rungumeta Fanan ta yi ta re da fad'in, "Wallahi za ki yi k'ok'ari sosai. Ki na da saurin fahimta". Anna da ke zaune can gyefan su ta na jin su, kuma ita ma ta lura Binty na da saurin fahimta, tun da ko wajan girki yanzu ta na barin ta ta dafa indomie da kuma white rice, duk da ta na gyefe ta na kallon ta saboda sharrin gas. Kuma alhamdulillah ta iya. Tun ta na shinkafar ta na cab'ewa, har ta iya sosai. Ta ma fi Fanan shiga kitchen saboda ita ta na gida ba makaranta ta ke zuwa ba, shiyasa su ke samun ishashshan lokacin da Anna. Barrister Fu'ad ne ya yi sallama ta re da knocking, Fanan ce ta bud'e ta je ta bud'e masa k'ofa. Ta na ganin sa ta rungume sa. Ita ma Binty ta ta so da gudu ta je ta masa oyoyo........ *SORRY IDAN KIN GA TYPING ERROR, MATSALAR KEYBOARD NE KUMA BA NA EDITING*🙏🏻 *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *27-28*🌹 Rungume su ya yi su duka ta re da manna ma su kiss a goshi. Ka na ya rik'o hannunsu ta re da k'arasowa wajan da Anna ta ke ya ce, "Anna ina wuni?". Ya fad'a ya na zama a k'asa. "Lafiya k'alau. Yau ba aiki ina ka je?". Anna ta fad'a. "Wallahi na je wajan Muhammad. Ya na ta min tsiya wai ban tab'a zuwa gidan sa ba. Kin san fa ba dani aka kai sa ba. To shine na je yau". Fad'in Fu'ad. "Ma sha Allah, to ya ka baro su?". Anna ta san ke tambaya. "Duk su na lafiya". Fu'ad ya fad'a ta re da kwanciya akan center carpet. "Ya barrister alk'awari na fa?". Fad'in Fanan ta na kallon Fu'ad cike da shagwab'a. "Kin fa ra ko? Alk'awarin mai na miki kuma?". Fu'ad ya fad'a ta re da k'ara gyara kwanciyar sa. "Yaya ba kai ka ce za ka kai ni shopping during weekend ba. Kuma yau Saturday". Fad'in Fanan. "Aikuwa ya Fu'ad haka ka ce ina wajan. Ni ma kuma ka ce idan har na iya nasi babu kuskure za ka siya min irin rigunan Fanan da cak'ulet". Fad'in Binty. "Ke dallah chocolate ake ce wa ba cak'ukate ba. Kar ki fara ba ni haushi mana". Fad'in Fanan ta na hararar ta. "Eh to shi, haka ka ce wallahi". Binty ta fad'a. "Ohhh Allah! Wai mi ya sa ba ku da mantuwa ne? To yanzu ya kuke so a yi?". "Ai kawai ka tashi mu tafi yanzu". Fad'in Fanan. "To uwar san yawo, to ba bu inda za ku". Anna ta fad'a. "Anna dan girman Allah ki yi hak'uri. Ya Fu'ad ka sa ka ba ki". Fanan ta fad'a ta na rik'o hannun Fu'ad d'in kamar za ta yi kuka. Shi kuwa Barrister Fu'ad har wani k'ara kwanciya ya yi ta re da lumshe idanu don da ma ba son fitar ya ke yi ba. Muryanta ya ji dai-dai cikin kunnan sa ta na fad'in, "Ya... Bar...rister, please ka sa ba ki". A hankali ya bud'e idanunsa ta re da saukewa a cikin na ta da ita ma ta zuba masa fararar idanuwan ta da su ke kamar zaiba a marairaice. "Har da ke Binty? Ba kya so Yayan ki ya huta ko?". Fu'ad ya fad'a shima a shagwab'e. "Yaya dan Allah". Fanan ta sa ke fad'i. Kamar had'in baki a ta re su ka kama hannun shi su na jijjigawa su na fad'in, "Yaya dan Allah, yaya dan Allah, yaya dan Allah". Sai su ka mai da abun kamar wak'a. Kallon Anna ya yi ta re sa fad'in, "Anna please ki yi hak'uri mu je, idan ba haka ba wad'annan yaran ba za su bar ni na huta ba, a can k'orafin mutane su ishe ni, anan kuma na su ya ishe ni". Kallon shi Anna ta yi ta re da fad'in, "Sai kun dawo, amma ka da Ku dad'e. Sannan ka tabbatar ka dawo min da su har cikin d'akin nan". "In sha Allah Anna. Sai Ku ta shi Ku je ku shirya mu ta fi". Ya k'arisa maganar ta re da mai da duban sa izuwa ga Binty da Fanan. Cike da farin ciki su ka kwasa zuwa sama. Dama sun yi wanka. Fanan ta yi wa Binty kwalliya ita ma ta yi wa kan ta. Ba k'aramin kyau su ka yi ba, musamman ma Binty da ke sanye da doguwar riga english wears kalar purple da tatsin fari. Sai ta ba ta farin takalmi mai d'an tudu ta re da farin baby hijjab bayan ta nad'e mata gashin ta a tsakiyar kan ta. Ita kuwa pink riga da wando ta saka. Sun yi kyau sosai. A ta re su ka sauko. Gaba d'aya idanun Fu'ad ya koma kan Binty ya na yaba irin kyawun da Allah ya yi mata. "Anna sai mun dawo". Fad'in su Binty ya yin da su ka nufi k'ofa. "To iyayanta zumud'i Ku dawo nan. Shi ko mik'ewa bai yi ba, amma kun saka kai za Ku fita. In ga wata ta saka k'afa a waje in karya k'afar". Fad'in Anna ta re da mai da duban ta izuwa ga Fu'ad ta ce, "Yarda za ku fita tare, haka na ke so ku dawo cikin d'akin nan ta re. Ka ji ni ko". "Yes Anna". Fad'in Fu'ad ta re da mik'ewa y kama hannun Fanan da Bintyn su ka fito. Kicibis su ka yi da Suhail as usual sanye da 3quarter da arm less, wuyan shi kuma wata shegiyar sark'a ce har ciki kamar kare. Ga uban gashin nan da ya tara tsaf mace za ta kitse shi. Shi kan shi 3quartern an zazzago shi k'asan d'uwawu sai wa ni tafiya ya ke yi yan bouncing. Cak ya tsaya ya na k'arewa Binty kallo. Binty kuwa ta na had'a idanuwa da shi ta koma bayan Fu'ad ta ri'ke masa rigar sa jikinta har ya soma rawa. Zagayo da ita gaban shi ya yi ta re da fad'in, "Kwantar da hankalin ki, ina wajan ai. Babu abunda ya isa ya miki". "Sai dai idan ban yi niyya ba". Fad'in Suhail ciki-ciki yadda Fu'ad d'in ba zai ji ba. "Gidan uban wa za ka je kamar d'an arna?". Fu'ad ya fad'a a fusace. "Ahhhh, ni fa ba mace ba qur'an ba bu wanda ya isa ya takuran. Ai ba gadi na aka baiwa mutum ba. Kowa ya yi rayuwar sa. Ba ruwan ka da ni". Suhail ya fad'a cike da gungunai. "Uban mai ka ke cewa dan uban ka?". Fad'in Fu'ad ya na zazzaro masa idanuwa. Shafa k'eyarsa ya yi ta re da juya idanuwan sa gyefe. "Idan ka ce kai d'an iska ne, to in dawo gidan nan ban sa me ka ba. Ni kuma sai na nuna maka d'an guguwa ne ni. Dan iska kawai". Fu'ad ya fad'a ta re kama hannun Fanan da duk ita ma a firgice ta ke su kai parking load. Dai-dai lokacin motar Mansura mahaifiyar Suhail ta danno kai, k'awarta na gyefan ta. A parking space d'in su ka yi parking. K'awar ta ta ce ta soma fitowa, idanuwan su ka sauka akan na Binty da ke yi wa Fanan magana ta na dariya. Kyawun ta ya bayyana sosai, ga lob'awar da kumatun ta da su ka yi duka biyun. Ga shi ta wani d'age girar ta d'aya. "Ya subhanallah! Inna lillahi. Zan mutu yau ni Zuwairah! Wannan kyakkyawar yarinyar fa?" Fad'in k'awar Hajiya Mansura ta na k'ara k'arewa Binty kallo. Hajiya Mansura ce ta fito daga motar ta na kallon inda Mansuran ta ke kallo. Cikin second 1 ta yi kicin-kicin da ranta ta re da watsawa Hajiya Zuwairah harara wacce ba ta ma San ta na yi ba, domin tuni ta mai da duban ta ga Binty da har ta shige mota. Shi ma kuma Fu'ad dakatawa ya yi daga shiga mortar kasancewar ya ga Hajiya Mansuran da k'awarta. K'arasawa ya yi inda su ke ta re da fad'in, "Sannu da zuwa Hajiya, ina wunin ku". Yak'e Hajiya Mansura ta yi ta re da fad'in, "Lafiya k'alau the great Barrister. Ya fama da jama'a?". Murmushi ya yi ta re da fad'in, "Alhamdulillah Hajiya". Fu'ad ya fad'a ta re da satar kallon k'awar Hajiya Mansurar da ko kallon shi ba ta yi ba saboda Binty da ta tafi da imanin ta. Juyawa Fu'ad ya yi ta re da komawa wajan mota ya bud'e ya shiga ta re da reverse ya bar wajan. Ajiyar zuciya Hajiya Zuwairah ta sauke ta re da fad'in, "Mansura ina kuka samu kyakkyawar yarinya haka? Wallahi ta yi min. Ki shigo da ita harka mana. Wallahi zan biya ko nawa ne. Kuma zan iya sacrificing komai a kan ta wallahi. Kallon ta kawai da na yi, dai da zuciya ta ta buga da k'arfi. Wani irin mugun sha'awar ta na ke ji wallahi". Wani harara Hajiya Mansuran ta jefe ta da shi ka na ta ce, "Wallahi, kin san ko no wacece. Kin san abunda zan iya yi akan duk abunda na ke so. Saboda haka, ki fita harkan wancan yarinyar domin ta wa ce. Ina nan ina babban shiri a kan ta, don auran ta ma zan yi. Zan kula da ita, zan ba ta rayuwar da ba ta tab'a tunanin shi ko a cikin mafarkin ta ba. Don haka ki had'iye miyan ki ka da ya jawo miki bak'untan lahira. Ke kin san mace ko namiji ba su isa su had'a kishi da ni ba akan abunda na ke so. Na rantse da girman Allah duk wanda ya yi k'ok'arin shiga tsakani na da wannan yarinyar duk yadda mu ke da shi, ke ko da kuwa d'an ciki na ne, wallahi sai na kashe shi. Ko wad'annan matan da ki ke ganin mun had'a miji da su, wallahi na kyale su ne kawai saboda ba mijin ba ne a gaba na, kuma da ma aurar na yi shi ne kawai don gudun zargi. Don Zuwairah ka da ki saki ki nai mi shiga gona ta. Don duk yadda mu ke da ke, zan d'au tsatstsautar mataki a kan ki wallahi. Ba bu ruwan ki da Binty". Hajiya Mansura na gama fad'in haka ta yi hanyar part d'in ta. Hajiya Zuwairah kuwa, wani killer smile ta sa ki ta re da jijjiga kan ta, ka na ta bi bayan Hajiya Mansuran. Da d'an gudu-gudu ta had'a saboda hajiyan ta yi ma ta nisa. Har bedroom ta bi Hajiya Mansuran da sai cika ta ke ta na batsewa. Gyalan jikin ta ta cire ta re da wurgi da shi a kan gadon. Ka na ta jinginar da kan ta a jikin gadon ta re da lumshe idanuwanta ta na ganin fuskan Binty na mata gizo a cikin idanuwanta. K'arasowa Hajiya Zuwairah ta yi ta re da hawa gadon ta kwanto kan hajiya Mansuran a cinyarta ta na shafa kanta ta re da fad'in, "Allah ya huci zuciyar shugaba, ki yafe ni akan abunda ya faru d'azu. Kuskure ne, ban san ta ki ba ce. Don Allah ki yi hak'uri. Yarinyar ta ki ce ke d'aya. Mai nai man kula ta mace ko namiji, ni da kai na zan ta ya ki yak'i a kan su. Yarinya kamar kin aure ta kin gama". Fad'in Hajiya Zuwairah ta na shashshafa jikin Hajiya mansuran. Wani irin mik'a Hajiya Mansura ta yi, domin ji ta ke kamar Bintyn ce ke shafata. Rungumo Hajiya Zuwairan ta yi ta re da had'e bakinsu. Hajiya Zuwairah kuma ta saka hannu ta zuge zip d'in rigar hajiya Mansura ta re da cire rigarta. Nan su ka fad'a duniyar halaka. Sai bayan sun gama iskancin su ne, sannan Hajiya Mansuran ta tashi ta isa wajan fridge d'in ta tare da bud'e shi da key ta d'auko kwalbar Brandy da cup su ka yi ta sha, sai da su ka yi mak'il ka na su ka zube su na bacci. *SSS SUPER MARKET* Parking ya yi a wajan aje motoci, ka na ya fito ya bud'e gidan baya kasancewar duk su na gidan baya. Fanan ce ta soma fitowa, ya yin da Binty ta biyo ta a baya. Hannunsu ya rik'o su ka nufi cikin tangameman super market d'in Mai su na SSS ( *SABRIN SAIFULLAHI SAKNA*). "Kun san dai Anna ta ce ka da mu dad'e ko? Saboda ko wacce ta zab'i abunda ta ke so cikin sauri, ban san b'ata lokaci da nawa. Idan ba haka ba zan k'ara zuwa da ku shopping ba". "Yes ya barrister". Fad'in Fanan. Ciki su ka shiga wanda tsaruwar sa kawai b'ata baki ne. Fanan ta rik'o hannun Binty su ka d'auko d'an kwandon nan da ake tura kaya su ka nufi wajan chocolate. A wajan kawai sun kwashi chocolate ya kai guda hamsin, ka na su ka nufi wajan biscuit irin manya-manyan nan na kwali, nan ma su ka jida. Ka na su ka koma wajan teddies. A nan wajan kuma Fanan ta ji di ya kai goma irin manya-manyan nan. Kallon Binty ta yi da ta tsurawa wani elephant idanu da aka masa kwalliya da wani irin kyalkyali mai kyau. "Ki na so ne?". Fanan ta tambaye ta. Gyad'a mata kai ta yi. Fanan d'in ta ce, "To. D'auko mana, ai Yaya barrister ya ce mu d'auko duk abunda mu ke so. Yi sauri mu tafi ka da mu dad'e.". Binty ta nu fi wajan, dai dai lokacin Sabrin ta taho ta ga ba da cikin kyakkyawar gown red colour shwaraski stones mai kyalkyali. Kan ta ya sha gyara sai kyalli ya ke yi. Ta ka ma gashin nan a can gaban kai irin yadda y'an China ke yi. Ga wani dogon takalmi da ke k'afarta. Sai tafiya ta ke yi kamar za ta karye don yanga da yauk'i bakin ta na taunar cingam k'as, k'as, k'as kamar karuwar titi. Bangaje ta Binty ta yi ba ta re da ta lura da ita ba sai da ta fad'i k'asa ta yi zaman y'an bori. Ita kuwa Binty duk da ta bige ta, ba ta bi ta kan ta ba, burin ta kawai ta je ta d'auko wannan elephant d'in. Fuskan Sabrin kuwa har ja-ja-ja ya yi saboda tsabar fushi da b'acin rai. Wani irin mik'ewa ta yi ta re da finciko rigar Binty ta ba ya ta yar da ita a k'asa. Ta d'aga hannu kenan za ta d'auke ta da mari idanuwan ta ya sauka akan kyakkyawar fuskan Binty. Lumshe idanuwa Binty ta yi ta re da bud'e su a lokaci d'aya, sai hakan ya k'ara bayyanar da tsantsan kyawun ta. Gaban Sabrin d'in ya buga da k'arfi. Ta ke ta ji hannunta da jikinta na wani irin rawa. Sai kallon fuskan Bintyn ta ke yi without blinking. Fanan da tun sanda Binty ta bangaje Sabrin tai Sabrin b'oyewa don ta san tabbas idan har Sabrin su kai idanuwa hu'du da Binty sai ta ji zawo saboda kyawun ta. Dole ta muzanta don a yadda ta ke kururuta kyawun ta Bintyn ta fita sau hamsin. Cike da bak'in ciki, kishi, b'acin rai, zafin zuciya ta re da hassada ta nu na Binty da yatsa bakinta har rawa ya ke yi wajan furta, "Uban waye uban da ya haifi uban ki a k'asar nan da za ki bangaji d'iyar Alhaji Saifullahi mai Naira? Shin ba ki san gaba d'aya wannan wajan da ki ke na uba ba ne? Duk'a k'asa ki ba ni hak'uri ko in yi k'asa-k'asa da ke ko kuma in saka bodyguard d'ina su ba wa karnukan su ke su yi yaga-yaga da namar jikin ki a cikin nan wajan". "Ban san abunda na miki ba da zan ba ki hak'uri. Anna ta ce min ya na da kyau idan har ka yi wa mutum laifi ka ba shi hak'uri. Ki fad'a min abunda na miki sai in ba ki hak'uri kin ji". Wani haske Binty ta ga ni ya gilma ta fuskanta sai da ta yi saurin dafe kuncin ta saboda azababbar zugin da ta ji a wajan. Fanan da ke lab'e sai da ta zaro idanuwa jikin ta ya soma rawa domin ta san Binty ba ta san miye fad'a ba, domin ba za ta tab'a iya rama abunda Sabrin d'in ta mata ba. K'ok'arin fitowa ta soma yi daga mab'uyar ta domin ta isa wajan da su ke. K'amewa ta yi k'am, mamaki ya cika ta ta re da zaro idanuwan ta sakamakon wani irin mik'ewa da Binty ta yi ta d'auke fuskan Sabrin da mari ta re da fad'in, "Bazan d'auka ba. Anna ta fad'i min ka da na saki na zalinci wani, kuma ka da ba bari a zalince ni. Na tambaye ta menene zalinci, kuma ta min bayani. A bayanin da tai min, irin wannan abun da ki ka min yanzu, zalinci ne. Duk da Anna ta ce min in kasance mai hak'uri da juriya, amma ba zan iya hak'uri da wannan abun da ki ka min ba shiyasa na rama. Da kin fad'a min abundan na miki, da ni kuma zan ba ki hak'uri kamar yadda ki ka buk'ata. Ko yanzu ma ki ka fad'a min abunda na miki, zan ba ki hak'uri". Fad'in Binty ta na kallon cikin idanun Sabrin da ta mutu da mamaki. Domin idan aka cire mahaifiyar ta, babu wani mahaluk'in da ya tab'a saka hannu ya mari fuskan ta sai wannan yarinyar da ke gabanta da ta ke jin tsantsar tsanar ta har cikin b'argon ta. "Binty, mai ki ka tsaya yi a nan wajan? Kun manta abunda na fad'a muku ko? To zo mu wuce. Ina Fanan d'in?". Ya Fu'ad ya fad'a. Saurin juyowa Binty ta yi ta re da nufo in da ya ke ta ce, "Yaya anan na bar ta, ban san in da ta yi ba". Fad'in Binty ta na waige-waige. Fanan na jin su, sai da su ka yi d'an nisa ka na ta kalli Sabrin da har a wannan lokacin ta na rik'e da kuncinta idanuwan nan na ta ya kad'a ya yi jazurr. Cikin sand'a Fanan ta bi bayan su Binty ba ta re da Sabrin d'in ta gan ta ba ta na jin wani irin farin ciki ya mamaye zuciyar ta saboda yadda Binty ta wanke fuskan Sabrin da mari. Sabrin da ke tsaye kamar statue kuwa, ji ta ke kamar ta k'ona kan ta a wajan da ta ke. Abubuwa sun had'u mata goma da ashirin. Ga wanke fuskan ta da mari da Binty ta yi, ga kuma tsananin tashin hankalin da ta ke ciki na ganin wacce ta ninninkata a kyawu. Wani irin k'ara ta saki mai k'arfi wanda ya saka hankalin mutane dawowa gare ta, wasu kuma da gudu suka nufo inda ta ke........... *DAN ALLAH KU YI HAK'URI DA RASHIN JI NA JIYA. GAJIYA CE WALLAHI. GA SUNAN DA MU KA SHA NA YA TA, GYEFE GUDA KUMA JIYAN OGA NA YA DAWO DAGA TAFIYA. SHIYA BAN MUKU TYPING BA. AMMA GA WANNAN DAI KU YI HAK'URI DA SHI* *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *29-30*🌹 .........."Lafiya Sabrin, what happen?". Amrah y'ar wajan aunty Junaina ta tambayeta. Yayin da Hanan tagwainiyar Amrah ta tab'e baki ta re da kallon gyefe. Bodyguard d'in da aka had'o su da ita kuwa, tuni har sun zagaye ta su na tabayarta abunda ke faruwa. "Take me homeeee". Sabrin ta fad'i a tsawace kamar tana magana da sa'o inta. Dogon tsaki Hanan ta ja ta re da yin gaba. Amrah ta bi bayan ta, ya yin da bodyguard su ka yi gaba, wasu kuma su ka tsaya a bayanta ita kuma ta kasance a tsakiya har wajan katuwar ranger over bulletproof. Bud'e mata su ka yi ta shiga gaban baya. Dama y'an biyu ba mota d'aya su ke shiga da Sabrin ba, komai na ta daban ne. Ba ta yarda ai mata abu iri d'aya da su ba. Ta na shiga cikin motar ta b'arke da kuka ta re da had'e kai da gwiwa. D'agowa ta yi ta re da shafa kumatunta ta furta, "She slapped me". Ta fad'i hakane ta re da k'ara rushewa da kuka. "Wallahi sai na nai mo yarinyar nan na ga uban da ta ke tak'ama da shi, sai na lalata fuskan da ta ke tak'ama da shi in kuma yanke hannun da ta yi amfani da shi ta tab'a fuska ta". ..........."Ai kun yi na farko kun yi na k'arshe. Ban k'ara fita da ku. Kun san dai Anna ta ce ka da mu dad'e, shi ke Fanan har da shigewa wani wajan muna ta nai ki". Fad'in Yaya Fu'ad ya na gallawa Fanan harara. "Sorry bro, wani tedy na je nai ma". Fad'in Fanan. "Tedo ba tedy ba. Ai gobe ma rana ce yara". "Yi hak'uri yayan muuuuuuu". Fad'in Binty a cikin kunnen sa da k'arfi sai da ya saka kafad'arshi ya toshe kunne d'aya. "Binty za ki cire min kunne ne? To na ji na hak'ura tun kan ku sa ni hatsari. Koma ki zauna". Fad'in Yaya Fu'ad. Ko ma wa Binty ta yi ta zauna ta re da d'aukar chocolate ta b'are ta saka a baki. Can kuma ta gutsiro chocolate d'in ta sai saitin bakin Fu'ad ta re da fad'in "Eat bro". Ta fad'i hakane ta re da tura masa chocolate d'in a baki. "Iyyeeeeeh, k'anwata ta iya turanci. Ahh lallai. Idan har ki na k'ok'ari haka, to na miki alk'awari duk weekend sai na kai ki shopping. Ki yi k'ok'ari ki iya turanci". Fad'in Yaya Fu'ad. "Yaya ni kuma na maka alk'awari zan ko yi turanci har in fi Fanan iyawa ma. Ai Fanan za ki koya min ko?". Ta k'arisa maganar ta re da kallon Fanan d'in. "Zan ko ya miki amma sai ni ma Yaya ya min alk'awari ta re zai rik'a kai mu shopping d'in". Fad'in Fanan ta na gutsirar chocolate. "To shikenan. Idan har ki ka yi k'ok'ari ki ka koya mata ta iya da kyau, to ta re zamu rik'a zuwa shopping d'in". Fad'in Yaya Fu'ad. "I promise daga yau zan fara koya mata. Magana ma mun dai na yi da hausa, daga turanci sai fulatanci". Fad'in Fanan. "Yauwa y'ar k'anwata. Ke kuma Binty sai ki dage kin ji". "To Yaya zan dage". Fad'in Binty. Haka su ka yi ta hira har su ka iso gida. Kamar yadda Anna ta ce, haka ya yi, sai da ya kai su har sama cikin d'akin ta, ka na ta fito ya koma na shi side d'in domin yai wanka ya d'an huta. Da daddare bayan Anna ta shigo as usual ta duba su ta fita ta re da rufo masu k'ofar. Fanan ta ta shi zaune ta re da kira sunan Binty. Ita ma Bintyn ta shi zaunen ta yi ta re da fad'in, "Fanan mai ya faru?". Binty ta fad'i ta na tab'a jikin Fanan d'in. "I saw what you did a cikin shopping mall d'in nan. Kin mari yarinyar nan. Na ga ni ai". Fad'in Fanan ta na kallon Binty duk da ba haske a d'akin don Anna sai da ta kashe wutan d'akin ka na ta fice. "Ai ita ta fara mari na ban san mai na mata ba. Kuma Anna ce ta ce min ka da na yarda a cuce ni". "Ai ni ma ban ce kin yi laifi ba, da ma na tsani yarinyar wallahi. Sam ba ta da kirki bare mutunci". Fad'in Fanan. "Kin san ta ne Fanan?". Binty ta tambaye ta. "School d'in mu d'aya da ita. In fact ajin mu d'aya da ita. Ni ina gaba, ita kuma ta na baya. Ina fad'a miki yarinyar sam ba ta da kirki. Ga nu na isa da mulki kamar d'iyar sarauta. Ko Anna da ke jinin saurata ba ta irin abunda ta ke yi. Ko fa siblings d'in ta hake ta ke masu. Hmm Sabrin, she's very wicked. Ai na k'osa ki shiga makaranta. Na san za ki samu fans da yawa fiye da ita". "Miye fans?". Binty ta tambaya. "Masoya mana". Fad'in Fanan. "Ni ma na k'osa in shiga makaranta in dai na zama a gida. Ina so in yi karatu sosai in zama kamar Yaya Fu'ad". Fad'in Binty. "Lawyer ki ke so ki zama kenan? Ai ya Fu'ad barrister ne. Shi ma law ya karanta ai. Big bro kuma ya karanta Medicine. Kuma har yanzu karatu ya ke yi". "Waye bigi bro kuma?". Fad'in Fanan. "Za ki fara shirman ko. Ba bigi na ce ba, big, big, big bro. Maimaita inji". Fad'in Fanan. "Big bro. Ai na iya tsokalar ki na ke yi. Ai tun tuni ki ka koya min". Binty ta fad'a ta na dariya. "Mu kwanta ka da Anna ta ji motsi. Kin ga kuma gobe Monday akwai school". "Okay bye, sai da safe". Fad'in Binty ta re da kwanciya. *___________________* Alhaji Usman Mai Rabo, d'an asalin jihar Gombe ne. Wato fulanin gombawa. Su takwas ne a wajan mahaifan sa. Idris shi ne babba, sai Mika'ilu, sai Lukman sai shi Usman sai Abubakar, sai Lurwanu, sai Shafi'i sai autar su da ta kasance mace Rumana. Su na da rufin asirin su dai-dai gwargwad'o. Mahaifiyar su mai su na Khadija, mace ce y'ar boko, haka ma mahaifin su mai su na Adamu. Shiyasa su ma su ka ta so gaba da son boko. Tun daga kan Mika'ilu har zuwa Rumana, sai da su ka had'a degree su ka yi aure. Kuma gaba d'ayan su aikin gwamnati su ke yi idan ka d'auke Alhaji Usman Mai rabo. Shi a Abuja ya yi karatunsa wajan wan mahaifin su Baba Salisu. Shi ya rik'e sa saboda shi Allah bai tab'a ba shi haihuwa ba, shiyasa k'anin na sa Alhaji Adamu ya ba shi Usman halak malak. Tun daga primary sa har zuwa jami'a ana abuja ya yi sa. Alhaji Usman ya na da kaifin fahimta sosai. Ya samu sunan mai rabo ne a wajan wan mahaifin na sa saboda a cewar shi shi mai rabo ne a rayuwa kuma ina sha Allah duk abunda ya tab'a sai ya yi albarka. A jami'a su ka had'u da Na'ima d'iyar k'anin sarkin gombe. Sosai kowa ya yi mamakin kasancewar ta re kasancewar kusan kowa ya san wacece ita. Babu abunda ya burge Alhaji Usman a wajan Na'ima sai rashin jijji da kai da kuma d'agawa irin na y'ay'an masarauta wanda ya kasance a jinin su ya ke. Farkon tarayyar su ba da soyayya ya soma ba, abunda ba ta gane ba ya ke koya mata. A hankali a hankali abun ya juye zuwa soyayya mai zafi wanda ko k'adan ba su son abun da zai gifta ya rabasu. Musamman ma alhaji Usman don gani ya ke shirman banza ya ke yi, shi da ba shi da komai, ta yaya zai samu d'iyar k'anin sarkin gombe a matsayin mata gare shi. Kasancewar shi ya na level 4 ita kuma ta na level 2, ya riga ta kammala makaranta har ya ta fi service. Cikin hukuncin ubangiji, ya na fitowa ya samu aiki da EFCC. A lokacin ne kuma Na'ima ta koma gida gombe Hutu. Da ma mahaifiyar ta ta san labarin Usman kaf don duk ta je hutu sai ta mata maganar shi. Usman kaza, Usman kaza. Da ya ke matar mutum k'abarin sa, Usman ya shaidawa mahaifin sa shi fa ga wacce ya ke so. Sam wan mahaifin na sa bai ji d'ar ba, ya kwashi jiki shi da abokan arziki da y'an uwa su ka nufi Gombe. Cikin mutunci kuwa aka karb'e su. Bayan sun karanto abunda su ke tafe da shi. Iyayan Na'ima su ka ce su je za su yi bincike akan yaro, za su nai me su daga baya. Haka kuwa aka yi, cikin k'ank'anin lokaci aka kira su ta re da shaida ma su an basu. Tu ni har an gama komai kamar ba jinin sarauta ba. An kai sadaki dubu d'ari da duk wani abunda ya ka mata. Bayan an d'aure aure aka had'o ta da kuyangi ta ce ita ba ta so bautar aure ta zo yi ba a yi mata bauta ba. Dama wan mahaifin na sa ya ba shi gida self-contained a nan cikin abuja mai kyau. A nan su ka cigaba da rayuwar su mai dad'i da kyautatawa juna. Har ta haifi d'an ta na fari aka saka masa suna Salis, takwara ya yi wa marik'in na sa, sai ake kiran sa da Julaibib. Julaibib na da shekara uku, aka kori Alhaji Usman a wajan aiki sakamakon sharri da aka k'ulla masa akan an binciki wani da satan Mayan gwamnati, shi kuma ya bai wa Alhaji Usman d'in cin hanci UA rufe case d'in. Sosai su ka shiga wani yanayi na rayuwa. Ga shi an buga can, an buga nan ba'a samu aikin ba. Haka nan ya fad'a sana'ar hannu domin ya rik'a iyalan sa. Babu sana'ar da bai yi ba har da ga ruwa da sai da pure water a tasha. Daga k'arshe ya wani bawan Allah ya ba shi taxi ya soma ja a cikin garin Abuja. Wata rana ya d'auki wani bawan Allah a cikin taxi d'in, sai bawan Allah ya mantuwar jakar sa. Kuma dama ya na sauke bawan Allahn nan gida ya ni niyyar komawa. Kwatsam sai ga jaka. Ya na bud'e wannan jakar yar arba da mak'udan kud'ed'en da ya firgita shi. Sai cikin hukunci ubangiji sai ya ga katin shaida na wannan mutumin. Cikin daran nan sai da ya bi diddigi har ya ga no gidan mutumin nan ya kai masa jakar nan. Mutumin kuwa shi har ya cire rai da ganin kud'in saboda yadda duniyar ta lalace na Allah sun yi k'aranci sai ga Alhaji Usman da jakan kud'i ya kawo masa kuma sile bai yi ciwon kai a ciki ba. Sosai bawan Allah ya din ga gode masa ta re da saka masa albarka. Daga k'arshe saboda dad'in da ya ji dama shi d'in d'an kasuwa ne, sai ya tsunduma shi cikin business d'in sa shi ma ya rik'a samu. Dama kaya ne kala-kala ya ke order daga k'asar waje ana kawo masa ta cikin ruwa. Ba k'aramin mai kud'i ba ne. Domin sai ka ga k'aton jirgin ruwa ya yi lodin kaya kuma na sa ne shi kad'ai. A hankali a hankali aka soma damawa da Alhaji Usman, cikin k'ank'anin lokaci kasancewar ya na da basira da kuma amana ga shi ya iya mu'amala da customer, shi ma ya soma yin order kamar yadda uban gidan na shi ya shawarce shi da kuma ba shi jali mai tsoka. Tuni ya soma shigowa da su keke napep, motoci, kayan Kitchen, shaddo ji da lesuka, da duk wani kayan electronics. Tuni shima ya soma suna saboda ka yan shi ma su ingan ci ne da kuma rahu sa. Ya bud'e tank'ameman mall. Lokacin y'ay'an sa uku. Bayan Julaibib, an sa ka haifan Fu'ad, sai k'anin sa Zaid. A wannan lokacin ne kuma Alhaji Usman ya k'ara aure ya auro Mansura yar gidan wani babban malamin zaure, zuwan ta ba dad'ewa ta haifi y'a mace mai suna Shema'u, bayan shema'u ta haifi Suhail wanda tun daga nan ba ta k'ara haihuwa ba. Bayan Mansura alhaji Usman ya sa ke auro wata mai suna Huriya, tantagaryar y'ar kasuwa kenan, don a wajan kasuwancin sa ma su ka had'u. Ita ma dai ta haifi d'iya d'aya da shi mai suna Sunainah. Sam Hajiya Huriya ba ta damu da harkan matan mijin ta ba, ita kawai ta yi Sana'a ta rik'e kud'i. Ya yin da Hajiya Mansura kuwa, aurar ma gaba d'aya ta yi sa ne don ka da jama'a su saka mata idanu. Sam ita namiji ba ya gaban ta, burin ta kawai ta yi ta yin lesbian da y'ay'an mutane. Ko Shema'u da Suhail ma, Allah ne ya sa da rabon zuwan su duniya. Wannan kenan. .............Su na isa gida ta b'alle murfin mota ta fito zuciyar ta na mata zafi. Cikin gidan ta yi, direct side d'in aunty Junaina ta yi ta na huci. Aunty Junaina da ke zaune a parlour ta na waya da aminiyarta ta d'ago ta kalli Sabrin d'in. Saurin d'aukar excuse ta yi ta re da katse kiran ta mik'e ta isa wajan Sabrin d'in ta re da fad'in, "Queen what going on? Why are you angry?". Aunty Junaina ta fad'i ta re da kamo hannun Sabrin d'in. Dai dai lokacin Hanan da Amrah su ka shigo. Sabrin ta fizge hannunta da ke rike da hannun aunty Junaina ta k'arisa in da Hanan ta ke ta d'aura mata mari ta re da nuna aunty Junaina da yatsa ta ce, "Kin ga wacce ki kai wa tsaki nan ba ni ba. Ko ita wallahi ta min ba kyale ta zan yi ba bare ke y'ar k'aramar y'ar iska. Ko uwar ki ga ta, yau na ce ina da muradin ta bar gidan nan, wallahi ba za ta sake ko minti d'aya ba za ta tattaro ta tafi gidan su. Saboda ki kiyayi yi min tsaki idan ki na son uwar ki ta cigaba da zama a gidan uba na". Hanan ta bud'e ba ki za ta yi magana aunty Junaina ta yi caraf ta ce, "Idan bakin ki ya kuskura ya ce wani abu a cikin d'akin nan, wallahi ni ka d'ai na san mai zan miki cikin gidan nan tun da ke ba ki jin magana. Kuma yanzu ba sai anjima, juya ki ba ta hak'uri ko in yi k'asa-k'asa da ke a nan wajan". Kamar Hanan ta had'iye kwad'o saboda tsabar kumbura, hawaye na saukowa daga idanunta ta kalli Sabrin ta re da fad'in, "Ki yi hak'uri Sabrin". Ta fad'in hakane ta re da fashewa da kukan bak'in ciki da kuma k'ara ruruwar wutar k'iyayyar Sabrin d'in a cikin ranta. "Better! Kuma kin ce ci babaar ki". Fad'in Sabrin ta re da ficewa daga d'akin ta nu fi side d'in su ta na jin kamar ta fashe saboda abunda UA faru earlier a shopping mall. "Mom yanzu haka kullum za mu rik'a jurewa muna hak'uri da da abunda Sabrin ta ke yi a cikin gidan nan? Ai muma y'ay'a ne. Kamar yadda ta ke tak'ama da daddy, haka muma muke tak'ama da shi". Fad'in Hanan ta na wani irin kuka mai cin rai. "Ku yi hak'uri kun ji, na muku rantsuwa lokacin mu na nan zuwa. Ko kallon banza aka ce ta yi muku, wallahi ba za ta yi ba. Ku dai kawai ku cigaba da hak'uri for now. Ranar karb'an y'anci na nan zuwa y'ay'ana". Fad'in aunty Junaina ta mai jin wutar k'una a ranta. Don ita ta fi y'ay'anta tsanar Sabrin da mahaifiyar ta. *°°°°°°°°°°°°°°°°* Abu kamar wasa Binty ta dage sai koyan turanci da fulatanci ta ke yi, gyefe guda kuma Anna na cigaba da koya mata girki. Yanzu har Anna na dai na mata Hausa, daga turanci sai fillanci. Wani abun idan ta fad'a a yi dariya, wani kuma a yi mamaki. Domin akwai ta da saurin d'auke abu. Fannin islamiya kuwa, ta iya falaq, nasi, ahad. Kuma ta iya alwala sosai. Sosai ta ke burge malamin na su. Haka ma fannin boko, yanzu kam turancin ta ya soma improving. Har had'a dictation ake mata. Mamakin kwakwalwarta sosai malamin ya ke yi. Don bai tab'a koyar da mai kwakwalwa irin na ta ba. Barrister Fu'ad kuma kamar yadda ya alk'awarta ma su, duk weekend sai ya kai su shopping. Binty ta waye, babu yadda za'a ka iya had'a ta da Bintyn baya ta kan bola. Ta k'ara haske da wani irin kyawu. Ga kwakwalwa ta bud'e. Yanzu haka su Fanan su na rubuta jarabawar zango na biyu wato second term. Kuma a first term ne idan su ka dawo za su koma ta re sa Binty. Binty ta dage ta bud'e wuta sai kwankwad'ar karatu ta ke yi. Ji ta ke kamar dama can a gidan ta taso. Har mantawa ta ke yi da rayuwar bolan da ta tab'a yi. Girki kuwa ya zama favourite d'in ta, don yanzu har tafi Fanan iya wasu abubuwa da dama. Suhail kuwa ya bi ta duk yadda zai yi ya sake had'uwa da Binty, amma Sam bai samu wannan damar ba don ya san ko giyar wake ya sha bai isa ya je part d'in su ba. Gyefe guda kuma, mahaifiyar sa kullum sai ta yi mafarkin Binty. Sai dai ita ma ba ta samu hanyar da za ta jawo ta jikin ta ba. Daga k'arshe dai ta yanke shawarar shiga jikin Fasila domin ta samu ganawa da Binty ko ta b'oye ne. *_____________* *CANADA* cikin babbar birnin su wato *Ontario*, wani kyakkyawan saurayi ne tsaye a gaban tank'ameman madubin hotel d'in. Jeans blue ya saka da farar rigar max n spencer sannan ya ďaura blue Tuxedo ta giorgio Armani daga sama, kayan ba k'aramin kyau suka mishi ba kasancewan shi dogo, agogon ciélo ya mak'ala sannan ya fesa turaren karenbkelly da vesace eros a jikin sa. Key d'in motar sa da ke gaban mirror ya d'auka ta re da k'ara kallon mirror ya na gyaran kwantancan gashin kan sa, ka na ya fito ya daga d'akin ya hau lifter ya sauko da shi k'asa ya nufi parking load. Danna key d'in motar da ke hannun shi ya yi, a take mota kamar maroon mai shegen kyau ta yi k'ara. Wajan motar ya nufa ta re da shiga ya yi reverse ta re da fitowa daga cikin hotel d'in. Kai tsaye *University of Toronto* ya nufa. Kasancewar tafiya ce mik'ak'k'a tsakinkin *Toronto* da kuma *Ontario* shi ya sa ya dunga sharara gudu. Gashi titinan su masu inganci ne ba kamar k'asar mu Nigeria ba. Ya ci rabin tafiyar ya kunna radion motar sa ta re da kunna wak'ar *West life* _My love_ ya shiga bin wak'ar kamar haka, 🎻An empty street, an empty house A hole inside my heart I'm all alone, the rooms are getting smaller I wonder how, I wonder why I wonder where they are The days we had, the songs we sang together Oh, yeah And oh, my love I'm holding on forever Reaching for the love that seems so far So, I say a little prayer And hope my dreams will take me there Where the skies are blue To see you once again, my love Overseas, from coast to coast To find a place I love the most Where the fields are green To see you once again My love I try to read, I go to work I'm laughing with my friends But I can't stop to keep myself from thinking, oh no I wonder how, I wonder why I wonder where they are The days we had, the songs we sang together, oh, yeah And oh, my love I'm holding on forever Reaching for the love that seems so far So, I say a little prayer And hope my dreams will take me there Where the skies are blue To see you l once again, my love Overseas, from coast to coast To find a place I love the most Where the fields are green To see you once again To hold you in my arms To promise you my love To tell you from the heart You're all I'm thinking of I'm reaching for the love that seems so far So, I say a little prayer And hope my dreams will take me there Where the skies are blue To see you once again, my love Overseas, from coast to coast To find the place I love the most Where the fields are green To see you once again (My love) Say a little prayer (my sweet love) Dreams will take me there Where the skies are blue (woah, yeah) To see you once again Overseas, from coast to coast To find the place I love the most Where the fields are green To see you once again My love🎻 Sosai wak'ar ke masa dad'i don har bugs steari ya ke yi. Ya sha hanya ka min ya iso cikin birnin *TORONTO* da ke *CANADA*, university d'in ya nufa. Parking ya yi ta re da nufar hall d'in da su ke gabatar da lecture. Wata baturiya da ake kira da Cecilia ta nufo shi ta na wani karairaye. Sanye ta ke da sweatpants kalar ash, sai riga arms les red color. Gashin nan na ta maroon ta zubo shi a kafad'un ta. Sai wani takalmi mai tsinin gaske a k'afarta. Hannun ta rike da iPhone ta taho da saurin ta na fad'in, "Hey Bibi wait a minute". Sauri ya k'ara ta re da shigewa cikin hall d'in da su ke gabatar da lecture ya nai mi waje ya zauna ta re da fiddo memo da wani Biro mai kyau ya d'aura akan desk ta re da furzar da iskan bakin shi. Cecilia kuwa da ke tsaye a waje kasancewar ba ta da damar shiga wajan ta saka hannunta a cikin gashin kan ta ta cukurkud'a ta re da fad'in "Dam it". Sai 4:00pm su ka gama gabatar da lecture. Cikin sauri ya fito ya nufi wajan motar. Cecilia ta tun da ya shiga hall d'in ta nai mi waje ta zauna ta na jiran fitowar shi. Ta na ganin shi ta bi bayan shi da sauri har wajan mota. Shi kuwa Julaibib sauri ya ke ya je ya yi sallar la'asar. Ya na bud'e murfin motar ta rik'e gam ta re da tsare shi idanunta irin na turawa ta re da fad'in, "Why Bibi? Why are you avoiding me all this days? It's because of happened last week? Then I'm so sorry it won't happen again I promise. I won't come to your house without your permission again. Please stop avoiding me, I can't take it. You known I love Bibi". Cecilia ta fad'a ta re da kamo hannun sa. "Let go of my hand". Julaibib ya fad'a in a very cool voice. Hakan ya ke yi idan ran shi ya b'aci. Don idan har zai yi ihu ko magana a cikin fushi, to lallai zai kai hannu, kuma abunda ya tsana a rayuwar sa, shi dukan mace. "Bibi please". Cecelia ta sa ke fad'a ta re da rik'o k'ugun shi. Wani irin tsawa ya daka mata da ba ta san sanda ta saki hannun shi ta re da jaa da baya ba ta dafe kirjin ta saboda yadda ya ke bugawa. Kasancewar idan ran shi ya kai k'ololuwa har in'ina ya ke yi saboda zuciya. Tuni ya soma buga k'afar shi a k'asa ya na so ya yi magana amma maganar ta k'i fitowa. Kawai ya bud'e motar ta re da shiga ya fizge ta ya fice daga makarantar saura kad'an ya takawa Cecilia k'afarta tai saurin ja baya. *MATAR SAYYADEE* *_KAR DAI KU MANTA, SATURDAY AND SUNDAY BA NA TYPING_* 🌹 *31-32*🌹 .............Kai tsaye daga *Toronto University*, wani masallaci ya nufa ya gabatar da sallar la'asar ka na ya fito ya shiga mota ya nufi *Lawrence Avenue* wajan abokin aikin sa Peter John. Parking ya yi a gaban gate d'in ka na ya fito daga motar ya shiga cikin gidan. Doorbell ya danna. Katrina matar shi ta zo ta bud'e masa k'ofar ta re da fad'in, "Ohhh welcome Mr Julieby(Julaibib d'in ne ba ta iya kira ba ta ke fad'in haka)". "Thank you". Julaibib ya fad'a a tak'aice ta re da nufar kujera ya zauna. San ye ya ke cikin jallabiya ash colour, ba k'aramin kyau kayan su ka masa ba. Julaibib ne ya sayo masa a wani zuwan shi umarah da ya yi kasancewar Peter John ya na son irin wannan shigar wanda ya je gani sometimes a jikin Julaibib d'in. "Welcome friend. Yaya haya (hanya)?". Fad'in Peter shi ala dole sai ya ko yi hausa. Wani kallo Julaibib ya bi shi da shi idanuwan shi a k'ank'an ce ta re da mik'ewa ya zura hannun shi cikin aljihun wandon shi ta re da fad'in, "Why are you looking like this? Won't you go to the hospital? You know I have someone to perform surgery on. Are you drunk? Can't you ever heed good counsel? You've been repeatedly reminded about the dangers of alcoholism but all that has fell on deaf ears. But you are a medical doctor I don't have to waste my time talking to you always about that. See, I'm on my way to the hospital." Julaibib ya fad'a heading to the door without listening to what Peter John is saying. Kallon matarsa John ya yi ta re da fad'in, "This friend of mine is highly temperamental. He has perceived the smell of the wine we took a while ago. You know he hates the smell of alcohol. Even now, he would want to distance himself from me unless I appease him with effort. I feel for the wife he's going to marry. He is strictly regular as if he is superhuman and he doesn't show any interest for marriage. And I can swear to you that he doesn't chase after women. My friend is indeed very difficult to understand." Katrina matar john ta zauna a kan kujera ta re da d'aukar remote ta ce, "The guy impresses me a lot. Very handsome and knowledgeable. Whoever marries him is indeed lucky. I like his style." "Bibi! Hmm, I'm speechless". Fad'in Peter ta re da zama kusa da ita. *_______* Kai tsaye ya na fitowa daga gidan Peter ya d'auki hanyar *Alexander street* in da gidan sa ya ke. Direct bedroom d'in sa ya yi ta re da shiga bathroom ya sa ke wanka ta re da d'auro sabon alwala. Don shi haka ya ke ba ya rabuwa da alwala a jikinsa. Gaban mirror ya isa ta re da shafa man shafawar sa ya kuma feshe jikinsa da turare don shi ma'aboci turare ne. Ya na matuk'ar k'aunar k'amshi a rayuwarsa. Wannan karan ma jeans ya saka ta re da t-shirts vneck. Ta je kan sa ya sake yi ka na ya sauko zuwa parlour. Kitchen ya shiga kasancewar kitchen d'in na a parlour ne. Tea ya had'a ta re da d'auko biscuit ya na had'awa da shi ya na sha kasancewar shi mara son cin abinci sosai idan ba na k'asar sa ba. Sai bayan ya gama ne ya fito daga gidan, kai tsaye *Mount sinai Hospital* ya nufa. Tun daga parking motar da ya yi a harabar asibitin mutane su ka zagaye motar kamar za su tsuguna masa. Ko da ya fito daga cikin mutar, manyan likitocin asibitin nan da kan su su ka fito suka taro shi su na gaisawa da shi kasancewar babba kuma kwararra doctor a fanni daban-daban. Domin dai degree biyar ga re shi, ya na kan na shidda yanzu. Farkon degree d'in sa shine ya karan ci fannin Gynaecology and obstetrics (Fannin cutukan mata da haihuwa), na biyu kuma ya karanci Paediatric (Fannin rashin lafiyar k'ananan yara), na uku kuma Oncology (Fannin ciwon sank'ara (Cancer)), na hud'u kuma, Nephrology (Fannin k'oda), na biyar Cardiology (Fannin Zuciya), Sai na shidda wanda ye kan karanta yanzu wato Orthopaedic (Fannin k'ashi). Sosai ya ke da kwarewa a wajajan nan. Booking ake yi idan za'a gan shi. Har da ga k'ashashe da dama ake zuwa ganin sa. Wanda Sai mutum ya na da sa'a ya ke samun hakan. Kai tsaye wani had'ad'd'an office ya nu fa ta re da sauya kayan jikinsa izuwa na tiyata saboda tiyatar da zai wa wata a zuciyarta. Kai tsaye ya na fitowa daga gidan Peter ya d'auki hanyar *Alexander street* in da gidan sa ya ke. Direct bedroom d'in sa ya yi ta re da shiga bathroom ya sa ke wanka ta re da d'auro sabon alwala. Don shi haka ya ke ba ya rabuwa da alwala a jikinsa. Gaban mirror ya isa ta re da shafa man shafawar sa ya kuma feshe jikinsa da turare don shi ma'aboci turare ne. Ya na matuk'ar k'aunar k'amshi a rayuwarsa. Wannan karan ma jeans ya saka ta re da t-shirts vneck. Ta je kan sa ya sake yi ka na ya sauko zuwa parlour. Kitchen ya shiga kasancewar kitchen d'in na a parlour ne. Tea ya had'a ta re da d'auko biscuit ya na had'awa da shi ya na sha kasancewar shi mara son cin abinci sosai idan ba na k'asar sa ba. Sai bayan ya gama ne ya fito daga gidan, kai tsaye *Mount sinai Hospital* ya nufa. Tun daga parking motar da ya yi a harabar asibitin mutane su ka zagaye motar kamar za su tsuguna masa. Ko da ya fito daga cikin mutar, manyan likitocin asibitin nan da kan su su ka fito suka taro shi su na gaisawa da shi kasancewar babba kuma kwararra doctor a fanni daban-daban. Domin dai degree biyar ga re shi, ya na kan na shidda yanzu. Farkon degree d'in sa shine ya karan ci fannin Gynaecology and obstetrics (Fannin cutukan mata da haihuwa), na biyu kuma ya karanci Paediatric (Fannin rashin lafiyar k'ananan yara), na uku kuma Oncology (Fannin ciwon sank'ara (Cancer)), na hud'u kuma, Nephrology (Fannin k'oda), na biyar Cardiology (Fannin Zuciya), Sai na shidda wanda ye kan karanta yanzu wato Orthopaedic (Fannin k'ashi). Sosai ya ke da kwarewa a wajajan nan. Booking ake yi idan za'a gan shi. Har da ga k'ashashe da dama ake zuwa ganin sa. Wanda Sai mutum ya na da sa'a ya ke samun hakan. Kai tsaye wani had'ad'd'an office ya nu fa ta re da sauya kayan jikinsa izuwa na tiyata saboda tiyatar da zai wa wata a zuciyarta. Fitowa ya yi daga cikin office d'in na shi ya yi theater room d'in, wasu daga cikin doctors su uku suka rufa masa baya da nurses hudu. Kayan aikin su ma kawai abum kallo ne. Hatta aikin da akai wa wannan mata ba tsagata aka yi ba, ko mai da machine aka yi mata. And the operation was successful. Cikin da godiyar ubangiji ya fito daga theater room d'in doctors su na congratulating d'in sa. Murmushi kawai ya ke ma su, don shi bai cika dariya ba. Bayan ya fito ya canza kayan sa, kai tsaye masallaci ya nufa ta re sa sa ke alwala kasancewar a cikin theatre d'in nan sallar magriba ta sa me shi, kuma abunda ya fi tsana a rayuwar sa shine sallah ta wuce sa. *NIGERIA* Hmm abun zai ba ku mamaki idan na fad'a maku cewar Binty yanzu ta kware a yaran fulatanci. Turanci kuwa ko wani d'an da ya je makaranta ba zai nu na mata turanci ba. Ba laifi ta na yi kuma ta na mayarwa. Gyefe guda kuma Malam Suhail ya fita sha'anin Binty, amma ba gaba d'aya ba. Don cewa ya yi kura na yawo, zabo na yawo, wata rana za'a had'u. Hajiya Mansura kuwa sai k'ara haukacewa ta ke yi, don yanzu ji ta ke yi ko ido hud'u ne kawai su yi da Binty ko ta samu ta ji sauk'i cikiin zuciyar ta. Tu ni ta tsiri zuwa shashin Anna duk da kasancewar da zan ba zuwa ta ke yi ba. Kuma Anna na karb'ata hannu biyu duk da a k'asan zuciyarta ta na mamakin yawan zuwa shashin na ta da ta ke yi. Sai dai duk zuwan ta, Allah bai tab'a sawa ta ga Binty ba. Haka za ta k'ariki zamanta ta tashi ta fita. Kuma ba ta so ta tambayi ina Bintyn ta ke ka da ta yi suspecting wani abu. Yanzu haka su Fanan sun na hutun third term ne. Sai farin ciki ta ke yi ta re za su koma makaranta sa Binty. Ta k'osa wannan ranar ta yi. Da ma tuni Ya Fu'ad ya je har makarantar ya ga ma wa Bintyn komai. Za'a saka ta primary 3 kasancewar ya yi wa principal d'in ba ya nin komai kuma yq shaida masa Bintyn ta na da saurin fahimta kuma sun d'aukar mata lesson teacher. Hatta uniform sun ba ta da kaf writing materials. Sai dai ya Fu'ad d'in bai shaida mata ba saboda surprise ya ke son ba ta. Kwanci tashi ba bu wuya wajan Allah. Nan da kwana uku dai Binty za ta so ma zuwa *LEAD BRITISH* a matsayin d'aliba. Ana gobe za su je makaranta, ya Fu'ad ya kwashe su ya yi masu shopping mai uban yawa har da su school bags da kuma takalman makaranta ba d'aya ba ba biyu ba. Tsabar murna, tun saura sati d'aya Binty ta fara zuwa makaranta, ta dai na ishashshan barci. Har mafarki ta ke yo ga ta a cikin school d'in. Daran ranar kuwa ba ta yi baccin kirki ba. Asubar fari ta tashi, ko da Anna ta zo tashin su, idanun Binty biyu ta ga ta. Dariya ta yo cikin harshan fillanci ta ce, "Wato Binty ba ki yi bacci ba saboda zumud'i ko? To ai sai ku ta shi ku yi wanka ta re da d'auro alwala". Binty ce ta fara saukowa daga kan gadon, ka na ta tada Fanan da ke bacci. Wanka ta soma yi ka na ta d'auro alwala. Doguwar riga ta saka ta re da hijjab ta tada sallah kasancewar ta iya sallah sosai yanzu. Bayan ta idar ta isa gaban madubi ta d'auko man shafawa ta soma shafawa a jikinta, dai-dai lokacin Fanan ita ma ta fito daga bayi. "Heeey! Kar ki wa fuskan ki komai. Ki ba ri in idar da sallah da kai na zan gyara miki fuska. Ai yau kwalliyar ki ta musamman ce". Fad'in Fanan ta re da kabbara sallah. Binty jiran ta ta yi har ta idar da sallah ka na ta zo ta yi mata kwalliya. Ba wani kwalliya ta mata ba, powder kawai ta shafa mata ta re da lipstick. Sai ta gyara mata gashin kan ta ta yi mata parking a tsakiyar kai ta kuma nannad'o gashin ta yi ma ta donut da shi. Anna ce ta shigo hannunta rik'e da uniform d'in Bintyn a hannunta. "Laa! Anna da ma an bata uniform?". Fad'in Fanan. "Eh, Barrister ne ya je ya karb'o mata a makaranta har da ID d'in ta ga shi nan". Fad'in Anna ta re da aje kayan a kan gado. D'aga kayan Fanan ta yi ta re da nuna wa Binty tana dariya. Skirt d'in ta mik'a mata ta saka, ka na ta ba ta shirt d'in ciki mai dogon hannu ta saka ta re da d'aura mata coat d'in ta kuma b'alle mata mab'allin rigar. Ba k'aramin kyau ka yan suka yi wa jikinta ba. Kamar dan ita aka yi su. Hular ta saka mata ta re da baby hijjab d'in. "Binty na kin gan ki kuwa? Kin yi kyau sosai". Fad'in Anna. Dariya Binty ta yi ta na jujjuyawa ta re da kallon kan ta cikin madubi dad'i ya gama kashe ta yau za ta makaranta. "Ga socks d'in ki nan ki saka ku fito ku karya ka da ku yi latti". Fad'in Anna ta re da fita daga d'akin. Safar ta saka, ka na ta saka dark purple shoe kalar kayan mai matuk'ar kyau. Cikin sauri Fanan ma ta shirya su ka fita parlour. A dinning su ka tara's da Daddy da Anna su ma su na karyawa. K'arasawa su ka yi su ma ta re da jan kujera su ka zauna. Gaba d'ayan su su ka gaida daddy da Anna. Ka na su ka had'a tea. Daddy ya kalli Fanan da Binty ta re da fad'in "My twins, dan Allah idan an je makaranta, a natsu a yi abunda ya da ce. Ban da fad'a da students. Sannan ke kuma Fanan ki kula da Binty sosai ta re da k'ara ko ya mata abubuwan da ba ta iya ba tun da ke kin san kan makarantar". "In sha Allah daddy". Fad'in Fanan. "Allah ya ma ku albarka". Fad'in Daddy. "Ameen". Su ka amsa gaba d'ayan su. Ta shi su ka yi kowacce ta d'auki jakar makarantar ta su ka sauko k'asa ta re da fita daga d'akin. As usual driver na nan a nesa da part d'in kad'an ya na jiran isowar su. Ya Fu'ad ne ya fito cikin shigar suit bak'ak'e ya nufo inda su ke. A tare su ka had'a ba ki wajan fad'in, "Ina kwana ya barrister?". "Lafiya k'alau autares d'in Anna. Binty kin gan ki kuwa cikin uniform d'in nan? Looking more beautiful". Ya Fu'ad ya k'arisa maganar ya na kallon Binty. "Thank you ya Fu'ad". Fad'in Binty ta na dariya har sai da kyawawan hak'oran ta su ka bayyana ta re da lotsewar kumatukan ta. "Mu je ni da kai na yau zan kai ku makaranta". Fad'in ya Fu'ad. Tsallan murna su ka yi dukan su ta re da nufar motar yaya Fu'ad d'in da gudu. Bayan su ya bi ta re da isa wajan motar ya danna key su ka bud'e. Binty ta shiga gidan gaba kasancewar ta na son zaman gaban mota saboda ta ga komai da komai ta na kuma tambaya abunda ba ta ga ne ba. Fanan kuma ta shiga gidan baya. Shiga motar ga yi ta re da kunnata ya yi reverse ya nu fi gate. Oga Solomon da ya dad'e bai ga Binty ba, da ya gan ta yau a gaban mota ba k'aramin mamaki ya sha ba, domin ta k'ara girma da kama kyau. Don gaba d'aya watan ta takwas a gidan. A hanya sai k'ara ja masu kunne ya Fu'ad ya ke yi a kan su dage su yi karatu musamman Binty. A k'ofar gate d'in ya sauke su ta re da jan kumatun Binty ya ce, "Binty na ki yi karatu sosai kin ji?". Gyad'a masa kai ta yi ta na murmushi. Fanan ita ma ta kai kumatun ta ta re da fad'in, "Ya Fu'ad ni ma" Ita ja kumatun na ta ya yi ta re da fad'in, "Rigimatu maza a shige makaranta". Isa wajan gate d'in makarantar su ka yi ta re da nu na ID d'in su su ka shige ciki. Gaba d'aya students d'in da su ke harabar makarantar su ka juyo ta re da zubawa Binty idanuwa su na fad'in "Wow!". *Ku yi min afuwa masoya. Ku yi hak'uri da wannan. In sha Allah za ku ji ni anjima da yamma* *paid book 08128755583* 🌹 *33-34*🌹 .........K'awayan Fanan da gudu su ka zo su ka zagaye su. Rukayya wacce su ke kira da Saje ta kalli Fanan ta re da fad'in, "Wannan ita ce surprise d'in da ki ka ce za ki taho mana da shi idan mun dawo first term. Lallai kam zuciyar Sabrin sai ta buga. Ba bu shakka sai an cire ta a sarauniyar kyawun *Lead British*, please sister will you be my friend?". Saje ta k'arishe maganar ta re da kallon Binty a marairaice. Murmushi Binty ta yi ta re da mik'awa Saje hannu ta ce, "Friend". Ka min Saje ta ce wani abu, gaba d'aya k'awayan Fanan su ka rik'e hannun binty ta re da fad'in, "Friends for rever and ever". Sun fad'i hakane ta re da d'aga hannun sama su na dariya. Dai-dai lokacin tawagar k'awayan Sabrin su ka k'araso in da su Binty su ke a tsaye. "Ku matsa mu na son ganin fuskan newcomer da ta zo yau". D'aya daga cikin k'awayan Sabrin mai su na Rufaida ta fad'a. Gaba d'ayan su su ka dare su ka bar Binty a tsakiya ta na kallon Rufaidan. Gaban Rufaida ne ta buga da k'arfi. Domin yadda students su ka zo su na fad'i masu irin kyawun newcomer d'in sai ta ga ta fi haka sosai. Juyawa Rufaida ta yi ta re da kallon sauran k'awayan da su ma tsananin kyawun Bintyn su ke kallo da mamaki. Ba ta re da fad'in komai ba, su ka juya su ka bar wajan ta re da nufar class inda Sabrin ke zaune idanuwan ta jazur, ga dukkan alama ma kuka ta ci. "Yana yin fuskokin ku kawai ya tabbatar min da abunda students su ka zo su ka fad'a. Ke nan ku na nufin kuma kyawun yarinyar ya haukata ku haka? Ku na nufin yanzu za'a samu wacce za ta done ni a kyau a cikin makarantar nan? Ba zai yu ba. Wallahi ko fuskan yarinyar ba na k'aunar ga ni. Ba na son in san ta ko in ga fuskan ta har in bar makarantar nan yau". Fad'in Sabrin ta re da rushewa da kuka. "Haba Ella. Kin san Allah, duk yadda ake fad'in kyawun yarinyar nan ko, kururutawa ne kawai amma ko k'unban ki ba ta kama ba. Kawai hasken fata ne irin bauu d'in nan kamar zabaya. Amma kin san Allah, kin fi ta komai, ba ma had'i". Fad'in Shamsiya Uba. D'ago kai Sabrin ta yi ta re da fad'in, "Duk wacce ta yi adoring yarinyar, ku ma idan har cikin team d'ina ta ke, a cire ta kuma za ta fuskanci hukunci". Fad'in Sabrin ta re da mik'ewa kasancewar an danna bell d'in assembly. A cikin k'aton hall d'in da ake gabatar da assembly, bayan kowa ya natsu, an gabatar da addu'a da kuma assembly. proprietor ya fito ya yi jawabi da kuma yi ma su barka da dawowa first term. Sanna ya k'ara da karanto wasu dokoki kamar haka cikin harshan turanci. "Kamar yadda ku ka sami, wannan makaranta ce da ake koyar da ilimi da kuma tarbiya. A kwai wasu dokoki da ni shugaba na shimfid'a sakamakon wasu abubuwa da su ka faru a shekarar da ta wuce. To hak'ik'a wannan karan idan haka ta k'ara faruwa, to za mu d'auki hukunci tsatstsaura akan ko wanenen. Ba ruwa da ko baban ka shine shugaban k'asa, idan ki/kai laifi, to hukuman makaranta za ta yi hukunci akan ko waye. Na farko, ba bu d'aukaf hukunci a hannu, duk abunda wani ya maka, ka kai k'arar shi, ba biyu ba'a yarda wani d'alibi/d'aliba ya takurawa wani ba, sannan ba a yarda ko waye ka d'auki bulala ka da ki wani ba ko da kuwa malami ne, sannan kuma duk house d'in da ka/ki ke, ba a yadda do ba ka san house d'in nan ka canza ba. Sannan duk abunda malami/malama ta saka ki/ka, wajibi ne ki yo idan har abun nan bai sab'awa dokar makaranta ba. Ina fatan kowa yaji bayani na". Fad'in proprietor. Gaba d'aya students d'in nan su ka amsa da, "Yes sir". Sallamar su ya yi kowa ya soma mik'ewa zuwa ajujuwan su. D'agowar da Sabrin za ta yi, su ka had'a idanu da Binty. Gaban ta ne ya buga da k'arfi ta wa ni zaro idanuwan ta. K'awayan ta da su ka ga abunda ke faruwa, da sauri su ka zagaye ta ta re da fad'in, "Ella ka da ki firgita, wallahi ba bu abunda ta fi ki da shi". K'ank'ance idanuwa Sabrin ta yi ta re da fad'in, "Da ma ita ce. Makarantar nan ta shigo kenan. Wallahi sai na saka ta gudu da k'afafun ta. Sai na d'aura mata k'ullin da ba za ta tab'a iya warware shi ba billahi". Fanan hannun Bintyn ta ka ma ta re da fad'in, "Mu je in nu na miki ajin ku, kin san amana Anna ta ba ni ke". Sai da ta kai ta har ajin su primary three, ka na ta wuce na su ajin P-4. Ka min teacher ta shigo ajin na su, kusan gaba d'aya y'an ajin su ka zo kan Binty su na mata magana. Kowa na san ya yi k'awa da ita. Kowa sai gabatar mata da kan sa ya ke a wajan ta. Class captain d'in ta kalli Binty ta re da fad'in, "I'm Na'ima Ahmad, and you?". Kasancewar ba laifi Binty na ga ne English sosai, sai ta kalli Na'ima ta re da fad'in, "I'm Binty Hisham mai goro". Ta fad'i hakane murmushi d'auke a fuskan ta. Teacher ce ta shigo ajin, kowa ya koma wajan zaman shi ta re da kunna computern da ke gaban shi. Binty kuwa sai raba idanuwa ta ke yi domin ba ta iya operating computern ba. Zayyishatou da ke gyefenta ta saka hannu ta kunna mata computer ta re da nu na mata yadda yi. Godiya ta mata ta re da mai da hankali a kan teacher da ke baya ni. Kad'an-kad'an Binty ke fahintar abunda teachern ke baya ni akai kasancewar turancin ya ma ta tsauri. Bayan ta kammala ta fita, Binty ta kalli Zayyishatou ta re da fad'in, "Ban ga ne abunda ta koyar ba, ban jin turanci sosai. Dan Allah ki min baya ni idan ke kin ga ne". Murmushi Zayyishatou ta yi ta re da fad'in, "Kar ki da mu, duk abunda ba ki ga ne ba, zan ko ya miki in dai za ki yadda in zama babbar k'awar ki". "A'a za dai ki zama ta biyu. Babbar k'awa ta Yaya ta ce Fanan. Anna ta ce min Fanan ta girme ni. Yayata ce kuma k'awata ce". Fad'in Binty. "To ai ba bu damuwa, sai in zama k'awar ki ta biyu" fad'in Zayyishatou. "Kin ma zama ai. Ke ce k'awata ta biyu. Ki koya min dan Allah". Gyara zama Zayyi ta yi ta re da matso da kujeran ta kusa da Binty sosai ta shiga koya mata abunda duk malamar ta koya masu. Kasancewar ta mai bud'ad'd'iyar kwakwalwa, tuni har ta fahimta. An fita break, Fanan ta zo ita da k'awayanta su ka fita zuwa capteria har da Zayyi sabuwar k'awar Binty. Zama s ka yi a wajan cin abincin, bayan sun fad'i abunda su ke son a kawo masu. Sabrin ce da zugar k'awayan ta su ka zagaye table d'in da su Bintyn su ke zaune. "Ke!". Sabrin ta daka mata tsawa. D'agowa Binty ta yi a razane kasancewar mai saurin tsorata ta kalli Sabrin d'in da ke tsaye a gaban ta. "Au ke ce. Kin zo ne ki fad'a min abunda na mini na ba ki hak'uri?". Fad'in Binty ta na kallon ta. "Ke ba ki da tarbiya ko? Kin zo har cikin mall d'in ubana kin bangaje ni, amma da ya ke ke dak'ik'iya ce sai ki ka wuce ba ta re da kin yi apologizing ba ko". Fad'in Sabrin ba ta re da ta fad'i cewar Bintyn ta mare ta ba, domin fad'in hakan a gaban mutane kamar zubar da k'imar ta ne a gaban su. Zaro idanuwa Binty ta yi ta re da mik'ewa ta ce, "Dan Allah ki yi hak'uri, wallahi ban san na bige ki ba. Shiyasa ki ka mare ni ashe. Da na sani ai da ban r........". "Ke dalla rufewa mutane baki". Sabrin tai saurin katse ta ba ta re da ta k'arisa abunda ta ke son fad'i ba. "To ai ba ba ki hak'uri. In sha Allah hakan ba zai sa ke faruwa ba. Ki yi hak'uri. Anna da daddy sun ce ka da na saki na yi fad'a da kowa a makaranta. Karatu aka turo mu ba fad'a ba". Fad'in Binty. "Wanna kuma ruwan ki. Ina mi ki gargad'i da shiga gona ta, idan kin kiyaye, kin tsira. Idan kuma ba ki kiyaye ba, za ko sha mamaki. Sai na saki kin koma ki na jan d'uwawu a cikin makarantar nan". Fad'in Sabrin. "Akan wani dalili kenan? Ina ce ta ba ki hak'uri. To dan Allah malama ki kwashi komatsatstsun k'awayan ki Ku yi gaba". Fad'in Fanan. "Ke! Ki shiga hankalin ki da ni a cikin makarantar nan. Idan ba haka ba, wallahi zan ba ki mamaki. Ba ruwa na da ko waye mahaifin ki a garin nan". Fad'in Sabrin. "To fah! Mi ya kawo maganar mahaifi a cikin maganar nan idan har ba kishi ki ke yi da mahaifin na ba". Fad'in Fanan ta na dariya k'asa-k'asa. Sabrin za ta yi magana, k'awarta Shamsiya ta dakatar da ita ta re da fad'in, "Haba Queen, wai ba ki fahimta ba ne. Fanan fa ta na zan ki da magana ne saboda ta zama cele a cikin school d'in nan ne. Ba ki ga gaba d'aya students d'in da ke capteria nan sun dawo da hankalin su nan ba ne. Hakan ai zai ja mata fans ne, kuma da ma abunda ta ke so kenan". Wani juya idanuwa Sabrin d'in ta yi ta re da fad'in, "Kuma hakane fa, na tsaya ina wasting sliver d'ina a ban za. Mu je dan Allah ban san yawan tsayuwa". Fad'in Sabrin ta re da yin gaba zugan k'awayan ta su ka bi ta a baya. Dariya ce ta kwacewa Fanan d'in. Kallon k'awayan ta ta yi ta re da fad'in, "Wai kun san mai ya faru kuwa?". "A'a sai kin fad'a". Ga ba d'ayan su su ka ba ta amsa. Nan fanan ta zayyane masu abunda ya faru a mall. Aiko gaba d'aya su ka kwashe da dariya ta re da cizan yatsa ina ma a gaban su ne aka Binty ta wanke fuskan Sabrin d'in da mari. Ita kuma Binty duk sai ta ji ba dad'i har ta ke dana sani akan marin da ta yi wa Sabrin d'in duk da ita ta fara marin ta. Alhamdulillah! Binty na gane duk abunda ake koya mata a makaranta. Tun ba ta iya amfani da computer ba, har ta zo ta kware da taimakon Zayyishatou. Kowa a school d'in nan Binty. Wata d'ayan da ta yi a makaranta, ba k'aramin k'ara waye wa ta yi ba. Sosai kwakwalwarta ke bud'ewa ga ta da shegen tambaya akan abunda ba ta sa ni ba. Babban bak'in cikin Sabrin shi ne kasancewar su a house d'aya(Red house). Hakan ba k'aramin bak'anta mata ya yi ba. Gashi House Captain d'in su na planning akan cire Sabrin a matsayin Queen su nad'ata princess of the house, Binty Ku ma ta maye gurbin ta a matsayin Queen. Da ya ke a makaranta ko test a ka yi, a na fitar da first second and third position. Na'ima wacce ita ce class captain ita ta zo na d'aya, Zayyishatou ta zo na biyu, yayin da Binty ta kasance na uku. Sosai Binty ta ji dad'i ta re da d'aukar alwashi in sha Allah second CA ita za ta zo na d'aya. Ko da su ka koma gida, sosai Anna ta yi farin ciki. Yaya Fu'ad ku wa d'aukar so ya yi ranar sun sha yawo. Mayan kwalam sai da ya cika boat d'in motar sa. Sannna kuma ya sayan masu Laptop Apple su dukan su biyun. Ba k'aramin dad'i hakan ya yi masu ba. Hakan ya sa Binty k'ara zagewa da dagewa. Cikin ikon ubangiji da aka yi jarabawar first term sai ga ta ta zo second position. Tun daga wannan lokacin Binty ta kwace ta yi wa y'an ajin nan fintinkau. Idan Binty na turanci, za ka d'auko ana bud'e dictionary a ka tsince ta a ciki saboda tsabar yarda ta ke karya harshe da fitar da ko wani sauti yadda ya kamata. Kwanci tashi ba bu wuya wajan ubangiji, sai ga su a zango na uku, wato third term. Sai shirye-shiryen inter house ake yi. Tu ni captain d'in Red house da ta kasance a SS3 ta mai da Binty a matsayin Queen of red house, Sabrin Ku ma princess. Sabrin har zazzab'i ta yi saboda bak'in ciki da tashin hankali. Ji ta yi ta k'ara tsanar Binty har cikin can cikin kwaryar zuciyar ta. Kullum cikin practical su ke na game and sport d'in da za su gabatar ranar hutu. Tu ni har an gwada Binty kasancewar gown red colour za ta saka ranar inter house d'in nan. Binty ta k'ara haske ta yi b'ul-b'ul abunda. Sai dad'a girma ta ke yi. Don yanzu shekarunta goma sha d'aya ta ma fita cikin na sha biyu ta ke. Ya yin da Fanan ke da cikin na sha uku. Sai dai kan su d'aya kasancewar Fanan d'in ba ta da girman jiki sosai. Yauwa dai su ke rubuta final paper d'in su, hakan ya yi dai-dai da saura kwana hud'u inter house d'in su. Bayan sun dawo gida, sun yi sallah sun ci abinci sun kimtsa, Binty ta d'auki wayar Anna kasancewar ta na ba su suyi game. Numbern barrister Fu'ad ta dannawa kira, lokacin ya na can cikin high coat su na wasu case har wayar ta gama ringing bai daga ba don wayar ma ta na Do not disturb. Sai da ta masa kira biyar ka na ta hak'ura. Sai bayan sun gama wannan shari'ar ya fito ya koma office d'in don harhad'a kayan shi ya dawo gida sannan ya ga miss calls d'in Anna. Hankalin ta she ya bi kiran lokacin wayar na hannun Fanan. D'agawa ta yi ta re da fad'in, "Ya Fu'ad Binty ce ta dunga kiran ka d'azu". Ajiyar zuciya Fu'ad ya sauke ta re da fad'in, "Ok. Yanzu ina ita Binty ta ke??". "Ta na parlourn k'asa ta na jira na mu wuce islamiya". Fad'in Fanan. "To ke mi kike yi da ba za ki wuce Ku tafi ba". "Yaya uniform ni ke sakawa". Fanan ta ba shi amsa. "To maza Ku wuce, ni ma na kusa dawowa. Zan zo na d'auke Ku idan kun ta shi". Fad'in Fu'ad ta re da yanke wayar. Cikin sauri-sauri Fanan ta k'arisa shirin ta fito ta re da samun Bintyn su ka fita ta re da shiga mota driver ya ja su zuwa islamiya. Kamar yadda ya Fu'ad ha yi alk'awari, shi ya je har ya d'auko su da aka ta shi daga islamiyan. Suna tafiya a cikin motar Fu'ad ya juyo ya kalli Binty ta re da fad'in, "Ki na ta kira na d'azu da yawar Anna, mi ya faru?". "Dama in tuna maka ne yau saura kwana hud'u inter house d'in mu, kuma ranar za mu yi hutu. Idan ba ka zo ba, za mu kwance da kai". "Aiko kamar na zo na gama, don bazan yarda mu kwance da sanyin idaniya ta ba". "Ya Fu'ad minene sanyin idaniya?". "Sai kin k'ara girma za ko sani. Yanzu ba za ki ga ne ba". "To shikenan, idan na k'ara girma zan zo na tambaye ka". "Ni kuma a wannan lokacin zan fad'a miki". Fad'in Fu'ad ta re da danna horn, Oga Solomon ya bud'e masu k'ofa su ka shiga ciki. *INTER HOUSE DAY* Finally, yau ce dai ranar da ake gudanar da inter house. Makarantar ta cika sosai da y'an uwa da iyayan yara. Kowa ya na son ya ga k'ok'arin y'ay'an. Anna ma ba'a barta a baya ba. Binty na hango sanye da Gown irin mai bud'e wan nan a k'asa red colour. Ba shi da hannu sai wani safa irin mai net d'in nan shi ma red colour a hannun ta har guiwar hannu. Gashin nan na ta yasha gyara an nannad'o ta re da saka wasu beat ma su kyalkyali red colour sai aka saki jelar har d'uwawun ta. Fuskan nan ya sha make up. Hannun ta rik'e da wani dunk'ulallan flowers red colour masu kyau a hannun ta. A gaban ta wasu k'ananan yara ne su ma cikin gown red colour hannun su rik'e da flowers. A bayan ta kuma wasu y'an mata ne cikin sport wear red colour su na rik'e da bindin kayanta da ke sharar k'asa. Gyefan daman ta wani kyakykyan yaro ne da ba zai wuce sa'an ta ba cikin shigar suit red colour. Gyefan hagun ta kuma Sabrin ce ita cikin grown red colour ta yi kyau sosai amma fuskan nan a murtuk'e k'iris ta ke jira ta fashe da kuka. A hankali su ke tafiya wasu cikin tawagar su suna watsa masu flowers. Sai sauran tawagar red house kuma, wasu na matching ta re da rubuta welcome to red house. Abun dai gwanin burgewa mutane sai d'auka su ke yi a waya. Sai da su ka je har gaban proprietor su ka gaishe shi ta re sa manyan bak'i ka na su ka dawo matsayar su. Haka gaba d'aya sauran houses 'din ma su ka yi. Bayan an gama gabatar da inter house d'in ne, aka fad'i sakamakon house d'in da su ka zo na farko. Kamar ko da yaushe red house dai ita ta zo na farko, ka na green house su ka zo na biyu sai yellow na uku. Nan aka kira su aka ba su kyaututtuka. Bayan an gama duk wannan, aka soma kiran students d'in da su ka zo first position a ko wa ni aji sai iyaye da kuma d'a/y'ar da aka kira iyayan ta su zo su karb'ar mata result ta re da kyautar ta. Lokacin da aka kira Binty Hisham mai goro a matsayin wacce ta zo na d'aya, Ya Fu'ad ne ya fito ya karb'an mata result d'in ta re da kyautar ta ka na aka masu hoto. Har sun kai tsakiyar fili za su koma wajan zaman su aka sake kiran sunan ta a matsayin mai saurin fahimta da kuma kwanya har PC ya fad'a mata suna Genius bayan ya gama wasa ta wanda a baya Sabrin akewa duk wannan. Wannan karan ma sun kusa isa wajan zaman su aka sake kiran ta aka bata muk'amin *Queen of Lead British* ta re da d'aura mata crown a kan ta. A take Sabrin ta fad'i ta su ma. Sosai hankalin Alhaji Saifullahi ya tashi. Bikin da ba'a k'arisa ba da su kenan. Aunty Junaina su ka yi kan ta su ka sa ka ta a cikin mota sai asibiti. Doctor da ya ke duba ta ya ce masu zuciyar da ke ciwo ne ya motsa sakamakon wani tashin hankali da ta shiga. Kuma idan shawara zai ba su kawai su d'auke ta su yi *CANADA* da ita wajan doctor da ya saba duba ta idan ta shiga irin wannan yanayin. Hankali ta shi Alhaji Saifullahi ya kira can k'asar *CANADA* akan a taimaka a yankar masa ticket d'in had'uwa da Doctor Salis Usman Mai rabo (Julaibib). *GA SH NAN, ALK'AWARIN DA NA MAKU JIYA NA BI YA. DUK DA DAI BA NA POSTING SATURDAY AND SUNDAY. A SHA WEEKEND LAFIYA* *MATAR SAYYADEE* 🌹 *35-36*🌹 ............. Cikin rashin sa'a aka shaida masu ya tafi US daran jiya, amma zai dawo nan da kwana biyar. Gaba d'aya Alhaji Saifullahi ya rasa natsuwarsa. Tuni har ya je ya yanki ticket d'in zuwa *CANADA* shi da matar sa Junaina. Hajiya Sakna kuwa, ko da ta ji labarin abunda ya faru wajan su twins kasancewar su ma sun baro na su makarantar sun zo ganin inter house a nan *LEAD BRITISH*, ta ji dad'in yadda hakan ta kasance da Sabrin d'in, amma gyefe guda kuma ta na jin tsananin tausayi irin na uwa da d'a saboda halin da Sabrin ta shiga. Ta yi fatan Allah ya sa hakan ya zama silar shiryiwarta. Abun ya yi wa Hajiya Sakna ciwo kasancewar ba da ita za'a je jinyar y'arta ba. Ta ka sa daurewa har sai da ta yi wa Alhaji Saifullahi magana. Ya ko ta so mata kamar zai cinye ta d'anya ta re da ce mata har ta na da bakin da za ta ce ba'a mata adalci ba bayan ba k'aunar Sabrin d'in ta ke yi ba. Ita kuwa Hajiya Sakna ta san a can d'in ma, k'ara gurb'ata mata tunanin ta za su yi daga Junaina har Alhaji Saifullahin. Washa gari kuwa, Alhaji Saifullahi da Junaina su ka haura gajimare su ka lula k'asar *CANADA* da Sabrin da ta ke kamar gawa don har oxygen aka saka mata a hancin ta. .............Binty tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a k'asa ta sha. Ba ta tab'a tunanin cewa akwai ranar da jama'a za su sota ba. Sai ga shi yau ko ta ina ta gitta magana ake mata ta re da son d'aukar hoto da ita. Yaya Fu'ad kuwa, ba za ta iya k'irga hotunan da su ka yi da shi ba. Camera man ya d'auke su, sannan shi kan shi Ya Fu'ad d'in ya masu salfie da wayar shi ya fi a k'irga. Wasu su yi su hud'u, shi, Binty da Anna da kuma Fanan, wa su kuma su uku, shi da Binty da Fanan. Wanda su ka yi su biyu kuwa, shi da Bintyn ya fi a k'irga. Sai wanda ya masu ita da Fanan. Haka su ka cika boat da gift d'in Binty da Fanan. Don Fanan ita ta zo second position a class d'in su. Bayan sun dawo gida, kaya kawai su ka canza ya Fu'ad ya kwashe su su ka je yawo. Ba su su ka dawo ba sai gab da magriba. Bayan sun idar da sallah su ka shiga bud'e gift d'insu su na gani su na murna. Daddy ma kan shi da ya dawo, sosai ya ji dad'in yadda y'ay'an na da su ke dagewa a makaranta. Shi kan shi sai da ya ba su na shi gift d'in. Don mota sabuwa dal ya canza masu wanda driver zai rik'a kai su makaranta. Sannan ya kuma cire rana d'aya a cikin ranakun sa masu matuk'ar amfani ha fita da su zuwa shopping. Ranar hatta front seat sai da aka cika da tarkacan kaya kamar a bishiya ake tsunko kud'i. *AFTER SEVEN DAYS* *CANADA* ...........Cikin hukuncin ubangiji ranar da su Alhaji Saifullahi su ka sauka a k'asar *CANADA*, shi kuma da kwana uku Julaibib ya sauka a k'asar, kasancewar shi da kan shi Alhaji Saifullahi ya yi magana da shi a waya ya na kuka saboda yadda numfashin Sabrin ya ke sama, sai ta yi kusan minti biyu kamin ya dawo k'asa. Haka ta ke ta yi. Hakan ne kuma ya firgita Alhaji Saifullahi har ya ke ganin zai rasa y'arsa. Da gudu ya fito daga d'akin da aka aje Sabrin d'in ya shiga office d'in wani doctor ya na kuka ya rok'on sa akan ya ba shi number Julaibib. Yadda Doctor ya ga babban mutum ya na kuka haka, sai ya d'aga mashi hankali. Kwantar masa da hankali ya shiga yi ka na daga bisani ya kira masa doctor Julaibib d'in, don ko ya ba shi numbern sa idan zai shekara ya na kira ba zai sa me shi ba. Doctor Julaibib na d'aga wayar Alhaji Saifullahi ya fashe masa da kuka ta re da soma rok'on sa akan ya dawo ya duba masa lafiyar y'arsa ka da ta mutu. Julaibib da a duniya ya tsani ya ji kukan mutum a kusa da shi, balle ma ace mutumin nan shi ya sa ka shi kuka ko kuma wani alfarma ya ke nai ma a wajan shi. Ga shi ya tsani a yi masa magana a cikin kunnan sa da ihu ko kuma da kuka, kai ko yaro ne bai son ya ji kukan sa a kusa da shi. Sam ya tsani surutu, hayaniya kk tashin hankali a inda ya ke, hakane ma ya sa ya ke yakon keb'ance k'ansa shi kad'ai don gudun b'acin rai saboda ya na da mugun zuciya. Katse kiran kawai ya yi ta re da saka hannunsa ya dafe goshin sa. Can kuma ya d'auki wayar sa ta re sa booking flight d'in *CANADA*. Alhaji Saifullahi kuwa ya na jin Julaibib ya katse kiran hankalin shi ya d'uk'unzuma domin a tunanin shi, wulak'anci Julaibib d'in ya masa. Kallon doctor da ya taimake shi ya kira masa Julaibib d'in ya yi ta re da fa'din, "He.. He just off the phone. What I'm I gonna do now". "Calm down sir, I a sure you he will be on his way tomorrow. Just go and rest". Fad'in wannan baturan doctorn. Alhaji Saifullahi zai sa ke magana, doctor Stephen ya yi saurin katse sa ta re da fa'din, "Sir please trust me. You daughter will get better by the grace of God. Just go back and rest". Doctor ya fad'a ta re da D'an bugun kafad'ar shi. Ajiyar zuciya Alhaji Saifullahi ya yi ta re da koma wa d'akin da Sabrin d'in ta ke still nunfashin ta na wannan sama da k'asar. Tsura mata idanuwa ya yi ya na mai k'ara jin k'aunar y'ar ta sa na huda zuciyar shi. A fakaice Junaina ta dallara masa harara ta re da fa'din k'asa-k'asa yadda Alhaji Saifullahi ba zai ji abunda ta fad'i ba, "Sai ma mun koma da gawarta shegiyar d'iyar ta ka za ka yi kuka mai tushe. Mara tsoran Allah kawai. Da sannu zan koya maku hankali daga kai har y'ar iskar uwar gidan na ka. Mtsw". Ta k'arishe maganar da tsaki k'asa-k'asa. "Nagode Junaina". Fad'in Alhaji Saifullahi. Gaban Junaina ne ya buga daam, har ba ta san lokacin da ta zaro idanuwa ta re da fa'din, "Alhaji godiya kuma ta me ka ke min?". "Yadda ki ke kula min da Sabrin kamar d'iyar cikin ki, Allah ya saka miki da alkhairi. Nagode sosai. Na mi ki alk'awarin Bugatti idan mun koma Nigeria in har Sabrin ta sa mu lafiya". Fad'in Alhaji Saifullahi. K'ara Zaro idanuwa Junaina ta yi ta re da fa'din, "Haba Alhaji! Har sai ka min godiya akan kula da d'iya ta. Ai ni kamar yadda na ke jin su Amrah da Hanan a rai na, haka na ke jin Sabrin. Fata na kawai ta samu lafiya". Cikin zuciyar ta kuwa fad'i ta ke, "Dan uwar ki ka da kk mutu, ki yi ta rik'e numfashin ki har Doctorn ki ya zo ya duba ki mu koma Nigeria da ran ki domin mahaifin ki ya cika min alk'awari na idan ya so bayan nan kya fad'i ki mutu, wa ya damu". "Ni kai na nasan duka ki ka d'auke su Junaina. Abunda Sakina ta kasa ganewa kenan". Hawayan munafurci ta soma sharcewa ta re da fa'din, "Hausawa sun ce mai d'a wawa ne, amma wannan maganar ba haka ta ke a wajan Sakna ba. Domin kullum ita gani ta ke ban k'aunar Sabrin. Kuma ni Allah ya san zuciya ta". "Allah ya san zuciyar ki, kuma ni ma nasan na ki. Saboda ki dai na damuwa akan Sakina. Ina ganin harda kishi ke d'awainiya da ita". Fad'in Alhaji Saifullahi. "Allah dai ya baiwa Sabrin lafiya. Shi ne fatana kawai". Fad'in aunty Junaina ta na share kwallar munahinci. "Ameen" Fad'in Alhaji Saifullahi ta re da zama akan kujera ta re da rik'o hannun Sabrin d'in. *WASHA GARI* ...........K'arfe 4:00pm a *MOUNT SINAI HOSPITAL* ta yi wa doctor Julaibib. Da Peter John ya ci karo ya na k'ok'arin fita daga asibitin. Tsaya cak ya yi murmushi d'auke a fuskan ci ta re da mik'awa Julaibib hannu don su yi musabaha. "I don't sake hands with an alcoholic. Get out of my way". Fad'in Julaibib ta re da murtuke fuska. "Ohhh come on, I sweat by god I'll never repeat such a thing again. Please stop avoiding me Julieby (Julaibib)". Ajiyar zuciya Julaibib ya yi, har ji ya yi kan shi ya soma sarawa saboda d'an maganar da Peter John ya tsare shi da shi. "OK, but don't repeat again". Ya na gama fad'in haka ya rab'e shi ya wuce office d'in shi direct. Girgiza kai Peter John ya yi ta re da fa'din, "Bibi, hmmm. My Best friend for ever". Ya fad'i hakane ya na tafiya zuwa wajan motar shi. Julaibib na gama abunda zai yi a office ya nufi office d'in doctor Stephen. Kwankwasa k'ofar ya yi ta re da turawa ya shiga ciki. D'ago kai doctor Stephen ya yi. Cikin second ya mik'e fuskan shi fad'ad'e da murmushi ta re da fa'din, "I knew it". Ta re da barin inda ya ke a zaune ya nufo doctor Julaibib d'in ta re da mik'a masa hannu ya ce, "Welcome sir, the patient is in room number 6 *DQR*". Ya yi saurin dad'in hakan ne saboda kowa na cikin asibitin ya san shi da rashin son magana da surutu a kai. Juyawa kawai doctor Julaibib d'in ya yi ta re da nufar Room 6 *DQR*. Julaibib na shiga ya ga halin da Sabrin ta ke ciki ya sa a ka yi *INTENSIVE CARE UNIT (ICU)* da ita cikin gaggawa. Da shi da Doctor Joshuah su ka rufar mata su na ba ta taimakon gaggawa. Sosai Julaibib ya shiga tashin hankali ganin yarinyar da ba ta wuce 11-12years ba ta har ta kai wannan stage d'in na ciwon zuciya. Bayan sun shawo kan matsalar ne, Doctor Julaibib ya fito daga *ICU* ya nufi office d'in shi bayan ya sa ka an kira masa Alhaji Saifullahi. Jiki na b'ari Alhaji Saifullahi ya zauna a kujerar da ta ke fuskantar na doctor Julaibib d'in ta re da zuba masa idanuwa ya ma kasa tambayar shi mai ke faruwa saboda yadda zuciyar sa ke bugawa. D'agowa Julaibib ya yi ta re da kallon Alhaji Saifullahi ta re da fa'din, "Amma dan Allah idan ban takura ba, zan so sanin shin yarinyar nan ta na hannun mahaifiyar ta ne, ko kuma hannun ruk'o ta ke?". Fad'in Julaibib har da sakin ajiyar zuciya. Domin ba k'aramin k'ok'ari ya yi ba wajan furta kalamar nan. Don shi sam magana na masa wuyar furtawa. "Doctor mai ya sa ka min wannan tambayar?". Fad'in Alhaji Saifullahi. "Saboda yarinyar ka ta kai mataki na biyu a cikin wannan ciwon, kuma idan har aka cigaba da gallaza mata, za ta kai matakin k'arshe da zai yi sanadin bugawar zuciyar ta. Kuma idan haka ta kasance, mutuwa za tayi" Zaro idanuwa Alhaji Saifullahi ya yi ta re da fa'din, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Doctor wallahi a hannun mahaifiyarta ke, mahaifiyar ce wani lokacin ta ke k'ok'arin takura mata. Amma wallahi sosai na ke d'aukar mataki a kan haka, dan girman Allah doctor ka ceci y'ata". Wani file da ke gaban shi ya bud'e ta re da yin rubuta ka na ta d'ago ya kalli Alhaji Saifullahi ta re da fa'din, "Allah ya kyauta. Yanzu dai y'ar ka ta fita daga matsala, sai dai Ku yi k'ok'ari Ku ga ne ko Ku tambaye ta abunda ke damun ta Ku yi mata shi. Saboda the more ta na shiga damuwa, the more ciwon na k'ara tafiya gaba". "In sha Allah doctor zan yi wannan k'ok'arin". Fad'in Alhaji Saifullahi. "Allah ya ba ta lafiya. Za ka iya tafiya". Fad'in Julaibib ta re da d'aukar briefcase d'in sa shi ma ya mik'e. *NIGERIA* ............Abubuwa na ta tafiya Binty normal. Ya yin da duk k'arshan wata sai Kandala ta zo ta karb'i y'an karancy (currency) ta re da uban kayan abinci. Sai da su ka yi wata biyu a gida ka na su ka koma school, kai tsaye aka yi wa Binty double promotion zuwa akin su Fanan wato primary five saboda yanayin kwazon ta da kuma k'ok'arin ta. Sai dai wannan karan Sabrin ba ta dawo makarantar ba don tuni Alhaji Saifullahi ya canza mata makaranta bayan dawowan su daga *CANADA* ya tsare ta ta fad'a mishi duk abunda ya ke damun ta. Ta fad'a mashi wata newcomer aka kawo da ta kwace mata duk wani abu na ta. Kuma ta tsani yarinyar. Wannan dalilin ne ya saka Alhaji Saifullahi ya canza mata makaranta ta koma *NIGERIAN TURKISH* da ke Kaduna. Ta koma boarding school. In da ana ne ta kuma had'uwa da k'awaye y'an k'arya kala-kala irin ta. Kuma tafiyar su ta zo d'aya kasancewar ta samu ma su zuga ta kamar daddyn ta da kuma aunty Junaina. ................Binty kuwa, sai k'ara girma ta ke yi, ya yin da kyawun ta da hasken ta ta re da ilimin da kuma shegen surutun (kamar zuly ta haife ta😂😂😂) ta ya ke dad'a fitowa fili. Gyefe guda kuma Ya Barrister ya na k'ara killace k'aunar Bintyn a ran shi domin har ga Allah har cikin zuciyar shi, rainon Bintyn ya ke yi kuma so ya ke ta zame ma sa uwar y'ay'an sa a nan gaba. D'ayan b'arin kuwa, Hajiya Mansura na nan na babban shiri a kan Binty. Gyefe guda k'awarta Juwairiyya ma na nata shirin. Suhail ne dai ya mance da wata Binty a gidan kasancewar ba ganin ta ya ke yi ba. Harkar shaye-shayan sa ya ke yi ta re da sai da tabar wiwi da cocaine a b'oye. Yanzu abun na shi ya girmama izuwa safarar y'ay'an mutane ya na tura su karuwanci k'asashan waje. ...........Binty sun yi Common entrance, an shiga JSS1. Idan Ku ka ga Binty ba za Ku tab'a gane ta ba. Domin shekarunta sha uku. Duk wani halitta na d'iya mace ya bayyana a jikinta, ba Wai k'iba ta yi can ba. Amma doguwa ce sosai, ga k'ira kamar ita ta yi kan ta. Halittan jikinta gaba d'aya ya fito don ta fi Fanan da ta girme ta cikan jiki. Sannan kuma ta fad'i (balaga) domin ta riga Fanan balaga ma. Don fanan ma ba bu komai a k'irjin ta sab'anin Binty da ba ma za'a kira shi da k'irgan dangi ba. Sannan hankali ya shige ta sosai. Ta fahinci ita wacece, ta kuma ga ne ita ba komai ba ce fa ce tsintacciya da ke cin arziki a gidan su Fanan d'in. Sannan ba ta manta rayuwar ta na kan bola ba, hatta Hamdan ba ta mance da shi ba kuma ta na fatan wata rana Allah ya had'a ta dashi. Ta kan yi kuka sosai a d'aki idan ta tuna cewar *BA TA DA GATA*, tabbas ba ta rasa komai ba a in da ta ke, kuma ta san Anna mutum ce kuma uwa wacce har gaban abada ba za ta mance da ita ba. Ba ta tunanin za ta iya compering Anna da ko wacce mace a duniya. Domin Anna ita ta fito da ita a cikin duhun jahilcin da ta ke ciki har ta san ubangijin ta da kuma yadda za ta bauta mishi. Sanna kuma ta bata ilimin zamani, wannan abun da ta mata kawai ba isa ta biya ta ba. Ta d'auke ta tamkar Fanan. Sannan kuma ta kasa fad'awa Anna ba bu abunda su ka had'a da Kandala ko don mak'udan kud'in da Anna da daddy su ke ba ta a d'aukar su duk abunda Kandalan ta fad'a gaskiya ne. Har gaban gobe ba ta tunanin za ta dai na kukan akan rashin sanin ita wacece, menene dalilin zaman ta akan bola, wani laifin ta aikata aka ya da ta a kan bola. A tunanin ta ko ta hanyar banza aka Samar da ita, bai kamata a yar da ita a kan bola ba. Duk lokacin da tunanin nan ya bijiro mata wuni ta ke yi ta na kuka a d'aki. Ranar rasa gane kan ta ake yi har da Anna. Ya Barrister ne kawai ke iya shawo kan ta. Fita ya ke yi da ita yai ta zaga gari da ita ta re da kai ta ice cream parlour har sai natsuwa ya dawo mata su ke dawowa gida. Kuma a yi tambayar duniya, ta k'i fad'in abunda ke da mun ta. *AFTER FOUR YEARS* ........Wata kyakkyawar yarinya ce sanye da graduation gown kalar blue, hannunta rik'e da hukar nan ta graduation. "Binty zo nan mu d'auki na tarihi dan Allah" Fad'in wata yarinya. K'arasawa Binty ta yi su ka d'auki hoton. Ta na barin wajan wasu dandazon su ma su ka rik'ota su ka d'auki hoton ta re. Da zarar ta yi can, za'a rik'o ta a d'au hoto da ita. So ta ke ta je su d'auka da ya Fu'ad da ke jingine da mota ya na kallon ta ya na murmushi. Da kyar ta iya kaucewa mutane ta tawo wajan Fu'ad ta re da fa'din, "Ya Fu'ad I'm sorry, sun hana ni zuwa mu d'auki hoto da sweet bro d'ina. Zo mu d'auka ta re". Fad'in Binty ta re da matsowa kusa da Ya Fu'ad. Camera man na d'auka shi ma ya na d'auka da wayar shi. Su na cikin d'aukar hoton, tawagar k'awayan ta su ka zo su ka jata. Bin su da idanuwa Ya Fu'ad ya yi ta re jin robar k'aunar Binty na narkewa a cikin zuciyar ta. Sai k'arfe biyu su ka ta shi daga makaranta bayan sun gama karb'an kyaututtuka cike da kewar k'awayan su. Sai dai sun karb'i numbers d'in junan su, duk da su Fanan numbern Anna su ka bayar kasancewar har yanzu ba su da waya. Bayan sun dawo Anna ta shirya masu walima kasancewar saura sati d'aya graduation d'in su suka sauke alqur'ani mai girma. Ranar kuwa Binty da ya Fu'ad zagewa su ka yi su ka d'ika rawa Fanan na masu video. Da daddare Ya Fu'ad ya kawo masu surprise d'in da har sai da Binty ta rungume shi don murna. Waya ce dalleliya k'irar IPhone 13pro max. Sosai su ka yi ta tsallen murna ta re da kwasa sai d'akin Anna su ka nuna mata ita ma ta taya su murna. .............Sanye ta ke cikin riga da wando pallazo kalar orange. Sai dogon takalmi mai tsini a k'afarta kalar fari. Gashin nan na ta ya sha gyara ta yi parking d'in shi a tsakiyar kan ta. Hannunta rik'e da wani jaka da ak'alla zai kai 48k Kalar fari. Sai glasses mai shape d'in love d'in da ta saka da ya cinye kusan rabin fuskan ta da ya sha make-up. Waya ce a kunnenta ta na waya cike da nisha'di. "Ayyaaah Ya Bibi dan Allah kar ka yi fushi da ni, Allah ina shan magani na. Yaushe rabon da mu zo *CANADA* domin ka duba ni ciwo na ya tashi? Ai sai dai kawai muzo checkup. Allah ina kula da kai na ya Bibi". Ban san abunda wanda ta ke wayar da shi na ya ce, sai ce wa ta yi, "Dan Allah ya Bibi na ka dawo, Allah kuwa zan yi kuka. Wai to ko kewan su mom d'in ka ba ka yi ne? Dan Allah ka dawo ko in yi kuka". Ga dukkan alamu cewa ya yi ba zai dawo, ai kuwa sai ta saki kuka ta re da bubbuga k'afa a k'asa kamar ya na ganin ta ta na fad'in, "Please yaaa Bibi ka dawo dan Allah". Washe baki ta yi ta re da yin tsalle ko tsoro ba ta yi ta turgud'e saboda dogon takalmim da ke k'afarta ta ce, "Yeeeeeee! I'm soo sooo happy you're coming back in next to month. Can't wait to see you Bibi". Katse wayar ya yi daga can b'angaran, ita kuma ta soma saukowa daga stairs takalmin ta na ba da sautin k'os k'os k'os. Hajiya Sakna da ke zaune a parlour ta na kallon TV ta d'ago ta kalli inda ta ke jin k'aran takalmi. K'ura mata idanuwa ta yi har ta k'araso wajan mom d'in na ta, ta ce, "Mom zan je gidan aunty, Best friend na birthday yau. Yanzu haka ma ina waya da doctor ya min miss call ya fi goma, so I've to be hurry". "To ni ba lalatacciyar uwa ba ce ba Sabrin, yanzu a haka a wannan shigar za ki fita? To idan kin ga kin fita a haka, to Allah ka ya ki ka canza". Buga k'afa Sabrin ta soma yi ta re da fa'din, "Ni wallahi mom sai na fita, mai shigar na wa ya yi. Hijjab ki ke so in saka a birthday d'in *HAMDAN*, ai wallahi cewa zai yi wulak'anci na zo yi masa. Kamar ni classic babe in saka hijjab, never". Fad'in Sabrin ta na turo ba ki. "Ubanki, uban da ya haife ki na ce Sabrin. Kin ji ko baki ji ba in sake mai-maita maki". Fad'in Fauwaz da shigowar shi kenan. Kallon Fauwaz d'in ta yi ta re da sakar masa harara ta kalli gefe. "Ubanki ki ka harara". Fauwaz ya fad'a. "Ga ni nan ai". Fad'in Alhaji Saifullahi da shigowar shi kenan ya na buga malum-malun. Da gudu Sabrin ta koma bayan shi ta tsaya ta re da rik'e masa malum-malum. *ARE YOU READY??? TO KU GYARA ZAMA KU KIMTSA, DOMIN YANZU LABARIN ZAI SO MA. AN GAMA SHIMFID'A, YANZU ZA KU SHIGA TSUNDUM CIKIN LABARIN*. *@DARMA* *@FAREEDA HARUNA DA SAURAN DA BAN KIRA SU NA BA,* *KU FEK'E ALK'ALUMAN KU, DOMIN YANZU COMMENT ZAI HWARA* *MATAR SAYYADEE* *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *37-38*🌹 ..........."Kun gama antaya min kwandon zagin kai da mahaifiyar ta ka? Na ce kun gama?". Fad'in Alhaji Saifullahi da ke kallon cikin idanun Fauwaz ya na buga malum-malum. Sunkuyar da kai Fauwaz d'in ya yi ta re da susa kyeyarsa ta re da fad'in, "I'm sorry dad, ita d'in ce ta ke wa Mom rashin kunya don kawai ta ce mata ba za ta fita da wannan shigar ba". "To ina ruwan ka? Shegen yaro mai ido a tsakiyar kai. Wannan wani irin bala'i ne haka? Yanzu har da kai Fauwaz ake ga na wa y'ar uwar ka uk'uba? Ko tausayin irin lalurar da ta ke d'auke da shi ba kwa yi. To shikenan, billahi duk na san maganin ku, kuma idan ba saka idanuwa da bak'in ciki ba, mi ye aibu a shigar da Sabrin ta yi? Wallahi ku kiyaye ni kai da uwar ka". Alhaji Saifullahi ya k'arishe maganar da kwafa ta re da kallon Sabrin d'in ya ce, "Shalele rabu da su kin ji. Duk za su sha mamaki. Yi tafiyar ki. Ina ce gidan mummyn ki Saratu za ki". Alhaji Saifullahi ya fad'a ya na shafa kan ta. Ita kuma sai narkewa ta ke yi wai ita daddy's girl. D'aga masa kai ta yi ta re da fad'in, "Eh daddy can za ni. Hamdan ne ke birthday. Kasan best friend d'i na ne shi". "To wani gift ki ka shirya masa?". Fad'in Alhaji Saifullahi. "Daddy suprice na ke son na ba shi, kawo kunnan ka ka ji". Fad'in Sabrin ta re da kai bakin ta dai-dai kunnansa. Hajiya Sakna da Fauwaz, sakin baki su ka yi su na kallon iskancin da Sabrin d'in ta ke zubawa, Alhaji Saifullahi na d'aure mata gindi. Fashewa da dariya Alhaji Saifullahi ya yi ta re da mik'awa Sabrin d'in hannu su ka tafa kamar k'awaye. Alhaji Saifullahi ya ce, "Kwarai kuwa wannan kyautar ta yi, na ma tuna ai shekaran jiya ki ka sa na miki transfern 1.2 zuwa account d'in ki. Gaskiya kin iya zab'e kuwa. Yi maza ki je ka da ki makara". Fauwaz da Hajiya Sakna zaro idanuwa su ka yi ta re da fad'in, "One point two million?". "Eh ina ruwan ku? Ko ku kuke nai mo min kud'in da za ku wani zazzaro min idanuwa kamar agolan nupawa". Gimtse baki Fauwaz ya yi ta re da yin hanyar stairs saboda idan ya cigaba da tsayuwa a wajan zuciyar tafarfasa za ta rik'a yi. Gaba d'aya daddy ya riga da ya gama lalata Sabrin. Hajiya Sakna kuwa galala haka ta bi su da idanuwa har Sabrin d'in ta b'acewa ganin ta. Alhaji Saifullahi kuwa dogon tsaki ya ja ta re da nufar hanyar part d'in sanyin idaniyar shi wato Junaina. Kasancewar ta na ta ya shi nunawa Sabrin d'in k'auna a cewar shi. .............Sabrin d'in na fitowa su ka yi kicib'is da Amrah sanye da lace toques blue da ratsin milk a jiki wanda akai mata doguwar riga abuja bubu. Ka na ta d'auko gyale milk colour ta yafa a kafad'arta ta re da flat shoe shi ma milk colour, sai wayar ta k'irar infinix a hannun ta. "Sister sai ina? Kin ga yadda ki ka had'u kuwa? Ka da fa ki sa go slow a hanya". Fad'in Amrah, kasancewar sannu a hankali aunty Junaina ta koya masu dabarun cin ribar zama da Sabrin d'in. Wani farrr da idanu Sabrin d'in ta yi ta re da jin dad'in kod'atan da Amrahn ta yi ta re da fad'in, "Yau ne birthday d'in best friend, shi ne na ke son na je. Na san yanzu haka ya na can ya na jira kamar zai yi bingiga". "To ko in zo muje ne? Kin ga sai in yi driving, don bai kamata yadda ki ka had'un nan ba ace ke za ki yi driving da kan ki". Ba ta re da Sabrin d'in ta ce komai ba ta jefe ta da key d'in motar ta, wanda a gidan bayan Ya Fauwaz da, mom da aunty Junaina ba bu wanda ke da mota sai ita. Kuma ko Yaya Fauwaz d'in, bai isa ya had'a motar shi da tata ba. Don duk shekara Alhaji Saifullahi ya ke canza mata mota. Gaba ta yi, Amrah na bin ta a baya ta re da antayawa bayan na ta harara. .............Tun daga bakin gate mutum zai fahimci ana wani shagali a gidan. Domin hatta gate sai da ya sha decoration da balloons sannan an ruba *IT'S ANOTHER YEAR* da wani abu mai kyalkyali. Horn Amrah ta yi, mai gadi ya wangale mata gate d'in gidan ta tura hancin motor ciki ta re da nai man waje ta yi parking kasancewar harabar gidan motoci ne da yawa a wajan na abokan *Hamdan* d'in. Tun daga shigowar motar, wani kyakkyawan matashin saurayin sanye da wasu tsadaddun k'ananan kaya, ba zai wuce 22 years ba ya ke ta sakin murmushin don ya san mai motar. Fitowar ta daga cikin motar ne ya saka saurin kallon dandazon abokan sa ta re da fad'in, "Guys, besty ta iso. Ya kuka ga best friend d'in tawa? Ba ri na k'arasa ka da na yi latti". Fad'in *Hamdan* ta re da nufar in da Sabrin d'in ta ke a jingine da jikin motar. Cire glasses d'in fuskarta ta yi ta re da nufar wajan sa ta bud'e hannayanta alamar oyoyo. Hamadan na isowa ya rungumeta ta re da fido wayar shi a cikin aljihun wandonsa ya shiga yi masu selfie su na yin different styles. Amrah da ke gyefe kuma, tsayawa ta yi ta na kallon ikon Allah don kuwa ta san bai da ce ba runguman junan da su ke yi tun da akwai aure tsakanin su. Su kuwa ba su d'auki hakan ba a matsayin komai fa ce wayewa. "Hannunta ya rik'o su ka isa filin da aka zagaye shi da kujeru ta re masa decoration mai kyau. Gyefe kuma DJ ne da kayan sautin sa. "Hello everyone! May I present you my best friend, Queen Sabrin". Fad'in Hamdan. Gaba d'aya wajan suka hau tafi duk da ba yau ba ce rana ta farko wasu daga cikin su su ka fara ganin ta. Don duk shekaran haihuwar *Hamdan* d'in ya zagayo, sai sun yi shagali. Sabrin wani fari ta yi ta re da d'aga masu hannu kamar mai campaign. Hamdan ya cigaba da fad'in, "Kun gan ta ko, kyakkyawa yarinyar, wacce ko India, k'asar larabawa aka je, samun kwatankwacin ta abun ne mai matuk'ar wuya balle a samu wacce ta fita. Ita d'in ta daban ce. Kyawun ba wai daga kayan da ta ke sakawa ba ne, daga jikin ne. Domin kaf matan da su ke nan, da za su yi kwaikwaiyon irin dressing d'in ta don su ga su ma sun haska, to fa ba za su kamo ko k'umbar ta ba, domin kyawun daga jikin ne". Sabrin da ke tsaye, ji ta ke kan ta har wani k'ara kumbura ya ke yi kamar zai fashe. Sosai ta ke jin dad'in abunda *Hamdan* ta ke fad'i har cikin b'argon ta. Ta na matuk'ar so a yabe ta. Kallon DJ *Hamdan* ya yi ta re da fad'in, "DJ, sakar mana sauti". Hamdan ya fad'i hakane ta re da kamo hannun ta duka biyun. DJ kuwa ya sakin masu wak'ar Assique, Hamdan ya shiga juya ta a cikin filin ya na bin wak'ar kamar haka, 🎻 *Hum tere bin ab reh nahi sakte* *Tere bina kya wajood mera x (2)* *Tujh se juda gar ho jaayenge* *To khud se hi ho jaayenge juda* *Kyun ki Tum hi ho, ab tum hi ho* *Ki zindagi ab tum hi ho* *Chain bhi, mera dard bhi* *Meri aashiqui ab tum hi ho* *Tera mera rishta hai kaisa* *Ek pal door gawara nahi* *Tere liye har roz hain jeete* *Tujhko diya mera waqt sabhi* *Koi lamha mera na ho tere bina* *Har saans pe naam tera* *Kyun ki tum hi ho, ab tum hi ho* *Zindagi ab tum hi ho* *Chain bhi, mera dard bhi* *Meri aashiqui ab tum hi ho* *Tum hi ho, tumhi ho* *Tere liye hi jiyaa main* *Khud ko jo yoon de diya hai* *Teri wafaa ne mujhko sambhala* *Saare gamon ko dil se nikaala* *Tere sath mera hai naseeb judaa* *Tujhe paa ke adhoora na raha* *Kyun ki tum hi ho, ab tum hi ho* *Zindagi ab tum hi ho* *Chain bhi, mera dard bhi* *Meri aashiqui ab tum hi ho* *Kyun ki tum hi ho, ab tum hi ho* *Zindagi ab tum hi ho* *Chain bhi, mera dard bhi* *Meri aashiqui ab tum hi ho*🎻 Yadda *Hamdan* ke bin wak'ar da yadda ya ke rawa da Sabrin d'in, za ka d'auka ba indiye ne shi da itan. Bayan wak'ar ya k'are, su ka tafi su ka yanka cake, aiko ta yi masa kaca-kaca da shi a fuskan shi ta kuma k'i bari ya shafa mata a fuska sai guje-guje su ke yi a filin. Bayan nan kowa da ke wajan ya shiga ba shi masa gift. Gimbiya kuwa wajan motor ta ta koma ta re da d'auko jakar magi star ta mik'a masa. Kowa a wajan ya shiga mamaki, kasancewar wannan shekarar ne kawai ta tab'a masa haka. Duk shekara gangariyar abu ta ke ba sa. Wani zuciyar ta ce masa ya bud'e ledar. Aikuwa ya na bud'e makullin power bike ya fad'o. Machine d'in da ya ke matuk'ar k'auna a rayuwar sa. Danna bottun d'in da ke jikin key d'in ya yi, aikuwa machine d'in da ke can gefe sabuwa dal da babu wanda ya lura da ita ta soma k'ara. Aikuwa bai san sanda ya buga wani tsalle ya rungume ta ba ya na murna. Gaba d'aya duk kyautukan da aka kawo masa babu kyautar da ta fi tafiya da shi kama power bike d'in nan. Bayan ya gama ihun jin dad'in shi, su ka cigaba da shagali ta re da rak'ashewa, sai watse-watsen sham pen su ke yi wa junan su a jiki. Sai bayan kowa ya watse ne, Sabrin da Hamdan su ka kwashi gift d'in shi su ka yi d'akin shi da shi. Zama Sabrin d'in ta yi a kan resting chair da ke d'akin na shi ta re da fad'in, "Washhh! I'm tired. Anya bazan kwana gidan nan ba kuwa, don wallahi ba zan iya driving ba, sai dai idan za ka kai ni gida". "Ba ta re Ku ka zo da k'anwar ki ba, ai kamar idan ba idanuwa na ba ne, na gan ta lokacin da mu ke rawa". Fad'in Hamdan. "Ita ce, ta wuce gida maman ta ta kira ta". Fad'in Sabrin ta re da kwanciya a kan resting chair d'in. "To ba ri na yi wanka, sai na raka ki. Ni ma ina son zuwa Kaduna jibi in sha Allah". Hamdan ya fad'a. Wani d'agowa Sabrin d'in ta yi ta watsa masa harara ta re da sakin dogon tsaki ka na ta ce, "Wahalallan banza kawai, ba Kaduna ba ka zagaye duniyar. Wallahi na san ba uncle Sauban za ka je ga ni ba, wannan gantalalliyar yarinyar y'ar kan bolan da kullum ka ke ishen mutum da labarin ta za ka nai ma, kuma wallahi idan ba kai wasa ba, sai na Shiva wajan mummy na fad'a mata". "Dan Allah ki fi jirgi gudu. Da ya ke ma iya mummyn da kan ta za ta aike ni Kadunan. Kuma idan dai Beauty ce, wallahi ba zan ga ji da nai man ta ba har sai Allah ya sake had'a fuskokin mu idan Allah ya k'adarta hakan a gaba. Wallahi ni fa duk wanda bai k'aunar Beauty, ni ma fa bai k'auna ta. A matsayin ki na Besty na, wallahi bai ka ma ta ki rik'a k'in Beauty ba. Na san ko ke kika gan ta, sai ta burge ki. Very beautiful girl. Ban tab'a ganin mace mai kyau irin ta ba". Fad'in Hamdan. Haba tuni Sabrin ta kawo wuya. A zafafe ta mik'e ta re da fad'in, "Mak'aryacin banza da wofi. D'azu a wajan birthday party d'in ka ka gama fad'awa mutane I'm the most beautiful girl you have ever seen, shi ne yanzu za ka ce wai wani ba ka tab'a ganin kyakkyawa kamar ta ba. Mayaudari kawai mai kan gwanda. I hate you. Kuma wallahi na fi ta kyau. Ita da *BA TA DA GATA*, y'ar *BOLA* da ita. Duk yarinyar da ka ga an yar da ita a bola, to *ZINA* a kan yi da uwarta aka haife ta. Shi ne har za ka tsaftatacciya kamar ni da datti irin ta. I hate.........". Ka fin ta k'arisa maganar Hamdan ya katse ta da fad'in, "Out..! Fitar min a d'aki right now. Sau nawa zan dunga fad'a mi ki akan ki bar kiran Beauty da y'ar *ZINA*? Idan ma haka aka yi aka haife ta, ai ba laifin ta ba ne. Ke ma ba dabarar ki ba ce da aka haife ki da aure. Out now before I loss my control". Hamdan ya k'arisa fad'in maganar da tsawa. Mik'ewa Sabrin d'in ta yi ta re da fad'in, "It Isn't your fault wallahi. Laifi na ne da Har na yi attending birthday party d'in ka shiyasa ka ke min wulak'anci. Kai da ba dan cousin d'ina ba ne, wallahi da yau ba za ka kwana a gidan uban ka ba, amma from now ka rubuta ka aje, ba ni ba ka, ni ba best friend d'in ka ba ce Ku ma. Kar ka sake kira na a waya. I'm deleting your number right now". Fad'in Sabrin ta re da fiddo wayarta ta yi deleting numbern Hamdan d'in ta re da fita daga d'angin ta bugo masa k'ofar. Kicib'is su ka yi da mummy Saudat, rab'e ta ta yi ta re da wuce wa ko gaishe ta ba ta yi ba. Mummy Saudat na kwad'a mata kira, amma ko juyowa ba ta yi ba ta wuce wajan motarta ta re da baron gidan. D'akin Hamdan d'in ta nufa ta na dariya ci kin zuciyar ta, domin idan da saboda Sabrin da Hamdan sun saba irin wannan fad'in, kuma cikin kwana biyu su shirya kan su, shiyasa ba mai shiga tsakanin su, don idan za ta iya tunawa, to wannan fad'an na su shine na d'ari da Saba'in kuma su na shirya kan su ba ta re da Sanin kowa ba. *_____________________* ............."Dan Allah Fanan ki yi sauri, wallahi na k'osa mu fita ka min Anna ta dawo ta ce ba za mu fita ba. Kin san fa ba nisa ta yi ba ". Fad'in Binty da ke tsaye a kan Fanan da ke kwalliya a jikin madubin d'akin na su. Sanye ta ke cikin atampa doguwar riga kamar maroon da toch of golden. Doguwar riga ce d'inkin zamani irin mai aljihun nan. Ba k'aramin kyau kayan su ka mata ba. D'aurin zamani, duk da nannad'e gashin ta da ta yi, sai da gashin ya fito ta k'asan d'aurin da ta yi. Sai dai ribom d'in da ta saka ta kama gashin, shi ya d'ago da d'an kwalin ta kamar ta yi irin ture ka ga tsiyan nan. Siririn gyale kalar maroon ne a k'afarta, sai flat shoe shi ma kalar maroon a k'afar na ta. Babu abunda ya fi d'aukar hanakali a jikinta kamar jan lallan da ke kan y'an yatsun ta da ya k'ara fito da kyawun hannun kasancewar ta farar mace. "Dan Allah one minute. Yanzu zan gama". Fad'in Fanan da ke shafa jan baki a leb'anta. Mik'ewa ta yi ta re da d'aukar gyalanta, ita ma irin shigar da ke jikin Binty shi ke jikinta. "Muje ka da ki cinye ni d'anya". Fad'in Fanan. Wayar ta da ke kan mirror ta d'auka ta re da fita Fanan na biye da ita a baya. Su na fitowa Hajiya Mansura ita ma ta fito za ta fita, kallon Bintyn ta ke yi from head to toes ka na ta ce, "Ina za ku je da ranar nan?". Ka min su ba ta amsa sai da su ka gaishe ta, ka na Fanan ta ce, "Za mu ce saloon ne, daga nan kuma za mu bi ya mu d'an yi shopping". "To Ku kula da kan ku. Ke idan kun dawo ki zo part d'ina ki same ni". Hajiya Mansura ta k'arisa maganar ta na kallon Bintyn. "To Hajiya". Fad'in Binty ta na kallon k'asa, don haka nan ta ji ta na mugun tsanar ta, shiyasa ko duk in da ta san za su had'u, ba ta bi ta wajan. Ganin sun fito, tuni driver ya d'auko mota ya nufo har in da su ke, kasancewar umarni Anna ta ba shi akan duk in da za su, idan har ba Ya Fu'ad ba ne zai fita da su, to ba ta yadda su fita su d'aya ba, ya kai su. Shiga motar su ka yi, saloon d'in su ka fara zuwa. Sun jima a wajan kasancewar gashin Binty na da yawa sosai. Ko da su ka fito su ka zo wajan mota, Kamale driver har ya soma bacci sai da su ka ta da shi. Daga nan shop rite su ka nufa. Wajan kayan shafa su ka soma zuwa kasancewar turare da kayan kwalliyan su sun k'are, kit kuma su ke so su sake had'awa. Bayan sun gama da nan kuma su ka koma wajan da su ka fi auki wato wajan kwalama. Juyowar da Binty za ta yi, idanuwan ta su ka sauka a kan shi. Gaban ta ne ya buga da k'arfi. Da sauri ta dafe saitin zuciyar ta da ke buga fat fat fat. Dogone sosai, irin kyakkyawan nan ajin k'arshe. Fari ne sosai don duk hasken fatan ta ya fi ta fari, ya fi kama da irin farin Indiyawa. Ya na da manya idanuwa da dogon hanci, bak'in shi k'arami irin wanda akewa lak'abi da pink lips d'in nan. Ga sajan da ya k'ara k'awata fuskan shi ta re da d'an gemu irin na gayun nan da ya aje bak'ik'k'irin. Ya na da dimple a both chick d'in sa wanda motsa bakin ya yi sai ya lob'a. Siriri ne amma ba irin can d'in nan ba. K'irjin shi a bud'e ya ke amma ba can sosai ba. Kasancewar ya na facing d'in ta ne shiyasa ta iya k'are masa kallo haka, amma Sam shi hankalin shi ma ba ya kan ta. "Uncle Yusuf chocolate please". Fad'in wata kyakkyawar yarinyar da ba za ta wuce 8 years ba ta fad'a ta na jan hannun shi. Kallan gefen da ta ke ya yi, Binty ba ta san lokacin da ta furta, "Hasbunallahu wani'imal wakeel. Wayyo Allah!". Ta fad'i hakane sakamakon side view d'in sa da ta ga ni, sai ta ga ya fi kyau idan ya kalli gefe. Chocolate ya d'auko ta re da mik'awa wannan kyakkyawar yarinyarta re da sakin mata murmushi. Yuuu Binty ta tafi za ta fad'i, Fanan da tun san da Binty ta k'urawa wannan bawan Allah idanu wanda ita kan ta ya tafi da imaninta ta ke kallon ta ta yi d'aurin taro Bintyn ta re da fad'in, "Haba sis kar ki ba da mu mana. Behave your self"......... *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *39-40*🌹 ............."Fanan ki na ganin abunda na ke ga ni kuwa? Wallahi guy d'in nan ya had'u sosai". Fad'in Binty. "To ko za ki je ki masa magana ne? Tun da ba ki da aji. Idan rabon ki ne, ki na nan zai zo ya kula ki. Dan Allah ki nutsu". Fanan ta fad'a a d'an zafafe. Sai a lokacin Binty ta dawo hayyacinta ta re da shan mur ta kuma dai-dai ta natsuwarta. Amma har a wannan lokacin ba ta dai na satar kallon shi ba. Hannunta Fanan ta rik'e ta re da barin wajan su ka nufi wajan biyan kud'in abunda su ka saya. Bayan sun biya an saka masu abubuwan a leda, Binty ta na d'auka ta na mai addu'ar Allah ya sa ta sa ke ganin wannan mutumin ko sau d'aya ne ka min ta bar shop rite d'in. Juyawar da za ta yi su ka ban ga ji juna, sai da kayan da ke hannunta ya watse, shi kuma tsadaddiyar wayar da ke hannunsa ya sub'uce ya fad'i, a ta ke screen d'in wayar ta yi watsa-watsa. "Yah subhanallah!". Guy d'in nan ya fad'i ta re da saurin duk'awa ya soma tattaro mata kayanta da su ka watse. Fanan kuwa saurin zuwa ta yi ta d'aga ta ta re da fad'in, "Kin ga irin abunda na ke guje miki ko. Ai Gashi nan garin kallon sa kin fad'i. Ai sai ki ta shi". "Ni wallahi ba shi na ke kallo ba, karo mu ka yi ban san ya na baya na ba". Binty ta fad'a ya yin da ta ke mik'ewa kamar za ta yi kuka. Wannan guy d'in k'arasowa ya yi hannun shi d'auke da ledar kayan Binty, wannan kyakkyawar yarinyar na biye da shi a baya ta na shan chocolate d'in da ke hannunta. "I'm very sorry ma'am, hope you're okay". Fad'in guy cikin wata zazzak'ar muryan da ya sumar da Binty ta shiga bin bakin shi da kallo ba ta re da ta ce uffan ba. Tsungilin ta Fanan ta yi a cinya wanda shi ya dawo da ita cikin hayyacinta ta re da saurin fad'in, "I'm.... I'm okay. I'm very sorry too". Fad'in Binty cike da rawar murya ka na kuma ta mayar da duban ta izuwa ga wayarsa da ke ya she a k'asa a farfashe. Cikin sauri ta k'arisa wajan wayar ta re da d'auko shi ta ce, "Na shiga uku na fasa masa waya". "Ohhh kar ki damu, tsautsayi ne ai ba laifin ki ba ne ba". Fad'in guy d'in nan ya na sakin murmushi da ke k'ara bayyanar da bayyanan nan kyawun sa. Daga Binty har Fanan sakin baki su ka yi su na kallon shi, domin ba su tab'a tunanin za su ji Hausa a bakinsa ba. Duk a tunanin idan yaruka su ka wuce ukun nan, to ba su tsammanin ya na jin wasu yaran, wato English, Hindi ko Arabic. "Ku na mamaki ne? Ina jin hausa sosai kamar jakin kano. By the way, I'm Yusuf Muhammad Ahlam. Can I know yours?". Binty ta kasa magana, domin muryan shi ba k'aramin rikita ta ya ke yi ba. Guy d'in ya yi ne sosai. Fanan ce ta iya k'arfin halin fad'in, "I'm Fanan Usman mai goro, and my sister, Binty". "Very nice name. You all have beautiful name". Fad'in guy d'in. "No one Care's about mine? Hmm my name is Ayeesha Fairuz Ahlam, his youngest niece. I'm the last born". Kyakkyawar yarinyar nan ta fad'i ta na dariya. Kamannin su d'aya da wanda ya kira kan shi da Yusuf, ko ba ta fad'a duk wanda ya gan ta ya ga k'anwar sa ko y'ar sa. "Ohhh you're soo beautiful dear". Fad'in Fanan ta re da rik'e kuncin yarinyar. "I knew it". Fad'in yarinyar ta re da sa ka chocolate a bakin ta. Gaba d'aya dariya su ka fashe da shi har da Binty da ta kasa magana. "If you don't mind, can I drop you?". Fad'in Yusuf. "Ohh no, don't worry, we are with our driver, he's waiting outside". Fad'in Fanan. Murmushi ya yi wanda hakan ya kasance d'abi'ar sa ne ta re da kallon Binty ya ce, "Hey miss Beauty, can't you talk?". Kunya duk ta rufe Binty, duk sai ta daburce ta rasa mai za ta ce. "She's so beautiful, please can we take a salfie?". Fad'in Ayeesha. "Indeed she's beautiful. Please za ki ba ni ita in aure ta?". Fad'in Yusuf ta re da kallon Fanan. Binty kuwa ba ta san lokacin da ta kwasa da sauri ba ta yi hanyar waje gabanta na fad'uwa at the same time kuwa ta na jin wani dad'i na mamaye zuciyarta. Bud'e mota ta yi ta shiga, driver na mata magana ko sauraran shi ba ta yi ba. "Indeed she's beautiful. Please za ki ba ni ita in aure ta". Maganar Yusuf ya k'ara yi ma ta gizo a kunnanta. Dariya ta yi ta re da saka kan ta a tsakanin cinyoyinta. Kusan mintuna goma Fanan ta taho da kayan da su ka siya. Both ta bud'e ta re da saka kayan, sannan ta zagayo ta bud'e gidan baya in da Bintyn ke zaune ta re da rufo motar. Driver na ganin haka ya ja motar ta re da kallo baya ya ce, "Gida mu ka nufa, ko kuwa akwai wani wajan da za ku sake zuwa?". "Ah mun gama komai, gida mu ka yi". Fanan ta ba shi amsa. Kallon ta Fanan ta yi ta re da fad'in, "Juliet ta had'u da Romeo d'in ta". "Ban ga ne ba, mai ki ke nufi da hakan?". Fad'in Binty ta na maka mata hararar wasa. "Love at first sight ko? Na ga wannan. Wannan irin kasa control d'in kai haka, lallai Yusuf ya daki zuciyar ki lokaci guda. To ki kwantar da hankalin ki, domin shi ma ya fowler, ba kuma ba shi numbern ki, sai ku yi ta k'onewa, amma kuma kar ki sake Anna ko ya Barrister su sani, na san ba ki manta dukan da ya barrister ya wa wannan anacin da ya din ga biyo ki tun daga wajan saloon ba har cikin gidan nan. Kar ki manta ya Barrister ya ce ba yanzu za mu fara kula samari ba, kuma Anna ta goyi da bayan shi. Saboda secret love za ku yi kamin a ba mu dama". Ya mutsa fuska Binty ta yi ta re da fad'in, "I don't understand, ki na nufin kin ba shi number ta, to wa ya saki? Ni fa kawai burge ni ya yi ba wai son shi na ke ba. Kin b'ata min rai. Ai wannan jawo min zubewar aji za ki yi". Fad'in Binty har da wani shan mur. "Iyyyeeee, to ki sa ni bariki dai babu riba. Ki fad'a uban da bai san halin ki ba. Ke ni fa ko da d'uwawu ki ka yi magana sai na fahimci abunda ki ka ce bare na ga abu b'aro-b'aro. Maza ki kula da titi". Dariya Binty ta yi sosai ta re da fad'in, "Ban ga ne in kula da titi ba". "Eh saboda motoci mana". Fad'in Fanan ta na hararar Binty. Dariya Binty ta yi ta re da fad'in, "Wai dan Allah dagaske ya karb'i number ta?". "Ni ma ban sa ni ba". Fad'in Fanan ta re da kallon window. "Haba sister, dan Allah ki fad'a min mana. Na bar miki autan, yanzu ke ce autares d'in Annan mu". Harara Fanan d'in ta k'ara sakar mata ta re fad'in, "Bariki". "Ke dai kalmar bariki ta ka ma bakin ki. Dan Allah Sister ya ki ka ga guy d'in, ya had'u sosai ko?". Fad'in Binty. "Kamar saman alalen gwangwani kuwa". Fad'in Fanan ta na dariya. "Wallahi k'arya ki ke yi, sai dai idan ba za ki fad'i gaskiya ba. Amma Yusuf had'ad'd'an guy ne wallahi. Komai na shi mai kyau ne. Fuskan shi, tsayin shi, maganar shi, murmushin shi, kai infact everything". Ba ki sa ke Fanan ke kallonta ta re da fad'in, "Har yaushe ki ka san shi haka da za ki ce everything about him? Yaushe ki ka san everything d'in?". "Man ta kawai, amma sincerely speaking guy d'in ya yi over". Fad'in Binty. "Kar dai ki haukace". Fanan ta fad'a ta re da daukar wayar Bintyn da ke kan ciyarta ta yi kwafe numbern Yusuf a wayarta ta re da sakawa a wayar Bintyn ta yi mata saving da Mr Right ta re da mik'a mata wayar. "Ga shi nan na miki saving numbern shi, kin ga da ya kira kin san ko waye, saura ki yi shirme". Fad'in Fanan. Karb'ar wayar ta yi ta re da tsurawa numbers d'in idanuwa. Cikin minti d'aya ta haddace numbers d'in kasancewar special number ce. Labarin Yusuf su ka din ga yi har su ka kai gida. Cikin ikon Allah kuwa, har wannan lokacin Annah ba ta dawo ba. ...........Ko da su ka shiga d'akin su, sallar la'asar su ka yi kasancewar a hanya ta riske su. Bayan sun idar kuma su ka d'aura hirar Yusuf. Sai k'arfe biyar su ka sauko don d'aura girki saboda tun sa su ka kammala makaranta su ke girkin dare. Idan wannan ta yi yau, gobe wannan za ta yi, ko kuma su had'u su duka su yi ta re, haka Anna ta tsara masu. Su na kitchen Fanan na gyara kayan miya, Binty kuma na blending, Fasila ta shigo. Sai da ta fakaici idanu ta watsawa Binty harara wacce ba ta ma San ta na yi ba, ka na ta yi gyaran murya duk su ka juyo su ka kalle ta ta re da fad'in, "Aunty Fasila ke ce?". Hakan su ke kiran ta, kasancewar ta girme su kusan da shekaru biyar. Don ita za ta kai ishirin da uku, su kuma sha takwas gare su. "Autan Anna sannun ku da aiki". Fad'in Fasila ta na murmushi. "Yauwa aunty Fasila". Ga ba d'ayan su suka amsa. Fasila mai da duban ta ta yi izuwa ga Binty ta re da fad'in, "Binty Hajiya Mansura na kiran ki, ta ce ki zo yanzu". Zaro idanuwa Binty ta yi ta re da fad'in, "Na shiga uku! Wallahi na man ce ta ce idan mun dawo in zo in sa me ta". "To ai sai ki hanzarta yanzu ki je ki ji kiran da ta ke miki. Ba ri ni na taya Fanan mu yi aiki". Binty ta ce, "To aunty nagode". Ta fad'i hakane ta re da tara hannun ta a panpo ta wanke ka na ta goge hannun ta towel ta re da cire apron d'in da ke ji jikinta ta aje a wajan da ake rataye shi a nan kitchen d'in ka na ta fito daga kitchen d'in ta d'auki hijjab d'in ta da ke parlour ta saka ta fito ta yi hanyar part d'in Hajiya Mansura. Za ta iya rantsewa da Allah yau ne karo na hud'u shigowarta part d'in Hajiya Mansuran. Gwara ma part d'in Hajiya Huriya, kasancewar ta na da d'iya mai suna Sunaina, to su kan d'an shiga wajan don ita kan ta Sunaina irin d'abi'ar mahaifiyar ta gare ta na nai man kud'i. Ka na duba status d'in ba bu abunda za ka ga ni sai uban kayan kitchen da lesis da atampopi har da kayan yara da ta ke ordering d'in su idan mutane sun mata magana su na so sai a kawo mata ta ruwa, sea shipping. Ba bu kowa a parlour, sai y'ar aikin ta Wasila da ke goge dinning. Kallon ta Wasilan ta yi ta re da hararar ta k'asa-k'asa ka na ta ce, "Ki hau sama, ta na can ta ke idan kin shigo ki je ki same ta". Fad'in Wasila kamar ta na da cuta a mak'ogwaro. Ba ta re da Binty ta ce komai ba ta haura sama. Sai da ta yi knocking aka ba ta izinin shiga kamin ta saka kai cikin d'akin. Kwance ta taras da Hajiya Mansuran daga ita sai brezia da underwear, ga ta ba ka d'an, don Mansura irin shiirgegiyar matan nan ne kamar giwa. Kawar da kai Binty ta yi don ta ji kunya da ta ga Hajiya Mansuran a haka. "Ina wuni Hajiya?". Binty ta fad'a ba ta re da ta kalle ta ba. "Lafiya lau. Ya a ka yi na ce idan kun dawo ki zo ki same ni, amma ba ki zo ba. Ko Na'ima ta hana ki zuwa waje na ne?". Fad'in Hajiya Mansuran. Girgiza kai Binty ta yi ta re da fad'in, "A'a wallahi. Anna ma ba ta nan. Mancewa na yi da muka dawo shiyasa ban zo ba". Kallon Binty ta ke yi ta na jin kamar ta tashi ta rungumeta ta re da sauke sha'awarta. Ji ta ke wani irin wutar sha'awar Bintyn na taso mata tun daga kwakwalwarta. "Zo ki zauna a nan, wani d'an abu za ki min". Fad'in Mansura ta re da nuna mata gefen ta. K'arasowa Bintyn ta yi ta re da zama a wajan da Hajiya Mansuran ta nu na mata. Shafa bayan Binty ta yi ta re da fad'in, "Yarinya ta tubarkalla ki na da kyau mai d'aukar hankali, ina ma ki zamo suruka ta". Banbara kwai haka Binty ta ji maganar, wai suruka. Tur Allah ya kiyaye mai za'a yi da Suhail a matsayin miji. Duk cikin zuciyar ta ta yi wannan maganar. "Jiki na duk ya min tsami wallahi. Kin san jikin tsufa. Dan Allah massage na ke so ki min in ji dad'in jikin nawa". Hajiya Mansura ta fad'a ta na k'ara shafa bayan Bintyn. Binty ba ta kawo komai a ranta ba, don Annah ma ta na sa su ita da Fanan su danna mata jikin ta har k'afafu. Ruf da ciki Hajiya Mansura ta yi, ita kuma ta shiga danna mata jikin tun daga k'eyarta har k'afafunta. Tuni Hajiya Mansura ta soma lumshe idanuwa, kasancewar ta saka wani abu daban a cikin zuciyar ta, sai ta ke ji kamar Bintyn romancing d'in ta ta ke yi. Binty ta fi k'arfi minti talatin ta na yi was Hajiya Mansura massage. Sai da Hajiya Mansura ta gamsu don bala'i, ka na ta ce wa Binty ya isa ta re da kwararo mata godiya har da mata kiss a kumatu. Ita kuwa baiwar Allah ba ta kawo komai a ranta ba, ta fice daga d'akin. A k'ofar fita daga part d'in su ka yi kicib'is da Suhail shi kuma zai shiga wajan mahaifiyar sa. "Keee!". Suhail ya fad'i ya na k'are mata kallo har da had'iyar yawu. Gitta shi ta zo yi za ta wuce, aikuwa ya damk'i hannunta da k'arfi ta re yin side d'in shi da ita. Binty turjewa ta ke yi, amma Sam ya k'i sakin ta gashi ba bu kowa balle wani ya cece ta. Sai da ya kai ta har kan gadon shi, ka na ya yasar da ita ta re da yi mata rumfa.......... *PLEASE MANAGE, WALLAHI INA WANI AIKI NE MAI MAHIMMANCI* *MATAR SAYYADEE* 🌹 *41-42*🌹 .............Wani ihu mai k'arfi ta saki sakamakon jikinsu da ya had'u waje d'aya da ya haifar mata da wani azaba a saman fatanta kamar ana d'iga mata ruwan dalma. Hannun shi ya saka ta re da toshe mata baki, d'ayan hannun Ku ma ya soma yawo da shi a jikinta. Binty ba ta san sanda ta saka duka k'arfinta ta cire hannun shi a kan bakinta ba ta re da k'ara sakin wani k'aran. Saboda the more hannun shi na tab'a jikinta, the more azabar da ta ke ji a jikinta na k'aruwa. "Hasbunallahu wani'imal wakeel, inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un. Dan girman Allah ka dai na tab'a ni. Fatan jikina na k'onewa. Na shiga uku Anna ki cece ni". Binty ta fad'i da k'arfi, amma babu mai jin ta saboda d'akin a rufe ya ke, ku ma ko za ta kwana ta na ihu babu mai jin ta. Mari ya d'auke ta da shi ta re da fad'in, "Uban baban ki, wallahi ko wa ya tsaya miki yau sai na d'and'ana roman ki, ba zai yu ki zauna a gidan nan mahaifi na na kula da ke ba, ba dangin iya ban mori wannan kyakkyawan jikin na ki ba. So gwara ma ki tsaya mu yi cikin jin dad'i, in ji dad'i ke ma ki ji". Fad'in Suhail ya na k'ok'arin farke rigar jikin na ta. Wani irin nin kin azaba ta ke jin a jikinta duk sa'adda ko farcensa ne ya tab'a jikinta. Bakin shi ya kai zai had'e da nata ta yi wani irin nishin azabar da ta ke ji ta re da wani irin huci wanda Suhail bai san sanda ya yi k'undun bala ya fad'o daga kan gadon ba, sakamakon hucin da ya fito daga bakin ta ya tab'a leb'an shi, sai ya ji kamar kyasta masa wuta aka yi a kan leb'an nasa, don har wajan ya tashi ya yi wani irin bororo kamar ya k'one. Ita kuwa Binty da ta ga ya d'aga ta ya koma gefe, wani irin tsalle ta yi ta sauko daga kan gadon ko hijjab d'in ta da d'an kwalinta da ke yashe a k'asan d'akin ba ta yi ba ta fita ta bud'e d'akin, da gudu ta yi side d'in su ta na kuka ta na soshe-soshe ta re da kwala kiran sunan Anna. Da gudu Anna da tun d'azu ta dawo ta zauna a parlour ta na jiran dawowar Binty ita da Barr Fu'ad da ke gefen Anna ya na cin apple su ka fito. Fanan da ke kitchen har ta riga su isa wajan da Bintyn ta ke ta re da ruk'o su. "Anna na shiga uku, Anna na shiga uku. Bayana, jiki na, Anna k'onewa na ke yi ki taimake ni". Fad'in Binty ta re da kwace jikinta a jikin Fanan d'in ta na wani irin kuka ta re da birgima a k'asa. "Na shiga uku, Fu'ad taimake ni ka d'auko min ita ka kawo ta d'aki". Fad'in Anna hankali ta she. Da sauri Barr Fu'ad ya je in da Binty ta ke ta re da ciccib'arta. Aikuwa ta Ku ma tsandara wani uban k'ara sakamakon jikin Barr Fu'ad da ya had'u da nata jikin sai azabar ya k'aru. "Wayyooooo Annah mutuwa zan yi wallahi. Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, na shiga uku". Binty ta sa ke fad'i. "Anna muje asibiti kawai". Fad'in Barr Fu'ad ta re da nufar parking space hannunsa rungume da Bintyn da sai zamewa ta ke yi ya na sa ke rik'eta ta na fizge-fizge kamar mai shigar aljanu. "Muje kawai, ke Fanan ki koma ki kula da girki". Fad'in Anna ta re da nufar parking space. Da gudu-gudu Fanan d'in ta bi bayan Anna ta na kuka ta re da fad'in, "Anna dan girman Allah ki ba ri na ni Ku, wallahi ba zan iya natsuwa ba idan har ban san halin da Binty ta ke ciki ba". Ba ta re da Anna ta sa ke cewa komai ba ta bud'e gidan baya ta shiga, Fanan ma ta yi saurin shiga motar. Da gudu Barr Fu'ad ya motar su ka bar gidan. Wani irin gudu ya ke yi wanda ya wuce misali, amma saboda tashin hankalin da Anna ta ke ciki, ba ta iya kwab'a masa ba har su ka isa asibiti. Parking ma ba mai kyau ya yi ba, hakanan duk su ka fito gaba d'ayan su. Barr Fu'ad ya fiddo Binty da ke ta kuka a gaban mota. Jikin su na kuma had'uwa ta tsandara wani irin ihun da sai da ya zawo hankulan jama'ar da ke farfajiyar asibitin. Gudu-gudu Barr ya nufi cikin asibitin, aikuwa cikin sauri nurses su ka kawo wanna gadon gungura marasa lafiya Fu'ad ya d'aura ta akai. Da shi aka gungura ta zuwa d'akin taimakon gaggawa, sai da su na zuwa bakin k'ofar aka hana Barr Fu'ad shiga. Anna da Fanan su ka k'araso in da ya ke hankalin su gaba d'aya a ta she. Babu wanda ya iya cewa kowa k'ala a cikin su. Idanuwa Barr Fu'ad ya kad'a ya yi jazur, ya yin da Annah sai share hawaye te yi. Fanan kuwa riris ta ke yin kuka. Sai da su ka kwashi awanni biyu a kan ta, ka na su ka fito da ita su ka kai ta d'akin hutu amma sun hana kowa ya shiga. Doctor ne da ya fito ya ce su bi shi office. Don tashin hankali gaba d'ayan su ka bi shi office d'in. Ko zama sun kasa yi, sai da doctor ya nu na masu wajan zama ka na su ka zauna. Gyaran murya doctor ya so ma yi ta re da fad'in, "Amma garin Yaya ta k'one haka a jikinta? Man gyad'a ne ya fallatsan mata ko kuma gobara ce ta tashi ta soma cin jikinta aka kawo mata d'auki?". Kallon-kallo aka shiga yi tsakanin Anna, Barr Fu'ad da kuma Fanan. Can dai Anna ta ce, "Wallahi doctor ba mu san mai ya same ta ba, ihunta kawai muka ji ta na fad'in jikinta na k'onewa". Ajiyar zuciya doctor ya sauke ta re da fad'in, "To Allah ya kyauta, amma dan Allah mu rik'a saka idanuwa akan yaran mu, domin idan wani abu ya same su, mune da asara. Sannan yanzu dai munyi iya abunda za mu yi, sauran mun barwa Allah, amma magana ta gaskiya, jikinta ba bu kyawun gani don duk ya sale ya yi bororo alaman k'una ce sosai ta yi". Fashewa da kuka Fanan ta yi har da shashshek'a. Anna da Barr Fu'ad kuma salati kawai su ka dunga yi, don Anna jikinta har wani rawa ya ke yi ta re da tunanin waye ya k'ona mata d'iyar. Kuma k'udurta a ran ta sai ta d'auki tsattsauran mataki akai. Bayan sun fito daga office d'in ne, Barr Fu'ad ya kalli Anna ta re da fad'in, "Wallahi tallahi wannan karan ba zan hak'ura ba, sai mun shiga kotu da ko ma wanene wanda ya aikata mata wannan d'anyan aiki". "Kwarai ina bayan ka 100%, ba zai yu a kashe y'ar mutane da aka bar min amana ba. Ga shi ni saboda tashin hankali na manta da waya ta a gida balle in kira Kandala in sanar mata da halin da y'arta ta ke ciki". Fad'in Anna. "To ba ri mu koma gidan ni da Fanan, sai mu harhad'o abubuwan da zamu buk'ata a nan d'in, daga nan sai mu tawo da wayar ta ki". Fu'ad ya fad'a. "Hakan ya kamata, amma yanzu ga ban wayar ka, ko kuma kira min baban ku in shaida masa muna asibiti". Fad'in Anna. Wayarsa ya fiddo ta re da dailing numbern mahaifin na su, ya na soma ringing ya mik'a mata wayar. "Assalamu alaikum, the great Barrister ya aka yi ne?". "Ameen wa'alaikumussalam, ba shi ba ne ni ce". Hankali ta she Alhaji Usman mai rabo ya ce, "Lafiya Ummu Julaibib?". "Da sauk'i dai kam. Yanzu haka muna asibiti Binty ta k'one". Fad'in Anna. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Ba Fu'ad wayan yanzu". Fad'in Alhaji Usman mai rabo. Mik'awa Fu'ad wayan ta yi. Karb'a ya yi ta re da d'aurawa a kunne. "Ka na ji na? Ka yi min text d'in address d'in asibitin yanzu ga ni nan zuwa". "OK dad". Fad'in Fu'ad ta re da yanke wayar in one minute ya tura maka address d'in ta re da kallon Fanan da ke ta kuka har fuskan ta ya canza kala ta re da fad'in, "Muje gida mu d'auko abunda ya kamata mu dawo". Ya na gama fad'in haka ya yi hanyar waje ta ni sa abaya ta na sharar hawaye. Bayan fitar su ne wata nurse ta zo wajan Anna ta re da shaida mata za ta iya shi ga in da Bintyn ta ke, amma kar ta yi hayaniya a kan majinyaciyar. Jiki a mace ta mik'e ta yi wajan d'akin da aka aje Bintyn. A hankali ta tura k'ofar ka na ta shiga. Binty lullub'e ta ke da blue d'in zani tun daga k'afarta har wuyar ta, kuma a ruf da ciki ta ke. K'arasa ta yi wajan hawaye na d'igowa daga idanunta ta d'aga zanin. Wani irin ja baya Anna ta yi ta re da zaro idanuwa jikinta na wani irin b'ari. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Allahumma arji'ini fi musibati, aklifni khairan minha. La'ila ha illallah muhammadar rasulillah. Mai zan ga ni haka Binty". Anna ta fad'a ta re da rushewa da kuka ta yi sauri to she bakin ta saboda kar k'arar ya fita. A karo na biyu ta k'ara zuwa ta d'aga zanin nan, tun daga k'ugunta har kafad'unta ya d'aye alamar k'una, ya yi wani iri ba kyawun gani. Hannunta da dama kuwa, gaba d'aya fatan ya sale, gyefan wuyanta ma haka. Sai bayan sandar k'afarta da ya yi wani irin bororo. Daga ita sai wani d'an gajeran wando iya cinyarta inda k'unan bai tab'a ba. Sosai Anna ke kuka ta na k'ara jin wani tururi na fitowa daga k'asan zuciyar ta re da k'ara d'aukar alwashin sai ta d'au fansa ba za ta kyale wannan ba. K'aran k'ofa ta ji ana turowa a hankali, saurin juyawa ta yi idanuwanta su ka sauka akan na Alhaji Usman mai rabo da zuwan shi kenan asibitin. Ai ta na ganin shi sai rauninta ya k'aru ba ta san ta fashe da kuka mai sauti ba. Da sauri Alhaji Usman mai rabo ya k'ariso ta re da jawo ta jikinsa ya soma lallashinta, sai da ya ga ta d'an natsu, ka na ya zaunar da ita akan kujera ta re da juyawa ya kalli inda Binty ta ke a kwance, kasancewar Anna ba ta rufe jikin Binty ba, hakan ya baiwa Alhaji Usman mai rabo ganin halin da ta ke ciki. Ba k'aramin dauriya ya yi ba wajan shanye fargabansa ba, domin ka da Anna ta k'ara shiga tashin hankali. K'arasawa ya yi ya rufe jikin ta re da kallon Anna ya ce, "Garin Yaya ta k'one haka Ummu Julaibib?". D'ago da jajayan idanuwanta ta yi ta re da fad'in, "Ni ma wallahi ban sani ba, na dawo daga wajan Rakiya sai na tambayi ta na ina don ban ji motsinta a kitchen ba, don idan na fita rige-rige su ke yi ita da Fanan wajan yi min oyoyo, sai na tambayi Fanan ta na iya sai Fanan ta ce min Mansura ce ta kirata ta na can part d'in ta tun d'azu. To bayan minti sha biyar mu na zaune da Fu'ad da shi ma bai jima da shigowar ba, sai kawai muryanta ta na ihu ta na kiran sunana ta na fad'in jikinta na k'onewa". Anna ta k'arisa maganar ta na kuka. Shuru Alhaji Usman mai rabo ya yi na y'an dak'ik'u ka na ya fiddo wayarsa daga aljihunsa ta re da dialing numbern Hajiya Mansura. "Ke Fasila kin tabbata da abunda ki ke fad'amin kuwa? Lafiya fa ta bar d'akin nan". Fad'in Hajiya Mansura. "To wallahi dai hajiya yanzu haka sun yi asibiti tun d'azu ma, ina lek'e ta window ba ki ga yadda yarinyar ta ke yi ba kamar mai tashin aljanu". Hankali Hajiya Mansura ya tashi, ba ta san lokacin da ta mik'e daga kan gadon ba ta re da nufar wardrobe d'in ta ta d'auko doguwar riga ta saka ba. Wayar ce ta soma ringing, Fasila ta d'auki wayar ta re da mik'amata. Hajiya Mansura kuwa ganin wanda ke kiranta a wayar sai da gabanta ya fad'i, amsa wayar ta yi ta re da karawa a kunnanta. Ka min ta yi sallama muryan Alhaji Usman ya daki kunnanta, "Mai ya sa mi Binty a part d'in ki? Mai ki ka mata?". "Binty kuma? Mai ya same ta Alhaji?". Hajiya Mansura ta fad'a kamar ba ta san abunda ke faruwa ba. "Ina tambayar ki, ki na tambaya ta. To ta k'one a jikinta, kuma daga part d'in ki ta fito ta na ihun jikinta na k'onewa. Ki fad'a min mai ki ka yi wa y'ar mutane?". Fad'in Alhaji Usman mai rabo rai b'ace. "Na rantse da girman ubangiji Alhaji ban mata komai ba. Wallahi ban san mai ya same ta ba. Lafiya ta bar part d'ina. Ku na wani asibiti ne?". Fad'in Hajiya Mansura. K'it ya katse wayarsa ta re da kallon Anna ya ce, "Ta yi rantsuwa da girman ubangiji ba ta san abunda ya sa mu Binty ba, kuma wai lafiya k'alau ta bar part d'inta. Shuru kawai Anna ta yi, don ita fa zuciyarta Hajiya Mansuran ta ke zargi, amma tunda ga Binty da ranta ba ta mutu ba, idan ta farka za ta fad'a masu ko ma menene ya faru da ita. Hajiya Mansura kuwa, Alhaji Usman na katse wayar ta figi hijjab d'inta ta re da fitowa daga dak'in hankali ta she. Don har ga Allah ta ji zan can k'unan da aka ce Binty ta yi har cikin zuciyar ta, don a wajanta idan wani abu ya sa mu Binty kamar ita ya sama kasancewar ta matar da ta ke so ta aura ba za ta so wani abu ya tab'a lafiyar jikinta ba. Don ba ta tunanin ko Anna ta kai ta son ta. Kicib'is su ka yi da Barrister Fu'ad da Fanan sun dawo kwasan abunda za su yi amfani da shi a asibiti. "Fu'ad ashe abunda ya faru kenan? To garin yaya ta k'one?". "Muma ba mu sa ni ba, an dai ce daga part d'in ki ta ke". Fad'in Barr Fu'ad a dak'ile don ita ce first suspect d'in shi. "Wallahi tallahi Fu'ad, Binty lafiya k'alau ta fito daga part d'ina. Ban san a ina ta k'one ba". Fanan da ba ta tsaya sauraran su ba, ciki ta shiga domin soma harhad'o duk wani abunda za su yi amfani da shi a asibitin. "Idan ta farka, ko ma wanene ya mata haka za muji". Fad'in barrister Fu'ad d'in ta re da nufar part d'in Anna. Da sauri-sauri ta biyo bayan shi ta re da fad'in, "Wani asibiti ta ke ne? Ina son zuwa yanzu". "Mu ma kaya muka zo d'auka, yanzu za mu koma asibitin". Fad'in Fu'ad. "OK to ba ri na jira ku sai mu koma ta re". Hajiya Mansura ta fad'a ta re da bin bayan Fu'ad da har ya shige d'aki. Cikin mintuna goma har Binty ta gama had'a komai. Barr Fu'ad ya taimaka mata da wasu kayan su ka fito Hajiya Mansura na biye da su a baya. A both su ka sa ka kayan, Fanan ta shiga gaba, Hajiya Mansura ta shiga bayan mota. Barrister Fu'ad tuk'i ya ke yi amma gefe guda tunani ya ke ta yadda zai yi shari'a da ko ma uban waye ya k'ona masa sanyin idaniyarsa. Wayarsa ce ta yi ringing, kallon screen d'in wayar ya yi da ke gefen sa. *Yaya Bibi* ya ga ni a jikin screen d'in. Duk da halin da ya ke ciki, sai da ya yi murmushi ta re da picking wayar ya kara a kunnansa ta re da fad'in, "Hello ya Bibi ina wuni?". Daga d'ayan b'angaran Julaibib ya ce, "Ina wuni a k'asar ku kenan, nan ko seven na safe bai yi ba". "Ohhh hakane fa, mancewa na yi ai". Fad'in Fu'ad. "Mai ya sa mu wayar Anna? Na kira ya fi sau uku a'a d'aga ba." Fad'in Julaibib cikin sanyin muryan shi. "Wallahi Anna dai na asibiti Binty ba lafiya, ga wayar yanzu muka dawo gida mu ka d'auko mata". "Wacece haka kuma?". Fad'in ya Bibi. "Kullum dai na kira sunan ta sai ka tambaya, yarinyar da Anna ke rik'e wan nan fa". Fad'in Fu'ad. "Allah ya sawwak'e". K'it ya kashe wayar. Ajiyar wayar ya yi a gyefe ta re da k'ara gudun motar. Su na isa asibitin ya yi parking ta re da fitowa. Fanan ma ta fito. Hajiya Mansura kuwa har ta yi gaba duk da ba sanin d'akin ta yi ba. "Daddy ya zo". Fad'in Fanan. "Kallon ta barrister ya yi ta re da fad'in, "Ya aka yi ki ka sani?". Barrister ya fad'a ta re da fiddo kayan da ke both. "Ga motar shi can, fad'in Fanan ita ma ta saka hannu su na fito da kayan ciki. Rufe both d'in ya yi ta re da kallon motar daddy ka na su ka nufi cikin asibitin. A tsaye su ka taras da Hajiya Mansura ta na nai man d'akin da aka aje Bintyn. "Ga d'akin can". Fad'in Fu'ad ya na nunawa Hajiya Mansura da hannu. Ta na ga ba su na bi ye da ita a baya. Ita ta tura k'ofar dai-dai lokacin da nurse ta d'aga zanin da aka lullub'e jikin Binty za ta shafa mata magani. Zaro idanuwa Hajiya Mansura ta yi, ya yin da Fanan da ke biye da ita ta yanke jiki ta suma sakamakon arba da ta yi da k'onannan jikin Binty. Barrister Fu'ad kuma saura ka d'an ya kai k'asa saboda kad'uwa. Cikin azama Daddy ya rik'o Fanan da ba ta ida kai wa k'asa ba amma ta suma. Barrister Fu'ad kuwa hawaye su ka soma saukowa cur-cur a idanunsa. Ya yin da Hajiya Mansura ta fashe da kuka ta re da k'arisawa in da Binty ta ke a kwance...... *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *43-44*🌹 *"AYYIRIRIIIIIII AHAYYEEEEE, IYEEEE NANAYEEEEEE,"* *"TO FA!! MATAR SAYYADEE, MI KE TSALLE NE HAKA YAU NA GAN KI CIKIN FARIN CIKI DA ANNASHUWA HAKA SAI GUD'A KI KE YI KAMAR ANYI BAK'UWAR AMARYA? SANNA KUMA GA Y'AN DUBU-DUBU NAN KI NA K'IRGAWA A HANNUN KI*" *KEEE TAKWARA! IDAN BA KI YI BA NI WAJE. AI NI YANZU WALLAHI SHARRR, Y'AR GABAN GOSHI NA KE WALLAHI*" *" NA GA ALAMA WALLAHI, JIYA BAN GAN KI A TSAKAR GIDA BA, SAI DOGON WUYA DA Y'AN WAK'E-WAK'E NA KE KO ZA KI JI MURYA TA KI FITO, AMMA SAI NA JI MULUNKWI*". *AI TAKWARA TUNDA MAMAN KHAIRAT TA KAWO MIN WANNAN SHU'UMIN HUMRAN NA WUCE RAINI, KE DAI ABUN BA'A MAGANA SAI KIN GWADA KAWAI*. *HABA! HABA MATAR SAYYADEE, ASHE HAKA ZAMAN TA RE YA KE, KI SA MU ABUN ARZIKI HAKA AMMA SAI KI SHA RE AMINIYAR TA KI KI YI LIKIMO A D'AKI KU NA SAN SOYAYYA DA MAI GIDA*. *"HABA TAKWARA, MAI ZAN JI NA K'ARUWA A DUNIYAR NAN DA BA ZAN FAD'A MIKI BA KE MA KI K'ARU, AI SHIYASA NA BUGA GUD'A DON KI JI KI FITO IN SHAIDA MIKI ABUN ARZIKIN*". *"INA JIN KI AMINIYAR KWARAI, ZAYYANO MIN*". *BA MA KE KAD'AI BA, SHELA ZAN YI HAR MAK'OTA SU JI DOMIN KO WACCE UWARGIDA DA AMARYA SU JI* *KU NA INAAA🗣️ KU FIRFITO MAZA KU JI ABUNDA NA KE TAFE DA SHI, SHARARRIYAR SHU'UMIN HUMRAH CE TA BAN MAMAKI MAI JAWO MIKI MIJIN DA SOYAYYAR SHI A KUSA DA KE. HUMRAH CE MAI MATUK'AR KYAU BA BU MIX, UWARGIDA KI GWADA, ZA KI BA NI LABARI, GUARANTEE NA KE BA KU DOMIN NA GWADA SHIYASA NI MA NA KE SO KU K'ARU. ZA KI GA SO, KULA DA TARAIRAYA A WAJAN MAI GIDA, RANAR DA KI KA YI AMFANI DA HUMRAN MAMAN KHAIRAT BA ZA KI K'ARA AMFANI DA WANI TURARE BA, KUMA NASAN SAI KIN GODE MIN. AKA CE SIYAN NAGARI, MAI DA KUD'I GIDA. ZA KI SAMU SHU'UMIN HUMRAH A WAJAN MAMAN KHAIRAT A KAN FARASHI MAI SAUK'I. YAR UWA BA ZA KI YI KUKAN KUD'IN KI BA. SAI AN GWADA A KAN SAN NA KWARAI. NAI MI MAMAN KHAIRAT A NUMBERN TA KAMAR HAKA👉🏻 07032294232* ..........."Dakata Hajiya kar ki matso nan wajan. Dan Allah ku fita waje ba'a son hayaniya a kusa da ita. Mutum d'aya kawai ya tsaya sauran duk ku fita please ". Fad'in nurse ta na kallan Hajiya Mansura da ta gama rud'ewa sakamakon arba da jikin Binty. Ruwan gora Fu'ad ya d'auko a kan drower ya mik'awa Alhaji Usman. Cikin sauri ya karb'i goran ta re da tsiyayar ruwan a hannunsa ya shafa mata a fuska, kasancewar Fu'ad d'in ya bud'e goran. Dogon ajiyar zuciya ta sauke ta re da bud'e idanunta ta soma kalle-kalle. Wani irin tsumamman kuka ta fashe da shi. Cikin sauri Barr Fu'ad ya kama hannun ta su ka fita daga d'akin su ka koma reception, daddy da Hajiya Mansura bi ye da su a baya. Lallashin Fanan Barrister ya dinga yi ta na kuka sosai. Daga k'arshe Alhaji Usman ya umarci Fu'ad d'in da ya mai da Fanan da Hajiya Mansura gida. Bayan ya kai su gida ya shiga bin diddigin ta inda Binty ta k'one. Gaba d'aya ma'aikatan gidan ya tattara ya na tambayan su akan su fad'a masa gaskiya ta yaya aka yi Binty ta k'one. Rantse-rantse su ka dinga masa har da kuka ta re da fad'in su ba su san yarda aka yi ta k'one ba. Kwafa ya yi ta re da sallamarsu su ka bar wajan. Bintoto mai kula da abincin kaji da ake kiwo a can bayan gida kuwa, ta ga san da Binty ta fito da gudu daga d'akin Suhail ta na soshe-soshen jiki ta na ihu, sai dai ka min ta k'arisa wajan Binty, Suhail ya fincikota ta fad'o d'akinsa kasancewar ya bi yo bayan Bintyn ne. Sai da ya wanka mata mari ka min ya mata gargad'i mai kyau akan idan har ta saki ta shaida wa wani cewar Binty daga d'akin shi ta fito to sai ya kashe ta. Kuma sosai Bintoto ta razana da maganar Suhail d'in don ta san wanene shi. Shine d'an iskan namijin da ya lalata rayuwarta wajan fara saninta a matsayin d'iya mace, kuma har gobe bai dai na lalata da ita ba. Wata rana ma a d'akin na shi ta ke kwana, ya kile ta kuma ya yi amfani da ita. Idan ma har ta sake kamin zuwan ta d'akinsa ba ta yi wanka ba, ranar sai ya mata mugun duka har da su fasa hanci kamin ya yi amfani da ita ta k'arfi tsiya, don har ta duburanta ya ke naiman ta, ya kai idan har ba amfani ya yi da ita ta duburanta ba, ba ta kwanciyar hankali, don ji ta ke kamar a na tsungumin duburan na ta. Duk wanda ya ga leb'an Suhail sai ya gudu saboda yadda ya yi wani irin bororo ta re da kumbura. Sai ya koma jawo da face marks. .............Anna dai a asibiti ta kwana, don ba ta yadda wani ya tsaya akan Binty bayan ita ba. Fanan kuwa da sassafe ita ma ta dawo asibitin, dama shi Fu'ad ba shi ya bar asibitin ba bayan ya dawo sai sha biyu da re, shi ma sai da wata nurse ta zo ta masa magana. Binty ba ta farfad'o ba sai goma na daren washa garin da aka kawo ta. Kuma ta farka ba ta jin ko wani irin ciwo a jikinta sai kan ta da ke d'an sarawa. Babu abunda ya baiwa Anna matuk'ar mamaki, sai fatan Binty da ta koma sumul kamar ba bu abunda ya tab'a tab'a jikin na ta. Su kan su nurses da doctor mamaki su ke yi matuk'a, domin ko kusa ba su bata samun sauk'i nan kusa ba. Sosai ta gyare, idan ta na hira da Fanan ma ba za ka d'auka ita ce mara lafiyar da aka kawo rai hannun Allah ba. Anna ta tambaye ta yadda aka yi ta k'one. Ganin yadda ya Fu'ad da ita kan ta Anna su ka d'au zafi ne, shiyasa ba ta fad'i abunda Fu'ad ya mata ba. Sai ce ma su ta yi ta fito daga part d'in Hajiya Mansura ne ta soma jin k'aik'aci, ta na susawa shine ya soma yi mata azaba da rad'ad'i. Anna dai ta d'aura alamar tambaya akan Hajiya Mansura, haka shi ma Fu'ad, sai dai tun da ba su da wani hujja, haka su ka bar maganar. Kwanan su biyu aka sallamo su su ka dawo gida. *_______________* .........Kwance ta ke a kan gadonsu ta na karanta wani novel da aka ba su da su ka siya jamb mai suna *INDEPENDENT* na *SARAH OLADIPO*, Fanan da ke gefen ta kuma ta na charting a wayarta. Wayar Binty ce ta soma fitar da sautin wak'ar p-square *I LOVE YOU*, jawo wayar ta yi, duk a tsammanin ta ya Fu'ad ne ko kuma k'awayanta na school, amma sai ta ga *MR RIGHT* a jikin screen d'in wayar. Wurgi ta yi da takardar hannuta ta re da fad'in, "Wayyo Allah, na shiga uku. Wallahi ya kira. Sabrin ya kira ni". Fad'in Binty ta re da toshe bakinta ta na kallon wayar har ya gama ringing ba ta d'aga ba. Tsaki Sabrin ta yi ta re da fad'in, "Wallahi Binty ki na da matsala, ya ki ka haukace a kan namiji lokaci d'aya haka? Ki fa natsu wallahi kar ya ga ne yadda ki ke son shi haka ya miki wulak'anci. Tom ni dai ba ruwana". Ka min Binty ta yi magana wayar ta sa ke k'ara, kallon Sabrin d'in ta yi ta re, "Ya sa ke kira wallahi. Yanzu d'auka zan yi?". "A'a barin shi za ki yi ya yi ta ringing. Shirme kawai. Dalla pick the call, kuma Sam kar ki nuna kin ga ne shi. Ki ja masa aji ku ma ki natsu". Fad'in Sabrin ta na hararar ta. Binty har da wani gyaran murya ka na ta d'auki wayar da ya ke gab da tsinkewa. "Who's on the line please?". Binty ta fad'a cikin lankwashashiyar muryar da ba ta ma san ta na da ita ba. "Ki na magana da Yousouf Muhammad Ahlam, wanda su ka had'u da shi a shop rite". Fad'in Yousouf cikin wani irin voice d'in shi mai sumar da y'an mata. Binty ba ta san sanda ta damk'i hannun Sabrin ba ta re da zaro idanuwa. Don jin muryan shi ta yi kamar busar sarewa. "Ki natsu kar ya raina ki fa". Sabrin ta fad'a a cikin kunnan Binty. "Gaskiya ban ga ne ka ba". Fad'in Binty har da wani d'an ya mutsa fuska kamar ya na ganin ta". Dariya ya yi mai d'an sauti wanda ya kusa tsayar da gudun numfashin Binty ka na ya ce, "Wanda mu ka bangaji juna har kayan da ke hannun ki su ka watse, na kuma ce ma sistern ki ta ba ni ke in aure ki ka ji kunya ki ka guduuuu". Sai da ya ja kalmar gudu wanda sai da ta ji shi har zuciyar ta. "OK" Shine abunda Binty ta fad'a. "Kin ga ne ni kenan?" Fad'in Yousouf. "Kamar haka". Fad'in Binty ta re da juya idanuwa kamar ya na ganin ta. "Hmm, to ya ki ke, ya kuka koma gida?". Fad'in Yousouf. "Lafiya k'alau alhamdulillah". Binty ta ba shi amsa. "Ina y'ar uwar ki? Ki ce ina gaishe ta". "Za ta ji in sha Allah". Binty ta fad'i ta na kallon Sabrin. "To ki kula da kan ki, sai na sa ke kiran ki". Fad'in Yousouf ta re da katse kiran. Tsalle ta yi akan gadon ta re da fad'in, "Wallahi ya kira ni, ya kira ni Sabrin. Na rantse miki ina matuk'ar son shi". Binty ta fad'a ta re da rungume Sabrin. "Dallah matsa can sakarya". Fad'in Sabrin ta re da ture ta a jikinta ka na ta cigaba da fad'in, "Na dai fad'a miki ka da ki saki ya ga wannan rawan kan na ki". Turo baki Binty ta yi ta re da fad'in, "To na ji big sis". ..............flowers ne a hannunshi wanda bai san adadin yawan su ba. D'aya bayan d'aya ya ke jefawa a cikin dustbin d'in gefen shi ya na fad'in, "In bayyana, a'a ba yanzun ba tukun". Idan ya jefa d'aya sai ya fad'i (In bayyana) idan ya kuma jefa d'aya sai ya ce (a'a ba yanzu ba). Haka ya dunga yi har ya rage saura kwara d'aya a hannun shi, kuma kalmar da ya rage ya fad'a shine, (A'a ba yanzu ba). Kallon shi Jabir amininshi kuma abokin aikin shi ya yi ta re da fad'in, "Fu'ad ni ko idan da za ka ji shawara ta, ka bayyana tun ka min kwad'o ya maka k'afa. Wallahi yanzu an dai na raino, sai ka ga ma raino wani ya wafce ya yi gaba da ita, amma idan ka ji shawara". "Hmm ka ke ganin haka Jabir. Yarinyar fa a gaba na ta ke. Ko fita ba sa yi ta ina za ta had'u da wani da har zai hure mata kunne. In sha Allah Binty tawa ce. Don tun ta na y'ar shekara goma na ke son abata, kuma ko Anna ba ta san da hakan ba. Kawai ka ta ya ni da addu'a kawai". "Hmm, tun da haka ka ce, zan ta ya ka. Allah ya sa rabon ka ce". Fad'in Jabir. "Ameen dai aboki na". Fad'in Fu'ad. ................. *CANADA* ................. Sosai ta ke kuwa ta re da fad'in, "Julieby, I swear to God I'm tired of him, all I want is divorce. I can't live with him ever again. I'm going back to my parents house". Fad'in matar Peter John. Ajiyar zuciya Julaibib ya sa ki mai k'arfi ka na ya kalle ta ta re da fad'in, "Where is he now?". "Club". Ta ba shi amsa ka tsaye ta na share jinin da ke gangarowa daga bakinta sakamakon make ta da Peter John ya yi kafin ya fita night Club d'in da ya saba zuwa. Don ko kwana a gidan ba ya yi. "Stay in the house, don't go anywhere. Just wait for me I'm coming back in 30minutes". Julaibib ya fad'a ta re da fita daga parlourn zuciyar sa na zafi. Don ya na d'aya daga cikin abunda ya tsana a rayuwar shi, wato dukan mace, ko wulak'antata bayan ka rabo ta daga gidan iyayanta. Kai tsaye Club d'in ya nufa, wanda a tarihin rayuwar shi bai tab'a zuwa ba sai dai ya wuce wajan da mota. Parking ya yi ta re da fitowa daga cikin motar ya na yamutsa fuska sakamakon warin giyar da ya doki hancin sa. Tsartar da miyau ya yi ta re da nufar cikin wajan Wajan na da girma sosai, gefe guda a wajan kwalaban giya ne mak'il a wajan. Ga y'an mata nan cike a wajan ba su da maraba da tsirara. Ba haske sosai a wajan kasancewar irin globe d'in nan mai launin green, blue da kuma ja. Sauti na ke tashi matan wajan na rawar rashin d'a'a a jikin mazajan wajan. Julaibib har kan shi ya fara sarawa saboda hayaniyar sautin da ke wajan da kuma shige da ficen mutane. Wata budurwa ce daga ita sai brezia da pant hannunta rik'e da kwalbar giya da cup ta nufo shi ta na karairaya. Hannu ta kai za ta shafo jikin sa ya yi saurin matsawa ta re da watsa mata wani irin kallon da ba ta san lokacin da ta juya ta bar wajan ba har ta na hard'ewa saboda tsinin takalmin da ke k'afarta. Wajan wani da ya gani a gefe ya nufa ta re da masa magana. Sama mutumin ya nu na masa. Julaibib ya bi hanyar da mutumin ya nu na masa, duk in da ya bi sai ya kauce saboda yadda mata ke kawo jikinsu. Wani wajan ya shiga wanda girman shi bai wuce wa d'akin ba, VIP ne, mata ba su fi su goma ba, sai Kazan su takwas, wak'ar Rihanna ne ke tashi wata y'ar tsamurarriyar baturiya ta na rawa a gaban Peter John ta re da shafo jikinsa ta na kuma bin wak'ar kamar haka, 🎻 *Work, work, work, work, work, work* *He said me haffi work, work, work, work, work, work* *He see me do mi dirt, dirt, dirt, dirt, dirt, dirt* *so me put in work, work, work, work, work, work* *when you ah gon' learn, learn, learn, learn, learn, learn?* *Me nuh care if him hurt, hurt, hurt, hurt, hurt*🎻 🎻 *Dry, me ah desert him* *No time ti have you lurking* *Him ah go act like he nuh like it* *You know I dealt with you the nicest* *Nuh body touch me you nuh righteous* *Nuh badda text me in crisis* *I believed all of your dreams, adoration* *You took my heart and my keys and my petience* *You took my heart on my sleeve for decoration* *You mistaken my love for you for foundation* *All that I wanted from you was to give me something that I never had* *Something that you've never seen* *Something that you've never been,mmh* *But I wake up andd act like nothing's wrong* *So me put in work, work, work, work, work, work*🎻 To she kunnansa ya yi saboda yadda wak'ar ke hargitsa masa kwakwalwa ta re da nufar wajan da Peter John ya ke ya jawo hannunsa, amma kasancewar a bige ya ke, sai kallon Julaibib d'in ya yi ta re da fad'in, "Heyyy Julieby, let go of my hand. Or do wanna join me?". Ya fad'a a bige. Mari Julaibib ya watsa masa ta re da fad'in, "Let go home now". Idanunshi har ya rine. Kwalbar giyan da ke hannun karuwarsa Julie ya fizge ta re da kai wa Julaibib du ka da shi. Cikin azama Julaibib ya rik'e kwalbar ta re da hankad'a sa ya fad'i. Saboda zuciyar da ya kawo masa wuya, idan har ya cigaba da tsaya wa a wajan to lallai za a yi b'ar na. Kawai sai ya juya ta re da barin club d'in gaba d'àya ya za motar shi sai gida. Cikin daran ya shiga net ya duba ko akwai flight d'in da zai ta shi zuwa Nigeria sai ya ga ba bu sai na Dubai, booking flight d'in da zai ta shi zuwa Dubai d'in ya yi. Ya na gamawa ya soma harhad'a kayanshi don bai fi saura mintuna arba'in ba jirgin ya ta shi. Da ma ya gama tsara komawar shi k'asar shi Nigeria ji bi, saboda wannan abun da ya faru ya b'ata masa rai shiyasa ya ke son barin k'asar. Ya na zuwa airport ana kiran passenger. Cikin tafiyar shi sauri-sauri kuma cikin natsuwa ya soma tafiya. Ko da ya shiga jirgi air phone ya saka a kunnan sa ya na saurara karatun Al'qur'ani. Su na sauka a Dubai, hotel ya nai ma ya kama, ka na ya yi wanka ta re da kwanciya kasancewar bacci ya ke ji sosai. Don gobe ne ya ke son ya sauka a k'asar Nigeria bayan shekaru masu yawa. *NIGERIA* "Anna, Ya Bibi ya min text d'azu wai gobe zai diro Nigeria, abunda ya sa ban kira shi ba, na san tun da ya min text bai son magana ne kuma ma a wajan su dare ne". Fad'in Ya Fu'ad. Wani sanyi Anna ta ji na ratsa zuciyar, don fisabillahi duka y'ay'anta ta na son su, amma Julaibib ne favourite d'in ta duk da ta na danne hakan a gaban sauran y'ay'an amma su kan su sin shan shak'uwar ta daban ce. Don takanas Anna na yankar ticket tun ya na *US* ta je wajan shi har ya koma *CANADA* ta na ziyartar shi ta yi kwana uku ta dawo. Don shi Alhaji Usman bai ci ka samun lokaci ba saboda kasuwancin sa, sun fi yin waya a kai a kai. "Kira min gaba d'aya ma'aikatan shashin nan right now". Anna ta fad'a farin ciki kwance a fuskan ta. "Aifa, su shalele za'a dawo. Har na ji tausayin su Binty, don fa Annan su za ta aje su gefe". Fad'in Fu'ad ta re da nufar maid quarters. Anna kuma wayarta ta d'auka ta kira Binty a waya ta ce su sauko k'asa ita da Fanan. Ta re su ka sauko, Binty ta kalli Fanan ta re da fad'in, "Me y'an aiki su ka yi wa Anna yau a kan ta ra su du ka a parlour?". "Ta re fa mu ka sauko, ma ji idan mu ka k'arasa". Fad'in Fanan. Ganin fuskan Anna k'umshe da farin ciki ya sa su ka ga ne ba laifi y'an aikin su ka yi ba. Nai man waje su ka yi kusa da Anna su ka zauna. Binty har da kwanciya a jikin Anna. "Hhuhmmm, yarinya na yau ne kawai, daga gobe idan ma ance ki zo kusa da Anna da k'afarki za ki gudu". Fad'in Barrister Fu'ad. "Anna kin ji shi ko, ba ni ce autares d'in ki ba. Wai haka ne abunda ya ce?". Fad'in Binty ci ke da shagwab'ar da ya k'ara mata kyau. "Rabu da shi kin ji, tsokanar ki ya ke yi. Wa ya isa ya hana ki zuwa jikin Annan ki". Gwalo Binty ta yi Wa barrister Fu'ad, shi kuma ya yi dariya ta re da kwafa. "Na ta ra ku anan ne domin in shaida muku babban d'a na ya na kan hanyar shi gobe in sha Allah, na san wasun Ku a nan sun san shi, wasun kuma ba su tab'a ganin sa ba. To magana ta gaskiya ya na da wani murd'ad'd'an hali. Sam ba ya san hayaniya da yawan magana a kan shi. Ga wanda bai san shi ba, zai d'auka kyamar mutane ya ke yi ko kuma shi d'in mugune saboda ya na sama da ku, amma ga wanda su ka san shi kuma su ka iya zama da shi, za su ga ne kyawawan halayen shi na wai dan ya na d'ana ba. Sannan ya na da matuk'ar zuciya sosai wanda a wasu lokutan ni kai na da na ke mahaifiyar sa, ba na iya shawo kah cikin sauk'i. So dan Allah ko wacce ta kiyaye ta tsira da aikinta". Fad'in Anna ta na kallon y'an aikin na ta. Cike da girmamawa su ka ce, "In sha Allah za mu kiyaye Hajiya". "Za Ku iya tafiya". Fad'in Anna. Ga ba d'aya su ka mik'e su ka fice. "Annah, ya Bibi ne zai dawo? Wayyo Allah dad'i kuma haushi". Fad'in Fanan. "Mi ye dad'in, kuma mi ye haushin?". Anna ta tambaye ta. "Anna dad'in na yi shekaru ban ga ya Bibi ba. Haushin kuma zai hana mu sak'at a ciki n gidan nan. "Ai abun ba wuya, sai Ku kiyaye shi". Fad'in Anna. Ita kuwa Binty hankalinta ma ya bar wajansu ya koma kan screen d'in wayarta ta na karanta daddad'an text d'in da Yousouf ya turo mata. Don kafin ya kira ta ya na jimawa, sai dai fa kullum sai ya mata dad'ad'an texts, na safe da ban, na rana da ban na dare da ban. Ku ma ba ta tab'a yin k'urin yi masa replay ba sai yau kawai ta ji ta na son ta yi masa. Sau uku ta na rubutawa ta goge, a na hud'un ne kuma ta daure ta tura. Yaya Fu'ad da ke kallon ta ba ta re da sanin abunda ta ke yi a cikin wayar ba, ya na jin son ta na k'ara huda ko wani sashe na jikinsa. "Fanan ki d'auko key d'in part d'in ya Bibi Ku je ke da Binty ku gyara masa tsaf, kin san bai san y'an aiki na shigar masa d'aki. Maza ku ta shi yanzu". Fad'in Anna. Ta shi Fanan ta yi ta re da kallon Binty da ke kallon sak'on da Yousouf ya sake turo mata yanzu sakamakon replay d'in da ta masa. Fizge wayar Fanan ta yi ta re da yin sama da gudu, sai a lokacin Binty ta dawo cikin natsuwarta ta re da bin bayan Fanan d'in da gudu ita ma. Har kan gado Binty ta ni ta ta re da fizge wayar ta maka mata harara, ka na ta cigaba da karantawa message d'in Yousouf d'in ta re da kwanciya a kan gado har da wani lumshe idanu. "Idan za ki ta shi ma gwara ki ta shi muje mu gyara d'akin ya Bibi". Fad'in Fanan. "Ki je ki yi ke d'aya, ni love na ke yi. Aikin ne ba za ki iya yi ke d'aya sai na ta ya ki?". Fad'in Binty. "To ba ri na je na fad'a wacce ta ce mu yi ni da ke, idan ya so sai ki ke da kan ki ki fad'a mata ke ba za ki yi ba". Fad'in Fanan ta re da sauka daga kan gadon. Rik'o hannunta Binty ta yi ta re da fad'in, "Ke fa muguwa ce, to na aje wayar muje. Kill joy kawai saboda ta ga ba ta da mai tura mata hot messages". Fad'in Binty. Tab'e baki Fanan ta yi ta re da fad'in, "Ni ma nawa Prince d'in ya na kan hanya". Fitowa su ka yi su ka nufi side d'in ya Bibi da ya kusan sumar da Binty saboda tsaruwarsa, da ta d'auka ba za'a samu d'akin da ya fi na Daddy kyau ba, sai ga na Julaibib ya ninninka na daddyn. Mai makon su tsaya su gyara d'akin da kyau, sai su ka b'ige da masa bincike a d'akin su na kallon old picture d'in sa. Hoton sa Binty ta ga ni lokacin da ya kammala degree d'in sa na farko hannunsa rik'e da award. "Kaiii ku kyawawa ne Fanan, yayan ki kyakkyawa ne sosai". "Ya su ke da Yousouf d'in ki?". Fad'in Fanan. Saurin ajiye hoton Binty ta yi, ka na ta kalli Fanan d'in ta re da fad'in, "Ko kusa ba bu had'i, wallahi Yousouf d'i na ya fi shi kyau". "Beauty is in the eyes of the beholder". Fad'in Fanan ta re da soma kakkab'e gadon. Haka su ka yi aikin ba cikin natsuwa ba, don su na yi sai su aje su ko ma kallon wani abun. Daga k'arshe ma haka su ka gama su ka manta ba su wanke bayi ba. Yaya Fu'ad da ke kallon ta ba ta re da sanin abunda ta ke yi a cikin wayar ba, ya na jin son ta na k'ara huda ko wani sashe na jikinsa. "Fanan ki d'auko key d'in part d'in ya Bibi Ku je ke da Binty ku gyara masa tsaf, kin san bai san y'an aiki na shigar masa d'aki. Maza ku ta shi yanzu". Fad'in Anna. Ta shi Fanan ta yi ta re da kallon Binty da ke kallon sak'on da Yousouf ya sake turo mata yanzu sakamakon replay d'in da ta masa. Fizge wayar Fanan ta yi ta re da yin sama da gudu, sai a lokacin Binty ta dawo cikin natsuwarta ta re da bin bayan Fanan d'in da gudu ita ma. Har kan gado Binty ta ni ta ta re da fizge wayar ta maka mata harara, ka na ta cigaba da karantawa message d'in Yousouf d'in ta re da kwanciya a kan gado har da wani lumshe idanu. "Idan za ki ta shi ma gwara ki ta shi muje mu gyara d'akin ya Bibi". Fad'in Fanan. "Ki je ki yi ke d'aya, ni love na ke yi. Aikin ne ba za ki iya yi ke d'aya sai na ta ya ki?". Fad'in Binty. "To ba ri na je na fad'a wacce ta ce mu yi ni da ke, idan ya so sai ki ke da kan ki ki fad'a mata ke ba za ki yi ba". Fad'in Fanan ta re da sauka daga kan gadon. Rik'o hannunta Binty ta yi ta re da fad'in, "Ke fa muguwa ce, to na aje wayar muje. Kill joy kawai saboda ta ga ba ta da mai tura mata hot messages". Fad'in Binty. Tab'e baki Fanan ta yi ta re da fad'in, "Ni ma nawa Prince d'in ya na kan hanya". Fitowa su ka yi su ka nufi side d'in ya Bibi da ya kusan sumar da Binty saboda tsaruwarsa, da ta d'auka ba za'a samu d'akin da ya fi na Daddy kyau ba, sai ga na Julaibib ya ninninka na daddyn. Mai makon su tsaya su gyara d'akin da kyau, sai su ka b'ige da masa bincike a d'akin su na kallon old picture d'in sa. Hoton sa Binty ta ga ni lokacin da ya kammala degree d'in sa na farko hannunsa rik'e da award. "Kaiii ku kyawawa ne Fanan, yayan ki kyakkyawa ne sosai". "Ya su ke da Yousouf d'in ki?". Fad'in Fanan. Saurin ajiye hoton Binty ta yi, ka na ta kalli Fanan d'in ta re da fad'in, "Ko kusa ba bu had'i, wallahi Yousouf d'i na ya fi shi kyau". "Beauty is in the eyes of the beholder". Fad'in Fanan ta re da soma kakkab'e gadon. Haka su ka yi aikin ba cikin natsuwa ba, don su na yi sai su aje su ko ma kallon wani abun. Daga k'arshe ma haka su ka gama su ka manta ba su wanke bayi ba...... ..............."Haba besty na, idan ki ka guje ni ina za ni. Dan Allah ki yi hak'uri mu shirya beauty". Fad'in Hamdan tsugunne a gaban Sabrin da ta had'a k'afa d'aya a kan d'aya ta na shan ice-cream ko kallon shi ba ta yi ba. "Dan Allah ki min magana Love, idan ki ka yi fushi da ni zan fad'a wancan sweeming pool d'in can in mutu". Fad'in Hamdan.. "Really? Mu je wajan to mu ga ni". Fad'in Sabrin ta re da hararar sa ta re da mik'ewa ta yi wajan pool d'in. Bin ta ya yi a baya ta re da cigaba da magiya. Sai da ta tabbar ya zo kusa da pool d'in ka na ta daddage ta tura shi ciki ta na masa dariya da gwalo ka na ta ce, "Beautyn ta ka ta zo ta cece ka. Ta yi tsuntsuwa daga kan bola ta zo ta ciro ka". "Haba ai Ke ce beauty na. A kwai wacce ta kai best friend d'ina kyau kuwa, ina tunanin fa ko Beauty a wajan ki aka sammata". "Hmm, sweet mouth. I hate you". Fad'in Sabrin da k'arfi. "And I love you besty". Fad'in Hamdan da k'arfi. Ko juyawa ba ta yi na ta so ma tafiya. Da sauri-sauri ya fito ruwa na d'iga a jikins ya nufi wajanta da har ta bud'e mota. Shi ma bud'e gaba ya yi ta re da shiga. Kallon shi ta yi ta re da yamutsa fuska ta ce, "Disgusting, please out". Ruwan goran da ke gyefan shi ya bud'e ya watsa mata a jiki ya na dariya. Ihu ta yi ta re da soma kukan shagwab'a ta na fad'in, "I hate you, I hate you, I hate youuuuuuuuuu". Fitowa ya yi daga motar ya jawo ta daga driver seat ya mai da ita in da ya tashi ta re da rufe mata k'ofa ka na ya ko ma driver seat d'in ya ja motar su ka bar park d'in. *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *45-46*🌹 *Bonus*✋🏻😂 ( *BARKA DA SABUWAR SHEK'ARA. YA UBANGIJI HALITTA, SA DA MU DA ALKHAIRI WANNAN SABUWAR SHEKARA DA MUKA SHIGA, SA'ANNAN KA KORE MANA FITINTINU DA BALA'IN DA KE CIKIN TA ALFARMAR FIYAYYAN HALITTA (AMEEN)*) ............."Besty dan Allah ki dai na saurin fushi haka, ki ga ne ke d'in ta daban ce. Amma fa ita ma Binty..." "Enough! Za ka saka in bud'e motar nan in fita idan har ka cigaba da kururta y'ar bolan ka a gaba na. Ka ba ri idan za ka fad'i kyawunta sai ba na wajan dan zan shak'e ka ka mutu in kuma canza besty". Fad'in Sabrin. "Da kad'an Binty na ta fiki kyau". Fad'in Hamdan ta re da yi mata gwalo. Shak'e shi ta yi ta ta re da fad'in, "Sai na kashe ka, sai na kashe ka, mai kan goruba kawai". Dariya ya shiga yi ta re da k'ok'arin kwace wuyar rigarsa da ta rik'e. Saura kad'an su yi karo da wata mota ya yi saurin juya steary ta re da ta ka burki. "Kin ga abunda ki ke so jawo mana ko?". Fad'in Hamdan ta re da dungure mata kai. "Drive jo! Sanyi na ke ji in yi ina son canza kaya". Fad'in Binty ta re da ja masa hancinsa. "Sannu ni kuma in ce me da kika tura ni cikin pool. Du be ni gaba d'aya na a jike na ke har d'iga na ke yi". Hamdan ya fad'a ta re da kunna motar ya soma tafiya a hankali. "Ai kai ka ja, idan za ka rik'a maganar beauty a gaba na zan to she ka yasin-yasin yaro". Fad'in Sabrin. "Ke wanene yaron? Na fasa miki baki". Turo bakin ta yi ta re da fad'in, "In ka fasa". Figar motar ya yi da guda sannan ya soma jan giyar ta na gama ta na bayan kamar ta na jacking. Hannun shi ta kai wa cizo shikuma ya saki k'ara ta re da fad'in, "Auuch! Wallahi sai dai ke ki yi driving, idan ba haka ba kuma mu kwana a nan". Hamdan ya fad'a ta re da folding hannunsa ya na kallonta. "Driving ko? Zan ko yi". Fad'in Sabrin ta re da fitowa daga cikin motar ta zagaya, shikuma ba ta re da ya fito ba ya koma inda ta tashi. "Ka tabbatar ka saka belt". Fad'in Sabrin ta re da saka belt a jikinta, shi ma Hamdan ya saka. Key ta yi wa motar ta re da figar motar da uban gudu. Da ba din Hamdan ya saka belt ba, sai ya yi tsalle ka na zai dawo wajan zaman sa. "Ki yi wa girman uban giji ki yi parking zan koma gida a k'afa". Fad'in Hamdan saboda irin uban gudun da Sabrin d'in ta ke yi, don motarsu har karkacewa ta ke yi kamar b'arayi y'an sanda sun biyo su. *________________* ............Gaba d'aya y'an aiki sai kai wa da komowa ake yi sakamakon babban d'an mai gidan da zai dawo yau daga k'asar *CANADA*. Anna da kanta yau ta shiga kitchen ta na had'awa shalelen na ta abuncin da ya fiso, gefe kuma Fanan da Binty na ta ya ta da wasu abubuwan. Wayar Bintyn ce ya yi k'ara, fiddo da wayar ta yi daga cikin aljihun apron d'in da ke jikinta. Text message Yousouf ya turo mata, murmushi ta saki ta re satar kallon Anna ta ga Sam hankalinta bai kan ta. Sak'on ta shiga karantawa ta na sakin murmushi har hak'oranta sai da su ka bayyana. Sai da ta gama karantawa tsaf, ka na ta shiga yi masa replay da dad'ad'an kalamai kamar yadda su ka saba. "Amma ban yi maku warning akan shigo da waya kitchen ba? Na fad'a maku ba'a zuwa da waya a in da akwai gas amma Sam ba kwa jin magana". Fad'in Anna ta na kallon Binty da ta yi saurin mayar da wayar cikin aljihun apron d'in gabanta na fad'uwa kuma ta na addu'ar Allah ya sa ka da Anna ta ce ta ba ta wayar ka da ta ga abunda ta ke yi. "Anna ita dai, don ni kam ban shigo da waya kitchen". Fad'in Fanan ta na yi wa Binty gwalo. "Keep quite, ai halin ku d'aya. Thank God Yayan ku na hanya, duk zai gyara maku zama ai". Fad'in Anna ta na hararar su duka. Dariya Binty ta yi ta re da yi wa Fanan gwalo kamar yadda ita ma ta yi mata. "Anna ki na ganin ta ta na min gwalo ko. Ki fad'a mata ni yayarta ce fa. Zan zane ta". Fad'in Fanan. Kallon Binty Anna ta yi ta re da fad'in, "Maza ki je ki aje wayar nan ki dawo. Ban son in k'ara ganin Ku da waya a hannun Ku in dai za Ku shigo kitchen. Idan kuma ba za Ku kiyaye ba, to zan kwace wayar". "Anna ki yi hak'uri za mu kiyaye". Gaba d'aya su ka fad'a saboda kwace waya da su ka ji Anna ta ce, don sun san hakan ba k'aramin aikin ta ba ne. Fitowa daga kitchen d'in Binty ta yi ta re da saurawa sama da sauri. Ta na shiga d'akin su ta k'arisa typing message d'in ta re da tura masa. Cikin second minti d'aya ya sake turo mata da wani message d'in. Ita ma ta sake masa replay. Kamar wasa su ka yi ta wa junan su musayan kalamai, su Binty har da kwanciya a kan gado, shaf ta ma manta da batun girki da su ke yi. " *_Mai yasa ka fiye son aiko min da sak'o fiye da ka k'ira ni a waya? Kwata-kwata sau biyu kawai mu ka tab'a yin magana ta waya_*". Ta na gama typing ta tura masa. Karan message ne ya shigo wayar ta. Bud'e message d'in ta yi. " *_I preferred message than talk, that the reason_*". Murmushi ta yi ta re da typing message. " *_Muryata ba dad'i ko? Na san haka ne ai_*". Wayar ta ce ta so ma k'ara. Sai da gabanta ya fad'i da ta ga shi ne ke kiran ta a waya. Kasa picking ta yi har wayar ta gama k'ara. Wayar na yankewa, ya tura mata message. " *_Ban tab'a jin murya mai dad'i kamar ta ki ba. Golden voice gare ki. Mai ya sa ki ka k'i picking call d'in? Are you angry?_*". Dad'i ne ya mamiye zuciyarta, message ta shiga yi masa typing. " *_Haka nan na ji na kasa d'aukar wayar. I'm not angry with you_*". Message d'in da ya sa ke turo mata ne ya sa k'irjinta bugawa. Kallon message d'in ta yi ta re da k'ara karantawa. " *_Idan ba matsala, mu had'u a wonderland by 4:00pm_*".. Ta karanta message d'in ya kusa sau goma. Wani message d'in ne ya sa ke shigowa. " *_Still waiting for your replay_*". Ta na gama karantawa ta kashe wayar gaba d'aya ta re da sauka daga kan gadon. Apron d'in da ta ga ni a jikinta, shi ya tuna mata abunci su ke yi a kitchen. "Wayyo Allah na". Shine abunda ta fad'a ta re da fita da gudu. Da gudu-gudu ta ke saukowa daga steps d'in, aikuwa tsautsayi ya sa ta yi missing step ta dunga gungurowa har ta fad'o can k'asa. K'aran ihunta ne ya fito da Anna da Fanan da ke kitchen da gudu. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!". Anna da Sabrin su ka fad'i ta re da nufar in da ta ke. A dai-dai lokacin ne kuma, motar Barrister Fu'ad ta dannawa Oga Solomon horn, dawowar shi kenan daga airport ya je ya d'auko ya Bibi. Kasancewar bai son magana da hayaniya, shiyasa jama'a da dama su ke zaton shi d'in mai girman kai ne. Wannan k'aron ba sai da ya yi wa Fu'ad warning akan ya tabbatar motar da zai zo d'aukar shi ta na da tinted. Hakan ne ya sa jama'ar gidan ba su san da shigowar sa ba. Ya Fu'ad na parking ya yi saurin fitowa, cikin tafiyar shi na ingarman namiji ya nufi side d'in Anna saboda bai k'aunar gaishe-gaishen nan sa y'an aiki su ke yi. Sallamar ya yi cikin siririyar muryansa ta re da kutsa kai cikin parlour ya na sakin ajiyar zuciya. Ita kuwa Anna ko sallamar shi ba ta ji ba, ta na duk'e a in da Binty ta ke kwance ta na fad'in, "Inna lillahi, wayyo Anna ta". Da ma ga ta da shegen raki. Anna kuwa cike da tausayawa har ta fara hawaye. Idanuwan Julaibib ne ya sauka akan Anna da ke sharan hawaye. Gaban shi ne ya ba da sautin dam, domin adunya ba ya k'aunar kukan mace, musamman ma a ce abun k'aunar na da duk duniya babu kamar ta ce ke yi. "Subhanallah!". Julaibib ya fad'a a hankali ta re da nufar wajan da su ke. Duk'awa ya yi ta re da ka mo hannun Anna ya ce, "Anna what's the problem? I'm here". Julaibib ga fad'a in a very cool voice da ke bayya tashin hankalin shi. Saurin kallon fuskan shi Anna ta yi ta re da fad'in, "Thanks God! Julaibin du ba min marainiyar Allah don Allah. Fad'owa ta yi daga sama". Fad'in Anna. Kallon gefen da ta ke ya yi sau d'aya ta re da saurin kau da kansa ya mai da kan Anna ta re da narke fuska kamar wani k'aramin yaro ya ce, "Anna zuwa na fa kenan, ko ruwa ban sha ba sai in fara aiki". "Do as I said now". Anna ta ba shi umarni cike da tsare gida don sarai ta san halin d'an nata abu mai sauk'i ne a wajan shi ya ce ba zai yi duba ta ba. "Wash, wash, wash! Wayyoooooh Allah na, Anna hannu na". Fad'in Binty da idamunta ke a kulle sai faman raki da kiran sunan Anna ta ke. Ya Fu'ad da shigowar sa ke nan ya yi saurin k'arasowa wajan ta re da fad'in, "Anna mai........". Bai k'arasa maganar ba idauwansa su ka sauka akan Binty da ke ya she a k'asa sai fad'in wayyo hannunta ta ke yi. Fu'ad bai san sanda ya d'auke ta cak ya aje ta akan three sitter ba ya shiga fad'in, "Beauty Anna lafiya? Mai ya same ki?". A rud'e ya fad'i haka ta re da kallon Anna ya sa ke fad'in, "Anna mai ya sa me Binty?". "Ta yi missing step ne". Anna ta fad'a ta re da kallon Julaibib ta antaya masa harara. Hannu Julaibib ya sa ka ga dafe kan shi, don ihun ''wayyo hannu na'' da Bintyn ta ke yi har ya soma damun shi. Ya Fu'ad kuwa kallo Binty ya yi ta re da fad'in, "Sannu kin ji Binty, ga ya Bibi nan zai du ba ki". Harara Julaibib ya makawa Fu'ad da bai ma san ya na yi ba. Yamutsa fuska ya yi ta re da nufar wajan da Bintyn ta ke a kwance ya d'an rankwafa ta re da rik'o hannun da ya ke mata ciwon. Wani k'ara ta kwalla ta re da rik'e hannun Julaibib d'in da d'ayan hannunta. Don lokaci d'aya ta ji wani azaba biyu ya ziyarci hannun. Na farko zafin da hannun ya ke mata, ba biyu kuma wani irin k'aik'aci mai kama da k'unan wuta da ta ji yayin da ya rik'e hannun na ta. D'an tsaki ya yi ta re da d'aure fuska ya ce, "Sake min hannu ko in mazge ki anan wajan. Sai shegen raki da shagwab'ar tsiya. 'Anya wayyoo hayyunaa'. Dallah matsa can". Julaibib ya maimaita abunda ta ke fad'i kamar yaro na magana. Duk irin tausayin da Fanan ke mata sai da ta dara saboda yadda Ya Bibi ya yi maganar. "Ka rai na ni ko Julaibib?". Fad'in Anna ta na kallon shi. "Anna ba laifi na ba ne. Y'ar ki za ki yi wa magana ta natsu in duba mata hannun. Kuma ma fa buguwa ce kawai ta yi tsabar raki ne kamar ta karye ko ta samu gocewar k'ashi". Julaibib ya k'arisa maganar ya na maka mata harara. Zama a gefen in da ta ke Anna ta yi ta re da shafa kan ta ka na ta ce, "Auta na ji tsaya yayanku ya duba miki hannunki kin ji ko, in sha Allah zai warke ya dai na miki zafi". Fad'in Anna a tausashe. "Annan mu dan Allah ace masa ya min a hankali. Zafi na ke ji". Fad'in Binty cikin shasshek'ar kuka. "To zan fad'a mishi, amma kar ki gardama kin ji Binty na". Fad'in Anna. Gyad'a mata kai Binty ta yi ta ra da kallon Julaibib ta wani narke fuska. Harara ya watsa mata ta re da kamo hannu. Wannan karan ba ta ji turirin azaba kamar ta k'one ba, sai azabar yadda yake murd'a hannun. Wani irin ihu ta saki da k'arfi har ba ta san san da ta afka jikinsa ba ta re da ruk'unk'ume shi ta na fad'in, "Wayyiooo Annah zai kashe mi ki ni. Dan Allah ki taimake ni". Shi kuwa Julaibib, ihunta har cikin kwanyar shi ya ji shi, ji ya yi kunnan shi ya yi masa wani duummmm. A hankali ya b'amb'are ta daga jikinsa ya bar ta nan kwance k'asa ta re mik'ewa tsam ya saka hannun shi biyu a kan kunnansa ka na ya juya ya soma tafiya. Da sauri ya Fu'ad ya bi bayansa Anna ta yi saurin dakatar da shi ta re da girgiza masa kai. Dawowa ya yi inda Binty ta ke ta re da sungumar ya mai da ta kan kujera. Julaibib be ya juyo ta re da watsa masa harara kamar zai yi magana, sai kuma ya fasa ya fice daga d'akin. "Fu'ad ina ganin gasa hannun za'a yi". Fad'in Anna. "Gasawa kuma Anna?". Fu'ad ya fad'a a marairaice ya na kallon idanunta. "Eh. Ba ka ji abunda ya ce ba. Ba karaya ba ce kuma ba tsagewar k'ashi ba ne. Buguwa ce. Saboda haka gasawa za'a yi sai a shafa mata maganin zafi". "To Anna ina da maganin zafi a d'aki na, ba ri na d'auko". Ya fad'i hakane ta re da mik'ewa ya fice daga d'akin. "Sister sannu kin ji". Fad'in Fanan kamar za ta yi kuka ta na kallon Binty da ke gunjin kuku. "Ba ri ba d'ai bo ruwan zafi a kitchen, ki zauna da ita". Fad'in Anna ta re da nufar kitchen. Fu'ad kuwa d'akin Julaibib ya so zuwa, nocking ya yi, sai da Julaibib d'in ya ba shi izinin shiga ka na ya shiga. Zaune ya sa me shi a bakin gado ya rik'e kan shi da hannu bibbiyu daga shi sai dogon wandon jikinsa da kuma singlet. D'ago jajayan idanuwan shi ya yi ta re da watsawa Fu'ad wani kallo sai da hantar cikinsa ya motsa. Mai da idanuwan shi ya yi ta re da lumshe su ka na ya mai da ya rufe. "Kar tsautsayi ya sa ka k'ara d'aukar yarinyar nan, ka san dai ba muharramar ka ba ce. Ka ba ri Anna da Fanan su taimaka mata. Ka ji abunda na ce?". Sai da Fu'ad ya had'iye wani bushasshen miyau har sai da Adams apple d'in shi ya motsa ka na ya ce, "In sha Allah haka ba zai sa ke faruwa ba Ya Bibi". Gyad'a kai kawai Julaibib ya yi ta re da mik'ewa ya nu fi toilet. Fu'ad na ganin haka, shi ma ya mik'e ya fice daga d'akin domin d'auko maganin zafi. Ko da Ya Fu'ad ya dawo, tu ni har Anna ta kawo ruwan zafi da tsumma shi kawai ta ke jira. Tsummar ta sa ka a ruwan ka na ta matse ta shiga dannawa a hannun na ta a hankali. "Wayyiiiiooo Annah zan yi fitsari wallahi. Dan Allah akwai zafi. Zafi, zafi zafi zafi zafiiiiiiiiii". Fanan ba ta san sanda ta b'arke da dariya ba saboda "Anna zan yi fitsarin" da Binty ta ce. "Bar nan ko in watsa miki ruwan zafin nan a wuya da sai kin yi fitsari ka min ita ta yi". Fad'in Ya Fu'ad ya na gintse dariyar shi bai so ya yi. Wani dariyar Fanan ta Ku ma bushewa da shi ka na ta ce, "Wallahi ya barrister kai ma ka d'ana. Ba ri Binty ta warke, kai da ita be ba ruwa na". "Assalamu alaikum". Muryan Kandala ta katsewa ya Fu'ad maganar da zai yi. Gaba d'aya su ka amsa mata sallamar har Anna da ta juya ta na kallon ta. "Ah! Kandala ke ce? K'araso ciki mana". Fad'in Anna murmushi d'auke a fuskan ta. K'arasowa Kandala ta yi, ta yi dumurmur da ita har wani haske ta yi. Kayan jikinta kawai idan mutum ya kalla zai san ta mugun samun sauyi a rayuwarta. Tsayunta biyu sanye da zinari da guda d'aya kawai kud'insa zai kai dubu d'ari shidda. "Maza kawo mata ruwa da abincin". Fad'in Anna ta na kallon Fanan. "Ina wuni?". Fu'ad ya fad'a ta re da mik'ewa ya nufi hanyar waje, don shi har ga Allah bai san mai ya sa ba, bai k'aunar matan sam. Ta na amsa mashi gaisuwar ma ko sauraranta bai yi ba. "Ina wuni Hajiya? Mun same ku lafiya?". Fad'in Kandala cike da fara'a a fuska. "To Alhamdulillah, sai dai d'iyar ta ki ce ta yi missing step ta gunguro daga sama hannunta ya bugu". Fad'in Anna ta na kallon Binty da ke ta raki a hankali. "Subhanallah! Allah ya kiyaye gaba. Sannu kin ji Binty". Sai a lokacin Binty ta d'ago ta kalle ta ta re da fad'in, "Ina wuni Baaba, kin zo lafiya?". "Lafiya k'alau Binty, ya k'arfin jiki". Fad'in Kandala cike da tausayawar bariki. "Da sauk'i". Binty ta fad'a a gajarce ta re da kallon gefe. Fanan ta aje mata faranti a gabanta. Sakwara ce miyan egusi da yaji stockfish da bushasshan kifi irin mai tsokar nan. Sai ruwan gora ta re juice d'in carrot. Favorite d'in Julaibib ke nan. Shiyasa Anna ta shiga kitchen da kan ta ta had'a masa. Babu kunya Kandala ta baje ta kwashi abinci babu algus. Wayar Anna ta ta yi k'ara. Ta na zubawa ta ga sunan Julaibibin ta na ke kira. Murmushi ta yi ta re da d'aga wayar. "Anna ba'a gyara min d'aki ba, toilet d'in ba bu tsafta ba zan iya amfani da shi ba". Fad'in Julaibib. "OK ban minti biyar". Fad'in Anna ta re da yanke wayar. Kallon Fanan da ke danna wayarta ta yi ta re da fad'in, "Da ma da na tura ku Ku gyarawa yayanku d'akin ba Ku gyara ba ko?". Fad'in Anna ta re da tsare Fanan da idanu. Zaro idanuwa Fanan ta yi ta re da, "Fad'in Allah Anna mun gyara". "To k'arya ya ke yi kenan? Ya ce ba Ku wanke masa toilet ba". Zaro ido Fanan ta sake yi ta re da kallon Binty da ke kwance. Ita kuwa Binty ta yi saurin mai da idanuwanta ta rufe don ka da Anna ma ta yi mata magana. "Maza yanzu ki je ki wanke masa, ke ya ke jira zai shiga ba yi". Fad'in Anna. Yarfe hannu Fanan ta so ma yai ta re da fad'in, "Anna na shiga uku, Annah dan Allah ba ni ba ki sa wata. Zai kashe ni". "Ai na fi son ya lallasa ki, tun da dai ban isa in saka Ku aiki ku yi ba. Haka zan maku aure Ku je ku na yi". Fad'in Anna. "Anna wayyo, Anna wayyo Allah". "Wallahi idan ba ki wuce ba na tashi za ki ji jiki". Fad'in Anna. Fanan har da guntun hawayanta ka na ta fita ta na addu'a a cikin zuciyarta. Knocking ta soma yi ka na ta shiga, su na had'a idanu da Julaibib ta tafi da gudu ta rungume shi ta re da fad'in, "Oyoyo Yaya Bibi na, welcome home my sweet bro. Na fa fi son ka a kan ya Fu'ad". Fad'in Fanan. "Wuce ki je ki wanke min bayi". Ya fad'a a murtuke. Cikin sauri ta yi wajan bayin ta re. Ba bu ma wani datti. Sosai ta natsu ta wanke shi tass, ka na ta fito ta re da fad'in, "Na gama Yaya". Ta fad'in hakane ta na jiran hukuncin ta na rashin wanke bayin da ba ta yi ba. Tasowa ya yi ta re da rab'e ta ya wuce bayin. Nannauyan ajiyar zuciya ta sa ki ta re da ficewa daga bayin. "Ina jin ki Kandala". Fad'in Anna. "Eh to, Hajiya dama dai Binty ce na ke so a ba ni ita za mu je Saminaka ta je ganin gida, kin san tun da ta zo nan ba ta sake lek'awa ba. To kin san mutane. Shine ake mini tunanin ko sai da ita na yi. Shine na ke so muje ta yi ko da sati ne sai mu dawo". "Dan Allah ki yafe min Kandala. Duk laifi na ne da ko sau d'aya ban tab'a wannan tunanin ba. Amma in sha Allah za ki tafi da Binty ta je ta ga gida ita ma. Ni ma kai na zan so bin Ku, sai dai hakan ba zai samu ba saboda wani d'an uzuri nawa, amma in sha Allah idan kun dawo ba za ta rufe wata biyu ba zan saka driver ya d'auke mu ni da ita da Fanan sai muje muga k'auyan na Ku. Amma yaushe tafiyar? Zan so ya kai jibi saboda in sa mu in mata tsaraba". Anna ta fad'a. "Ayya ai babu komai Hajiya, ki dai na rok'on gafarata. Binty d'iyarki ce ai". Kandala ta fad'a ta re da share zufar da ta tsiyayo mata a goshin ta. "Nagode Kandala. Jibi ki zo ki d'auke ta sai Ku tafi". Fad'in Anna ta na kallon fuskan Binty da ta yi kicin-kicin. 🌹 *47-48*🌹 ............."To Hajiya nagode Allah ya k'ara girma. Ni zan koma ka da dare ya min". Fad'in Kandala ta re da satar kallon Binty da ko in da ta ke bata k'ara kallo ba tun da ta gaishe ta. "D'an jira ni ina zuwa". Fad'in Anna kuma dai-dai lokacin Fanan ta shigo d'akin ta re da zama kusa da Binty a inda Anna ta tashi. Ita kuwa Binty zuciyar ta ne ya rabu gida biyu. Na farko ta na son sanin menene manufar Kandala a kan ta, na biyu kuma ta yadda za ta samu damar fita ta je wonderland park su had'u da Yousouf. "Ke tunanin me kike yi ki ka yi shuru haka?". Fad'in Fanan ta re da girgiza Binty. "Tunanin ta ke za ta yi tafiya har na tsawon sati guda ta barki. Kewarki ta soma yi". Kandala ta yi saurin baiwa Fanan amsa. Tuni har Fanan ta rud'e ta re da kallon Binty ta ce, "Sister ina za ki tafi ko bar ni? Dan Allah kar ki je ko ina". Fad'in Fanan har kwalla ya ciko mata a idanunta. "Hak'uri za ki yi Fanan. Ita ma za ta je ta ga y'an uwanta ne. Ai ba jima za ta yi ba". Fad'in Anna da saukowarta kenan hannunta rik'e da wata babbar leda. "Anna wallahi gidan ba zai min dad'i ba idan har ba bu Binty. Dan Allah ta fasa zuwa". Fanan ta fad'a hawaye na gangarowa daga idanunta. "Gidan ku Fanan. Allah ki ka min shirme zan had'a ki da yayan ku ya ci min k'aniyar ki. So gwara ma ki natsu. Na ce miki ba dad'ewa za ta yi ba. Sati za ta yi". Fad'in Anna wacce ita kanta bata k'aunar Binty ta yi nesa da ita kawai dauriya ta ke yi saboda tabbas ya kamata Binty ta ga y'an uwanta. Ta shi Fanan ta yi da gudu Fanan yi hanyar sama har saura kad'an ta fad'i sai da Binty ta saki wani dogon ajiyar zuciya na jin dad'in Fanan d'in ba ta kai k'asa ba. "Allah sarki, sun shak'u matuk'a ne". Fad'in Kandala wacce ta ke ta addu'ar Allah ya sa Anna ka da ta ce Fanan d'in ta bi su. Don idan ta ce haka, za ta b'ata mata shirin da ta yi. "Ga wannan Kandala, kya rabawa y'an uwa da abokan arziki. Wannan kuma ki yi kud'in mota. Allah ya kiyaye hanya". Fad'in Anna ta re da mik'a mata ledan da kuma dubu ashirin. Sosai Kandala ta yi ta godiya kamar za ta duk'a, ka na ta kalli Binty ta re da fad'in, "To Binty Allah ya k'ara sauk'i. Sai na zo d'aukar ki". Ba ta re da Bintyn ta kalle ta ba ta ce, "Allah ya kiyaye hanya". Ta fad'i hakane ta na jin wasu kwalla na zubo mata don ita kanta ba ta k'aunar matsawa kusa da Anna da Fanan don su ne duniyarta. Waya Anna ta d'aga ta kira ya Fu'ad ta re da shaida masa ya zo part d'in ta yanzu, kuma ka min ya zo ya biya ya kira Julaibib shi ma ya zo. Bayan ta gama wayarne ta nufi kitchen don kai abincin dinning d'in da ke nan parlour. Binty kuwa tuni ta mik'e ta yi saman don zuwa ganin halin da y'ar uwarta ta ke ciki. Ka min ta shiga corridorn da zai sa da ta da bedroom d'in su, ta ji kamar an rik'e hannun da ke mata zafi wanda sai da ta tallabo shi da d'ayan hannunta saboda ba za ta iya sakin shi ta yi tafiya ba. Azaba ta dunga ji har cikin kwanyanta kuma kamar an toshe bakinta ta kasa kuka. Sai da ta yi kusan minti uku kamin ta ji an saki hannun. Don har kwallar azaba sai da ta yi. Amma abunda ya matuk'ar ba ta mamaki, shine hannun na ta ya dai na mata zafi ko kad'an, kamar ba ta fad'i ba. Har gwada jujjuya hannun sai da ta yi, kuma lafiya k'alau hannun bai mata ciwo ba. "Ikon Allah!". Binty ta fad'i ta re da shiga bin corridor ta murd'a handle d'in d'akin su ta re da shiga ciki. Kwance ta samu Fanan ta na shasshek'ar kuka. Hawa kan gadon ta yi ta re da juyo da fuskan Fanan d'in ta ce, "Sister ki dai na kuka, wa ya isa ya raba mu. Ko aure ne, dole mazajan mu su hak'ura mu zauna a waje d'aya. Ga part d'i na ga na ki. Ko wannan tafiyar ma k'afa ta k'afar ki. Idan har ba za ki ba, to ni ma babu inda zan je". Saurin ta shi Fanan ta yi ta re da fad'in, "Kai amma ni wawiya ce, Sam ban kawo haka ba. Dama ni ban tab'a tafiya wani garin mai nisa ba Idan ba Gombe ba, shi ma ina k'arama mu ka je dukkan mu har da su ya Bibi". "K'afa ta k'afar ki ai". Binty ta fad'a ta re da d'aga pillow ta d'auko wayar ta ta kunna. "Ke wai har hannun ya warke". Fad'in Fanan cike da mamaki. Don ko d'an kumburin da ya yi ma ya sace. "Wallahi kam. Ni ma haka nagani. Abu kamar tsafi". Fad'in Binty. "Anya maganar ya Bibi ba gaskiya ba ce kuwa, har da d'an banzan rakin ki". Fad'in Fanan. Harara ta maka mata ta re da shiga message ta soma typing. " *Mu had'u 4:30. Ka jira ni a wajan*". Ta na gama rubutawan ta kalli Fanan ta re da fad'in, "Sister wani taimaki za ki min dan girman Allah". "Wani irin taimako kenan? Fad'a min. Babu taimakon da ba zan iya miki shi ba Idan har zan iya yin sa". Fanan ta fad'a ta re da ba ta natsuwarta. Shuru Binty ta na tunanin ta inda za ta fara maganar. Can ta nisa ta re da fad'in, "Fita na ke so na yi daga gidan nan. Zan had'u da Yousouf a wonderland by 4:30". Wani irin zaro idanuwa Fanan ta yi ta re da fad'in, "Are you out of your sense. Fita fa ki ka ce? Ta yaya za ki iya barin first and second gate ba ta re da an gan ki ba?". " Shiyasa na ce ina buk'atar taimakon ki ai. Ke za ki taimake ni in fita ai". Fad'in Binty. "Lallai kin d'auko ta da zafi. Kin san dai fire to fire ya dawo ko, sannan Anna ba ta bari mu fita kk bakin first gate ne sai da driver ko ya Fu'ad". Fanan ta fad'a ta na kallonta. Kwal-kwal Binty ta yi kamar za ta yi hawaye ta na kallon Fanan. Can sai ga hawaye shaaaaaa. "Na shiga uku! Why are you crying? Dan Allah ki ba ri. Zan yi k'ok'arin yi wa Anna magana sai mu fita ta re da driver, sai ki je ki ga romeo d'in na ki". Fad'in Fanan. Rungumeta Binty ta yi ta re da fad'in, "That's why I love you my beloved sis". Wayar Fanan d'in ce ta yi ringing, kallon wayar ta yi ta re da kallon Binty ka na ta ce, "Let go downstairs, Anna is calling". Fanan ta fad'i ta re da sauka daga kan gadon. Tun da su ke saukowa Anna ta zubawa Binty idanuwa ta re da k'arewa hannun na ta kallo ta na mamakin yadda lokaci guda hannun ya sab'e. Barrister Fu'ad ma kallon ta ya ke yi ya na sakar mata murmushi. Shi kuwa gogon da k'amshin turaransa ya game d'akin ko kallon inda su ke bai yi ba. Sakwaran sa ya ke ci kicin natsuwa. "Zo ki zauna a nan daughter". Anna ta nunawa Binty kujeran da ke kusa da ita, kuma shi ya ke fuskantar inda ya Bibi ya ke zaune. "Queen ya hannun?". Fad'in Barrister Fu'ad ya na kallon Binty. "Da sauk'i yaya. Na ma dai na jin ciwon kamar ban fad'i ba. Ka gani". Binty ta k'arisa maganar ta re da jujjuya hannun har da lankwasa shi ta na dariya. "Ah Alhamdulillah. Har na ji dad'i da na gan ki haka". Wani wawan kallo Ya Bibi ya jefi Barr Fu'ad da shi ta re da fad'in, "Idan surutun za ku yi, kwashesu ku yi can part d'in ka da su. Ka fi kowa sanin ban san yawan surutu a kai na, beside abinci mu ke yi". Fad'in Julaibib fuska a d'aure. "I'm sorry big bro". Fad'in Fu'ad ta re da kashewa k'annan na sa idanuwa. Binty kuwa kallon Julaibib d'in ta yi ta re da turo baki. Karaf su ka had'a idanuwa ta yi saurin saka tafukan hannunta ta rufe bakin ta na zare idanuwa. Shikuwa kallo d'aya ya mata ta re da jan tsaki k'asa-k'asa ya cigaba da cin abuncin sa. Duk d'agowar Binty sai ta kalle shi, shi ma kuma duk d'agowarta ya na kallonta ta gefen idanunsa wanda ita ba ta sani ba. Jan kujera baya ya yi ta re da d'aukar tissues ya goge bakinsa ka na ya kalli Anna ta re da fad'in, "Zan shiga cikin gida na gaida mutanan gida, sannan zan d'an kwanta in huta don gobe da asubha zan fita. Asibiti biyar su ke nai ma na. Wanda su kad'ai na yanke zan je a goben, amma idan zan biyewa mutanan da suke kira na, bazan samu lokaci na ko minti biyar ba idan ba sallah ba". "Gaskiya kam, gwara ka je ka huta. Kuma daddyn ku ma nasan ya na dawowa zai nai me ka". Fad'in Anna. "A nan side d'in ya ke ne?". Fad'in Julaibib. "A'a ya na part d'in Huriya ne". Anna ta fad'a. Binty kuwa zuba masa idanuwa ta yi ta na mamakin yadda ya ke magana kamar wanda aka sa shi dole sai ya yi. "Bar kallo na ko in zo in kwakwule idanuwanki". Fad'in Julaibib ta re da zazzaro mata idanuwa. Binty ta yi saurin Kai da idanuwanta ta re da tura baki tana guna guni. Juyawa ya yi ta re da ficewa daga d'akin. "Na fad'a ma ku sai kun kiyaye shi ai". Fad'in Anna ta re da mik'ewa ita ma ta bar wajan. Barrister Fu'ad ya kalli su Binty ta re da fad'in, "Ya Bibi ba mugu ba ne, wanda ya zauna da shi sosai zan gane hakan. Kawai shi bai son surutu da hayaniya ne. Idan ya na waje ku rik'a k'ok'arin gimtsewa. Yanzu zan je court, mai zan taho maku da shi idan zan dawo. "Vanilla ice cream". Fad'in Binty. "Ni ba na son ice cream, pizza na ke so sai strawberry". Fad'in Fanan. "To shikenan. Duk zan sayo maku. Sai na dawo". Fad'in Fu'ad ta re da barin wajan shima. "Ba ri na je na lallab'o Anna mu samu damar fita". Fad'in Fanan. "Yauwa sister dan Allah yi sauri. Kar ki fito sai ta amince". Binty ta fad'a. Bayan minti biyar Fanan ta sauko fuskan nan b'utu-b'utu kamar za ta fashe da kuka. Tun da Binty ta ga hakan jikinta ya yi sanyi ta san Anna ba ta amince ba kenan. "I'm sorry sister, Anna ta ce muje ka da mu dad'e". Wani tsalle Binty ta yi ta re da rungume Fanan d'in duk su ka sa dariya. Cikin abunda bai fi minti goma ba, su ka kammala shirin su su ka fito, kai tsaye wajan motarsu suka nufa, dama tunda driver ya hango su ya san fita ce, tuni ya riga su isa wajan motar. Su na shiga ya ja motar su ka fice. Supermarket ya fara kai su, ka na ya kai su wajan yin lalle. Kasancewar Fanan cewa Anna ta yi za su lalle kuma za su siyo pad na su ya k'are kuna Fanan d'in na gab da ganin al'adarta. Dalilin hakane ma yasa Anna ta amince su ka fita. Binty aka so ma yai wa lalle bak'i da ja a hannunta. Ba k'aramin kyau ya mata ba. Sai wanke mata kai da akayi ta re da busarwa da handryer. A na gama mata kamin a fara yi wa Fanan su ka d'auki excuse su ka fita. Ta baya su ka zaga saboda ka da driver ya gan su. "Binty Dan Allah ki tabbata biyar ta miki a nan wajan mu koma gida. Dan Allah ka da ki dad'e". Fad'in Fanan. "In sha Allah ba zan dad'e ba Fanan". Fad'in Binty ta re da saurin yin a gaba. Ta na fita ta samu taxi ta re da tare shi ta ce masa drop ya kai ta wonderland. Tun a cikin taxi d'in ta yi wa yousouf text a kan ta na hanya su had'u a can. Replay ya mata da shi ya na can ma tun tuni. Ba su wani jima sosai na su ka isa wajan. Kud'i ta ciro ta mik'a masa ta re da shiga wajan kasancewar ya Fu'ad ya na yawan kawo su wajan. Wayarta ta fido za ta kira shi. K'amshin wani turare mai dad'i ya daki hamcinta. A hankali ya juya bayanta idanuwan su suka had'u da na juna. Luuu ta yi da idanunta ta re da bud'e su a kan sa. Bak'aramin kyau ya mata ba. Sanye ya ke cikin wani d'anyan shadda kalar silver-silver, ash-ash. Gajeran riga ce mai gajeran hannu, sai hulla da ya turo shi gaban kan shi kad'an, kwantancan gashin kan shi kwance a k'eyarsa. Sai bak'in glasses da ya manna a fuskan shi hannun shi d'aya cikin aljihun wandonsa. Murmushi ya sakar mata ta re da zare glasses d'in da ke fuskan shi ta re da nuna mata hanya alamar su yi gaba. Binty ta kasa magana sai gaba da ta yi ya na bi ye da ita a baya. "Yauwa, to zauna ana gimbiya". Muryan shi mai dad'i ya daki dodon kunnanta. Sai da ta lumshe idanuwa ka min ta zauna a inda ya nuna mata, shi kuma ya zauna ya na fuskantar ta. Ka sa cigaba da had'a idanu da shi ta yi ta re sa sakin murmushi ta kalli k'asa ta re da furta, "Ina wuni". Cikin wani irin salo da bata san ma ta iya shi ba. Bai iya amsawa ba, sai kafe ta da idanuwa da yi for 1minute ka na a hankali ya furta, "Binty ina sonki, ina k'aunar ki har cikin jini na. Dan Allah ki so ni ko da kwatan yadda na ke son ki ne. Tun ranar da na fara ganin ki a shop rite, ki ka tafi da natsuwata. Y'an uwa da abokai na, sun kasa gane kai na. Wannan shine karo na na farko da na fad'a soyayya. Shin Binty za ki iya ba ni so?". Wani dad'i Binty ta ke ji tun daga can k'asan ranta na ta so mata. A hankali ta d'ago ta kalli idanuwan shi. Saurin janyewa ta yi saboda wani kunya da ya kama ta. Dariya ta ke yi a hankali ta re da murza d'an yatsan ta. "Binty dan Allah ka da ki ji kunya ta. Ba zan takura ki ba idan har akwai wanda ki ke so, amma na san dai ba zan kai labari ba idan har ki ka ce ba ki so na Binty. Dan Allah ka da ki ji kunya. Ki fad'a min ki na so na". Yousouf ya sake fad'i ya na kallonta. "Kullum tambayar kenan ko a message. Da ban son ka ba zan baka lokaci na ba har mu rik'a musayan kalamai. Ko a haka kawai zai tabbatar maka da ka karb'u a zuciya ta". Fad'in Binty kan ta a k'asa. Wani lumshe idanuwa Yousouf ya yi ta re da bud'e su ya na kallon cikin idanun Binty cike da shauk'i. "Ki min alk'awari ki na ta re da ni Binty duk runtsi. Ni ma kuka bazan tab'a guje miki ba a duk halin da kika ciki. Mu yi wa juna alk'awarin kasancewa da juna sai mutuwa za ta raba mu". Fad'in Yousouf. Ba ta re da wani dogon tunani ba Binty ta ce, "Yousouf na yi alka'warin kasancewa da kai a kowani irin hali sai mutuwa ce za ta raba mu. Ina k'aunar ka Yousouf". Binty ta fad'a babu d'ar ta na kallon cikin idanun Yousouf. Lumshe idanuwa Yousouf ya yi wanda ya kasance d'abi'ar sa ka na ya sa ka hannu cikin aljihun wandonsa ya fiddo wani d'an akwati ya aje akan table ta re da fad'in "Bud'e Binty, wannan shine zai zama shaidan alk'awarin mu". Bud'ewa Binty ta yi, zoben diamond ne mai kyau da shek'i har guda biyu. D'aukar babban ya yi ta re da mik'awa Binty ka na ya mata alama da idanu akan ta sa ka masa zoben a yatsan sa. Karb'a ta yi, ta re da kai hannu za ta sa ka masa ya yi saurin janye hannu ta re da girgiza kai ya ce, "Ki mai-maita abunda ki ka ce kamin ki sa ka min". "Na yi alk'awarin kasancewa da kai a ko wani irin hali sai mutuwa ce za ta raba mu". Ta na gama fad'in haka ta zura masa zoben a hannunsa. Sai dai a lokacin da hannunsu ya had'u sai taji wannan tururin ya daki hannunta har ba ta san lokacin da ta yi saurin janye hannunta ba. "Lafiya?". Yousouf ya tambaya saboda ganin reaction d'in ta. Murmushi ta sakar masa ta re da fad'in, "Ba ko mai". Ta fad'i hakane ta na d'an murza hannunta da har ya soma yi mata zafi. "Ba ni d'an yatsar ki". Fad'in Yousouf. Mik'awa d'an yatsar hannun hagunta ta yi, shi kuma ya fiddo zoben a cikin box d'in ta re da fad'in "Na yi alk'awarin kasancewa da kai har k'arshan numfashi na, sannna zan kula da ke fiye da kai na, ba zan bari abun cutarwa ya zo kusa da ke ba, zan kare ki da iya k'arfin da Allah ya ba ni, zan nu na miki so zan kuma kare ki daga ko wani irin cuta in sha Allah". Ya na gama fad'in haka ya zura mata zoben a yatsarta. Hannun shi da ya tab'a fatar yatsarta, ji ta yi kamar wajan ya sale saboda rad'ad'in da ta ji. Amma haka ta daure har ya gama saka mata. "Allah ne shaidan mu akan haka". A ta re su ka had'a baki wajan fad'in haka. "Bari na je na kawo miki drinks da snack". Ba ta re da ya ji ra'ayin ta ba ya yi saurin barin wajan. A hanyar shi ta dawo wa su ka had'u da abokinsa Ramadan shi ma yazo da budurwansa. "Kai wa na ke gani kamar Yousouf?". Fad'in Ramadan. "Ni ne wallahi". Fad'in Yousouf ya na shafa k'eyarsa. "Shegen gora, mai ka ke yi a nan?". Ya sa ke tambayan sa. Ba ta re sa Yousouf ya ba shi amsa ba ya kalli in da Binty ta ke a zaune ta na waya. Zaro idanuwa Ramadan ya yi ta re da fad'in, "Iyyeee, yau ina su Fauwaz in fad'a masu ka shigo hannu. Da ma mun fad'a maka ai". Fad'in Ramadan. "Na bar baby ita kad'ai. Kar ta ji ba dad'i kai ma yi wajan ta ka babyn". Fad'in Yousouf. Dariya Ramadan ya yi ta re da fad'in, "Naga wannan salon". Ya fad'i hakane ta re da mik'a masa hannu su ka tafa. K'arasowa ya yi wajan Binty ta re da zama ya aje mata drinks d'in da ya kawo mata da straw a jiki, shi ma ya ajiye na shi a gaban shi ya na kallon ta. "Ya dai, kallon fa?". Fad'in Binty ta re da d'age gira. "Da wa ki ke waya?". Fad'in Yousouf ta re da tsare ta da idanu. Farrr ta yi da idanu ta re da fad'in, "Saurayi na ne ya kira ni". Tsare ta da idanuwa ya yi ta re da fad'in, "Aiko zan kashe shi". Zaro idanuwa ta yi ta re da fad'in, "Wayyo! Ka dai na maganar kisa. Ni ba da namiji na ke waya ba. Fanan ce ta kira ni akan in yi sauri in dawo. Kasan gidan mu ba'a ba ri mu na fita. Yauwa dabara mu ka yi wa Anna". "Wallahi da gaske na ke. A kan ki zan iya ko mai. Zan iya kashe mutum ko aljani idan ya yi k'ok'arin zuwa kusa da ke Binty. Ban tab'a son wata mace ba sai a kan ki, kuma ban tab'a jin ina jin matsanaicin kishi mace ba sai a kan ki. Dan Allah kar ki yarda wani namiji ya yi kusa da ke don wallahi zuciyata za ta buga Binty. Yanzu mu ka had'u da aboki na tun na yarinta, ko shi ban yadda ya zo in da ki ke ba har ya yi dogon magana da ke ya ji dad'i a ransa, hakan yasa na masa dubura bai biyo ni domin ganin fuskan ki ba. Binty dan Allah ni kad'ai, ni kad'ai a ran ki". Fad'in Yousouf. Gaban Binty haka ya ke bugawa dum-dum-dum saboda kalmar kisan da ya furta. "Naji, na amince kai kad'ai za ka kasance cikin zuciya ta, amma dan Allah ka janye kalmar kisan kai da ka ambata. A musulunce ma haramun ne. Kuma duk wanda ya kashe wani rai wuta zai shiga". Fad'in Binty. Ajiyar zuciya ya sauke ta re da fad'in, "To shikenan mai sona, amma ke ma sai kin ta ya ni kiyaye hakan kin ji?". Fad'in Yousouf. Gyad'a masa kai ta yi ta re da fad'in, "Zan koma ka da Fanan ta yi ta jira na". "To yanzu kuma sai yaushe? Tun dai gidan ku ba barin fita ake yi ba". Fad'in Yousouf. "Laa! Na manta ban fad'a maka ba, jibi zan yi tafiya zan je garin mu, amma ba zan dad'e ba. Idan na dawo za mu had'u". Fad'in Binty. *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *49-50*🌹 ............."Gaskiya zan bi ki, mu tafi ta re kawai don ba zan juri rashin ki har na tsawon sati guda ba, zan samu matsala". Fad'in Yousouf. Dariya Binty ta yi sai da kumatun ya lob'a ta re da rera masa baiti cikin zazzak'ar muryanta, " *Sai wata rana masoyi zan bar ka, sai wata rana rabuwa ba mutuwa ba. D'an uwa rabin raina ban so mu yo rabuwa*" "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Mai sona sassauta muryan ki dan Allah ka da wani ya ji. Don na tabbata wannan zazzak'ar muryan ta ki zai iya haifar wa da mazaje da dama matsalar da zai jawo abunda ki ke gudu kuma ki ka hana ni furtawa". Fad'in Yousouf. Hannu ta sa ka ta rufe bakinta ta re da fad'in, "Afwan Reality, hakan ba za ta sake faruwa ba. Ka san ban k'aunar b'acin ran ka". "A'a, hakan fa za ta sake faruwa, amma sai muna a kad'aice in da babu wani namijin da zai ji muryan ki sai ni d'aya". Fad'in Yousouf ta re da lumshe idanuwansa. "An gama my reality, daga yau rowan muryata zan rik'awa mutane". "Da kin kuwa kyauta wa Yousouf". Dariya su ka yi gaba d'ayan su. Hanya ya nuna mata ta re da fad'in, "Mu je ko in kai ki ka da sister Fanan ta ji shuru". Yousouf ya fad'a. Jerawa su ka yi su na tafiya ta re da hira cikin nisha'di irin na saurayi da budurwa. Sanye ta ke cikin riga da wando pallazo red colour, as usual ta yi parking d'in gashin ta a tsakiyar kan ta. Sai d'an siririn farin gyale da ta yafa a wuyanta zuwa kafad'unta da kuma farin takalmi mai tsini. Ba k'aramin kyau ta yi ba, sai dai gaba d'aya suran jikinta a waje ya ke. Duk inda su ka wuce maza da mata kallonta ake yi. "Besty ba ka ganin yadda ake bi na da idanuwa kamar za'a cinye ni. Ni kai na na san ni mai kyau ne. Ni madubin dubawa ce ga jama'a wallahi". "Hmm". Shi ne abubda Hamdan ya fad'a ta re da kallonta ta gefen idanu. Duka ta d'aka masa a tsakiyar baya ta re da fad'in, "Uban hmm, na tsane ka! Na gama koro magana sai ka wani ce min hmm kamar bai ciwon hak'ori". Fad'in Sabrin. "Ai ni matsala ta da ke kenan gajen hak'uri gare ki. So fa na ke na ce miki ai ke d'in ce kyan ki ya yi yawa. Ba ki ga wani har kusan fad'awa kan wata budurwa ya yi ba garin kallon ki". Hamdan ya fad'a. "Shege ina kallon shi ai, kuma ni kwalelen sa ce. Back to maganar mu, mai ka ke tunanin zan yi in burgesa? Shi mutum ne mara son magana da hayaniya. Wallahi besty ina matuk'ar son shi sosai. Ban tab'a son wani namiji a duniya ba kamar sa. Ya ce min in sha Allah zai samu lokaci ya zo next tomorrow. Dan Allah wani tarba zan masa ya burge sa?". Fad'in Sabrin dai-dai lokacin lokacin da za su shigo ta wani k'ofa, su Binty kuma za su fita. Ba ta re da gaba d'ayansu sun kula da juna ba, Sabrin ta bangaje ta. K'urawa juna idanu su ka yi. Shi kuma Hamdan wani d'an allura ya soki takalminsa ya duk'a ya na k'ok'arin zarewa. "Binty lafiya?". Fad'in Yousouf. "Lafiya k'alau Binty ta yi saurin fad'a ta re da yin gaba. "Binty Hisham mai goro?". Sabrin ta fad'a gabanta na tsananta fad'uwa. Cak Binty ta tsaya, dama zargi ta ke yi amma kiran cikakkiyar sunanta da Sabrin d'in ta yi ne ya sa ta tabbar ita d'in ce. Juyowa ta yi ta re da d'an sakin murmushi ta re da fad'in, "Kamar Sabrin ko?". Ta fad'i hakane ta re da d'an matsowa. Sai da Sabrin ta isa daf da ita, ka na ta ce, "Wanna fuska ta ki ba zai yi sauri mantuwa a waje na ba, billahi na yi alk'awarin in dai ni jinin Alhaji Saifullahi ce, sai na lallata wannan d'an k'aramin kyawun da ki ke tak'ama da shi". Ta na gama fad'in haka shi kuma Hamdan ya d'ago ta re da kallon in da Sabrin d'in ta ke. Hakanan ya ji gabansa ya buga da k'arfi ya na k'ara k'arewa Binty kallo zuciyar sa na wani irin zillo da buguwa. Juyo wa Sabrin d'in ta yi ta re da dawowa wajan Hamdan ta ce, "Mu je". Ta fad'i hakane ta re da yin kicin-kicin da fuska. Shikuwa Hamdan sai kallon Binty ya ke yi da ta tsaya kamar statue ta na kallon Sabrin d'in. Yousouf da ke gefe ya k'araso kusa da Binty ta re da fad'in, "Mai sona lafiya? Ya naga duk jikin ki ya yi sanyi. Kin san ta ne?". K'ak'alo murmushi ta yi ta re da fad'in, "Eh na santa, ta re mu ka yi primary school a *Lead British*". "OK. Mu je to". Fad'in Yousouf ta re da sa ta a gaba ya na biye da ita a baya. "Ko za ka bi ta ne?". Fad'in Sabrin a k'ufule. "Wallahi haka na ke ji a jikina kamar na Santa". Fad'in Hamdan. Banzan kallo ta watsa masa ta re sa yin tsaki ta yi gaba. Shikuwa Hamdan sai da ya k'ara bin su Binty da kallo ka min ya bi bayan Sabrin da ta ke ji kamar ta buga saboda ganin halittar da ta tsana a duniya. Bud'e mata gidan gaba ya yi, sai da ta shiga ya rufe ka na ya zagaya ya shiga driver seat ta re da rufe motar. Ita kuwa Binty gaba d'aya jikinta ne ya yi sanyi k'alau da maganar da Sabrin d'in ta fad'a mata. Ta d'auka Sabrin d'in za ta canza a gaba, amma sai ta ga kamar abun na ta k'aruwa ya yi. "Ba zan yi wa motar nan key ba idan har ba ki fad'a min abunda ke damun ki ba, wallahi ko da hakan na nufin za mu kai sha biyun dare a nan wajan". Fad'in Yousouf da ya zuba mata fararan idanuwansa. Saurin kallon sa ta yi ta re da k'ak'alo murmushi ta ce, "Ba fa abunda ke damu na, kawai schoolmate d'ina ce da na ga ni ta ba ni mamaki". Fad'in Binty. "Wani irin mamaki kenan ta ba ki?". Ya sake je ho mata tambaya ta re da tsare ta da idanu. "Ta na da isa da tak'ama ne tun muna yara, sai na ga abun bai ragu ba ko da mu ka girma, shi ne abun ke ba ni mamaki". Murmushi Yousouf ya yi ta re da fad'in, "To hakan ya dai na damun ki, ko wani mutun da ki ka gani a duniya da irin yanayin sa da kuma d'abi'ar sa. Ki saki jikin ki, ko mu kwana a nan". Zaro idanuwa ta yi ta re da fad'in, "Wallahi na saki, mu tafi". Ta fad'i hakane ta re sa sakin fuskanta. Dariya ya yi ta re sa yi wa motar key ya yi reverse ta re da fita daga wajan. Ita ta yi masa kwantance har su ka iso wajan. Sai da ya k'ara rik'e ta kusan mintuna biyar ya na k'ara zayyane mata yadda ya ke jin ta a zuciyar sa da kuma jaddada mata alk'awarin su Ka na ya bar ta ta wuce. Ta baya ta biyo kamar yadda ta fita ta baya. Ko da ta shiga shagon, tuni har an kammalawa Fanan lalle har ta wanke. Kan ta ake busar mata. Fanan d'in na ganinta ta saki ajiyar zuciya ta re da fad'in, "Ina nan ina zullumi wallahi. Gaskiya kin kyauta da ba ki makara ba". Ta fad'i hakane ta re da karb'an ribom a hannun mai saloon d'in ta kama gashin da kan ta, ka na ta mik'e ta kakkab'e jikinta ta re da ba mai saloon d'in kud'inta har da na lalle ka na su ka fito. Driver na zaune a mota ya na sauraran labarai a wayar shi, ya na ganin su ya gyara zama ta re da yi wa mota key. Su na shiga ya d'aga su ka nausa titi. K'arfe shidda saura minti goma su ka shigo gida. Da ya Fu'ad su ka ci karo a parlour ya na cin pop corn ya na kuma kallon wani Indian series mai suna *JODHA AKBAR* a tashar Bollywood, sam shi ba ma fahimta ya ke yi ba, kawai ya canza tasha ne ya ga su na yi kawai ya bar shi. "Kai, ina ku ka je ku ka yi yamma haka?". Fad'in ya Fu'ad ya na kallon su. K'arasawa wajan sa su ka yi ta re da zama a gyefansa. Binty na gefen dama, Fanan kuma na hagu ta re sa saka hannu su ka soma cin pop corn d'in. "Ba ma sai kun ban amsa ba, hannun ku kawai ya shaida min inda ku ka je. Masha Allah lalle ya yi kyau". Fad'in Ya Fu'ad ya na kallon zanen lallan hannun Binty da ya yi bala'in yi mata kyau kamar dan ita aka k'irk'ire shi. "Anna ta ce in ce maku idan kun dawo ku d'aura girki. Kuma ku nutsu don yaya Bibi zai ci abincin kuma ta re za su zo da abokinsa. Don haka kallo ba na ku ba ne, aje a sauya kaya a shiga kitchen". Fad'in ya Fu'ad. Ai har rige-rigen wuntsulowa su ka yi ta re da nufar sama don canza kaya su shiga kitchen d'in. Barr Fu'ad ba masu dariya. *WAYE YOUSOUF MUHAMMAD AHLAM* ..........Cikakken bakatsine ne haifaffan garin Abuja. Mahaifin ya tara dukiya sosai do min shi ya ke da *SUNCITY ESTATE*. Mahaifin sa mace d'aya gare shi mai suna Saratu. Y'ay'an su takwas, hud'u maza hud'u mata. Sai dai estate d'in damk'am ya ke da zuri'arsa. Muhammad Ahlam mutum ne mai k'aunar zumuni, wannan dalilin ne ya sa gaba estate d'in shi, zuri'ar sa ne. Ana kiran sunan estates d'in da gidan kyawawa kasancewar mazan su da matan su kyawawa ne. Yousouf shi ne d'a na biyu a cikin y'ay'an Dr Muhammad wanda ya kasance a da shi d'in likitan Tsohon sarkin Adamawa ne wanda ya mutu d'an sa ya hau, kasancewar sa mai amana ya sa ya zama kamar family a masarautar Adamawa kuma har gobe bai dai na ziyarta su ba duk da ya yi retired. Yousouf ya yi karatunsa a k'asar *US*, engineer na'ura ne. Kamar yadda cikakkiya mace ta kware a sarrafa tukunya, haka Yousouf ya kware wajan sarrafa computer ko da kuwa idanuwansa a rufe ya ke. Kullum cikin busy ya ke, wannan dalilin ne ya sa ko kusa mata ba sa gabansa. Computers d'in sa su ne matansa. Mace ba ta gaban sa sam, kuma hakan ba Wai ya na nufin bai da lafiya ba ne. K'alau ya ke. Abokansa sun yi tsiyar har sun gaji sun kyalesa. Yousouf na da matuk'ar kishin abunda ya ke so, hakan na d'aya daga cikin dalilan da ya sa ye gujewa mata saboda ya na da matuk'ar saka abu a zuciyarsa. Idan har ya na son abu to fa ya na san shi har abada kuma bai son a kusanci abun nan. Yousouf na da wani ciwo tun ya na yaro, babu k'asar da ba'a je ba domin nai ma masa magani ba, amma har yanzu cutar ba ta warke ba, sai da kuma ya na dad'ewa bai ta shi ba. Wata cuta ce da idan ta taso masa, zai iya wata biyu zuwa uku a kwance, ba ci ba sha, kuma sai dai a ba shi abinci a drip. Sannan kuma bai motsi sai dai ya yi ta bin mutane da idanuwa. Hankalin ahalin Dr Muhammad ba k'aramin tashi ya ke yi ba duk san da ciwon Yousouf ya ta shi. Kwatsam kuma sai ga shi ya had'u da sahibul ruhinsa da ya ji ya na matuk'ar k'aunarta kuma zai iya ko mai saboda ita. Har cikin ran shi ya ke jin ta. _wannan kenan._ *_____________________* Cikin abunda bai fi awa guda ba, har sun kammala girki. Lafiyayyan tuwon shinkafa su ka girka da miyan wake da yaji bushasshen kifi da nama, sannan kuma su ka sake yin miyan ayoyo da kuma stew a gefe. Sai da su ka jera komai a dinning ka na su ka haura sama don yin wanka. 7miss calls Binty ta ga ni a wayanta duk na Yousouf. Ba ta bi bayan call d'in ba sai da ta yi wanka ta re da d'aura alwala don an kusa kira isha'i. Su na girki aka yi magriba su ka sake su ka je su ka yi. Mai kawai Binty ta murzawa jikinta ta zura doguwar riga mai hula ta re da saka dogon hijjab don har an riga da an yi kiran sallar isha'i. Bayan ta idar da sallar ne ta bi kiran Yousouf. Katse kiran ya yi ta re da bin bayan kiran na ta. Ringing biyu ta d'aga ta re da karawa a kunnanta, "Amincin Allah ya tabbata a gare ki mai sona". Fad'in Yousouf. "Ameen ta re da kai *Reality*". Binty ta fad'i ta re da kwanciya flat a kan gado. "Ya ki ka ko ma gida?". "Alhamdulillah! Kai fa?". Fad'in Binty. "Cike da tunanin ni". Anna ce ta turo k'ofar ta shigo ta re da fad'in, "Da wa ki ke waya Binty?"....... *KU YI HAK'URI DA WANNAN MU HAD'E GOBE* 🌹 *51-52*🌹 ............Cikin saurin ta yanke wayar ta re da mik'ewa zaune ta ce, "Annah da school mate d'ina ce, mu na magana ne akan admission da zai fito". "To maza ki sauko ki zo ku ci abinci, ke kad'ai ake jira a k'asa". Fad'in Annah. "To Anna ga ni nan". Binty ta fad'a ta re da saukowa daga kan gadon ta bi bayan Anna da ta fita. Gaba d'ayan su ne zaune akan dinning d'in. Yanzu ma Binty a kan kujeran da ta zauna d'azu ta zauna, ta na fuskantar ya Bibi. Ganin ba bu abokin ya Bibi da ya Fu'ad ya ce ta re za su zo, kallon ya Fu'ad d'in ta yi ta re da masa nu ni da hannu alamar ina abokin na shi. D'aga mata kafad'a ya yi alamar oho ta re da jan zip a bakinsa ya kuma nu na mata ya Bibin alamar ta yi shuru. Sai da su ka kammala cin abincin ka na Ya Bibi ya kalli Anna ta re da fad'in, "Anna ba ki ganin ya kamata Zaid ya dawo kusa damu? Kin san fa rik'on d'a sai iyayansa". Saurin d'agowa Binty ta yi ta re da zuba masa idanuwa saboda kalmar rik'on d'a sai iyayansa da ya furta. Harara Anna ta ma ka masa ta re da fad'in, "Ya fad'a maka ana kankaran naman jikinsa ne a can? To ba zai dawo ba d'in. Idan kuma kai ne ubansa, sai ka je ka d'auko sa a wajan mai martaba. Don Zaid ya bar hannun Dattijo ya na wajan uwar gidan mai martaba". Fad'in Anna. Kasancewar Zaid mai bi ma Fu'ad tun wajan yaye mahaifiyar Anna ta amshe shi, ita kuma uwar gidan mai martaba ta yi mata fin k'arfi ita ma ta amshe shi. Da Julaibib d'in ma su ka so amshewa. "Allah ya huci zuciyar ki Anna, dama kawai yadda na ga duk kan mu zuri'ar ki muna cin abinci a waje d'aya, shiyasa shi ma na yi masa kwad'ayin haka". Fad'in Julaibib ta re da mik'ewa. "Kai ma ka kusa dai na cin abincin ta re da mu a nan kuma nan kusa don kwanaki zan yanke maka ka fiddo matar aure". Fad'in Anna ta re da harararsa. "Anna a gaba yara. Dan Allah ki dai na min maganar aure a gaban su kar su raina ni". "Au na manta fa, kai ka yankewa k'asa cibi. (Kwafa) kar ka fiddo macan aure sai na baka mamaki nan kusa". Anna ta sake fad'i. "Ku bar nan ko in karya k'afafuwan ku". Julaibib ya fad'a ya na zazzarowa su Binty idanuwan sa. Aikuwa da sauri su ka bar wajan, Binty kuwa saura kad'an ta zame, ya Fu'ad ya yi sauri kai hannu zai rik'o ta Allah ya ba ta sa'a ta dafa bango. Anna har ta mik'e. Julaibib d'in kuwa wani arnen harara ya jefi Fu'ad da shi ka na ya juya ta re da nufar k'ofa don zuwa wajan mahaifin sa. Girgiza kai Anna ta yi ta re da kallon Fu'ad ta ce, "Yauwa Fu'ad, gobe idan Allah ya kai mu, za ka d'auki Binty da Fanan ka kai su supermarket ka yi masu siyayya sosai, jibi za ta je k'auyansu ganin gida". Fad'in Anna. Gaban ya Fu'ad d'in ne ya buga dam dam ta re da kallon Anna da sauri ya ce, "Anna kuma kin yarda su tafi d'in?". "Ka ji wani maganar banza da wofi. Na ce maka wajan danginta za ta je kuma sai ka ce na yarda ni da aka min kara da kawaici tsawon shekaru ba ta je ba run da ta zo nan. Amma ba ka da hankalin Fu'ad". Fad'in Anna. "Anna wallahi ni kawai matar ce ba ta kwanta min a rai ba". Fad'in Fu'ad. Harara Anna ta ma ka masa ta re da fad'in, "Ka dai ji abunda na fad'a maka ko? Karfe sha d'aya na ke so ku tafi". "To Anna Allah ya kai mu". Fad'in Fu'ad jiki a sanyaye. Harara ta k'ara maka mashi ka min ta yi hanyar stairs. Julaibib na fita hanyar part d'in Hajiya Huriya ya nufa domin ganawa da mahaifin sa. Ya gitta side d'in Suhail kad'an ya yi saurin dawowa baya saboda warin wiwin da ya ji ta k'ofofin hancinsa da kuma hayak'in da ya ke gani ya na fita duk da d'akin a kulle ya ke. Hanyar k'ofar ya yi ran shi a matuk'ar b'ace ta re da dukan k'ofar da k'arfi kamar zai karya. "Wani d'an hegiyar ne ya ke dukan k'ofata haka iyeeee". Fad'in Suhail cike da maye. K'ara dukan k'ofar Julaibib ya yi da mugun k'arfi. A zafafe Suhail ya taso ya na rangaji daga shi sai boxer, tattoo d'in nan ya fito rad'o rad'o a jikinsa sai wani uban chain a wuyan shi har ciki, karuwarsa kuma ta na kwance a three sitter ta na zuk'an sigari da ga ita sai wani arnan rigar baccin da gaba d'aya jikinta ana ganinsa a waje. Gadan gadan k'ofar ya nufo ta re da bud'e shi kamar zai kifa. Wani irin kallo Julaibib d'in ya ke bin sa da shi har jikinsa ya so ma rawa don hatta naman kumatun shi rawa su ke yi. Tuni har idanuwansa sun kad'a. Shi kuwa Suhail duk da ya na cikin maye hakan bai hana shi wani iri zabura ba ta re da komawa baya, don ko a mafarki bai tab'a tunanin Julaibib ba ne. Don shi bai da labarin ma ya dawo k'asar. "Yyyyyyaya Bibi". Fad'in Suhail bakinsa na rawa kamar zai fad'o. Wani wawan mari Ya Bibi ya d'auke sa da shi sai da ya kifa k'asa wanwar. "Baby whats going on". Karuwar Suhail ta fad'a ta re da tasowa daga in da ta ke ta na rangaji. Wani irin tuk'uk'in bak'in ciki ne ya k'ara mamaye zuciyar Julaibib har bai san san da ya saka k'afa ya take gaban Suhail d'in ba da k'arfi. Wani irin ihu Suhail d'in ya saki ta re saka hannu biyu ya rik'e gabansa ya na tumbling. Ita kuwa karuwar jikinta ne ya soma b'ari, saurin d'aukar hijjab d'inta har k'asa ta yi ta saka ta na k'ok'arin fita daga d'akin. Wani irin fincikota ya yi ta re da yasar da ita a tsakar d'akin sai da ta kwallara k'ara saboda cikinta da ya bugu da k'asa. K'arasawa wajan kayan kallo Julaibib ya yi ta re da fizgo wata waya ya shiga lafka masu ta ko ina a jikinsu dai dai lokacin Ya Fu'ad ya fad'o d'akin sakamakon ihun Suhail da kuma na mace da ya ji. Fu'ad jikinsa b'ari ya soma yi saboda irin dukan da Julaibib d'in ya ke ma su. Ran shi ya yi b'acin da zai iya aikata komai. Da gudu Fu'ad d'in ya juya domin kiran Anna. Ko kafin Anna ta shigo, Suhail da karuwansa sun yi suma uku su na farfad'owa. "Julaibib ka bari na ce!". Amma ta fad'a a tsawace. Amma inah Julaibib bai ma san ta na yi ba sai dad'a dagewa ya ke yi ya na bugun su. "Julaibib ba da kai na ke magana ba". Anna ta sake fad'i amma duk da hakan bai bari ba. "Salissssss!". Anna ta kira ainahin sunan sa a tsawace sai da d'akin ya d'auka. Sai a lokacin ya yar da bulalan da har ya tsintsinke saboda irin dukan da Julaibib ya yi masu. Suhail numfashi sama sama ya ke yi, ya yin da karuwar ta sa ko motsi ba ta yi. Fu'ad bai ankara ba ya ji an d'auke sa da maruka har kala uku masu gigitarwa ka na ya nuna sa da yatsa, "Kkkkkana kalll'o yii yah ron nan ya na is...kkan cin nan am..ma baza kullll...a da shi ba". Fad'in Julaibib cike da in'i na saboda b'acin ran da ya ke ciki. Kauuuuuuuuuu! Anna ta d'auke shi da mari hagu da dama ta re da fad'in, "Ban isa ba ko? Ni ban isa in fad'a maka ka bari ka yi ba ko? Yanzu idan ka yi kisan kai fa?". Julaibib na son yin magana amma ya kasa saboda in inar da ta ci k'arfin sa. Hargitsa gashin kansa ya so ma yi ta re da soma buga k'afarshi a k'asa. Hankalin Anna ne ya yi mugun tashi don ta san halin d'an na ta. "Wuce side d'in nan right now". Anna ta fad'a wa Fu'ad. Cikin sauri Fu'ad d'in ya fita saboda ya san wanene wan na shi. Ita kuwa Anna hannun Julaibib d'in ta kama ta re da nufar side d'in sa. Sai da ta aje sa akan kujera ka na ta d'auko ruwa mai sanyi a fridge ta tsiyaya masa a cup ta re da mik'a masa. Ba musu ya karb'a ya shanye. K'ara masa ta kuma yi, nan ma ya kuma shanye wa. "Ta shi ka shiga ba yi ka je ka yi alwala ka yi sallah ka kwanta". Anna ta fad'a. Ba musu ya yi wajan bayi, ita kuma ajiyar zuciya ta saki ta re da fita ta koma part d'in Suhail d'in. Yadda ta bar su, haka ta sa me su. Ruwa ta d'auko a fridge ta re da bud'ewa ta d'iba ta shafa a fuskan yarinyar. Wawiyar ajiyar zuciya ta sauke ta re da rushewa da kuka. "Ta shi ki wuce gidan ku tun kafin ki rasa k'afar ki d'aya a cikin gidan nan". Fad'in Anna. Cikin sauri yarinyar ta mik'e ta re da d'aukar takalminta mai tsini a hannu. Har ta kai k'ofa Anna ta ce, "Ki ji tsoran Allah yarinya. Ka da ki manta ke macece, zaman gidan iyayanki ko gidan miji shi ya kamace ki ba bin gidajan samari ba su na yaudarar ki da kud'i da kayan shaye-shaye ba. Ki ko ma gaban iyayan ki kk ji tsoran Allah". "Nagode". Shine abubda yarinyar ta fad'a ta re da saurin barin wajan gabanta ba fad'uwa don ba ta tab'a zaton za ta farka ba ta ji ta a kabari ba. kallon Suhail da ke ta murd'e murd'e hannunsa rik'e da al'aurarsa ta yi ta re da fad'in, "Ka d'an ka ga ni in dai ba za ka kiyayi duniya ka kuma natsu ba". Ta na gama fad'in haka ta yi waje. *WASHA GARI* 🌙🌙🌙 Fuska kumbure Fu'ad ya tashi saboda marin da ya sha a wajan babban yaya. Shikuwa Julaibib a masallaci wajan sallar asubha su ka had'u da daddy su ka gaisa, bai tambayesa dalilin rashin zuwansa ba, kasancewar ya na ganin duk abunda ya faru daga CCTV CAMERA da ke d'akinsa. Duk abunda Suhail d'in ya ke yi, Alhaji Usman na sane, wani abu ya ke jira akan sa saboda mummunar shiri da yake masa don har safarar cocaine d'in da ya ke yi ya na sane da shi. Julaibib daga masallaci ya wuce asibiti ko saboda jiransa da ake yi kuma ya yi wa Sabrin alk'awarin zai za wajanta yau da daddare idan ya gama abunda ya ke yi da wuri. "Fu'ad, mai ya samu fuskan ka?" Fad'in Anna wanda hakan ya sa daga Binty har Fanan da ke breakfast su ka juya su na kallon shi. Binty har sai da ta b'arar da shayin da ke gabanta wajan mik'ewa. Sai da ta isa gaban Fu'ad ka na ta ce, "Yaya na mai ya samu fuskan ka?". Ta fad'i hakane siraran hawaye na zubowa daga idanuwan ta. "No kar ki kuka beauty, kwanciya na yi a kan tiles kuma jikina bai san sanyi shiyasa wajan ya kumbura, kuma zuwa anjima ma zai sace". Fad'in Fu'ad ya na sakin murmushi. "Dan Allah Yaya kar ka k'ara kwanciya a k'asa". Fad'in Binty a marairaice. "In sha Allah". Fad'in Fu'ad ta re da nufar dinning d'in. Sai da ya je dai-dai kunnan Anna ka na ya ce, "Anna ke ki ka jawo min jin hannu maza a fuskata, aradu har na yi bacci ina jin zugi. Da kin bar ni na d'au mataki da ban samu kafta a fuska ba". Fad'in Fu'ad ta re da jan kujera ya zauna. *Walleh ban yi niyyar yi ba yau, kawai tausay ma ku na yi. Amma ga shi nan ku d'and'ana* 🌹 *53-54*🌹 ............Gimtse dariya Anna ta yi, don fisabilillah Fu'ad ya ba ta tausayi kuma ya ba ta dariya. "Ka ba ri zan kai su supermarket d'in da kai na, kai na je ka huta kawai". Fad'in Anna. "Anna a kan me? Zan iya kai su da kai na Allah, ba sai kin je ba". Fad'in Fu'ad da sauri. "To ai shikenan, idan lokacin ya yi, sai ka zo ka karb'i ATM d'i na, don tafiyarta gobe ne". Anna ta fad'a ta re da cigaba da kurb'an tea. "Ina da kud'i enough a account d'i na ba sai na karb'i ATM d'in ki ba". Fad'in ya Fu'ad. Binty kuwa sai da ta had'a wani kasancewar ta zubar da na ta garin tashi ta je wajan ya Fu'ad don jin abunda ya same shi a fuskan shi. "Anna amma ta re zamu tafi ko?". Fad'in Fanan ta na kallon Anna. "Eh ta re za ku tafi mana". Anna ta fad'a duk a tunanin ta supermarket d'in ta ke nu fi. Dad'i ne ya kama Fanan kamar ta tashi ta taka rawa. Bayan sun gama breakfast d'in ne, su ka tattara kayan wajan su ka kai kitchen ta re da wanke su, don haka Anna ta ce masu in dai suna gida to su za su yi aikin gida ka da su je gidan miji ba su iya komai ba. K'arfe goma da rabi Fanan da Binty su ka yi wanka ta re da kimtsawa cikin wani ora Orange less wanda aka masu d'inkin riga da skirt. D'inkin ya amshi jikin su. Farin gyale su ka yafa ta re da farin takalmi. Ko man su iri d'aya su ka saka har d'an kunne. "Anna mun shirya". Fad'in Binty". Fad'in Binty. "Ku sauka ku jira shi a k'asa, nasan shi ma jiran ku ya ke yi". Anna ta fad'a. Saukowan su ka yi, aikuwa su ka yi arba da Ya Fu'ad d'in zaune a kan kujera ya na jiran su. Ya na ganin su ya mik'e ta re da fad'in, "Yauwa muje ko?" Ya fad'i haka ne ta re da yin gaba su ma su na biye da shi a baya. A tsakar gidan ya fiddo wayar shi ta re da yi masu salfie su duka, ka na ya yi da Binty ya kuma ko ma ya yi da Fanan. Ba k'aramin kaya su ka jida ba, har Binty ta ga abun ya yi yawa ta ce masa ya isa haka. Sai bayan azahar su ka shigo gida da kaya nik'i nik'i. Anna sai sa masa albarka ta ke yi. Sama su ka hau su ka gabatar da sallar Azahar ka na ko wacce ta shiga had'a kayanta a cikin jaka da duk wani abun da za su buk'ata. *8:30pm* .............Sanye ya ke cikin k'ananan kaya wanda ya ke fito da shi kamar k'aramin yaro. Sosai ya yi kyau gashin kan nan nashi ya kwanta luf-luf, ga sajen nan da ya ke k'ara fito da kyawun sa. Babu abunda ke tashi a jikinsa sai k'amshin turaren Karen Kelly da vesace eros. Sallama ya yi can k'asan mak'oshinsa ka na ya murd'a handle d'in k'ofar ya shigo parlour. "Wallahi ban yarda ba wannan ai cuta ce, zan ta da ke ki ka wuce min da na baya kuma ki ka mai da ni gida. Allah sai an sake game d'in nan". Fad'in Fanan ta na k'ok'arin kwace wayar da ke hannun Binty ita kuma sai dariya ta ke yi ta k'i ba ta dama wanda hakan ya sa ba su ji k'a ran bud'e k'ofar da Julaibib d'in ya yi ba. "Ke!" Wa ni tsawa ya da ka masu wanda gaba d'ayan su ba su san lokacin da su ka hantsila daka kan kujeran da su ke kai ta baya ma ta re da mik'ewa a guje su ka yi sama. Fu'ad da ke gefe kuma da shi ake buga Ludo d'in sai sunnar da kai k'asa ya ke yi ta re da tuno azabar da ya gifta ta kuncinsa jiya da daddare. Wani uban harara Julaibib d'in ya maka masa ta re da yin kwafa ka na ya bi stairs don zuwa d'akin Anna. Ya na juya baya Fu'ad ya sulale ya bar d'akin don gudun tsautsayi. "Assalamu alaikum". Julaibib ya fad'a a k'ofar d'akin Anna ta re da kwankwasawa. "Shigo". Shi ne abunda Anna ta ce ba yan ta amsa sallamar kasancewar k'ofar ba a datse ta ke ba. Tura kai ya yi ta re da shiga d'akin, zama ya yi a kusa da ita, ita kuma ta juya kanta gefe. "Annata ina wuni?". Fad'in Julaibib. "Da ban wuni ba za ka ganni? D'azu da ba ka zo da safe ka gaida ni ba saboda ka na fushi da ni, mutuwa na yi?". "Anna I'm sorry". Julaibib ya fad'a a marairaice don ya san Anna ba za ta juri dogon fushi da shi ba. "Ka rage wannan zuciyar fa Ina fad'a maka. Don Allah ba bu wanda zai yarda ya ba ka y'ar shi ka illatata a banza". Fad'in Anna. "Anna ni kuma mai zai kai ni dukan mace, macen ma matata". Julaibib ya fad'a har da wani karya wuya. "To wa ya sani. Du bi dai irin dukan da ka yi wa d'an uwan ka da wannan yarinyar". Anna ta fad'a. Nan da nan ran shi ya b'aci saboda tuno masa da abunda k'anin na sa ya ke yi a cikin gidan ubansa. Magana ya soma yi cikin in'ina, "Annn..na yanzu abun.....da yyyaron nan yyyyy....yyyy... yake yyyyi". "Yi hak'uri ka yi shuru, Sam na san bai kyauta ba. Kuma maganar gaskiya k'anin ka Fu'ad ya na iya kacin bakin k'ok'arin sa ni ke hana sa". Anna ta yi saurin katse ta don yanzu sai ya fara bubbuga mata k'afa a k'asa ya na dukan kan shi. "Amma An....." "Yi hakuri ka bar maganar dan Allah". Anna ta k'ara katse yi. Mik'ewa ya yi ta re da fad'in, "Zan d'an.... D'an je wwwani waje". Ya sa ke fad'i cike da in'ina saboda har yanzu ya na cikin b'acin rai, kuma in har ya na cikin b'acin rai bai iya magana sai da in'ina. "Sai ka dawo Allah ya tsare". Anna ta fad'a. Ba ta re da ya ce komai ba ya juya ta re da fita daga d'akin. Bayansa ta bi da kallo ta re da fad'in, "Allah ya ye maka wannan bak'ar zuciya". 🪂🪂🪂 ...........Horn ya yi a k'ofar gate d'in, mai gadi ya wangale masa gate d'in shi kuma ya danna hancin motar ciki ta re da nai man waje ya yi parking. K'afarshi d'aya ya zaro waje ta re da d'aukar wayar shi ya shiga contact ya yi searching my p (my patient) ta re da dialing. Sabrin da ke zaune a gyefen Hamdan sanye da wani wando jean mai kyau ta re da rigar shi, ka na ta daura komono a kai kan ta ba d'an kwali as usual sai parking gashin da ta yi a gefe. "Duk kin wani rud'e kamar wacce sarkin maka zai kawo wa ziyara". Fad'in Hamdan ta re da hararar ta. "Are you joulos?" Sabrin ta fad'a ta re da murgud'a masa baki. "Why? Sai ka ce Beautyna ce wani zai kawo mata ziyara ta ke rawan jiki haka". Fad'in Hamdan ya na yamutsa baki. Nuna shi ta yi da yatsa za ta yi magana wayarta da ke hannunta ya soma ringing. Kallon screen d'in ta yi ta re da zaro idanuwa ta ce, "He's calling". Ta fad'a out of exited. Tab'e baki Hamdan ya yi ta re da fad'in, "Yauwa dai zan ga wannan Bibi d'in da ake kurantawa always". Ba ta re da ta ba shi amsa ba ta yi picking call d'in ta kara a kunne. Julaibib bai jira ta yi magana ya ce, "Ina waje". Ta re da katse kiran ya fito daga motar gaba d'aya. Da gudu Sabrin ta yi sama don shaidawa Mom d'in ta ya Bibi is outside. Sallah ta taras da mom d'in na ta ba yi, saukowa ta yi ta fita daga side d'in ta yi side d'in aunty Junaina kasancewar daddyn ta a can ya ke. Murd'a handle ta yi ta re da fad'awa d'akin, zaune su ke a kan dinning su na cin abincin har da su twince. "Daddy daddy daddy, ya zo ya na waje. Aunty Junaina ya ya Bibi ya zo ya na waje". Mik'ewa aunty Junaina ta yi cike da fara'a ta re da fad'in, "Ahhh muna da babban bak'o, maza kai shi parlourn bak'i ka da ya gaji da jira". Ta fad'i haka ne ta re da mai da dubanta izuwa ga y'an biyu ta ce, "Maza ku tashi ku je ku kai masa snacks da drink ka min ya isa d'akin". Daddy kuwa tu ni ya bar cin abincin ya kama hannun Sabrin d'in ta re da fita daga d'akin. Twins kuwa ba dan sun so ba su ka fita zuwa abunda maman na su ta sa ka su. Hannun Alhaji Saifullahi cikin na Sabrin su ka isa in da Julaibib ya ke. Ba bu kunya Sabrin d'in ta nufi Julaibib ta re da rungume sa a gaban mahaifin ta. Shikuwa Julaibib kunya ce duk ta ka ma shi sai sunnar da kai ya ke yi. Hannu Alhaji Saifullahi ya mik'a masa su ka yi musabah ka na Julaibib d'in ya d'an rusuna ta re da fad'in, "Ina wuni daddy, mun sa me ku lafiya?". D'an rungumo shi Alhaji Saifullahi ya yi ta re da fad'in "Lafiya k'alau doctor, ya fama da patients?". "Alhamdulillah". Fad'in Julaibib. Hannun shi ya ka ma har parlourn bak'i, ana d'in ma k'ara gaisawa su ka yi, ita kuwa Sabrin d'in dad'i ya gama kasheta yau ga Yaya Bibin ta a cikin gidan su. Lallai hak'anta zai cimma ruwa. Fita daga d'akin Alhaji Saifullahi ya yi don ba su waje su gana. Zama ta yi kusa da shi ta re da fad'in, "Ya ya Bibi na". "My patient ya ki ke? Ina fatan yanzu dai babu wani matsala ko?". Duk da ta ji wani irin saboda sunan da ya kira ta da shi wanda da ma haka ya ke kiran ta da shi, amma sai ta yi murmushi ta re da fad'in, "Ka dawo lafiya?". "Alhamdulillah!" Ya fad'a a gajarce. Dai-dai lokacin Hamdan ya shigo da sallama a bakin sa. Gaba d'aya su ka amsa masa, murmushi akan fuskan Sabrin ta ce, "Yaya Bibi sannan shi ne best friend d'ina da na ke ba ka labari, kuma shi cousin d'i na ne, yaron k'anwar mama ne". Kallon shi Julaibib ya yi, shi kuma ya yi saurin fad'in, "Barka da zuwa ya Bibi? Ka dawo lafiya?". "Lafiya k'alau alhamdulillah. Ya karatu? A na dai yi ko? K'awarka ta ke min ta kammala secondary". "Eh ya ya Bibi ta kammala. Ni kuma ina 200level ina karanta civil engineering". Fad'in Hamdan. "Masha Allah, Allah ya taimaka". Fad'in Julaibib. "Besty, sai da safe na ga Yaya Bibi zan koma gida dare na yi". Fad'in Hamdan. "To bye sai da safe". Fad'in Sabrin. Ficewa Hamdan ya yi cikin zuciyar sa kuwa ya na jinjinawa Sabrin d'in don tabbas ta iya zab'e. Bai dad'e ba ya yi mata sallama zai koma gida. Aikuwa ta shiga buga k'afa ta na shagwaba akan bai dade ba kuma bai ci komai ba. Shi kuma ya ce mata dare ya yi, ina sha Allah idan ya sake dawowa zai ci. Sosai ta ji dad'i da ta ji zai sake dawowa, shikuma ya fad'a ne kawai don kauce mata don ya lura ta na da shegen rawan kai da surutu kamar uwar aku, shi kuma sam bai son hayaniya. Har mota ta raka shi ta na masa bye-bye. Sai da ta ga motar ta fice ka na ta juya ta koma cikin gida cike da farin ciki. *The next day* ...........Tun asuba Fanan da Binty ke kuka da su ka ji ba da Fanan d'in za'a tafi ba. Anna ta yi lallashin har ta gaji ta yi banza da su. Shi kuwa Fu'ad tun 7:00am ya fita saboda kiran gaggawan da aka masa a court. "Ni wallahi Anna ba zan je ba in dai ba da Fanan za mu tafi ba". Fad'in Binty ta na shasshek'ar kuka. "Haba Binty, ni ban isa in fad'a maku magana ba kenan? To shikenan ku yi abunda kuka ga dama". Anna ta fad'a a tunanin ta za su saduda. Amma ga mamakin ta sai ta ga Fanan d'in ta hau sama ta re da jawo jakar kayanta dai-dai lokacin Julaibib ya shigo d'akin fuskan nan b'utu-b'utu sanye cikin farin coat, na cikin kuma ja da ya fito da kyawunsa. "Alhamdulillah! Julaibib yi min maganin wad'annan yaran. Tafiya Binty za ta yi wajan danginta, ka ga Baabarta nan ta fi k'arfin awa guda da zuwa amma Binty ta k'i ta bita wai ita dole sai da Fanan za ta tafi, ni kuma na fi son Binty ta je ta shiga y'an uwanta tun da ta kai kusan shekara takwas rabonta da gida, wasu ma duk ba su santa ba. Amma yarinyar nan ka gan ta ta k'i bin baabar tata". Fad'in Anna. Tun ka min Julaibib ya ce wani abu Fanan ta yar da jakar hannunta ta re da fashewa da kuka ta yi sama da gudu. Ita ma Bintyn kuka ta fashe da shi ta re da rungume Anna. Tuni har Anna ta ji hawaye sun cicciko mata a idanuwan ta. Kallon Kandala ta yi ta re da fad'in, "Kama ta ku wuce Kandala, rana na yi kuma za ku yi doguwar tafiya. Allah ya tsare hanya". Fad'in Anna ta re da janye jikinta Binty na dad'a kwakwume ta. "Anna su tafi da Fanan d'in". Fad'in Julaibib. Saurin kallon shi Kandala ta yi karaf su ka had'a idanuwa ta yi saurin janye na ta. Hanyar stairs d'in ya nufa, minti biyu sai ga shi rik'e da hannun Fanan d'in. "Su tafi tare Anna, ni ina ganin tafiyar ta su ta re zai fi". Julaibib ya sake fad'i. Dad'i ne ya mamaye zuciyar Fanan da Binty. "To kandala kin ji abunda wan su ya ce, ina fatan hakan ba matsala?". Yak'e ta yi wanda ya fi kuka ciwo ka na ta ce, "Aahh ba matsala wallahi, ai da Binty da Fanan duk d'aya ne a waje na". "To Allah ya kiyaye hanya". Fad'in Anna. "Ku kula da kan ku ban da yawo". Julaibib ya fad'a, amma idan ka kalle shi ba za ka tab'a yarda shi ya yi maganar ba. Kayan su su ka d'auka har wajan motar su kasancewar drivern gidan ne zai kai su. D'agawa Anna hannu su ka yi ta re da shiga motar driver ya ja. Kandala kuwa zufa ce ke ta wanke mata jikinta don ba haka ta so ba, kuma idan Hajiya Mansura ta ji hakan, za ta iya kwace kud'in da ta bata. Dad'in ta d'aya ma ta riga da ta gama tsara komai a can Saminakan. ............Tafiya su ka yi mik'ak'k'a duk sun gaji saboda ba su saba irin wannan doguwar tafiya ba, don ita Binty za ta iya cewa wannan shine karonta na biyu, lokacin da zo garin Abuja da kuma yau, Fanan d'in ma dai haka ne, sau d'aya ta tab'a zuwa Gombe sai kuma yau, gomben ma ba za ta iya cewa ga yanayin nisan ba don tun ta na yarinya ne. Sai gab da magriba su ka shigo k'auyan Saminaka. Yara sai bin motar su ke yi da gudu. Hatta manyan ma bin motar su ke yi da idanuwa. Kandala ce ta soma fitowa, aikuwa wad'and'a su ka san ta su ka yi mata caaaa su na mata oyoyo. Matan gida kuwa duk an firfito waje, wasu ma daga su sai d'aurin kirji. Wasu kuma yara ne d'auke a hannunsu su na shan nono amma haka su ka fito waje su na lek'e. *KO YA ZA'A KWASHE A K'AUYAN SAMINAKA?* *PAID BOOK 08128755586* 🌹 *55-56*🌹 .............Binty da Fanan su ma su ka fito sai bin mutanan su ke yi da idanuwa kamar yarda su ma mutanan su ke bin su da kallo. Kandala ce ta dubi driver ba yan ya gama firfito masu da duka kayan su ta ce, "Bawan Allah amma kwana nan za ka yi ko? Na ga dare ya yi kuma tafiyan dare akwai damuwa musamman yadda k'asar ba tsaro yanzu ga kuma mutanan nan da su ke garkuwa da mutane". Kandala ta fad'a kamar mutuniyar arziki. "In sha Allah, Allah zai tsare ni kamar yadda mu ka zo lafiya, zan koma gida lafiya. Yanzun nan zan juya". Fad'in driver ya na rufe both d'in mota. Karyar da wuya Kandala ta yi ta re da fad'in, "To shikenan, Allah ya tsare ya kai ka lafiya. Amma wallahi ni ban son tafiyar daran nan. Ko fa abinci ba ka ci ba". "Kar ki damu Hajiya" Fad'in driver ta re da zagayawa ya shiga mazaunin sa ya yi reverse ya bar k'auyan. Kandala ajiyar zuciya ta sauke ta re da umartan yaran nan da su ka zagaye su akan su d'auki jakan kunan su Binty su shiga da shi cikin gida. Wani irin babban gida ne mai shashe-shashe. Ka na ganin yanayin gidan ka san gida ne na mutune irin gidan gandun nan. Haka gaba d'aya yaron su ka bi yo su Binty wanda su ka masu lak'abi da bak'in Larabawa har cikin gida. Wata tsohuwa ce da ke zaune bi sa kujera y'ar tsuguno ta d'ago da kan ta kasancewar bakace ta ke yi don tuni ta d'aura sauwa. "Kai kai! Gidan uban wa za ku haka da ku ka shigo min gida riii kamar kun rako amarya? Maza ku fice ku ban......." Ta kasa k'arisa maganar saboda ido hud'u da ta yi da Kandala. "Jakar uban can! B'atan kai ki ka yi ne, ko kuwa gizo ki ke min ni shatu d'iyar Duna?". "Goggo Shatu ni ce, ba gizo ki ke gani ba. D'iyar y'ar uwar ki ce ta dawo gare ki". Fad'in Kandala. "Ke dalla tafi can ki baiwa mutane waje gantalalla kawai. Uban wa za ki yi wa bariki? To kar na ke kallon ki gulmamma, wai wani d'iyar y'ar uwar ki ce ta dawo gare ki. To maza tun muna mu biyu ki fice daga gidan nan tun kamin in miki yekuwa jama'a billahi". Fad'in Goggo Shatu. Hayaniyar Goggo Shatu ce ta fito da kafatanin mutanan gida yaransu da manyan su don baiwa ido abinci. Bagazan-bagazan ya shigo cikin gida. Alwala ya ke yi wa ni yaro ya tafi da gudu ya shaida masa Baaba Kandala ta zo daga birni. Su na had'a idanu da Kandala ya fashe da kuka har da face majina ya na fad'in, "Kandala ke ce? Ke ni ke gani yau da idanuwa na? Don Allah ki kai ni wajan d'iyar Hashimu in gan ta ko zan samu sauk'i a zuciyata. Allah sarki Hashimu Allah ya ji'kan ka". Fad'in Buba ya na k'ara face majina. "Ga d'iyar Hashimu nan a gaban ka yau na kawo maku ita". Fad'in Kandala ta na nuna Binty da gaba d'aya mamaki da takaici sun cika ta. Kawai ikon Allah ta ke kallo. Fanan kuwa tausayi ne ya cika zuciyar ta da ta ga irin kukan da Buba ya ke yi ta re da rok'arwa Mahaifin Bintyn gafara. Wajanta ya k'ara sa ta re da fad'in, "Wayyiiyoo Allah! Yarinya ina kallon fuskan ki na ga Hashimu. Kamar ku d'aya kamar ya yi kaki kwarankwatsi. Allah dai ya ji'kan ka Hashimu. Ga y'arka nan kyakkyawa kamar uwarta Karime. Karime ba dai kyau ba duk k'auyan su ba kamar ta kwaran kwashi". "Wai mi ka ke hwad'i ne haka Buba? D'iyar wacece na ji ka ke hid'i. Kamar sunan Hashimu na naji ka na hid'i ko ban jiya da kyau ba ne?". "Kwaran kwashi hakannan na hid'i Goggo. Yau ga jikan yar ki a kusa da ke billahi". Fad'in Buba. Mik'ewa Goggo Shatu ta yi ta na d'ingisawa har ta k'araso wajan da Binty ta ke tsaye ta na k'are mata kallo tun daga ka. Wani irin kuka ta fashe da shi ta re da fad'in, "Allah na gode maka da ka hadd'a huskata da na d'iyat Hashimu. Kande ya akai ki ka kwatota wajan dangin mahaifiyar na ta?". Fad'in Goggo Shatu ta na kallon Kandala ta re da share kwallar fuskan ta da bakin zanen ta. "Goggo wannan dogon bayani ne, ki ba ri mu nutsa tukun sai in miki bayani. Yanzu mun kwaso hanya ga yunwa da k'ishirwa. Ai duk wannan dad'ewar da na yi ban zo ba duk a kan ta ne billahi". "Muje ciki kande. Allah dai ya miki albarka". Fad'in Goggo ta re da ka mo hannun Binty. Ita kuma Binty ta kamo na Fanan su ka nufi D'akin Goggon. Cikin k'ank'anin lokaci har kwanuka sun cika a sasan Goggo kasancewar matan y'ay'an ta maza kaf a cikin gidan su ke zaune da iyalansu. Goggo ta mak'ale Binty ku sa da ita wacce ita Sam ta kasa sakin jiki da ita don ta san sam babu wani alak'a ta jini da su ka had'a. Sai dai kwakwalwarta cike su ke da tambayoyin da ta kasa bawa kanta amsa game da Kandala da kuma Hashimu da ake alak'antawa da mahaifinta. Sam Binty ta kasa sakin jiki ta ci abinci, Fanan kuwa ta ci dambu wanda ya mata dad'i sosai ga shi ya sha zogale da gyad'a ga yaji mai dad'i har da man k'uli Goggo Shatu ta tsiyaya mata cikin na sana'arta saboda dambun ya mata dad'in ci sosai. Goggo Shatu ba ta samu damar keb'ewa da kandala ba domin ta mata bayanin yadda aka yi ta iya zuwa gari i gari har Bauchi ta taho da d'iyar Hashimu kuma dangin mahaifiyar ta su ka yadda su ka ba ta. Sasa-sasa haka aka dunga bi da Binty da Fanan su na gaida mutane. Duk in da aka je za a ce mata wannan shine wane, ko kuma wannan ita ce goggo wance. Sai da aka karad'e kaf gidan da ita ka na su ka dawo d'akin Goggo a gajiye don har mak'ota sun fara shiga sai Binty ta ce masu su na son yin sallah kuma ana bin su azahar da la'asar kasancewar a hanya ta riske su. Bayan sun idar da sallah ne su ka nai mi ruwan wanka domin sun saba wanka duk dare kamin su kwanta. Aikuwa nan da nan Goggo Shatu ta sa matar Buhari d'an ta na uku ta hura wuta ta saka masu ruwan wankan. Sabrin d'in ce ta fara zuwa domin ta yi wanka. Da kyar ta iya yin wanka saboda yadda bayin ya ke. Ba wai kazanta ne a bayin ba, k'asa ne a k'asab ba flour, idan ta zuba ruwa sai kasan ya rik'a tab'a ta wanda hakan ke sa ta ke jin kyankyamin jikinta. Binty ma dai haka ta k'ok'arta ta yi wankan ta dawo d'aki. Kayan bacci ta saka ka na ta jawo wayarta domin yi wa Yousouf message kasancewar rabon da su yi magana tun su na gab da shigowa k'auyan Saminaka. Kuma a yanzu haka k'auyan da su ke ba network sai mutum ya fita ta wajan wani k'aton dutsi network d'in me dawowa. Tsaki ta yi k'asa-k'asa saboda takaicin rashin network d'in da za ta hau WhatsApp ta yi charting da ruhinta ta samu natsuwa. "Yaushe za mu koma gida ne?". Binty ta fad'a a kunnan Fanan. "Ke yau fa mu ka zo har kin fara tambayar yaushe za mu koma gida". Fanan ta fad'a. "Ni ban iya rayuwa ba network. Ba waya da Anna, ya barrister da kuma ruhi na Yousouf. Yanzu haka wallahi ji na na ke kamar a kan k'aya". "Haka nan za ki yi hak'uri. Ai na ji Baaba Kandala ta na fad'in sai an hau wani dutse ake samun network. Gobe ba sai muje wajan ba. Na san Anna ita ma na can cikin damuwan ko mun sauka lafiya". "Ke dai bari. Allah dai ya kai mu goben, da sassafe zan je wajan dutsin nan". Fad'in Binty. *Washa gari* **************** Kasancewar su Binty sun saba tashi da asuba, da asubar fari su ka ta shi da ciwon baya kasancewar a gadon kara su ka kwana. Abunda ya ba su mamaki gaba d'aya gidan sun ta shi sai kai wa da komowa su ke yi kasancewar kusan duka gidan kowa da sana'ar sa. Wasu kunu da k'osai, wasu masa, wasu d'an wake, wasu kuma alale. Shiyasa su ke tashi da safar assalatu su soma hada-hadan sana'ar su. Ko kafin bakwai har kowacce ta fita da kayan sana'ar ta, kuma kamar jiya lokacin da su ka iso, haka ma yau aka cika su da abinci kala-kala. Duk mai sana'ar nan sai da ta aje kwana silver na abincin sana'arta. Binty dai alale ta ci, Fanan kuma kasancewar ta na son d'an wake kuma ba ko da haushe Anna ke yi ba, shi ta ci, shi ma da ta ci, sai ta ji na Anna ya fi dad'i. Wajajan k'arfe goma, Kandala ta saka su Binty a gaba ta na ta zaga dangi da ita. Duk in da su ka je, wasu har hawaye su ke yi, wasu kuma mamaki ne k'umshe a fuskokin su na canzawar d'iyar Hashimu zuwa baturiya duk da mahaifiyarta d'in fara ce amma a kashi d'ari na farin d'iyar tata kashi biyu ta ke da. Sai bayan azahar su ka gama bulayin bin dangi. Daga nan kuma wani yaro ya raka su can kan dutse domin su kira gida. Anna su ka fara kira a waya, sun kusa awa su na waya da ita. Fanan sai fad'a mata yanayin k'auyan ta ke yi cike da nisha'di. Bayan sun gama waya da Anna ne su ka kira Barrister Fu'ad. Shi ma haka suka kwashi tsayin lokaci su na waya da shi ta re da fad'a masa yadda su ka yi missing d'in sa. Binty na yanke wayar kasancewar da wayarta gaba d'aya aka yi kiran. Sak'onni ne su ka shigo wayar tata har guda sha d'aya kuma duk daga Yousouf ne ya na fad'a mata yadda hankalin shi ya ke a tashe saboda rashin samun ta a waya. Ta na k'ok'arin kiran shi, kiran na shi ya shigo wayar. Murmushi ta yi ta re da picking call d'in. Wa ni ajiyar zuciya ya sauke ta re da fad'in, "Haba mai sona kin san yadda na damu kuwa da rashin jin ki a waya? Ina ki ka shige ne ba'a samun ki a waya?". Fad'in Yousouf. "I'm sorry love, wallahi garin ne ba network sai an zo wajan wani dutsi ake samun network d'in kuma ban samu damar zuwa wajan ba sai yanzu saboda kai ni wajan dangi da aka yi ta yi tun safe". Ajiyar zuciya ya sa ke saukewa ta re da fad'in, "Mai sona ni dai zan biyo ki kawai". Dariya ta yi mai d'an sauti ta re da fad'in, "Haba Love ka kwantar da hankalin ka, ai saura kwana shidda mu dawo. Ke nan haka na nufin bayan mun yi aure ba za ka iya ba ri na na yi tafiyan wata d'aya ba kenan?". Tari ne ya sark'e shi. Sai da ya gama sanna ya ce, "Haba mai sona, kashe love d'in na ki za ki yi? Kin san Allah, tafiya idan ta wuce ta kwana biyu ba ki zuwanta". Zaro idanuwa ta yi kamar ya na ganinta ta re da fad'in, "Haba mana love. Kar ka yi min haka. Ni da na ke so duk bayan kwana biyu in rik'a zuwa gidan Anna in yi sati guda ka min in dawo gida". Dariya ta ba shi, sai da ya dara ka na ya ce, "Ai Anna ma ba za ta yadda ba. Ke idan ma ta yadda tu bak'i biyu za ta rik'a gani duk bayan kwana biyun nan". "Suwa da wa kenan?". Fad'in Binty. "Ni da ke mana". Dariya sosai Binty ta yi ta re da fad'in, "To ina za ka ri'ka kwana kenan? Gwara dai ni ina da d'aki na". "To ni ma ai a d'akin na ki zan kwana". Fad'in Yousouf. "Kai". Ta fad'a da sauri. "Ke". Shi ma ya fad'a. Dariya su ka kwashe da shi. Nan su ka cigaba da musayan kalaman soyayya. Fanan da duk ta k'osa saboda ranar da ta kwallo ta na gasa ta, ita kuwa Binty da ta fad'a kogin soyayyan ko zafin ranar ba ta ji. "Ke wallahi ki kashe wayar nan ko in wuce in bar ki kwarankwatsi". Bushewa da dariya Binty ta yi saboda yadda Fanan ta furta kwarankwatsi kamar yadda ta ji Kawu Buba ya fad'a jiya wanda hakan ya kasance d'abi'ar y'an k'auyan. "Dariyan mai ki ke yi haka mai sona?". Fad'in Yousouf. "Zan ba ka labari idan mun dawo. Sai mun yi waya gobe. I love you". Ta na gama fad'in haka ta katse wayar baki d'aya saboda ta san idan shi ne bai k'i su kwana su na waya ba. Don wani lokaci a gida haka su ke yi sai su raba dare su na waya har kunnanta zafi ya ke mata. Sometimes a hands free ta ke saka wayar ta aje a gefe. Saukowa su ka yi daga can saman dutsin rik'e da hannun juna. "Kwarankwatsi ban kuma rako ki waya. Ni ba da soyayya ni da dukan rana. To kusa ki nai mi mai rako ki tad'i walleh". Dariya Binty ta yi ta re da dukan bayan ta ta ce, "Allah ya ba ki sa'a Allah ta ji wannan rantsuwa a bakin ki, za ki fad'a masu". Fad'in Binty. "Kin tuna dukan da Anna ta yi mana ni da ke a d'aki lokacin da mu ka yi wa Fasila rashin kunya?". Fad'in Fanan. "Bar tuna min. Don yanzu haka jin zafin dukan na ke a jiki na. Ai Anna gwana ce wajan iya sarrafa bulala a jikin mutum". Fad'in Binty. "Ai gidan sarauta ta tashi, ta na ganin yadda ake cafala mutane idan sun yi laifi da shirgegiyar bulaliyar da fadawa suke rik'ewa a hannunsu". Fad'in Fanan. "Zan so watarana in je masarauta in ga yadda ake gudanar da mulki. Idan ina gani a cikin film abun burge ni ya ke yi walleh. Amma fa ban da zalincin wasun su". Binty ta fad'a. "In da rai za mu je Binty in sha Allah. Za ki sha mamaki. Za ki ga yadda za'a rik'a mana wallahi ". "Can't wait to see me their".. *___________* .........Bayan sun dawo gida, Goggo ta ba su abinci, shinkafa ce da wake da man k'uli da yaji. Sun ji dad'in abincin sosai don ba su tab'a ci ba sai yau. Kandala ce ta shigo d'akin ta re da fad'in, "Y'an matan Anna har kun dawo? Sannun ku da dawowa. Yauwa Binty zo kawun ki ya ce ki zo idan kun dawo". Mik'ewa Binty ta yi ta re rik'o hannun Fanan, amma sai Fanan d'in ta nok'e ta re da fad'in, "Dan Allah Binty ki je ki dawo, Allah na gaji so na ke na d'an kwanta ka min la'asar". Fad'in Fanan ba wai don abunda ta fad'a gaskiya ba ne, sai don bawa Binty damar kasancewar da kawun na ta ita kad'ai. May be akwai sirrin da su ke yin wanda ba su buk'atar ta a wajan. Ba dan Binty ta so ba ta saki hannun na ta ta re da bin bayan Kandala har can k'uryan gidan d'akin matar Buba mai kwarankwatsi... Su na shiga matar Buba Rahine ta fito ita da y'ay'anta kamar yadda mijinta idon cin naira ya fad'a mata. Bayan sun fita, Kandala ta sakayo rub'arb'iyar k'ofar ta re da kunna torch light d'in sha kid'an ka bak'auyenta saboda d'akin ya yi duhu. "Zauna magana za mu yi mai muhimmanci". Fad'in Kandala ta re da nu na mata tabarmar da ke shimfid'e a tsakar d'akin. Ba ta re da musu ba ta zauna don ita kan ta ta na son tambayar ta manufarta a kanta. Ita ma Kandalar samun waje ta yi ta zauna ta re da fad'in, 'Yauwa y'ar albarka. Kin san dai a fad'in duniyar nan ba ki da wata kamar ni ko?". Wani irin d'ago idanuwa ta yi ta re da zubawa Kandala ka na ta yi murmushi ta re da fad'in, "Ba ni da kamar Anna dai da zuri'ar ta. Na san dai ke ce silar had'uwata da su tabbas. Amma ban san menene manufarki a kai na da kuma wad'annan mutane ma su karamci ba. Ta sanadiyata kin samu kud'in da ko wani mai aikin gwannati bai samun haka. Ban to na miki asiri akan babu abunda mu ka had'a da ke ba, amma ban san menene dalilin ki na yin duk wannan abun da ki ke yi ba. Idan har da ba ni da wayau, yanzu ina da shi. Kar na ke kallon ki. Na san ba ni da wata alak'a da ke da kuma wannan k'auye da ki ka kawo ni. Amma zan iya aje hakan a mazaunin gudun ka da Anna ta zarge ki tsawon shekaru takwas ba ki ta b'a kai ni wajan sauran dangi ba. Amma abunda ya matuk'ar daure min kai shi ne, yadda y'an garin nan su ka aminta ni d'iyar wanda ki ka ba ni a matsayin mahaifi ne wato Hashimu. Mai ya sa ki ke duk wannan abun? Mai ya sa tun tuni ba ki tab'a kawo ni nan ba sai wannan karon? Tabbas akwai wani abunda ki ke shiryawa. Kuma ina san sanin menene shi". Fad'in Binty ta re da tsare Kandala da idanuwa. Sosai mamaki da tsoro su ka bayyana a kan Binty. Don a wautar Kandala, Binty a wancan lokacin ta yi k'ank'antar ta fahimci ba ta da alak'a da ita. Duk a nata wautar saboda Binty ba ta tab'a yi mata maganar ta san ba su da alak'a ba, sai ta ke tunanin dagaske Binty ta yarda ita d'in yar mahaifin ta ce. D'aure fuska Kandala ta yi ta re da fad'in, "Sai me idan kin fahimci ba ni da alak'a ta jini da ke. Ko ki na tunanin za ki iya fad'awa Hajiya ne kuma ta yarda. Ton yarinya kin riga kin bar shiri tun rani. A yanzu haka zan iya miki ramin da zai afka da ke. Don haka gwara ma ki cigaba da amince akan ni d'in Baabar ki ce ko kuma ki bar daular da ki ke ciki kuma ki k'are a magark'ama. Ni a waje na ba abun damuwa ba ne idan na k'are a magark'ama don na gama cin nawa zamanin. Ke kuma yanzu ki ke gan ganiyar ki". "Da ina da niyyar to na miki asiri, da tuni na tona. Saboda ki kwantar da hankalin ki, ni ba zan tona miki asiri ba sai dai idan Allah shi ya tona ki da kan shi. Amma ki sanj ramin k'arya, k'urarre ne. Ni yanzu abunda na ke so, ki fad'a min manufar zuwan mu k'auyan nan". Fad'in Binty. Gyara zama Kandala ta yi ta re da fad'in, "Yarinya kin kyautawa kan ki. Kuma ni manufata ta arziki ce, abun alheri na ke tafe miki da shi musamman yadda ba *BA KI DA GATAN* nan, za ki tara kud'i masu d'umbin yawa wanda idan Allah ya yi kin yi wani auran, hatta jikokin ki ba za su yi talauci ba". Wani kallo Binty ta bi ta da shi ta re da fad'in, "Ban ga ne idan na yi wani auran ba, da ma na tab'a aure ne da har zan sake wani auran?". "Kash! Matsala ta da ke sauri. Ki ba ri ko mai zan warware ma ki. Yanzu kam ai budurwa ki ke ba ki tab'a aure ba. Amma fa wannan abu da zan miki hanyar shi, za ki ji dad'in shi. Amma hakan zai kasance sirri tsakanin ki da wacce za ku yi abun. Yanzu ba ni da hurumin fad'a miki komai sai kun had'u da matar tukun. Sanna akwai wani abun da ba ki sani ba, fallasa matar na nufin abubuwa uku ne, na farko rasa rayuwar wacce ki ke matuk'ar k'auna fiye da kan ki wato Annah, mai bi Mata, Fanan wacce ku ke ta re yanzu, sai na ukun su Fu'ad".................. *PAID BOOK 08128755583* *57-58*🌹 .............Dam! Dam! Dam! Haka zuciyar Binty ke bugawa kamar zai tsaga k'irjinta ya fito har Kandala da ke gabanta ta na jin bugun k'irjin na ta wanda hakan ya tabbatar mata da lallai Binty ta tsorata da abunda ta ce mata. "Dan girman ubangijin halitta ka da ku tab'a mahaifiyata da y'an uwana, idan ku ka min haka ba ku min adalci ba. Baaba Kandala ka da ki alkhairi da sharri, ka da ki manta na san babu abunda na had'a da ke, amma dalili na ki ke amsar kud'in da ko wani ma'aikacin gwantanin bai samun haka amma na yi shuru na rufa miki asiri don ta sanadin ki na samu duk abunda na ke tak'ama da shi yanzu. *BA NI DA GATA*, ina rayuwa ne a kan bola cike da tarin jahilci da daud'a, amma yanzu na samu ilimi na addini da na boko duk ta sanadiyar Anna da ta mai da ni tamkar d'iyar cikinta ko in ce fiye da hakan, don say ta ri ta min abu ba ta re da ta yi wa Fanan ba. To ki na tunanin zan iya bari wani abu ya cutar da ita ko zuri'arta? Zan iya yin komai don Allah ta rayu in dai ba kauce hanya ba ne. Dan Allah ka da komai ya sa my Anna ta". Fad'in Binty ta re da k'arishe maganar da kuka mai sauti. Tab'e baki Kandala ta yi ta re da harararta ka na ta ce, "Ni ba kuka na kira ki ki min a nan ba, na dai fad'a miki sharud'd'an kin ji. Kuma wallahi ina mai k'ara tabbatar mi ki da cewar fitar da maganar ko rashin bin umarnita shi zai yanki tikitin salwantar rayuwar Anna da y'ay'anta. Kuma da ki ke maganar rama alkhairi da sharri, ni nan idan naga kud'i babu abunda ba zan iya yi ba, ku ma kud'in da aka ba ni, zan iya gyara k'auyan nan kaf in mai da shi ginin zamani, to ya kike tunanin zan iya ganin wad'annan kud'an nan in rintse idanuwana. Ai ba zai yuwu ba". Fad'in Kandala. "Ki ji tsoron Allah, ki tuna ya na ganin duk abubuwan da ki ke aikatawa kuma da sannu za ki girbi abunda ki ke shukawa. Ki gaggawan fad'a min abunda zan maku don in bar garin nan gobe". Fad'in Binty. "Hehehehhh! Kwantar da hankalin ki, da ma kwana ukun za ku yi ku koma, saboda biyo kin da wancan sha-sha-shar ta yi, da ace ba ta biyo ki ba, da ko garin nan ba za mu zo ba, za mu yi abun mu cikin kwanciyar hankali, amma tunda ta biyo ki, dole mu yi hak'uri har sai kin koma. Sannan abu na gaba, mutane biyu ne za ku yi wannan sirrin ta re, sai dai d'aya ba za ta tab'a sanin d'aya ta na sirrin da ke ba. Ke! Wallahi ya kamata ma ma ki dode min don ke kowa k'aunar ki ya ke yi za ki zama ta gaban goshi". Fad'in Kandala ta re da washe hak'ora. Harara Binty ta watsa mata ta re da kau da kai ta na tunanin wannan wani irin sirri ne da za ta yi da wasu. Fatan ta dai Allah ya sa ba abunda zai cutar da Anna ba ne ko kuma ya cutar da wanda ba su ji ba ku ma ba su gani ba. "Ki ta shi ki je ka da y'ar uwar ta ki ta ji shurun ya yi yawa. Dama ni abunda na kira in fad'a miki kenan". Fad'in Kandala. Matar Buba da ke mak'ale a jikin taga ta yi saurin yin hanyar kewaye don gudun ka da Binty ko Kandala su fito su ganta a wajan su ga ne ta ji duka tattaunawar su. Binty ce ta fito ta re da wuce wa sasan Goggo Shatu. Buta ta d'auka kamar za ta zaga ta shige ba yi ta re da had'e kai da bango ta na wani irin kukan da ke fitowa tun daga k'asan zuciyarta. Ba ta tabbatar da lallai cewar *BA TA DA GATA* ba sai yau.yau da ace da iyayanta kusa da ita wa ya isa ya mata wannan abu. Gashi yanzu ta dalilinta ta na naiman jefa wanda ba su ji ba, ba su gani ba a halaka. Ta kusa minti talatin a bayin ka na ta fito. Allah ya so ma babu wanda ya yi k'ok'arin shiga bayin. Amma idanuwanta sun yi ja jawur alamar ta ci kuka ma'ishi. Ko da ta shiga d'akin Goggo Shatu, hankali tashe Fanan ta k'ariso wajanta ta na fad'in, "Sister mai ya faru? Wa ya saki kuka?". Ta fad'i hakane gaba d'aya hankalinta a matuk'ar tashe kamar za ta saki kukan itama. Goggo da ke goga goro a magogi ita ma ta zubo masu idanuwa ta na tambayar abunda ya sa mu Binty. Ita kuwa Binty ganin yadda Fanan d'in ta rud'e saboda ganin halin da ta me ciki, sai hakan ya k'ara zaburar da tashin hankalinta ta saki kukan mai sauti ta re da rungume Fanan d'in ta na fad'in, "Ku ka d'ai gare ni, idan har babu ku ba zan iya rayuwa ba. Wallahi ina matuk'ar k'aunar Anna da zuri'arta. Ba zan ba ri wani abu ya same ku ba, zan iya ba da lafiya da rai na wa ku. Ina son ku Fanan". Binty ta fad'a cikin wani irin rikitacciyar muryan kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Wani irin kuka Fanan ita ma ta saki ta re da k'ara ruk'unk'ume Binty ta ma kasa magana. Goggo Shatu kuwa wani irin jan d'uwawu ta yi ta re da rarrafe ta dafa bango ta mik'e ta rungumo Fanan da Binty ta re da fad'in, "Ku bar kuka y'ay'an nan dan Allah. Ke kuma Binty dole ne ki yi kuka saboda rashin iyaye ai babban abu ne. Mu kan mu run da Hashimu ya mutu katanga ya zube. Ga shi kin zo kin ga irin rayuwar da mu ke yi a cikin k'auye ke kuma ki na can cikin daula wajan mutanan kirki. Ai Kandala ta hwad'i min komai. Kwarankwatsi ni kai na zan so ganin wannan uwa ta ki mai karamci baiwar Allah". Goggo ta k'arishe maganar ta re da mai da kallonta izuwa ga Fanan da ke gunjin kuka. "Goggo ki ce ta dai na kuka dan Allah, wallahi ban son kukan ta. Na san Anna na can gabanta na fad'uwa". Fad'in Fanan. "Kin ji ko? Dan Allah ki bar kuka idan ba so kike kan yarinyar mutane ya yi ciwo ba". Fad'in Goggo ta re da kama hanna yansu ta zaunar da su a bakin gado. Da sauri ta saka bayan hannunta ta goge fuskan ta re da kallon Fanan ta ce, "Sister na bar kukan, dan Allah ka da ki bari kan ki ya yi ciwo kin ji?". Fad'in Fanan ta na k'are share fuskanta. "Na dai na, ke ma ki daina dan Allah". Fanan ta fad'a ta na had'iye kukan da ke tawo mata. "Yauwa y'an albarka ku bar kuka kun ji. Ke kuma Binty addu'a da biyayya shine kawai za ki yi wa marik'anki ki biya su ba kuka ba, kin ji?". Fad'in Goggo. Gyad'a kai Binty ta yi ta na mai had'iye sauran kukan da ke taho mata a duk sa'ar da ta tuna da maganar da Kandala ta yi mata ba cewar idan ba ta amince da sirrin nan ba to a bakin ran Anna da y'ay'anta. *ABUJA* ............."Anna ni fa zan je Saminakar nan in d'auko su Binty. Gidan ba bu dad'i ko kad'an wallahi. Ke kan ki Anna na san dauriya kawai ki ke yi amma ki na missing d'in su over and over". Fad'in Barrister Fu'ad. Wani wawan kallo Ya Bibi ya bi sa da shi ta re da fad'in, "Yanzu ma za ka iya hawa hanya ka je ka d'auko su". Sosa k'eya Barrister ya yi ta re da kallon Anna da ita kan ta gidan bai mata dad'i. "To ya za mu yi Fu'ad? Dole mu yi hak'uri tunda wajan y'an uwanta ta je, su ma su na da buk'atarta. Ai saura kwana hud'u su dawo". Fad'in Anna. "Ni babu abunda me b'atan rai kamar rashin network a garin. Ba dama ka kira ka ji wani hali su ke ciki". Fu'ad ya sake fad'i. Tsaki Julaibib ya ja ta re da d'aukar key d'in motar shi, dama abinci ya gama ci ta re da kallon Anna ya ce, "Sai na dawo Anna". Ya na gama fad'in haka ya fice daga parlourn. "Anna dan Allah ki bari na je na d'auko su". "Kai ta shi ka ban waje tun da ba ka da hankali". Anna ta fad'a ta re da hararar shi. "Na yi shuru to". Fu'ad ya fad'a ta re da gyara kwanciya a kan three sitter. ..............Yaune su ka cika kwana hud'u a Saminaka, kuma yau ne su ke shirin komawa Abuja. Kwana hud'un nan kawai Binty da yi bala'in ramewa saboda tunanin abunda Kandala ta fad'a mata. Mak'ota sai kawo tsaraba su ke su na basu dangin su kalwa, kub'ewa, kuka, barkono, da shambo har da su goruba da taura. Sai da su ka cika babban bako na kayan tsaraba. Goggo Shatu kuwa har da matsar kwalla ta re da musu alk'awarin in sha Allah za ta zo. Shatar mota Kandala ta yi masu har garin Abuja. Kasancewar fitar sassafe su ka yi, k'arfe hud'u a Abuja ta musu, kuma da ya ke mota ce golf mai kyau kuma driver ya san hannunsa. Gaban Binty fad'uwa ya ke yi sosai duk san da ta tino da maganar Kandala. A k'ofar tank'ameman gate d'in ya yi parking su ka fito. Kandala ta biya shi kud'in sa lokacin tuni har Fanan ta isa gate ta re da kwankwasa gate. "Who be that". Fad'in Oga Solomon. "It's me, open the gate". Fad'in Fanan a gajiye saboda zaman motar da su ka yi". Bud'e gate d'in ya yi ta re da washe hak'ora. "Welcome back madam". Fad'in Oga Soloman. "Welcome". Fanan ta fad'a a gajarce ta re da shiga ciki Binty na biye da ita a baya. "Ah'ahhh beauty, beauty. Welcome home". Solomon ya fad'a ya na washe ba ki. Murmushi kawai Binty ta masa ta re da wuce sa. Kandala kuwa sai k'ik'i k'ik'i ta ke da k'atuwar bakon hannunta. Tab'e baki ya yi ka na ya juya ya kalli Baban Haruna ta re fad'in "Helf that human carry her load". Tasowa Baban Haruna ya yi ta re da d'aukar jakar ya d'aura a ka ita kuma ta shige ta na hararar Solomon. Kasancewar akwai nisa tsakanin first gate da ainahin cika gida, Binty da Fanan kamar za su fad'i don gajiya. Barrister Fu'ad ne ya fito daga part d'in sa sanye da kaftan kasancewar yau juma'a ce kuma bai je aiki ba, yanzu ne ya ke son ya fitan. Idanuwansa ne ya sauka a kan Binty da ke tafiya da kyar kamar an tilasta mata tafiyar. "Bintyyyyyyyyyyy!". Barrister Fu'ad ya fad'a da k'arfi kuma cike da jin dad'i. Cikin sassarfa ya nufi wajansu ya na washe bakin jin dad'in dawowar ta su. Ita kuwa Binty sai ta k'ara shagwab'ewa ita alan dole ta gaji. "Wannan wani irin surprise ne mai dad'i haka? Gaskiya na ji dad'in dawowar ku. Dubi tantabarun gidan nan, su kan su dad'in dawowar ku su ke ji gasu nan sai oyoyo su ke maku". Fad'in Barr Fu'ad ya na nu na tantabarun da gaba d'ayan su su ka sauko k'asa gwanin sha'awa. "Yaya we miss you irin lodi-lodi d'in nan". Fad'in Binty. Fanan kuwa d'aura kanta ta yi a kafad'ar shi ta na fad'in, "Yaya garin akwai nisa, we're very tired". "Ai ni ma na fasa fita, muje ciki". Fad'in Barr Fu'ad ta re da rik'o hannunsu. Kandala kallon bayansu ta yi ta re da tab'e baki ta na harararsu. Ba bu kowa a parlour gaba d'ayansu sama su ka yi su na kwad'a kiran sunan Anna. Anna da ke zaune a parlour ta na tunanin autares d'inta ta jiyo muryansu. Cikin sauri ta mik'e ta re sa nufar k'ofar parlourn. Kicib'is su ka yi da juna, aikuwa gaba d'aya suka daka tsalle su ka d'are jikinta. Rungume su ta yi ita tana jin dad'in ganinsu. "Ya aka yi ku ka dawo yau? Ai na d'auka sai kun yi sati ka min ku dawo". Fad'in Anna. "Anna kewarku ce ta hana mu sukuni wallahi". Fad'in Binty. "To ku dawa ku ka dawo?" Fad'in Anna. "Mu da Baaba Kandala, ta na parlourn k'asa". Fanan ta fad'a. "To maza aje ayi wanka ayi sallah azo aci abinci". Fad'in Anna ita kuwa ta sauka zuwa wajan Kandala. Barr Fu'ad ku ma wani tsallan murna ya yi na jin dad'in dawowar sahibar shi. Su Binty kuwa bayan sun yi wanka sun yi sallah, ko bi ta kan abinci ba su yi ba su ka bi lafiyar gado don yin baccin gajiya. Ko da Anna ta sallami Kandala wacce ta yi da ita a kan ta kwana gobe ta juya amma ta yi ta kawo mata excuses akan akwai buk'atar komawarta yau. D'akin su Bintyn ta shiga ta tadda su su na ta sharar barcin gajiya. Ta da su ta yi ta re da fad'in, "Ku ta shi daga wannan barcin haka, haramun ne bacci bayan la'asar". Haka nan ba don sun so ba su ka tashi. Abincin ma zai ciwu musu ba sai after isha'i lokacin cin abincin dare Wanda su ne na k'arshan zuwa kan dinning d'in. Kallo d'aya yaya Bibi ya yi masu ta re da d'auke kan sa ya na mamakin yaushe su ka dawo amma ya basar don bai son raini. "Yaya Bibi ina yini?". Su ka had'a baki wajan fad'i. "Lafiya". Ya fad'a a tak'aice ta re da cigaba da cin abincinsa. As usual shi ya riga su ta shi ta re da goge bakinsa da tissue ya fita. Kai tsaye d'akin Suhail ya nufa. Key ya saka ya bud'e ta re da shiga ka na ya mai da k'ofar ya rufe. Har k'uryan d'akin ya shiga inda Suhail ya ke a k'ulle da kaca a k'afarsa har hannu. Key ya saka ya bud'e kwad'on ta re da kwance masa hannun ya kuma yage seletep d'in da ke bakinsa ka na ya ce, "Ka shirya yin magana ko mu cigaba a haka?". Fad'in Julaibib. Tsabar taurin kai irin na Suhail ya k'i magana. "So be it". Fad'in Julaibib ta re da fiddo burger a cikin aljihunsa ya mik'a masa. Cikin sauri ya karb'a ya cinye ya na hawaye. Mai da kwado ya yi ta re saka masa seletep d'in a baki ka na ya juya zai fita. Ni shi sosai Suhail ya soma yi alamar ya na son yin magana ta re da girgiza kansa. Dawowa baya Julaibib ya yi ta re da yage seletep d'in bakinsa ya ya na kallon shi. "Dan Allah ka yi hak'uri yaya Bibi, wallahi zan yi magana, zan fad'a". Fad'in Suhail. Duk'awa ya yi a gaban Suhail d'in ta re kallonsa alamar ina jinka. "Kusan kaf yaran da ake kawo wa daga k'auyan don su yi aiki a gidan nan, sai na yi amfani da su duk k'ank'antarsu. Akwai wata ma da har ta baya na ke amfani da ita, yarinyar da ke wajan Anna ma sau biyu ina yunk'urin keta mata haddi amma Allah bai ba ni nasara ba"... "What?". Julaibib ya fad'a a matuk'ar k'ausashe ta re da d'auke shi da wani magigicin mari sai da jini ya fito daga ramukan hancinsa. Ta ke ku ma ya ji d'au sautin sa ya dod'e na wucin gadi. "Fad'a min, ka yi mata wani abu ko baka yi ba? Na ce fad'a min ko in kashe ka a d'akin nan". Julaibib ya fad'a ya na haurin ko ina ya samu a jikinsa, har a gabansa da ke a kumbure saboda dukan da ya masa wancan lokacin. "Wallahi wallahi wallahi ban mata komai ba, na farko Fu'ad ya kawo mata d'auki, na biyi kum.....". Wani naushi da ya kai masa a ciki ne ya saka ya yi saurin shanye maganar da zai yi saboda azabar da yaji. Da gudu Alhaji Usman da ke kallon duk abunda ke faruwa daga d'akinsa na side d'in haijya Mansura, kasancewa a kowa ni part ya na da computer da ku ma CCTV a wajan, ya fito da gudu ya hajiya Mansura ma ta biyo bayansa kasancewar ta ga fitowarsa. D'akin Fu'ad d'in su ka nufo hajiya Mansura na biye da shi a baya, hankali ta she kasancewar d'akin tilon d'anta namiji wanda ta kuma kwallafa rai a Kansa. Shigansu d'akin ya yi dai-dai da lokacin da Julaibib ya saka k'afa ya take gaban Suhail d'in. A take kuwa ya numfashinsa ya tsaya cak, idanuwansa su ka kakkafe. Please manage za mu had'e gobe. 🌹 *59-60*🌹 ............."Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Julaibib mai yasa ba ka amfani da hankali idan za ka yi hukunci ne? Yan zu idan ya mutu fa? Ka san jagulewa zai yi ya dawo kan ka ko. Ka rik'a abu da natsuwa mana". Fad'in Alhaji Usman rai b'ace ta re da nufar in da Suhail d'in ya ke a kwance ba ya numfashi. Kuka Hajiya Mansura ke yi kamar za ta shid'e na ganin halin da tilon d'anta namiji ya ke ciki. "Ya mutu ko Alhaji? Wani irin mugunta da azaba ne haka? Ai ko kisan kai ya yi sai haka. Dubi irin yadda aka k'ulle shi da kaca sai kace k'asurgumin b'arawo". Hajiya Mansura ta fad'i ta na sharar hawaye. "Umarni na ke ba ka a matsayina na mahaifinka idan har na isa kuma ina da wannan matsayin. Ka duba d'an uwanka ka na shi taimakon gaggawa yanzu haka". Tsabar zuciya Julaibib ya shiga taune harshansa jikinsa na wani irin rawa kamar yana k'asar Moscow ba suwaita a jikinsa. "Ba ka ji abunda na ce ba ne Salis?". Alhaji Usman ya fad'a a tsawace ya na kallon cikin idanuwan Julaibib da su ka rine kamar gauta kuma still ya na taune harshansa. A hankali ya ta tawo har inda Suhail d'in ya ke a kwance ya duk'a ta re da d'aura d'an yatsansa biyu a wuyansa da kuma k'ofofin hancinsa. Ka na ya mik'e ya isa in da goron ruwa a kan center table ya bud'e ta re da tsiyayar ruwan ya dawo wajan Suhail d'in ta re da shafa masa ruwan cike da mugunta. A matuk'ar razane ya farfad'o ta re da wawwaro idanuwa ya na fad'in, "Na tuba, wallahi ba zan sakewa ko wacce yarinya fyad'e ba. Wallahi ita ma ban mata komai ba". Fad'in Suhail. "Wani magana ya ke yi haka? Wa ya yiwa fyad'en a cikin gidan nan?". Fad'in Hajiya Mansura a birkice. "Fito da mota mu kai shi asibiti, ba ka ganin yadda gaban shi ya kumbura". Fad'in Alhaji Usman ta re da k'ok'arin warware sark'an da ke jikinsa. Mik'a masa key d'in da ya kulle kacan Julaibib ya yi ta re da ficewa daga d'akin ya nufi side d'in Anna rai b'ace. Ganinsa kawai su ka yi a kansa. Ba su kad'ai ba hatta Anna sai da ta tsorata da yanayin sa. Barr Fu'ad kuwa wani k'undunbala ya yi kasancewar ya na kan kujera ne ya na facing su Binty da har yanzu su ke kan dinning duk da sun gama cin abinci su na baiwa Anna da Ya Fu'ad d'in labarin k'auye. Kau kau kau! Julaibib ya tsinke fuskan Binty da mari hagu da ya sa ta ji tsigar jikinta ya tashi ta re da jin wani shocking na bin jikinta saboda azabar marin da ya sauka akan kuncinta. "Ubbbban... Me yya kkai ki d'd'aakin Suhhaiil har ya nai mi rrraping d'inki?". Fad'in Julaibib cike da in'ina. Daga Anna har barrister waro idanuwa su ka yi ta re da fad'in, "Raping kuma?". Binty kuwa hanyar nai man wajan b'uya ta ke yi amma ba hanya don ya yi fankan-fankan a kan hanya. Jikinta sai b'ari ya ke yi ta ma kasa kuka sai fiki-fiki ta ke yi da idanuwa. Hannu ya k'ara d'agawa zai wanketa da mari ta saki wani gigitaccan k'ara don ta tabbatar wannan karan idan har ya samu fuskanta to babu shakka sai ta kurmance. Caraf Anna ta rik'e hannun ta re da tura shi gefe amma ko motsi bai yi ba, sai taunan harce ya ke yi da har ya soma jini. "Kar ka sake tab'a ta Julaibib. Wallahi ka sake tab'a y'ar nan sai ranka ya mummunar b'aci. Sakarai kawai wanda wanda bai iya controling fushin sa ba". Fad'in Anna, amma can k'asan zuciyarta dad'i ta ke ji saboda wani abu da ta hango a fuskan d'an na ta. Huci ya ke yi kamar za ki, can kuma ya juya ta re da ficewa daga d'akin kamar zai fashe. Hanyar gate ya nufa. Fitar shi ko minti d'aya bai yi ba, Alhaji Usman ya shigo ta re da fad'in, "Maza Fu'ad fito mu kai d'an Uwanka asibiti bai da lafiya, d'an uwanka ya masa mummunan illa". Fad'in Alhaji Usman. Saurin bin bayansa Fu'ad ya yi, Anna ma ta bi bayansu hankali ta she. Numfashin Suhail sai sama da k'asa ya ke yi kamar zai tafi gaba d'aya. Ya yin da Hajiya Mansura ke tsugunne ta tallabe da kansa ta na kuka sosai. Ita kan ta Anna ganin yadda gaban Suhail ya wani irin kumbura sai da ta na da baya ta dafe k'irji ta na salati da sallallami. Ciccib'arsa Fu'ad ya yi har wajan mota, Alhaji Usman ya shiga gidan gaba, Anna da Hajiya Mansura su ma su ka shiga. Kan Suhail na kan cinyar Anna sai fad'in, "Na shiga uku na lalace, wallahi mutuwa zan yi". Duk ya ce haka sai Hajiya Mansura ta tsananta kukanta. Anna ce ke shafa kansa ta re da tofa masa addu'a a kansa har su ka isa asibiti. *________________* Tun su Binty na tsammanin ganin su Anna nan kusa har bacci ya yi awon gaba da su cike da zullumin abunda ya faru, barin ma Binty da ke tunanin ta yaya ya Bibi ya san Suhail ya yi yunk'urin yi mata fyad'e. Fanan ma sai da ta mata wannan tambayar, kuma ba ta b'oye mata komai ba ta shaida mata komai da ya faru a wancan ranar. Ranar dai daddare Yousouf bai gane kanta ba, kuma ya yi da ita ta fad'a masa abunda ke damunta, amma sai ta ce masa ita babu abunda ke damunta kawai gajiyar tafiya ce. Haka ya hak'ura ya kyaleta. Da kumburarriyar fuska Binty ta tashi, sai dai still ba su ga Anna a gida ba hakane ya tabbatar masu da Anna a can ta kwana. Ko karyawa sun kasa yi, duk sun yi jugum-jugum a parlour su na jiran dawowar Anna ko ya Fu'ad. Murd'a handle d'in kofar aka yi za'a shigo. Gaba d'aya suka zubawa k'ofar idanuwa su na jiran ganin wa zai shigo. Wani irin mik'ewa su ka yi gaba d'ayansu cike da tsoro. Don Binty har wani zawo-zawo ta soma ji kamar zai zubo mata. "Zo nan". Julaibib ya fad'a ya na kallon Binty. Alamu ya nuna ba a gidan ya kwana ba. Domin kayan jiya ne a jikinsa. Jikin Binty na rawa ta taka ta isa gaban shi ta re da fad'in, "Yaya Bibi ina kwana?". Ta fad'i haka muryanta na rawa sosai. "Ki had'a min tea ki kawo min d'aki na yanzun nan". Ya fad'a ta re da juyawa ya fice. A tare su ka sauke ajiyar zuciya ita da Fanan. "Wallahi ki yi sauri, don dad'ewarki zai jawo maki wasu zafafan marukan da yafi na jiya dama gashi fuskan ta ki ba ta gama sacewa ba". Fad'in Fanan. Ba ta re da Binty ta ce komai ba, ta isa wajan dinning d'in ta re da tattaro duk wani natsuwarta ta soma had'a shayin. A kan wani kyakkyawan ture ta d'aura ka na ta kalli Fanan ta re da fad'in, "Sister dan Allah ki raka ni". Da gudu Fanan ta yi stairs, sai da ta kai na k'arshe ka na ta tsaya ta re da juyowa ta ce, "Wallahi idan kin ganni a lahira kai ni aka yi. Ke dai ki je tunda ke ya sa. Yanzu ina bin ki zan jawo wa kai na duka da sassafe ban karya ba ga shi Anna ba ta nan balle ta ceceni". Rausayar da kai Binty ta yi idanuwanta sun yi kwal-kwal ta re da nufar k'ofar. Ta kusa minti biyar a bakin k'ofar shi ka na ta saka hannu ta kwankwasa. Sai da ta yo knocking sau uku ba'a amsa ba. Har za ta aje farantin a k'ofar d'akin wani zuciyar ya gargad'eta. Murd'a handle d'in ta yi ta re da shiga ciki. Babu kowa a parlour. Wajan center table d'in shi ta nufa ta re da d'aura parantin. A nan ta ci karo da wani k'aramin paper da wani kyakkyawan gajeran rubutu. D'aukar papern ta yi ta soma karantawa cikin zuciya kamar haka, "Ki zauna ki jira ni har in fito". Gabanta ne ya buga dam ta re da fad'in, "Kashi na ya bushe billahil lazi". Jikinta na rawa ta d'an d'osana d'uwawunta a kan kujeran 1sitter sai rarraba idanuwa ta ke yi. Kusan mintuna sha biyar ka na ya fito sanye da sweatpant da rigarsa farare k'al-k'al. Gashin kan shi sai shinning ya ke yi. Ga kwantaccan sajansa da ke k'ara masa kyau. Agogon hannu ya ke k'ok'ari sakawa a hannunshi. Kallo d'aya ta yi masa ta re da saurin kau da kai gudun ka da ta yi laifi don ta ga alamar ya tsani kallo. Julaibib kuwa ya na kallonta ta gefen idanuwa ta re da tab'e bakinsa. Ba ta re da ya ce mata komai ba ya nai mi waje ya zauna a kan 2sitter ta re da jawo farantin kusa da shi ya d'au cup d'in ta re da kai shi ba ki ya yi sipping shayin. Saurin aje cup d'in ya yi ta re da kallonta da har hantar cikinta sai da ya katsa. Had'a wani wannan ya yi min sanyi". Yanda ya yi maganar kamar ba daga bakinsa ya fito ba. Jiki ba kwari Binty ta mik'e ta re da yin hanyar k'ofa. "Dawo wan". Ta tsinkayi muryansa a cikin kunnanta. A hankali ta dawo baya ta re da fad'in, "Ga ni yaya Bibi". "Na gan ki. Ina za ki je da ki ka yi hanyar k'ofa". Fad'in Julaibib. "Zan je part d'in mu ne in had'o maka wani tea d'in". Binty ta fad'a ta na kallon k'asa. "To ki je ga kitchen can ki had'o a can. Kuma ki min sauri". Fad'in Julaibib ta re da nu na mata hanyar kitchen d'in. Sum-sum ta nufi kitchen d'in. A tsanake ta had'a komai ka na ta dawo parlour ta aje masa a kan center table d'in da ke gabansa. "Zauna ki jira ni". Ya fad'a a tak'aice ta re da d'aukar cup d'in ya soma sipping ya na lumshe idanuwa. Zama ta yi kamar yadda ya buk'ata. Sai da ya gama shanye tea d'in ya aje cup ka na ya juyo ta re da fuskantarta. "Ina son ki bud'e bakinki ki fad'amin gaskiya. Domin gaskiyar ce za ta cece ki. Kin san dai daga ni sai ke a d'akin nan ko? To gwara ki fad'a min gaskiya". "Zan fad'a maka gaskiya duk abunda ka tambaye ni yaya Bibi". Fad'in Binty. "Good". Fad'in Julaibib ta re da k'ara gyara zama ya na fuskantarta. "Sau nawa ya tab'a amfani da ke?". Dam dam gabanta ya buga ta zuba masa idanuwa ba ta re da ta iya cewa komai ba. "Ba ki ji tambayar da na miki ba ne?". Fad'in Julaibib ta re da watso mata idanuwansa. "Yaya ban gane tambayar ka ba ne". Binty ta fad'a. "Ina nufin sau nawa Suhail ya kwanta dake a d'akinsa". Waro masa idanuwa ta yi har da su dafe k'irji sai da ta ba shi dariya amma ya gimtse don ba wasa ya kira ta ya mata ba. Shi ma waro mata idanuwan ya yi. "Wallahi wallahi wallahi ko sau d'aya bai tab'a ba. Ya dai tab'a yink'urin yi min fyad'e Allah ya tseratar da ni". Fad'in Binty ta na son fashewa da kuka. "Shshsss! Ba kuka na kira ki min ba, naji bai tab'a. Kuma ki bud'e kunnan ki da kyau, ka da ki kuskura ko a cikin mafarki na in gan ki da wani ko hannun ki ya rik'e , idan haka ta faru, karya ki zan yi. Don ni ba yayan banza ba ne da zan bar k'annai na su lallace a banza ba. Kin dai ji abunda na fad'a miki ko?". Fad'in Julaibib har da rik'e kunnansa. Cikin sauri ta gyad'a kanta ta na share hawayan da ya silalo mata daga idanuwanta. "Yauwa. Kuma maza yanzu ki je ku karya ke da Fanan, idan kuma ku ka k'i karyawa, ni zan zo na karya ku". Fad'in Julaibib ta re da mik'ewa ya nufi bedroom d'in sa. Binty na ganin haka, ta fice da sauri har da had'awa da gudu-gudu. Sai da ta ganta a bedroom d'in su, ka na ta sauke ajiyar zuciya. Kallo Fanan ta yi wacce ta lullub'e har kai ta re da fashewa da dariya ta kuma yaye bargon. "Ya aka yi, dukan ki ya yi ko?". Fad'in Fanan. "Eh. Ke ma ya ce ki je ki amshi na ki rabon". Fad'in Binty. "Dan Allah ki bar wasa ki fad'a min gaskiya". Fanan ta fad'a. "Gaskiyan kenan ya ce idan har ba mu karya ba, shi zai zo ya karya mu". Fad'in Binty. Wani wuntsilowa Fanan ta yi ta re da nufar k'ofa Binty ta mara mata baya. Su na cikin karyawarne Anna ta turo k'ofa ta shigo. Da gudu su ka nufe ta su ka rungume ta tare da fad'in, "Anna we miss you". "Ni ma haka. Yayan ku Suhail ne jikin sai dai Alhamdulillah, yanzu haka ma cuku-cikun fitar da shi k'asan baban ku ke yi". "Ayya Allah ya ba shi lafiya". Fad'in Fanan da Binty. Ta re su ka haura sama, Anna ta shiga d'akinta domin yin wanka ta kuma karya. K'asan ranta kuma ta k'udurta yin banza da Julaibib ta re da share sa saboda irin b'arnan da ya tafka. Don Suhail dai sai an kai shi India saboda mazantakarshi ta samu matsalar da ba zai tab'a iya mu'amala da mace ba har sai an masa aiki shi ma babu tabbacin zai warke ya dawo normal. ..........Bayan Kwana uku Hajiya Mansura da da Suhail har da Fu'ad wanda ya d'au excuse wajan aiki su ka lula India domin rashin lafiyar Suhail. Sai da Alhaji Usman da Fu'ad sun dawo bayan kwana biyar saboda aikin su ya yin da su ka bar Hajiya Mansura da babbar y'arta mace wacce ta zo daga baya. Anna kuwa Sam ta fita daga harkan Julaibib, ko gaisheta ya yi daga Lafiya babu abunda ta ke k'ara ce masa. Binty kuwa kasancewar Kandala ba ta sake mata magana ba akan sirrin da ta ce za su yi ita da wasu, sai hankalinta ya kwanta har ta tattara zancan ta watsar da shi. Wanda shurun da taji ya samu ne saboda tafiya jinya da Hajiya Mansura ta yi. Binty Kuwa kusan duk bayan kwana biyu sai sun had'a dabara ita da Fanan wacce ke taimakonta wajan had'uwa da sahibinta wato Yousouf wanda yanzu soyayyarsa da k'aunarsa ya wuce misali a zuciyarta. Yauwa kamar kullum sun had'u a wonderland su na shan soyayyarsu. Yousouf ya kalleta ta re da fad'in, "Mai sona, ni fa na gaji da wannan b'oye-b'oyen da muke yi. Dan Allah ki gabatar da ni a gidan ku muyi aure. Wallahi ba zan hanaki karatu ba". Fad'in Yousouf. Dogon ajiyar zuciya Binty ta sauke ta re da fad'in, "Reality". "Na'am mai sona". Yousouf ya amsa ya na kallon ta. "Akwai wata magana mai mahimmanci da na ke so muyi da kai wanda na dad's ina son yi maka amma ina jin tsoran rasa ka". Ta fad'i hakane idanuwanta na ciccikowa da hawaye. Tuni hankalin Yousouf ya ta shi sosai saboda ganin hawaye kwance cikin idanuwanta . Cikin sauri ya tashi ta re da zagayowa ya duk'a a gabanta ta re da fad'in, "Idan har akwai ranar da hawaye za su zubo daga idanuwanki idan ba na farin ciki ba ne kuma a gaba na, to zan yi fatan mutuwata ka min wannan ranar mai sona. Dan girman Allah ka da ki bari wannan hawayan su zubo a kan kyakkyawan fuskanki". Fad'in Yousouf in a cracking voice shi ma kamar zai yi kukan. Saurin mai da hawayan ta yi ta re da kallon shi ka na ta ce, "Reality za ka iya had'a zuri'a dani ko da ace ni d'in *BA NI DA GATA*? Ina nufin ban da uwa kuma ban da uba, babu dangi da zan yi tutiya ta re da nunawa duniya in ce wad'annna jini na ne". "Mai sona, wace irin magana ce wannan? Har ki na da shakku haka a kai na? wallahi Allah ka nan, ko da ace cutar HIV ki ke da ita, zan iya zama da ke a matsayin matata kuma inyi kowaccce irin mu'amala na aure da ke, idan na ce mu'amala ina nufin ko wacce. Ina fatan kin fahimce ni". Jijjiga Kai Binty ta yi ta na jin wutan k'aunar shi na ruruwa a zuciyarta. "Reality ni d'in nan da ka ke gani ba kowa ba ce face wacce ta ke cin arziki a gidansu Fanan. Babu wata alak'a tsakanina da su na jini sai tarin kyautatawa da soyayyar da ta haifar har na ke jin tamkar ni su d'in jini na ne. Ban san kowa nawa ba. Ta shi na yi na tsinci kai na a bola har Allah ya had'a ni da mutanan arzikin da su ka d'auke ni kamkar y'arsu ta cikinsu. Mai zan yi wa mutanan nan da su ka mai da ni yadda na ke yanzu". Binty ta k'arisa maganar ta re da k'ok'arin mai da kukan da ke taho mata. Ajiyar zuciya Yousouf ya sauke mai k'arfi ta re da fad'in, "Wannan shine abunda tashin hankali da har ki ke son yi min asarar hawayan ki? To ki sani, ni zan aure ki a duk yadda ki ke. Ko kin manta da alk'awarin da mu ka yi wa junan mu ne? Ba ki da matsala da ni da kuma y'an uwa na. Saboda haka ka da in k'ara ji kin ce *BA KI DA GATA*, Allah shi ne ga tan ki, kuma ni ne nan gatan ki". Fad'in Yousouf. "Nagode da k'aunar da ka ke nuna min a ko wani irin hali". "I love unconditionaly Binty". Fad'in Yousouf. "Same to me here". Binty ta fad'a ta na mai sakar masa murmushi. "Haba ko ke fa, ta shi in miki wak'a kin ji masoyiya". Fad'in Yousouf. Mik'ewa ta yi, shikuma ya bud'e wayar shi a key ka na ya shiga video ta re da soma d'aukarsu ta re ya na bin wak'ar kamar haka, 🎻 _*Duba ki ga yadda son ki yai mini, duk da na san ki na sa ne. Ki kalli cikin idanuwa naahh na san za su zayyane. Wannan al'ajab na so neee da k'auna, aiki na kiran ki ne. Dana fad'a kiji, ki ba ni agaji, in dai na rangajiii ki d'an yi tsokaci. Ki ba ni ma'ajih, ba zancan nagaji, ki kauda k'uduji, a so b yaaji. Labarin zuciyaaah, ni za ki tambaya, abinda nakkajiiii ya zarce duniyaaah. Idan na waiwaya, ko ko na sunkuya, amsar guda na ke ji kin zaman habibiya. Da sonki na banu, a kan ki na sanu, abunda baki so nai nai tai in bar shi na hanu, ke da sirri zai ganu, ki damk'am a hannu, shi zai fi min yau sauk'i in bar maganganu. Ki zo ki daf dani, so zai min lahani, ki tausayawa ruhina ki ce ki nai da niiii. Ba na ji ban gani, to wa zai kula da ni, I Dan ya zamma sab'aninki to a bar ni ni. Ina k'ulafuci, sai kin ci za ni ci, har wanda za na cin ki ci tun da ba bu rikkici. Ya za ai in burge wacce na ke so da k'auna, ya zaaa'ayi? Kalamai na sun kad'anta fahimce ni sannan ba hanyaaa. Kalamainaah sun kad'anta fahimce ni sannan baaa hanyaah. Ina so ta soni ni ba guru ba bu laya, babu d'age babu k'arya, ni bani san riyah. Ba dan kwalliya ba kuma ba dan dukiya ba, ba dan zantuka ba kullum tai min maraba. Ina son ki , ina son ki , ina sonki. Ina son ki so na gaske ba yaudara ba. Ina son ki, ina son ki, ina son kiiii. Ina son ki so na gaske ba yaudara baaaaah*_🎻 Ya k'arisa ina son ki so na gaske ba yaudara ba ta re da kashe wayan ya na kallon idanuwanta. "Ina son ka ni ma yousouf ba da yaudara ba". Fad'in Binty. "Naji dad'i sosai da na saki cikin nishad'i. Wannan videon shi ne zai zama abun kallo na through out yau idan na koma gida". "To ni ma ka tura min". Fad'in Binty. "Ina son ka, zamu kasance ta re har abada". Fad'in Binty. "Wannan maganar mai dad'i da ki ka min ma kawai ya ishe ni. Shiva xender in tura miki, ko kuma zan tura mi ki ta WhatsApp". Fad'in Yousouf. "OK to shikenan, raka ni gate, ka min sister ta fara jera min kiran da zai kashe min waya yanzu". Fad'in Binty. "You wish is my command my lady". Fad'in Yousouf ta re da yin gaba ta na biye da shi a baya. *________________* ............Abu kamar wasa, sai da su Suhail su ka washi wata tara a India ka min Suhail ya samu sauk'i cikin hukuncin ubangiji, kuma ya yi wa kan sa alk'awarin da Binty zai fara gwada lafiyar mazantakarsa. Ya yin da a gefe guda Hajiya Mansura ta yi bala'in rama saboda sawa zuciyarta soyayya da sha'awarta cikin zuciyarta ta re da k'osawa su dawo Nigeria domin nufar da k'udirinta. Yau dai su ka duro k'asar, Julaibib bai yi jinkiri ba, har d'akin uwarsa ya tadda sa ta re da shimfid'a masa concrete warning akan y'an aikin gida da kuma Binty wacce ya yi masa alk'awarin ko yatsarsa ya yi k'ok'arin kai wa jikinta, wannan karan mazantakar na shi gaba d'aya zai cire masa. Kuma a gaban Hajiya Mansura ya fad'i haka wanda ya kusa saka ta fitsari a tsayan da ta ke yi saboda hango wani b'oyayyan sirri a idanuwan Julaibib a game da Binty wacce ta d'auki d'amarar mai da ita abokiyar shaid'ancin ta. "Lallai akwai babban bala'in da ke tunkaro gidan nan soon akan duk wanda ke k'ok'arin shiga tsakani na da buri na". Fad'in Hajiya Mansura cikin zuciyarta. *BAYAN SATI GUDA* ............Wayar Binty ce ta yi k'ara alamar shigowar kira. Kallon screen d'in wayar ta yi. Gabanta ne ya buga da mugun k'arfi har sai da ta dafe k'irjin na ta ganin sunan Kandala b'aro-b'aro a jikin screen d'in. Hannunta na rawa ta d'aga wayar ta re da karawakarawa a kunnanta ba ta re da ta yi ko tari ba. "Yanzu nan ki je d'akin Hajiya Mansura, kuma ka da ki saki wani ya gan ki. Ina fatan kuma ba ki manta da sharud'd'an da na karanto miki ba idan ki ka sab'a?". Fad'in Kandala. "Ban man ta ba". Fad'in Binty ba ki na rawa. "Madallah. Sai ki hanzarta". Fad'in Kandala ta re da yanke wayar. *PAID BOOK 08128755583* *YAN ZU BA ZA KU RIK'A GANIN UPDATE DA SASSAFE BA SABODA AN KO MA SCHOOL KUMA NI D'IN TEACHER CE. DOLE SAI NA DAWO DAGA SCHOOL SANNA ZAN MA KU TYPING NAGODE* : 🌹 *61-62*🌹 💃🏻🔥🔥 _Ku na inahh nee?🗣️ to maza ku firfito ka da wannan garab'asar ta wuce ku. Shin ko kun san Mrs Abubakar ta k'ara zuwan maku da zuma gangariya mai jawo maki martaba da soyayya a wajan mijin ki?_ _Ta shi maza ki karb'o kud'in adashen ki da ki ke zubi wajan Ladidi domin ki siya ke ma ki zama sarauniya_💃🏻💃🏻💃🏻 _Gangarar gangariyar zuma mai k'ara kuzari da ni'ima ta re da k'ara miki sha'awa. Ta na sa ka wani dad'i da d'and'ano na musamman ta re da saka mai gida sambatu da zumar miyau 🙈 da gigicewa. Wannan zuma guarantee ne sai kin gwada na tabbata sai kin godewa Hassana (Mrs Abubakar). Haka kazalika ina macen da ke k'orafi akan miji bai kai mata? To kwantar da hankalin ki Mrs Abubakar ta kawo miki waraka da izinin Allah domin idan ki ka yi amfani da wannan zuma mijin ki zai jima bai yi inzali ba kuma ya na k'ara ruwan maniyyi da lafiya a jikin mai gida_ _Maza garzaya ki nai mi Mrs Abubakar a lambar wayarta kamar haka_ _+234 814 193 4442_ _Sayan nagari, mai da kud'i gida_🤸🏻‍♀️🤸🏻‍♀️💃🏻💃🏻🔥 ...............Gaba d'aya hankalin Binty ya gama tashi musamman da ta ji part d'in Hajiya Mansura za ta. Tunanin ta dunga yi wani sirri ne za su yi da Hajiyan da har za ta kafa mata wad'annan sharud'd'a haka. Da kyar ta iya jan k'afafuwanta ta sauko daga sama. Babu kowa a parlourn, hakan ya mata dad'i. Cikin sauri ta fita daga part d'in ta yi part d'in Hajiya Mansura ta na waige-waige. Murd'a handle d'in k'ofar ta yi gabanta na dukan tara-tara don ba ta san abunda za ta taras ba. Ba bu kowa a parlour, kai tsaye stairs d'in ta hau ta isa k'ofar d'akin Hajiya Mansura zuciyara na tsananta bugawa. Kwankwasawa ta yi, da ga ciki Hajiya Mansura ta ce ta shigo. Tura k'ofar ta yi ta re da shiga zuciyarta na bugawa. Tsaye ta sa mu Hajiya Mansura hannunta biyu goye a bayanta ta kuma zuba mata idanuwa. "Ina wuni Hajiya". Fad'in Binty bakinta na wani irin rawa. Wani malalacin murmushi Hajiya Mansura ta yi ta re da matsawa kusa da Binty ta kamo kafad'unta ta re da zaunar da ita a bakin gado ka na ta duk'a a gabanta ta na kallon tun daga kanta har k'afafunta ka na ta ce, "Binty ki kwantar da hankalin ki, ni ba cutar da ke ba zan yi ba. Na san Kandala ta riga da ta miki duk wani bayani so akan rashin bin umarni na, kuma wallahi har cikin zuciya idan har ki ka sab'a umarni na, zan kashe su kuma dole ki yi abunda na ke so don na san ke wacece. Ke ba komai ba ce face *MARA GATA* wacce uwarta ta yi cikinta ta yasar da ita a kan bola. Kin ga kenan b'atar da ke ba zai min wahala ba don na buga da wad'and'a su ke da *GA TA* ma kuma ni na ci riba. Don haka kawai ko ba da kai ki ceci rayuwar masoyanki na asali idan har za ki masu halacci". Ta k'arisa maganar ta na wani shu'umin murmushi. Jikin Binty har tsuma ya ke tsabar tsoratar da ta yi, hawaye har ya wanke idanunta, cikin kuka ta ce, "Dan Allah ki fad'amin abunda ki ke so min in miki. Dan Allah kar ki cutar da Anna ta". Mik'ewa Hajiya Mansura ta yi ta re da k'arisawa wajan k'ofa ta murza key ka na ta dawo inda Binty ta ke zaune ta cire hulan da ke kanta kasancewar doguwar riga ce mai hula a jikinta. Dogon gashin kanta ya zubo har bayanta. Hannu ta kai ta shafo wuyanta zuwa bakinta, ka na ta mata kiss a goshi. Mamaki ya kashe Binty da ke zaune zuciyarta na k'aryata abunda kwakwalwarta na hasaso mata. Doguwar rigar atampar da ke jikinta ta zame kasancewar ta zuge zip rigar sai ya fad'o k'asa ta kasance haihuwar uwarta don ko brezia da pant ba bu. A gigice Binty ta mik'e ta re da runtse idanunwanta ta na maimaita, "Inna lillahi wa inna ilaihir raju'un, Astagfurullah, Allahumma arji'ini fi musibati". Jikinta rawa ya ke yi sosai ta na mai dana sanin zuwan da ta. Dariya Hajiya Mansura ta fashe da ita ta re da kwanciya a kan gado ta yi pillow da hannayanta ta na kallon Binty da ke tsaye idanuwanta rufe kuma jikinta na wani irin rawa. "Hmmm! Yarinya ka da ki wasa da wuta za ta k'ona ki. Wannan shi ne abunda na ke so mu ruk'a yi ni da ke. Zan aure ki in kula da ke, zan mai da ke sarauniya. Ki amince da wannan harka za ki k'aru kuma za ki samu dukiya mai tarin yawa. Ba zan tab'a bari ko yatsa mace ko namiji su d'aga mi ki ba. Kar ki da mu, ko na aure ki, zan bar ki ki auri namiji don gudun zargin mutane, ni kai na abunda ya sa na yi auran kenan ba wai don namiji na gaba na ba, don namiji babu abunda zai iya min. Amma for now ba zan takuraki ki aminta dole ba, sai dai za'a fara zaman makoki a gidan nan, don tabbas sai na kashe su, kuma Na'ima ita ce first target d'ina, daga ita sai Fanan sai Fu'ad, wani ma na nan shigowa wanda mutuwarki shi ne ta ki". Hajiya Mansura ta k'arisa maganar ta re da wani shu'umin dariya da ihu-ihu. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Hajiya ki ji tsoran Allah. Wannan abu da ki ke so mu aikata ba k'aramin bala'i da masifa ba ne. Don darajar Allah ki yi hak'uri ki janye wannan maganar na miki alk'awarin rufa miki asiri babu wanda zai ji har gaban abada. Kuma ke ma ki tuba don ki na cikin bala'i da tsinuwar ubangiji kuma wallahi ki ka mutu a haka wuta za ki ba makawa". Fad'in Binty still idanuwanta a rufe don ba ta k'aunar sa ke arba da tsiraicin wacce ta isa ta haifi irinta guda biyar. "Ke! Ba wa'azi na kira ki min ba, idan wa'azi ne, wajan ki ka zo don ni mahaifina ma malami ne. Saboda haka wa'azin ki ba zai yi tasiri a nan ba. Kuma dole ki yarda ki aure ni mu rik'a biyawa junan mu buk'ata". Fad'in Hajiya Mansura a tsawace. "Wallahi ba zan yi wannan masifa da bala'i ba. Ba zan aikata wannan sab'on ba, kuma wallahi babu abunda ki ka isa ki yi wa Anna don mu na tare da ubangiji kuma zan kai k'aran ki wajan sa. Kuma na tabbata idan na amince da buk'atarki don in tseratar da Allah daga abunda ki ka shirya masu, wallahi Anna ba za ta tab'a yafe min ba don wannan ba tarbiyanta ba ne, no wonder d'an ki ya kasance kamar bunsuru, a she a nono ya tsotsa. Ina sha Allah ke da d'an ki ba za ku tab'a samun abunda ku ke so a waje na ba". Fad'in Binty ta re da nufar k'ofa. "Yarinya kenan, da k'afafuwarki za ki zo ki na rok'ona lokacin da lokaci ya riga ya k'ure miki don tabbas Anna sai ta bak'unci lahira". Cikin sauri Binty ta murd'a key d'in ta fice saboda lokacin da Hajiya Mansura ta kulle ba ta zare key d'in ba. Sai da ta goge hawayanta sosai ka na ta fito daga part d'in, amma duk da haka duk wanda ya ganta zai ga ne ta na cikin firgici. Ta shawo kwana su ka yi kicib'is da Julaibib shi kuma zai wuce part d'in sa don yin wanka zai fita an kira shi. Kallonta ya yi from head to toes, ita kuwa zuciyarta ce ta tsananta bugu har wanda ke kusa da ita ya na iya jiyo bugun zuciyarta. Hannunta ya damk'a ta re da nufar part d'in sa da ita ran shi a b'ace. Sai da ya bud'e k'ofar da d'aya hannunsa ka na ya tura ta ciki ya shigo ciki ka na ya mai da k'ofar ya rufe ta re da k'ura mata idanuwa ko kyaftawa ba ya yi. Ita kuwa kallo d'aya ta yi masa ta sunkuyar da kanta ta saboda yadda zuciyarta ke bugawa kuma ba za ta iya jurar kallon cikin idanuwansa ba. "Binty asara ki ke so ki min?". Fad'in Julaibib in a very cool voice ya na kuma kallonta. Saurin d'agowa Binty ta yi ta kalle sa ta na mamakin asarar mai kuma za ta masa. "Daga ina kike? D'akin Suhail ko?". Ya sa ke fad'i. Girgiza kai ta soma yi tuni har hawaye sun wanke mata idanuwa ta re da fad'in, "Wallahi yaya Bibi ban je d'akin shi ba. Ni tun da su ka dawo ma ban gan shi ba. Yaya mai zai kai ni d'akinsa kuma? Wallahi ba daga can na ke ba". Fad'in Binty ta na hawaye. "To daga ina kike? Kuma mai ya ke damun ki? Dole akwai abunda ya b'ata ran ki don naga mode d'in ki alamu ya nuna ki na cikin firgici. Kin san I study psychology, zan iya karantar ki tsaf". Fad'in Julaibib. Tsoro ne ya cika Binty, kuwa ba ta tunanin za ta iya fad'a masa abunda ke faruwa sam. Kallon sa ta yi for one second ka na ta ce, "Ina jin ba dad'i ne na rashin fara school d'in mu bayan Fanan ta samu admission amma ta k'i fara makaranta saboda ni ban samu ba. Kuma na yi da ita ta fara idan ya so next year ni kuma sai in fara in sha Allah amma ta k'i. Kuma gashi gaba d'aya y'an set d'in mu duk su na school". Kallonta ya ke yi har na kusan minti biyu ka na ya k'ara rage muryansa ta re da fad'in, "OK to ki kwantar da hankalin ki kin ji? Ban son ku na damuwa kin san ni doctor ne kuma damuwa na saka ciwo a zuciya, idan har na bar ki kina yawan tunanin Anna ba za ta ji dad'i ba za ta ce ni yayan banza ne, kuma kin ga dole in tashi tsaye in kula da ku ka da wani abu ya samu lafiyar ku, ko ba haka ba?". Sosai mamaki ya ka ma Binty, don ba ta tab'a tunanin yaya Bibi ya iya rarrashi haka ba, saboda ta san shi mutum mara son magana da hayaniya ga zuciya, kuma bai cika sake mata fuska ba. "Ko ba haka ba?". Julaibib ya sa ke fad'a. Murmushi ta yi ko in ce yak'e ta re da fad'in, "Hakane yaya Bibi". "Good girl, yanzu ki je d'aki ki kuma dai na tunanin komai. Da kin ji tunanin zai zo miki ki d'au Qur'ani ki karanta ko kuma ki yi alwala ki yi sallah kin ji". Fad'in Julaibib. Gyad'a kai Binty ta yi ta re da fad'in, "Nagode yaya Bibi". Ta fad'i hakane ta re da fita daga d'akin. Ya kai minti biyar ya na kallon k'ofar d'akin ka min ya saki ajiyar zuciya ya shige bedroom. "Ke ina ki ka je ina ta nai man ki? Anacin ki sai kira ya ke yi a waya kamar zai fasa wayan. Da ya katse wani kiran ya ke k'ara shigowa". Fad'in Fanan. "Kin san yanzu jiki sai ka na yi ka na motsa shi saboda kar in yi kib'a kamar *MATAR SAYYADEE*". Fad'in Binty. "To ai sai ki je ki kira d'an anacin na ki ya na can sai faman kira ya ke yi. Ni gajiya ma na yi ba bar d'akin". "Kar dai ki za ge shi wallahi". Fad'in Binty ta re da hayewa sama. Ko da ta shiga d'aki, kashe wayar ta yi gaba d'aya ta fad'a duniyar tunanin abubda ya faru. Can kuma ta d'auki shawarar da Ya Bibi ya ba ta shiga bayi ta re da d'auro alwala ta yi raka'a biyu ta re rok'on Allah ya tseratar da Anna da zuri'arta daga Hajiya Mansura. Kullum Binty cikin zullumin abunda Hajiya Mansura za ta yi was su Anna ta ke yi, har hakan sai da ya haifar mata da y'ar rama. Gashi ta saka numbern Kandala a blacklist saboda yawan damunta da kira da ta ke yi ta na k'ara tsoratar da ita. An kwashi sati d'aya, biyu har uku ba ta re da Binty ta ga wani yunk'uri daga hajiya Mansura ba. Sai hakan ya d'an kwantar da hankalinta har ta saki jiki ta cigaba da walwalarta saboda a tunaninta Hajiya Mansura ta tuba ta hak'ura. *_______________* Hankali ta she ta ke kallon screen d'in wayarsa har k'ara gwalo idanuwanta ta ke yi ta na kallon fuskan Binty da ta yi wani irin kyau. Riga da wando ne da ya fito da shape d'inta, sai hulan sanyin da ke kan ta, ana kuma ganin gashin kanta da ta ra ba shi gida biyu, d'aya ya zubo har k'an k'irjinta, d'aya kuma zube a bayanta hannunta d'auke da irin k'aton lollipop d'in nan ta saka shi a bakinta ta na tsotsa, sannan ga emoji na heart k'ato a d'an sama daga gefe. Gabanta haka ya ke bugawa fat-fat-fat saboda tsabar rikicewa da mugun kishi da kuma tashin hankali. Kallon shi ta ke yi hannun shi rik'e da ice-cream ya na tawowa in da ta ke a zaune. Idanuwanta sun kad'a sun yi jazur. "Yaya Bibi wacece wannan a wajan ka?". Fad'in Sabrin da ta ke ji kamar zuciyarta zai fasa k'irjinta ya fito don tsabar kishi. Aje ice cream d'in ya yi a kan d'an teburin gabansa ta re da karb'an wayar. Sai da ya sake kallon hoton ya yi murmushi ta re da saka wayar a aljihun gaban rigar shi ka na ya zauna ta re da fad'in, "Ga ice-cream nan sha mu tafi". "Ba zan sha sai ka fad'a min wacece wannan". Fad'in Sabrin hawaye na zubo mata daga idanuwanta. Wani irin kallo ya watsa mata ta re da fad'in, "Ki na hauka ne za ki tasa ni ki na min kuka kamar na miki wani abu? Ma ye ruwan ki da ita, menene damuwan ki da sanin alak'ana da ita?". "Saboda ina son ka ina k'aunar ka. Kuma ba na k'aunar ko wacce mace kusa da kai idan ba ni ba. Haba ya Bibi, za ka ce min ba ka fahinci irin son da na ke maka ba? Tun ina k'ank'anuwata lokaci da ma ceto rayuwata na ji duk duniya babu namijin da na ke son kasancewa ta re da shi idan ba kai ba. Kai ka d'ai na ke gani naji kwarin guiwar cigaba da rayuwa a doran k'asa. Dan Allah ka da ma bari wata ta kwace min kai. Wallahi na fita komai". Fad'in Sabrin cikin kuka ta re da ka mo hannun Julaibib. "Ki na hauka ne? Ni na tab'a cewa ina son ki ne? Duk wasu abubuwan da na ke mini da kulawan da na ke ba ki, aiki na na ke yi da kuma tausaya mi ki saboda irin lalurar da ki ke d'auke da shi. Amma ba na tuna nin akwai wata macen da na tab'a bawa lokaci na har na ke jure surutunki kuma na ke zuwa irin wajajan nan da ita idan ba ke ba har k'anwata da mu ke ciki d'aya da ita wanda na sa nta dad's ta na fatan haka. OK hakane ya ba ki damar yi min rashin kunya har ki ce ki na sona ko? To data yau Kim dai na ganin hak'ora na a wake balls har ki samu in fita da ke. Kuma yarinyar da ki ka gani a wallpaper na, ita na ke da burin aura, ban ga wata macen da ta fita ba a waje na. Kin ji ko ba ki ji ba?". Fad'in Julaibib. Wani irin gunjin kuka Sabrin ta saki ta re da d'aukar Jakarta da ke kan teburin ta yi hanyar da zai fitar da ita daga part d'in da gudu. Tsaki Julaibib ya yi ta re da mik'ewa, juyawar da zai yi idanuwansa su ka sauka a kan ta ta na wani irin dariya cikin nishad'i ita da wani saurayi da kuma y'an mata guda biyu. Gaban shi ne ya buga da k'arfi ya na tunanin mai ya kawo ta wajan nan a wannan lokacin su da ba fita su ke yi ba. A fusace ya mik'e dai-dai lokacin da su ma su ka mik'e su ka shiga wani waje. Da sauri ya bi bayansu, amma bai ga ko kyallinsu ba. Cizon yatsar shi ya yi k'udurta irin Fad'an da zai yi mata. Ya dad'e ya na dudduba si bai gan su ba, dag bisani ya fito ya yi wajan motarsa ta re da yi mata key. Kai tsaye gida ya nufa. Parking ya yi, kai tsaye ya nufi part d'in Anna ya na huci. Murd'a handle d'in ya yi ta re da shiga, da ita ya soma cin karo kunnanta mak'ale da earpies ta na miming wak'ar namenj ba ta ma san ya shigo don ta k'ure wak'ar. Fizge earpiece d'in ya yi ya tsittsinka. A furgice ta mik'e za ta gudi ya damk'o ta aiko ta ce, "Annaaahhh ki cece ni ya Bibi zai karya ni". Da gudu Anna ta fito saga kitchen Fanan a bayanta. "Da uban wa na gan ki a park? Shine don munafurci har kin dawo kin canza kaya ko. Za ki yi magana ko sai na ta ka maki kai". "Wallahi wallahi wani billahil azeem yau ko k'ofar nan ban je ba kuma ka tambayi Anna ka ji through out mu na ta re". *WASAN YA SO MA* _MATAR SAYYADEE_ 🌹 *63-64*🌹 💃🏻🔥🔥 _Ku na inahh nee?🗣️ to maza ku firfito ka da wannan garab'asar ta wuce ku. Shin ko kun san Mrs Abubakar ta k'ara zuwan maku da zuma gangariya mai jawo maki martaba da soyayya a wajan mijin ki?_ _Ta shi maza ki karb'o kud'in adashen ki da ki ke zubi wajan Ladidi domin ki siya ke ma ki zama sarauniya_💃🏻💃🏻💃🏻 _Gangararriyar gangariyar zuma mai k'ara kuzari da ni'ima ta re da k'ara miki sha'awa da kuma sa ka miki wani dad'i da d'and'ano na musamman ta re da saka mai gida sambatu da zubar miyau 🙈 da gigicewa. Wannan zuma guarantee ne sai kin gwada na tabbata sai kin godewa Hassana (Mrs Abubakar). Haka kazalika ina macen da ke k'orafi akan miji bai kai mata? To kwantar da hankalin ki Mrs Abubakar ta kawo miki waraka da izinin Allah domin idan ki ka yi amfani da wannan zuma mijin ki zai jima bai yi inzali ba kuma ya na k'ara ruwan maniyyi da lafiya a jikin mai gida_ _Maza garzaya ki nai mi Mrs Abubakar a lambar wayarta kamar haka_ _+234 814 193 4442_ _Sayan nagari, mai da kud'i gida_🤸🏻‍♀️🤸🏻‍♀️💃🏻💃🏻🔥 ..............Wani harara ya watsa mata ta re da mai da dubansa izuwa ga Anna ka na ya ce, "Kin san a ina naga yarinyar kuwa Anna? A park fa, ita da wasu k'awayanta guda biyu da wani saurayi wanda sam ni ban yarda da shi ba. Da ma kenan haka ake barin su sakaka su na fita su na had'uwa da kowani kare da doki? Sam ba zai yu ba wallahi". Fad'in Julaibib har ya soma in'ina. "To Mr Julaibib ka gama?". Fad'in Anna ta na kallon shi don tsaf tuni ta dad'e da harbo jirginsa akan Binty. "Anna ban gama ba fa, wallahi yaran nan su ka k'ara fita daga gidan nan, sai na b'alla k'afarsu". Fad'in Julaibib. "Amma wai ba ka ji abunda ta ce ba ne? Yaran nan ba bu in da su ka je yau wallahi. Kuma ko fita ne, idan har ba da driver ko Yayan su Fu'ad ba ban yar da su fita". Fad'in Anna. "To daga yau na hana. Duk in da za su je su fad'amin ni da kai na zan kai su, ban son abunda za'a zo a ce ni babban banza ne. Dole in kula da su in kuma kare mutuncin k'annai na". Fad'in Julaibib. Har Anna ta bud'e ba ki za ta ce da ya ke CANADA wa ke kula da su, sai kuma ta fasa ta re da fad'in, "To naji uban y'an zuciya". Sai da ya kalli Binty ta re da yin kwafa ka na ya fice daga d'akin. Ita kuwa Binty doguwar ajiyar zuciya ta saki ta na kuma tunanin shin wa ya gani mai kama da ita haka. Julaibib kuwa da ya isa d'akinsa mamaki ya ke tayaya haka har yarinya k'arama ta soma yi masa gizo. "Kai tabbas ita ce". Julaibib ya fad'a kamar wani zautacce. "Sai na binciki yarinyar nan. Ba zan iya jura ba wallahi". Ya sa ke maimaitawa ta re da d'aukar wayarshi ya shiga kallon hotonta da ke kan wallpapern shi. *___________* Tun da mahaifiyarta ta haifeta, ba ta tab'a tafiyan k'afa ba sai yau. Domin tun daga park d'in nan haka ta tako har Wuse II da k'afarta ta na tafiya ta na hawaye. Kai tsaye part d'in aunty Junaina ta nufa har bedroom d'in ta. Hanan da Amrah ido su ka bi ta da shi ta re da tab'e baki su ka mai da duban su ga Tv. Fad'awa jikin aunty Junaina ta yi ta re da fashewa da kuka har da shasshek'a. Sai da aunty Junaina ta tab'e baki ka na ta d'ago kafad'unta ta re da fad'in, "Sabrin lafiya? Wa ya tab'a min ke?". Fad'in aunty Junaina cike da damuwa. "Aunty na shiga uku, ta ki bari na. Duk in da na bi sai ta bini. Ta kwace min komai a *LEAD BRITISH*, har makarantar na hak'ura na bar mata. Yanzu kuma ta kwace min shi". Ta gama fad'in hakane ta re da rushewa da kuka. Shafa bayanta aunty Junaina ta yi ta re da fad'in, "Ban fahimce ki ba, yi min bayani domin in ga ne". "Aunty ya Bibi ya ce bai tab'a so na ba, wai tausayi na ya ke ji kuma wai ita zai aura ba ni ba". Sabrin ta fad'a kamar numfashinta zai fita. "Ban ga ne ba, wace yarinya ce wannan?". Fad'in aunty Junaina. Fiddo wayarta ta yi daga cikin Jakarta ta shiga gallery ta re da fiddo hoton Binty wanda ta tura a wayarta ta nu na wa aunty Junainan. Wani irin waro idanuwa aunty Junaina ta yi ta re da fad'in, "Wannan ai yarinyar da Zuwairah ta nu na min ce. Tabbas ita ce. Idan ko hakane zan jefi tsun-tsu biyu da dutsi d'aya yasin". Duk cikin zuciyarta ta yi maganar a fili kuma wani murmurshi ta yi ta re da fad'in, "Maza share hawayanki Sabrin. Wallahi wannan yarinyar ta bar ta da miki da hankali. Kawo kunnen ki kiji". Ba ta re da ta jira Sabrin d'in ta kawo kunne ba ita ta kai bakinta kunnan Sabrin d'in ta yi mata wasu maganganu. Cikin sauri Binty ta kalli aunty Junaina ta re da fad'in, "Really?". "I'm very sure my lovely daughter". Ta fad'i hakane ta re da ba shi hannu su ka tafa. ..............Fitowarshi kenan daga cikin asibitin ya nufi wajan motarshi hannunsa rik'e da fara k'al d'in rigar likitoci idanuwansa su ka sauka a kanta ta na yi wa wata mata magana hannunta rik'e da wani kyakkyawan yaron da ba zai wuce 8 years ba. Wannan saurayin da ya gan su ta re da shi a park shi ne ya bud'e ma su mota su ka shiga shi kuma ya zagaya ya shiga driver seat ya ta da mota. Cikin azama Julaibib ya shiga motar ta re da yi mata key, sai dai abun takaici a kwai wata mota da ta yi blocking d'in sa. Tsaki ya yi mai tsawo ka na ya bud'e murfin motar ya fito ya nufi motar da ya ga ta shiga. Sai dai kash tuni har sun fice daga asibitin. "Kaiiiiiiiiiii! Dam it". Shine abunda fad'a ta re da buga gaban wata motar da ke gefensa. Can kuma ya juya ya nufi cikin asibitin ya na balbale fad'a akan wanda ya yi blocking d'in sa. Cikin sauri mai motar ya fito ya na ta na shi hak'uri ta re da matsar da motarsa. Shiga motar ya yi ta re da nufar gida direct. Saboda gudun da ya ke yi, cikin mintuna k'alilan ya isa gida. Sai dai abunda ya ba shi mamaki, ya na parking Alhaji Usman na parking kuma ta re su ke da Binty, Fanan har da Anna. Sosai mamaki ya bayyana a kan fuskan shi ya na tunanin to wa ya gani a hospital. Hakanan ya had'iye duk abunda ya taho da shi ta re da isa wajan su ya gaida daddy da Anna ka na ya wuce side d'in sa cike da sak'e-sak'e. Binty kuwa tunda Anna ta hana su fita kamar yadda Julaibib d'in ya tsara sai ta shiga tashin hankalin rashin ganin masoyinta Yousouf. Daga baya ta tsiri fita ta na had'uwa da shi a can gaban layin su kad'an ba ta re da sanin ko Fanan ba. Oga Soloman dai kullum ya na ganin ta na fita, amma ba shi da damar magana tun da ba huruminsa ba ne. Yauwa kamar kullum Yousouf ya kira ta, ta fita. Bayan sun gama zancan su ta shafo hanya za ta dawo gida, daidai lokacin Julaibib ya danno hancin motarsa layin. Gaban shi ne ya buga saboda ganinta da ya yi ta na ta sauri domin zuwa gida. Parking ya yi ta re da fitowa, cikin sauri ya k'arasa wajanta ta re da fincikota ya wanka mata mari ka na ya nufi wajan mota da ita ya bud'e ta re da tura ta ciki shi ma ya zagaya ya Shiga. Babu abunda k'irjinta ya ke yi fa ce bugawa dam dam dam har su ka isa cikin gida. Ko parking mai kyai bai yi ba ya kamo hannunta ta re da yin part d'in Anna da ita. "Alhamdulillah Anna ga ta nan". Fad'in Barr Fu'ad da su ka ci nai man Binty ba su ganta ba, hankalin Anna ya yi mugun tashi. "Ina ki ka je Binty?". Fad'in Anna ta re da k'arisa wajanta. "Ba na fad'a mini yarinyar nan fita ta ke yi waje ba ta re da izini ba baki yarda ba. To can na ganta ta na ta zuba sauri za ta dawo gida". Gaban Anna da na Fu'ad a ta re su ka buga dam dam dam. Dai-dai lokacin Alhaji Usman ke saukowa daga stairs. "Binty ki ji tsoran Allah ki fad'a min gaskiya in da ki ke zuwa". Hawaye tuni sun soma wanke fuskan Binty jikinta sai rawa ya ke yi har da Fanan da ke gefe wacce tasan idan magana ta fito ta shiga uku don ta sha taimaka mata ta na fita su had'u da Yousouf su fa ke da zuwa saloon ko shopping. "Ba da ke ake magana". Julaibib ya fad'a da tsawa. "Kai ban san hauka. Ku yi mata a hankali. Zo nan y'ata ki fad'a min in da ki ke zuwa". Fad'in Alhaji Usman. Mik'ewa Binty ta yi kamar an tsoma jab'a a koko ta isa wajan Alhaji Usman ta re da tsugunawa. Zama ya yi a kan kujera ta re da fad'in, "Da wa ki ke had'uwa idan kin fita?". Bakinta na rawa ta ce, "Ka yi hak'uri daddy ba zan k'ara ba". "Waye shi?". Daddy ya sa ke fad'i. "Sunan sa Yousouf Muhammad Ahlam". Ta fad'a bakinta na rawa. "Yousouf Muhammad Ahlam". Julaibib ya maimata sunan. Yayin da Barr Fu'ad ya ji wani jiri na nai man kaisa k'asa ya yi saurin dafe bango. "Abun mai sauk'i ne ai. Ai mahaifinsa aminina ne ta re mu ka yi makaranta. Da shi d'in doctorn sarkin Adamawa ne wanda ya rasu. Ai gidan mutanan kirki ne. Da ma d'azu ai na ke maka magana a kan ku shirya kai da Fu'ad za mu je gaida wani d'an sa da ya dad'e bai da lafiya". Fad'in daddy ya na mai kallon Julaibib da idanuwansa su ka yi jazur. "Ke Binty ka da ki sake yin irin wannan kuskuran kin ji abunda na fad'a miki ko?". Gyad'a Kai ta yi ta re da fad'in, "Nagode daddy". Anna ko haushi ne ya kamata domin ko cikin mafarkinta ba ta tab'a kawo Binty za ta iya fita su had'u da wani a waje ba don ba tarbiyan da ta d'aura su akai ba kenan. Ba ta re da Julaibib ya ce komai ba ya fice daga d'akin haka ma Fu'ad. Binty kuwa da Fanan saurin hayewa sama su ka yi. Su na shiga d'aki Fanan ta turo k'ofa har da murza key ka na ta kalli Binty ta re da fad'in, "Ke ki na hauka ne Binty? Da ma fita ki ke yi ku na had'uwa da Yousouf duk da an hana mu fita? Mai yasa bakya jin magane Binty?". Fad'in Fanan. "Ki yi hak'uri Fanan, wallahi idan ya kira ni ne ban iya hak'uri har sai mun had'u tukun na ke samun salama. Wallahi ina matuk'ar k'aunar Yousouf". Fad'in Binty. "Na san ki na son shi sis, but d'an Allah ki rik'a controlling feelings d'in ki". Fad'in Fanan. "Ni wallahi tsoro na Anna, na san sai ta yi fushi da ni sosai". "Gaskiya kam wallahi. Don ba ki ga yadda ta yi da fuska ba". Fanan ta fad'a. Zama Binty ta yi ta re da zuba tagumi hannu bibbiyu. *AFTER ISHA* Gaba d'ayansu cikin shiga iri d'aya. Shadda ce gezna mai matuk'ar kyau da maik'o kalar sararin samaniya a jikinsu. Fu'ad ne ke tuk'i yayin da Julaibib ke gidan gaba Alhaji Usman kuma a gidan baya su ka nufi gidan Alhaji Muhammad Ahlam da ke Maitama. A gaban babban gate d'in gidan Barr da ke ji kamar zuciyarsa za ta buga ya danna horn. Cikin 'y'an seconni mai gadi ya wangale gate d'in gidan. Alhaji Muhammad Ahlam da kan shi ya zo ya ta re su cike da fara'a ta re da kai su parlourn bak'i. Nan da nan aka cika masu gabansu da abinci da kuma drinks. "Alhaji mu k'ara gaisawa, ina wuni ya harkoki da kuma iyalai?". Fad'in Alhaji Muhammad Ahlam. "Alhamdulillah, ya na k'ara harkokin da kuma mai jiki?". Fad'in Alhaji Usman. "To, sai dai mu ce alhamdulillah". Fad'in Alhaji Muhammad Ahlam a sanyaye. Ajiyar zuciya ya saki ta re da fad'in, "Allah ubangiji ya ba shi lafiya". Fad'in Alhaji Usman. Gaba d'aya daga Barrister har Julaibib su ka gaishe sa ta re da tambayansa ya mai jiki. Amsa masu ya yi da alhamdulillah ta re da fad'in, "Wannan shine babban d'an ka Julaibib ko? Shugaban gwagwaran Africa ko?". Alhaji Muhammad ya fad'i hakane ya na dariya. Shima Julaibib d'in murmushin yak'e ya yi don shi ka d'ai yasan mai ya ke ji a zuciyarsa. "Shi ne nan". Fad'in Alhaji Usman. Kallon shi Alhaji Muhammad Ahlam ya yi ta re da fad'in, "Kai Julaibib, ga mata nan da yawa a gari. Ka fiddo mata ko mu yi maka irin na da". Fad'in Alhaji Muhammad ya na dariya. Murmushin dai ya sake yi wanda bai kai ciki ba. "Mu je ciki ku ga jikin na shi ko". Fad'in Alhaji Muhammad Ahlam. "OK muje". Fad'in Alhaji Usman ta re da mik'ewa dukan su suka fito daga part d'in su ka yi cikin gida. Kusan gaba d'aya gidan ne a kan mara lafiyan wasu na kuka wasu na addu'a. Su kan su Julaibib, Fu'ad da Alhaji Usman sai da jikinsu ya yi matuk'ar sanyi. Ga mutun nan dai a kwance amma kamar gawa, abinci ta drip ake ba shi. Sosai su ka masa addu'a ka na su ka fito jiki a mace. D'akin bak'i su ka koma su na k'ara jajantawa Alhaji Muhammad Ahlam d'in. Alhaji Usman ne ya gyara zama ta re da fuskantar Alhaji Muhammad Ahlam ta re da fad'in, "Ni ko a cikin y'ay'an ka wanene yusouf?". Kallon shi Alhaji Muhammad Ahlam ya yi ci ke da mamaki ta re da fad'in, "Yawan y'ay'an har ya sa ba ka iya banbance su kenan? Ai Yousouf shi ne mara lafiyan da ke kwance. Yanzu haka watan shi biyar a kwance wanda a da k'ark'ari wata uku ya ke yi ya mik'e, amma wanna karan ya kai har wata biyar, ko lokacin ne ya yi". Fad'in Alhaji Muhammad Ahlam. Daga Alhaji Usman, Fu'ad da barrister gaba d'aya zaro idanuwa su ka yi su na kallon Alhaji Muhammad cike da mamaki. "To idan har Yousouf na kwance wata biyar bai motsi, wanene wanda Binty ke fita su na had'uwa?". Fad'in Julaibib a zuciya wanda Fu'ad shi ma tunanin da ya ke yi kenan. *_______________* "Hello ki na jina kuwa?". Da fad'in Yousouf. "Ina jin ka masoyi, na k'osa ka fad'amin wallahi". "Kin tuna min yi wa junan mu alk'awatrin zamu rayu da junan mu a kowani irin hali, kuma d'aya ba zai guji d'aya ba?". Fad'in Yousouf. "Kwari kuwa, kuma ba zan tab'a canzawa a kan haka ba". Fad'in Binty da ke juyi a kan gado ta na kallon zoben da ke hannunta da Yousouf ya sa ka mata. "Binty akwai abunda na dad's ina b'oye miki saboda gudun ka da ki gujemin". "Haba reality, mai ba ka guje min ba bayan ka san ni ba kowa ba ce, sai ni CE zan guje maka. Sam ba zan tab'a guje maka ba ko kai wanene". Fad'in Binty. "Kin tabbata mai sona?". Fad'in Yousouf. "Na tabbata masoyi". Fad'in Binty. "Mai sons ni da ke jinsun mu ba d'aya ba ne. Ma'ana ni aljani ne". Dariya Binty ta bushe da shi ta re da fad'in, "Yau kuma zolaya ka ke jin yi?". Fad'in Binty ta na dariya. "Ba ki yarda ba kenan? To ban minti d'aya". Ya na fad'in haka ya kashe wayar. Kallon screen d'in ta yi still ta na dariya. Wani irin zabura ta yi ta re da mik'ewa ta zaro damuwa sakamakon ganin Yousouf da ta yi a jikin bango zaune a kan kujera. "Binty kar ki tsorata, bayyana miki wanene ni ya zama dole saboda tone-tone da babanki na nan gidan da y'ay'ansa su ka yi. Binty na dad'e ina d'awainiya da ke tun ki na jaririya. Ke ce macen da na fara so....". Wani irin ihuu Binty ta yi ta re da zubewa a k'asa sumammiya. Dai dai lokacin Fanan ta turo k'ofar ta shigo........ *DAN DAN DAN! MUJE ZUWA* *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *65-66*🌹 .............."Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Binty, Binty, mai ya sa me ki?". Fad'in Fanan ta re da k'arasawa wajanta ta na jijjigata amma ko motsi ba ta yi. Da gudu Fanan d'in ta sauko k'asa ta na ihun kiran Anna da ke zuba Andrew liver salt a cikin cup saboda cikinta da ya lumbura sakamakon cin alale mai zafin da ta yi. A zubure Anna ke kallonta ta re da fad'in "Mai ya faru ke?". "Anna Binty ce.... Ta.. Ta mutu. Ta na kwance ko motsi ba ta yi". Fad'in Fanan jikinta na rawa. Da gudu-guda Anna ta yi sama ta re da tura d'akin su Binty da k'arfi saboda yadda ta rud'e ta yi wajan Bintyn da ke ya she a k'asa ba numfashi. Jijjigata ta soma yi ta na salati da kiran sunanta amma shuru. "Ban ruwa Fanan". Fad'in Anna ta na k'ara jijjiga Binty. Cikin sauri Fanan ta yi cikin toilet saboda rud'ewa ta d'ebo ruwan ta kawo mata. Hannu hannunta har rawa ya ke yi wajan karb'a ta d'iba ta shafa mata har sau uku a fuskanta, amma shuru ba ta farfad'o ba. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Fanan d'auko min wayata a parlour". Fad'in Anna. Da gudu Fanan da ke kuka ta fito ta d'auko wayar Anna ta re da dawowa d'akin ta mik'awa Anna wayar. "Kira min Julaibib ki saka a hands free". ************* "Ku ma ba ka da wani d'an mai suna Yousouf bayan mara lafiyan?". Fad'in Alhaji Usman. "Gaskiya ba bu, wanda ka ga ni dai a kwance shi ka d'ai ne d'ana mai suna Yousouf. Wani abun ne ya faru?". Fad'in Alhaji Muhammad Ahlam. "Lallai kam da kwai matsala, don wani me ke zuwa wajan y'ar waje na, kuma sunan da ya fad'a shine Yousouf Muhammad Ahlam". Fad'in Alhaji Usman. "To gaskiya k'arya ya ke yi ina ganin irin y'an yaudaran nan ne kawai. Ni d'ana ma a tarihin rayuwarsa sam bai tab'a budurwa kuma haka na da nasaba da lalurar shi don ya ce ba zai auri yarinyar da zai zama mata liability ba". fad'in Alhaji Muhammad Ahlam. Jikin Julaibin har ya soma tsuma ta re da rayawa a zuciyarsa irin mugun rashin mutuncin da zai yi wa wannan d'an iskan saurayin da ya ke k'arya da sunan wani ya na yaudarar Binty. Fu'ad kuwa ya yi wa kan sa alk'awarin ba zai cuci kan sa ba, su na komawa zai fallasa sirrin zuciyarsa a wajan Binty idan ya so a yi masu aure kawai kowa ya huta. Wayar Julaibib ce ta shiga ringing. Kasancewar ringing tone d'in da ya sawa Anna da ban ne shiyasa ya gane ita ke kiran wayar. Fiddota ya yi daga cikin aljihu ta re da picking ya daura a kunnansa. "Julaibib duk in da Ku ke ku dawo yanzu Binty ba ta numfashi". Mik'ewa ya yi da sauri ta re da fad'in, "Ga ni nan zuwa yanzu nan". "Mai ke faruwa?". Fad'in Alhaji Usman. "Anna ce ta kira Binty ba lafiya". Cikin sauri Fu'ad ya mik'e, Alhaji Muhammad kuwa cewa ya yi, "Subhanallah! Ku hanzarta ku je Ku ga halin da ta ke ciki". Tuni har Julaibib ya fice Fu'ad bi ye da shi. Shi ya zauna a driver seat ya yin da Fu'ad ke gefensa. Alhaji Usman Ku ma ya zauna a gidan baya. "Ka na hauka ne Julaibib? Ka dai na gudu da mu haka kamar za ka ta shi sama". Fad'in alhaji Usman. Shi kuwa Fu'ad tu ni wani abu ya darsu a zuciyarsa ga me da wan na shi. Hankalin sa ne ya ta shi saboda sawa kan shi wannan tunanin. Cikin mintuna k'alilan ya suka isa gida. Ko cikakakken parking bai yi ba ya fito da sauri ya nufi side d'in Anna. Sama ya hau har d'akin su Binty wanda shi ne karon shi na farko. Ta na nan kwance jikin Anna, Fanan kuwa sai kuka ta ke yi. Ciccib'arta ya yi ta re da kwantar da ita a kan gadonsu ka na ya shiga k'ok'arin ceto rayuwarta dai-dai lokacin Alhaji Usman ta re Fu'ad su ka danno kai. Ganin numfashinta ya k'i dawowa sai ya rik'e hancinta ta re da kai bakinsa kan nata ya shiga hura mata iskan bakin shi. Fu'ad saurin saukar da idanuwansa k'asa ya yi hawaye na tsiyayo masa daga idanunsa. Cikin second biyar ta ja wani irin dogon numfashi ta re da ware idanuwa. "Alhamdulillah!". Gaba d'aya d'akin su ka fad'i. "Wayyo Allah. Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, wallahi aljani ne, ya na d'akin nan. Yousouf ba mutum ba ne". Fad'in Binty a gigice cikin fitar hayyaci. Runguneta Julaibib ya yi tsam a jikinsa ya na mata addu'a cikin kunnanta. Cikin k'ank'anin lokaci kuwa bacci ya yi awon gaba da ita. Kwantar da ita ya yi a hankali ta re da ja mata bargo. Anna da Alhaji Usman na kallonsa, ya yin da Fu'ad ya bud'e k'ofa ya fice daga d'akin. "Anna I'matsala wallahi". Fad'in Julaibibi cikin harshan fulatanci. "Muje parlour ka da maganar mu ya ta she ta". Anna ta fad'a ita ma cikin harshan fillancin. Ta re su ka fita zuwa parlour dukan su. A nan su ka taras da Fu'ad zaune a kan kujera ya rik'e kanshi da hannu biyu. Bayan sun zauna ne Alhaji Usman ya kalli Anna ta re da fad'in, "Ummu Julaibib yarinya nan ina ganin gamo ta yi. Don magana ta gaskiya yaron da ta ke fita ta samu da ta ce mana sunansa Yousouf Muhammad Ahlam, ba haka ba ne. Shi ainahin yaron shi muka je gaishewa ya na nan kwance kamar gawa a gidansu tsawon wata biyar. Ku ma kun dai ji sambatun da ta ke yi lokacin da ta farfad'o". "Wannan shine ma babban damuwa ta". Fad'in Julaibib. Anna kuwa ta kasa magana sai jikinta da ke rawa. "Anna bazan jure ba sam wallahi". Julaibib ya sa ke fad'i. Kallon shi gaba d'ayansu su ka yi. Anna ta ce, "Kamar ya ke nan?". Sai a lokacin Julaibib ya dawo cikin natsuwarsa jin katob'arar da ya yi. "Ba bu komai". Ya fad'a ya na wani sunnar da kai k'asa kamar wanda ke gaban surukansa. Anna da alhaji Usman ba su san lokacin da dariya ta kubce ma su ba. Saurin mik'ewa Julaibib ya yi ta re da barin d'akin ya na sosa k'eya. *Washa gari* Anna ba ta samu cikakkan barci ba, bini-bini ta ke zuwa d'akin su Binty domin duba jikinta. Duk lokacin da ta je sai ta samu ta na sharar baccinta. Hakan ya sawa Anna baccin bayan sallar asubha. Gefen Julaibib kuwa kasa rintsawa ya yi, tunanuka ne ke masa yawo sosai a kwakwalwarsa ga me da Binty. Ita kuwa Binty, ko da ta farka wasai ta tashi, sai dai jikinta da ke d'an mata tsami-tsami. Hannu ta kai domin mai da gashin da ya zubo mata ya rufe fuskanta. Karaf idanwanta ya sauka a kan zoben da Yousouf ya saka mata wanda su ka yi wa juna alk'awari. Tsurawa zoben idanuwa ta yi ba ta re da kyafatawa ba, sai ta ga kamar fuskan Yousouf ta ke gani a jiki. Tuni komai na jiya ya dawo mata cikin kwakwalwarta. "Dagaske kai aljani ne masoyi?". Fad'in Binty ta na kallon zoben. Saurin b'oye hannun ta yi a bayanta gabanta na fad'uwa ganin zahiri fuskan Yousouf d'in ya fito a jikin zoben ya na d'aga mata kai. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!". Shi ne abunda ta fad'a ta re da dafe k'irjinta. Ta dad'e a haka ka min ta mik'e ta shiga bayi. Wanke fuska ta soma yi ka na ta kalli fuskanta a jikin madubin da ke jikin bayin. Waro idanuwa ta yi ta na son yin ihu amma ta kasa ganin Yousouf b'aro-b'aro a jikin mirror ya na kallonta. "Mai sona, ba haka mu ka tsara rayuwar mu ba. Kin manta alk'awarin da mu ka yi wa junan mu? Kin yi alk'awari za ki rayu da ni cikin ko wani irin hali, shin kin shirya karya alk'awarin ne?". Ya fad'a ya na mai fitowa daga cikin mirror d'in. Matsawa baya ta yi ta re da jingina da bango. Sai da ya zo daf da ita har su na jin numfashin juna ka na ya ce, "Mai Sona mun kasance ta re ni da ke tun ina k'arami ke kuma ki na jaririya. Da wannan hannun nawa na ke shayar da ke madaran shanu har ki ka rayu. Zafi, sanyi, ruwa ina ta re da ke ban tab'a ba ri wani abu ya cutar da ke ba. A duk lokacin da ki ka kwanta rashin lafiya ta re muke jin ya. Du bi baya na....". Ya fad'i hakane ta re da kware rigar da ke jikinsa ya juya bayan na shi domin ta ga ni. Wani irin zaro idanuwa ta yi sakamakon manya-manyan yanka na wuka har cikin jikinsa ta ko'ina a bayansa. Mai da rigarsa ya yi ta re da fuskantar ta ya ce, "Kullum wanna yanka da ki ke gani a jikina shine karin safe ne. Zuri'a sun kasance su na yak'i da bil'adama ne a sanadiyar wani tsautsayi da ku bil'adama Ku ka yi ya jawo rasa rayuwar kaka na na bakwai tun ya na jariri. Ni kuma ina karb'an wannan hukuncin ne saboda ke kasancewar na tsaya tsayin daka sai na taimake ni. Yanzu haka kaka na kurkukun Daulatun Bahashan ya na karb'an azaba daga sarkin hukuncin Daulatul Sira wato masarautar mu. Kaka shi babban amintaccan bawan sarkin da ya mulki Daulatul Sira tun daga zamanin sarauniya Oumul Quwaisi wacce ta yi mulki shekara dubu arba'in da hud'u da suka wuce. Yanzu haka sarauniyar da ke mulkar k'asar mu ta ba da umarni a kamo ni ko da rai ko ba rai duk a sanadiyar tsaya miki da na yi. Dan Allah Binty kar ko guje ni". Yousouf ya k'arisa maganar hawayan jini na zubo masa daga idanuwansa. *Wallahi tausayinku na Ji na d'an yi maku* 🌹 *67-68*🌹 .............Tausayin sa ne ya ka ma ta. Jikinta na rawa ta ce, "Mai ya sa kai min k'arya tun farko? Ku ma ta yaya ni da na ke bil'adama zan yi rayuwa da jinni? Ka duba ka gani kai ma". Fad'in Binty. Zuba mata idanuwa ya yi sai da ta tsorata saboda yadda idanuwan na sa su ka koma kamar jini tsabar ja. Ajiyar zuciya ya sauke ta re da fad'in, "Mai sona, abunda ya sa na b'oye miki ni wanene saboda gudun ka da ki guje ni ne. Ku ma zancan ke bil'adama ce ni kuma jinni ki aje a gefe. A wajan ubangiji duk d'aya muke. Kamar yadda aka halicce ku domin bautawa ubangiji, mu ma haka ne. Ba mu da banbanci a wajansa. Zan iya rayuwa da ke kamar yadda jinsin ki zai yi rayuwa da ke, fiye da su ma saboda bil'adama bai da amana, ya na wulak'anta mace da cin mutuncinta. Kar ki manta Binty, ba ki da kowa a cikin duniyar nan sai ni. Ko wad'annan mutanan da ki ke zama da su, ba su san komai a kan ki ba, kuma ka da ki cire tsammanin ranar da za su juya maki baya. Kowa na shi ya ke so a wannan zamanin da mu ke ciki. Binty ki min halacci, da yanzu ba ki cikin wannan duniyar amma na jure azaba da tashin hankali a kan ki. Na k'auracewa mahaifiyata da dangina da masarautar mu wanda a tarihi bai kamata tsatson amintaccan bawan sarki ya yi wa masarauta butulci ba. Ni nan saboda ke Binty na jawo wa masarautar mu wani gagarumin yak'in da ke tunkaraso su. A kwai wani dad'ad'd'iyar yarjejeniya tsakanin Masarautar Daulatul Bahashan da da Masarautarmu wato Daulatul Sira wanda Oumul Sahwat ke mulka. Masarautun nan biyu sun dad'e su na fad'a da juna tun shekaru dubu tamanin da shidda da su ka wuce. Yak'in ya soma ne sakamon jinnun Daulatul Sira da su ke shiga cikin bil'adama su na aiki da su, wanda hakan ya ja Masyush d'a ga Dahdaz wato sarkin Daulatul Bahashan kuma magaji tilon namiji kasancewar y'an uwansa matane ya nai mi d'an wajan Sarki Hawan kakan Oumul Sahwat da ke mulki a Daulatul Sira a yanzu da ya fitar da shi zuwa duniyar mutane kasancewar su an haramta masu shiga cikinsu. Cikin tsautsayi dawowar da ba su yi ba kenan saboda juye trailern siminti da wani attajiri ya sa aka yi a companyn shi, su kuma su na wajan kasancewar yara ne su a wannan lokacin don ba za su wuce shekaru saba'in ba. A kan su a ka juye wannan siminti wanda ya yi ajalinsu har lahira. Wannan abune ya jawo mummunan yak'i tsakanin Daulatul Sira da Daulatul Bahashan. Sai bayan hawan kakan Oumul Sahwat ne ya kira sulhu a bisa yarjejeniya akan Daulatul Sira ba za su k'ara shiga Bil'adama ba, kuma ko cikin mafarki ba za su shiga duniyarsu ba. Daulatul Sira ta amince da sharad'insu har ta sarkin wannan zamanin ya saka hannu da jinin jikinsa. Hakane ya samar da sulhu tsakanin masarautun biyu. Sai dai zuwanki cikin rayuwa ya k'ara d'ad'd'ago wani bargon bala'in fitinan da na ke gani babu makawa Daulatul Sira za ta shafe a tarihi saboda wacce ta ke mulkar Daulatul Bahashan Bak'ayatul maharuri ba k'aramin azzaluma ba ce, don bayan hawanta mulk'i sai da ta bibiyi tsatson wanda ya yi sanadiyar mutuwan kakanta na uku ta shiga jifansu da bala'i wanda yanzu haka d'an jikan tattab'a kunnan bawan Allah nan ya na halin matsanaicin ciwo yanzu haka, kuma shine wanda na yi k'arya da sunan shi, wato Yousouf Muhammad Ahlam. Saboda san kasancewa da ke shiyasa na ke ta yawo k'asa-k'asa ina gujewa hukuncin sarauniyar Daulatul Sira, duk da haka kullum sai na karb'i hukunci duka da takobi mai k'aifi a baya. Ke ce kwarin guiwata shiyasa na kasa nesa da duniyar nan. Dan Allah ki bi ni mu gudu zuwa wata duniyar da babu wanda zai takura mana. Ki Cuba halaccin kaka na a wajanki wanda ta re da shi muke ta jigila da ke". Sosai Binty ke kuka har da shasshek'ar tausayin Yousouf. "Yanzu duk a kai na ka yi wannan Yousouf? A kai na ka ke jure azaba haka? Mai zan yi in saka maka Yousouf? Ina ma zan iya abunda ka ke so na aikata". Fad'in Binty ta na kuka sosai. "Ki rayu da ni Binty, za ki iya, dan Allah". Sosai ta k'ura masa idanuwa ta re da fad'in, "Su waye iyaye na?". Girigiza kai ya yi ta re da fad'in, "Ni ma ban sa ni ba Binty". "A ina ku ka tsince ni? Ko ni ma aljanar ce kamar kai?". Fad'in Binty. "Binty ke mutun ce, labarin tsintar ki kuma, kaka ne kawai zai iya ba da shi, ni ban san komai ga me da haka ba". Fad'in Yousouf. "Ya za'a yi na ga kaka?". Binty ta fad'a. "Idan ki ka amince ki ka bi ni domin mu rayu mu zama d'aya, dole kaka da kan shi zai nai me mu, a lokacin za ki san labarin ki da na mahaifan ki". "Zan bi ka, amma ka ba ni lokaci tukun don shawara". Fad'in Binty. "Nagode mai sona. Na ba ki lokaci har sai kin nai me ni. Da gin buk'aci gani na ki murza zoben hanunki zan bayyana". Fad'in Yousouf ta re da juyawa ya koma cikin mirror, sai da ya mata bye-bye ka na ya b'ace. Dogon ajiyar zuciya ta sauke ta re da cire kaya ta sakarwa kanta ruwa ta yi wanka ka na ta fito daga bayin. Sai da ta shafa mai ta saka kaya ka na ta nufi d'akin Anna domin gaishe ta. Kwance ta sa me ta a kan darduma ta na bacci. Duk'awa ta yi ta re da sumbatar kumatun Anna ka na ta ce, "Anna ina son ki, ke uwa ce a gare ni wacce ban da kamarta. Nagode miki Anna, Allah ya saka miki da mafificin alkhairi". "Ameen d'iya ta, ni ma ina sonki". Fad'in Anna da ta tashi zaune ta na kallon fuskan Binty. "Ya jikin na ki?". Anna ta sa ke fad'i. "Naji sauk'i Anna". Fad'in Binty ta re da mai da dubanta izuwa ga k'afar Anna da ya yi wani irin fushi har kyalli ya ke yi kamar wacce maciji ya sara a k'afar. Zaro idanuwa binty ta yi ta re da fad'in, "Wayyo Allah Anna mai ya samu k'afarki?". Fad'in Binty ta na kai hannu zuwa k'afar Anna. Ita sam Anna ma ba ta lura da k'afar na ta ba ma sai Binty ta yi magana. Ita ma zaro idanuwa ta yi ta na kallon k'afar da ya yi wani irin kumbura don sai ka had'a k'afar Binty sau goma zai ba ka k'afar Anna d'aya. Kuma k'afa d'aya ce ta yi wannan kumburin. Sosai hankalin Anna ya ta shi, amma sai ta danne domin ta kwantarwa da Binty hankali ta re da fad'in, "Ke kar ki damu, ina ga kwanciyar k'asan da na yi ne ya jawo min kumburin amma zai sace in sha Allah. Yanzu sauka k'asa ki je ki karya maza". Rushewa da kuka Binty ta yi ta re da fad'in, "Anna wallahi ba ko da lafiya, kalli fa yadda k'afar ki ta yi". Ta fad'i hakane daidai lokacin da Barr da Julaibib su ka shigo d'akin. Turus dukansu su ka tsaya su na kallon Binty da ke duk'e ta na kuka. Saurin k'arasawa Julaibib ya yi ta re da fad'in, "Ke me......." Bai k'arasa ba sakamakon idanunsa da ya fad'a a kan k'afar Anna da ya yi suntum. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Anna mai ya faru?". Fad'in Julaibib. Fu'ad da ke tsaye, da bai yi niyyar k'arisawa ba ya yi sauri isa wajan, bai kai ga tambayar abunda ke faruwa ba ya yi arba da k'afar Anna. "Je ka kawo mota gaban part d'in nan right now". Fad'in Julaibib. Cikin saurin Barr Fu'ad ya mik'e ya fice. Ita kuwa Anna da ba ta ma san k'afar na ta a kumbure ya ke ba, amma da ta ankara sai k'afar ta soma mata wani irin azaba kamar ana kwankwatsa k'ashin k'afar da diga. Tu ni ta soma karanto duk addu'oin da ya zo bakinta. Kinkimarta Julaibib ya yi ta re da fitowa daga d'akin Binty bi ye a bayansa ta na kuka kamar ranta zai fita. Da gudu Fanan da ke had'a masu breakfast a kitchen ta fito. Ta na arba da k'afar Anna ta saki wani irin ihu ta re da fashewa da kuka ta rungume Binty su ka had'a kai su na kuka. Kwantar da ita flat a bayan motar Julaibib ya yi ta re da shiga gidan gaba, Barr Fu'ad ya ja motar da gudu. Binty da Fanan kuwa da gudu su ka yi wajan driver ta re da ce masa ya bi bayan motar ya Fu'ad d'in da su yanzu. A harabar wani babban asibiti su ka yi parking ta re da fiddo Anna, kasancewar Julaibib sananne ne kuma wanda su ka dad'e su na buk'atarshi a asibitinsu, cikin sauri su ka karb'i Anna su ka yi ICU da ita har da Julaibib kasancewar aikin k'ashi ya na d'aya daga cikin abunuwan da ya karanta. Sai dai abunda ya baiwa likitocin da ke kan Anna mamaki da matuk'ar tsoro shi ne duk sa'anda su ka tab'a k'afar Anna ko su ka yi mata allura, k'afar sai ta k'afa fushi ta re da kumbura. Hankalinsa ya kai k'ololuwa wajan tashi don ba su tab'a cin karo da makamancin haka ba a tsawon rayuwar aikin su. Sai uban zufa su ke yi. Ya kai yanzu duk wanda ya kalli k'afar Anna zai iya zubawa da gudu don tsabar firgici. Anna sai fizge-fizge ta ke yi ta na kuka. Duk dauriya irin na Julaibib sai da ya koka don ya San ba k'aramin ciwo ba ne ke saka zubar hawayan Anna. Daga k'arshe dai sai da aka fitar da Julaibib don nai man sumar masu da ya ke son yi. Kasancewar Fu'ad ya kira Alhaji Usman ya shaida masa komai, cikin k'ank'anin lokaci sai ga shi ya zo zufa babu in da bai keto masa don ya na matuk'ar k'aunar matar tasa. Abu kamar wasa sai da doctors su ka shafa awanni har takwas a kan Anna ka na ta d'an dai na jin rad'ad'in kuma sun ka sa gano abunda ya haddasa kumburin k'afar. Sun k'i barin kowa ya shiga ya gan ta ba yan Alhaji Usman. Shi kan sa fitowa ya yi ya na sharar hawaye don ganin halin da matar ta shi ta ke ciki. Ranar dai gaba d'aya wanna family su na cikin tashin hankali. Binty da Fanan kuwa da ke gefe ko ruwa ba su iya sakawa a baki ba saboda tashin hankali ga shi an k'i ba ri su ga Anna d'in. Da kyar daddy ya lallab'a su driver ya mai da su gida. Gaba d'ayansu yadda su ka ga rana haka su ka ga dare. Kuma ba bu wacce ta saka wani abu a bakin ta. Da sassafe su ka da driver ya mai da su asibiti wanda zuwansu ya k'ara masa wani tashi hankalin domin d'ayar k'afar Anna ya harbu ya ma fi d'ayan kumbura da kyalli kamar an shafa mai a jiki. Sannan ta zama wata kamar mutum mutumi kwana d'aya kacal kawai. Lokacin da aka bar su su ka tsaya ta wani wawakeken window mai d'auke da glass don ganin Anna kasancewar ba'a yadda wani ya shiga ba, sumewa Binty ta yi wanda sai da aka ba ta gado na tsawon sa'o'i uku ka na ta dawo hayyacinta ta na kuka kamar za ta mutu. Julaibib da kan shi ya shiga in da ta ke ya yi lallashin duniya amma tak'i yin shuru. Shi da kan shi duk da ya na cikin tashin hankali ya d'ibe su a mota ya mai da su gida ta re da buga masu concrete warning ka da ya k'ara ganin su a asibitin idan har ba da daddy su ka zo ba. Abu kamar wasa ciwon Anna sai dad'a gaba ya ke yi, don yanzu ba ta iya gane kowa. K'ok'arin fita da ita k'asar ma ake yi zuwa India. Zaune ta ke a d'akin su ta zuba uban tagumi, ta yi wani bala'in rama babu abunda ka ke hangowa a fuskanta sai karan hancinta. Idanuwanta duk sun zurma. Wayarta ce ta soma k'ara, kallon wayar ta yi ta ga bak'uwar number ce ke kiranta. Sai da ta kusa tsinkewa ka na ta d'aga ta re da karawa a kunne ta yi cikakkiyar sallama. Daga d'ayan b'angaran ba ta re da an amsa mata sallamar ba ta soma fad'in, "Ki na tunanin zan fad'i magana ce na kuma kasa cikawa? To kin yi kuskure y'an mata. Idanuwan ki dai sun gane miki yadda na yi da Annan ki, kuma ina mai tabbatar miki idan asibitin duniyar nan za'a zagaye baza'a tab'a samun maganin matsalarta ba. Ni da na saka mata cutar, ni kad'ai zan iya warware wa. Saboda haka zab'i na gare ki, Anna za ta iya warkewa amma da sharad'in amincewarki ki zamo matata mai d'auke min sha'awata, idan ba haka ba, nan da kwana biyu za'ayi kukan mutuwarta, daga nan kuma sai Fanan". K'it ta katse wayar. Hankali a matukar ta she har ta na mik'ewa ta re da zaman y'an bori a k'asa ta re da rarrafe ta fita daga d'akin ka na ta mik'e. Da gudu-gudu ta sauko daga stairs d'in ta fita daga part d'in ta nufi part d'in Hajiya Mansura. Caraf ta ji an cafki hannunta daga baya ta re da jan ta har garden d'in da ke gidan kasancewar bai fi taku goma ba daga in da su ke zuwa garden d'in. "Natsu ki kwantar da hankalinki. Na san duk abunda ke faruwa, kuma ni nan da ki ke ga ni na zo ne domin ceton ki ta re da tseratar da ke daga muguwar matan nan Mansura". Fad'in Hajiya Zuwairah da ke kallo Binty cikin zuciya ta na had'iyar miyau. "Na san duk wani sharrin da ta ke bin ki da shi, kuma na san abunda ta aikatawa Anna. Asiri ta mata mai matuk'ar k'arfi wanda zai iya salwantar da rayuwarta har abada. Idan ki na buk'ata zan iya taimakonki". Fad'in Hajiya Zuwairah. "Dan girman Allah ki taimake ni wallahi zan mutu idan har Anna ta wani abu ya sa me ta". Fad'in Binty ta na kuma ta re da rik'e hannun Zuwairah k'am. "Abu d'aya ne zai karya asirin da Mansura ta yi wa Anna, ba kuma wani abu ba ne fa ce barin ki cikin gidan nan". Fad'in Zuwairah ta na mai kallonta. A zabure ta mik'e ta na kallon ta re da fad'in, "Na shiga uku! Idan har na bar nan wallahi ban da wajan zuw...". Na ta k'arisa maganar ba saboda fad'owar da Yousouf ya yo mata a rai. "Kar ki da mu, ni ina da in da zan kai ki, sai dai za ki d'an zauna ne na wani lokaci ka min ki samu wajan zama. Tausayinki da maraicin ki na duba shiyasa na ke son taimakar ki wanda hakan ni ma zai iya jawo min babbar masifa idan ta gano ni ta taimake ki. Yanzu ki yanke, shin za ki bar gidan nan ki ceci Anna ko kuwa za ki cigaba da zama ki mai da Fanan marainiya kamar ki, sannan ita kan ta ki salwantar da rayuwarta da yayunta?". Ba ta re da wani dogon tunani ba Binty ta CE, "Na zab'i barin gida domin ceton rayuwar mahaifiyata, zan bi ki in zauna a ta re da ke na kwanaki bakwai ka min na tafi in da zani. Nagode ta taimakon ki a gare ni". Fad'in Binty ta na sharar hawaye. "Yauwa, wanna shine right time na guduwa saboda mazan gidan ba su nan, amma yanzu zan shiga wajan Mansura gudun zargi, ke kuma ki yi dabara ba ta re da wani ya gan ki ba ki shige motata ki kwanta a back seat, ba zan dad'e ba zan fito mu wuce". Fad'in Zuwairah. Gyad'a mata kai Binty ta yi ta re da yin hanyar part d'in Anna ta na mai jin tsananin kewar Anna da Fanan tun ka min ta bar gidan. Ta na tura k'ofar ta yi kicib'is da shi ya na tsaye a parlourn, cikin sauri ta nufe shi ta re da fad'in, "Yayanmu ya jikin Annar mu?". Ta fad'i hakane hawaye na zuba. "Ki kwantar da hankalinki kin ji? Anna za ta sa mu lafiya". Julaibib ya fad'a ta re da shafa kan ta ya na kallon fuskanta. Langab'ar da kan ta ta yi, tsautsayi ya sa d'an kunnna kunnanta ya ka ma hulan sanyin da ke kanta. Zame hukar ya yi ta re da cire d'an kunnan da ya mak'ale a hankali. Idanunsa ne ya sauka a k'eyarta, k'urawa wajan idanu ya yi har sai da ya kai hannu ya shafi wajan don tabbatarwa. "Mai ya faru yaya?". Fad'in Binty ita ma ta na shafa wajan. "Babu komai, ki je d'aki zan koma asibiti yanzu, anjima zan zo in kai ku. Ku kula da kan ku kun ji?". Gyad'a masa kai ta yi hawaye na zuba. Hannu ya sa ka ya share mata hawayan ta re da nuna mata stairs. Wajan ta nufa ta na tafiya ta na juyowa ta na kallon, duk san da ta juya tsaye ta ke ganinsa ya na kallonta har ta shige ka na ya fita. Fanan ta sa mu ta na saka masu kayan guga a cikin wardrobe. Ta baya ta rungume Fanan d'in ta re da fad'in, "Ina k'aunar ku Fanan irin wanda ba zan iya misaltawa ba". Juyowa Fanan d'in ta yi ta re da sakar mata murmushi ta re da fad'in, "Mu ma muna k'aunarki sister". Bayi Binty ta yi saurin shigewa ta turo k'ofar ta kunna panpo ta re da rushewa da kuka. Ta jima ta na kuka a bayin ka min ta fito. Ko da ta fito ba ta samu Fanan a d'akin ba. Saukowa k'asa ta yi, nan ma ba Fanan. Ta kitchen ta fita ta k'ofar baya cikin sauri-sauri ta re da nufar motar Hajiya Zuwairah ta yi saurin bud'ewa ta shiga gidan baya ta kwanta. "Da har na cire rai ba za ki zo ba saboda ganin wannan babban wan na ku ya fito ya bar gidan". Fad'in Hajiya Zuwairah da ta dad'e a cikin motar ta na jiran zuwan Bintyn. "Ki yi sauri mu bar gidan nan". Fad'in Binty. Ta da mota Hajiya Zuwairah ta yi ta re da reverse su ka nufi gate. Tafiya su ka yi ba tsawon mintuna sha biyar ka na Hajiya Zuwairan ta yi parking a bayan wata mota. "Jira ni ina zuwa". Fad'in hajiya Zuwairah ta re da fita daga motar ta nufi motar gabanta. Kwankwasa tinted glass d'in ta yi. Zuge glass d'in ta ciki ta yi. "Kin bar ni ina ta jira Zuwairah". Fad'in matar cikin motar. "Ke dai ba ri Junaina, da har na d'auka plan d'in mu ba zai yi aiki ba saboda dawowar babban d'an ta daga asibiti, cikin sa'a kuma bai dad'e ba ya fita. Yanzu haka ma muna ta re ita ta na mota". Fad'in Hajiya Zuwairah. "To ki je ki zo da ita". Fad'in Hajiya Zuwairah. Juyawa Hajiya Zuwairah ta yi ta re da komawa wajan motarta. "Yauwa fito Binty". Fad'in Hajiya Zuwairah. Fitowa Binty ta yi ta na kallon Hajiya Zuwairah ta na son k'arin bayani. "Yauwa kin ga ba dama in aje ki a gida na saboda Hajiya Mansura ta na yawan zuwa waje na, kuma idan ta gan ki wani bala'in ne zai biyo baya, shiyasa na yanke shawarar ki bi k'awata ki zauna ka min komai ya daidaita, ko y'an aikace-aikace kya tayata". Shuru Binty ta yi ra d'an wasu dak'ik'u ka min daga bi sa ni ta ce, "To shikenan zan zauna a wajanta d'in in dai hakan shi zai fitar da Anna daga halin da ta ke ciki. *A SHA WEEKEND LAFIYA🤪🤪🤪* 🌹 *69-70*🌹 ..............."Gaskiya ki na son Anna sosai, kuma kin kyauta don wannan shi ake kira halacci. Mu je ki shiga mota ku wuce". Fad'in Hajiya Zuwairah. Gaba Binty ta yi ta re da nufar motar Junaina hajiya Zuwairan na biye da ita a baya. "To Junaina ga ta nan, sai kin ji ni". Fad'in Zuwairah ta re da komawa wajan motarta. Ita kuma Binty zagayawa ta yi ta re da bud'e gidan gaba ta shiga ta re da gaida Junaina. Aunty Junaina ka sa amsawa ta yi saboda ganin tsananin kyawun Binty a fili ya zarce na hoto. Murmushi kawai ta yi ta re da tada motar. Sai da su ka isa bakin gate sannan Junaina ta kashe mota ta re da kallon Binty da ke hawayen kewan Fanan da Anna har da ya barrister tun San da su ka soma tafiya. "Yarinya ki na jina? Na amincewa Zuwairah za ki zauna da ni a cikin gidan nan bisa ga sharad'i guda biyu ne kawai. Na farko, mai gida na ba zai amince ki zauna da ni ba har sai dai idan matsayin y'ar aiki za ki shiga. Kar ki damu, aikin ba wani mai wahala ba ne, kula za ki rik'a yi da y'ar mijina ta re da yi mata biyyata da kuma gudun b'acin ranta. Sharad'i na biyu kuwa, sai nan gama zan fad'a miki, ina fatan kin fahimta". Shuru Binty ta yi ta na mai jin gudun hawaye a kan fuskanta. Jinjiga kai ta yi alamun ta aminci don duk a tunaninta yarinyar da za Junaina ta ce za ta kula da ita ba ta wuce three years ba. Ba ta re da ta k'ara magana ba ta tada mota ta re da yi wasa gate man horn. Cikin sauri ya wangale gate ita kuma ta tura hancin motar ciki ta re da nai man waje ta yi parking. Junaina ce ta fara fitowa ka na Binty ta fito. Kai tsaye part d'in Junaina su ka nufa ta na gaba Binty na biye da ita a baya wanda haka nan ta ji gabanta na fad'uwa. Murd'a handle d'in ta yi ta re da kutsa kai ciki sa'annan Binty ma ta biyo baya. Zaune ta ke a kan two sitter cikin riga da wato da tasha tocking gashin nan ya sha gyara ta kuma yi parking d'in sa a gefe, fuskanta ya sha glasses da ya kusa cinye rabin fuskanta ta re d'aura k'afa d'aya a kan d'aya ta na taunar cingam k'as-k'as-k'as. "Yauwa k'araso ciki, kin ga wacce za ki yi wa hidima nan, ki kuma tabbatar kin yi mata duk wani abunda ta ke buk'ata ban san jin k'orafinta". Fad'in aunty Junaina ta na mai nunawa Binty Sabrin d'in. Cire glasses d'in fuskanta ta yi ta re da huro cingam d'in bakinta ya yi kwai ka na ta fasa ta re da mik'ewa ta na kallon Binty da mamaki ya gama kasheta baki sake sakamakon ganin fuskan Sabrin. Sabrin d'in kuwa zagayeta ta soma yi ta re da k'are mata kallo ta na wani shu'umin murmushi ta re da hura mata cingam a fuska. Aunty Junaina dariya ta yi ta re da wucewa side d'inta da ke upstairs. "Wa ma ki ke da suna? Binty ki ke ko wa?". Fad'in Sabrin ta na dariya. Wani murmushi Binty ta yi mai k'ona zuciyar wanda aka yi wa gashi ya k'ara fito da tsantsan kyawunta ka na ta ce, "Lallai! Ashe na tsaya a ran ki haka? Gaskiya a gaishe ni domin tsayin shekaru kin ka sa manta ni, hakan na nufin ina d'aya daga cikin mutanan da ki ke tsoro su ke kuma sa ki fargaba". "Ki iya bakinki yarinya! Domin ki na cikin gidana ne, gidan ubana". Fad'in Sabrin a tsawace. "Haba? Sannu dodon kod'i wanda ko wani lokaci shi da gidansa ya ke yawo". Fad'in Binty. "Lallai ni na ke fad'e ki na fad'e a cikin gidan ubana? Sai na koya miki hankali, sai na b'ata wannan banzan fuskan da ki ke tak'ama da shi ta yadda ba za ki k'ara burge wani d'a namiji a raguwarki ba. Ba ki isa ki kwace duk wani abu da ya ke mallaki na ba. Julaibib nawa ne ni d'aya, babu wata mace da ta isa in yi takara da ita, kin tafka babban kuskure a rayuwarki na son duk wani abunda ya ke mallakin Sabrin". Fad'in Sabrin ta na nuna Binty da yatsa. "Ke ba ki kai matsayin da zan yi takara da abu d'aya da ke ba, hasali ke ce ki ke bakin ciki kasancewar na fiki komai. Ba ri ki ji in fad'a miki wani abu, tun lokacin da ki ka bar *LEAD BRITISH*, na manta da wata yarinya mai suna Sabrin, ni ba kya rai na saboda ban d'auke ki komai ba, ke ce na tsayawa anan". Fad'in Binty ta re da nuna mak'ogoranta. "Waye ubanki? Kin san ko ni wacece kuwa?". Fad'in Sabrin a fusace. "Ke wacece ki ke tambayata? To saurara ki ji, ke ba komai ba ce face d'igon maniyi, wacce a hankali ki ka koma gudan jini ki ka ko ma tsoka akai ma ki halitta sannan aka busa ma ki rai, kuma a karshe za ki mutu a binne ki a k'asa a barki daga ke sai halinki, aikin da ki ka shuka a duniya walau na khairi ko akasin haka, shi za girbe". Hannu Sabrin ta d'aga za ta wanke fuskanta da mari, caraf Binty ta rik'e hannun. Sabrin ta yi- ta yi ta kwace amma ta kasa sai da Binty ita da kanta saki hannun da izza ta ra da fad'in, "Kada ki k'ara tunanin kwatanta haka, za ki yi nadama don na san ba ki manta had'uwan mu na farko ba a mall d'in babanki". "Za ki yi nadamar abunda ki ka aikata, sai kin duk'a bisa k'afafuna ki na nai man gafarata, ni kuma wallahi ba zan yafe miki ba, sai na koya miki hankali, banza wacce ba'asan asalinta ba". Fad'in Sabrin ta re da hayewa sama ta na huci. Zama Binty ta yi a kan kujera ta re da rik'e kanta ta na jin sam ba za ta iya zaman gidan ba. Murd'a handle d'in k'ofar ta yi ta re da shiga ta yi banging k'ofar. Aunty Junaina da ke cire d'an kunne a gaban mirror ta yi saurin juyawa ta kalleta. "Kin saka na tura miki 10million a account d'in ba ta re da daddy ya sani ba, ki ka kuma k'ara buk'atar wa ni 5million na kuma d'aukar wayar daddy na miki transfer shi ma ba ta re da ya sani ba duk a dalilin alk'awarin da ki ka min na cewar za ki kawo min Binty har cikin gidan nan kuma sai ta duk'a min. Tabbas kin kawo ta ga ta can a k'asa, amma ba ta duk'a min ba sai maganganu da ta yi min masu zafi da k'ona zuciya, dama kin shirya hakane don zuciyata ta buga in mutu?". Fad'in Sabrin ta na nuna saitin zuciyarta. Kamo ta aunty Junaina ta yi ta re da zaunar da ita a bakin gado ka na ta ce, "Relax my daughter, tabbas yarinyar nan sai ta duk'a a gabanki, za ki juyata fiye da tunaninki. Sai dai ina so ki nutsu mu yi komai cikin natsuwa. Yau ta zo gidan nan, mun d'ana mata tarkon da dole ne ma ta duk'a miki, ke dai ba ni daga nan zuwa kwana uku". Fad'in aunty Junaina. Ajiyar zuciya Sabrin ta saki, ba ta re sa ta sake cewa komai ba ta d'auki wayarta da ke kan gadon ta fice daga d'akin. Ko da ta sauko k'asa, sai da ta watsawa Binty wani irin kallo wacce kan ta ke duk'e a k'asa ta ba sak'e-sak'e cikin zuciyarta. Kwata ta yi ta re da fita ta buga k'ofar wanda k'arar k'ofar ya firgita Binty da ta lula duniyar tunani. Binty ta kusa awa biyu a zaune ka na Amrah da Hanan su ka shigo wanda dawowansu kenan daga gidan kakarsu da ke suleja. Kallonta su ka yi ka na su ka juya su ka kalli juna. Tab'e baki Hanan ta yi ta re da shigewa side d'in su. Ya yin da Amrah ta ke kallonta ta re da fad'awa kogin tunanin maganganun kawar mummyn na su da su ke tattaunawa. Ajiyar zuciya Amrah ta yi ta re da bin bayan Hanan zuwa d'aki ba ta re da sun ce mata k'ala ba ita ma kuma ba ta masu magana ba don a ganinta su ya ka ma ta su yi mata sallama tunda su su ka shigo su ka same ta. ............"Sister wai ki na ina ne?". Fad'in Fanan da ke ta faman kwalawa Binty kira ta re da duba lungu da sak'o na part d'in na su. K'ofar bayi ta nufa ta re da kwankwasawa, nan ma shuru. Tura bayin ta yi, nan ma ta ga wayam. Fita ta yi daga part d'in ta nufi garden, nan ma ta duba sak'o da lungu ba ta ganta ba. "To ina ta ke? Ba dai ta sake fita sun don had'uwa da mayaudarin nan ba mai k'arya da sunan wani?". Fad'in Fanan cikin zuciyarta. Komawa part d'in su ta yi da gudu ta haura sama ta re da d'auko wayarta ta re da kiran numbern Bintyn amma sai ta ji wayar na k'ara a d'akin. D'auko wayar ta yi da ke k'ark'ashin pilo gabanta na fad'uwa. Wani gudun ta kwasa ta re da yowa k'asa. Kicib'isa su ka yi da Barr Fu'ad hannun shi d'auke da kaya, sai ya Bibi hannun shi rik'e da hannun Anna da ta warke sumul ga kuma Daddy a bayansu ya na murmushi. "Annaaaaaah!". Fad'in Fanan ta re da nufarta da gudu ta rungumeta ta na hawayan murnar ganin Anna ta warke. "Kin ga Annar ki kamar mai cutar jinnu ko, gobe fa muke shirin fita k'asar, cikin hukuncin ubangiji sai ga Anna sumul k'afa sun sace har ta na takawa da kafarta ko ina, shi ne fa ta kafa k'ahon zuwa dole sai an dawo gida kuma na san saboda ku ne, ta yi kewarku". Fad'in Daddy. Rungumeta Fanan ta kuma yi ta re da fad'in, "Anna munyi kuka kamar idon mu zai fita". Anna da ke murmushi ta ce, "To gani nan ai, kuka ya k'are naji sauk'i. Ina autata?". Sai a lokacin gaban Fanan ya buga ta shiga zare idanuwa ta na kallonsu. "Ta na ina?". Fad'in Julaibib tashin hankali bayyane a fuskan shi. "Yaya Bibi wallahi ni ma ban sani ba, tun d'azu na ke ta nai man ta har garden ban ganta ba. Kuma na kira wayarta na ji ta na ringing a d'aki". Fad'in Fanan. Da gudu Julaibib ya nufi upstairs ta re da bubbud'e ko ina amma wayam. Anna kuwa ji ta yi cikinta ya wani irin murd'awa yayin da Barr Fu'ad ya nufi wajen gida domin dubo ta. Daddy kuwa hankalinshi bai wani tashi ba don a tunanin shi Binty ba za ta b'ace ba ta na gidan sai dai idan wani wajan ta shiga. Abu kamar wasa har dare ba Binty ba labarinta. Julaibib ya yi wajan su Oga Solomon ta re da tambayansu ko Binty ta fita, amma su ka shaida masa cewar ko wajan first gate Binty ba ta je ba balle ta fita. Tun alhaji Usman na d'aukar abun da sauk'i har shi ma hankalinsa ya ta shi don shi ma ya soma tunanin ko Binty ta bi saurayin da ya yi mata karya da sunan Yousouf d'an gidan abokinsa. Anna da Fanan kuwa kuka kawai su ke yi. Ranar dai gaba d'ayansu babu wanda ya yi bacci don wani irin bincike a ka shiga yi har d'akin Suhail in da aka ci karo da manya-manyan kwalaye guda arba'in na cocaine da kuma ticket na zuwa k'asar hongkong guda hamsin. Hatta d'akin Hajiya Mansura bai tsira ba wajan bincike, don Julaibib haukace masu ya yi kamar zaki. 🌙🌙 .............Kuka Binty ke yi sosai tsugune a gaban Junaina da Hajiya Zuwairah ta re da fad'in, "Mai yasa za ku yi min haka? Ban cutar da ku ba ka da ku cutar da ni ba, don kun ga *BA NI DA GATA* shiyasa Ku ke gwara rayuwata kamar kwallo? Duk abunda Ku ke buk'ata da in yi maku abu d'aya kawai zan iya yin sa shine rayuwa a matsayin baiwar Sabrin har k'arshan rayuwata in dai har Anna ba za ta cutu ba. Ka da ku cutar da bayin Allahn nan don soyayyar da Allah ke wa manzon my SAW. Na rok'e ku". Fad'in Binty ta na kuka sosai ta re da had'e hannayanta biyu. "Mu dai kin ji abunda mu ka ce miki don abunda Mansura ta yi kad'an ne a kan Wanda mu za mu yi mata. Mun ba ki nan da wata d'aya ki yi shawara". Fad'in Hajiya Zuwairah ta re da mik'ewa ta kalli aunty Junaina ta re da fad'in, "Na yi nan, sai kin ji daga gare ni". Ta na gama fad'in haka ta fice daga parlourn. Aunty Junaina kallon Binty da ke durk'ushe ta yi ta re da fad'in, "Ki zagaya ta baya, ta na can wajan garden ki je ki tab'a k'afafuwanta ki nai mi gafararta". Ita ma ta na gama fad'in haka ta haye sama. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!'. Fad'in Binty ta re da mik'ewa ta nufi waje. Amrah da ke mak'ale jikin labule ta na hawaye ta fito da sauri ta yi d'akinta. "Besty ka ba ni shawara ya zan yi da wannan guy d'in dan Allah. Wallahi ina matuk'ar son shi sosai". Fad'in Sabrin da ke kallon Hamdan hannun shi rik'e da smoothie ya na sipping. "Hmm, ni dai idan da za ki ji shawarata, to ki fita harkan shi tun da ya nu na miki shi ba son ki ya ke ba". Fad'in Hamdan. "Ni ba zan iya rayuwa babu shi ba". Fad'in Sabrin ta re da marairaicewa. "Da ai da babu shi ki na rayuwan ki, saboda haka yanzu ma za ki iya rayuwar ki ko ba bu shi". Fad'in Hamdan. Sabrin ta bud'e baki za ta yi magana ta hangi Binty na zuwa. Wani murmushin jin dad'i ta yi saboda yanayin Bintyn ka d'ai ya isa ya fallasa abundan ta zo yi. Binty na k'arasowa wajan ta rik'e kafafun Sabrin ta na hawaye ta re da fad'in, "Ki min aikin gafara da yin sa'in sa da ke, kuskure ne da kuma sharrin shaid'an amma ko kusa ke ba tsara ta na ce. Kin min fintinkau a komai. Ke d'in cikakkiyar d'iya ce ni kuma ba komai ba ce face *MARA GATA* wacce ta ke ba ta da kowa sai bolan da ta ke rayuwa a kai. Ta yaya kamar ni zan had'a kai na da cikakkiyar d'iya kamar ki, don Allah ki wa Binty y'ar bola aikin gafara da yau za ta kasance a matsayin baiwarki har k'arshan rayuwarta". Wani irin mik'ewa Hamdan ya yi bakinsa na rawa ta re da fad'in, "Binty! Binty na. Bintyn Hamdan. Ki ce min ke ce dan Allah ba mafarki na ke ba Binty na k'arasowa wajan ta rik'e kafafun Sabrin ta na hawaye ta re da fad'in, "Ki min aikin gafara da yin sa'in sa da ke, kuskure ne da kuma sharrin shaid'an amma ko kusa ke ba tsara ta na ce. Kin min fintinkau a komai. Ke d'in cikakkiyar d'iya ce ni kuma ba komai ba ce face *MARA GATA* wacce ta ke ba ta da kowa sai bolan da ta ke rayuwa a kai. Ta yaya kamar ni zan had'a kai na da cikakkiyar d'iya kamar ki, don Allah ki wa Binty y'ar bola aikin gafara da yau za ta kasance a matsayin baiwarki har k'arshan rayuwarta". Wani irin mik'ewa Hamdan ya yi bakinsa na rawa ta re da fad'in, "Binty! Binty na. Bintyn Hamdan. Ki ce min ke ce dan Allah ba mafarki na ke ba, Beauty da ma zan k'ara ganinki?". Fad'in Hamdan ya na kallonta jikinsa na rawa hawaye na taruwa a idanuwansa. Sabrin kuwa ganin yadda Hamdan d'in ya wani rikice ya na kiran Binty haushi da takaici ya turnik'e. Juice d'in da ke cikin glass cup a gabanta ta d'auka ta re da watsawa Binty a fuska ka na ta saka k'afarta mai d'auke da dogon takalmi mai tsini ta tokareta a ciki sai da ta wuntsila. Binty saurin mik'ewa ta yi ta na kallon fuskan Hamdan hawaye na k'ara gudu a fuskanta ta na son kiran sunansa bakinta na rawa. ............Gidan Alhaji Usman kuwa, bincike ya yi bincike har Alhaji Usman da kan shi ya shiga d'akin sirrinsa shi da kuma Barr Fu'ad kasancewar Julaibib ya tafi wonderland don nai man Binty kasancewar Fanan ta fad'a masa a can su ke had'uwa da Yousouf idan ya kira ta. Alhaji Usman ne da kan shi ya kunna Computer kasancewar ya saka b'oyayyiyar cemara a ko wani sak'o na gidan shi don ganin hali da kuma abunda ma'aikata da kuma y'ay'an na sa ke yi a cikin gidan har da kuwa d'akunan matansa. Daga d'akin Barr Fu'ad ya soma bincikensa, bai ci karo da wani abu kaico ba, daga nan ya yi d'akin Julaibib, shi kuwa ba shi da aiki sai na kallon hoton Binty ya na wak'a sai kuma shan lemun tsami, daga nan ya yi d'akin Suhail, nan ne ya ci karo da abun assha wanda wasu daga ciki ya sani har kok'arin raping Binty da yi sai da su ka gani a nan ne kuma su ka gane daga d'akinsa ta fito ta na ihun k'onewar nan amma ba su ga wani alama da ke nu na ya na da hannu a b'acewar Binty ba. Daga nan part d'in y'an aikin aka shiga, nan aka yi katari da b'arayi irin su Fasila masu satar abinci. Wasila kuwa har muciya ta ke amfani da shi ta na yin masturbation cikin sauri alhaji Usman ya mayar sha-shin Huriya, ita kuma babu abunda ta ke yi sai kasuwanci da mugun sa aiki, don y'an aikinta ba su hutawa. Ko da ya koma shashin Hajiya Mansura, zuciyarsa ce ta kusa bugawa saboda ganin yadda ta ke lalata y'an aiki da mad'igo. Barr Fu'ad kuwa saurin rintse idanuwa ya yi. Forwarding alhaji Usman ya yi daidai wajan da hajiya Mansura ke threatening Binty akan ta amince da buk'atunta ko kuwa ta kashe su Anna da barrister. Zufa babu ta Inda baya tsattsafowa Alhaji Usman da Barrister Fu'ad. Cemaran waje ya kunna, a nan ne kuma ya ga lokacin hajiya Zuwairah ta ja Binty zuwa garden ta yi mata wad'annan maganganun da kuma lokacin da Binty ta shiga motar hajiya Zuwairah su ka fice daga gidan. ............Waige-waige kawai ya ke yi a cikin wonderland d'in nan ko Allah zai sa ya gan ta amma ko kyallinta bai ga ni ba. Dafe kan shi ya yi ya na jin wani tuk'uk'in bak'in ciki a ransa. Gitta shi ta re da tattaro gashin kanta ta na k'ok'arin nad'e shi ta kuma d'aure da ribom, saurin d'agowa ya yi ya ta re da kallon bayanta. Gaban shi ne ya buga da k'arfi ta re da waro idanuwa sakamakon tambarin d'awisun da ya gani a k'eyarta jiya. Kamar an kafashi a wajan haka ya tsaya ya na kallonta ta na yi wa wannan saurayin dai da ya na gan su rannar a nan wonderland d'in da kuma harabar asibiti. Ganin za su yi mass nisa ya yi saurin bin bayansu. *GA SHI NAN NA CIKA MA KU ALK'AWARIN KU, MU HAD'E MONDAY 🌹 *71-72*🌹 ..............Cikin rashin sa'a wannan karan ma sun b'acewa ganinsa. Hannunsa ya buga a jikin bango sai da hannu ya karce ta re da soma zuban jini saboda. Wayarshi da ke aljihu ne ta yi k'ara, ko damuwa da ya fiddo wayan cikin aljihunsa bai yi ba ya cigaba da zaga cikin park d'in ko Allah zai sa ya ganta. An kira wayar ya kusa sau goma ba ta re da ya fiddo wayar daga aljihu ya ga mai kiran ba. Sai da ya gaji da zagayan ka na ya nai mi wani waje ya zauna ta re da duk'ar da kan shi ya na kallon ciyawar da ke kwance a wajan idanunsa sun yi jazurr. Wayarce ta k'ara yin k'ara, wannan karan ya fiddo wayar daga aljihun. Kasancewar bak'uwar number ce, kamar ba zai d'aga ba, sai wata zuciyar ta ba shi shawarar da ya d'aga. D'agawa ya yi ta re da karawa a kunnansa ba ta re da ya ce komai ba. "Assalamu alaikum, dan Allah ina magana da doctorn da ke duba Sabrin ne, doctor Julaibib?". A dak'ile ya amsa ya bata amsa da, "Eh shine menene?". "Yarinyar da Ku ke nai ma ta na gidan mu, ina nufin Binty". Wani irin mik'ewa Julaibib ya yi ta re da fad'in, "Wacece ke? Ina ne gidan na Ku? A wani unguwa ki ke?". Duk ya koro mata tambayoyi. "Ni y'ar uwar Sabrin ce da ka ke dubawa a Canada. Wallahi Binty na gidan mu yanzu haka". "Alhamdulillah". Fad'in Julaibib ta re da yanke wayar daidai lokacin da kiran Barr Fu'ad ya shigo wayarsa. D'aga kiran ya yi bai jira Barr ya ce wani abu, shi ya riga shi magana, "Maza-maza ka fito ka same ni a wajan spicy d'in nan, na gano in da Binty ta ke". Julaibib na gama fad'in haka ya yanke wayar. Barr Fu'ad kallon daddy da idanuwansa su ka kad'a saboda abubuwan da ya yi katari da su ya yi ta re da fad'in, "Yaya Bibi ya ce ya gano in da Binty ta ke ya ce in sa me shi a Spicy yanzu". "Je ka, ni kuma yanzu zan kira commissioner of police a turo min da mota uku na police". Fad'in Alhaji Usman. "Shikenan daddy, ba ri na yi maza na je mu had'u da ya Bibi". Fad'in Fu'ad. Gyad'a masa kai ya yi ta re da danna number commissioner a wayansa. .............Sosai bakinta ke rawa ta re da fad'in, "Hadan, kai ne? Kai na ke gani yau da idanuwata?". Wani haske ta ga ni ya gilma ta idanunta. A ta ke ta ji ta dai na gani na wucin gadi saboda yadda zafin marin ya shigeta. Glass cup d'in da ta watsa mata juice a fuska ta dauka ta re da ratsa mata a goshi nan da nan kuwa jini ya b'alle. A gigice Hamdan ya yi kan ta ya na duba mata goshinta da ta saka hannu ta dafe ya na kuma zubda jini. Wani irin juyawa Hamdan d'in ya yi ta re da d'auke fuskan Sabrin da mari hagu da dama ka na ya yi ball da ita sai da ta wuntsila baya. Ba ta gama dawowa cikin hayyacinta ba ya kuma kai mata wani marin a tsakiyar fuskanta wanda sai da ta saki wani ihu ta re da rarrafe saboda gigicewa. Binty kuwa tuni ta manta da jinin da ke zuba a fuskanta ta shiga tsakiyan su da sauri ta re da duk'awa ta na fad'in, "Don rahamar ubangiji ka da ka k'ara kai hannu jikinta in dai don ni ka ke yi hakan. Yau ni na shiga uku ni Binty, daga wannan sai wancan. Yaushe zan samu salama da natsuwa ne ni kam? Ka san irin bala'in da za ka jawo min sanadiyar dukanta da ka yi? Ka san asarar da za ka jawo min kuwa? Idan wani abu ya samu Anna ba zan tab'a yafe maka ba wallahi". "Bintyyy!". Da wani irin sauri ta juya sakamakon muryan Fu'ad da ta ji ya daki dodon kunnanta. Wani irin zaro idanuwa ta yi gabanta na wani irin bugawa saboda arba da ta yi da Ya Bibi da Ya Fu'ad su na dumfaro so. "Me ki ke yi ana? Mai ya kawo ki gidan nan?". Fad'in Barr Fu'ad. Julaibib kuwa ya na zuwa hannunta ya fizgo ta re da wanke fuskanta da mari kasancewar a hanyar su ta zuba barrister ya shaida masa da komai da su ka ga ni a CCTV camera "Ki na hauka ne? Mai ya sa ba ki fad'amin ko Anna ko Fu'ad abunda ke faruwa ba? Da yanzu wani abu ya sa me ki fa ya ki ke so in yi? Kar ko da wasa ki sake gangancin maimaita wannan kuskuren Binty. Kuma wallahi Allah kenan, duk Wanda ke da hannu a cikin wannan abu ko waye shi ba zan bar shi ba. Ta ho mu wuce gida kuma ki sai kin fad'amin abunda ki ke zuwa yi ke da wannan d'an iskan yaron da na ke ganin ku da shi a wonderland da wasu wajajan". Fad'in Julaibib. Ka min Binty ta yi magana, wani guguwa mai bala'in k'arfi ya ta so ya lullub'e su har ba sa ina ganin na kusa da su. Guguwan nan ta kusa minti biyar ta na ta shi ka min daga bisani ta tsaya cak ta re da yin rimi a sama ka na ta b'ace b'at ta re da su gaba d'aya.... ............Cikin abunda bai fi awa guda ba motocin police guda uku su ka iso gidan Alhaji Usman. Kai tsaye d'akin Suhail ya fara yi da su ta re da nu na masu cocaine da wiwin da Suhail d'in ya aje a d'akinsa da kuma wad'annan tickets d'in na k'asar Hongkong. Kasancewar Suhail na d'akin mahaifiyarsa bai san wainar da ake toyawa ba shi da mahaifiyar ta sa. Police d'in tsayawa su ka yi a waje su na jiran umarni daga alhaji Usman. Sama alhaji Usman ya nufa ta re da tura d'akin Hajiya Mansura. Zaune ta ke a bakin gado, ya yin da Suhail ke zaune a kan stool ya na cin Apple. "Ku fito ku duka Ku na da bak'i a waje" Fad'in Alhaji Usman. "Bak'i kuma? To suwaye?". Fad'in hajiya Mansura. "Idan kun fito kwa gan su". Alhaji Usman ya fad'a ta re ficewa ya sauko k'asa. Hajiya Mansura kallon Suhail ta yi wanda shi ma itan ya ke kallo ta re da fad'in, "Ta shi muje mu ga kk su waye ne". A tare su ka fito ita da Suhail d'in. Turus su ka tsaya su na kallon polisawan da ke bakin kofar na ta. "Alhaji wad'annan fa? Mai su ka zo yi ne haka har nan wajan?". Fad'in Hajiya Mansura. "Ku tafi da su" Fad'in Alhaji Usman. Gaba d'aya kallonsa su ka yi a razane don Suhail har ya na tumbling ta re da fad'in, "Dad...." "Ka nai mi wani uban daga yau don ni na yafe ka daga cikin y'ay'ana, ai ba kai kad'ai gare ni ba, kuma wannna ta yi ma ku jagora har gidan k'awarta Zuwairah, ita ma Ku had'a da ita". Fad'in Alhaji Usman. "An gama yallab'ai". Fad'in wani police ta re da sakawa Hajiya Mansura ankwa a hannunta ita da Suhail su ka ta sa k'eyarsu. Sai da su ka bi ya su ka d'auko hajiya Mansura wacce su yi da ga da ita ka min ta bi su ka na su ka wuce police station. Gaba d'ayansu bayan kanta aka watsa su ba ko d'an kunne a kunnan su. Don shi Suhail ma daga shi sai gajeran wando duk case d'in sa ya fi na kowa a cikinsu. Kasancewar sun san Hajiya Mansura matar Alhaji Usman ce, dalilinsa shiyasa ba su san tozartata, don sun yi sun yi ta magantu, amma fad'i ta ke ita ba ta san komai ba, ganin haka ita Zuwairah ta ce ba ta sa ni ba, shi ma Suhail ya ce bai san daga in da Cocaine d'in nan da tickets d'in nan su ka fito ba har da wani ciccijewa. Mai da su bayan kanta ya sa aka yi ka na ya kira Alhaji Usman ya masa bayani ta re da ce masa kunyansa fa su ke ji shiyasa ba su d'auki tsattsauran mataki ba. Magana Alhaji Usman ya yi da shi mai tsawo shi kuwa sai cewa ya ke ''OK sir''. A ranar aka d'ebe su sai state CID. Tun shigar su wajan Suhail ya soma sakin zawo ganin irin nau'ikan azabar da akewa mutane a wajan. Hajiya Mansura kuwa zufa har ta d'uwawunta, ya yin da Zuwairah tai ta sakin tusoshin tsoro ta re da son zagayawa zuwa ban d'aki. Da ma tuni an yi was babban su bayanin komai kamin a tura su zuwa can. Shiyasa a na zuwa da su ya ce a sa su a dak'in duhu na awa awa d'aya. D'akin duhun nan ko tafin hannunsa mutum bai iya gani ga shi window Ku ma idan za ka shekara ka na ihu ba mai jin ka. Wasu ma idan an saka su a wajan aka fito da su sanadiyar makancewar su kenan. Ko na minti ko aka tura mutum d'akin duhu sai ya gwammaci mutuwa ba re har na awa d'aya. Bayan awa d'aya ya cika, DSP ya sa aka ciro su idawuwansu a rufe sun bala'in jigata. Gaba d'ayansu zarni su ke yi ta re da warin kashi saboda zawowi da su ka dunga saki. Suhail kuwa sai cewa ya ke yi, "Wallahi zan fad'i komai, zan fad'i gaskiya". Wa ni d'akin aka kai su, ta kan Suhail d'in aka soma tuhuma, "Ka shirya bayani ko a sai an sa ke mai da ka d'akin duhu?". Idanuwansa a kulle har da d'aga hannu sama ta re da fad'in, "Wallahi na shirya, zan fad'i komai yasin". "Muna jin ka". Oga ya sa ke fad'a. "Ni na ke sa abokai na da ke Mexico su na shigo min da Cocaine ina sayarwa a nan k'asar. Da a can mu ke sana'ar mu. To mahaifina da ya kai min ziyara ya ga irin shiriritar da na ke yi shi ne ya mai do ni k'asata. Ni kuma ba zan ita dai na wa ba sai mu ka yi shawara da friends d'i na na can shi ne su ke turo min ta nan, sannan kuma wannan tickets d'in na wasu y'an matane da wata hajiya ta ke kawo min daga k'auye ina turasu karuwanci k'asashe daban-daban ita kuma a duk yarinya d'aya ina ba ta dubu d'ari da hamsin. Hatta y'an aikin gidan mahaifina akwai wad'anda na tura, sannan ba zan iya k'irga y'an aikin gidan mu da na yi wa fyad'e ba, wasu ma har ta duburansu na ke amfani da su ta re da yi ma su barazana da bindiga idan su ka k'i amincewa". Hajiya Mansura jin bayanin da d'anta ya ke yi ba ta san ta na sakin zawo a in da ta ke ba saboda tsananin firgita. "Ke nan har da safarar makamai ka ke yi?". Oga ya sa ke tambayansa. "Eh shi ma na kan d'an tab'a". Fad'in Suhail. "Wa Ku ke sayarwa wa?". Ya sa ke tambayarsa. "Ni dai wani mutum na ke kai wa, shike sayewa duka ban san mai ya ke yi da su ba". Jinjiga kai Police d'in nan ya yi ta re da fad'in, "Cigaba ina jin ka". "Wallahi yallab'ai shikenan, na gama fad'in komai". Suhail ya fad'a. "Ke nan ba ka da hannu a b'acewar yarinyar gidan ke nan?". Fad'in Police d'in. "Wallahi ban san ko mai a kan haka ba, ni dai na san ina ta d'ana mata tarko don yi mata mummunar fyad'e, amma ta na tsallakewa". Fad'in Suhail. Mai da kallonsa ya yi izuwa ga Hajiya Mansura da ta yi wik'i-wik'i idanuwanta sun yi jazur sun k'ank'ance saboda shigarsu d'akin duhunnan. Tun ka min ya yi magana ta soma bayani, "Tun ina budurwa na ke harkan mad'igo (lesbian) kasancewar makaranta kwana na yi, a can na ko yi wannan d'abi'ar da babu wanda ya san ina aikatawa a zuri'a ta, don ni d'iyar malamai ne, idan ka na jin malam Hafizu Nazifi mai almajirai, shi ne mahaifina, tun muna yi yamu-yamu k'awaye har abun ya bunk'asa mu ka kafa k'ungiyar mu wanda ni ce shugabarsu. Na yi aure ne ba dan komai ba sai don gudun zargin zama'a amma ni sam namiji bai gabana. Mu na amfani da asiri ta yadda duk yarinyar da muka gani ko d'iyar uban wacece ita da kan ta za ta nai me mu don yin mad'igo da ita don saka mata sha'awarmu da k'aunar mu muke a zukatun duk wacce mu ke so. Yanzu haka ni mata na sha takwas wanda na aure su, bayan ni ba bu wacce ta isa ta yi mad'igo da su. Binty kuma tun ranar da na fara ganinta na ji k'aunarta da sha'awarta ya darsu cikin rai na. Sai dai abun mamaki, na yi asiri a kan ta amma bai kamata ba, hakan ya sa na kafa tarko da Hajiya Na'ima da kuma y'ay'anta akan idan ba ta amince da ni ba zan kashe su. Kuma duk mun had'a hakane da wacce ta yi sanadiyar zuwanta gidan wato Kandala wacce babu abunda su ka had'a da ita, ita ma tsintarta ta yi ta kawo gidan matsayin y'ar aiki su kuma su ka rik'e ta tamkar y'ar su. Na yi amfani da Anna don in sa mu Binty, ni na yi wa Anna asiri ta re da taimakon y'ar aikinta Fasila mu ka zuba mata magani ta ta ka shi ne k'afafuwanta su ka kumbuta har aka kai ta asibiti. Ni kuma na kira Binty na ce ko ta amince ko kuma Anna ta mutu yay'anta su biyo bayanta. Bayan na kashe wayar na kwanta cike da farin ciki da kuma tabbacin Binty za ta zo har in da na ke in yi mad'igo da ita kuma in aure ta. Amma wallahi wallahi ban san in da ta ke ba a yanzu haka, ba ni na b'oye ta ba". Ta k'arisa maganar ta na kuka. K'ura mata idanuwa police d'in nan ya yi ka na ya mai da kallonsa izuwa wajan Zuwairah da ta yi saurin sunkuyar da kai k'asa. "Ba na buk'atar ba ki umarnin yin magana" Fad'in officern nan. Hajiya Zuwairah ta fara magana cikin kuka kamar haka, "Duk abubuwan da Mansura ta lissafo ta re mu ke yin sa, ita ce shugaba ni kuma mataimakiyar ta, kamar yarda ta ka mu da K'aunar Binty, ni ma haka na ka mu da k'aunarta. Sai dai ta ja min dogon layi akan fita daga harkarta idan kuma ba haka ba za ta b'atar da ni. Na nu na mata na bar maganar Binty, amma cikin zuciyata ban bari ba, lokacin da ta buk'aci Kandala da ta d'auko Binty ta re da yi wa uwargidan ta k'aryan cewa za ta kai ta wajan danginta sai ita kuma ta kai Binty wajanta a wani gida daban ta re da tsoratar da ita akan idan ba ta yarda da buk'atarta ba to za ta ka she Hajiya Na'ima da iyalanta. Kandala ta amince da buk'atun Mansura sakamakon naira million biyu da ta ba ta. Ni kuma na k'arawa Kandala million uku a kan ta ba ni Binty ni na san yanda zan b'ullowa al'amarin, to bisa tsauyayi sai y'ar wajan Hajiya Na'ima ta bi su wanda hakan ne ya lalata mana shiri. Kuma ni na san shirin Mansura kasancewar komai ta re mu ke yi. To bayan sun dawo daga can Saminaka ne Mansura ta yi wa uwargidanta asiri a har ta shiga wannan hali na ciwon k'afa wanda ta dasa tarko da shi, ni kuma a ranar na zo gidan na yi wa Binty k'aryan zan taimake ta ta kuma fad'a tarkona na kai ta gidan d'aya daga cikin members d'in mu wanda ita ma ta na da na ta k'udurin a kan mu, yanzu haka ta na can gidan". A matukar firgice da kuma tsananin Hajiya Mansura ta ke kallon Zuwairah ta re da fad'in, "Zuwairah ni ki ka ciwa amana? Lallai za ki san kin ci amanata". Tsawa police d'in nan ya daka ma su ta re da fad'in duk sai kun gwammaci mutuwa da aikata wad'annan abubuwan da Ku ka yi. Ya kalli Zuwairah ta re da fad'in, "Za ki ba mu address d'in ita wannan matar domin mu kwamusota ita ma". Ya mai da du ban sa ga hajiya Mansura ta re da fad'in, "Duk sauran members d'in ku su ma sai kun fiddo da su ta re da y'ar iskan Kandalan nan. Shegu y'an iska ma su b'ata tarbiyyan y'ay'an jama'a". "Kai kuma, na ka case d'in babba ne, sunan ka CC condemn. Duk wad'annan abokan na ka sai ka fito da su ta re da wannan d'an iskan da ka ke kai wa makamai ya siya. D'an iska ubanka na k'ok'ari da kai ba ka rasa komai ba amma ka na naiman zubar masa da mutunci kai da shaid'aniyar uwarka, ka mai da su d'akin hayaki su d'an d'umamu na iya lokacin da Alhaji Usman zai d'auka ka min ya k'araso state CIDn nan. Yanzu zan kira shi"... *YA KA MA TA KU HAUKATA NI DA RUWAN COMMENTS SABODA GARAB'ASAR SATI DA LAHADIN NAN DA NA BAKU. KAMAR YANDA NA FARANTA MA KU, NI MA KU FARANTA MIN* 😌😌🤓 🌹 *73-74*🌹 .............Fita ya yi ta re da dannawa Alhaji Usman kira ya yin da ya ke nufar office d'insa. Bugu biyu Alhaji Usman ya d'aga ta re da sallam kasancewar da ma su na da contact d'in ju na. Amsa sallamar Officern ya yi ta re da fad'in, "Yallab'ai sun yi confessing, yanzu kai muke jira sannan akwai wasu mutanan da su ka ambata wanda na ke so a taho min da su nan, sannan kai ma ina son ka ji duk abunda su ka fad'a da kunnanka don komai mu nan sai mun yi recording". "Haka na ke so ai, bari na kira y'ay'ana my taho ta re yanzu". Fad'in Alhaji Usman ta re da katse wayar. Bayan ya katse wayar ya shiga lalubar numbern Julaibib sai dai abun mamaki ya kira ya fi sau shurin masak'i amsa d'aya ake ba shi *THE NUMBER YOU'RE TRYING TO CALL IS NOT REACHABLE AT THIS MOMENT, PLEASE TRY AGAIN LATER*. Duk a tunaninsa sharrin network ne, mai da ak'alar kiran ya yi zuwa ga Barrister Fu'ad, sai dai shi ma hakan ta kasance. D'an tsuka ya ja ta re da yi wa drivern sa magana zai fita. Nan da nan driver ya fito da mota, sannan ya yi umarni da sauran su dakata da mota d'aya kawai zai fita. Sai da ya fara zuwa part d'in Anna su ka fito ta re kasancewar da ita ya ke so su je saboda ayi komai a gabanta tun da su Julaibib d'in bai samu numbers d'in su ta shiga ba. Mintuna arba'in ya kawo su State CID kasancewar bai k'aunar gudu a mota a hankali ya ake tafiya da shi. Cikin mutunci da karramawa aka yi Office d'in Officern da case d'in ke hannunsa da su. Anna kuwa duk a rud'e da tashin hankali ta ke, burinta kawai ta ga Binty hankalinta ya kwanta. Ko zama ba su yi ba officer ya yi d'akin bincike da su ta re da kunna wani computer videon su Hajiya Na'ima ya bayyana. Anna kuka shab'e-shab'e da idanuwanta ganin halin da aka bai nai mi jefa Binty da kuma sacrificing d'in da ta yi a kanta. Sannan ta sha mamaki da kuma tsoron jin abunda Mansura da Zuwairah su ke aikatawa. Babu abunda ya fi bata mamaki kamar zanzan da Mansura ta yi na cewar Binty ba ta had'a komai da Kandala ba da kuma b'arnar da Suhail d'in ya yi ta aikatawa a cikin gidan. Sosai Anna ta yi da na sanin hana Fu'ad d'aukar matakin da ya so yi tun farko. Wani police ne ya shigo ta re sa sarawa wannan Officern ka na ya ce, "Sir ga sunan zo da su duka, su na d'akin tuhuma". "OK to ga ni nan zuwa". Fad'in Officer ta re da kashe computer ka na ya ce wa Alhaji Usman su ta so su je. Anna k'afafuwanta har wani sanyi su ka mata saboda abubuwan tashin hankalin da ta ji. Can d'akin su ka shiga, Kandala kuwa ta yi fitsari sau babu adadi, suma kuwa ta yi sau bakwai a na farfad'o da ita da ruwan k'ank'ara. Junaina kuwa sai gwalalo idanuwa ta ke yi kamar an tsare kwarto a d'aki. Shi kuwa tirk'ek'en Alhajin nan ko a jikinsa don wannan ba shi ne karon farkon kama shi ba manya k'asar su na sawa ana sako sa. "Are you ready to confess?". Fad'in Officern nan ya na kallonsu d'aya bayan d'aya kasancewar su ma sun shiga d'akin duhu don sun riga Alhaji Usman k'arasowa. Kuma ta re aka fito da su har da su Mansura wanda gaba d'aya sun canza kamanni saboda d'akin hayakin da aka kai su. Akwai wani makeken glass da ke tsakaninsu don da mic su ke magana da ke kai masu maganar can b'angaransu haka suma. Ta kan Kandala aka fara tuhuma. Aikuwa kamar kanya haka ta shiga zuba, "Yallab'ai ayi min afuwa wallahi sharrin shaid'an, tabbas babu abunda na had'a da Binty, asalima ni a hanya na cintse ta ta na kuka a kai ta wajan wani da ta kira sunan sa da ba zan iya tunawa ba, wallahi har ga Allah ban so cutar da ita ba, musamman yadda ta san cewar ban had'a komai da ita ba, amma ba ta fad'i gaskiyar haka wajan uwar rik'onta ba, haka duk wata na ke karb'an dubu d'ari da kayan abinci ina sayarwa ta re baiwa aminiyata Datu ta na juya min y'an currency. Kwatsam sai ita wannan hajiya Mansura ta kawo min wani ba tu ta re da tayin naira million biyu, jin kud'i masu yawa haka sai na amince da buk'atar na auran Binty ta mai da ta y'ar mad'igo, to a gaban ita wannan hajiya Zuwairah mu ka yi komai, shi ne ita kuma ta k'ara min million uku a kan ita ma za ta rik'a mad'igo da ita Binty amma in yi shiru da ba ki na ka da ita Hajiya Mansura ta san da zan can. Wallahi na san na yi kuskure kuma na zalinci hajiya Na'ima mutuniyar kirki wacce duk na ziyarceta sai ta ba ni kud'i da kayan abinci masu uban yawa kuma a had'ani da driver don kai ni gida". Kandala ta k'arisa maganar ta na kuka har da majina don ta ci azaba a d'akin duhun nan. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un". Shi ne abunda Anna ta ke ta maimaitawa a fili. Kan Junaina aka koma wacce ke ta wik'i-wik'i da idanuwa. "Wallahi tallahi ni ba amshi Binty don yin mad'igo da ita ba, kuma ba saboda haka na sa aka kawo Binty gida na ba, ni saboda d'iyar mijina na sa aka kawo ta. Mijina ya kasance azzalumi mara adalci a kan y'ay'ansa. Banbanci sosai y'ay'ana su ke gani aka y'ar uwargina. Sabrin ta kasance mai son kan ta tun ta na k'arama ta re da son ta burge mutum, sai dai ta na da lalurar ciwon zuciya wacce aka haifata da ita kuma hakan ne ya sakawa mahaifinta tsananin k'aunarta fiye da duka y'ay'ansa. Haka na min ciwo a zuciyata sosai saboda yanda y'ay'a na kullum ke kukan yadda mahaifinsu ke nuna bambanci a kan su. Haka ya sa na je wajan boka ya ba ni maganin da idan na sakawa Sabrin jijji da kan ta da kuma san rai ta re da son ta fi kowa a duniya zai nin Ku sau dubu a kan yadda ta ke. Tabbas sabrin na da duka halayan nan da na lissafo sai dai a kashi d'arin yadda ta ke a yanzu, ni na k'ara mata kashi casa'in saboda nasan dole-dole sai ta gamu da wad'and'a su ka fita wanda idan haka ta kasance saboda tsabar kishin da na saka mata zai iya sanadin bugawar zuciyarta ta mutu kowa ya huta. Na yi hakane saboda na fi son ta mutu ta hanyar buguwar zuciyata ta yadda mahaifinta shi ma zuciyarsa ta bugu mu tattare dukiyarsa ni da y'ay'a na mu yi gaba. Tabbas ina cikin k'ungiyar mad'igo, amma ni ba buri na ba ne in yi mad'igo da Binty don ni a cikin k'ungiyar ma ni k'aramar member ce kuma na shiga ne saboda k'ungiyar akwai har kan samun kud'i saboda sun had'a da tsafi don duk lokacin da aka kawo budurwar da ba ta tab'a sanin d'a namiji ba ta yi joining kud'i su ke samu wanda ak'alla zai kai billion bakwai duk sacrifice d'aya". Ta fad'i haka ta na mai fashewa da kuka. Anna saboda firgici har fitsari sai da ya cika mata mararta. Alhajin nan da aka so kan shi sai wani ciccijewa ya ke yi ya k'i ya yi magana. "Ku kai shi d'akin lantarki, bai horu ba". Fad'in Officer. "Alhaji ku ko ma gida, duk yan da ake ciki zan kira ka, sai dai fa akwai matsala, ba'a San in da y'ay'anka su ke ba, mai gadi kuma ya tabbatar mana da sun shiga amma ba su fito ba, kuma mun ga motocinsa, sai dai akwai wani abun tashin hankali da mu ka ga ni a gidan, domin sawun dawakai mu ka gani wanda ba zai k'irgu ba ta re da wani rami mai zurfin gaske, kum...........". Bai k'arasa ba Anna ta fashe da kuka mai sauti ta re da fad'in "Wallahi duk in da y'ay'ana su ke sai an fito min da su ba zan yarda ba". "Hajiya ki kwantar da hankalin ki, duk in da y'ay'an ki su ke za su bayyana da izinin lillahi". Fad'in Officer ci ke da lallami. Alhaji Usman ne ya kamata su ka fita ya na lallashinta har wajan mota ya sata ciki. Sun kai kusan 15minutes su na tattaunawa da officer ka na ya shiga mota driver ya ja wanda a hanya sai aikin lallashi ya ke saboda yadda Anna duk ta bi ta d'aga hankalinta. *____________________* ...........lulawa kawai su ke yi cikin sararin samaniya har na wajan sa'o'i uku ka na su na sauk'o k'asa. Babu abunda ke ta shi sai kuka da haniniyar dawakai kuma su ba su ganin koma jin su kawai su ke bisa wani abunda su ba su san ko menene ba, shi ma dai a k'asar sun yi gudu wanda su ke da tabbacin dawakai ne sai dai ba su ganinsu har na tsawon mintuna talatin ka na su ka fara ganin hayak'i daga nesa da su kad'an. Sabrin ta yi fitsari a jikinta ya fi sau babu adadi ya yin da Hamdan ke ta fad'in, "Allahumma inni a'ouzu bika minal khubisi wal kaba isa" kamar wanda zai shiga ba yi. Julaibib kuwa addu'o i kawai ya ke karantawa cikin zuciyarsa, Fu'ad kuwa ya na addu'a ta re da fad'in, "Shikenan Anna mun yi ban kwana". Binty kuwa sai fizgan numfashi ta ke yi kamar mai asthma. Wani dank'areran masarauta su ka hango wanda baki ba zai iya misalta girmansa ba da kuma tsaruwarsa. Domin da zallar d'anyan gwal aka k'era masarautar re da yi mata kwalliya abun sai wanda ya gani. Tun daga nesa daga masarautar dakaru ne sama da guda dubu cikin shigar yak'i fuskansu a rufe amma k'afafuwansu na kofato ne. K'ofofi kuwa sun kai hamsin wanda ko wani k'ofa nan ma dakaru dubu ne masu bud'e shi saboda tsabar girma da nauyinsa. A lokacin ne kuma, Su Julaibib su ka ga wad'anda su ka d'auko su, suma fuskokinsu a rufe ya ke sai k'afafuwansu na kofato. Masarautar nan girmansa da kyawunsa ya fi gaban fad'e. Su ma rayuwa su ke kamar bil'adama. Akwai kasuwa a ciki, ga kuma aljanu nan cikin suffar mutane kowa na hidimansa, kyawunsu kuwa ya fi gaban kwatance, akwai bak'ake amma ba irin bak'in fatar da mutum ya sa ni ba, bak'insu mai masifar kyau ne da d'aukar hankali, gashin kan su kuwa har k'asa ya ke ja saboda yawa da tsawansa. Gaba d'aya yuuuuu aka aljanun nan su ka yi da idanuwa su na kallon su kamar za su cinye su d'anye. Daga k'ofar da za ta sa da su da ainahin fad'ar Oumul Sahwat su ka tsaya, su dai Su Julaibib su na ganin ikon Allah domin su ba'a sama ba, kuma su ba a k'asa ba haka su ke. "Ai mana iso wajan Shugaban mu, na sanar da ita na cika mata alk'awarinta ga bil'adama nan na kawo mata su". Fad'in d'aya daga cikin dakarun nan. Uku daga cikin dakarun kofar da zai sada su cikin fadar Oumul Sahwat su ka shiga ciki don sanar da Oumul Sahwat. Cikin mintuna uku su ka dawo ta re da fad'in, "Sarauniya Oumul Sahwat ta ba da umarni Badakkare Oulbub shi kad'ai ya shigo da bil'adama cikin fad'a". Gaba d'aya sauran darewa su ka yi, ya yin da Su Julaibib su ka ji su a k'asa timm sun fad'o. Sabrin k'ank'ame hannun Binty ta yi ta re da fad'in, "Ki taimake ni Dan girman Allah, wallahi ban so in mutu yanzu". Ta fad'a jikinta na b'ari. Duk da kasancewar Binty cikin gigicewan tsoran da ta ke ji ta ma fi Sabrin d'in amma sai ta ka mo hannunta ta re da fad'in, "Ki yi ta addu'a, in sha Allah za mu koma gida babu abunda zai sa me mu". Gaba d'ayansu kuwa ji su ka yi kamar ana tura su har cikin fadar da sai da gaba d'ayansu numfashin ya d'auke na wucin gadi sakamakon arba da su ka yi da tsaruwar wannan fada da girmansa ya wuce kwatance. Daga bakin kof'ar zuwa can wajan zaman Oumul Sahwat tafiyar kwana uku ce idan aljani ne kuma bai yi amfani da tsafi ba, amma idan mutun ne zai shekara ka min ya isa. Wani tsararran kujeran zinari ne ya ke saukowa daga sama, ga kuma gashin da ya zuba har a gaban su Binty da ke bakin k'ofar fada saboda tsayi da yawansa. Sai da kujeran ya kusa tab'a k'asa ka na ya tsaya cak. Bayan wata farar mace ya bayyana tun daga kan tsakiyar kan ta har kwankwasonta ado ne na zinari. Wasu fararan kayane a jikinta masu stone na gold sai kyalli su ke yi, jelar rigar da ya ke a tsattsage sai da mamaye masarautar nan. Kanta ne kawai ya juya ba ta re da gangan jikinta ya motsa ba. Wani irin ajiyar zuciya Hamdan, Sabrin, Barr Fu'ad su ka saki yayinda Sabrin da Binty da Hamdan su ka zube a sume. *DAN ALLAH KU YI HAK'URI DA WANNAN ABUBUWA NE SU KA MIN YAWA A SCHOOL* 🌹 *75-76*🌹 ............Fuskanta ne ke kallonsu ya yin da gangan jikinta ke kallon gabanta, kyakkyawace ta wuce misali. Idanuwanta sak irin na mage. Farinta kuwa kamar Snow white. Da hannu ta yi alamar sai ga su su na tahowa har da Sabrin, Binty da Hamdan da ke ya she a sume. Cikin minti d'aya su ka isa gabanta. Ta ke ta jujjuya hannunta ta re da watsa su a kan fuskan su Binty da ke ya she a sume, cikin dak'ik'u su ka farfad'o a matuk'ar razane, don Sabrin k'ank'ame Binty ta yi ta na hawaye cikinta na murd'awa. Oumul Sahwat d'ab yatsanta ta d'aga ta re da jujjuya sa ka na ta tsayar da shi a nan tsakiyar fadar nesa da su k'adan. Ta ke Yousouf ya bayyana a k'uk'k'ulle da wani kaca wanda idan za'a warware kacan mutane dubu ba za su iya ba. Gaba d'aya jikinsa jini ne ke zuba har ta idanuwansa da kunnansa. Daga kan karagar ta mik'e still fuskanta na kallansu kuma gabanta na kallon baya ta re da nufo in da Yousouf ya ke a k'ulle, sai a lokacin ta mai da sauran jikin na ta ya na fuskantar in da fuskanta ya ke ta re da kecewa da wani irin dariyar da ya kusa tsayar da numfashinsu duka ka na ta k'arasa kusa da sarkin k'ofar fada ta re da fad'in, "Ayi shela gaba d'aya aljanun masarautar Daulatul Sira su yi gangami, a kuma shaida mu su da fitowa ta ta re da bil'adama da kuma bak'in mugu jinin adali kuma amintaccan bawan wannan masarauta da ke nai man jefa mu cikin tasku da fuskantar barazana daga azzaluma wato sarauniyar da ke mulkar Daulatul Bahshan da a yanzu haka ta ke tafe da rundunarta domin yak'armu ta kuma had'e harda masarautar nan ta mulka". Cike da girmamawa sarkin k'ofa ya rusuna ta re da juyawa ya nufi fad'awa sarkin shela domin aljanu su yi gangami. Cikin abunda bai fi minti biyu ba, tu ni har kowa da ke cikin masarauta da ma wanda ke wajan gari su ka yi gangami domin amsa kiran Oumul Sahwat. Komawa ta yi gaban Yousouf ta re da d'ago hab'ar shi da d'an yatsar ta ta re da fad'in, "Sai na k'ona zuciyarka kamar yarda ka k'ona tawa zuciyar. Sai na sa ka tafi lahira da tabo mafi muni a zuciyarka na jawo mana fitina da ka yi akan wancan bil'adamar da ba jinsu ku d'aya ba. A cikin wannan Masarauta akai y'antattu da kuma bayin da su ka fi wannan kyawu sau dubu tamanin amma ka k'etare duka jinsinka ka fad'a soyayya da jinsun da ka ke so saboda ka rai na alk'awarin kakana na Uku da ya yi alk'awari da kuma sa hannu da jinin jikinsa akan babu mu ba bil'adama. Ka ci amanar kaka na da kuma na masarautar nan, ka fusata sarauniyar Daulatul Sira wanda a yanzu zan d'and'ana maka azaba wacce ba ka tab'a tunaninsa ba, zan wulak'antaka in kuma tozarta abun k'aunarka da duk wanda ke da alak'a da ita. Sai na saka dakaruna dubu hud'u wanda duk d'ayan su ya na da k'arfin dawakai hamsin su yi mata mummunar fyad'e a gabanka da duk aljanun da ke cikin wannan masarauta, sannan in sadaukar da sauran bil'adaman can wa Sarauniyar Daulatul Bahshan domin fansar masarautata da kuma aljanun da ke cikinsa, kai kuma da Kakan ka mai d'aure maka gindi, zan sa ke baiwa sarauniyar Daulatul Bahshan Ku a matsayin kyauta domin ga na maku azaba a kowacce rana ta na jin sanyi da dad'i har ku shud'e wannan shi zai ragewa zuciyarta rad'ad'in hallakar kakanta na goma sha biyu da bil'adama su ka yi sanadin mutuwarsa". "Allah ba zai tab'a baki wannan damar ba, domin Allah bai ce mu zalinci kowa ba. Ya halicce mu ne don mu bauta masa, kuma mutuwar kakan Sarauniyar Daulatul Bahshan ba laifin bil'adama ba ne, domin Allah ya halicce mu, mu za mu gan su, amma su ba za su gan mu ba, kuma su ne su ka je duniyarsu ba su su ka zo har na su duniyar su ka yi sanadin mutuwarsu ba. Hakan na daga cikin k'addararsu ne. Kuma taimako taimako ne kuma ladarsa na wajan ubangiji. Walau Aljani ka taimaka ko mutum. Ni dai na san ni da Kakana rai muka tseratar". Fad'in Yousouf da ke a k'ulle. Wani kibiya Oumul Sahwat ta zaro daga cikin fatar hannunta ta cakawa Yousouf a cinyarsa sai da ta fito ta baya ta kuma zarowa ta caka masa a d'ayan cinyarsa ta re da mak'ure wuyansa da zara-zaran hannunta wanda ke d'auke da dogayan k'umbuna. Wata tsohuwace ta taho a kan iska a gigice ta zube a k'asa ta re tab'a k'afafuwan Oumul Sahwat ta re da fad'in, "Ki gafarcesa shugawa, a bisa shi ina mai naiman gafararki ki yi hak'uri alfarmar kakansa na goma kuma amintacce bawa a cikin wannan masarauta". Sakin wuyarsa Oumul Sahwat ta yi ta re da nufar kujerarta ta zauna ta re da d'aura k'afa d'aya a kan d'aya. Su Julaibib mutuwar tsaye su ka yi yayin abubuwan ya ke faruwa a gabansu. Ba ki ba zai iya misalta tashin hankalin da su ke ciki ba. Gaba d'aya kowa ya hallara fitowar Sarauniya kawai ake jira. Daga can filin yak'i kuwa, dakaru ne kusan guda million dubu hud'u cikin shigar yak'i. Oumul Sahwat b'acewa ta yi domin komawa cikin d'akinta don kuyanginta su shiryata. Wannan tsohuwa da ta duk'a ta nai man wa Yousouf afuwa a wajan Oumul Sahwat, kallon Yousouf d'in ta yi hawaye na gangaro daga idanuwanta ta re da fad'in, "Ya kai d'ana, ka jajirce kamar yanda ka so ma tun farko to ka kai shi k'arshe. Ka cikasa ladanka, ka da ka tab'a bari a cutar da wad'annan bil'adaman da kai ne sanadiyar shigowarsu duniyar mu. Zan mutu cikin salama tun da har Allah ya sake had'a fuskokin mu. Allah ya yi maka albarka sannan ka warware k'ullin da ka k'ulle ka min ruhinka ya bar gangan jikinka. Ka da ka bari d'an tsokar da ke k'irjinka ya rinjayeka idan har da gakse ka shaida babu abun bautawa da gaskiya sai Allah. Allah ya taya ka d'ana". Ta k'arishe maganar da kuka ta re da ta shi sama ta nufi in da Julaibib ya ke. Bud'e tafukan hannunsa ta yi ta re da d'aura masa wani d'an tantabara mai d'auke da sarka. Can kuma ta d'auki sark'an ta re da saka masa a wuyansa ta kuma cusa tantabarar cikin rigar jikinsa. A ta ke ka yan jikinsa su ka canza kala su ka koma Orange, can kuma su ka koma green daga baya kuma su ka koma farare k'al wanda da ainahin kalar su brown ne. Tafin hannun ta kuma rik'ewa ta re da fiddo wani tawada ta yi gajeran rubutu ka na ta kalle shi ta re da fad'in, "Duk rintsi ka da ka yadda wannan sarkar ya bar jikinka, sannan idan kun koma ka samu ruwan zam-zam ka wanke wannan rubutun da na maka a da shi ka baiwa takwaran d'ana wato Yousouf in sha Allah shi da wannan cutar har abada da ma duk wani cutar da aljani ya yi ajiya". Fad'in Wannan aljana ka na ta b'ace b'at. Sabrin dai ta yi fitsari ya fi a k'irga. Ya yin da Binty kuwa cikinta sai katsawa ya ke yi ta na addu'ar Allah ya sa ta tashi daga wannan baccin da ta ke yi haka mai munanan mafarkai. Shikuwa Hamdan sai "Qul ya ayyuhal kafirun" ya ke ambata a fili. Fu'ad kuwa jikinsa karkarwa ya ke yi ta re da uban zufar da ke gangaro masa. Julaibib kuwa kai tsaye ba za ka ga tsoro a fuskanci ba, amma a zahiri ya na cikin firgici amma sai jero addu'o i ya ke yi cikin zuciya. Ganin su kawai su ka yi a waje gaban dandazon jama'a da ke ta ihu wasu na rawa wasu na kid'a wasu kuma na yi kamar za su cafko su. Cikin second biyu ko'ina ya yi tsit hatta tsuntsu da ke wajan saboda bayyanar Oumul Sahwat akan wani k'erarriyar kujeran mulki da aka yi sa da zallar gold, ita kanta saga samanta har k'asanta kwalliyace da gwala-gwalai. Sanye ta ke cikin wani doguwar riga mai wasu irin kyalkyali kalar baki da ja, gashin kanta da ya zuba har ya na tab'a kafafun aljanun da ke k'asa shi kan shi ya sha ado da gwala-gwalai. Wani irin crown ne a kan ta na zallar gold mai d'aukar ido. Gefen hagu da damarta y'an mata ne guda uku-uku kyawawa da fiffike a bayansu su na mata firfita. Sai wasu murtuka-murmukan aljanu cikin shigar yak'i hannunsu rik'e da kaifaffiyar takobi a hannunsu fuskansu a rufe su na jiran umarni. Mahaifiyar Yousouf ce ta bayyana hannayanta rik'e a hannun wasu dakaru bakinta na fitar da jini. Sarauniya Oumul Sahwat ta kalli wani badakkare da ke gefenta ta re da kallon d'unbin aljanun nan. Cikin sauri wannan badakkare ya yi gaba ta re da kallon kafatanin aljanun nan ta re da fad'in, "Sarauniya Oumul Sahwat ta na yi ma ku albishir kukan Ku da fargabarku ya k'are daga yai domin ta samo maganin damuwarku bayan tsawon shekaru sha takwas da wani la'ananne a cikin mu ya nai mi jefa mu cikin masifa. Kuma ta yi alk'awarin zartar da hukunci cikin gaggawa ga dukkanin mai taimakawa wannan d'an iska da ya jawo mana afkuwar yak'in da zai kashe mana masarauta da kuma y'ancin mu. Don haka yanzu za ta fara hukunci ga mahaifiyarsa wacce ta kasance ita ma ta na taimaka masa har a wani karo ta yi mummunar kuskure wajan kwaikwayon halitta da fuskan shugabar mu wajan taimakon bil'adama wanda kowa a nan ya san an rubuta wani yarjejeniya wanda kakan shugabarmu ya saka hannu da jinin jikinsa akan babu mu ba shiga duniyar bil'adama. Sai dai an sa mu mai kunnan k'ashi cikin mu ya karya wannan doka ta re da shi da mahaifiyarsa da kuma mahaifin mahaifiyarsa wanda dukkaninsu sun kasance zuri'ar amintaccan bawan wannan masarauta. Don haka yanzu za su fara fuskantar hukunci". Gaba d'aya aljanun nan su ka shiga ihu su na fad'in, "Hukunci! Hukunci!! Hukunci!!! Sai sun fuskanci hukunci". Kallon wannan badakkare Oumul Sahwat ta yi ta re da jinjina kan ta. Kaifaffiyar doguwar wuk'a ya zaro daga k'ugunsa ya saita k'eyar mahaifiyarsa Yousouf wacce ke hawaye ta na kallon Yousouf d'in ta re da girgiza masa kai ta na kuma furta "kar ka karaya ko sun kashe ni" a leb'anta. Sai da ya d'aga wannan wuk'ar sama ka na ya aza da k'arfi bi sa k'eyar mahaifiyar Yousouf sai da jini ya yi tsartuwa ta re da wanke fuskan Yousouf ka na kan ya fita daga gangan jikinta ya gungura k'asa. Gaba d'aya aljanun nan su ka d'au shewa da ihu ya yin da Sabrin da Binty su ka sa ke zubewa k'asa sumammu karo na biyu. A gigice su ka farfad'o sakamakon wani irin ruwan sanyin da su ka ji a kan fuskokinsu da wannan badakkare ya zuba masu. Yousouf kuwa wani irin zabure-zabure ya fara yi ta re sa fizge-fizge jijiyoyin jikinsa sun yi burd'un burd'un yayin da idanuwansa su ka koma kamar garwashin wuta. Julaibib kuwa ji ya yi gaba d'aya tsoro ya fice a ranshi sai wa ni irin tsana da yaji ya na yi wa Oumul Sahwat na kisan gillar da ta yi wa mahaifiyar Yousouf. "Ke azzaluma ce wacce ba ta tsoran Allah. Muguwa kuwa in Allah ya yarda k'arshan ki ya zo don sai na yi sanadiyar ajalinki". Fad'in Julaibib cikin fusata har jikinsa ya soma rawa. Wani irin d'agowa Oumul Sahwat ta yi ta kalli cikin idanuwarsa ya yin da Badakkare ya yi kan shi don sare wuyansa. Sai da wani tsawa da ta daka masa shi yayi saurin dakatar da shi. Jikinta na b'ari ta mik'e cikin iska ta re da nufar in da Julaibib d'in ya ke babu kwayar zarra na tsoro a fuska da zuciyarsa. "Ciro abunda ke wuyarka ka mik'o shi kan tafin hannu yanzu". Fad'in Oumul Sahwat cikin ba da umarni. Wani k'ask'antaccan kallo ya watsa mata ta re da fad'in, "Ba ki isa ba, domin ni ba kya mulkata. Wad'annan su za ki yiwa umarni su bi ba Julaibib ba". Ya k'arisa maganar ya na nuna aljanun da ke tsattsaye wajan. Saurin dafe saitin zuciyarta ta yi saboda jin alamun k'arasowar Sarauniyar Daulatul Bahshan wato Bak'ayatul Mahruri da tawagarta. Cikin sauri ta juya ta re da nufar in da Yousouf ya ke ta zaro wannan takobi a cikin naman hannunta da ke da tsini da tsawo ta soka shi a gefen cikin Yousouf sai da ya fito ta baya ta re da mik'a tafukan hannunta wanda ya yi dogo gar gaban Julaibib ta re da fad'in d'aura min sarkar nan a nan ko ya bar duniya". Cikin sauri Yousouf ya d'ago su ka had'a idanuwa da Julaibib ta re da fad'in, "Idan har cikin zuciyarka ka na k'aunar Rukhsana ina nufin Binty da gaskiya har zuciyarka to ka da ka ba ta abunda mahaifiyata ta ba ka, shi ne lagonta don da shi ba za ta tab'a iya cin galaba a kan ka ba, kuma ko da ta yi maka barazana da wad'anda su ke ta re da kai, ka da ka ji tsoro domin da wannan abun da ke wuyanka babu abunda za ta iya ma su". Fad'in Yousouf daidai lokacin da ta d'aga mashin nan ta so ke shi ta cikin ramin cibiyarshi sai da gudan jini ya fito daga bakinsa............. 🌹 *77-78*🌹 ...............B'angaran Anna kuwa bayan sun ko ma gida hankali ta she ta re da tunanin halin da Binty ta ke ciki da kuma inda sauran y'ay'anta su ke. Fanan kuwa da Anna ke shaida mata duk abubuwan da su ke faruwa, fitsari ta saki a tsaye ba ta re da sanin ta na yi ba saboda firgici da tsoro. Alhaji Usman kuwa, komawa State CID ya yi don shaidawa DG ko mai za'a yi a yi don ganin y'ay'ansa sun dawo gare sa. Hakan ne ya sa aka tsanantawa dukkannin su azaba mai gigitarwa da fitar hayyaci akan sai sun fad'i in da su ka kai su Julaibib, musamman Junaina wanda a gidanta su ka b'ace. An kira Alhaji Saifullahi ta re da kunna masa wannan video na confessing da matarsa da sauran gaba d'aya su ka yi. Kusan haukace masu ya yi a wajan nan ya na ihu ta re da fad'in duk in da y'ar shi ta ke sai an fito masa da ita. Da kyar aka kwantar da hankalinsa ta re da shaida masa duk in da su ke za'a gan su. Cikin hikima DG da alhaji Usman su ka shiga yi wa alhaji Saifullahi nasiha akan irin nu na banbanci akan y'ay'ansa da ya ke yi wanda haka na iya janyo muguwar rikici da tsana tsakanin y'ay'ansa ko da kuwa mahaifiyarsu d'aya. Sosai nadama ta shigi alhaji Saifullahi domin ya san idan da laifin Junaina to tabbas da laifinsa. Abu kamar wasa an yi bincike matuk'a amma ba'a ga in da su Julaibib su ke ba, kuma bincike ya nuna ba su fita daga gidan su Junaina. Wanda hakan ya k'arawa Junaina zargi da su kan su hajiya Mansura da Zuwairah tun da da ma su na cikin k'ungiyar asiri. Tu ni aka tura mota biyar ta re da jagorancin Hajiya Mansura wacce aka ce ta kira meeting d'in gaggawa wanda hakan shi zai ba da umarnin kwamushe duka sauran members d'inta. Sun yi nasarar kwamushe mata ak'alla za su kai guda Hamsin da uku, don motocin da su ka zo da shi ma bai isa ba sai da aka k'aro wasu duk aka watsa su kamar akuyoyi. Anna alwala ta yi ita da Fanan ta re da yin sallah raka'a biyu su ka shiga yin addu'a akan Allah ya kare su a duk inda su ke. *_____________________* A matuk'ar razane da mugun tashin hankali Julaibib ya yi wani irin tsalle ta re da isa wajan da Yousouf d'in ya ke a d'aure. Ya na tab'a wannan kaca da aka d'aure Yousouf da shi kacan ya zube k'asa, Yousouf d'in kuma ya taho gaba d'aya jikinsa ya na wani tari mai fidda guda-gudan jini. Tallabosa Julaibib ya yi idanuwansa sun cika da hawaye, jijiyoyin kansa sun yi burd'in-burd'in ya shiga k'ok'arin b'arke rigar jikin Yousouf d'in. Caraf Yousouf ya rik'e hannunsa ta re da fad'in, "Ka da ka yi k'ok'arin ceto na, ka d'auki Binty da sauran mutane ku gudu. Abun da ke wuyanka ba zai kare ka daga tsafi da takobin sarauniya Bak'ayatul Mahruri ba. Don Allah Ku gudu ka min ta shigo cikin masarautar nan". Fad'in Yousouf jini na b'ulb'ulowa daga hancinsa da kuma bakinsa. Mik'ewa ya yi ta re da sab'a Yousouf a kafad'arsa, ka na ya nufi inda su Binty su ke jikinsu na rama, kama hannun Binty ya yi ta re da kallon sauran ya ce ku biyo baya na, kuma ko wanne a cikinku ya rik'a karanta ayatul qursiyu da duk addu'ar da ta zo bakinku. Ka da Ku yadda bakinku ya yi shuru ba ya ambaton Allah". Gaba d'ayansu a tsorace duk su ka tsaya a bayansa. Ya yin da Oumul Sahwat ta tsaya a gaban Julaibib ta re da fad'in, "Za ka ja ni ka yi nasara saboda abun da ke wuyanka, amma ka sani ba za ka tab'a iya ja da Bak'ayatul Mahruri ba". "Allah ya fi ta domin shi ne mahaliccinta". Fad'in Julaibib ta re da yin gaba. Wani irin ihuu Oumul Sahwat ta yi wanda ya yi sanadiyar mutuwar aljanun dubu biyu. Ta shi sama ta yi ta re da rikita ta koma tsuntsuwa, sai da ta yi nisa a sararin samaniya ka na ta b'ace b'at. Tafiya kawai su ke yi ba ta re da sanin in da su ka nufa ba cikin daji. Wani tsoho ne tukuf ya bayyana a gare su jikinsa duk jini idanuwansa na tsiyayar da hawaye. Nuni ya yi da hannunsa izuwa gangan jikin Yousouf, ta ke Yousouf ya ko ma hannunsa, shimfid'ar da shi ya yi a k'asa ta re da shafa fuskanta. Bud'e idanuwa Yousouf ya yi cike da azaba ya na kallon kakan na sa kuma ya na murmushi kamar bai jin azaba a jikinsa. "Ya kai jika na, ka da ka tafi ka bar ni. Kai ka d'ai ka rage a cikin tsatso na. Y'ata ta mutu ta bar wannan duniyar duk a sanadiyar taimakon bil'adama. Ya Allah ka sa haka ya zama silar shigarta Aljanna". Da gudu Binty ta isa in da Yousouf d'in ya ke a kwance ta na kuka ta re da fad'in, "Ka da ka mutu ka bar ni masoyi, ka manta alk'awarin da mu kai wa junan mu ne? Mun yi alk'awari za mu ra yu da junanmu duk rintsi. Kalla zoben da ka saka min, kalli wanda na saka maka a hannunka". Fad'in Binty ta re da d'aga d'an yatsarsa wanda zoben ke mak'ale. Murmushi ya sakar mata mai cin rai ta re da fad'in, "Mai sona, tabbas ina k'aunarki kuma zan mutu da sonki. Sai dai idan har na kasance da ke Allah ba zai bar ni ba domin na cutar da ke. Wanna na daga cikin wasiyya na k'arshe da mahaifiyata ta bar min akan ka da na bari tsokar da ke k'irjina ta rinjaye ne. Ba zai yu mu rayu ta re ba saboda jinsin mu ba d'aya ba ne. Sai dai ina miki albishir don ki na da wanda ya ke miki k'aunar da na ke miki ko in ce fiye da ni ma". Ya k'arisa maganar ne ta re da kallon fuskan Julaibib ka na ya ce, "Yaya Bibi ga ta nan ka amana, don Allah ka kula da ita fiye da yadda za ka kula da kan ka dan Allah. Ka ba ta soyayya ka da ta yi kuka domin ka". Idanuwan Julaibib ya rine kamar gauta sabida tsabar jan da ya yi. Bai iya cewa ko mai ba sai juya baya da ya yi saboda bai son hawayan da ya ke mak'alewa su zuba. Kuka sosai Binty ta ke yi ta na jijjiga Yousouf ta re da fad'in, "Kar ka bar ni, Yousouf kar ka bar ni dan Allahhhhh". Ta k'arashe maganar da wani irin narkakken kuka mai narka zuciyar mai sauraro. Sabrin ita kan ta kuka ta ke yi sosai ta re da jin tausayin Yousouf d'in da ita kan ta Bintyn. "Su waye iyayena?". Fad'in Binty cikin kuka ta na kallon fuskan Yousouf da shi ma fuskan na ta ya ke kallo. Kallo fuska kaka Yousouf ya yi shikuma ya jinjina masa kai. Dawo da kan shi ya yi wajan Binty wanda a ta re su ka yi haka don Julaibib don jin abunda Binty ta tambaya. Shi kan shi ya na son sanin haka. "Asalin sunan ki Rukhsana wanda haka na gani ajikin showel d'in da aka nannad'e ki da shi, kaka ya tsinci wannan a cikin jikinki". Ya fad'i hakane ta re da yink'uri ya girgiza jikinsa ya fiddo wani k'atotan kwarya wanda a cikinsa akwai kwalliyar d'awisu wanda aka yi sa kamar mafici da kuma wani awarwaro na zinari sai rigan sanyi na yara riga da wando. "Sauran bayani kaka zai miki shi". Hannunta na rawa ta karb'i wannan kwarya idanuwanta na k'ara kwararar da hawaye. Sai da ta d'ad'd'aga kayan ka na ta mai da dubanta izuwa ga kaka, kaka ya bud'e baki zai yi magana barrister Fu'ad ya ce, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!". Da mugun k'arfi ya yin da ya yi wani tsalle domin isa wajan da kaka ya ke ya ture sa, sai dai ka min ya har mashin da Bak'ayatul Mahruri ta jefo ya caki bayansa ya kuma b'ullo ta cikinsa har sai da ya tab'a cinyar Barr Fu'ad da ya isa gaban Kakan. Gaba d'ayansu mik'ewa su ka yi a razane ta re da ja da baya don ganin dandazon aljanun da su ka zagaye su. Hamdan rik'e hannun Julaibib ya yi da k'arfi ya na karanta ayatul kursiyyu ya yin da Binty ta sume sakamakon jinin kaka da ya fallatso ya wanke mata fuska. Barr Fu'ad kuwa k'afafuwansa ke wani irin rawa sakamakon tsoro da kuma azabar da ya ke ji a cinyarsa. B'akayatul Mahruri ce ta k'araso wajan ta re da yin kwallo da gawar Kaka sai da ya lula can sama ka na ya fado bisa bishiyoyin da ke dajin. Sai da ta saita takobinta ka na ta d'aga za ta cakawa Binty a zuciyarta, Julaibib ya yi wani irin tsalle don ture Binty takobin ya sa me shi amma sai Barr Fu'ad ya riga sa takobin ya caki k'irjinsa ta ke ya fad'i ko shurawa bai yi ba. K'arar ballewar wuyarta su ka ji wanda tsabar zuciya Julaibib bai san lokacin da ya yi bismillah ta re da murd'e wuyanta ba. Ta ke ta fad'i k'asa ta na shuru-shuren mutuwa. Yousouf gaba d'aya sauran jarumtarsa ya yi amfani da shi ta re da mik'ewa ka na ya d'auki takobin bak'ayatul Mahruri ya datse mata kai wanda ya yi sanadiyar rusunawar gaba d'aya dakarunta wa Yousouf d'in. Cikin azama Oumul Sahwat ta k'ariso wajan ta re da fad'in, "Lallai dole in mayar da kai matsayin kakan kakanka wato amintaccan bawan masarauta kasancewar jarumi wanda ya kashe azzalumar sarauniyar Daukatul Bahshan. Yanzu aljanun masarautar za su kasance cikin salama da.....". Bai bari ta k'arisa ba ya yi amfani da takobin hannunsa ya fille mata kai saboda hango yadda ta fille kan mahaifiyarsa. K'ok'arin fad'uwa ya ke yi Julaibib ya yi saurin taro shi ya fad'o jikinsa. Magana ya ke son yi amma ya kasa saboda jinin da ke kwararowa daga hancinsa, bakinsa da kuma kunnansa. K'ok'ari ya ke ta yi ka da ya kulle idanuwansa amma ya kasa. Jikinsa ne ya yi nauyi sosai har Julaibib ya ji nauyin ya masa yawa sai da ya kwantar da shi a k'asa idanhwansa na tsiyayar da hawaye. Wani irin guguwa ne ya taso mai k'arfi ya lullub'e su na kusan mintuna goma ka na su ka b'ace b'attt. A nan cikin garden su ka tsinci kan su kamar yadda anan aka kwamushe su. Sabrin sakin wani tsumamman kuka ta yi yayin da ta yi kan Binty da ke yashe a k'asa ba ta numfashi. Julaibib kuwa kan Fu'ad da ke zubda jini ta cikinsa ya yi kuma bai numfashi. Daga Hamdan har Sabrin d'in an rasa wa zai bai wa wani hak'uri. Wayarshi da ke aljihunsa ya ji ya na k'ara wacce ya ma mance da ita a jikinsa ya yi saurin fiddowa ta re da picking call d'in kasancewar daddy ne ya sake kira ko Allah zai sa ya dace. "Ku na ina Julaibib?". Fad'in daddy. "Daddy ka yi sauri akwai matsala mu na gidan su Sabrin". Fad'in Julaibib. Kasancewar alhaji Usman su na ta re da alhaji Saifullahi ta re su ka nufo gidan a mota daban-daban. Hankali ta she su ka nufo garden d'in. Sabrin na ganin mahaifinta ta nufesa da gudu ta rungume ya yin da Alhaji Usman ya yi kan Fu'ad da gudu wanda ke zubda jini. Fu'ad d'in ya fara sawa cikin mota ka na ya saka Binty ta re da kwantar da kan ta jikin motar. Sam ba su lura da wani mutum wanda a k'alla zai yi sa'a da alhaji Saifullahi a gefe ba sai wawware idanuwa ya ke yi ya yi wani irin bala'in rama ta re da fita hayyacinsa. Ko bi takansa ba su ba. Alhaji Usman ya shiga gaban mota ya yin da Julaibib ya zauna a baya ta re kwantar da kan Fu'ad a cinyarsa ya na jin tashin hankali cikin ransa. Alhaji Saifullahin ma sai mota ya nufa Sabrin ita ma ta shiga ta re da kayan Binty da Yousouf ya ba ta cikin kwarya. Hamdan bi ye da ita su ka nufi asibiti. Kai tsaye ICU aka nufi da Barr Fu'ad wanda Julaibib ya kasa shiga sai safa da marwa ya ke yi a ciki. Alhaji Saifullahi kuwa jikinsa rawa ya ke yi don idan Julaibib favourite d'in Anna ne, shikuma Fu'ad d'in ne fav d'in sa. Cikin hukuncin ubangiji doctor su ka samu ceto rayuwar Barr bayan sun masa theater don sakamakon wannan wuk'a da ya soke shi ya b'ula masa hanji. Lokacin da su ka fito daga theather nan k'arfe biyu da kwata na dare saboda sun matuk'ar dad'ewa a ciki tun magriba. Binty kuwa dama suma ta yi sakamakon firgici ita ma dai sai da aka k'ara mata ruwa. Sabrin ke zaune da ita. Hamdan kuwa ta re su ke safa da marwa da Julaibib. ............Can wajan Anna kuwa hankalinta ne ya tsananta tashi saboda ganin har biyu amma alhaji Usman bai dawo ba kuma ta kira wayarsa ta k'i shiga. Fanan ta yi kuka har ta na sik'ewa. Sai da Alhaji Usman su ka yi sallar asuba ta re da tabbatar da farfad'owar Fu'ad ka na ya kira Anna ya shaida mata bayyanar su Binty ta re da fad'a mata Fu'ad na kwance a asibiti. Shi ma dai Alhaji Saifullahi ya kira Hajiya Sakna mahaifiyar Sabrin ta re da shaida mata halin da ake ciki. *MANAGE PLEASE* 🌹 *79-80*🌹 ................Hajiya Sakna ta fito ne ta ga wannan tsamurarran dattijon ya na tafiya da kyar kamar iska za ta hure shi. "Bawan Allah, daga ina haka?". Fad'in mahaifiyar Sabrin ta na mai k'ara k'are masa kallo. Shi dai da idanuwa kawai ya ke bin ta saboda kamar kwakwalwarsa ya tab'u. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Shafi'u! Shafi'u!!". Hajiya sakna ta saki salati ta re da kwalawa driver kira wanda ya zo da gudu ta re da d'an rusunawa ya ce, "Ran ki shi dad'e ga ni. Wani wajan za'a kai ki ne? " Fad'in Shafi'u driver. Nu na wannan bawan Allahn ta yi ta re da fad'in, "Daga ina haka wannan? Yaushe ya shigo gidan nan?". Fad'in Hajiya Sakna ta na nuna shi. "Hajiya gaskiya tun jiya bayan fitar alhaji da hajiya k'arama da kuma wani bawan Allah da su ka fita babu wanda ya sake shigowa". Fad'in Shafi'u. Shuru Hajiya Sakna ta yi, can kuma ta d'auko wayarsa cikin jaka ta kira alhaji Saifullahi ta shaida masa komai. Cikin mintuna talatin ya dawo gidan k'urawa wannan bawan Allahn idanuwa ya yi ya na son ya ga ne ko ya san shi, amma Sam bai ga ne sa ba. "Bawan Allah daga ina?". Fad'in alhaji Saifullahi ta re da ware hannayansa ya na kallonsa. Still shuru sai zare idanuwa ya ke yi. "Ku fita da shi daga gidan nan yanzu" Fad'in alhaji Saifullahi. Hannunsa Shafi'u da mai gadi su ka yi ta re da tura k'eyarsa zuwa waje ka na su ka rufo k'ofa. Asibitin su ka koma, in da su ka taras Binty ta farfad'o sai kuka ta ke yi kamar ranta zai fita. Julaibibi ya shiga d'akin har da turo k'ofa. Hanky ya ciro daga aljihun wandonsa ta re da share mata hawayan da ke zubowa ka na ya ce, "Ki dai na kuka please, kukan ki a nan na ke jin sa" ya k'arisa maganar ta re da nu na zuciyarsa. Mai makon ta yi shuru sai ta k'ara sautin kukan na ta. Rungumo kanta ya yi zuwa k'irjinsa ya shiga bubbuga bayanta ya na mata magana cikin kunnanta. Anna ne da Fanan su ka shigo hankali ta she. Cikin sauri Alhaji Saifullahi ya taro su ya na mai kwantar da hankalin su. Sai washa gari aka ba su damar shiga d'akin da Fu'ad ya ke ciki wanda ta farfad'o sai wajan aikin da ke masa ciwo kad'an-kad'an. Su na had'a idanuwa da Binty ya sakar mata murmushi. Da gudu ta k'arisa wajan gadon ta re da fad'in, "Ya Fu'ad". Sai kuma ta fashe da kuka mai sauti Sabrin da ke gefe ita ma ta saki na ta hawayan. Fanan kuwa k'arisawa wajan Binty ta yi ita ma ta shiga tayata kukan. Da kyar Fu'ad ya iya lallashinsu wanda muryansa ke fitowa dakyar. Satinsa biyu a asibiti aka sallamesa, kuma dalilin ciwona ya sa aka aje komai a gefe har da case d'in su hajiya Mansura wanda ake son tura su koti domin ta yanke masu hukunci. Bayan sun dawo gida da kwana uku, mahaifin Sabrin da mahaifiyarta da ita kan ta Sabrin d'in da kuma y'ay'an aunty Junaina duk su ka d'ugunzuma state CID wanda tu ni Alhaji Usman da iyalansa sun isa can. Videon su Kandala aka sa ke kunnawa, hajiya Sakna da y'ay'an Junaina da kuma Sabrin da ba su ga ni ba su ka sa ke gani. Amrah ba ta gigice ba kamar yadda Hanan ta gigice ba sakancewar ita ta san abunda uwar ta su ta ke aikatawa. Hanan kuwa ihun tashin hankali ta rik'a yi har sai da aka fidda ta zuwa mota. Julaibibi kuwa ji ya ke yi kamar ya fiddo su Kandala ya kashe su. Daga nan gaba d'aya gida su ka dawo anan side d'in bak'i da ke gefen side d'in Anna. Barr Fu'ad shi ya zayyane ma su abunda ya faru a can duniyarsu Yousouf. Gaba d'aya al'ajabi da mamaki ya gama kashe su wanda gaba d'aya sun ka sa magana. Kwaryan da Yousouf ya baiwa Binty, Sabrin ta aje a gaban Anna. Anna ce ta d'auki kwaryan ta re da fiddo kayan ciki ta shiga dubawa. Maficin d'awisun ta d'aga ta yi ta jujjuya shi. Murmushi ta yi ta re da mai da kayan cikin kwaryan ka na ta ce, "Allah ya bayyanar da iyayanki a duk in da su ke". Gaba d'aya da amin su ka amsa ka na Anna ta shiga yi wa Binty fad'a akan b'oye mata wasu abubuwan da ta yi. Daga nan ma ta koma kan Sabrin ita ma ta yi mata fad'a akan duk abubuwan da ta ke yi duk da dai sun ji har da sharrin sammu. Sosai ta ke kuka ta re nuna tsantsan nadama da kuma rok'ar gafarar mahaifiyarta. Shi ma alhaji Saifullahi ya rok'i gafarar mahaifiyar Sabrin. Ta na kukan jin dad'in shiryuwar d'iyar tata ta ce, "Na ya fe mu ku duka, Allah ya yafe mana baki d'ayan mu". Julaibib kuwa hankalinsa ne ya tafi wani waje sabida kallon k'urillan da ya yi ta maficin d'awisun nan da kuma tuno tambarin d'awisun da ya ga ni a k'eyar Binty ranar da ta b'ace ba'a ganta ba. "To wacece wacce na ke ga ni a wonderland?". Fad'in Julaibib cikin zuciyarsa. Bayan Binty ta kasance ita d'aya a d'aki ta fad'a duniyar tunanin ta yadda za'a yi ta gano iyayanta da kuma dalilin yar da ita a bola. B'angaran Fu'ad kuwa ya yi k'ok'ari sosai wajan cire Binty daga cikin zuciyarsa kasancewar ganin soyayyar Bintyn b'aro b'aro cikin idanuwar wan na shi. Sai ya shiga avoiding zama kusa da Binty gudun ta da mashi da miki. Gidan ma gaba d'aya ya dai na zaman sa kullum sai bayan isha ga ke shigowa. ............Kallon tafin hannunsa na dama ya yi ta re da k'urawa rubutun da ke hannun na sa don sanin abunda mahaifiyar Yousouf ta rubuta. Sai dai bai fahimci komai ba. Kallan ruwan zam-zam d'in da ke gabansa ya yi ta re da d'auka. Sai da ya yi bismillah ta re da karanto ayatul kursiyyu ka na ya wanke tafin hannun cikin wani k'aramin jug sannan ya tsiyaye a cikin gora. Aje goran ya yi ta re da shiga cikin bayi don yin kana ya tafi gidan Alhaji Muhammad Ahlam don kai wa Yousouf maganinsa da mahaifiyar Yousouf ta ba shi. Cikin rabin awa ya gama kimtsawa cikin wata gezna dark blue ta re da hula bak'i sai takalminsa halve cover kalar bak'i wanda samansa ya sha stone masu walwali. Kai tsaye fitowa ya yi ya nufi side d'in Anna. Sai da ya kwankwasa sannan ya tura ta re da shiga ciki. Zaune Binty ta ke a kan 1sitter. Riga da straight skirt ne a jikinta irin na y'an kanti. Ba bu d'an kwali a kanta parking d'in gashinta ta yi a tsakiyar kan ta. D'an ramar da ta yi ya k'ara fito da haske da kyawunta earpies mak'ale a kunnanta ta na sauraran wa'azin Yousouf Guruntum mai su na (MAZINACIYA JAKAR GAYU). Har ya iso kan ta ba ta sa ni ba sabida hankalinta gaba d'aya da ta tsayar a wajan wa'azin da ta ke ji. Hannu ya kyasta a fuskanta ta re da zare earpiece d'in kunnanta. Cikin sauri ta d'ago ta kalle shi ta re da saurin mik'ewa tsaye ta na rarraba idanuwa. D'age mata gira ya yi ta re da fad'in, "Mi ye na tsoran to? Ni dodo ne?". Fad'in Julaibib. "Bbb.... Ba komai?". Fad'in Binty cikin in'ina. "Za ki raka ni?". Fad'in Julaibib ya na matsota kamar zai had'e jikinsa da na ta. "A'a". Fad'in Binty had da girgiza kai. "Mai ya sa to?". Julaibib ya sa ke fad'i ta re da kuma matso ta kad'an. "Zan yi aikin a kitchen ne. Zzan yi girki?". Fad'in Binty ta na mai zama jab'ar akan kujeran saboda k'ara matsowa da ya yi. Sabrin da ke mak'ale a bakin k'ofar kitchen sai gimtse dariya ta ke yi sabida kan ya Bibi ya ganta. D'aga k'afarsa ya yi ta re da d'aurawa a kan kujera ta re da fad'in, "Baki ce na yi kyau ba. Na yi kyau??". "Ka yi kyau!". Fad'in Binty da sauri don sabon yanayi da Ya Bibin ke mata kwanan nan. "Ki kula da kan ki, idan na dawo za mu yi hira kin ji". "Ttttt to". Fad'in Binty baki na rawa cike da mamaki. Hura mata iska a fuska ya yi ta re da sauke k'afarsa ya juya ya nufi upstairs don zuwa wajan Anna. Doguwar ajiyar zuciya ta sauke ta re da murgud'a baki ka na ta mai da earpiece d'inta. "Babi!". Fad'in Fanan ta re da nufota da gudu ta rungumeta ta na mai jin dad'i. "Ke dalla menene kuma haka? Menene Babi kuma?". Fad'in Binty. "Au duk kallon Indian ki ba ki san menene Babi ba? To ki je ki yi searching". Fad'in Sabrin ta re da nufar kitchen ta na fad'in, "Kaho na pyar ri heee". Ta fad'i hakane ta re da rungume hannunta a kirjinta. .............."Ummu Julaibib kin tabbata da abunda ki ke fad'amin kuwa?". Fad'in Alhaji Usman. "Eh to, ban tabbatar ba, shiyasa na ke so na je na yi confirming. Shiyama ko a wancan lokacin ban ce komai ba. Amma gaskiya ban kaso sittin ina ji a jiki na ita ce". Fad'in Anna. "To yaushe za mu tafi kenan?". Fad'in Alhaji Usman. "Nan da sati d'aya idan an gama case d'in su Suhail". Fad'in Anna. "Akwai fa abunda ban fad'a miki ba, na saki Mansura saki uku, domin ba za'a yanke mata hukunci da aure na a kan ta ba. Alhaji Saifullahi shi ma ya saki matarsa saki uku kuma ya hana y'ay'ansa ganinta. Na yi na yi da shi ya bar su su je su ganta ya ce su ma y'ay'an ba su son ganinta". "To Allah ya kyauta". Shi ne abunda Anna ta fad'a dai dai lokacin Julaibib ya yi sallama a k'ofar d'akin. Amsa masa sallamar su ka yi ta re da ba shi izinin shigowa. Shiga ya yi ta re da mai man waje ya zauna, sai da ya gaishe su ka na ya ce, "Daddy zan je gidan baba Muhammad in kai wa Yousouf maganinsa". "Alhamdulillah! Da na tun tuni na ke son yi maka magana ka hanzarta ka kai masa don yaron na jin jiki sosai. Allah ya sa dai k'arshan wahalar kenan". A ta re Alhaji Usman da Anna su ka amsa da "Ameen". "Julaibib yaushe za ka fito da matar aure? Na gaji da ganin ka haka wallahi". Fad'in Alhaji Usman. Sosa k'eya ya yi ta re sa sunkuyar da kai ka na ya ce, "In sha Allah nan kusa daddy". Fad'in Julaibib. "Ka bar shi ga shinan ai har k'anwar shi za ta yi ta bar shi ai". Fad'in Anna. "Anna wata k'anwar ta wa ce za ta yi aure?" Fad'in Julaibib. "Binty ce ta samu mijin aure". Fad'in Anna. "Binty kuwa? Yaushe? Waye shi wannan mara kunyar? Kuma kun yarda Anna. Ni wallahi ban yarda ba yasin". Fad'in Julaibib hankali ta she. Anna da Alhaji Usman gimtse dariyarsu su ka yi, ya yin da Anna ta ce, "Kai a wa kenan da za ka ce baka yarda ba". "Auranta zan yi, wallahi ina son ta tun ranar da fara ganinta. Anna dan Allah Ku taimake ni ka da in rasa Binty". Anna da Alhaji Usman sun kasa rik'e dariyarsu su ka bushe da dariya. Sai alokacin Julaibib ya ga ne tsokalarsa su ye yi. Saurin mik'ewa ya yi ta re da ficewa daga d'akin. Kai tsaye gidan Alhaji Muhammad Ahlam ya nufa. Kasancewar ya kira alhaji Muhammad d'in ya shaida masa da zuwansa. Ya na isowa aka shiga da shi d'akin da Yousouf ya ke a kwance kamar gawa. Sai da yi addu'a sosai ka na ya bud'e bakinsa ta re da tsiyaya masa cikin bakinsa dakyar kasancewar ya dates bakinsa. Cikin hukuncin ubangiji ko minti d'aya ba'a yi ba k'afafuwansa su ka fara motsi. Daga bisani ya d'aga hannunsa na dama. Can kuma ya juyo da kansa bakinsa na motsawa ya na karanto salati ta re da mik'ewa ya zauna digirgir. Gaba d'aya gidan nan ya haukace da ihun murnan Yousouf ya dawo cikin hayyacinsa. Ya na mik'ewa ya yi sujjada ta re da fashewa da kukan murna. Nan aka yi ta murna da koke-koke. Sab'ule jikinsa ya yi ta re da guduwa don barin y'an uwa su yi murna da kyau. A hanyarsa na dawowa wajan traffic kasancewar an dakatar da shi. Juya kansa ya yi ya kalli gefe ta re mayar da kan shi ga titi. Cikin sauri ya k'ara kallon gefen da ya kalla. Tabbas ita ce dai dai lokacin kuma aka ba su umarni su wuce. Da wani irin gudu ta figi motar, shi ma kuwa da gudu ya bi bayan motar kamar. A wani katon gate ta yi horn mai gadi ya wangale mata gate d'in. Ta na danna hancin motar shi ma ya na biye da ita a baya. *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *81-82*🌹 ...............Har zai tura motar cikin gidan sai kuma wani zuciyarsa ta hane sa. Dakatawa ya yi ta re da yin reverse ya yi parking ta re da fitowa daga cikin motar. Wajan driver ya nufa da sauri wanda ke k'ok'arin rufe gate d'in. "Bawan Allah dan Allah minti d'aya". Ya fad'a ya na d'an yin gaba. Washe baki mai gadi ya yi ta re da fad'in, "Ai na san mai ya kawo ki, ai Rauhiyya haka ta ke had'a go-slow a cikin gidan nan. D'aga kai gare ta ga yauk'i kamar kub'ewa. Amma ai na ga kai d'in ka had'u watak'ila kai ka yi da ce". Fad'in mai gadi ba ta re da an tambayesa ba. "Nan ne gidan su kenan?". Fad'in Julaibib ya na kallon cikin gidan cike da tsananin mamakin kenan Binty twins ne. "Eh nan ne gidan iyayanta". Fad'in mai gadi. "Nagode da ma abunda zan tambayeka kenan". Fad'in Julaibib ta re da komawa wajan mota ya shiga. Kai tsaye gida ya nufa cike da tunanuka cikin ran shi. "Rauhiyyah!" Ya maimaita sunan cikin zuciyarsa ya na mamakin wannan wani irin suna ne. A duniyar aljanu Yousouf ya ce masa ainahin sunan Binty Rukhsana, sai ka ce wasu india, yanzu kuma ya ji wani wai Rauhiyyah. Ya na isa gida ya haura sama. Anna na nan sai dai alhaji Usman bai nan. Knocking bedroom d'inta ya yi, ita kuma ta ba shi izinin shiga. "A'ah, har ka dawo?" Fad'in Anna. "Anna ni fa ina tunanin na ga iyayan Binty na asali". Fad'in Julaibib. Zaro idanuwa Anna ta yi ta na kallonsa ta re da fad'in, "A ina kenan? Ya aka yi ka san su d'in iyayanta ne? Wani alama ka gani?". Fad'in Anna. Nan ya kwashe labarin Rauhiyyah tun ranar da ya fara ganinta a wonderland har zuwa yau da ya bi ta a baya. Anna har ta na watsar da kayan da ke hannunta wajan mik'ewa tsaye. "Maza muje ka kai ni gidan yanzun nan". Ta fad'i hakane ta na lalubar wayarta a kan gado ta dannawa alhaji Usman Kira ta re da shaida masa abunda Julaibib ya fad'a mata. "Ku jira gani nan zuwa yanzu mu tafi ta re". Fad'in Alhaji Usman. Katse wayar Anna ta yi ta re da fitowa daga bedroom d'in Julaibib bi ye da ita a baya. D'akin Binty Anna ta shiga ta re da fad'in, "Binty fito za muje wani waje yanzu". Caraf Fanan ta ce, "Anna ni ma za ni dan Allah". To duk ku fito my tafi. Gaba d'aya parlourn k'asa su ka sauko dai-dai lokacin da Barr Fu'ad ya shigo d'akin shi ma. Nan Anna ta shiga shaida masa an gano iyayan Binty. Sosai ya ji dad'in ya kuma ce ta re da shi za'a je. Fanan ma sai murna ta ke yi an gano iyayan Binty. Binty kuwa ba za ka ce ka yanayin da ta ke ciki ba. Walau farin ciki ko akasin haka. Cikakkiyar mintuna talatin ba'ayi ba Alhaji Usman ya shigo gidan. "Ni fa duk na rud'e Na'ima, ya aka yi hakan to?". Fad'in alhaji Usman ya na kallon Anna. "Shssssss! Muje ka wai" Fad'in Anna. Gimtse sauran maganarsa ya yi, ya yin da Barr Fu'ad ya kalli Julaibib, shi kuma Julaibib ya kalli Anna da Daddy. Anna d'aura fuska ta yi ta re da yin sama ta d'auko wannan kwarya da Yousouf ya baiwa Binty ka na ta fito. Fanan ta rik'o hannun Binty su ka fice. Julaibib shi ne na k'arshan fita ya na son ga no abunda su Anna ke b'oyewa amma ya kasa kuma tabbas ya san da wata a k'asa. Shi ya masu jagora har gidan da ya ga mai kama da Binty wato Rauhiyyah. Horn ya yi mai gadi ya wangale gate su ka shi ga ta re da parking ka na gaba d'ayansu su ka fito. Hannu Julaibib ya d'aga ta re da yafito mai gadi. Cikin sauri ya k'ariso wajansu. "Ahh! Hajiya wallahi ban ga fitarki ba, ta ina ki ka fita to?". Fad'in mai gadi ya na kallon Binty. D'auke kai Binty ta yi ba ta re da ta fahimce abunda mai gadin ya ke nufi ba. "Dan Allah sallama za ka yi mana da mai gidan nan idan ya na nan". Kallon Binty mai gafi ya sake yi ya na son cewa ga Rauhiyyah ai ba sai ya yi masu iso ba. Amma kuwa sai ya juya ta re da nufar cikin gidan. Danna k'ararrawar k'ofar ya yi, second goma wani kyakkyawan yaro ya zo ya bud'e masa k'ofar. "Fakarar yaron kirki kai ne?". Fad'in mai gadi. "Ni ba sunana Fakahar ba Fakhri, understand?". Fad'in kyakkyawan yaron. Washe baki mai gadi ya yi ta re da fad'in, "To fakare, wasu bak'i ne a waje ke sallama da Babanka su na waje, amma fa har da auntynka Rauhiyyah". "Aunty na na d'aki ta na wanka. Ba ita ba ce". Fad'in Fakhri. "To je kira babanka ka ce ya yi bak'i". Fad'in mai gadi ba don ya yarda da abunda Fakri ya fad'a ba. Zai juya kenan ya hango Rauhiyyah sanye da doguwar rigar material pitch colour kan ta sanye da hula mai kunnuwa hannunta rik'e da laptop ta na dannawa. "Wa'innahu sulaimanu!". Fad'in mai gafi ta re da mitsittsike idanuwa ya na k'ara dallarosu ya na kallon Rauhiyyah da har ta zauna a kan kujera ta mai da laptop d'in bi sa cinyarta ta na danne-danne. "Aunty Rauhiy, wai Bala ya ce wasu na nai man daddy kuma har da ke a wajan". Fad'in Fakhri. D'ago da idanuwanta ta yi wanda ke d'auke da zara-zaran gashin idanuwa ta sauke a kan bakin k'ofar ta re da fad'in, "Kai ban san shirme, zo ka wuce ka je ka fad'awa daddy ya yi bak'i awaje". Ta fad'i hakane ta re da mai da kallonta izuwa ga laptop d'in ta. Cikin sauri mai gadi ya juya ta re da nufar wajan da su Binty su ke domin tabbatar wa idanuwansa abunda ya gani. Har ya na tuntub'e saboda tsabar kallon da ya ke wa Binty. "Matsowa kusa ya kamata ka yi sai ka k'are mata kallon da kyau". Fad'in Julaibib fuska a d'aure. "Auu... Ummm amm yanzu zai fito in sha Allah". Mai gadi ya sake fad'i har ya na cin tuntub'e saboda kallon Binty da kuma mamakin kamannin da su ke yi da Rauhiyyah idan akwai abunda ya fi y'an biyu to sun fi haka. Tsayin, hasken fatan, kamannin da yanayin k'iran jikinsu duk iri d'aya ne. Juyawa Binty ta yi ta had'a kai da mota dai-dai lokacin da wani mutum fari tass dogo siriri ya fito hannun shi sab'e da wata kyakkyawan yarinyar da ba za ta wuce 3years ba a kafad'arsa fuskansa fad'ad'e da farara. "Assalamu alaikum, sannunku da zuwa". Ya fad'a ya na mai mik'awa Julaibib da Fu'ad hannu. Daddy ma saurin mik'a masa hannunsa ya yi su ka yi musabaha. Anna ma ta yi saurin gaishe sa, dai-dai lokacin da Binty ta juyo kuma idanuwansu su ka had'u cikin na juna. Yarinyar da ke hannunsa sai da ta kusa sub'ucewa Julaibib ya yi saurin taro ta. Bakinsa na rawa ya ke nuna Binty da ita ma kallon na sa ta ke yi, "Rauhiyyah! Wannan ai Rauhiyyah ce. Amma kuma ai a parlour na baro ta ta na danna laptop". Dafasa Alhaji Usman ya yi ta re da fad'in, "Kwantar da hankalinka, abunda ya kawo mu kenan, wannan ba Rauhiyyah ba ce, kamannin jini ka ke gani". Shuru bawan Allahn nan yi jikinsa na b'ari ya na kuma k'ara kallon Binty da ita ma shi d'in ta ke kallo. Da ky'ar ya iya bud'e baki ya ce, "Muje daga ciki to". Ya fad'i hakane ta re da yin gaba su na biye da shi a baya. Amma duk tafiya sai ya juyo ya kalli Binty. Parlourn bak'i ya kai su ka na ya fito kasancewar yarinyar da ya rik'o a ta na hannun Julaibib. Har da gudu-gudu ya k'arisa gaban k'ofar part d'in cikin gidan ta re da murd'a handle d'in ya shiga. Da gudu ya haura sama. Rauhiyyah da ke danne-danne ta d'ago ta kallesa ta na mamakin mai ya faru ya saka Da-da gudu haka. "Rahima fito fito ki zo muje ki ga abun al'ajabi da mamaki yau". Fad'in Da-da ya na mai ka mo hannun matarsa da ke bakin gado ta na warware wani zani. Sakin zanin ta yi ta re da bin sa a baya. Su na saukowa parlourn ya kamo hannun Rauhiyyah da d'ayan hannunsa. Aje laptop d'in ta yi ta re da bin sa ba ta re da ta ce ko mai ba. Parlourn bak'in su ka isa gaba d'ayansu. Numfashin Rahima kusan tsayawa cak ya yi sakamakon arba da Binty da ta yi. Yayin da Fu'ad, Binty, Fanan, da Anna su ka mik'e cike da zallar mamaki su na kallon Rauhiyyah da ke tsaye a bakin k'ofa. "Inna lillahi!". Fad'in Fu'ad cike da wani irin mamaki kamannin Binty da Rauhiyyah. "Binty! What am I seeing. Subhanallah! Wallahi komai iri d'aya". Fad'in Fanan. Binty kuwa a hankali ta ke takawa har gaban Rauhiyyah ta re da kama hannunta hawaye na zuba daga idanuwanta. Rauhiyyah kuwa kallon zallar mamaki ta ke yi wa Binty ko kyaftawa ba ta yi. "Qalby da ma ba ni kad'ai ki ka haifa ba? Da ma mu twince ne? Ya aka yi haka?". Fad'in Rauhiyyah ta na kallon mahaifiyarta hawaye na ziraro daga idanuwanta. Wani irin rushewa da kuka Rahima ta saki ta re da k'arisawa ta rungumesu duka a jikinta kamar ranta zai bar jikinta. "Shikenan lokacin rabuwarmu ya yi Rauhiyy. Dan Allah ka da ku kwace Rauhiyy ku bar min ita har na aurar da ita". Fad'in Rahima ta na kuka sosai. Kallon kallo aka shiga yi tsakanin Julaibib, Fu'ad da kuma Fanan. Anna da Daddy kuwa wani murmushin da su kad'ai su ka san nufinsa su ka yi. "Qalby mai ki ke fad'i haka? Kamar ya su bar miki ni har ki aurar da ni, mai hakan ya ke nufi? Dan Allah ka da Ku ce min ba Ku kuka haife ni ba". Fad'in Rauhiyy ta na kuka sosai da ya zawo hankalin Mas'ud da fitowarsa kenan daga part d'insa zai shiga main part. Cikin sauri ya k'ariso parlourn don sanin abunda ke faruwa. Cak ya tsaya har ya na wani lilo kamar zai kifa k'asa saboda gigicewa da kuma mamakin ganin Rauhiyyah ta zama biyu. Hannu biyu ya kai ya yi weaving a dai-dai fuskan su duka don ganin idanuwansa ke masa gizo, ko kuwa dagaske ne. "Momma dan Allah idona ne ke da matsala ko kuwa abunda na ke ga ni gaskiya ne?". Fad'in Mas'ud. "Dan Allah duk ku nutsu ku zauna ayi komai dalla-dalla. Ku nutsu dan Allah". Fad'in Alhaji Usman. Kowa samun waje ya yi ya zauna ya yin da Mas'ud d'osana d'uwawunsa ya yi a kan kujeran don ya na cikin mamaki kuma ya na buk'atar a warware masa komai. "Dan Allah bawan Allah mu na san jin ta yadda wannan yarinya ta zo hannunku". Fad'in Alhaji Usman ya na kallon bawan Allahn nan. Ajiyar zuciya ya saki ta re da fad'in, "Mu y'an asalin Adamawa state ne, aiki ne ya dawo damu nan garin shekaru sha bakwai bakwai da su ka wuce. Tun bayan haihuwar Mas'ad Allah bai sa ke ba mu haihuwa ba wanda shi kan shi Mas'ud d'in sai da mu ka shekara Bihar ni da matat ka mun Allah ya ba mu cikinsa. Mas'ud sai da ya cika shekara bakwai sannan matata ta sa ke samun wani cikin. Lokacin da cikinta ya isa haihuwa, cikin dare wajajan sha biyun dare nak'uda ya ka ma ta. A rud'e na d'au mota mu ka nufi asibiti mafi kusa da mu. Muna zuwa cikin ikon Allah ta haihu lafiya sai dai d'iyar ba ta zo da rai ba, matata ta yi kuka sosai saboda ta kwallafa rai musamman ma da ta kasance mace kuma ta na son d'iya mace.. Kasancewar matata ta haihu lafiya sai ta ce a ba mu gawar kawai mu koma gida tun da dai lafiyar ta k'alau. Haka aka yi duk da sun so rik'e mu zuwa safe. To ahanyar mu ta dawowa mota ta tsaya mana dai-dai wajan wani bola, fitowa na yi don duba motar gashi dare ya yi don d'aya ta wuce da minti arba'in. Kukan jariri muka ji wanda ya firgita mu don duk a tunanin mu jaririyarmu ce. Sai dai jin kukan ba daga cikin mota ya ke fitowa ba sai hankalinmu ya k'ara tashi. Ita ta umurce ni da na duba kasancewar shekarar an yi yayin haihuwa a jefar da jariri. Cikin sauri na zagaya na aikuwa na yi arba da jaririya sanye cikin kayan sayin nannad'e da showel da kuma wani mafifici na d'awisu da kuma warwaro na zinari wanda aka rubuta sunan jaririyar a tsakiya. A nan ne muka san asalin sunanta kuma ba mu canza mata ba, yanzu haka ma su na d'aki na zan d'auko su. D'auko jaririyar na yi na kawo wa matata cikin mota. Cikin ikon Allah ina shiga na kunna motar ta ta shi mu ka nufi gida. Cikin daran nan muka yanke hukucin rike ta. Kuma a daran matata Rahima ta so ma shayar da Rauhiyyah wanda haka ya k'ara shak'uwa tsakaninsu. Kuma ba mu shaidawa kowa cewar ba y'ar mu ba ce. Washagari mu ka na sanar da dangi da abokai cewar ta haihu y'an biyu amm d'aya ba ta zo da rai ba. Sosai aka yi shagalin suna, cikin ikon Allah kuwa ba mu cika shekara ba aka canza min wajan aiki zuwa nan garin abuja". ..........Mik'ewa Rauhiyyah ta yi jikinta na rawa, can kuma ta tafi luuuuu ta suma. Cikin sauri Julaibib ya shiga ba ta taimakon gaggawa. Ba ta jima ba ta farfad'o ta na sakin kuka ta re da k'ank'ame uwar rik'onta ta na wani irin narkakken kuka. "Qalby ki ce mafarki na ke yi dan Allah. Ku ce ku ne ainahin mahaifa na dan girman Allah. Zan mutu idan Ku ka ce ba ki ne iyaye na ba". Fanan da Binty, Anna da mahaifiyar rik'on Rauhiyyah kuwa kuka su ke yi su ma sabida Rauhiyyah ta ba su tausayi sosai. Dakyar aka su daddy su ka lallashe su. Nan Anna ita ma ta kwashe duk labarin Binty ta shaida masu. Sosai su ka shiga tashin hankalin shin su waye aihanin iyayan Binty da Rauhiyyah. "Ina son mu yi magana a keb'ance ni da Ku ban da yara" Fad'in Allah. Mahaifin Rauhiyyah saurin ta shi ya yi ta re da fad'in, "To ku fito muje wancan side d'in sai muyi magana". Duk ta re su ka fice daga d'akin. Sun kai kusan awa d'aya ka na su ka fito daga cikin d'akin. Sallama Anna su ka masu su ka fice don komawa gida. Kasancewar Anna za ta yi tafiya nan da sati bayan yanke hukunci a kotu. *KOTU* *PAID BOOK* : 🌹 *83-84*🌹 *KOTU* .............Cike yake mak'il da jama'a. Daga can gaba kuwa, lauyoyi ne daga ciki kuwa har da Barr Fu'ad da abokan aikinsa. Daga can gefe kuma wajan tsayiwar wad'and'a ake tuhuma, Suhail ne sanye da sark'a, su hajiya Mansura kuma gaba d'aunsu hannunsu sanye da ankwa ta re da dandazon members d'in su. Alk'aline ya shigo gaba d'aya kowa ya tashi. Bayan ya zauna sai ko wa ya zauna, ka na mai karanto k'ara ya karanto k'ara. Daga kan su Hajiya Mansura aka fara, alk'ali ya kalli Hajiya Mansura kasancewar ba su d'auki lauya ba ta re da fad'in, "Shin kun amince da duk abubuwan da aka karanto ko kuwa Ku na da ja, kuma Ku na da lauya ne?". "A'a ya mai girma mai shari'a ba mu da ja, duk abunda aka karanto mun aikata". Fad'in Hajiya Mansura ta na sharar hawaye. D'an rubuce-rubuce mai shari'a ya yi ta re da kallon Suhail ya ce, "Kai kuma fa, ka na da ja da abubuwan da aka kama ka da su a d'aki, kuma mai yasa ka ke aikata ta'addacin a k'asarka?". Kuka Suhail ya soma yi ta re da fad'in, "A gafarce ni ya mai girma mai shari'a, wallahi ban rasa komai ba daga wajan mahaifina ba, sharri shad'an ne da kuma sharrin abokai". Fad'in Suhail ta re da rushewa da kuka. D'an rubuce-rubuce alk'ali ya sake yi ta re da fad'in, "Ke kuma baiwar Allah menene ribar ki na d'aukar y'ay'an mutane Ku na tura su aikatau da kuma jefa su cikin wasu munanan harkan". Alk'ali ya fad'a ta re da kallon Kandala da sai zazzare idanuwa ta ke yi. "Ya mai girma mai shari'a yasin-yasin sabida kud'i ne. Son kud'i ne ya yi min yawa ga shi zai jawo min k'arewa a gidan yari. Don Allah Ku yi min rai". Fad'in Kandala cikin Kuka. Jinjina kai alk'ali ya sa ke yi ka na ya yi y'an rubuce-rubuce ka na ya d'ago ta re da fad'in, "A bisa duba da kuma hujjojin da kotu ta gabatar da kuma amsa laifin da masu laifin su ka yi, kotu ta yankewa Suhail Usman mai rabo hukunci shekara goma sha biyar gidan yari ta re da horo mai tsanani, sannan kuma ta kotu ta sake yankewa Hajiya Mansura da tawagarta shekara goma sha takwas-takwas a gidan yari su ma da horo mai tsanani. Ita kuma Kandala kotu ta yanke mata shekara uku a gidan yari. Alhaji Mudi kuwa wanda Suhail ke kai masa makamai shi kuma ya baiwa y'an ta'adda da muke fama da su a k'asarmu, shi ma kotu ta yanke masa shekara ashirin a gidan yari da horo mai tsanani. Allah ya sa hakan ya zama izina ga wad'anda su ke son aikata irin wannan rayuwa da ma Wanda su ke ciki su tuba su sai da. Courttt". Ya na gama fad'in haka ya bubbuga sandar gabansa ta re da mik'ewa. Gaba d'aya kotun ta hargitse da hayaniya wasu na tsine masu, wasu ba jin tausayi. Yayin da Kandala ke ta sakin zawo a jiki, Suhail kuwa suma ya dunga yi, su Hajiya Mansura kuwa sai kuka su ke yi. Ya yin da Amrah da Hanan ke kuwa kamar ran su zai fita saboda hukunci da aka yankewa mahaifiyarsu domin uwa uwa ce. Alhaji Saifullahi ya rungumesu a jikinsa ya na lallashinsu ta re da alk'awarin kyautata masu da kuma sauke dak wani hak'k'i na su da ya rataya a wuyansa kamar yadda zan yi wa Sabrin. Ya kuma k'ara da alk'awarin yin adalci tsakaninsu da Sabrin. Ita kan ta Sabrin d'in kuka ta ke yi sabida ganin halin da y'an uwanta su ke ciki. Kuma ba ta tab'a sanin haka ta ke jin su cikin zuciyarta ba sai yau da wannan al'amari ya kasance wanda ita Amrah ta na daga cikin sanadin tonuwar asirin mahaifiyarsu duk da ita ta ce ta yi don kub'utar mahaifiyarsu daga halaka ne ganin za ka saka rayuwarta da na su da kuma wacce ba ta ji ba, ba ta gani ba a bala'i. Julaibib kuwa ya na daga can sama Binty (Rukhsana) na kusa da shi ya hana ta ko motsi, shi kuwa Fu'ad sai satan kallon Rauhiyyah ya ke yi, da sun had'a idanuwa sai ya yi saurin kau da kai. Kasancewar ta na da miskilanci sai ta yi kamar ba ta san ya na kallonta amma kuma ita ma ta na kallonsa da gefen idanuwanta duk motsinsa. Shi dai Fu'ad zai ita cewa idan aka shak'e shi ba zai ce ga hukunci da aka Yankewa su Suhail ba. Duk da ya na gaba, amma idanuwansa na baya wajan Rauhiyyah inda ta ke zaune da Rahima mahaifiyar ruk'onta. ...........Bayan sun baro kotu, gaba d'aya gidan Alhaji Usman mai rabo su ka nufa har da su Rauhiyyah da kuma su Binty nan aka k'ara jajantawa juna. Alhaji Usman ya kira kaf ma'aikatan shashin Hajiya Mansura ya sallame su, ka na ya kira Fasila da Wasila gaban kowa ya nuna masu duk abubuwan da su ke yi a cikin gidan ta re da sallamarsu bayan ya biyasu albashinsu har da k'ari ta re da yi masu dogon nasiha. Wasila da Fasila har da kuka da majina ta kuma kasa had'a idanuwa da Anna. Har gaban Anna ta je ta duk'a ta na kuka majina na bin hancinta ta ce, "Hajiya ki yi wa girman ubangiji ki yafe min duk abubuwan da ba aikata miki wanda ki ka sani da wanda ba ki sani ba dan soyayyar Allah da ke wa manzo SAW". "Ba komai Fasila Allah ya yafe maka baki d'aya ke kuwa Allah ya sa sanadin shiryiwar kenan". Fad'in Anna. Kayansu su ka tattaro daga maid parts su ka fice daga gidan cike da takaicin abunda su ka aikata ga shi ba su ci ribar komai ba sai tarin kunya da takaicin da da na sani. Bayan sun ci sun sha, Fanan ta zo ta duk'a gaban Maman Rauhiyyah ta re da fad'in, "Mommah dan girman Allah ki bar mana Rauhiyy ta kwana biyu a gidan nan mu sa ba da juna dan Allah". Fad'in Fanan a marairaice. Murmushi ta yi ta re da shafa kan Fanan ta re da fad'in, "Ba komai Fanan ga Rauhiyy nan ta zauna da ku tun da ma Anna tafiya za ta yi jibi sai ta taya Ku hira ta kuma saba da tagwainiyarta". "Anna wai ni da ita wanene babba? Ni ce ko?" Fad'in Rauhiyyah ci ke da son girma". "Ke dallah matsa can, ana ganin mu an san ni ce babba kwarankwatsi". Gaba d'aya dariya su ka fashe dashi saboda tuno masu da Buba mai kwarankwatsi da ta yi kasancewar sun ba su labarin sa. "Allahu masanin gaibu". Fad'in Anna ta na dariya don ta ga alamu daga Rauhiyy har Binty akwai son girma. Sai dai Rauhiyyah ita ta na da kyaliya da kuma rashin son magana idan ba ta ga dama ba, amma Binty ita uwar aku ce sanna ba ta da kyaliya. Ranar dai a nan gidan aka bar Rauhiyyah, Sabrin, da kuma twince wato Amrah da Hanan. Wuni su ka yi a d'aki su na hiran school da kuma tuno halayan Sabrin d'in a da. Ita kan ta dariya ta ke yi sosai sai ta ji kamar ba ita ba ce ta yi hakan. Sai cin abinci da sallah ke tada su. Barrister Fu'ad da Julaibib ranar wuni su ka yi a parlour su na lek'en upstairs ta inda Rauhiyyah da Binty za su fito su kuma su can sama su na jirarsu ta mata har da shewa don't su na jin muryansu daga nan parlour. ...........Ranar da Anna za su tafi kasancewar jirgi za su bi ita da alhaji Usman d'in, kiran Julaibib ta yi har d'aki. Bayan ya shigo ya zauna ta kallesa ta re da fad'in, "Alhamdulillah zan ta fi yau, kuma kai ne babba na san mahaifinka ya fad'a maka abunda zan je yi, sabida haka daga nan ka min na dawo, ka tabbatar ka fayyace sirrin zuciyarka idan ba haka ba ina dawowa zan ba ka mamaki". Fad'in Anna ba ta re da ta k'ara kallon inda ya ke ba ta sauka k'asa. Gaba d'ayansu su ka raka Anna da daddy zuwa airport. Rauhiyyah, Sabrin, Hanan da Amrah a motar Fu'ad yayin da Anna Binty da daddy a motar Julaibib. Ba su baro Airport d'in nan ba sai da su ka ga tashin jirginsu Annan. Kuma ka min Anna ta wuce sai da ta k'ara jajjadawa Julaibib maganarsu na d'azu. Wajan dawowa Binty ta nufi wajan motar Barr Fu'ad amma ka min ta isa wajan ta ji muryan Julaibib d'in na fad'in, "Hayatiey zonan". Sai da ta waiga dama da hagu ka na ta kalli gabanta ko a kwai wata amma ta ga wayam ka na ta kalli Julaibib ta re da nuna kan ta da d'an yatsa ka na ta ce, "Ya Bibi ni ka ke kira". Ta fad'in hakane ta re da zaro idanuwa. Shi ma waro mata idanuwan ya yi ta re da jinjina mata kai. Kanta ne ya d'aure duk ta daburce. "Hayatiey" Ta maimaita sunan cikin zuciyarta. "Ki zo a motata za mu koma? Ko da ma a wancan motar Ki ka zo airport d'in?". Fad'in Julaibib. Girgiza Kai ta yi ta re da dawowa har in da motar ta ke kanta kuma a d'aure. Bud'e motar ta yi za ta shiga ta ji muryan Fanan da k'arfi ta na fad'in, "Babiiiii". Saurin juyawa Bintyn ta yi ta re da zabga mata harara. Julaibib kuwa da ya san ma'anar babi d'in jinjina ya yi mata da babban d'anyatsarsa wanda ya sa ta zaro idanuwa don ba ta tab'a tunanin zai yi mata hakan ba a yadda ta san ya Bibi mara wasa. "Ba gida mu ka yi ba daga nan mun tafi shan ice-cream". Fanan ta sa ke fad'i ta re da shigewa motar Fu'ad. Langwab'ar da Kai ta yi ta re da fad'in, "Please yaya Bibi in bi su?". "Please Hayatiey ka da ki bi su ni ma zan kai ki wajan shan ice-cream d'in". Fad'in Julaibib kamar yanda ita ma ta yi maganar. Zaro idanuwa ta yi ta re bud'e baki ta na kallonsa. Hannu ya saka ya rufe mata bakin ta re da nuna mata cikin motar. Shiga ta yi ta na kallonsa har kan ta na buguwa da saman motar. "Aauch!". Su ka fad'a a ta re kamar wani shi ya bige. "Ki yi a hankali ka da ki jimin ciwo ki jawo min aiki Kin ji Nuriyyah". "Biyu kenan". Fad'in Binty cikin zuciya da ba ta san ma ya fito fili ba. "Ai idan dai sunaye ne za ki ji fiye da d'ari ma". Fad'in Julaibib ta re da rufo motar ya zagaya ya shiga mazaunin driver. Kallonsa ta ke yi ko kyaftawa ba ta yi sabida tsantsan mamakinsa. Hura mata iska a idanuwanta ya yi ta re da fad'in, "Ya dai? Wannan kallon fa Khairiyyah". "Na shiga uku". Fad'in Binty ta re da saurin saka kan ta tsakanin cinyoyinta gabanta na fad'uwa. Dariya ya yi ta re da jan motar bai tsaya a ko ina ba sai wani park d'in da duk yawonsu da Barr Fu'ad ba su tab'a zuwa ba. Wajan ba hayaniya sosai irin wajan da manyan mutane su ke zuwa ne. Wajen wani shukoki flowers ma su kyau ya kai ta. Sosai wajan ya burgeta har ba ta san lokacin da ta fara murmushi ba. Jin mutum kawai ta yi a bayanta ya na fad'in, "Wajan ya k'ayatar da ke ko? Zan rik'a kawo ki bayan auran duk weekend". Ya fad'i hakane har ta na jin sautin fitar numfashinsa a wuyanta. Wani irin saurin juyowa ta yi ta re da zaro idanuwa sabida kalmar bayan mun yi auran da ya ce har sai da ta bugu da k'irjinsa kasancewar ya na gab da ita sosai. Wayarsa ya yi saurin d'agawa ta re da yi masu salfie a hakan yadda su ke. Saurin ja baya ta yi nan ma ta yi baya da yawa saura kad'an ta kai k'asa ya yi saurin rik'o hannunta ta re da jawota jikinsa gaba d'aya. Waro idanuwa ta ta yi ta re da rasa inda za ta saka kan ta don wani irin kunya, tsoro da mamaki da su ka taru mata lokaci guda. Juyata ya yi ta kalli gabanta yayin da ya rungumo waist d'in ta ta re da d'aura Kansas a kafad'arta sai da ta waro idanuwanta. "Ina son kin tun ranar da na fara ganinki. Ke ce farin ciki na. Ban tab'a son wata mace a rayuwata ba sai ke, ina son ki kasance matata sirrina kuma uwar y'ay'ana. Ki ba ni soyayyar ki dan Allah ba don wanini dalili ba Binty. Ka da ki cuci kan ki, ki soni dan Allah ba don wata alfarma ba kin ji". Ya fad'i hakane ta re da sake mata nauyin Kansa a kafad'arta sai da ta yi kamar za ta zame a hannunsa ya yi saurin k'ara damk'o waist d'in ta. Ita kuwa kunyace mai tsanani ta dabaibayeta ta re da jinta a wani yanayi daban ga kuma wani abu da take ji tun daga kwakwalwar kan ta wanda ba ta tab'a jin sa ba. Sakinta ya yi jin yadda jikinta ke rawa sosai. Aikuwa ya na sakinta ta yi saurin yin gaba ta re da b'oyewa a jikin wata bishiya da ke gabansu kad'an ta re da dafe k'irjinta ta na sauke numfashi. D'an lek'o da kanta ta yi, karaf su ka had'a idanuwa ya na sakin murmushi, saurin komawa ta yi ta na k'ara dafe k'irjinta ta re da zaro idanuwa. "A'a wannan ba yaya Bibi ba ne Allah. Mafarki na ke yi". Ta fad'a k'asa-k'asa. Can kuma ta kai hannu ta re da tsungulin hannunta don tabbatar da mafarki ne ko gaske. "Aauch!" Ta fad'a sabida zafin da ta ji. Saurin isa wajan ya yi ta re don sanin abunda ya sa me ta. Su na had'a idanuwa ta yi sauri rufe idanuwanta ta re da juya baya ta rungume bishiyan. Sosai ta ba shi dariya. K'arasawa wajan ya yi ta re da juyota ka na ya ce, "Ke dan Allah tun 1888 aka dai na wannan gulmar da kinibibi. Idan ki na sona kawai ki fad'a babe". Ba ta san lokacin da ta fad'a k'irjinsa ba don kunya ta rufe fuskanta da k'irjinsa ji ta ke kamar ta nitse. "Mu tafi gida?". Ya rad'a mata a kunne said da ta ji tsigar jikinta ya ta shi har ba ta san lokacin da ta d'aga masa kai ba. Hannunta ya kama ta re da nufar parking space, sai da ya sakata a mota ka na ya zagaya ya shiga. Kanta ta saka tsakanin cinyoyinta ta b'oye fuskanta. Dariya ya yi ta re da reverse su ka bar wajan. Sai da ya hau titi ka na ya kunna wak'ar Umar M Shariff *CIKIN D'AYA*. Hannunta ya rik'o ta yi k'ok'arin kwacewa amma ta kasa, bin wak'ar ya shiga yi kamar haka, 🎻 _Cikin d'aya a cire d'aya, zai zamo ba ko d'aya ni da ke mu zan d'aya ba mu fatan rabuwa. In za ni ba da labari, wa ke saka ni annuri, sunanki zan kira farii, lallai ki da da alkhairi. Kyawun halinki ne ya Jani, ga natsuwa da kyan tsari, auran ki shi na sa buri daga ke ba ni yin k'ari, gun ki kai na sunkuyar, hankali na na tsayar, ke na baiwa ajiyar zuciyata bai d'aya. Ku kalleta kyakkyawa, gu na ta wuce kowa, Idan gaki, idan gani, ni dai ba ni son kowa. Ko da ba ni motsawa, ko da na zamo gawa, da ke zan yi kwantawa ajinina kin ka narkewa. So da k'auna kin shigar, ba bu kowa kin kawar, ke kad'ai ce mallakar zuciyata guda d'ayaaa. O'o'oohh! Lokaci na bak'in ciki, ke ki ka sani na yi darawa, kin sa ni farin ciki duk damuwata na yi mantawa, komai daki-daki na ke a yanzu ba ni rud'ewa, in an yi farmaki gare ki dole na yi karewa. Wajibi in tabbatar, masoyiya na tseratar, ko da rai za na salwatar za na yi maki kariya. Cikin d'aya a cire d'aya, zai zamo ba ko d'aya, ni da ke mun zan d'aya ba mu fatan rabuwa_🎻 Rar cikin jinin jikinta ta ke jin wak'ar, ba ta tab'a tunanin yaya Bibi ya na sauraran wak'ok'in Hausa ba balle ma har ya ita rerata haka ba. Mamaki duk ya gama kasheta. Ta san da za ta baiwa Fanan wannan labarin sam ba za ta yarda ba sai dai ma ta yi mata dariyar k'aryar da ta shararo. Haka ya dunga mata kalaman soyaya cikin wak'ar Umar m shariiff kala-kala ga shi ba gudu ya ke yi kad'an-kad'an ya ke tafiya don ka da su isa gida da wuri. Bayan sun isa gida ya yi locking motar ta re da fuskantarta ya zuba mata idanuwa ita kuma ta k'udundune cikin cinyoyinta. "Ba ki ce komai ba Ruhiey, kin amince da ni a matsayin mijinki na gobe". Fad'in Julaibib. "Wayyoo dan Allah ka bud'e min in shiga gida dan Allah". Fad'in Binty a marairaice. "Dan Allah ki fad'a min ki na sona". Shi ma ya fad'a kamar yarda ta yi cike da shagwab'a. "Wayyoooo Allah". Binty ta sa ke fad'i. Dariya ya yi sosai saboda ya fahimci kunya ta ke ji sosai. Bud'e lock d'in ya yi. Ai kuwa cikin sauri ta bud'e motar ta fice da gudu saura kad'an ta fad'i har da wani zabura ya yi kamar irin shine zai fad'i. Da gudu ta wuce su Rauhiyyah da Fanan da ke ciye-ciye har da Fu'ad. Gaba d'aya dariya su ka fashe da shi kasancewar tuni sun harbo jirgin ya Bibi. "Babi!" Fanan ta kwala mata kira cike da tsokana. Ko juyowa ba ta yi ba ta haye sama da gudu. Sai da ta turo k'ofar d'akin ta rufe ta re da jinginar da jikinta a jikin k'ofar ta shiga mai da numfashi. Tun daga ranar su ka soma wasan b'uya, ba ta yadda ta tsaya in da zai ganta. Shikuwa har ya shiga wani hali na rashin ganinta kwana biyu. Rauhiyyah kuwa ita da Fu'ad kamar da wasa soyayyah ta shiga tsakanin su, tuni Fanan da ma su Sabrin su ka canza masu suna zuwa Babi (matar yaya da yaran Hindi). Mas'ud kuwa tun da ya kyallara idanuwansa akan Sabrin ta tafi da shi, shi ma bai cuci kansa ba ya fito masa da manufarsa, kuma said Allah ya had'a zuciyoyinsu, gidan Anna dai ya koma gidan masoya, don kullum Mas'ud na can su na shan soyayyarsu da Sabrin ya yin da Fu'ad su ke shan na su da Rauhiyy. Mai gayyar ne dai har yanzu ba ta ba shi had'in kai ba. Ta fito daga kitchen kenan cikin sauri ta na son guduwa zuwa sama ka da ya ganta. Sai da ta isa tsakiyar parlour caraf ta ji an damk'i hannunta. *PAID BOOK 08128755583* 🌹 *85-86*🌹 ...........Juyawar da za ta yi idanuwansu su ka had'u da na juna. Ji ta yi kamar ta kurma ihu saboda kunyan da ya lullub'eta. "Mai ya sa ki ke guduna Habibty? Kin san yadda hakan ya ke min zafi ana kuwa?". Ya k'arasa maganar ta re da nuna saitin zuciyarsa. "Dan Allah wallahi kunya na ke ji". Fad'in Binty har da wani karyar da wuya irin marainiyar nan. "Dan Allah wallahi na k'osa in ji kin fad'a da bakin ki kina sona". Fad'in Julaibib cikin shagwab'a shi ma. Kallonsa ta yi na second biyu ba ta san lokacin da ta bushe da dariya ba saboda yadda ya yi da fuska kamar d'an two years. Ka mo hannunta ya yi ta re da matsota kusa da shi ka na ya d'aure idanuwata da hanky ka na ya rik'o hannun su ka fita, can garden su ka nufa. Sai da ya kawota tsakiya ka na ya kwance idanuwan na ta tare da tsayawa a bayanta. A hankali ta fara bud'e idanuwan har ta bud'e su duka. Zaro idanuwa ta yi sakamakon arba da ta yi da wasu flowers multi colours da aka shimfid'a a filin. Ga wasu balloons ma su shape d'in love a jiki kuma an rubuta I love you Rukhsana, wani kuma an rubuta I love you Bintyn Anna, wasu kuma a jiki an rubuta can't live without you. Du ka balloons d'in ba bu wanda ba kalmomin k'auna a jiki. Duk'awa ya yi a gabanta ta re da kamo hannunta ya ce, "Will you be my wife? I mean will you be the one and only mother of my children?". "Yyy.. Yes". Fad'in Binty in a very cool voice ta re da rufe fuskanta da d'aya hannunta". "Na yi alk'awarin zama da ke cikin aminci da soyayya in sha Allah har k'arshan rayuwarmu. Zan kula da ke fiye da yadda zan kula da kai na, zan shayar da ke zallar zuma da madarar soyayyar da ba ki tab'a ga ni ba. Wallahi Salis na son ki irin sosai d'in nan". Gaba d'aya maganganunsa sai su ka tu na mata da Yousouf lokacin da su ke musayar zobe. Kwal-kwal ta yi da idanuwa kamar za ta yi kuka sai ta yi saurin shanye hawayanta. Fu'ad da Rauhiyyah da ke mak'ale can cikin garden d'in su ma su ma shan na su soyayyar su na kallon su. Rauhiyy ce ta fiddo wayarta k'irar iPhone 13pro max ta soma yi masu video tun sanda ya kwance mata hanky a fuska. "Kin ga love ko?". Fad'in Fu'ad ya na tallabe k'eyar Rauhiyy. Shafa k'eyar ta yi ta na dariya ta re da fad'in, "Kwarankwatsi na ga ni, ni ma ai min irin haka ko inyi rejecting". Fad'in Rauhiyyah. "Ke kin ma isa? Ni da ke ai mun zama hatta da jini". Fad'in Fu'ad. "Allah ya sa su hango ku yasin". Fad'in Sabrin wacce su ke yowa inda su ke ita da Mas'ud. Dariya su ka yi gaba d'ayan su ta re da nufo in da ya Bibi da Binty su ke su na tafi. Binty na ganin su ta yi ta rud'e ta rasa in da za ta saka kan ta, bayan ya Bibi ta yi da gudu ta b'oye fuskanta a bayansa. Aikuwa nan ma su ka k'ara kwashe da dariya ta re had'a baki su ka soma yi mata wak'a kamar haka, 🎻 _Binty! Ayaya_ _Binty! Aya_ _Binty Binty Binty! Aya_ _Binty mai miji Ayayah_🎻 Balloon d'aya ya d'auka ya bi su da shi da gudu, gaba d'aya su ka dare su na dariya. Tun daga wannan ranar aka shiga soyayyah ruwa-ruwa tsakanin Binty da Julaibib, abinci daban ta ke dafa masa gidan kuma sai abunda ya zab'a ta ke yi masa ta kai masa har d'aki. Raba dare su ke yi suna waya. Kasancewar idan ya fita tun safe sai dare saboda yanayin aikinsa kuma gashi dama daddy ya sayan masa wani makeken fili ana gina masa asibitinsa a wajan. Yanzu haka asibitin ya kai linta. ..........Kwanansu Anna goma su ka dawo daga bauchi ci ke da farin ciki, sai dai ba su cewa kowa komai ba. Washa garin ranar da su Anna su ka dawo, su Binty su ka d'ugunzuma sai gidan Maman Fakri (uwar rik'on Rauhiyy). Har da su Sabrin da y'an biyu. Sabrin sai duk'ar da kai da sum-sum ta ke yi ita ala dole ta na gidan surukai. Ita kuwa mommah ba ta ma san ta na yi ba duk da Mas'ud d'in ya fad'a mata shi fa ya sa mu matar aure kuma Sabrin d'in ce. Kullum Julaibib da ya dawo daga aiki ya ke tafiya gidan su Rauhiyy dan ganin sahibarshi. Sosai Anna ta ji dad'in ganin sun had'e kawunansu don dama ita burinta kenan. Kwanansu takwas a gidan Mommah su ka dawo gidan Anna, amma ban da Rauhiyy wanda hakan bai yi wa Fu'ad dad'i ba. Yau bak'o su ke da shi, kuma bak'on ba wani ba ne fa ce Yousouf Muhammad Ahlam don godiya ga Julaibib da ya sa mo masa maganin cutarsa har ya warke garas. Kyakkyawan tarba aka yi ma su shi da abokinsa. Tun da Yousouf ya kyallara idanuwa akan Amrah ya ka mu, kuma ita ma haka ya ke a wajanta. Musamman da ya kasance kyakkyawa kuma mai sanyi. Bai yi k'asa a gwiwa ba ya k'arb'i numbernta ka min ya wuce. Washa gari Hamdan ya taho da akwati nik'i-nik'i ya na ta zuba bala'i kowa ya manta da shi har da bestyn shi da ya yi ta dungurewa kai har sai da ta fad'a kan kujera. Nan su ka shiga mai da yadda aka yi lokacin da su ka tsince su a duniyar aljanu. Fanan da su y'an biyu sun yi dariya don Fanan har da hawa sama da gudu ta shiga toilet ta yi fitsari don tsabar dariyar fitsarin da ta yi ta saki don tsoro. Sabrin ta shak'a ta watsa masa ruwa a fuska ta re da shiga ba su labari shi ma ai ya yi fitsarin har da zawo. Nan ma aka shiga yin dariya. Sai kuma aka koma kwantanta yadda Binty ta dunga suman tsoro da kuma kamannin Oumul Sahwat da ba Bak'ayatul mahruri. *AFTER TEN DAYS* .............Gaba d'ayan su su ka shiga kintsawa na tafiyar da za su yi zuwa bauchi, don dukkansu za su tafi, tun daga kan daddy, Anna, Julaibib, Fu'ad, Binty, Fanan, Rauhiyy, mommah, mijin mommah, mas'ud, Hamdan, Amrah da Hanan. Kowa sai kimtsa jakarsa ya ke yi don Anna ta ce masu tafiya ce ta kusan wata d'aya. Duk da kasancewar Hamdan ya na final year d'in sa amma hakan bai hana ya k'i bin su ba. Washa gari su ka bi jirgi sai Gombe (Ku yi hak'uri last page na saka Anna sun je bauchi, ba bauchi zan sa ba Gombe ne mistake ne). Kai tsaye gidan sarkin Gombe su ka nufa wanda wa ne a wajan mahaifin Anna. Gaba d'aya tsoro ne ya kama Binty ganin yadda ake karrama su da kuma gaida su duk in da su ka shiga. Rauhiyyah ce dai ko a jikinta don sai d'aga kai ta ke yi ta re da basarwa kamar d'iyar sarauta. Kai tsaye wajan kilishi su ka nufa wato uwar gidan mai martaba. Nan su ka ga mulki ganin yadda kuyangi su ke mata da su kan su. Cikin k'ank'anin lokaci har an cika gabansu da abinci. Julaibib kuwa tuni har an yi masa iso wajan mai martaba. Zaid ya hango cikin alkyabba mai shegen kyau, idan ka gan shi ka ga Julaibib don kamanninsu d'aya tsaf. Cikin sauri ya mik'e ya je ya rungume Julaibib d'in ta re da farin cikin ganin d'an uwan na shi cike da kewarsa. Duk'awa ya yi ta re gaida mai martaba cike da girmamawa. Ka na ya shiga tambayarsa aiki da kuma Canada. Binty kuwa sai fik'i-fik'i ta ke yi da idanuwa duk da ta na bala'in gidan sarauta sai ta ke jin ta wani iri. Da daddare misalin isha'i su ka taru a parlour mai martaba gaba d'ayan su. Kallon Binty da rauhiyyah ya yi ta re da sakin murmushi ka na ya ce cike da k'asaita "Masha Allah, har na tuna lokacin da mu ka je Sudan d'auro auran mahaifiyarku. Allah ya muku albarka". Ci ke da mamaki kowa na wajan ya ce ameen. "In sha Allah gobe za mu tafi yola da ku duka wajan mai martaba, mun yi waya da shi na ce masa gobe ina ta fe da manyan bak'i". "Allah uban giji ya kai mu". Fad'in gaba d'aya d'akin. Nan duk aka fita aka bar shi daga shi sai mijin mommah da momma da kuma Anna da daddy. Washa gari su ka k'ara shiga jirgi dukkansu har da mai martaba sarkin Gombe sai yola. Nan ma uban motoci aka turo masu daga masarautar yola da kuma dogarai su ka zo su ka d'auke su. Masarauta ce mai girma da tsari wanda tsaruwarta ya fi gaban kwantance. Gaba d'aya masarautar an canza masa launi da kuma wasu abubuwan k'awa. Tun daga jama'ar gari da kuma na cikin masarautar a su na wajan masarauta domin tarbar mai martaba sarkin gombe da bak'in sa. Lokacin da su ka shiga cikin masarautar, mai girma sarki na fitowa gaba d'aya fadawa su ka rufesa da rigunarsu har ya isa part d'in sarkin yola shi d'aya, sauran kuma Jakadiya ta yi masu iso zuwa part d'in Fulani uwar gida wajan sarkin yola. Kishingid'e ta ke ta na cin apple cike da is a da Yakama kuyangi na mammatsa mata k'afa. Farar bafulatana ce kyakkyawa sosai kuma mace mara jiki ko kad'an, za ta iya kai wa shekaru hamsin da biyar a duniya. Ta na yin arba da su Binty da Rauhiyyah ta yi wani irin zabura da gigicewa, ita kan ta jakadiyar da ta yi masu iso sai d'igar zufa ta ke yi kamar wacce kunama ya cijeta. "Ina ki ka samo wad'annan?". Fad'in sarauniya Fulani cikin harshan fillanci wanda gaba d'ayan su idan ka cire Amrah da Hanan sun ji abunda ta ce saboda su ma su na jin fillancin. "Mai martaba ya ce in kawo wajanki, bak'i ne daga masarautar Gombe, kuma ta re su ke da mai girma sarkin Gombe d'in". Fad'in Jakadiya wacce ta ke ji ina ma a kwai hanyar ta gudu. Zama Fulani ta yi ta re da korar kuyangin da ke wajan ta shige d'aki ba ta re da tankawa bak'in ko ba su wajan zama ba. Daga can part d'in mai martabar sarkin yola kuwa, bayan gaisuwa ta girmama tsakanin sarakan biyu, sai su ka shi ga mai da magana. Sarkin Gombe ya yi gyaran murya ta re da fad'in, "Ita Na'ima (Anna) ni na rik'e ta, mahaifinsu k'ani na ne uwa d'aya uba d'aya ai ka san shi. To lokacin da aka ta jimamin b'acewar y'an biyun amarya ta san labarin komai kasancewar ta zo mana ziyara daga can abuja gidan mijin ta. Cikin hukuncin ubangiji kuma sai d'aya daga cikin y'ay'an su ka kasance a hannunta. Yanzu dai duk mun tawo da marik'an y'ay'an za su yi maka bayani da kan su". Cike da farin cikin da ya ka sa b'oyiwa a fuskan mai martaba ya ce, "Alhamdulillah! Allah nagode ma ka. Huta idan ya so sai in sa a kawo su nan d'in". Fad'in Mai martana sarkin yola da ke kishingid'e. *AFTER 3HOURS* ............Tun daga kan Sarauniya Fulani, Sarauniya Zameelah (matar sarki ta biyu), Sarauniya Maimoon wacce ita ce ta uku, sai babban d'an sarki wanda ya kusa sa'a da Julaibib, sai da ba shi da lafiya, irin yaran nan ne da aka haife su abnormal, duk da shi lafiya lau aka haifesa, sai dai ya na kai wa shekara bakwai ya ka mu da wannan lalura. Kyakkyawa ne sosai na gaban kwatance kuma d'a ga gimbiya Zameelah, wanda bayan shi ba ta k'ara haihuwa ba sai da ya shekara goma sha takwas ta haifi y'an biyu kuma washa garin sunan su aka nai me su aka rasa wanda haka ya tada hankali gaba d'aya masarauta. Ya na gefe wanda mai martaba ko kallansa bai son yi saboda wani tsanarsa da ya ke ji wanda hakan ya shafi mahaifiyarsu da ta zama saniyar ware a cikin masarautar wanda Fulani ke juya komai. Sai mahaifiyarsu mai martaba sarkin yola wanda shi kad'ai ne d'a namiji a wajanta. Da kuma waziri da ke ta zazzare idanuwa da kuma Jakadiyar sarki da ta ke ji kamar ta saki zawo don firgici. Shuri d'akin ya yi, ya yin da ko makawo ya kalli Sarauniya Zaheeda ya kuma kalli su Binty ya San daga jikinta su ka fito, ka na ganin ta ka ga cikakkiyar Sudanese wacce kyawunta har yanzu ya na ta re da ita kuma daga wajan ta su ka yi gadon kyau da kuma irin launin fata duk da mai martaba shi ma ba baya ba ne. Sabrin kuwa da su twins mamaki su ke yi wai yau ga su ka sarkin Gombe da na Yola wanda ko a mafarki ba su tab'a kawo hakan ba. Hamdan kuwa cewa ya ke cikin zuciyarsa, "Mummy, uncle Sauban ku zo ku ga asalin Binty ku girgiza ta re da fad'uwa a gabanta don ita d'in jinin sarautace wata muna-munan ce ta kawo ta kan bola. *PAID BOOK* 🌹 *87-88*🌹 .............Anna ce ta mik'awa Sarauniya Zameelah wannan kwarya da Yousouf aljani ya bai wa Binty, idanuwanta na zubda hawaye ta karb'a ta re da fiddo kayan da ya ke ciki. Kuka ta saka sosai saboda wannan shi ya k'ara tabbatar da lallai su Binty y'ay'anta. Jakadiya ma kukan ta ke yi domin ita ce da hannunta ta saka masu wad'annan kayan da kuma awarwaron nan a cikin showel d'in su da kuma maficin d'awisu wanda wannan d'in tambarin sarautar Sudan ce, kuma d'in wanda ya had'a jini mai k'arfi da masarautan ana haifansa ne da zanen d'awisu a wuyansa. Ita ma Rauhiyyah duk abunda ke cikin kwaryan Binty haka ya ke cikin na ta. Da kanta jakadiya ta isa zuwa wajen Binty ta duba k'eyarta, ka na ta koma ta duba k'eyar Rauhiyy. Kallon mai martaba ta yi hawaye na gudu a idanuwanta da kuma murmushi ka na ta fad'i a gabansa ta re da fad'in, "Allah shi k'ara maka girma da yawan rai da lafiya, babu tantama wad'annan y'ay'anka ne, domin akwai zanen d'awisu da aka haifesu da shi wanda ke nuni da tambarin masarautar Sudan a wuyansu, sannan ga awarwaro na d'anyan zinari da mai girma Katanga (Mahaifiyarsa) ta ba su". Ta fad'i hakane ta re da mik'awa mai girma Kantanga awarwaron cike da girmamawa. Duk da ta tsufa sosai bai hanata ga ne wad'annan awarwaro ba, domin kyautace da sarakuwarta kakar mai martaba ta ba ta a matsayin kyautar budurci don har da sunan kowannansu a ciki, ita da kan ta ta saka aka yi wannan ka na ta sakawa kowannen su a hannu. Julaibib kuwa gaba d'aya hankalinsa ya na kan Mahensh da ke jirarar da miyau ya na nazartar ciwonsa. Waziri kuwa fitsari ne ke nai man kufce masa domin bai tab'a tunanin wannan ranar za ta zo ba, Sarauniya Fulani kuwa ita har da zawo-zawo ta ke ji. Cike da tak'ama da gadara mai martaba ya yi gyaran muryan ka na ya kalli jakadiya ta re da fad'in, "Ina son sanin ta yadda y'ay'ana su ka b'ata a masarauta washa garin sunan su, idan ki ka yi karya ki sa ni a bakin ran ki ya ke". Jakadiya fad'uwa ta yi a gaban sarki ta na burgima ta re da fad'in, "Wane ni in yi was sarki na k'arya. Wallahi na amince ko kalma d'aya idan ban fad'i ba ayi gangani ka na a fille kai na". Gaba d'aya d'akin zuba mata idanuwa aka yi, Fulani da waziri babu abunda zuciyarsu ke yi sai bugawa kuma k'ani ne ga mai martaba. "Kowa a nan ya San cewa Gimbiya Fulani ita ce matar Sarki ta fari wacce kuma y'ar uwa ce a gare sa don k'anin mahaifin mai martaba ne wanda su ke uba d'aya ya haife ta, auran zumunci aka ma su, kuma lokaci d'aya ya aure su da Sarauniya Zameelah wacce su ka had'u a jami'atul Madina soyayyar da shak'uwa ta k'ullu tsakaninsu. Sosai mai martaba ya ke son gimbiya Zameelah kasancewarta kyakkyawar mace kuma mace wacce ta iya rik'e miji da tarairayarsa. Haka na matuk'ar k'ona zuciyar Sarauniya Fulani kuma ta na mugun kishi da Sarauniya Zameelah musamman yadda ta yi wani irin suna da farin jini a cikin gidan da kuma wajan Sarauniya Katanga. Cikin hukuncin Allah ba ta dad'e ba ta samu ciki wanda ya sa ka mai martaba cikin wani irin farin ciki, don ba zan manta irin kyautar da na samu mai tsoka ba saboda isar da wannan sak'on farin cikin. Sai dai cikin bai yi wata biyu cikakke ba ya zube wanda kowa yaji bak'in cikin haka musamman mai martaba da har ya fara hango an haifa masa magaji. Bayan wannan lokacin gimbiya Zameelah ba ta rufe wata uku ba ta kuma samun wani cikin wanda shi sai da ya kai wata biyar ka na jini ya b'alle mata babu wanda ya yi zaton za ta yi rai haka kuma ya k'ara ta da hankalin mai martaba, an sa mu nasarar ceto ranta sai dai cikin ne ya fita. Duk maganar nan da na ke ma ku gimbiya Fulani ba ta tab'a ko b'atan wata ba kuma haka na damunta sosai ganin ga wata ba re zata haifi magaji a masarautan ta. A tak'aice dai gimbiya Zameelah sai da ta yi b'arin ciki har takwas ka mun ta sa mu cikin Mahensh bawan Allah, lokacin da ta sa mu cikin ba ta fad'awa kowa ba idan ka cire mai martaba da Katanga, kuma sai ta dai na fita har sai da cikinta ya kai wata takwas ka na na san da cikin a wani zuwa shashinta da na yi domin kai sak'o. Sosai na yi mamaki da ganin cikin nan. Na ja baki na na yi shuru kamar yarda ta gargad'e ni. Lokacin da cikin ya isa haihuwa shi ne kowa ya san da zaman ciki wanda ya kusa saka gimbiya Fulani zarewa domin ta yi kondo-kondo na masifa akan b'oye mata cikin da na yi. Cikin ikon Allah gimbiya Zameelah ta haifo d'anta k'atoto kuma kyakkyawan gaske fari tass mai kama da mahaifiyarsa ga gashi. Ranar duk wanda ya ke cikin masarautan ya shaida haihuwan nan domin kyauta mai martaba ya yi na ban mamaki don wani ma sanadin arzikinsa kenan. Ranar su na yaro ya ci suna Ibraheem sunan mahaifin mai martaba sai ake mishi kara da Mahensh. Sosai aka yi shagalin suna wanda aka kashe kud'i da kuma raba kyaututtuka na ban mamaki. Mai martaba idan ya bar Fada bai rabu da Mahensh a wajansa, don ko barci a k'irjin mai martaba ya ke yin sa. Sun shak'u matuka irin shak'uwar da ko mahaifiyarsa ba ta yi da shi ba don tsakaninsu shi ne idan ya buk'aci abinci ta ba shi ya sa a kuma mai da shi wajan mahaifinsa. Mahensh na girma kyawu da wayonsa na dad'a fitowa sosai da kuma basira da wayonsa. Ga wani tak'ama da isa ka na ganinsa ka ga jinin sarauta, sosai ya ke da shiga ran mutane. Sai dai ya na kai wa shekara bakwai a wata safiya ni da Kai na na isa d'akinsa domin shiryasa zuwa makaranta na yi katari da tashin hankali da masifa, domin dai ga shinan kwance cikin fitsari, kwayan idanuwansa ya juye bakinsa ya shagid'e sai zirarar da miyau ya ke yi kamar irin yaran nan da aka haifesu ba dai-dai ba ko kuma wanda su ka kamu da ciwon b'arin jiki sakamakon fad'uwar hawan jini. Da kyar na iya sanar da Sarauniya Zameelah halin da ake ciki wanda ya ta da hankalinta haka ma mai martaba. An kai Mahensh asibitoci da ba za su k'irgu ba, amma bai samu lafiya ba kuma ba'a gano lalurarsa ba, an dawo an yi na gida shi ma dai kamar an shuka duka. A hankali a hankali mai martaba ya fara zame jikinsa daga lamuran Mahensh har bai son ganinsa saboda kyamarsa da ya ke ji hakan har ya shafi mahaifiyarsa. Daga ni sai Sarauniya Zameelah da kuma Katanga mu ke kula da Mahensh. Ba'a a k'ara haihuwa a masarautan nan ba tsawon shekara biyar wanda haka ya sa mai martaba k'ara aure ya auro Sarauniya Maimoon wacce ita m sai da ta yi shekara biyu ta haifi d'iya mace mai suna gimbiya Rufaida wacce a yanzu haka ta na gidan mijinta. Sarauniya ba ta k'ara samun ciki ba sai da Mahensh ya yi shekaru sha takwas, kuma abunda zai ba ku mamaki, duk da lalurar Mahensh ya na kararu kuma ya na ga ne karatu don yanzu haka ma degree d'in sa uku don ma ba'a k'arfafa masa gwiwa ba, don mai martaba ma cewa ya yi ba zai kashewa gawa kud'i ba bai ga amfanin karatun a wajansa ba, Katanga ita ta buga tsalle ta ce mai martaba bai isa ba. Haka kuma ya yaddace Qur'ani. Ranar da Sarauniya Zameelah ta sa mu ciki ta yi matuk'ar mamaki don ta cire rai da haihuwa, sosai hankalin Fulani ya ta shi da sanin cikin nan, sai dai duk abunda su ke k'ullawa ita da waziri sai da y'an biyu su ka ta ka duniya, haihuwarsu ita ta d'an farfad'o da soyayyan Sarauniya Zameelah a wajan mai martaba har ya yi mata gagarumar kyautar takobin zinarin masarauta mai matuk'ar tarihi. Hakan ya bak'anta ran sarauniya Fulani wanda sun dad'e da ma su na y'an k'ulle-k'ullen su a kan haihuwa da ta ke yi, kasancewar Sarauniya Fulani ta san ta na da matsala kuma ba za ta tab'a haihuwa ba. Shi kuma Waziri ba bu abunda ya ke face mulki ganin sarki ya haifi d'a namiji sai hankalinsa ya ta shi tunda ya san hakan na nufin ba zai yi mulki ba, wanda hakan ya sa su ka yi k'ulla k'ulla su ka jefi Mahensh da mummunar asirin da ya koma haka, sannan ni kuma su ka ba ni mak'udan kud'i da zinari akan kashe y'an biyun da Sarauniya ta haifa, hakan ya ta da hankali na sosai na nu na ni bazan iya wannan aiki ba, sai su ka ce to a bakin raina don kuwa za su had'a min makirci wajan sarki da zai yi sanadin mutuwata. Ni na kawo masu tsarin sa ce y'ay'an idan ya so wanda zai fitar da su ya kashe su, sun amince da hakan. Ni da kai na shirya su na kuma saka duk wani shaida da zai nuna su d'in daga nan su ka fito ko da nan gaba an haife su. Ni da sarkin k'ofa mu ka yi hakan, na ce a yi nisa da su daga yola, wanda aka baiwa kwangilan a Adamawa ya aje su, sai dai ni ban san in da ya kai su ba. Amma ya ce min ya raba su ne. Wallahi tallahi wannan shi ne abunda na sa ni". Fad'in Jakadiya ta na kuka sosai. Da waziri da Sarauniya Fulani kuwa zufa ta gama jik'a su sosai. Mai martaba ran shi ya b'aci matuka, shi kan shi bai san dalilin da ya sa ya tsani d'an shi ba, ashe da walakin. Kallon Fulani kawai ya ke wacce ta sunkuyar da kan ta k'asa kuma hakane ya tabbatar masa da abunda Jakadiya ta fad'i gaskiya ne. Cikin b'acin rai ya sallami kowa ba ta re da ya ce komai, mahaifiyarsu ce da shi kawai su ka rage. Masarauta tu ni ta d'auka da zancan gimbiyoyin masarauta sun bayyana. "Lallai ashe jijji da kai da tak'ama a jinin Rauhiyy ya ke, dole ta yi tak'ama ko ta ina ita d'in jinin sarauta ce". Fad'in Momma wacce ta ke kallon mijinta. Shuru ya yi shi hankalinsa gaba d'aya ya na ko ma wajan muna-munan da ake yi cikin masarauta saboda mulki kawai. Sosai aka yi zama a tsakaninsu Mai martaba da mahaifiyarsu da nuna Fulani da waziri da kuma wasu manya. In da Fulani ta yi confessing ita da waziri, a take mai martaba ya sake ta saki d'aya ta re da jefa ta cikin kurkukun masarauta haka shi ma waziri bayan cire sa daga muk'amin sa. Julaibib da kan shi ya sa mu mai martaba ta re da ce masa ya na buk'atar bin jirgi ya ko ma abuja don d'auko maganin da ya ke tunanin zai iya warkar da cutar da Mahensh ke fama da shi. Mai martaba ya yi na'am, kuma bayan kwana biyu ya tafi Abuja shi da Zain washa gari su ka dawo d'auke da maganin da mahaifiyar Yousouf aljani ta ba shi, don ba zai manta ba ta ce masa duk wani cuta idan dai aljani ya sa ka to zai warke da izinin lillahi. Mai martaba da kan shi ya yi bismillah ya baiwa Mahensh a baki, maganin na wuce mak'ogoransa ya suma, suman da ya ta da hankalinsu domin bai farfad'o ba sai bayan kwana uku. Sai dai cikin hukuncin ubangiji ya farfad'o ne garas kamar bai tab'a kwanciya ciwo. Ko da Mai martaba ya gan shi rungumesa ya yi kuma cikin sauri ya sake sa ta re da nufar part d'in sa ya share kwalla don gudun ka da wani ya gani. Gaba d'aya masarautan ta d'auki murnan dawowa hayyacin yarima Mahensh in da sarakuna daban-daban su ka yi ta zuwa yi wa mai martaban yola murna. Ranar juma'a shi da kan shi ya ja sallah a babban masallacin masarautan in da ya sa mu dubbannin mutane ba matsaka tsinke. Tu ni ya watsu ko ina a media hotonsa kawai ke yawo. Duk budurwan da ta gan shi sai ta ce dama-dama. (Can naga Darma, Queen Zahra, Haleematou, Farida H, Farida S, maman minal, Oumul da sauran y'an paid group ana turere niya wajan shiga. Aikuwa wani dogari ya bi su da zabgegiyar bulala su na gudu. Darma har da tuntub'e ta fasa baki. Haleematou kuwa jakar kud'inta wacce ke dauke da d'ari takwas da hansin😂😂😂😂😂🤪🤪) .............Malam Yarima Mahensh fa tun da ya hango Fanan ya ce ya yi mata, kuma tuni ya sanar da mai martaba kuma a gaban Julaibib aka yi haka. Nan mai martaba ya ce was Julaibib shi ma ya fidda matar aure ko ya yi masa auran dole. Sinne-sinne ya shiga yi ya na sosa k'eya ta re da jan yatsun k'afarsa. Zaid kasancewar shi ma ya na wajan shi ya kalli mai martaba ta re da fad'in, "Allah ya k'ara yawan rai ai Julaibib Binty ya ke so, ina nufin Rukhsana". Cikin sauri Juliabib ya fice wai shi kunya wanda ya sa sauran y'an fada fashewa da dariya, shi kan shi mai martaba sai da ya murmusa. Mai martaba sarkin Gombe sa kan shi takanas ya zo nai ma wa Julaibib auran Binty, Fu'ad kuma Rauhiyy, nan ma mai martaba sarkin Yola ya ke shaidawa sarkin Gomben su ma za su zo nai man auran Fanan. Sarkin Gombe ya ce ai ba sai ya zo ba tin da shi ga shi yazo ya kuma ya baiwa Mahensh auran Fanan. Shi ma sarkin Yola ya ce ya bai wa Julaibib da Fu'ad auran twins. Lokacin da Julaibib ya sa mu labari, kamar ya zuba ruwa a k'asa ya sha haka yaji. Gaba d'aya sun dawo abuja ban da Rukhsana (Binty) da kuma Rauhiyy don an bar su da mahaifiyarsu kuma za su je Sudan ne wajan dangin mahaifiyarsu. Bayan sun dawo ne Mas'ud ya matsa shi ma aje a nai ma masu auran Sabrin, alhaji Usman shi ya je nai ma masa auran wajan alhaji Saifullahi, kasancewar duk an san juna, aka ba shi auranta a tare ya nai ma har da na Amrah kasancewar mahaifin Yousouf shi ya wakilta akan nai man auran saboda shi babban amininsa ne. Ashe daga can gefe Hamdan sun gama d'inkewa da tagwainiyar Amrah wato Hanan shi ma bai yi k'asa a guiwa duk da kuma ya na final year d'in sa ne. Sai dai shi ba'a saka ranar auran ba an bari har sai ya kammala school ya kuma samu aiki. Julaibib, Fu'ad, Mas'ud, Yousouf an saka ranar auren su nan da wata uku masu zuwa, in da gadan gadan ya shiga k'arisa gininsa dama har an riga an saka kwano sauran k'adan ya rage irin su saka k'ofa da windows da kuma penti da dai sauran abubuwa. Su Binty kuwa su na can Sudan, su na ganin tsan-tsan mulki da kuma k'awa fiye da sarautar Nigeria. Yadda ake masu kuwa abun sai wanda ya gani. Gyara kuwa da aka shiga yi masu abun ba magana domin duk inda su ka gitta sai sun bar k'amshi a wajan. Al'ada iri-iri sun gan shi awaya. Sai da su ka yi wata biyi cir ka min su dawo shi ma sai da aka had'o su da mai gyaran jikinsu. Rama kuwa Julaibib ya yi shi na rashin ganin Binty ga shi ko ishasshan waya ba sa yi. Ranar da su ka duro yola, ranar Julaibib da Fu'ad su ma su ka duro. Julaibib ji ya yi kamar ya d'auke Binty su tafi, don wani irin kamshi da sihirtaccan kyau ta k'ara yi masa wanda ya dunga d'ad'dago sha'awarsa na shekaru da ya tara don har ji ya ke kamar ya matso da wata d'ayan da ya rage. Kwanan su bakwai da dawowa su ka bi jirgi zuwa Abuja su da mai gyaran jikinsu da uban kayan gyara, Rauhiyy ta yi gidan iyayan rik'onsa, Binty kuma ta yi wajan Anna wanda su ka cika gidan da ihu ita da Fanan. Anna kuwa kafad'arta ya kusa cirewa sakamakon daka tsalle da Binty ta yi ta d'are ta. Washa gari gaba d'aya amaran su ka dawo gidan Anna da zama. Anna kuwa ta yi fankan-fankan ta hana su Julaibib shigo mata side idan ba abinci za su ci ba, shi ma kuma su Binty na sama har su gama su fice. Sosai su ke shan gyara gaba d'ayansu. Sun canza sun yi b'ul-b'ul jikinsu ya yi fresh da santsi da laushi ga kuma sihirtaccen k'amshi da su ke yi. Bikin ya rage saura kwana goma gaba d'ayan su ka yi Yola amma ban da Anna kasancewar za ta yi taronta ita ma. Tun bikin na saura kwana shidda aka soma shagalin. Al'adu na y'an Sudan kuwa sun gan su kala-kala. Domin ranar lafaya mai matuk'ar tsada su ka sa ka, ga wani kalli da aka masu da ya yi matuk'ar yi masu kyau. Takanas tun daga Sudan aka yi wa shahararriyar mawak'iya jirgi ta zo ta wak'e su. Ranar su Binty sun sha kyau ga kuma b'arin kud'i da aka dunga yi. Ranar d'auri aure kuwa, mai martaba ya ce marik'an su Binty su da kan su za su ba da auran su don su ne iyayansu. Sosai haka ya masu fad'i kuwa. Mai martaba kuwa shi ya yi wakilin auran Yousouf da Mas'ud wanda iyayan su ka wakiltashi kuma shi ma yaji dad'i. Daga nan aka yo Abuja da su Binty da Rauhiyy ba y'an sun sha kukan rabuwa da Fanan kasancewar ita ta na can masarauta part d'in Yarima Mahensh. Binty gidan Anna Anna ka ta ka min a kai su gidan miji, Rauhiyy ma can wajan iyayan rik'onta aka kai ta. Daga baya dai Anna sai da ta yi danasanin wuto da Binty gidan ta saboda irin kukan da ta yi lokacin da za'a kai ta gidan Julaibib. Domin tsadaddiyar lace d'in jikin Anna sai da ya b'arke don tsabar jan shi da ta dunga yi ta na ihun kukan rabuwa da Annan. Shi kuwa Julaibib ya na can ya na zumud'in zuwan amaryan ta shi. Bayan an kai ta an baro ta, Julaibib ya shigo da malum-malum a hannu sai washe baki ya ke yi. A tsakiyar gado ya sameta kwance ta na shivering saboda zazzab'in da ke son kamata dalilin kukan da ta yi. Hawa gadon ya yi ta re da jawota jikinsa ta re da so ma yi mata magana a kunne, "Haba Qalby, sai ka ce wacce akai wa auran dole, wannan irin Kuka haka gashi ki na son ki b'ata min dare na, uhmmmiym! Haba masoyiya ki bar kukan haka mana ban jin dad'i kwarankwatsi". Duk da kukan da ta ke yi sai da ta saki murmushi tuno kawu Buban Kandala. "Yauwa ko ke fa". Ya fad'a ya na k'ara rungumeta a jikinsa. "Ta so ki je ki yi alwala ki zo mu yi sallah mu godewa ubangji da ya nuna mana wannan ranar". Fad'in Julaibib ta re da sauko da ita daga kan gadon, ta re su ka shiga bayin ta yi alwala shi ma ya yi, bayan sun gabatar da sallah ya yi mata addu'ar da ko wani Ango ya kamata ya yi wa amaryansa. Ka na ya shiga ciyar da ita kaza da fresh yoghurt wanda ta ci kad'aan (Ta bar zuly da zubar miyau😂). "Ta shi muje d'aki na, don ban yarda da wannan d'akin ba don naga kamar kwayar ido na leke kuma na tabbar Darma ce ko Queen zarah, idan ba su ba to Haleematou ce kuma ba za su ga komai ba". Fad'in Julaibib ta re da ka ma hannunta su ka koma d'akinsa ta re da turo k'ofa dai-dai Darma ta kawo kai aikuwa k'ofar ya bugu a goshinta sai da ya yi k'ulu.😂😂🤪🤪 Daran ranar Binty ta yi kuka, ta yi ihu, ta yi magiya da cizo amma Julaibib bai saurara mata ba sai da fanshe zaman gwagwarcin da ya yi a kanta don har suma sai da ta yi. Washa gari kuwa ya gyara abunsa tasss. Haka ma a can Yola ya faru, kasancewar har gobe su na al'adar farin kyalle, Jakadiya ta yi shela akan matar yarima ta kawo budurcinta. Sarauniya Zameelah ita ta fara isar da kyautarta na awarwaron zinari guda hud'u, Katanga ma ta ba ta na ta kyautar na sarkan gold ya yin da mai martaba ya saya mata mota ta re ba ta kujeran hajji har na mutun goma ta zab'i wanda zai je a danginta. ..........Sabrin kuwa bakin nan mutuwa ya yi don ita ma ba k'arya ta gurzu sai ta koma owners corner ta yi shuruuuuuuu. Hajiya Rauhiyyah kuwa kamar jab'a ta fad'a a koko tsabar jigata don har carbi ta d'auko ta na ta jaa, sallah ko ta yi ya kai raka'a goma saboda ka da ya shigo wani tsautsayin ya sa ya ce zai sa ke. Su Hajiya Amrah ba magana don idanuwanta gaba d'aya sun kumbura. ...........Bayan wata d'aya da auransu, Julaibib ya yi lunching k'atotan asibitin da babu kamar shi a abuja, wanda mai martaba sarkin Yola sirikinsa da kuma sarkin Gombe da ministern Abuja su suka bud'e asibitin. Binty a gida kuwa ta had'a kwarya-kwaryan waliman ta da gaba d'aya amaran sun zo har da Fanan da ke Yola. Kuma gaba d'ayan su su na da shigan k'aramin ciki. Na Binty ya fi nunawa kasancewar laulayi ta ke yi mai zafi don jinin Julaibib na da k'arfi don O'negative ne. Genotype d'in sa kuma AA. O'negative sai ka tara mutane d'ari da kyar ka samu d'aya mai irin jinin. AFTER 10TH MONTH Sabrin ce ta fara haihuwa, ta haifi d'anta namiji Aahil, bayan kwana uku Rauhiyy ta haifi y'an biyu mace da namiji, su ka ci suna Aayad da Airah, tsakaninsu da Binty kwana d'aya ta haifo mace mai kama da ita sak ta ci sunan Anna Na'ima, su na kiranta da little Anna, Amrah ce k'arshan haihuwa ta haifi mace ita ma ta cire sunan mommah Rahima suna kiranta da khairat. Lokacin an saka bikin Hanan da Hamdan wata takwas masu zuwa don har ya gama service kuma mai martaba sarkin Gombe da kan shi ya karb'i takardunsa ya nai ma masa aiki. Soyayyar ruwa-ruwa ya ke gudana tsakanin Julaibibda da Binty, ba sa fushi mai tsayi da junansu. Sun shimfid'a rayuwarsu cikin fahintar juna, idan d'aya ya yi fushi, d'aya zai sauko ya taushi d'aya. Ranar bikin Hamdan kuwa sun yi rawa sun cashe ka na su ka mik'a amarya Hanan gidan mijita wanda su ka b'oye su ka yi kuka sosai na rashin mahaifiyarsu akusa ta na can prison ta lalace don duk wata sai sun je ganinta. Hajiya Kandala an yi shekara uku an fito daga gidan yari ta kod'e ta jeme. Kai tsaye Datu ta fara naima wacce gaba d'aya kud'inta na hannunta da ta k'arba da sunan juya mata kud'in. Sai dai ta yi katari da abunda ya kusan tsayar da numfashinta domin kuwa Datu ta yi aure ta da d'an damfara ya damfareta ya kwashe komai ya gudu zuwa Dubai. Kai tsaye Saminaka ta nufa, in da aka yi mata koran kare domin bayan tafiyanta matar Buba mai kwarankwatsi ta tona asirin komai wa Goggo Shatu. Wannan tsoho kuma da su ka dawo duniyar aljanu da su Binty ba kowa ba ne fa ce alhaji mai tumbi da mahaifiyar Yousouf ta tafi duniyar aljanuda shi wanda tashin hankali ya sa ka ya yi loosing memory don iyalansa ma sun dad'e da gama Rabin gadon shi ta re sake sure don sun d'auka ya mutu, kuma bayan barin gida na tsawon lokaci su ka Shiga d'akin sirrinsa da bai bari a shiga su ka ga ne ya fad'a k'ungiyar asiri ne. *TAMMATA BIHAMDULLAHI* _NAN NA KAWO K'ARSHAN WANNAN LITTAFI WANDA BA HAKA NA SO TAFIYAR TA TSAYA NA, WALLAHI UZURI NE GARE NI BABBA DA FATAN ZA KU MIN AFUWA._ _KUSKURAN DA NA AIKATA YAYIN RUBUTA WANNAN LABARI ALLAH KA YA MIN, ZAN YI AMFANI DA WANNAN DAMAR IN ROK'I YAFIYAR KU WAD'AND'A NA B'ATAWA RAI, NI NA YAFE MAKU HAR CIKIN ZUCIYATA, ZAN TAFI OFFLINE WANDA BAN SAN RANAR DAWOWA TA BA, DAN ALLAH KU YAFE MIN WATAKIL WANNAN SHI NE BOOK D'INA NA K'ARSHE. ALLAH SHI YA SAN GAIBU._ _NAGODE NAGODE NAGODE DON KUN NU NA MIN AMANA, DON BA KU FITAR MIN DA BOOK BA, HAKAN YA TABBAR MIN DA KU D'IN YAN HALAS NE WANDA KU KASAN AMANA DA KUMA HUKUNCIN WANDA YACI AMANA. ALLAH YA K'ARA BA KU IKON RIK'E AMANA YA SA HAKAN SHI ZAI SAMO SILAR SHIGAR KU ALJANNA_ 😭😭😭🤧🤧 _SAI MUN SA KE HAD'UWA IDAN DA RABON HAKA_ *MATAR SAYYADEE*🥰