✨✨ HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 20........ Saiku karanta din en barii kawe...... Khaleesat ta gama Laundry da take a kitchen ta fito, a reading nook din parlon ta tarar da Housemate dinta yana duba textbooks dinsa, cikin few seconds ya dau wanda zai dauka ya dawo cikin parlon yana kallonta yace "Har kin gama kenan" Kai kawai ta gyada masa ta fara tidying din parlon, rana na farko kenan da ta fara ganinsa yayi shiga irin ta Hausa cikin fararen kaya, Taji yace "Hope you are studying well Halysaah" kai kawai ta gyada masa, yace "Alright, till later" Ta ɗan kallesa tace "Are you Nigerian?" Ya buda ido yace "Why do u ask?" Tace "Kawai nayi zatan ko daga Chad kake, or Niger" Dariya yayi yace "Hope it's fine now tunda kin rama?" Hanyar dakinta ta nufa ba tare da ta basa amsa ba, ya dau makullin motarsa ya nufi kofar parlon, sai bayan da ya fita sannan ta dawo cikin parlon ta tafi gun window ta ɗan bude drapery din jiki tana leka garage, ganin har ya tafi ta ci gaba da aikin da take yi a parlor. Wajen karfe biyar na yamma Khaleesat na kitchen tana girki at the same time suna waya da Abdul, tun 40 mins ago ya kirata suke magana har sannan, duk kwanan nan dai lafiya suke waya da shi, ya kuma ɗan rage mata wasu abubuwan da yake mata, he is being a little caring these days, a rana sai su yi waya sau biyu wani lkcn har sau uku har hakan na bata mamaki kamar dai ba shi ba, yanzun ma shi ne yayi encouraging dinta ta tashi ta fara girkin da take yi don bata yi niyyar girki ba, for weeks now kullum Housemate dinta ke masu takeaway na dinner wani lkcn har lunch, this made her soo lazy to go to the kitchen, breakfast dama tea and cookies take ci yawanci ko kuma ta ci da bread idan Housemate dinta ya siyo, wani lkcn ta ci french fries da kwai ko ketchup, kwankwasa kofar parlor taji ana yi, ta ɗan zaro ido sanin bazai wuce Housemate dinta ba, kilan ya mance makullinsa ko kuma yayi misplacing dinsa as usual, ta kalli wayarta dake ajiye a kan kitchen cabinet har sannan Abdul was on the line kuma a handsfree ta sa wayar, tana ɗan kame kame tace masa "Can u excuse me pls, i will call u back in the next 2 minutes pls" Abdul yace "Why? Me zaki yi? Is the call hindering you from doing anything?" Da sauri tace "Noo" don bata son tayi laifi, sai kuma a hankali tace "Just want to round up the cooking ne, na kusa gamawa ai" Yace "But my call isn't preventing you from doing so, wayan ba a ajiye yake ba? Continue with ur work kawai" Knocking ta sake ji, ta ma san Housemate dinta ne cause haka yake knocking dinsa, ta kalli wayarta tace "Ohk then" Abdul ya ci gaba da maganar da yake mata, a hankali ta dau wayar ta fita daga kitchen din almost tiptoeing kamar tana tsoron yaji sound din tafiyarta, ta nufi kofar parlon ta bude at the same time tana kokarin yi ma Housemate dinta alamar da yayi shiru ta hanyar dora finger dinta daya a lips dinta, lkci daya taji komai nata ya tsaya cak, a hankali ta zame finger dinta daga lebbenta tana kallonsa bata ko kiftawa zuciyarta na bugawa, ta cire wayar dake kunnenta looking speechless and Surprise at the same time, Calmly yace "Ko in koma ne?" Ta zaro ido cikin in ina tace "No, no, not at all, i... i was just being surprise, sannu da zuwa" Da sauri ta koma gefe zuciyarta na bugawa da karfi, Ya katse wayar dake kare kunnensa sannan ya shiga parlon, ta bi sa da kallo still shocked, gani take kamar she is daydreaming, ta kikkifta idanuwanta ta bude to be sure but still she is still seeing him, har sai da ya karasa cikin parlon ya zauna sannan ta bi bayansa, a hankali ta duka kusa da shi tana yaƙen karfin hali tace "Wai dama all this while kana garin nan ne? I am so confuse" Yace "Gashi kin gan ni, in baki yarda ba sai ki taɓa ki ji don ki tabbatar" Still feigning smile tace "I am seriously surprise, this is the least thing i expected today wallahi..." Sai kuma ta tashi da sauri tace "Let me get u water" Kitchen ta tafi zuciyarta na bugawa, sai da ta jingina jikin cabinet ta dafe kirjinta a hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku" Tasan at anytime Housemate dinta zai iya shigowa gidan don yamma yayi sosai, cikin hanzari ta bude fridge ta dauko masa ruwan gora da drink with glass cup sannan ta fita da sauri, tana kirkiran murmushi ta durkusa gabansa ta ajiye masa tace "Tun yaushe kake garin nan amma?" Ya dau ruwan goran yana kallo yace "You are buying expensive water now? Sannu er gayu" Tayi dariyar karfin hali tace "Not at all, miyar ma ya kusa yi sai in zuba maka abincin, ko dama shi sa kace sai nayi girki?" Kawai murmushi yayi bai bata amsa ba, ta mike ta koma kitchen, gaba daya she is confuse on what to do, ta fara dube duben wayarta ta tuna ta ajiyesa kan kujera a parlor, fitowa ta sake yi ta tarar Abdul yayi picking din kiran da ake masa ta waya, cikin dubara ta dau wayarta ta nufi dakinta da sauri tana kallonsa ta gefen ido taga attention dinsa na kan wayar da ya fara, bandakinta ta shige ta kulle tace "Na shiga uku" Da ta tuna bata ma da lambar Housemate din nata ta sake jin mugun tashin hankali, yanzu ya zata yi? Da sauri ta fara dialing number Salem, ai ko yana fara ring ya daga, murya can kasa ta gaishesa without waiting for his full reply tace "Plsss how can i get in contact with my Housemate? ina son zan masa magana ne urgently" Salem yace "Ohk, muna ma tare, gashi nan" Bata san sanda ta sauke wani irin ajiyar zuciyar relieve ba, taji muryar Housemate dinta yace "Hello Halysaah, is everything alright?" Ta girgiza masa kai da sauri kamar yana ganinta tace "Plss i am sorry amma kar kace zaka dawo yau, my fiance is around, he just came without notice" Yace "Tohhhh, haka kuma aka yi ashe?" Ta wani turo baki kamar yana ganinta, yayi murmushi yace "Alright Halysaah, keep ur cool, duk sanda ya tafi sai ki sanar min" A hankali tace "Thank you" Yace "Not a problem" Shi ya fara katse wayar, ta kalli screen din sannan ta sauke ajiyar zuciya ta fito da sauri bayan ta bar wayar a dakinta, har sannan ta tarar Abdul bai gama wayar da yake ba, da alama business call ne, Khaleesat na tafiya a hankali ta tafi kitchen don saka masa abincin da ta girka, har sannan she is shock, babban damuwarta yanzu kasantuwarsu su biyu kadai a gidan, a da bata jin tsoron kasancewa da shi guri daya and that was almost 4 years back, but not anymore, he is complete changed all of a sudden in just a year, da tunanin nan ta fito daga kitchen, ta karasa har gabansa ta ajiye masa abincin, yana kallonta yace "How about ur Housemate, bata nan ne?" Ta ɗan yi murmushin karfin hali tace "Yeah bata nan" Ta mike ta koma edge din kujera ta zauna kamar bakuwa a gidan, a hankali tace "Ya su Momy da Aunty Hafsah?" Yace "Lafiya lau" Bata sake cewa komai ba, Ya kalli abincin da ta ajiye masa yace "I am full, ki rufe sai dai anjima" A hankali tace "Ok tafiya zaka yi da shi?" Yana dubanta yace "In tafi da shi ina?" Ta kirkiri murmushi tace "A'a ai tambaya kawai nayi" Yace "Na riga nayi lodging out of the hotel, i was in Maryland since morning" Khaleesat was speechless, bata gane yayi lodging out of the hotel ba, to ina zai kwana ko kuma wani hotel din zai kama? kai bata ma yarda ba don in yayi lodge out to ina trolley din kayansa yake, Tana murmushi da kyar tace "To ina akwatin ka?" Yace "Tana cikin mota" Ta hadiye abu da kyar tace "Motar wa?" A takaice yace "Ban sani ba" sunkuyar da kai tayi bata sake cewa komai ba, yace "Ko kina da plans ne yau? Naga kinyi mamakin zuwana da gaske" Ta zaro ido tace "Not at all wallahi, ai kai ma kasan daga schl babu inda nake zuwa, kawai dai nayi mamakin muna ta waya tun daxu ashe kana garin nan" Ya mike yace "To ki dena mamaki tunda ba ke kika siya min ticket din ba" Ta sunkuyar da kanta tayi shiru, dakinta ya nufa yace "Let me take a shower" Khaleesat ta gyada masa kai kawai ta bi sa da kallo, a very tall and masculine guy he is, just like her Housemate, and they are all handsome in their own different ways kamar su suka yi kan su, sai dai ita tafi ganin kyan, Housemate dinta ko me zuciyarta ya dinga bugawa, har ji take kafafuwanta suna neman kasa daukarta, ya matso da ita dab da shi har tana iya jiyo breathing dinsa, calmly yace "Kinsan menene yasa nake kwanciya a parlor a sannan?" Ta girgiza masa kai without looking at him don she is soo uncomfortable with him drawing her closer to himself, yayi kasa da murya yace "Saboda u were still a baby sannan" Ta daga idanuwanta da kyar ta kallesa amma ta kasa cewa komai, yace "Yanzu kuwa ke ba baby bace, how old are you?" Ta kasa basa amsa, ya ɗan mata tsawa yace "Tambayarki nake?" Ta hadiye wani abu da kyar tace "I am 20" yace "To a sannan ina keeping distance between us because i was still grooming you" Ta kauda kai seeing how closer he was coming to her, juyo da kanta yayi yace "Meye haka?" Muryarta na rawa tace "This is against the teaching of islam Ya Abdul, ni ba muharramarka bace"a Yace "Oh really? Dama wani ne zai aure ki ba ni ba ashe?" Ta kasa ce masa komai lkci daya hawaye ya cika idonta, duk tsiyar da yake mata da yaga hawaye idont 21 Khaleesat ta kusa minti sha biyar a bandakin cikin tashin hankali da confusion, banda kuka babu abinda take yi, she can't even think straight tsabar yanda ta shiga tashin hankali, to ko dai kawai ta fita ta gudu ta bar gidan ne, ko kuma taje ta basa hakuri ya rufa mata asiri, ta ma san bazai taɓa sauraronta ba, da kyar ta mike daga durkushen da take hawaye sosai na zuba idonta har sannan jikinta rawa yake, gani take kamar the world have come to an end for her, hannunta na rawa ta wanke fuskarta tayi karfin halin bude kofar bandakin a hankali tana leka Bedroom dinta, zaune ta gansa edge din gado yana danna wayarsa, suna hada ido ta bude kofar ta fito, ya dinga kallonta daga sama har kasa, hakan yasa ta sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa, Mikewa tsaye yayi yana mata wani kallo yace "So you just wasted my time all this while ba wankan kike ba dama?" tears was just rolling down her cheek tana girgiza masa kai muryarta na rawa tace "Don girman Allah kayi hakuri, kar kace zaka...." Dakatar da ita yayi ta hanyar daga mata hannu, tuni ta ja bakinta tayi shiru tana kallonsa a tsorace ganin yanda lkci daya yanayinsa ya canza, tana ganin ya nufota ta juya zata koma bandakin da gudu yayi saurin fixgota, ta rushe da kuka sosai tana cewa "Don girman Allah kar ka min haka ka rufa min asiri Ya Abdul" Yana mata wani kallo yace "You think i will just waste my time and money coming here at the end in kyaleki da childishness dinki in koma Nigeria? You must be joking, In kika ga na kyaleki yau sai in faduwa nayi na mutu" Zuwa sannan Khaleesat bata ma san kalmomin dake fitowa bakinta ba ta dinga basa hakuri a rikice, ta dai san ko da wasa bazata ce zata yi kokuwa da shi ba, ta ina ma zata fara, da hannu daya in ya riketa ko kwakkwaran motsi bazata iya ba balle ta kwace kanta, Knocking kofar da ta jiyo a kunnenta ne yasa ta zaro ido bakinta na rawa tace "Wallahi Housemate dita ce ta dawo kuma bata da makulli nata ya ɓata..." Yace "And so what? Ita zata hanani abinda nayi niyya ne?" Hawaye na sauka idonta tace "Don Allah ka bar ni in bude mata kilan mantuwa tayi, she is not spending the night here" Saketa yayi fuskarsa babu yabo babu fallasa yace "Remain here, i will open the door for her" Gyada masa kai kawai take zuciyarta na bugawa da karfi, ya dau rigarsa ya saka sannan ya nufi kofa ya fita, a hankali Khaleesat ta sulale kasa tana jin kamar numfashinta zai dauke tsabar tashin hankali, gashi sai knocking kofar parlon ake babu kakkautawa, da sauri ta mike jikinta na rawa ta bi bayansa tana shesshekar kuka at the same time tana tunanin to wa ke kwankwasa kofar Allah Ubangiji ya sa Housemate dinta ne, nan corridor ta makale don tuni har Abdul ya isa kofar parlon zai bude, ya murda makullin ya bude kofar, Khaleesat couldn't believe who she saw standing at the doorstep, ai bata san sanda ta karaso parlon da sauri ba hawaye na sauka idonta, Abdul dake kallonsa daga sama har kasa Calmy yace "How may we help you? Who are you looking for?" Maimakon wanda ke bakin kofar ya basa amsa kawai ya bi gefensa ya shigo parlon yana kallonta yace "Why did you call my line?" Da mamaki Abdul ya juya ya kalli Khaleesat da ta sunkuyar da kanta hawaye na sauka idonta ta lumshe ido, bata san sanda wani relieve ya zo mata ba lokaci daya, ta sake jin muryarsa yace "Me yasa kika kirani?" Ta daga kai ta kalli Abdul ganin irin kallon da yake mata at the same time ya nufo inda take cikin zafin nama, ganin haka ta fara komawa baya cikin rawar murya tana kallon AJ tace "I need you to help me pls" Ko rufe baki bata yi ba taji Abdul ya sauke mata wani wawan mari a kuncinta, AJ could not believe what he just saw cause bude baki yayi at first, ganin ya kara sauke mata wani marin cikin few seconds AJ ya isa gaban Abdul sending him double fist a fuska, he took Abdul unaware don bai gama recover daga fist din ba ya kara masa wasu ukun a jere, kan kace me ya fara punching dinsa kamar an aikosa, Rikicewa Khaleesat tayi da karfi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku plss stop it" Tana matsowa kusa da su zata rike AJ da ya wani hankadata sai da ta fada kan kujera, Dai dai sanda aka bude kofar parlon Jay ya shigo, buda baki yayi ya jefar da wayar hannunsa saman kujera ganin Abdul a hannun AJ kamar ya samu punching bag, AJ gave Abdul no single space to retaliate, dukansa kawai yake kamar suna gidan dambe, Jay ya nufesu da sauri yana kiran AJ, da kyar ya samu nasaran rabasu yana ma AJ tsawa yace "Are you out of your mind Junaid? Are you mad, Meye haka?" Jay bai rufe baki ba Abdul ya koma kansa da fist din da bai samu yi ma AJ ba, ai ko ya kara ja ma kansa wani dukan wajen AJ, Jay that was shock at the attack Abdul just attacked him ya bude baki yana kallonsu, kar AJ yaje ya ma Abdul illa su shiga uku ya sa Jay ya kara rike AJ, Abdul that was beaten blue black ya nufi kitchen kamar mahaukaci vowing to unalive AJ, Khaleesat tsabar shock ko motsin kirki bata yi a inda AJ ya wurgar da ita, Jay na ganin Abdul ya shiga kitchen yasan makami kawai yaje daukowa, ya kalli Khaleesat da sauri yace "Tashi ki tafi daki" Ai kamar jira take ko rufe baki Jay bai yi ba ta mike a guje tayi Corridor ta tsaya tana zare ido, Jay ya fara jan AJ su tafi daki amma AJ yaki yana cewa "Don babansa me yake takama da shi a Nigeria? Who the F is he? Kakkaryasa zanyi in karya banza wallahi, in ya cika shege mu hadu a Nigeria" Jay yaki biye AJ haka dai ya ja sa har corridor zai shigar da shi daki, sai ga Abdul da wuka ya nufo su kamar Ɗan daba, ai ko karasa shigewa dakin basu yi ba Khaleesat ta riga su, tuni Jay ya sa ma dakin Key ya zare makullin ya saka a aljihu don tsaf yasan AJ sai yace zai bude kofar ga makami hannun Abdul, Abdul ya dinga bubbuga kofar saying all sort of abusive words at the same time yana alkawarin sai ya ma AJ illa, AJ ya tafi jikin window ya tsaya yayi crossing kafa yana kallon kofar dakin, Jay dai ya zauna gefen gado looking speechless and confuse, sai kuma ya dafe kirjinsa da ya fara masa ciwo saboda fist din Abdul, ita dai Khaleesat na rakube jikin gado hawaye na sauka idonta tana kuka a hankali, banda bugawa da karfi babu abinda zuciyarta ke yi, taji muryar Abdul na cewa "Ke kuma sai na maki abinda har ki koma ga mahaliccinki baza ki mance ba, i will make sure you become useless and miserable, i promise you this, kasar nan kuma kamar kin bar sa don karatun ki ya zo karshe" Khaleesat ta kara sautin kukanta, Ajay ya daka mata tsawa yace "I will fling you out of this room in baki rufe ma mutane baki a nan ba" Jay ya wani kallesa, ita dai Khaleesat ko kallonsa bata yi ba kukanta kawai take, after a while ko ina yayi tsit a gidan ko tafiya Abdul din yayi oho, da kyar Khaleesat ta mike bayan kusan minti goma zata dau hijab dinta, Jay ya bi ta da kallo, bayan ta saka Hijab din ta juya suka hada ido, sauke idonta da ya kumbura don kuka tayi, sai kuma ta tafi ta dau karamin towel da ta gani gefen gado seeing traces of blood in Jay's lips, bandaki ta tafi ta jika towel din da ruwan dumi sannan ta dawo dakin without looking at him ta duka gabansa ta dafa gadon ta fara goge masa lip dinsa a hankali, AJ ya wani kallesu sai kuma ya tabe baki ya kauda kai yana kallon outside of the window, Jay dake kallonta yace "Thank you Halysaah" Ita dai bata ce komai ba kuma bata yarda ta hada ido da shi ba ta mike ta tafi bandaki da towel din, AJ ya juyo yace "Kai Malam bani makulli in bude kofar nan in fita" Mikewa Jay yayi ya nufi kofar ya fara budewa a hankali, AJ ya bi bayansa incase of necessity, yana bude kofar AJ ya rigasa fita at the same time being very conscious of everywhere in the house, both angle and corner, a haka ya fito parlon Jay ma that was at alert na biye da shi a baya amma fa sai da ya kulle kofar dakin da makulli sbda Khaleesat, and they realized Abdul ya fice daga gidan, AJ ya juya ya kalli Jay yace "Dau wayarka mu tafi gida" Jay yace "You think i can just go and leave her in here?" AJ ya masa wani kallo yace "How sure are you u are safe being in this apartment tonight? Mahaukaci ne fa gayen kuma zai iya dawowa at anytime, it's already dark now" Jay yace "Nasani, but bazan iya barin ta ita kadai gidan nan ba" AJ yace "Are you her family member or something?" Jay yace "Kai da ka taho nan family member dinka ce?" AJ yace "Look Jay, Billah bazan bari ka zauna a gidan nan ba, koma wani taimako zaka mata kayi mata ni babu ruwana amma baza ka zauna a gidan nan ba, i can't risk leaving you here even for 1 second" Jay that was quiet for a while yace "Toh ka tafi, zan biyoka a baya" AJ yace "Kafata kafar ka Malam, kaji nayi rantsuwa bazan bar ka gidan nan ba, dubi kullin da ya dinga maka babu abinda ka tabuka sai sake baki kayi kana kallonsa" A hankali Jay yace "So kake mu hade masa at the end mu zo mu yi abinda za ayi da an sani, ai gwara da na kyalesa kawai kai ba gashi ka basa kashi yanda ya kamata ba, beside in muka ce zamu dokesa tare hakan zai sa mu gigita yarinyar ne" AJ yace "Aa haukatar da ita za mu yi ba gigita ta ba, pls do what ever you want to do ka fito mu tafi gida, ni yunwa ma nake ji" Jay ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Wait for me outside then" Yana fadin haka ya juya ya koma dakinsa da Khaleesat take, AJ kuma ya fice daga parlon ya tsaya nan bakin kofa yana jiransa, bayan Jay ya bude dakin da makulli sai da yayi knocking sannan ya shiga ciki, tsaye ya ganta jikin bangon dakin hawaye na sauka idonta tana shessheka, ya tafi can jikin window ya tsaya yana kallonta, ita dai ta sunkuyar da kanta tana kuka a hankali, Calmly yace "Halysaah" Ta kasa daga kai ta kallesa, yace "Tell me how did you get to know this guy? A ina ku ka hadu? For how long ku ke tare da shi, kuma who is he? Iyayenki sun san da alakar ku?" Sai a sannan ta daga kai wasu hawayen na sauka idonta tana kallonsa, ya sauke ajiyar zuciya yana shafa kansa yace "Where are ur reading material? Suna dakin ki ne?" Kai ta gyada masa kawai, yace "Mu je ki dauka" A tare suka tafi dakinta, bayan yaga inda reading materials din nata suke ya karasa ya dauka har da laptop dinta, ya kalleta yace "Ina wayarki fa?" A hankali tace "Ya fada ruwa" Shiru yayi sai kuma yace "To mu je" Ta ɗan yi jim tana kallonsa, yace "Mu je mana" ba musu ta nufi kofa ya bi bayanta bayan sun fita ya kullo kofar, ita dai duk a tsorace take sai zare ido take tana ganin kamar Abdul zai sake dawowa gidan at anytime, ganin a tsorace take Jay ya shiga gaba yace "Follow me" Bin bayansa ta dinga yi hawaye na sauka idonta har suka fita daga parlon, har sannan Ajay na tsaye waje, ya juya ya kallesu, Jay ya nufi motarsa ganin Khaleesat ta tsaya yace "Mu je mana Halysaah" tana tafiya a hankali ta ci gaba da bin sa, back seat ya bude ya ajiye laptop dinta da sauran reading material dinta ya kulle sannan ya bude mata front seat, ta sauke idonta ta shiga motar ya kulle, yana kallon direction din AJ yaga har ya nufi gun motarsa ya shiga, zagawa yayi ya shiga driver seat ya tada motar, tuni AJ yayi zoom off, Jay ya bi bayansa. A hankali Khaleesat ta sauko daga motar tana kallon Jay da shi ma ya sauka ya bude back seat ya dauko laptop dinta da takardu ya kulle motar yace "Mu je" Sauke idonta tayi ta fara bin sa a baya walking slowly har suka shiga parlon gidan, ya nuna mata kujera yana kallonta, ta sunkuyar da kai sannan ta zauna, ya ajiye laptop da takardunta dake hannunsa sannan ya wuce sama, ta bi sa da kallo hawaye na taruwa idonta, sai kuma ta fara kuka a hankali tana jin kanta na sara mata, Jay ya tafi dakin AJ yana bude kofar dakin yaji yana wanka a bandaki, hakan yasa ya tsaya bakin kofar dakin don baya son issue, yana ta tsaye da tunani iri iri a ransa har AJ ya fito bandakin, AJ na ganinsa ya dakata da goge gashin kansa da karamin towel yace "Me kake nema a nan kuma?" Jay yace "Ban sani ba" Sai kuma ya karasa cikin dakin that was extra clean, kan kujera ya zauna without looking at AJ yace "We need to talk AJ" Ajay yace "Shi ne sai ka shigo min daki?" Jay yace "Zauna mu yi magana" Ɗan tsaki AJ ya ja yana ci gaba da goge gashinsa yace "Ina jin ka ba sai na zauna ba" Jay yace "I think my Housemate will stay here for a day or 2, before she sort her self out" AJ yace "As per you are her family member or who? Bata da iyaye ne? Ko nan din hotel ne?" Jay yace "Ban sani ba" AJ yace "No i am just asking a harmless question, like naga dai ba daga sama ta fado ba, kuma ba kai ka kawota America ba balle kace zaka samar mata solution, who are you to her? Yayanta ko Ubanta? Wanda muka mata ma Allah ya bamu lada, come off it Jawwad" Jay yace "Ai ba permission din ka na shigo nema ba Junaid, kawai sanar maka nake yarinyar nan zata yi kwana daya zuwa biyu a gidan nan kafin komai yayi settle" AJ yace "Toh ni na haifeka da zaka shigo ka gaya min zaka kawo yarinya tayi kwana biyu gidan nan? Ai sai dai ka kira su Abba ka gaya masu, beside the house is very big with multiple rooms to accommodate her, so ni ina ruwana, i just pray u don't have to explain ur self one day" Jay ya mike ya fice daga dakin banging the door behind him, AJ ya tabe baki yana feshe jikinsa da turaren jiki. Bangaren masu aikin gidan Jay ya nufa bayan ya sauko downstairs, ya basu umarnin da zai basu sannan ya dawo babban parlon gidan, Khaleesat dai na zaune ta jinginar da kanta jikin kujera tayi nisa tunanin da ta fada, ganin komai take kamar a mafarki, sai in taji tana da ta sanin abinda ya faru amma da ta tuna raping dinta Abdul yayi niyyar yi da Ajay bai zo ba sai taji ta nemi da ta sanin ta rasa, amma fa bata da nutsuwa bata da kwanciyar hankali, she was just restless and sick, bata san kuma me zai faru next ba a rayuwarta, muryar Jay ne ya dawo da ita daga tunanin da take ta gyara zama tana kallonsa a sanyaye, ya zauna kujeran dake kallon wanda take zaune yace "Bana son ki sa ma kanki damuwa Halysaah, ki kwantar da hankalinki pls kin ga kina da jarabawa a gabanki" Khaleesat ta sunkuyar da kanta hawaye ya fara sauka idonta, Yace "Kin yi sallah?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk za a kawo maki abinci sai ki ci kafin mu yi magana" Ta girgiza masa kai tace "Bana jin yunwa" Yace "No, sai kin ci abinci ko ba yawa" Dai dai nan kukun gidan wanda bature ne ya taho da abinci zai kai dinning Area, Jay ya masa umarnin ya kawo parlon sanin abincin AJ na kan dinning din, dawowa kukun yayi Jay ya nuna masa inda zai ajiye abincin, nan ya jerasu a kasan lallausan Centre carpet, ya koma ya dauko sauran, bayan ya ajiye komai ya tafi Jay ya mike yana kallonta yace "Ki sauko ki ci abinci, let me pray" Ta gyada masa kai kawai, ya wuce sama sannan ta sauko kasa a hankali tana duba abincin da aka kawo mata taga duk abincin jajaye ne gashi abincinsu da yawa ita ba iya ci tayi ba duk shekarun da tayi a kasar su. Almost 30 mins after Khaleesat dake ta zaune tana tunane tunane ko abincin ta kasa ci ta daga kai taga Ajay ne ya shigo parlon, sunkuyar da kanta tayi, bai kalli inda take ba yayi wucewarsa dinning Area ya fara cin abincinsa, after a while Khaleesat ta daga kai a hankali jin footstep, taga Housemate dinta ne ke saukowa downstairs, ya karaso har inda take ya zauna kan kujera yace "Kin ci abincin?" Ta gyada masa kai, cook din gidan ya kira ya dauke sauran abincin ya tafi da su, Jay yace "To ki koma kan kujera" Ita dai Khaleesat kanta na kasa bata ce komai ba, har sai da Jay ya sake mata magana sannan ta mike ta koma kan kujeran ta zauna, AJ ya dawo cikin parlon ya tafi reading nook dake parlon, Jay ya bi sa da wani kallo har ya gama kakkabe kakkabensa ya zauna, ko uban me zai yi a can don yasan dai baya ma zuwa nan balle yayi karatun a nan, muryar Jay ya dawo da hankalin Khaleesat jikinta, taji yace "So Halysaah i want to even know what happen first of all at ur apartment today, don ni ban san me ya faru ba, Salem called me yace kin kirani ban daga ba and you sound disturb, and he gave you AJ's number, i rang you back quickly sai kiran bai shiga ba, shine nayi deciding in je can gidan kawai, menene ya faru?" Khaleesat ta sunkuyar da kai don bata ma san me zata ce masa ba, ta yaya ma zata fara cewa raping dinta Abdul ya so yi, muryar AJ suka ji a parlon yace "Allah ma yasa ba rashin kunyan da ta saba yi ma mutane taje tayi masa ba, kawai ta sa na doki bawan Allah a banza" Khaleesat dai bata dago kanta ba, shi dai Jay yayi murmushin da bai yi niyya ba yana kallon direction din da AJ yake, A hankali Jay yace "You are not saying anything Khaleesat" Hawaye ne ya cika idonta, ganin haka Jay yace "Or you don't want to talk about it?" Ta girgiza masa kai hawaye na sauka idonta da kyar tace "Ba haka bane, he tried molesting me" AJ that heard what she said duk da ba kallon direction dinta yake ba yace "He tried molesting you, amma da hannunki ai kika bude masa kofar ba ta window ya shigo ba" Jay ya wani kallesa yace "Stop this please AJ, why are you so wicked and heartless" AJ yayi wata dariyar bosawa, Jay ya dinga hararansa, ita dai Khaleesat hawaye ne kawai ke zuba idonta, tsabar ciwon da kanta ke mata har wani dishi dishi take gani, Cikin kwantar da murya Jay dake kallonta yace "Tell me who he is, and where did you know him from" Ta gyada masa kai tana share hawayen da yaki tsaya mata a hankali tace "Shekara hudu kenan na san shi....." *Don't even know where to start from, the patronage was massive🥺, thank you soo much for encouraging me fans, Allah ya biya maku bukatunku na alkhairi, Allah ya raya zuri'a, i soo much appreciate ur patronage, marasu auren cikin ku Allah ya baku mazaje na gari, masu aure kuma Allah ya ci gaba da baku zaman lafiya a gidajenku, Allah ya karo maku budi ninkin ba ninki, ya raba ku da iyayenku lafiya* 🥺 _Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta i owe you 500_ 22 Khaleesat ta sunkuyar da kanta har sannan bata daina goge hawayen da ya ki tsaya mata ba, she look pained and traumatized, Shi dai Jay kallonta kawai yake waiting for her to continue with what she is saying, jin tayi shiru yace "Halysaah" Ta daga idanuwanta ta kallesa, Calmly yace "I am listening" muryarta na rawa tace "Kawai dai shi ne ke sponsoring dina" Ba Jay da ya kafeta da ido ba yana mata kallon mamaki, har AJ sai da ya juya ya kalleta daga inda yake zaune jin abinda tace, Jay was just speechlessly staring at her, can dai ya gyara zama yace "You mean shi yake sponsoring dinki a kasar nan? Are you related in anyway with him?" Ta girgiza masa kai kawai, da mamaki kawai yake kallonta, after few seconds yace "And ur parent allowed him to sponsor you har zuwa nan America?" Ta gyada masa kai without looking at him, mikewa AJ yayi, yayi wucewarsa sama, Jay ya bi sa da kallo don shi ma ya rasa abun cewa don mamaki, Jay ya maida dubansa kan Khaleesat a hankali yace "Ya kai kudin aurenki ne an sa maku rana?" Ta daga idanuwanta ta kallesa cikin sanyin murya tace "Nima ban sani ba, amma kamar ya kai" Jay yayi shiru for almost 3 minutes with different thoughts running his mind, everything just took him unaware, bai taɓa tunanin saurayin nata ne sponsor dinta all this while ba, can ya daga kai ya kalleta yaga ta jinginar da kanta jikin kujera looking so tired and pale, yana son sanin me ya hadata da Abdul, meye ma dalilin haduwarsu, sannan a ina ma suka hadu da shi din, what is this great thing that motivated her parent har suka amince ma stranger da basu hada komai da shi ba ya turo er su har wata kasa karatu, he just don't want to believe it's because of money they did this.... amma ganin yanayinta yasa yayi keeping all the questions to himself for now don baya son ya kara stressing dinta, she is already stressed, mikewa yayi calmly yace "I will be back now" Ita dai ta bi sa da kallo har ya haura sama, wasu hawaye taji na taruwa idonta, kawai so take tayi kuka me sauti ko zata ji saukin abinda take ji a ranta, ta hade kanta da kujera tana shessheka a hankali, Jay na haurawa sama ya tafi dakin da ya sa daya daga worker din gidan ya kara gyarawa, the room was big sai dai bai kai nasa da na AJ ba, kuma babu abinda babu a dakin sai Duvet na saman bed spread, ya bude press din dakin yaga babu a nan ma, juyawa yayi ya fita ya dau hanyar dakin AJ, yana isa ya danna code din bude kofar dakin ya murda yaga bai buduwa, yasan canzawa yayi kenan saboda ya shigo masa dakin daxu, knocking din kofar yayi, after a while AJ ya bude kofar yana kallonsa alamar what happen, Jay ya turasa gefe ya shiga cikin dakin, AJ ya bi sa da kallo yace "Ka dai san bana son haka Jawwad, what are you looking for?" Jay ya kunna wutan dakin that is more brighter yace "Duvet zaka bani, i don't understand dalilin da yasa zaka kwashe kaf duvet din sauran rooms din all to ur self, this is greed" AJ dai kallonsa kawai yake cause he is already angry shigo masa da Jay yayi daki, ganin Jay ya nufi inda duvet dinsa suke yace "Jay me zaka yi da duvet bayan kana da naka a daki?" A takaice Jay yace "I am giving my visitor" AJ ya bude baki yana kallonsa yace "What??? I don't understand, Duvet dina zaka dauka ka kai ma visitor dinka? are you even okay? Can you hear ur self pls?" Jay bai tanka sa ba ya dau na saman gadonsa kawai ya nufi kofa, AJ ya tare kofar on a serious note yace "In ka fita da duvet din nan ka canza min suna yau" Jay ya wani turasa daga bakin kofar har sai da ya kusa faduwa sannan ya fice daga dakin, sai bayan da ya fita ya juya ya kalli AJ da ya bude baki yana kallonsa with shock, Jay yace "Emmanuel" daga haka yayi wucewarsa ya bar AJ da bin sa da kallo, Jay na komawa ya ajiye duvet din kan gadon dakin da aka gyara ma Khaleesat sannan ya sauka downstairs, tana nan zaune yanda ya bar ta idonta a lumshe amma ba bacci take ba, yace "Halysaah" Bude ido tayi da sauri bayan ta dawo duniyar tunanin da ta tafi, yace "Tashi mu je sama, u need rest" Ita dai tayi shiru bata ce komai ba, ya dau laptop dinta da takardunta yace "Mu je" Sai bayan da ya fara tafiya sannan ta mike a hankali ta bi bayansa, har wani jiri take ji amma a haka ta daure ta bi sa har zuwa sama, ya bude kofar dakin ya shiga tana biye da shi, bayan ya ajiye laptop din hannunsa ya kunna mata na'uran da zai dumama dakin, ya nuna mata hanyar bandaki ita dai kai kawai ta gyada masa, ya ciro wayarsa a aljihu yayi dialing number sannan ya mika mata yace "In case u need anything sai ki kira number da nayi dialing it's my other line" Nan ma dai kai kawai ta iya gyada masa, yace "Good night Halysaah, pls kiyi bacci sosai, do not bother ur self kin ji?" a hankali tace "Toh" kofa ya nufa ta bi sa da kallo sai da ya bude kofar a hankali tace "Nagode" Ya juya ya sakar mata murmushi yace "I gat ur back" Daga haka ya fita ya kullo mata kofar dakin, Khaleesat ta ajiye wayar tasa da ya bata sannan ta zauna gefen gadon dakin a hankali staring at the window absently. Har karfe dayan dare Khaleesat bata ji ko digon bacci ya zo mata ba, tana dai kwance tayi lamo cikin duvet, her heart is soo heavy, har wani zafi take jin yake mata, ga wani zazzabin da taji ya lullubeta, tun da Jay ya bar ta take kuka, gani take kamar duniyar ya tsaya mata ne cak, ta ma rasa wani kalan tunani zata yi, abubuwan da suka faru daxu suka dinga dawo mata abun sai yake mata kamar mafarki, she wish mafarkin ne ma kawai, yanzu babban tashin hankalinta bata san me zai faru a Nigeria ba, bata san next step din Abdul ba, bata san me zai ma iyayenta ba, duk wannan tunanin ya hadu yayi distabilizing dinta, zazzabin da take ji ya karu sosai, tana son tashi taje tayi alwala tayi sallah ko zata samu sukuni amma ta kasa, duk jikinta ciwo yake mata ga ciwon kai kamar kanta zai fashe, da taji azaban yayi mata yawa kamar zata kira Housemate dinta ta tambayesa maganin ciwon kai amma ta fasa don bata san ko bacci yake ba, haka tayi ta juye juye jikinta yayi zafi sosai, yanda taga rana haka taga daren nan that was soo long to her, bacci ko na barawo bai dauketa ba, jin vibration din da wayarsa yayi yasa tayi karfin halin jawowa tana kallon screen taga alarm ne na karfe biyar, ta kashe alarm din tana son tashi don tayi sallah amma ta kasa, daga karshe dai haka tayi karfin hali ta daure ta tafi bandaki ta dauro alwalan, tana idar da sallan taji zazzabin da yafi na baya ya lullubeta gaba daya, kwanciya tayi saman gado ta rufe har kanta da duvet din. Wajen karfe takwas na safe Jay yayi knocking kofar dakinta, tana ji amma ta kasa amsawa, sau uku yana knocking jin bata amsa ba sai ya kira wayarsa dake wajenta nan ma tana kallon kiran amma ta kasa daga hannu ma ta dau wayar, sai da ya katse sannan ya bude kofar dakin da sallama ya shiga, yana kallonta da mamaki ya nufeta yace "Are you Okay Halysaah?" Kai kawai ta girgiza masa, ya duka kusa da ita yace "Baki da lafiya ne? Why didn't you call my line?" Hawaye ya gani idonta, yace "Haba Halysaah, ba nace kar ki sa ma kanki damuwa ba? Did you want to hurt ur self?" Ita dai bata ce komai ba, ya juya ya fita daga dakin, after some minutes ya dawo da Hot chocolate ya ajiye mata yace "Ki daure ki sha pls, let me get you medicine" Yana fadin haka ya juya ya fita daga dakin, ko da ya dawo ya ga bata tashi ba still, duk yanda yayi da ita ta tashi ta sha shayin ya bata magani taki tashi, gaba daya ya ma rasa yanda zai yi da ita, can ya kara dukawa kusa da ita yace "Did you have ur frnd safiyyah's number offhand?" Da kyar ta girgiza masa kai, yace "U have her IG handle? Is she active on IG?" Bata ce masa komai ba don ta ma kasa maganan, he look confuse at this point, can dai yace "To zaki iya daurewa ki tashi mu tafi asibiti?" Ta girgiza masa kai, mikewa yayi kawai ya fita daga dakin, downstairs ya sauka don AJ na dinning yana breakfast ga Legend dinsa zaune ɗan nesa da shi a dinning area din, Jay ya nufesa looking confuse yace "AJ, the girl is seriously sick fa" AJ dake sipping tea dinsa yace "Which girl?" Jay ya masa wani kallo yace "Please be serious AJ, wallahi bata da lafiya sosai" AJ yace "To yanzu daukar ta zaka yi ka kai ta Hospital kenan..." Jay yace "How?? ko tashi fa bata iya yi, plss ko zaka mata allura ta ɗan samu relieve tukun?" A hankali AJ ya ajiye Mug din hannunsa yana kallon Jay baya ko kiftawa, can ya matsar da shayin gabansa yace "Amma dai don Allah me yasa ka raina ni haka ne Jay? Me nayi maka? Kai me hannunka yake da bazaka mata allura ba sai ni?" On a serious note Ajay ke masa tambayoyin nan looking at him and waiting for his answer, Jay yace "Da gaske fa you are Heartless Junaid, ince maka yarinya ko tashi bata iya yi? Why are you like this pls?" AJ yace "But like seriously kai uban me hannunka yake da bazaka mata allura ba sai ni? Baka fi ni zama likita ba? Wato ni ne ɗan iska ko?" Juyawa Jay yayi ya bar wajen ya koma sama, yana bude kofar dakin ya ganta duke kusa da kofar bandaki, ya karasa kusa da ita da sauri ganin yanda ta galabaita yace "Did you throw up?" Kai kawai ta gyada masa tana maida numfashi, gun da ya ajiye hot chocolate din ya tafi ya dauko mata yace "Pls ki sha ko kadan ne sai in baki magani" Ta girgiza masa kai, yace "C'mon Halysaah, kadan fa za ki sha" Yana rike da cup din don kar ya sakar mata ta zubar, a haka ta kurbi shayin kadan, sai da yasa ta kara sha sannan ya ajiye shayin ya dauko magani, tana ganin maganin ta fara girgiza masa kai da sauri don har taji wani aman zai taho mata, bude kofar dakin aka yi Jay ya juya, AJ ya gani tsaye bakin kofar yana kallonsu, Jay bai sake kallon inda yake ba ya maida dubansa kan Khaleesat yace "Pls ki daure ki sha Halysaah, ko baki son ki samu relieve?" Kara girgiza masa kai tayi hawaye ya fara sauka idonta, lallabata Jay ya fara yi akan ta sha maganin, AJ ya wani hade rai yace "Kee baza ki amshi maganin da ake baki ba? Wa zaki ba wahala?" Jay yace "Ba ruwanka pls AJ, get out" Ita dai Khaleesat ko kallonsa bata yi ba tana fama da kanta, Jay bai sake takurata kan ta sha maganin ba ya mike yace "Toh ki daure ki hau kan gado ki kwanta, i am coming now" Ta gyada masa kai, ya juya ya nufi kofa, ko kallon Ajay bai yi ba ya fita daga dakin, AJ ya tabe baki ya juya ya koma downstairs. Haka nan Jay ya hado alluran da za mata don saukar mata da zazzabin, sai da ta ga ya dawo dakin sannan ta daure ta koma saman gadon tana ganin jiri ta kwanta, ya tsaya gefen gadon yana rike da alluran yana kallonta, ta marairaice ta girgiza masa kai kawai alamar bata so, ya kwantar da murya yace "To ya kike son in maki Halysaah? Kin ki shan magani" wayarsa dake aljihunsa ya ciro jin yana ringing ganin Salem ke kiransa ya ajiye alluran hannunsa yace "I am coming Halysaah" Fita yayi daga dakin, ya sauka downstairs ya tarar da Salem zaune parlor, bayan sun gaisa Salem yace "Slide dina nake son zaka duba min Jay" Shi dai AJ na zaune yana kallon kwallo ga Legend a gefensa, Jay yace "Ohk, but tunda ka zo pls zaka yi injecting Housemate dita she is sick" Salem yace "Ayya, shi sa ta kira jiya, Allah ya bata lafiya, tana can gidan nata ne?" Jay yace "No, she is upstairs, mu je in nuna maka dakin da take" A tare suka wuce sama, AJ dai kallonsa kawai yake a TV kamar bai san suna parlon ba, Jay bai shiga dakin ba bayan ya nuna ma Salem ya dawo downstairs ya zauna, Khaleesat bata yi ma Salem wani musu ba don ba ma ta da wannan strength din duk da yanda bata son allura haka nan ta bari ya mata, tsabar zazzabin dake jikinta ko zafin shigar alluran bata wani ji ba, Salem yayi mata Allah ya sauwake sannan ya fita daga dakin ya koma downstairs, Jay yace "Thank you, bari in duba maka" Sai bayan kusan minti talatin Jay ya tafi dakin Khaleesat ya sameta tayi bacci, ya sauke ajiyar zuciya ya karasa kusa da gadon ya kai hannu kusa da goshinta sai dai bai taɓa ta ba, nan yaji temperature dinta ya fara sauka, juyawa yayi ya dau sauran shayin da ta bari ya fita daga dakin..... Wajen karfe sha daya da rabi Khaleesat na kwance hannunta rike da wayar Housemate dinta, tun 20 min ago ta tashi daga baccin da ya dauketa daxu, she felt a bit relieved now da alluran da Salem yayi mata, sai dai har sannan kanta bai daina mata ciwo ba kamar ta cire ta huta, tayi kokarin ta tashi ma ta tafi bandaki amma ta kasa, she is so weak kamar warce ta dade tana ciwo, hakan yasa kawai ta jawo wayar Jay, da har zata shiga gallery dinsa to while away time amma sai taga it's not proper ta shiga hotunansa, hakan yasa ta shiga wani game da ta gani kawai tana yi daga kwancen da take, bude kofar dakin aka yi ta daga idonta, Jay ne ya shigo dakin AJ dake bayansa yaki karasowa ciki ya tsaya daga bakin kofar, Jay ya nufota yace "Ashe kin tashi, how are you feeling now Halysaah?" Ta gyada masa kai a hankali tace "Good morning" Yace "Morning Housemate, are you feeling much better now?" Kai kawai ta gyada masa, yace "Ohk bari a kawo maki breakfast, idan kinyi sai ki daure ki sha magani kin ji" Ita dai bata ce masa komai ba ya juya ya nufi kofa ya fita ya mika ma AJ wayarsa sannan ya sauka downstairs zai kawo mata breakfast, shi dai AJ daga sama har kasa yake kallonta, ta ɗan saci kallonsa to see if he is still standing by the door ko ya tafi, hada ido suka yi ta dauke idonta tana ci gaba da game dinta da take, after a while ta kara satan kallon bakin kofar taga ya bar wajen, sai ga Jay ya shigo ya ajiye mata tray din breakfast ta dinga kallon plate din baked beans irin na turawa a gefe da soyayyen kwai a gefe, with veggies, sai sausages, ga cup din hot chocolate with few slices of bread a gefe su ma, ita dai tasan ba iya cin wannan abincin zata yi ba, yana kallonta yace "Can you give me ur frnd Safiyyah's Home address?" Ta sauke idonta ta gaya masa address din, yace "Ohk, na ma san area din, i have a frnd there" Ita dai tayi shiru, ya dauko mata maganin da taki sha daxu ya ajiye kusa da ita yace "Pls ki daure kiyi breakfast din, sai ki sha drug din kafin in dawo" A hankali tace "Toh nagode" ya mata murmushi ya juya ya fita daga dakin ta bi sa da kallo. Jay ya tarar da AJ zaune a waje gurin shan iska dake compound din yanna danna wayarsa, hakan yasa ya nufesa ya zauna kujeran dake facing dinsa yace "AJ, i think i am confuse at this point, what do u suggest about this young girl's issue?" AJ ya daga ido ya kalli Jay yace "My suggestion is that... ka barta ta tafi duk inda ma zata ka cire hannunka da bakinka cikin wannan case din babu abinda ya shafe ka, a cikin kunnenka kaji tace shi gayen ne ke sponsoring dinta, babu kuma ta yanda zai yi sponsoring dinta without the consent of her parent, kaga they are comfortable with that, so who are you to intrude Jawwad? Baka san komai akan ta ko kan saurayin ba don me zaka zakalkale haka? Tare fa ka gansu, da can baya zuwa America din ya sameta ne a gidan? sai yanzu tasan yana molesting dinta? Girl's can be very cunning fiye da tunaninka, don't start what u can't finish Jawwad" Jay dake ta kallonsa yace "So now what are you insinuating?" AJ yace "Since you are daft kar Allah ya sa ka gane abinda nake insinuating" Jay dai kallonsa kawai yake, after a while a hankali yace "But duba da abinda ya faru tsakaninka da guy din kasan zai iya hurting dinta idan nace ta koma gidan nan AJ, she is no longer safe in that apartment, ka dai ga ba ma cikakken hankali ke gare gayen ba, ka duba fa wuka yaje ya dauko a kitchen" AJ ya gyara zama yace "Sai kayi mata hanyar komawa gun iyayenta as the good Samaritan that you are from Samaria, kaga in ta koma sai ta gaya ma iyayen nata abinda ke faruwa da abinda selfishness dinsu ya ja mata a kasar mutane, sai su yi sorting kansu a can kawai" Jay yace "Kar kace haka, we know nothing about why they allowed him to sponsor their daughter, we shouldn't judge them har sai mun san dalilinsu AJ" AJ yace "Dalilin banza, babu responsible parent din da za su damka ma kato irin wannan mutumin er su ya kai ta wata kasa da sunan karatu, it doesn't even make sense, sai kace ba musulmai ba, ko da cousin brother dinta ne ma abun bai yi tsari ba balle babu ko wani relationship na jini tsakaninsu, who does that" Jay ya sauke ajiyar zuciya yace "Duk da haka dai ni bazan yi judging dinsu ba tare da nasan komai ba, let give them benefit of doubt" AJ yace "Sai kayi ta basu ai, ni kam bazan bayar ba" Jay yace "But komawarta Nigeria yanzu bazai yiwu ba AJ, ba shine solution ba, Monday za su fara exams, John Hopkins university take ita ma fa" AJ yayi dariya har da kyakyatawa yace "Tabb, lallai gayen ya kashe kudi ba na wasa ba" Jay dai kallonsa kawai yake, AJ yace "Toh za a fara exams me kake nufi kenan? Naji ka ce apartment din nata is not safe for her anymore..." Jay yace "She will remain here har su gama exam kafin ta koma Nigeria wajen iyayenta" AJ ya wani kallesa da sauri yace "What do you mean? Kana nufin mu zauna gida daya da balagaggiyar yarinya da ba muharramar mu ba kamar wasu jahilai marasu tsoron Allah? Kai da wa za ku yi wannan nonsense din??" Jay yace "Duk yan iskan turawan da kake kawowa gidan nan ka basu daki su zauna dama muharramanka ne ban sani ba?" AJ yace "Turawa kace ai, kuma babu komai tsakanina da su kai ma ka sani, i am only helping most of them tunda ba a garin nan suke ba" Jay ya mike yace "Ita ma haka za mu yi helping dinta tunda ba a garin take ba, take it or leave it" yana kai wa nan yayi wucewarsa inda yayi parking motarsa, Ajay ya bi sa da wani kallo, can yace "Sai dai ku je can ku biya wani apartment din ku zauna tare, babu wanda zai takurani a gidan nan wallahi, dama ai kun saba zama gida daya tare, it's not a new thing, dole ne sae ta zauna gidan nan cikinmu mu ba maguzawa ba" Shi dai Jay ya shiga motarsa ya fita daga compound din ya kama hanyar gidansu Safiyyah.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* 23 Jay na isa unguwan da gidansu Safiyyah yake sai ya mance apartment din da Khaleesat ta gaya masa, hakan yasa ya kira wayarsa dake wajenta, Khaleesat na zaune saman gado har sannan tana playing game da wayar, sosai gabanta ya fadi ta dinga kallon screen din wayar ganin image din hotonsa da number da yayi appearing, sai taga kamar shi din ne a gabanta take gani, sai da kiran ya katse ta zaro ido bayan tayi realizing bata yi picking ba har ya katse, bayan few seconds ya sake kira, dagawa tayi ta sa handsfree tayi shiru, yace "Halysaah" Tace "Na'am" Yace "I think i forgot the apartment u told me" Gaya masa ta sake yi yace "Thank you" Daga haka ya katse wayar ya ci gaba da driving dinsa, dai dai gaban apartment din yayi parking don motar Mustapha baya nan, yana tsaye bakin kofa yayi knocking gently, after a minute aka bude kofar parlon, komawa baya Safiyyah tayi tana kallonsa da mamaki daga sama har kasa, ya ɗan mata murmushi yace "Hi Safiyyah" Ta bude ido sosai tana leka motarsa da taga yayi parking thinking may be he is together with Khaleesat, ganin motar ba kowa ciki tace "Hi, good afternoon" Yace "How are you doing Safiyyah?" Lokaci daya tace "Ko dai Khaleesat bata da lafiya ne?" Da damuwa sosai tayi tambayar, Yace "Yeah bata da lafiya" Tace "Wallahi yanzu na gama shiryawa nake son in ci abinci inje gidan naga miss call dinta jiya ina ta kira har yau wayar baya shiga, and i am disturb" Yace "Shi yasa na zo in dauke ki idan ba damuwa so you can be together with her she is sick, probably idan kin mata magana zata ci abinci ta sha magani" Da sauri Safiyyah tace "Sure, bari in dauko gyalena" Juyawa tayi da sauri ta koma cikin gidan, shi kuma ya koma parking space, Surayya dake zaune a parlon ta kasa kunne duk tana jin conversation dinsu kafin Safiyyah ta shigo, Safiyyah ko kallon direction dinta bata yi ba ta tafi dakinta da sauri ta dauko jakarta da gyale sai wayarta sannan ta fice daga gidan, ganin Jay cikin motarsa yana jiranta ta bude gaban motar ta shiga tana cewa "Tun jiya ne bata da lafiyan? Kuma me yasa ta kashe wayarta?" Jay yace "Tace wayar ya fada ruwa ne" Safiyyah tace "Ohk" Sai da suka dau hanya sannan Jay yace "Amma tana can gidanmu fa, can za mu je yanzu" Safiyyah ta juya da sauri tana kallonsa da mamaki tace "Gidanku? Why? What happened?" Calmly yace "Before then za mu fara zuwa apartment dinmu sai ki dau mata kayanta da zata yi amfani da shi, we left yesterday with nothing" Safiyyah bata sake cewa komai ba tunani iri iri na yawo a ranta, to me ya faru? ta yaya Khaleesat da ta sani me shegen taurin kai ta yarda har ta bi sa can gidan nasu? Ko dai rashin lafiyar nata is critical ne haka? Da tunane tunanen nan suka isa apartment din, suka shiga ciki tare da Jay ta nufi dakin Khaleesat shi kuma ya zauna a parlor, bayan few minutes ta fito tace "Kala daya zan dau mata kayan ai ko?" Jay ya mike yace "No, 3 to 4 will be okay" Duk da confusion din da Safiyyah ta shiga bata dai ce masa komai ba ta juya ta koma cikin dakin, ta dau akwati ta saka ma Khaleesat kayanta da duk abinda zata bukata a ciki, tana fitowa daga dakin Jay ya mike yace "Kin dau mata duk abinda zata bukata?" Safiyyah ta gyada masa kai, suka fita daga parlon, duk ta kagu taje wajen Khaleesat ita dae, silently suka yi tafiyar har suka iso gidan, bayan Jay yayi parking ya sauka Safiyyah ma ta sauka, ya fiddo akwatin sannan suka nufi entrance din apartment din Safiyyah na biye da shi, bai ga motar AJ a gidan ba alamar ya fita, suna haurawa sama Jay ya tafi dakin da Khaleesat take yayi knocking, ya mika ma Safiyyah akwatin yace "Zaki iya shiga, zan je inyi sallah" Safiyyah ta amshi box din tace "Ohk" Bude kofar dakin tayi Khaleesat ta dinga kallonta har ta shigo, Safiyyah ta ajiye box din hannunta ta nufeta da sauri tace "Me ya sameki Khaleesat?" A hankali Khaleesat ta sauke idonta ta kasa cewa komai don bata ma san ta inda zata fara ba, sai ga hawaye. Safiyyah na tsaye dakin kusa da window bayan Khaleesat ta bata labarin duk abinda ya faru, tsabar yanda labarin ya kidima Safiyyah kasa ci gaba da zama tayi gefen gadon, Safiyyah tayi shiru for almost 2 minute tana tsaye jikin window tana girgiza kafa, ita dai Khaleesat goge hawayen dake sauka idonta kawai take, can Safiyyah ta sauke wani ajiyar zuciya me cike da takaici tace "A baya da nake gaya maki Abdul ɗan daba ne ba kin maida maganata abun wasa ba? Tunda uwata ta haifeni ban taɓa ganin ɗan iska kamar Abdul ba, yanzu da baki samu lambar kowa ba haka zai lalata maki rayuwa babu digon tsoron Allah a ransa? Ya kashe uban kudin zuwa USA kawai don ya zo yayi lalata? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, amma naji haushi da ɗan uwan Housemate dinki bai sumar da shi ba an maida sa Airport a haka, tirr da Abdul, tirr da halinsa, i am so happy that things turn out this way, in sha Allahu karshensa ne ya zo a rayuwarki" Khaleesat ta fashe da kuka tace "Sophie ban san next action dinsa ba idan ya koma Nigeria, i am so restless" Safiyyah tace "Next action dinsa? Sai ya koma ya gaya masu uban da ya kawosa USA da Intention dinsa, ke in zaki dena wannan crocodile tears din naki ki dena don ba tausayinki zan ji ba, tunda dai bai samu nasaran lalata maki rayuwa ba ni duk abinda zai faru ma ya dade bai faru ba, kukan uban me kuma kike ma mutane? Ko nasaran da bai samu a kanki bane ya dame ki? Kuma wallahi ya ci sa'ar baki sameni a waya ba don kafin in karaso gidan sai 911 sun riga ni, tuni zan kirasu ince gashi can za ayi fyade, banda iskanci duk karuwansa basu ishesa ba sai ya zo ya kara dake? Gaskiya ki rike Housemate dinki da ɗan uwan nan nasa da kyau don mutane ne su wallahi, da ba don su ba da yanzu wani zancen ake ba wannan ba, don da na kai maki ruwan zafi yafi a kirga zuwa bandaki yanzu" Khaleesat dai bata sake ce mata komai ba tana share hawayen da yaki tsaya mata, Safiyyah ta rike haɓa har sannan tana mamakin Abdul, can tace "Kamar irin ya zo wajen matar nan tasa, ni wallahi da yaji suka barbada masa mu ga ta iskanci, shege kawai prostitute" Duk tashin hankalin da Khaleesat ke ciki sai da tayi dariya don ita bata taɓa jin inda aka ce ma namiji prostitute ba sai yau a bakin Sophie, Safiyyah tace "Ga dai katon daki an baki, kiyi karatun exams dinki cikin kwanciyar hankali, nima in abun duniya ya isheni in taho nan in sameki kafin dare yayi in koma den dina, don ko da wasa bazan ce ki dawo gidanmu ba ni kaina ban tsira gun tsinanniyar matar Yaya Musty ba kuma yaki kwatar min en ci, da zai bar ni ba nima sai in dawo nan kusa dake ba tunda ba rasa abincin da za su bamu mu ci za su yi ba, wannan dakin ai ya ishemu rayuwar America, bari kiji Khaleesat dama Allah ya riga ya rubuta Abdul ne silan zuwan ki Amurka ki hadu da mutanen arzikin ki, babu me canza haka ko yaki ko ya so dole sai ya kawoki ya hadaki da mutanen arzikin ki tunda Allah ya rubuta haka, iya role dinsa kenan a rayuwarki, kuma Allah ne zai basa ladan hakan bamu ba, ba shikenan ba?" Khaleesat dake ta kallonta ta girgiza mata kai tace "Ni bazan zauna gidan nan ba Sophie" Safiyyah na mata wani kallo tace "Ohk, Apartment din naki zaki koma ki kai ma Abdul din kanki kenan?" Khaleesat ta sauke idonta kasa muryarta na rawa tace "Bazan iya jarabawan ba Sophie, gwara kawai in koma gida, i want to go home, i want to go to my mother" Safiyyah zata yi magana aka yi knocking kofar dakin, Safiyyah ta amsa aka bude kofar Jay ya shigo, kallon Khaleesat yake yace "Kin sha maganin Housemate?" Ta gyada masa kai without looking at him, Safiyyah ta kallesa cike da damuwa tace "Ashe kuma iftila'in da ya faru kenan jiya Yaya Housemate? To Allah Ubangiji ya tsare na gaba, ku kuma Allah ya saka maku da alkhairi ya baku ladan hidimar da ku ke yi da kawata don bata da kowa a garin nan sai Allah sai ni da ku, kuma she is not longer safe in this state don Abdul can be cunning, azzalumi ne mugu, nasan har yanzu yana labe garin nan bai tafi ba, kuma ba imani ne da shi ba ina jin tsoron next move dinsa, Allah kadai yasan sau nawa ya koma apartment din nan yaga babu kowa ciki" Jay dai ya ɗan yi murmushi yace "She will remain here har ta gama exams dinta in sha Allah" Khaleesat ta kallesa ta girgiza kai cikin sanyin murya tace "Bazan iya exam din ba, Nigeria nake son tafiya" Safiyyah ta mata wani kallo kamar zata ce in tana da kudin jirgi ta tafi sai dai kuma kawai tayi shiru tana hararanta, Jay ya kwantar da murya yace "Saboda me baza ki iya exam ba Khaleesat, stop saying that pls, in sha Allah zaki yi jarabawan ki lafiya, in kun gama sai ki koma Nigeria" Safiyyah tace "Atoh shi dai na gani, kan wani tantirin ɗan iska take son lalata future dinta, duka duka fa shekarar karshe za mu shiga yanzu a makarantar" Khaleesat ta sauke idonta hawaye na sauka idonta don tasan baza su gane abinda take nufi ba, Jay ya sauke ajiyar zuciya yace "Try calming her down Safiyyah, and naga tun jiya bata wani ci abinci ba ban san ko tafi son abincin Nigeria ne ba, nasa cook din gidan yayi ordering ingredient din har an kawo, i don't know ko zaki girka mata a kitchen tunda kina nan" Safiyyah tace "To ba damuwa, let me cook for her" Yace "Alright" a tare suka bar dakin Khaleesat ta bi su da kallo hawaye na bin fuskarta. Tunda suka shigo kitchen din Safiyyah ke bin ko ina da kallo don the kitchen is so big and well equipped, irin modernize kitchen din nan, bayan Jay ya fita cook din gidan ya nuna mata ingredients din shinkafa da miya sannan shi ma ya fita, tuni ta hau girkin a kitchen din. Wajen karfe biyar Safiyyah na daki tare da Khaleesat hira kawai take mata kamar ba abinda ya faru, ita dai Khaleesat tayi shiru tana kallonta amma gaba daya hankalinta baya kan hiran, wayar Safiyyah ya fara ring ta jawo jakarta ta ciro wayar ganin Mustapha ke kiranta ta wani turo baki sannan tayi pick ta sa handsfree tace "Ina wuni yaya" Ko amsa gaisuwar bai yi ba yace "Waye ya zo ya daukeki a mota Safiyyah?" Safiyyah ta bude baki tace "Ohh haka matar taka tace maka? to ta manta a jirgi aka zo aka daukeni ba a mota ba, kuma munafurcinta zai kare mata wallahi" Tsawa ya daka mata yace "Ina maki magana kina min maganar banza? Are you okay?" Ta wani murguda baki tace "Toh ba ina hanya bane wai, haka kawai dai babu dalili bazan kama hanya in fito cikin sanyin nan ba yaya, ko ka manta jibi za mu fara exams ne?" Kashe wayarsa yayi, Safiyyah tace "Allah dai ya tsine ma Surayya albarka, kuma wallahi kafin mu gama exam mu bar kasar nan sai na mata abinda bazata taɓa mantawa ba a rayuwarta, ko da wasa kuma bazan ma gaya masa abinda ya faru dake ba kar yayi burgan cewa ki dawo gidansa ya kara ma matarsa extra nama" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, Safiyyah ta mike ta dau jakarta da gyale tace "Sai na zo gobe in sha Allahu, saura kar ki karasa cinye abincin ki zauna kina asaran hawayenki akan ɗan daba, ga lambata na sa maki a waya in da wani abu ko kuma kina bukatar komai kawai ki kirani" Daga haka ta fice daga dakin, Khaleesat ta sauke idonta kasa, Downstairs Safiyyah ta hadu da AJ wanda shigowarsa gidan kenan tana ɗan murmushi ta gaishesa ya tsaya ya amsa yana danna wayarsa yace "How are you doing" Tace "Alhmdlh ya karatu" Yace "Fine, ya naki" Tace "Muna ta fafatawa dai, to fa mun gode da hidima yaya, Allah ya saka da alkhairi da abinda ku ka ma kawata, Allah ya biya ku" Sai a sannan ya daga kai ya kalleta jin wai tana masa godiya, ita dai ta ci gaba da godiyar ta ba kakkautawa, Yace "Ameen" Tace "Yaya Housemate din ya fita ne, ni zan koma gida ne yanxu" Sai ga Jay ya shigo parlon from outside, ganinta yace "Ohk zaki koma Safiyyah?" Tace "Eh wallahi yamma tayi amma in sha Allahu zan shigo gobe da safe" Yace "To Allah ya kai mu, mu je inyi dropping dinki" Tuni AJ yayi wucewarsa sama, Safiyyah ta bi bayan Jay suka fita daga parlon tana mamakin inda karen gidan yake bata gansa ba tun daxu, sai bayan da suka dau hanya tace "Yaya Housemate...." Dariya ta ba Jay bai jira me zata ce ba yace "I am Jawwad Safiyyah" Tace "To ni dai don Allah kayi dubara ka amshe wayar da ka ba Khaleesat kar taje ta kira yan gidansu su gigita ta, kaga bamu san ko Abdul din na kasar nan ba ko ya koma Nigeria, in ta kira suka gaya mata wani maganar da kyar ta iya abun arziki a jarabawan nan" Jay yayi shiru cause he reason with what Safiyyah is saying, can yace "Haka ne kuma, i will tell her not to speak to anyone for now, amma bazan iya amsan wayar ba naga kamar it's whiling away her time" Safiyyah tace "To in da kati a wayar don Allah ka kone sa, in da WhatsApp kayi uninstalling dinsa kaga ta haka babu wanda zata ma magana, the exams is just for a few weeks, kamar gobe ne za mu gama" Yace "Sure i will do so Safiyyah" A haka suka isa gidansu ta sauka daga motar ta masa godiya yace "Ki gaida mutanen gidan" Tace "To za su ji" Yayi reverse ya dau hanyar gida hoping Khaleesat bata riga ta ma kowa magana back in Nigeria ba. Washegari da safe Jay yayi booking appointment na ganin likita saboda daren ranan ma Khaleesat dai bata yi bacci ba, yasan dai ba lallai su samu ganin likitan a ranan ba, so he was just helping her to manage her self with the drugs available, da Safiyyah kuma ta zo sai taji ta nemi zazzabin ta rasa dama kadaici ne da damuwa suka mata yawa. Ranan monday da safe Jay yayi dropping din Khaleesat school for her first exam, and he stayed behind har zuwa sanda za su gama don su koma gida tare, kawai shi dai baya son barin ta ita kadai, Jay is trying his very best na ganin Khaleesat ta sake ranta domin tayi karatun jarabawanta da kyau kar ta samu matsala, ga kuma Safiyyah dake encouraging dinta a gefe ita ma, kuma hakan yayi tasiri sosai don ta ɗan sake ranta tana karatun, AJ dai tun ranan da ya shigo ya ganta zaune a daki har bayan da suka yi Exams uku bata sake saka shi a ido ba, bata san ko yana gidan ba ma ko baya gidan, ita dai 24/7 tana daki, hatta abinci cook din gidan ne ke kai mata sama yayi knocking ta fito ta amsa, in ta gama still shi yake zuwa ya amshi tray din, bayan sati biyu da fara exam dinsu ranan suna da interval Safiyyah ta zo gidan da yamma, abinci ta kawo ma Khaleesat, Khaleesat taji dadi sosai ganin tuwo ne don dama tun jiya take sha'awan tuwon, Safiyyah tace "Kinga ba dadewa zan yi ba yanzu zan tafi kafin mutumin can ya fara kirana kamar Surayya ce ta bar gida" A hankali Khaleesat tace "Baza ki bari anjima kadan ba pls" Safiyyah tace "Wallahi yanzu Ya Mustapha zai fara kirana, bai ma san na fito ba, kuma nayi order din Lyft ma da zai maidani gashi nan ya kusa karasowa nan, tashi ki rakani kofar gida" Khaleesat ta girgiza kai tace "Kawai ki tafi za mu hadu schl tomorrow in sha Allah" Safiyyah tace "Wai ke baki gajiya da zama ke kadai a daki, don Allah ni dai tashi ki rakani kema ki ɗan yi strolling kafafuwanki" a hankali Khaleesat tace "Baza ki gane ba Sophie, wallahi i am not comfortable staying in this house, na kagu mu gama jarabawan nan in koma Nigeria" Safiyyah tace "Ae ranan Housemate dinki ya gaya min wai kince masa zaki koma apartment dinki nace lallai baki da hankali, Allah ma yasa Abdul bai sake gidan ba" Tana dariya ta kare maganar, sai kuma ta kwantar da murya tace "Kiyi hakuri kawata, nan da sati kadan zaki ga mun gama exams din in sha Allah, ki kwantar da hankalinki pls, yanzu dai tashi ki rakani" a hankali Khaleesat ta sauko daga kan gadon ta dau gyalenta suka fita dakin tare da Safiyyah, suna saukowa downstairs suka tarar da AJ a parlor da Jay, Khaleesat dai ta sunkuyar da kanta don sai yau taga AJ for almost 2 weeks, ita ta zata ma baya gidan ne, Jay na kallon Safiyyah yace "Are you going soon Safiyyah?" Safiyyah tace "Eh wallahi Yaya Jawwad Lyft dina yana hanya ya kusa" Yace "Alright, ki gaida mutanen gidan" Tace "In sha Allah za su ji" Sallama tayi ma AJ ya amsa mata, sannan ta kama hannun Khaleesat suka fita daga parlon, suna tsaye waje suna jiran karasowar Lyft wata mota ta shiga gidan bayan matukin motar ya fito daga cikin motar ya bude gate, Safiyyah tayi kasa da murya bayan sun shiga ciki tace "Ke kinga wani Ride me suna ride Khaleesat? Su dai da masu kudi kawai suke harkar su a kasar nan, in kin bibiya abokansu ne 'ya yan masu kudi irinsu" Khaleesat dai bata ce komai ba, bayan kusan minti uku sai ga Lyft din Safiyyah ya iso, Safiyyah ta bude bayan motar ta shiga, Khaleesat ta daga mata hannu, Safiyyah na mata murmushi tace "Sai mun hadu a schl kawata, kiyi karatu da kyau fa" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata sannan ta koma cikin gidan, duk a dar dar take tafiya a babban compound din gidan, har yau ita dai ta kasa sakin jiki a gidan nan gani take kamar a kaya ma take she is so very uncomfortable, a haka ta isa parlon gidan ganin baki biyu dake parlon tare da su Jay wanda da alama abokansu ne Khaleesat ta sauke kai ta gaishesu, suka amsa da fara'a, ita dai ta nufi stairs, daya daga frnds din nasu taji yace "Bakuwa ku ka yi a gidan" AJ dake shan fruit salad yace "Eh, yarinyar wani abokinmu ne a Nigeria ta zo jarabawa" Jay ya saki baki yana kallon AJ da ke ta shan fruit salad dinsa ko ajikinsa, Ita kanta Khaleesat sai da ta ɗan juya ta kallesa sannan ta wuce sama, abokin na gyara zama yace "Waow, amma da gani da wuri abokin nan naku yayi aure, ya huta abunsa gashi mu duk mun kasa har yanzu" AJ dai ya ci gaba da shan fruit salad dinsa yace "Ai kam ya huta, mu ma da munyi auren da wuri duk da mun haifi kamarta ai" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 24 Parlon dake sama Jay ya ja AJ zuwa can yace "Ohk now, let me explain Bruh" AJ na girgiza kai yace "I am not interested pls Jay, ni fa bana son ma kana min magana a gidan nan kar ayi zaton tare mu ka kawota" Jay yace "Naji.... bayan yanzu bazan sake maka magana ba, kawai dai na duba naga duk gidan nan dakin ka ne kadai yake da wahalan shiga..." Nan da nan AJ ya hade girar sama da ta kasa yana kallonsa yace "I don't understand, me yasa kake using dakina kake misali? What are you insinuating? What is ur point??" Jay ya shafa sumar kansa a hankali yace "My point is, na kai Housemate dita dakin ka for the meantime before i find a way out, nasan can ne kadai su Aunty baza su ganta ba, tunda dakin ka out of bound ne" Haka AJ yayi dropping jaw yana kallon Jay baya ko kiftawa with shock written all over his face, Jay ya sosa kansa zai yi magana suka ji muryar Hajiya Rukayya warce suke kira da Aunty, ta karaso parlon tace "Jay ka je Abbanku na magana a parlor" Jay yace "To gani nan zuwa Aunty" Ta ɗan kalli AJ sannan ta juya ta bar parlon, Jay ya sauke ajiyar zuciya yana kallon AJ that was still looking at him ko kwakkwaran motsi baya yi, da alama ya ma kasa cewa komai, Jay yayi patting ɗin shoulder dinsa yace "I know u gat my back Bruh, you won't love seeing Abba Mad at me" Yana fadin haka ya juya ya bi bayan Aunty yana sauke wani ajiyar zuciya, after almost 15 mins Jay ya dawo sama, zaune ya tarda AJ a parlon dake sama ya tallabi chin dinsa da duk hannunsa biyu yana girgiza kafa, he looks restless, Jay dai ya danne dariyar da ya taho masa da kamar zai juya ya koma downstairs, AJ na ganinsa ya mike ya nufesa a fusace ya fixgosa yace "What offense have i done to you Jawwad? Why my room? Why will u take her to my privacy, my own comfort zone, what sort of nonsense is this plss? Dakina fa? Meye hadina da ita zaka kai ta har Bedroom dina?" AJ was so mad at him, nan da nan idonsa suka sauya launi, Jay yace "To Abba dai na kiran ka, je ka dawo sai ka ci gaba" AJ dai sai kallonsa yake yana huci, can ya turasa ya bar parlon kamar zai tashi sama, Jay ya wara ido yana shafa kansa yana ɗan murmushi, karkari dai iya abinda zai yi kenan bazai wuce haka ba, kuma ba wani kiransa da Abba yake yi kawai wahala ne bai so yasa yace masa ana kiransa downstairs, dakin Khaleesat ya koma ya dauko mata box dinta da abubuwan da yasan zata yi needing ya kai dakin AJ, Khaleesat ta mike da sauri ganinsa, a hankali tace "But Housemate i am not comfortable in this room" ya ɗan bude ido yace "Why? Meye da dakin Halysaah?" Tayi shiru bata ce komai ba, Calmly yace "C'mon Halysaah wannan ma ai yafi wancan da kike ciki" Yana murmushi ya kare maganar, ita dai tayi shiru bata ce komai ba, ya ajiye mata kayanta da wayarsa yace "If you need anything just call my line" Ta gyada masa kai, ya nuna mata hanyar bandakin dake babban dakin yace "In zaki yi sallah ga bandaki can" Nan ma dai ta gyada masa kai kawai, ya juya ya fita daga dakin ta koma ta zauna, gajiya tayi da zama tana son kwanciya amma ta kasa kwantawa saman gadon, ita kanta ta rasa dalili, can dai ta zamo kasa a hankali ta kwanta saman lallausan carpet dake dakin ai ko nan da nan bacci ya dauketa, throughout ranan haka Khaleesat ta yini a dakin ita kadai, tun da Housemate dinta ya kawo mata lunch har lokacin magrib yayi bai dawo dakin ba, sai Cook din gidan ne ya kawo mata dinner, tana zaune saman darduma bayan ta idar da sallahn isha taji an bude kofar dakin ta daga kai, sosai gabanta ya fadi ganin AJ, ta sauke idonta daga kallonsa, shi kam ko kallon inda take bai yi ba fuskarsa a murtuke ya tafi ya dau second phone dinsa da laptop, ya bude press dinsa ya dau pajamas dinsa sannan ya fice daga dakin, sai a sannan ta daga kai ta bi sa da kallo tana mamakin abinda ya shigo yi, don bata san me ma ya dauka a dakin ba, har sannan bata kawo cewar dakinsa bane, har ta fara bacci Jay ya shigo dakin da sallama, ta mike zaune daga kwancen da take a kasa, da mamaki yake kallonta yace "Me yasa kika kwanta a kasa Halysaah?" Ta girgiza masa kai kawai, yace "C'mon don't do that pls, ga gado zaki wani kwanta a kasa" Ta kalli gadon tace "Zan kwanta" Yace "Good, hope u need nothing?" Tace "Bana bukatar komai" Yace "Alright then, good night" A hankali tace "Thank you" ya mata murmushi yace "In kashe maki wutan dakin ko a maida maki dim light?" Tace "Dim light" Ya mayar mata wutan mara haske sosai sannan ya juya ya fita daga dakin, bayan fitarsa ta koma tayi kwanciyarta a kasa, ita gani take kamar master bedroom din gidan ne, may be that's why she is not comfortable, wajen karfe dayan dare dakin yayi sanyi sosai amma taki daukan duvet din saman gadon ta rufa, kawai ta lullube da Hijab dinta, she was so cold gashi Safiyyah bata hado mata kayanta da Sweater ba, tana ta kwance ta kasa bacci saboda sanyin da ya dameta sai juye juye take taji an bude kofar dakin, a hankali ta sauke Hijab dinta kasa kadan tana son ganin wanda ya shigo don har kanta ta rufe, taga AJ ne ya shigo, kallo daya yayi mata ya tafi daukar abinda zai dauka, zaro ido tayi bayan ta zargi anya ba dakinsa bane nan kuwa, sai bayan da ya fita taji ya kullo kofar ta mike zaune tana sake bin dakin da kallo with shock, dumin da taji dakin ya fara dauka gradually ne yasa ta gane ya kunna mata heatern dakin, ta koma a hankali ta kwanta sai da dakin yayi dumi sannan bacci ya dauketa..... Washegari da safe Jay na zaune main parlor tare da Abba da Aunty, cikin nutsuwa Abba ke masa magana amma shi gaba daya hankalinsa na sama kan Halysaah don tun da gari ya waye bai je wajenta ba, kawai dai Cook din gidan ne ya kai mata breakfast, AJ ya shigo parlon daga reading nook da yake zaune ya nufi dinning area zai yi breakfast, Abba ya bi sa da kallo, after a while yace "Baka yi breakfast din bane" Jay ya ɗan kalli AJ, Aunty kanta kallonsa take ita ma, without turning back AJ yace "Ban yi ba" Aunty tace "To ai naga cook din gidan ya kai maka Breakfast din sama daxu" Ko tankata AJ bai yi ba ya tafi dinning ya zauna, Abba na kallon Jay calmly yace "Is he Okay?" Jay ya ɗan shafa kai yayi kasa da murya yace "I think supervisor dinsa ne bai yi approving Article din da yayi publishing ba tukunna" Aunty tace "To banda abun sa ai ba wani abu bane he should add in more effort to his work kawai" Shi dai Jay bai ce komai ba, haka shi kansa Abba, after a while Jay ya mike ya tafi sama, direct part din AJ ya nufa bayan yayi sallama ya tura kofar dakin ya shiga. Wajen la'asar AJ na zaune parlorn dake sama, gaba daya he look moody, dama jiya da daddare a nan parlorn ya kwana tsabar takaici, har zuwa yanzu yaki ce ma Jay komai a gidan, Jay kuwa ko a jikinsa don ko kallonsa ma baya yi, su biyu ne kadai a gidan don Abba ya fita tare da Aunty da autarta zuwa gidan wani prominent friend dinsa a garin, da yake gobe da safe za su bar kasar zuwa Nigeria, AJ ya gyara zama yana bin Jay da kallo trying to be sure of what he is holding in his hand, he was very shock ya dai bi sa da kallo har yaga ya nufi bangarensa, ya tallabi chin dinsa yana girgiza kafa, sai bayan da Jay ya fito for the first time since yesterday AJ yace "Wallahi i will never forgive you for these Jawwad, i promise you am not forgiving you" Jay dai ya dake bai yi dariyar da ya basa ba, kuma yaki tankasa yayi wucewarsa ya bar sa zaune a gun, da daddare Khaleesat na duba laptop dinta Jay ya shigo dakin da sallama ta daga kai tana kallonsa ya zauna kan kujeran dakin yace "Hope you are better now?" Ta gyada masa kai, yace "Toh Allah ya sauwake, amma ki tabbatar kin sha maganin so that u get enough night rest" Tace "Zan sha" Yace "Alright Good night Housemate, bacci nake ji" Ta ɗan yi murmushi tana kallon agogo dake nuna karfe goma tace "Ai baka ma yi da wuri ba" Yayi murmushi kawai yace "Saura kar ki kwanta saman gadon yau" A hankali tace "Zan kwanta" Yace "Good" Daga haka ya fita daga dakin, shi kansa yasan tunda ta dawo gidan yake tauye ma kansa bacci, kuma ba wai baccin baya damunsa bane kawai daurewa yake yi, har ciwon kai yake yawan yi yanzu saboda baya bacci sosai, Khaleesat ta kashe laptop dinta ta ajiye sannan ta mike a hankali ta dauko maganin da ya kawo mata daxu ta sha sannan ta kwanta saman gadon, amma fa a dar dar take saman gadon, Jay na isa parlorn dake sama ganin AJ kwance kan kujera yana danna wayarsa yace "Do you care sharing my room with me today?" AJ yaki tankasa yana danna wayarsa, Jay ya daga kafada yayi wucewarsa dakinsa, after like an hour AJ ya mike zaune jin muryar Abbansa, Abba dake kallonsa yace "Is everything Alright Ahmad? Why are you lying down on the Couch?" AJ ya fara sosa kai yace "Eh yanzu zan tafi daki Dad, ban san sanda bacci ya daukeni ba" Yana fadin haka ya mike tsaye ya dau wayarsa ya nufi dakinsa, Khaleesat ta juya jin an bude kofa don ba bacci take ba, yana shigowa dakin kuma ya kulle kofar ya tsaya nan bakin kofar, rufe har kanta tayi da duvet, ya tafi gaban madubi ya tsaya yana tunanin Jay bai taɓa cutarsa ba irin na wannan lokacin, sosai abun nan ya tsaya masa a rai, ita dai Khaleesat tana ta sauraren taji ya bude kofar ya fita daga dakin amma taji shiru, hakan yasa ta sauke duvet din kanta a hankali suna hada ido ya watsa mata kallo yace "Meye kike kallona?" Ta wani kallesa, sai kuma ta juya masa baya bata ce komai ba, after almost 5 minutes ya bude kofar dakin ya fice, tsabar yanda bai yarda da neatness din duk dakunan dake gidan ba ya sa ya gwammace ya kwanta a parlor instead of going into any of the room. Da Asuba Jay ya fito dakinsa kenan zai sauka downstairs su yi sallah da Abba, tunda Abba ya zo tare suke sallah amma banda AJ da baya saukowa ayi sallan da shi sai dai yayi shi kadai a sama, Jay ya hadu da Abba yana haurowa sama, Abba yace "This shows baku sallah tare a gidan nan Jawwad, ma'aikatan gidan nan guda biyu duk Musulmai ne, ga ka ga Junaid, amma ace baza ku hadu ku yi sallah ba?" Da sauri Jay yace "Muna yi Abba..." Abba bai ce masa komai ba ya nufi bangaren AJ, Jay ya buda ido sosai, sai kuma ya bi sa da sauri yace "Zan kira maka shi Abba..." Abba yace "Jiya da nace ka kirasa ya sauko?" Jay ya kasa cewa komai, duk tunanin Jay za su ga AJ a Parlor a kwance amma sai yaga baya parlon, nan hankalin Jay ya tashi ya tsaya a inda yake tsaye ya kasa ci gaba da bin bayan Abba, he wish Junaid bai cire code din nambobin kofar dakinsa ba, Abba na tura kofan sai ga AJ da ya shiga bandakin dake parlorn da suka baro yayi alwala ya taho zai dau pray mat, shi ma zaro ido yayi yana kallon Abba kamar yanda Jay ma ya tsaya kallonsa, AJ ya juya suka kalli juna da Jay, tunda Abba ya kunna wutan dakin ya tsaya for like a minute bakin kofar dakin yana kallon Khaleesat dake bacci, sai kuma ya juyo ya fito closing the door gently, Daga AJ har Jay suka sunkuyar da kai a tare kamar munafukai, Abba dai sai kallon AJ yake, after 30 seconds of silence, speaking Calmly Abba dake kallon Jay yace "Abinda ke faruwa gidan nan kenan Jawwad, and you told me nothing about it?" Jay ya kasa cewa komai kuma ya kasa barin su hada ido da Abba, cikin nutsuwa babu fada Abba yace "Magana nake maka Jawwad" Da kyar Jay ya girgiza kai yace "I know nothing about it Abba" AJ ya bude baki yana kallon Jay da yaki kallonsa, Abba ya gyada kai yace "Ohk then, ku mu je mu yi sallah lokaci na wucewa" Daga haka ya juya ya bar su tsaye a wajen, Jay ya bi bayan Abba da sauri, AJ ya bi sa da kallo baya ko kiftawa, tuni har Abba ya sauka downstairs hakan yasa Jay ya tsaya Parlor sai ya tuna tuggun da AJ ya hada masa gun Hadeeyah just 3 days back, bai san sanda dariya ya taho masa ba, sai ga AJ da jikinsa yayi sanyi ya shigo parlon yana kallonsa, hakan yasa Jay ya danne dariyarsa ya hade rai ya sauka downstairs da sauri, AJ ya bi sa da kallo, sai kuma a hankali ya zauna saman kujera ya kai hannunsa baki, ganin abinda Jay yayi masa yake kamar a mafarki, bai taɓa shiga shock irin na wannan lokacin ba. Da safe kamar babu abinda Abba ya gani a gidan don bai sake masu maganar baz kuma da alama ko Aunty bai gaya ma ba, Jay ma yasan bazai taɓa gaya mata ba, karfe sha daya jirginsu zai tashi zuwa Nigeria don haka har sun gama shirin tafiya Airport, Abba ya kalli Jay yace "Junaid bai sauko yayi Breakfast ba ko an kai masa sama ne?" Jay yace "I don't really know" Abba ya dau wayarsa ya kira AJ, ba a dau lkci ba sai ga AJ ya sauko parlor shi dai ya kasa hada ido da Abbansa, Abba na kallonsa yace "Kayi breakfast ne, naga baka sauko ba" Without looking at his Dad yace "Na yi" Abba yace "Ohk, za mu tafi airport ne yanzu, get ready" a hankali AJ yace "Ohk" Daga haka ya juya ya koma sama, sai da AJ ya fara zaunawa a parlon sama for almost 5 mins, gaba daya jikinsa a sanyaye yake, gashi ya tsani shirun Abbansa don ba alkhairi bane shirun, gwara ace ma fada yayi ta masa ba kakkautawa da wannan basarwan da yayi kamar bai ga komai ba, his next move might not be funny, Jay ya cucesa, bai taɓa zaton haka daga Jay ba, to ko yace ma Abba bai santa ba ta yaya zai yarda da shi tunda a dakinsa ya ganta ba dakin Jay ba, ganin bata lkci kawai yake ya mike yana tafiya a hankali ya tafi dakinsa don dauko kayan da zai sa, yana shiga dakin Khaleesat na fitowa daga bandaki da hijab dinta har kasa ta fito wanka, ya wani kalleta daga sama har kasa fuskarsa a daure, ita dai tunda suka hada ido ta dauke kanta bata sake yarda ta kallesa ba tana dai tsaye hanyar shiga bandakin, ya dau kayan da zai dauka ya karasa gaban madubi ya dau tsadadden turarensa ya fice daga dakin, ta wani kyabe baki ta karasa shigowa cikin dakin. Har Abba suka isa Airport bai ce ma AJ komai ba akan daxu da asuba, kuma da alamar babu abinda zai ce masa, he was just speaking about something different in the car, a haka suka rabu normal normal a airport kamar babu komai, AJ yaki jiran Jay ya ja mota ya bar airport din ya kama hanyar gida, dole sai Uber Jay ya samu da zai maida shi gida, ko da ya isa gida ya ga AJ zaune a compound da non alcoholic wine a gabansa trying to use it to calm himself down at the same time trying to figure out wani hukuncin Abbansa zai ce zai dauka a kansa..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 25... Khaleesat felt so much relieve after leaving AJ's room, tana biye da Jay ta koma dakin da take, ba tare da Jay ya kalleta ba bayan ya ajiye laptop dinta dake hannunsa yace "Kin ji sanda aka bude kofa da asuba ne?" Khaleesat na kallonsa ta girgiza kai tace "I am not sure, may be ina bacci sannan, banyi bacci da wuri ba" Yace "Ohk" Tace "Why are you asking?" Ya juyo yana kallonta, ya ɗan mata murmushi yace "Nothing" Tace "But ai frnd din ka yana shigowa ya dau stuffs dinsa wani lkcn" Jay yace "Ohk" Har ya juya sai kuma ya sake dawowa yace "Kince baki yi bacci da wuri, ciwon kan ke damunki har yanzu?" Ta girgiza kai tace "A'a, kawai baccin ne dai bai zo ba" Yace "Ohk" Khaleesat ta bi sa da ido har ya fita daga dakin sannan ta zauna gefen gado a hankali, har cikin ranta take jin kamar ta jawo ranan talata, she is so tired tana bukatar kawai ta ganta kusa da Ummanta, she need her Mom's hug, Jay na fita ya kira ma'aikatan gidan su gyara ma AJ dakinsa, Jay made sure the workers left nothing untouched a dakin duk da babu abinda dakin yayi, amma irin gyaran da aka ma dakin da bandakin ba na wasa bane, sai da ko ina ya dawo yana sparkling tsabar gyara sannan Jay ya koma downstairs, amma still a ranan ma AJ bai kwana dakin ba, yayi kwanciyarsa a parlor kan kujera. Washegari which was monday AJ na zaune usual spot dinsa a compound da Coke din gwangwani a gabansa, har a sannan yaki ce ma Jay komai a gidan, not even Jay hatta ma'aikatan gidan duk ba wanda yake yi ma magana he is just keeping straight face, Jay ya fito daga cikin gida ya karasa har inda yake zaune, ko kallon direction dinsa AJ bai yi ba yana juya counter din hannunsa, Jay na kallonsa yace "Abba wants to speak to you" Yana fadin haka yace "Abba gashi nan" Ya ajiye wayar gaban AJ, Calmly Abba yace "How are you doing Junaid" AJ ya sauke idonsa ya gaida Abba, Abba ya amsa yace "You didn't call to know if we arrived safely" AJ yace "Ayi hakuri" Abba yace "It's fine, yaushe za ku dawo hutu" AJ yace "Ran Thursday zan dawo in sha Allah" Abba yace "What about Jawwad" A takaice AJ yace "I don't know" Abba yace "Hand the phone over to him" Jay ya dau wayarsa sitting in one of the chairs beside AJ yace "Na'am ina ji Abba" Abba yace "Kai yaushe zaka dawo" Jay ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Probably next week in sha Allah" Abba yace "Ohk Allah ya kai mu, earlier today you said you have something to tell me unfortunately ina tare da baƙi a lkcn, so what is it Jawwad" Jay ya ɗan shafa kansa thinking of where to start, can dai yace "Abba dama it's about the girl u saw yesterday" Abba yayi shiru at first, sai kuma "Ohk, what about her?" Jay yace "Abba ni ne na kawota gidan ba AJ ba, she is a student of John Hopkins also, she is having issue with House rent and she's writing exam, so shine kawai na kawota gidan nan zuwa sanda zata gama jarabawan...." Abba ya dakatar da shi yace "Did you and Junaid birth me or i birth you both?" Jay ya girgiza kai da sauri yace "Billah Abba i am not cooking up stories, believe me, all what i am saying is the truth ai kasan bana maka karya Abba, kawai dai ni na kai ta dakin AJ ne without even his knowledge cause Aunty will definitely see her in the house, part din AJ ne kawai nasan bazata shiga ba, kuma because of this... AJ parlor ya dawo yake kwana, wallahi babu komai tsakaninmu da ita kawai taimako ne, you can even speak to her to confirm ranka ya dade" Abba yace "If she is having rent issue don menene baza ku bata kudin hayan ta biya ba ko kuma ni ku min magana, na menene sai kun kawota nan gida cikin ku ta zauna? Is that ur home training? Dama addininku ya yarje maku da haka?" Jay ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace "Kayi hakuri ka gafarce mu Abba, she will be rounding up her exam on Tuesday, and she will leave in sha Allah" Abba yace "Kaga da ba don nasan baza ka min karya ba Ahmad i won't listen to you, da Junaid ne ya tsaya mun wannan bayani bazan yarda da shi ba, and my plan was to start making arrangement na samar masa mace da zan aura masa a kai masa ita can ƙasar, tunda ka min wannan bayanin naji na kuma yarda amma daga kai har shi sati biyar na baku kacal ku gabatar min da macen da za ku aura, ita kuma i will send you some money to sort out her House rent" AJ ya daga kai yana kallon Jay bayan yaji abinda Abbansa yace, sai kuma ya mike kamar zai tashi sama ya bar wajen, shi dai Jay was speechless this was the least thing he was expecting to hear from Abba, jin Abba ya katse wayar ya zuba ma screen din ido, ya basu 5 weeks?? jay ya fi minti goma zaune a wajen kafin daga karshe ya sauke ajiyar zuciya ya mike ya dau wayarsa ya shiga cikin gida. The next day Khaleesat suka gama jarabawansu na karshe and she was so happy amma kuma da ta tuna wasu abubuwa kawai sai mood dinta ya canza, suna zaune tare da Safiyyah a cikin makarantar ganin yanayinta da yanda ta sauya lokaci daya tayi shiru, Safiyyah ta kalleta tace "Why are you like this Khaleesat?" Khaleesat ta daga kai ta kalleta, a hankali tace "I don't have the means of going back to Nigeria Sophie, the burden i am placing on my Housemate is too much ba shi ya kawo ni kasar nan karatu ba, he knows nothing about me, don me zan yi ta dora masa nauyina har haka?" Safiyyah tace "To ya za kiyi Khaleesat, tunda ba ke kika rokesa ya maki ba ai kawai addu'a zaki masa Allah ya saka masa da alkhairi, he is ur God sent Angel, ba gashi with or without Abdul kin gama jarabawanki lafiya ba" Khaleesat ta sauke idonta jin hawaye ya ciko mata, Safiyyah ta hade rai tace "To meye na kuka kuma?" Muryarta na rawa tace "Ni dai bana son yace zai sake kashe min kudi masu yawa in koma Nigeria, i am feeling guilty" Safiyyah ta wani kalleta, can tace "Kya rube a kasar nan kuwa, ke kina da hanyar komawa ne? Ko kuma aikatau zaki nema a kasar ki tara kudin komawa Nigeria? In ba dai kudaden Abdul dake account dinki zaki yi using ki biya kudin jirgi ba" Safiyyah na kai wa nan ta kyalkyale da dariya tace "Ko ya kwashe en kudaden nasa ne?" Ita dai Khaleesat tayi shiru taki ce mata komai, Safiyyah tayi dariyarta me isarta sannan tace "Allah ba batun wasa ba, ya kwashe kudaden nasa ne?" Khaleesat ta girgiza kai a hankali tace "Suna nan" Safiyyah tace "Miliyan nawa ne ma?" Khaleesat ta sauke idonta tace "Almost 9.5 Million" Safiyyah tace "To kawai ki siya Ticket abunki tunda dai yasan ba uban wani gareki a kasar ba da zai baki kudin komawa Nigeria ba, bayan shi kawo ki, in nice ke ma har shopping sai nayi na komawa Nigeria a cikin kudin wallahi, ai bazai san kin taɓa ba tunda ba shi ke ganin alert ba" Safiyyah na dariya ta kare maganar, ita dai Khaleesat bata tanka ta ba, Safiyya tace "Naji kinyi shiru ko baza ki taɓa ba? Wallahi yanzun nan in raka ki shopping mu fatattake kudin" Khaleesat tace "Ai ba nawa bane da zan fatattake su" Safiyyah ta kwashe da dariya tace "To ai sai kiyi ta zama a kasar, dama gulma ce yasa kika kawo maganar ba wani abu ba don nasan Jay kike saka ran ya biya maki ticket" Khaleesat dai kallon Safiyyah kawai take ta kasa ce mata komai, amma ita kadai tasan abinda take ji a zuciyarta, Safiyyah tace "In kuma in ma Ya Musty magana to, don dai Economy class ticket da zai siya mana bazai ce ya gagaresa ba" Da sauri Khaleesat tace "A'a, zan yi amfani da kudin account dina" Safiyyah tace "Atoh dai" Khaleesat ta gaya mata haka ne kawai don bata son taje ta ma Ya Musty magana.... Jay ne ya zo daukansu a schl din as usual, sai da ya fara dropping din Safiyyah sannan ya kama hanyar gida da Khaleesat, daxun nan yaga Abba ya sako masa dala dubu goma wai na House rent dinta, da ya gaya ma AJ sai cewa yayi ya masa transfer din Dala dubu biyar shi ma ya rike dubu biyar din tunda ba su suka kawota kasar ba, shi da Jay bai tankasa ba, Jay dake driving ya ɗan kalli Khaleesat jin shirun yayi yawa, yaga alamar tayi nisa tunanin da take, sai a sannan ya kula da idonta da yayi ja, a hankali yace "Halysaah" Juyawa tayi ta kallesa trying to look alright ta ɗan yi murmushi tace "Na'am" Yace "Are you okay?" Tayi yake tace "Na gaji ne kawai" Jay yayi shiru, bai sake ce mata komai ba amma yasan ba gaskiya ta fada masa ba, a ɗan few months din da yayi da ita har ya gama studying dinta gaba daya, he knows when she is happy, sad, bored, disturbed, and even tired, wannan karan yaga damuwa ne karara a fuskarta, ya dai ci gaba da driving dinsa har suka isa gida, bayan yayi parking ya juya yana kallonta, a hankali yace "Me ke damunki Halysaah?" Duk kokarinta na ganin ta nuna masa ba komai hakan yaci tura, don kawai ita ma gani tayi kuka ya taho mata, Jay ya jinginar da kansa da kujeran motar bai ce mata komai ba, kwana biyu ya huta da kukanta don a sanda ya dawo da ita gidan rana daddaya ne bata kuka don ma Safiyyah na taka mata burki kuma ya ga tana ɗan jin maganar Safiyyar wani lokaci, sai da tayi kukanta me isanta sannan yace "Sauka mu shiga ciki to" Ba musu ta bude motar ta sauka tana goge idonta, shi ma ya sauka, yana gaba tana biye da shi suka shiga cikin gidan. Khaleesat na kwance da yamma ta shiga Hisnul Muslim dake wayar Jay sai ga kira ya shigo wayar, a hankali ta mike zaune tayi picking call din ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren taji yace "Kin tashi?" Tace "Uhm" Yace "Kin yi sallah?" Tace "Nayi" yace "Ohk will you mind going out to the park with me?" Khaleesat tayi shiru, sai kuma a hankali tace "Ohk, thank you" Yace "You are welcome, i will be waiting for you at the parlor downstairs" Tace "Ohk" After almost 15 mins Khaleesat ta sauko downstairs cikin shiri, sosai kayan jikinta yayi mata kyau sai dai ta rame sosai, shi kadai ne zaune parlon yana jiranta, tun da suka hada ido ta sunkuyar da kanta, ya mike ya jira har ta iso parlon yana kallonta, a tare suka fita zuwa parking space din gidan ya bude mata motar, ta ɗan kallesa tayi murmushi tace "Thank you" Ya bude ido yace "No thanks" bayan ta shiga ya kulle motar sannan ya zaga ya shiga driver seat, one of the best park na state din ya kai ta and she love everything about the park, the view was so fascinating and breathe taking, she felt so refresh and relieve taji kamar bata da wani damuwa a lkcn, Jay ya siya masu Wraps da fresh lemonade, wannan karan bata ji kunyar cin abinci gabansa ba, lkci lkci yake daga kai ya kalleta, ita dai ta dinga kallon feral horses dake park din from a far distance, can ta kallesa tace "Su ba a hawansu ne?" Yayi murmushi ya girgiza mata kai yace "Ba a hawa" Tace "And nobody is controlling them?" Yace "Sort of, they are just on their own with no supervision, ko kina son in kai ki inda zaki hau doki ne?" Er dariya tayi ta girgiza masa kai kawai, ya ɗan kalleta, kana ganinta kasan tana cikin farin ciki a lokacin, ta kalli wraps dinsa da bai karasa ci ba tace "You are not eating?" Yace "Za ki ci ne?" Tayi murmushi tace "A'a, na koshi, kawai naga baka ci da yawa bane" Yace "Na ci abinci daxu ne, i am full" Ta kalli lemonade din gabansa tace "To in dauka?" Yace "A karo maki wani kenan?" Ta girgiza kai da sauri tace "Aa fa, i just don't want it to waste ne" Ya dauki sauran lemonade din nasa ya ajiye mata a gabanta yana kallonta, ta dau straw din ta fara shan lemonade din a hankali, dauke ido yayi daga kallonta, wayarsa ya fara ring yana dubawa yaga AJ ne ke kiransa, yayi picking ya kai kunne, ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, after few seconds Jay yace "Ni sai next week probably, ban gama abinda nake ba, do not book with me" Ajiye wayar yayi bayan AJ ya katse, ya kalli Khaleesat yace "Zaki jira har next week mu tafi Nigeria, or you will leave before then?" Khaleesat tayi shiru at first, a hankali ta sauke idonta tace "Yanda kace" Yana murmushi yace "Ko zaki bi AJ, he is leaving soon, yanzu ma ticket zai yi booking" Ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, sai kuma tace "He that dislikes me shi ne zan bi sa?" Jay yayi dariya yace "How will you say he dislikes you Halysaah? He dislikes you shi ne yaje har apartment dinki yayi rescuing dinki? Ke ce dai baki ganesa ba har yanzu, AJ is nice just that yana da son girma ne kuma baya son raini, which i understand him because that's our heritage, kinga ke ko gaishesa baki yi" Tana wasa da straw din lemonade din gabanta tace "To ai nasan ko na gaishesa bazai amsa ba, saboda na taɓa gaishesa bai amsa min ba" Jay dai yayi murmushi yace "In kin ci gaba da gaishesa ae zae amsa" Tace "Ur frnd doesn't like me at all, he prefer my frnd" Jay yace "Who told you he is my frnd? AJ is my cousin bro Halysaah" Khaleesat ta daga kai ta kallesa tace "Da gaske?" Yayi murmushi yace "Ba ma kama ne?" Khaleesat ta buda hannu tace "Ni ban wani san yanda fuskarsa yake ba ai, ban taɓa kallonsa sosai ba" Jay yayi dariya, a hankali yace "To cousin brother dina ne, His dad is my father's junior bro" Khaleesat tace "To amma dai ka girmesa ko?" Jay na murmushi yace "Not at all, just 3 months ne tsakaninmu, we will clock 34 next year" Khaleesat tace "Shi ne yace ya haifeni?" Jay bai san sanda yayi dariya ba sosai, sai kuma yace "Zolayarki fa yake, but how old are you?" Ta sauke idonta kasa kamar bazata ce komai ba, sai kuma a hankali tace "I am 20" Jay ya wara ido yace "Waw, you are still a Baby Halysaah" ta wani kallesa, yana murmushi yace "To ai in AJ mace ne kuma an masa auren wuri ya isa ya haifeki" Yana dariya ya kare maganar, Khaleesat dai taki cewa komai still playing with the straw in front of her, a hankali Jay yace "Are you angry?" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma tayi murmushi ta girgiza masa kai still looking at him, Jay ya kwantar da murya yace "U misunderstood AJ, yana da kirki sosai, kuma yana da tausayi, just that he is a no nonsense kuma baya son raini, sannan truly yana da girman kai na sani, but that doesn't make him bad, kuma da kinsan wanene shi zaki san yana ma da saukin kai" Khaleesat ta karasa shan lemonade din gabanta taki ce ma Jay komai, Jay ya kalli agogon wrist dinsa yace "Let go for horseback riding before it gets late" Khaleesat ta zaro ido tace "A'a ni dai bazan hau doki ba" Yana murmushi yace "To mu je dai" Shi ya fara tashi sannan ita ma ta mike suna tafiya a tare, satan kallonsa tayi suka hada ido ya ciro wayarsa yace "Let's take some pictures with this beautiful view" A hankali tace "Ok" Tana tsaye kusa da shi yayi masu hoton da wayarsa, yana kallon hoton da yayi masu ya taɓa hancinsa yace "Ya naga hancinki yafi nawa tsayi, ya naga kamar kin fi ni kyau" duk lokaci daya ya jero tambayar yana sake kallon hoton da kyau, ita dai Khaleesat tayi murmushi tace "Uhm is that an irony?" Jay yayi dariya yace "I am serious Halysaah" Wata er Africa ce ta zo wucewa ya mika mata wayarsa politely yace ta masu hoto pls, yarinyar ta amshi wayar zata masu hoton, yanda Khaleesat taji ta uncomfortable kusa da shi, shi ma dai kamar hakan ne cause he left a little gap between them, yarinyar ta masu hotuna masu kyau kuwa, ita kanta yarinyar sai kallon hoton take kafin ta mika ma jay wayarsa tana kallon Khaleesat admiringly tana murmushi tace "You are so Beautiful" Khaleesat ta sauke idonta tace "Thank you" Yarinyar ta daga masu hannu ta bar wajen, bayan Jay yayi mata godiya, kallo daya yayi ma hotunan ya mayar da wayar cikin aljihunsa yace "Let go for horseback riding Housemate" Wani park din ya kai su daban da ake hawa doki, duk yanda yayi da Khaleesat ta hau doki bayan ya biya masu kudi taki wai ita bata iya ba tsoro take ji, daga karshe ta marairaice tace "Ni dai kawai ka bani wayarka in dinga maka video sai kai ka je ka hau" Yayi murmushi kawai ya mika mata wayarsa yace "To ai shikenan" Khaleesat was so impressed with his horse riding skills kamar irin dama ya saba din nan, sai murmushi take masa, mutanen wajen ma suna ta kallonsa, Khaleesat's eyes were glued to him all through, tana yi tana masa video, sai after 7 suka bar wajen, tana kallonsa kafin su shiga mota tace "Where did you learn to ride horse confidently?" Yayi dariya yace "Back home" Tana murmushi tace "To ka taɓa zuwa nan ne?" Jay yace "Tab ai nan wajen zuwan AJ ne, kawai dai of recent ne muka dena zuwa" Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, sai da ya fara biyawa African Restaurant ya siya mata abinci, ganin leda daya ya mika mata yace "This is for you" Tace "Kai fa?" Yace "No, i am taking tea and bread this night" A hankali tace "Ohk, thank you" Bayan sun isa gida yayi parking, ta juya tana kallonsa a hankali tace "Thank you so much, Allah ya saka maka da alkhairi, i appreciate you" Without looking at her yace "Amma nace ki dena min godiya ko Housemate?" Tayi shiru, ya bude motar ya sauka sannan ita ma ta sauka, yana gaba tana biye da shi har suka shiga gidan, AJay na zaune parlor yana shan fruit salad yana kallon kwallo, ya juya ya kalleta don shi bai ma san bata gidan ba, suna hada ido abinda Jay yace mata daxu ya fado mata, ta sunkuyar da kai, kamar munafuka tace masa "Good evening" AJ ya gyara zama yana kallonta yace "Kin saba gaisheni ne zaki ce min Good evening??" Khaleesat ta ɗan kalli Jay da ya karasa cikin parlon, Jay yace "Good night Halysaah, if you need anything you call my line" A hankali tace "Thank you" Daga haka ta wuce sama, Jay na kallon AJ yace "Ba don na mata magana ba kana tunanin zata gaisheka ne dama? Ni ne nan na saka ta, sai me kuma in baka amsa ba?" AJ yace "Zamana take a gidan da zata gaisheni" Jay dai yaki tanka masa. HALYSAAH 26 Khaleesat na zaune gefen gado tana kallon Jay dake kulle mata akwatunan ta, yana dagowa ta juya a hankali tana kallon window dake dakin, ya dau boxes din biyu yace "Let me get them in the car" Daga haka ya fita daga dakin, ta jinginar da kanta jikin gadon dakin har ya dawo, yana kallonta yace "Hope you didn't forget anything Halysaah" Ta gyada masa kai, yace "Ok, you know what? in dai muka fita kika hadu da AJ thank him and tell him you are leaving" With a smile on his face ya kare maganar yana kallonta, ta sauke idonta tana wasa da fingers dinta a hankali tace "Ohk" Yace "Good gal, mu tafi" Mikewa tayi ta bi bayansa tana rike da karamin handbag dinta walking slowly, suna fitowa walk way din babban corridor din sama sai ga AJ ya taho daga parlorn dake nan sama, Jay ya kalli kayan jikinsa ganin iri daya suka sa kuma tun safe ba wai sun hadu bane kawai coincidence, tunda AJ ya kallesu sau daya ya ci gaba da tafiyarsa, Khaleesat ta ɗan kalli Jay, ya gyada mata kai sannan ya nufi stairs, ita dai tana tsaye ta jira har AJ ya iso kusa da inda take sannan ta sauke idonta a hankali tace "Good morning, i want to thank and appreciate you for everything, i will be leaving today in sha Allah" Without looking at her yace "Jay dai zaki ma godiya ni me na maki" Ta bi sa da kallo har ya fara sauka downstairs, sai bayan da ya sauka sannan ta tabe baki ta bi bayansa tana tafiya a hankali, parlor ta tarar da Jay zaune yana jiranta, Jay ya bi AJ da kallo yace "Flight din naka na gobe ne amma?" AJ yace "I am leaving for the airport now" Jay yace "Ohk, zaka jira inyi dropping Housemate dina sai in dawo in kai ka airport din?" AJ yace "No, don't bother" Daga haka ya fita daga parlon tare da daya daga workers din gidan wanda da alama shi zai yi dropping dinsa airport din, Jay ya daga kai ya kalli Khaleesat, ya lura tunda gari ya waye jikinta yake a sanyaye, yana kallonta yace "Are you Okay Halysaah?" Ɗan murmushi tayi tace "Sure" yace "Kin gaya ma kawarki yau zaki tafi?" Khaleesat ta gyada masa kai tace "Na gaya mata" Yace "Ok, ita yaushe zata tafi?" Khaleesat tace "Yayanta yace ta bari ranan lahadi" Jay yace "Kin tabbatar baki mance komai ba kuwa a sama?" Ta gyada masa kai, yace "Je dai ki sake dubawa Housemate" Bata masa musu ba ta juya zata koma sama yace "Toh ki ajiye jakar taki mana" Ta dawo ta ajiye jakarta a kan kujera sannan ta wuce sama, Mikewa Jay yayi ya tafi gun jakar ya dauka ya bude sannan ya ciro Dala dubu daya a aljihunsa ya sa mata a jakar ya kulle ya mayar ya ajiye mata ya koma ya zauna, ba a dau lokaci ba Khaleesat ta dawo downstairs tace "Ban manta komai ba" Yace "Good" Mikewa yayi bayan yaji fitar motar AJ don dama jira yake yaji sun fita daga gidan, yana kallonta yace "Mu je, ur Flight is in an hour time in sha Allah" Khaleesat ta gyada masa kai ta dau handbag dinta, tana biye da shi suka fita daga parlon gidan, har gari ya fara duhu, suna shiga motarsa ta mika masa wayarsa dake hannunta kar ta manta, a hankali tace "Thank you so much" Ya amshi wayar sannan ya dauko pin a motar ya cire sim card din cikin wayar snn ya mayar mata yace "Your ticket is on the phone, in kin koma Nigeria sai kiyi SIM card replacement, in kuma baki son wayar sai in sa a kai maki sabo a Nigeria" Tayi murmushin karfin hali tace "Saboda me zance bana so, nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Yace "To ai nasan ku mata da son sabon abu" Ta girgiza masa kai kawai tana murmushi bata ce komai ba, a haka suka bar gidan suka dau hanyar airport da tunani iri iri a ran Khaleesat, ko baccin kirki bata yi ba daren jiya ga wani daren, ko me zata je ta tarar a Nigeria sai Allah, it's now that reality is dawning on her, bayan sun isa airport Jay ya juya ya kalleta yace "You can sort ur self out ba sai na shiga ciki ba ai ko?" Ta gyada masa kai, da kyar tayi karfin halin cewa "Thank you so much Housemate, Allah ya saka da alkhairi da abubuwan da ka min" Kasa ci gaba tayi saboda hawayen da ya fara sauka a idonta she just can't thank him enough, gani take words aren't enough to thank him, shi dai Jay kallonta kawai yake with surprise, can yace "C'mon Halysaah, to menene abun kuka?" Ta kasa basa amsa ta rufe fuskarta da gyalenta tana kuka a hankali, Jay ya kwantar da murya yace "Pls ki dena wannan kukan, in nasan abinda zaki yi kenan i will have just order either Lfyt or an Uber that will be taking you to the airport" Dena kukan tayi tana goge hawayen da yaki tsaya mata tana kallonsa, ya bude motar ya sauka ta bi sa da ido taga Luggages dinta dake booth zai dauko, a hankali ta bude side dinta ta sauka daga motar tana bin sa da kallo, daya daga porters dake wajen ya ba luggages din nata ya shigar mata da shi ciki ya hada masa da tip dinsa, ita dai Khaleesat kallonsa take, ya juya ya dawo kusa da ita yace "Alright safe trip Halysaah, idan kinyi replacing Sim card dinki sai ki min magana ta WhatsApp, my regards to everyone back home" Ta sauke idonta a hankali tace "I will miss you" sai bayan da ta fada haka ita kanta tayi realizing abinda ta fada, sai kuma ta kasa dago kanta, ya ɗan yi murmushi yace "I will miss you too Housemate, in sha Allah next week i will be in Nigeria too" Bata iya ta kallesa ba ta gyada masa kai kawai ta juya a hankali ta bi bayan porter din da ya shigar mata da luggages dinta zuwa check in counter for her Boarding pass, kasancewar Business class ticket gareta all the processes were smooth and straight for her, daga karshe ta nufi waiting lounge don in 15 mins time za su fara boarding jirgi, tunda ta shiga lounge din take kallon wanda ta gani zaune da mamaki, ta kalli boarding pass dinta sannan ta kalli na hannunsa taga iri daya, wayarsa kawai yake dannawa, ganin bai ganta ba ta juya a hankali ta koma wani wajen daban ta zauna ta inda ma bazai ganta ba, bata sake waigen inda yake ba, iya drink kawai ta amsa a lounge din unlike wasu da ke ta cin abinci duk a cikin kudinsu, gaba daya ta nemi appetite dinta ta rasa saboda damuwa, da ta tuna inda zata sae taji har wani juya mata kanta yake kamar bata da lafiya, ta saƙa wancen a ranta ta kwance har daga karshe aka fara boarding din jirgi, sai da Khaleesat ta jira AJ ya fara tafiya sannan ta mike ta bi bayansa walking slowly, Har seat dinta wata Flight Attendance da ke welcoming dinta da fara'a ta kai ta, hada ido Khaleesat tayi da AJ that was sitting few seats away from hers, ta sunkuyar da kanta ta zauna Seat dinta tana mayar da Amenity kit din da aka ajiye mata a gefe, AJ ya kasa daina kallonta fuskarsa babu yabo babu fallasa, he can't even explain what he is feeling at that moment don bai taɓa ganin wanda ya gama rena masa wayo a duniyar nan kamar Jay ba, jiya wajen karfe sha biyun dare ya farka ya gansa yana duba masa waya ashe ticket din da ya siya yake dubawa, he felt like just leaving the plane at that moment, after a while kawai ya dauke kai yana kara gyara barrier din da zai sa ko hangota bazai dinga yi ba, Ita ma Khaleesat ko by mistake bata sake kallon direction din sa ba, a haka jirgin ya tashi, Khaleesat bata taɓa jin motion sickness ba tun da ta fara tafiya a jirgi amma yau ko don saboda pressure din da ta saka ma ranta ne kawai sai ji tayi as if she wants to throw up tun da jirgin ya daga, ta cire seat belt dinta da sauri ta mike ta nufi Lavatory din jirgin almost running, shi dai ya bi ta da kallo, Flight Attendance din da ta kawo mata Hot towel kafin tashin jirgin ne ta bi bayanta tana tambayar if she's okay, Khaleesat ta gyada mata kai kawai bayan ta fito daga Lavatory din, AJ ya bi ta da kallo har ta koma seat dinta ta zauna sannan ya tabe baki, Flight Attendance din ta duka kusa da ita tana tambayarta ko tana bukatar wani abu ne, Khaleesat ta girgiza kai tana murmushin karfin hali tace "Thank you, i am okay" Matar ta sake tafiya sai ga ta ta dawo da ruwa da orange drink, sai kuma wani drink daban duk a glass daban daban akan tray daya, ta duka tana mika ma Khaleesat ta dauki wanda take so, glass din ruwa kawai Khaleesat ta dauka ta mata godiya sannan ta sanar mata bazata ci abinci ba all throughout the flight don ma kar matar ta sake dawo mata, gani take tana cin abu zata yi aman da bata yi ba daxu, gyara kujeranta tayi ta kwanta ta lulluba da blanket din da jirgin yayi providing for business class passengers, nan da nan bacci ya dauketa, da za su sauka Turkey wajen karfe hudun asuba sai da wata Flight Attendance daban ta zo ta tasheta ta sanar mata jirgi zai sauka, Khaleesat ta mike zaune da kyar don ciwo kanta ke mata, tayi fastening seat belt dinta, bayan sun sauka Istanbul ta bi AJ da kallo har sai da ta daina hangosa sannan ta mike ta dau handbag dinta da waya ta bi bayansa tana tafiya da kyar leaving her Amenity kit behind, jiran awa biyu za su yi a Business Class waiting lounge na airport din kafin a canza masu jirgin da zai kai su Nigeria, ta riga AJ shigowa lounge din kilan masallaci ya tafi, ita ma tana ganin lokacin sallahn asuba yayi ta tafi tayi sannan ta dawo ta zauna a business lounge din, after like 15 mins sai gashi ya shigo, not far away from her ya zauna da ruwan gora a hannunsa, Ita dai ta jinginar da kanta jikin kujeran da take zaune ta daura handbag dinta a kafarta, she is having a terrible headache a lokacin, after almost 30 mins of sitting wani ɗan Nigeria ya dawo kusa da ita ya zauna, wanda shi ma daga nan Turkey zai je Nigeria a Business class, kuma jirginsu daya kamar yanda ta ga ticket irin wanda ta amsa bayan sun sauka Istanbul din a hannunsa shima, yana kallonta yayi mata sallama cikin nutsuwa, ta ɗan kallesa sannan ta amsa, yace "Guess you are coming from America right?" Tace "Uhm" Yana kallon Flight ticket dinta yace "Oops you are having the same name as my Mum, can i call you Jiddah instead of the real name?" Khaleesat dake sauraronsa without looking at him tace "Ohk" Yana murmushi yace "Alright, are you traveling alone Jiddah?" Ta girgiza kai tace "No" Ya buda ido yace "Ohk with who?" Ta kalli direction din AJ, shi ma mutumin ya kallesa suka hada ido don kallonsu kawai Ajayn yake yana jin conversation dinsu, mutumin na murmushi ya tashi yaje ya gaisa da AJ sannan ya koma ya zauna, shikenan Khaleesat ta samu lafiya, don bai sake ce mata komai ba kawai danna wayarsa yake tayi tunda shi dai bai san ko waye Ajayn a gunta ba, daga karshe ma ya tashi ya bar wajen, at last aka fara boarding din jirgin da zai kai su Lagos Nigeria daga Istanbul, Usman ya juya ya kalli Khaleesat da ta mike tana rike da handbag dinta, har AJ ya wucesu sai kuma ya tsaya amma bai juyo ba, ita dai tana tafiya a hankali har ta isa inda yake tsaye sannan ya ci gaba da tafiya tana biye da shi, har jirgi ya tashi Usman dake zaune not far from Khaleesat but close to AJ bai ce mata komai ba, this time around ma dai bacci kawai tayi har zuwa Nigeria. Karfe hudu saura suka sauka Nigeria washegari Friday, ita dai Khaleesat tun da ta ganta Lagos bayan ta gama da Custom da Immigration ta fara tunanin kuma yanda zata yi, to ko dai kawai ta tafi gidan Aunty Farida tunda a nan Lagos take, to ko tace zata je bata da sim din da zata kirata don ba gane anguwan zata yi ba kuma bata da lambarta a kai balle ko waya ne ta ara ta kirata a airport din, sai kuma tayi tunanin kiran Ummanta tunda tana da numberta a kai sai tace ta turo mata number Aunty Farida, gun wata mata warce taga kamar Bahaushiya ce ta nufa, ta gaisheta sannan tace "Don Allah Aunty wayarki zaki ara min in ɗan yi kira nawa ba caji" Matar ta fara kallonta daga sama har kasa, sai kuma ta bude handbag dinta ta ciro wayarta ta mika mata, Khaleesat ta amsa tace "Nagode" Dialing number Umma tayi ta kira taji a kashe, sosai jikinta yayi sanyi, ta kira har sau uku duk ana ce mata a kashe, a hankali ta zame wayar a kunnenta ta mika ma matar tace "Nagode, wayar ma a kashe yake" sai da matar tayi dialing wayar ta tabbatar eh a kashe din yake, kana ganin matar kasan she is not comfortable giving off her phone, Khaleesat na jan trolley dinta a hankali ta fito daga cikin airport din tana tunanin yanda zata yi, ko dai kawai ta tafi tashan da zata samu mota zuwa kano, since she have some money in her bank account, wani mutumi ne taga ya nufota, ya gaisheta da ladabi yana mata barka da zuwa, sannan ya nuna mata mota yace "Ke mu ke jira ki fito dama" She was looking at him with confusion, can ta kalli motar, shi ko har ya amshi Akwatunanta yayi booth din mota da su, sannan ya dawo ya bude mata back seat, zata yi magana sai ta hango AJ zaune front seat din motar, ta ɗan yi jim, sai kuma ta fasa cewa komai, ta tafi ta shiga motar, hotel drivern ya kai su kasancewar next available flight to lagos na karfe bakwai na magrib ne, dakin da aka biya mata na downstairs, shi kuma AJ sama taga ya tafi, All this while kuma bai ce mata komai ba, ita dai tana son ce masa ta gode amma bai bar space din hakan ba, ko tsayawa bai yi ba balle tayi godiyan, sai da driver din ya amshi passport din ta da zai mata booking din jirgi tare da AJ zuwa kano sannan ya bar hotel din, bayan Khaleesat ta shiga dakin babu dadewa aka kawo mata lafiyayyen lunch, duk da tana jin yunwa bata iya ta ci da yawa ba she is just restless, taje bandaki ta wanke baki tayi wanka ta dauro alwala ta fito, bayan ta saka wasu kayan tayi sallah sannan ta dau handbag ta bude zata ciro lip gloss dinta, a nan taga kudin da Jay ya saka mata, ta dinga kallon kudin ko kiftawa bata yi a sanyaye. Karfe shidda da yan mintuna drivern ya sake zuwa ya daukesu ya maida su airport, daga nan kuma suka hau jirgi zuwa garin kano, inda suka sauka airport din Aminu kano karfe tara saura na dare, this time around ma sai da drivern da ya zo daukan AJ ya sauka yayi mata magana tare da kai akwatunanta booth, ita dai tana ta tsaye don taxi kawai ta so dauka da zai kai ta gida, ganin drivern ya bude mata back seat ta karasa jiki a sanyaye ta shiga motar, sai da suka fita daga Airport din drivern ya kalleta ta madubi yace "Ranki shi dade wani anguwan za a ajiye ki?" Khaleesat ta ɗan kalli AJ dake zaune gaban motar yana danna wayarsa, sai kuma ta kalli drivern tace "Inda zan je da nisa, kar in bata maku lokaci gashi dare yayi, duk inda ka samu kawai ka ajiye ni zan samu abun hawa" Sai a sannan AJ yace "Ce maki yayi sauri yake?" Khaleesat tayi shiru, sai kuma tace "Ni Mariri zan je" Driver yace "Toh Allah ya kai mu lafiya Hajiya" Bayan tafiyar kusan minti arba'in suka iso Maririn, A hankali Khaleesat dake kallon drivern tace "Zan iya sauka a nan sai in karasa cikin layin saboda kar ku shiga baku samu wajen juyawa ba...." Drivern yace "Layin baya bulla ne? In dai yana bulla babu damuwa za mu samu hanya in sha Allah" Tace "Toh shikenan, nagode" Nan ta nuna masa inda zai bi ya shiga unguwan, shi dai AJ kallon ikon Allah kawai yake without uttering a word, haka jama'an anguwan suka dinga bin motar da ya dalle ko ina da haske da kallo, ba ko wani mai mota bane zai yarda ya shiga hanyar nan da motarsa cause driving is uncomfortable there in baka yi hankali ba sai ka goge motarka, gashi gidan nasu can ciki ciki ne, at last dai tace "Kawai in ka samu waje a nan zan sauka, ga gidan can" Drivern yace "Toh shikenan Hajiya" Haka ya samu yayi parking motar, sannan ya sauka zai dauko mata akwatunanta a bayan booth, ta bude motar ta sauka tana kallon kofar gidansu hankalinta ya ɗan kwanta ganin bata ga Babanta a kofar gidan ba, kan kace me yara yaran anguwan da suka ga ita ce a motar suka taho da gudu ana mata oyoyo, haka dai ta samu ta hadasu da akwatunanta sannan ta zaga zuwa side din da Ajay yake, tana wasa da gefen gyalenta ta kasa kallonsa tace "Thank you so much Allah ya saka da alkhairi" yace "Wanda ya hada ki jirgi daya da ni zaki ma godiya, Jay kenan" Sai a sannan ta ɗan kallesa, bata dai ce komai ba ta juya tana tafiya a hankali ta bar wajen, godiya tayi ma drivern ta masa kwatancen unguwan da zai shiga wanda a nan zai samu hanyar billa zuwa titi, yayi mata godiya shima ya shiga mota sannan ta nufi cikin gidansu gabanta na faduwa, a hankali tayi raising sack din cement that was use as barrier between the door and inside of the house zata shiga cikin gidan ta ci karo da kanninta da suka fito yi mata oyoyo da gudu bayan yara sun shiga da akwatunan ta, a haka suka shiga cikin gidan tare tana Rungume da su, zazzaune taga kishiyoyin ummanta biyu da 'ya yansu rakacaa a tsakar gidan har a lkcn ba a sauke tuwon dare ba gashi ana neman karfe goma, kananun yaransu ne kawai suka taso yi mata oyoyo da gudu, muryar wata makociyarsu dake zaune cikin gidan taji tana cewa "Ikon Allah sannu da zuwa Amarya ashe dai kina hanya dama" Khaleesat dai kallonta kawai take jin abinda tace, taji kishiyoyin ummanta na cewa "Ai ko dai, kinga mu da muke gidan ma ko gaya mana ba ayi ba balle mu shiga mu fita tahowar nata ya fasu, kinsan haka aka maida mu a gidan, to ga dai ta mun ganta kamar an jefota, mun kuma yi murna" Khaleesat ta gaishesu without waiting for response ta shige dakin Ummanta, zaune ta ganta a bakin kofa Umma dake kallonta cike da damuwa tace "Khaleesat me ya samu wayarki kusan wata daya? Dama kina hanya shine Abdul din bai gaya mana ba?" Khaleesat ta rungumeta a hankali tace "Umma lalacewa wayar yayi" Umma ta dago kanta tana kallonta tace "To shi ya dauko ki a tashar jirgin?" Khaleesat ta sauke idonta tace "A'a" Muryar kawar Ummanta da taji a dakin yasa ta daga kai don bata ma san tana ciki ba, Khaleesat ta gaisheta da murmushi, Mama Salame ta amsa da fara'a tace "Ashe dai kina hanya amarya" Khaleesat tace "Amarya kuma Mama?" Mama Salame tace "Au shi Awdul din bai gaya maki ba dama, ai yau ana saukowa sallan juma'a aka daura auran ku" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 27... Khaleesat na zaune gefen gado tana kallon Jay dake kulle mata akwatunan ta, yana dagowa ta juya a hankali tana kallon window dake dakin, ya dau boxes din biyu yace "Let me get them in the car" Daga haka ya fita daga dakin, ta jinginar da kanta jikin gadon dakin har ya dawo, yana kallonta yace "Hope you didn't forget anything Halysaah" Ta gyada masa kai, yace "Ok, you know what? in dai muka fita kika hadu da AJ thank him and tell him you are leaving" With a smile on his face ya kare maganar yana kallonta, ta sauke idonta tana wasa da fingers dinta a hankali tace "Ohk" Yace "Good gal, mu tafi" Mikewa tayi ta bi bayansa tana rike da karamin handbag dinta walking slowly, suna fitowa walk way din babban corridor din sama sai ga AJ ya taho daga parlorn dake nan sama, Jay ya kalli kayan jikinsa ganin iri daya suka sa kuma tun safe ba wai sun hadu bane kawai coincidence, tunda AJ ya kallesu sau daya ya ci gaba da tafiyarsa, Khaleesat ta ɗan kalli Jay, ya gyada mata kai sannan ya nufi stairs, ita dai tana tsaye ta jira har AJ ya iso kusa da inda take sannan ta sauke idonta a hankali tace "Good morning, i want to thank and appreciate you for everything, i will be leaving today in sha Allah" Without looking at her yace "Jay dai zaki ma godiya ni me na maki" Ta bi sa da kallo har ya fara sauka downstairs, sai bayan da ya sauka sannan ta tabe baki ta bi bayansa tana tafiya a hankali, parlor ta tarar da Jay zaune yana jiranta, Jay ya bi AJ da kallo yace "Flight din naka na gobe ne amma?" AJ yace "I am leaving for the airport now" Jay yace "Ohk, zaka jira inyi dropping Housemate dina sai in dawo in kai ka airport din?" AJ yace "No, don't bother" Daga haka ya fita daga parlon tare da daya daga workers din gidan wanda da alama shi zai yi dropping dinsa airport din, Jay ya daga kai ya kalli Khaleesat, ya lura tunda gari ya waye jikinta yake a sanyaye, yana kallonta yace "Are you Okay Halysaah?" Ɗan murmushi tayi tace "Sure" yace "Kin gaya ma kawarki yau zaki tafi?" Khaleesat ta gyada masa kai tace "Na gaya mata" Yace "Ok, ita yaushe zata tafi?" Khaleesat tace "Yayanta yace ta bari ranan lahadi" Jay yace "Kin tabbatar baki mance komai ba kuwa a sama?" Ta gyada masa kai, yace "Je dai ki sake dubawa Housemate" Bata masa musu ba ta juya zata koma sama yace "Toh ki ajiye jakar taki mana" Ta dawo ta ajiye jakarta a kan kujera sannan ta wuce sama, Mikewa Jay yayi ya tafi gun jakar ya dauka ya bude sannan ya ciro Dala dubu daya a aljihunsa ya sa mata a jakar ya kulle ya mayar ya ajiye mata ya koma ya zauna, ba a dau lokaci ba Khaleesat ta dawo downstairs tace "Ban manta komai ba" Yace "Good" Mikewa yayi bayan yaji fitar motar AJ don dama jira yake yaji sun fita daga gidan, yana kallonta yace "Mu je, ur Flight is in an hour time in sha Allah" Khaleesat ta gyada masa kai ta dau handbag dinta, tana biye da shi suka fita daga parlon gidan, har gari ya fara duhu, suna shiga motarsa ta mika masa wayarsa dake hannunta kar ta manta, a hankali tace "Thank you so much" Ya amshi wayar sannan ya dauko pin a motar ya cire sim card din cikin wayar snn ya mayar mata yace "Your ticket is on the phone, in kin koma Nigeria sai kiyi SIM card replacement, in kuma baki son wayar sai in sa a kai maki sabo a Nigeria" Tayi murmushin karfin hali tace "Saboda me zance bana so, nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Yace "To ai nasan ku mata da son sabon abu" Ta girgiza masa kai kawai tana murmushi bata ce komai ba, a haka suka bar gidan suka dau hanyar airport da tunani iri iri a ran Khaleesat, ko baccin kirki bata yi ba daren jiya ga wani daren, ko me zata je ta tarar a Nigeria sai Allah, it's now that reality is dawning on her, bayan sun isa airport Jay ya juya ya kalleta yace "You can sort ur self out ba sai na shiga ciki ba ai ko?" Ta gyada masa kai, da kyar tayi karfin halin cewa "Thank you so much Housemate, Allah ya saka da alkhairi da abubuwan da ka min" Kasa ci gaba tayi saboda hawayen da ya fara sauka a idonta she just can't thank him enough, gani take words aren't enough to thank him, shi dai Jay kallonta kawai yake with surprise, can yace "C'mon Halysaah, to menene abun kuka?" Ta kasa basa amsa ta rufe fuskarta da gyalenta tana kuka a hankali, Jay ya kwantar da murya yace "Pls ki dena wannan kukan, in nasan abinda zaki yi kenan i will have just order either Lfyt or an Uber that will be taking you to the airport" Dena kukan tayi tana goge hawayen da yaki tsaya mata tana kallonsa, ya bude motar ya sauka ta bi sa da ido taga Luggages dinta dake booth zai dauko, a hankali ta bude side dinta ta sauka daga motar tana bin sa da kallo, daya daga porters dake wajen ya ba luggages din nata ya shigar mata da shi ciki ya hada masa da tip dinsa, ita dai Khaleesat kallonsa take, ya juya ya dawo kusa da ita yace "Alright safe trip Halysaah, idan kinyi replacing Sim card dinki sai ki min magana ta WhatsApp, my regards to everyone back home" Ta sauke idonta a hankali tace "I will miss you" sai bayan da ta fada haka ita kanta tayi realizing abinda ta fada, sai kuma ta kasa dago kanta, ya ɗan yi murmushi yace "I will miss you too Housemate, in sha Allah next week i will be in Nigeria too" Bata iya ta kallesa ba ta gyada masa kai kawai ta juya a hankali ta bi bayan porter din da ya shigar mata da luggages dinta zuwa check in counter for her Boarding pass, kasancewar Business class ticket gareta all the processes were smooth and straight for her, daga karshe ta nufi waiting lounge don in 15 mins time za su fara boarding jirgi, tunda ta shiga lounge din take kallon wanda ta gani zaune da mamaki, ta kalli boarding pass dinta sannan ta kalli na hannunsa taga iri daya, wayarsa kawai yake dannawa, ganin bai ganta ba ta juya a hankali ta koma wani wajen daban ta zauna ta inda ma bazai ganta ba, bata sake waigen inda yake ba, iya drink kawai ta amsa a lounge din unlike wasu da ke ta cin abinci duk a cikin kudinsu, gaba daya ta nemi appetite dinta ta rasa saboda damuwa, da ta tuna inda zata sae taji har wani juya mata kanta yake kamar bata da lafiya, ta saƙa wancen a ranta ta kwance har daga karshe aka fara boarding din jirgi, sai da Khaleesat ta jira AJ ya fara tafiya sannan ta mike ta bi bayansa walking slowly, Har seat dinta wata Flight Attendance da ke welcoming dinta da fara'a ta kai ta, hada ido Khaleesat tayi da AJ that was sitting few seats away from hers, ta sunkuyar da kanta ta zauna Seat dinta tana mayar da Amenity kit din da aka ajiye mata a gefe, AJ ya kasa daina kallonta fuskarsa babu yabo babu fallasa, he can't even explain what he is feeling at that moment don bai taɓa ganin wanda ya gama rena masa wayo a duniyar nan kamar Jay ba, jiya wajen karfe sha biyun dare ya farka ya gansa yana duba masa waya ashe ticket din da ya siya yake dubawa, he felt like just leaving the plane at that moment, after a while kawai ya dauke kai yana kara gyara barrier din da zai sa ko hangota bazai dinga yi ba, Ita ma Khaleesat ko by mistake bata sake kallon direction din sa ba, a haka jirgin ya tashi, Khaleesat bata taɓa jin motion sickness ba tun da ta fara tafiya a jirgi amma yau ko don saboda pressure din da ta saka ma ranta ne kawai sai ji tayi as if she wants to throw up tun da jirgin ya daga, ta cire seat belt dinta da sauri ta mike ta nufi Lavatory din jirgin almost running, shi dai ya bi ta da kallo, Flight Attendance din da ta kawo mata Hot towel kafin tashin jirgin ne ta bi bayanta tana tambayar if she's okay, Khaleesat ta gyada mata kai kawai bayan ta fito daga Lavatory din, AJ ya bi ta da kallo har ta koma seat dinta ta zauna sannan ya tabe baki, Flight Attendance din ta duka kusa da ita tana tambayarta ko tana bukatar wani abu ne, Khaleesat ta girgiza kai tana murmushin karfin hali tace "Thank you, i am okay" Matar ta sake tafiya sai ga ta ta dawo da ruwa da orange drink, sai kuma wani drink daban duk a glass daban daban akan tray daya, ta duka tana mika ma Khaleesat ta dauki wanda take so, glass din ruwa kawai Khaleesat ta dauka ta mata godiya sannan ta sanar mata bazata ci abinci ba all throughout the flight don ma kar matar ta sake dawo mata, gani take tana cin abu zata yi aman da bata yi ba daxu, gyara kujeranta tayi ta kwanta ta lulluba da blanket din da jirgin yayi providing for business class passengers, nan da nan bacci ya dauketa, da za su sauka Turkey wajen karfe hudun asuba sai da wata Flight Attendance daban ta zo ta tasheta ta sanar mata jirgi zai sauka, Khaleesat ta mike zaune da kyar don ciwo kanta ke mata, tayi fastening seat belt dinta, bayan sun sauka Istanbul ta bi AJ da kallo har sai da ta daina hangosa sannan ta mike ta dau handbag dinta da waya ta bi bayansa tana tafiya da kyar leaving her Amenity kit behind, jiran awa biyu za su yi a Business Class waiting lounge na airport din kafin a canza masu jirgin da zai kai su Nigeria, ta riga AJ shigowa lounge din kilan masallaci ya tafi, ita ma tana ganin lokacin sallahn asuba yayi ta tafi tayi sannan ta dawo ta zauna a business lounge din, after like 15 mins sai gashi ya shigo, not far away from her ya zauna da ruwan gora a hannunsa, Ita dai ta jinginar da kanta jikin kujeran da take zaune ta daura handbag dinta a kafarta, she is having a terrible headache a lokacin, after almost 30 mins of sitting wani ɗan Nigeria ya dawo kusa da ita ya zauna, wanda shi ma daga nan Turkey zai je Nigeria a Business class, kuma jirginsu daya kamar yanda ta ga ticket irin wanda ta amsa bayan sun sauka Istanbul din a hannunsa shima, yana kallonta yayi mata sallama cikin nutsuwa, ta ɗan kallesa sannan ta amsa, yace "Guess you are coming from America right?" Tace "Uhm" Yana kallon Flight ticket dinta yace "Oops you are having the same name as my Mum, can i call you Jiddah instead of the real name?" Khaleesat dake sauraronsa without looking at him tace "Ohk" Yana murmushi yace "Alright, are you traveling alone Jiddah?" Ta girgiza kai tace "No" Ya buda ido yace "Ohk with who?" Ta kalli direction din AJ, shi ma mutumin ya kallesa suka hada ido don kallonsu kawai Ajayn yake yana jin conversation dinsu, mutumin na murmushi ya tashi yaje ya gaisa da AJ sannan ya koma ya zauna, shikenan Khaleesat ta samu lafiya, don bai sake ce mata komai ba kawai danna wayarsa yake tayi tunda shi dai bai san ko waye Ajayn a gunta ba, daga karshe ma ya tashi ya bar wajen, at last aka fara boarding din jirgin da zai kai su Lagos Nigeria daga Istanbul, Usman ya juya ya kalli Khaleesat da ta mike tana rike da handbag dinta, har AJ ya wucesu sai kuma ya tsaya amma bai juyo ba, ita dai tana tafiya a hankali har ta isa inda yake tsaye sannan ya ci gaba da tafiya tana biye da shi, har jirgi ya tashi Usman dake zaune not far from Khaleesat but close to AJ bai ce mata komai ba, this time around ma dai bacci kawai tayi har zuwa Nigeria. Karfe hudu saura suka sauka Nigeria washegari Friday, ita dai Khaleesat tun da ta ganta Lagos bayan ta gama da Custom da Immigration ta fara tunanin kuma yanda zata yi, to ko dai kawai ta tafi gidan Aunty Farida tunda a nan Lagos take, to ko tace zata je bata da sim din da zata kirata don ba gane anguwan zata yi ba kuma bata da lambarta a kai balle ko waya ne ta ara ta kirata a airport din, sai kuma tayi tunanin kiran Ummanta tunda tana da numberta a kai sai tace ta turo mata number Aunty Farida, gun wata mata warce taga kamar Bahaushiya ce ta nufa, ta gaisheta sannan tace "Don Allah Aunty wayarki zaki ara min in ɗan yi kira nawa ba caji" Matar ta fara kallonta daga sama har kasa, sai kuma ta bude handbag dinta ta ciro wayarta ta mika mata, Khaleesat ta amsa tace "Nagode" Dialing number Umma tayi ta kira taji a kashe, sosai jikinta yayi sanyi, ta kira har sau uku duk ana ce mata a kashe, a hankali ta zame wayar a kunnenta ta mika ma matar tace "Nagode, wayar ma a kashe yake" sai da matar tayi dialing wayar ta tabbatar eh a kashe din yake, kana ganin matar kasan she is not comfortable giving off her phone, Khaleesat na jan trolley dinta a hankali ta fito daga cikin airport din tana tunanin yanda zata yi, ko dai kawai ta tafi tashan da zata samu mota zuwa kano, since she have some money in her bank account, wani mutumi ne taga ya nufota, ya gaisheta da ladabi yana mata barka da zuwa, sannan ya nuna mata mota yace "Ke mu ke jira ki fito dama" She was looking at him with confusion, can ta kalli motar, shi ko har ya amshi Akwatunanta yayi booth din mota da su, sannan ya dawo ya bude mata back seat, zata yi magana sai ta hango AJ zaune front seat din motar, ta ɗan yi jim, sai kuma ta fasa cewa komai, ta tafi ta shiga motar, hotel drivern ya kai su kasancewar next available flight to lagos na karfe bakwai na magrib ne, dakin da aka biya mata na downstairs, shi kuma AJ sama taga ya tafi, All this while kuma bai ce mata komai ba, ita dai tana son ce masa ta gode amma bai bar space din hakan ba, ko tsayawa bai yi ba balle tayi godiyan, sai da driver din ya amshi passport din ta da zai mata booking din jirgi tare da AJ zuwa kano sannan ya bar hotel din, bayan Khaleesat ta shiga dakin babu dadewa aka kawo mata lafiyayyen lunch, duk da tana jin yunwa bata iya ta ci da yawa ba she is just restless, taje bandaki ta wanke baki tayi wanka ta dauro alwala ta fito, bayan ta saka wasu kayan tayi sallah sannan ta dau handbag ta bude zata ciro lip gloss dinta, a nan taga kudin da Jay ya saka mata, ta dinga kallon kudin ko kiftawa bata yi a sanyaye. Karfe shidda da yan mintuna drivern ya sake zuwa ya daukesu ya maida su airport, daga nan kuma suka hau jirgi zuwa garin kano, inda suka sauka airport din Aminu kano karfe tara saura na dare, this time around ma sai da drivern da ya zo daukan AJ ya sauka yayi mata magana tare da kai akwatunanta booth, ita dai tana ta tsaye don taxi kawai ta so dauka da zai kai ta gida, ganin drivern ya bude mata back seat ta karasa jiki a sanyaye ta shiga motar, sai da suka fita daga Airport din drivern ya kalleta ta madubi yace "Ranki shi dade wani anguwan za a ajiye ki?" Khaleesat ta ɗan kalli AJ dake zaune gaban motar yana danna wayarsa, sai kuma ta kalli drivern tace "Inda zan je da nisa, kar in bata maku lokaci gashi dare yayi, duk inda ka samu kawai ka ajiye ni zan samu abun hawa" Sai a sannan AJ yace "Ce maki yayi sauri yake?" Khaleesat tayi shiru, sai kuma tace "Ni Mariri zan je" Driver yace "Toh Allah ya kai mu lafiya Hajiya" Bayan tafiyar kusan minti arba'in suka iso Maririn, A hankali Khaleesat dake kallon drivern tace "Zan iya sauka a nan sai in karasa cikin layin saboda kar ku shiga baku samu wajen juyawa ba...." Drivern yace "Layin baya bulla ne? In dai yana bulla babu damuwa za mu samu hanya in sha Allah" Tace "Toh shikenan, nagode" Nan ta nuna masa inda zai bi ya shiga unguwan, shi dai AJ kallon ikon Allah kawai yake without uttering a word, haka jama'an anguwan suka dinga bin motar da ya dalle ko ina da haske da kallo, ba ko wani mai mota bane zai yarda ya shiga hanyar nan da motarsa cause driving is uncomfortable there in baka yi hankali ba sai ka goge motarka, gashi gidan nasu can ciki ciki ne, at last dai tace "Kawai in ka samu waje a nan zan sauka, ga gidan can" Drivern yace "Toh shikenan Hajiya" Haka ya samu yayi parking motar, sannan ya sauka zai dauko mata akwatunanta a bayan booth, ta bude motar ta sauka tana kallon kofar gidansu hankalinta ya ɗan kwanta ganin bata ga Babanta a kofar gidan ba, kan kace me yara yaran anguwan da suka ga ita ce a motar suka taho da gudu ana mata oyoyo, haka dai ta samu ta hadasu da akwatunanta sannan ta zaga zuwa side din da Ajay yake, tana wasa da gefen gyalenta ta kasa kallonsa tace "Thank you so much Allah ya saka da alkhairi" yace "Wanda ya hada ki jirgi daya da ni zaki ma godiya, Jay kenan" Sai a sannan ta ɗan kallesa, bata dai ce komai ba ta juya tana tafiya a hankali ta bar wajen, godiya tayi ma drivern ta masa kwatancen unguwan da zai shiga wanda a nan zai samu hanyar billa zuwa titi, yayi mata godiya shima ya shiga mota sannan ta nufi cikin gidansu gabanta na faduwa, a hankali tayi raising sack din cement that was use as barrier between the door and inside of the house zata shiga cikin gidan ta ci karo da kanninta da suka fito yi mata oyoyo da gudu bayan yara sun shiga da akwatunan ta, a haka suka shiga cikin gidan tare tana Rungume da su, zazzaune taga kishiyoyin ummanta biyu da 'ya yansu rakacaa a tsakar gidan har a lkcn ba a sauke tuwon dare ba gashi ana neman karfe goma, kananun yaransu ne kawai suka taso yi mata oyoyo da gudu, muryar wata makociyarsu dake zaune cikin gidan taji tana cewa "Ikon Allah sannu da zuwa Amarya ashe dai kina hanya dama" Khaleesat dai kallonta kawai take jin abinda tace, taji kishiyoyin ummanta na cewa "Ai ko dai, kinga mu da muke gidan ma ko gaya mana ba ayi ba balle mu shiga mu fita tahowar nata ya fasu, kinsan haka aka maida mu a gidan, to ga dai ta mun ganta kamar an jefota, mun kuma yi murna" Khaleesat ta gaishesu without waiting for response ta shige dakin Ummanta, zaune ta ganta a bakin kofa Umma dake kallonta cike da damuwa tace "Khaleesat me ya samu wayarki kusan wata daya? Dama kina hanya shine Abdul din bai gaya mana ba?" Khaleesat ta rungumeta a hankali tace "Umma lalacewa wayar yayi" Umma ta dago kanta tana kallonta tace "To shi ya dauko ki a tashar jirgin?" Khaleesat ta sauke idonta tace "A'a" Muryar kawar Ummanta da taji a dakin yasa ta daga kai don bata ma san tana ciki ba, Khaleesat ta gaisheta da murmushi, Mama Salame ta amsa da fara'a tace "Ashe dai kina hanya amarya" Khaleesat tace "Amarya kuma Mama?" Mama Salame tace "Au shi Awdul din bai gaya maki ba dama, ai yau ana saukowa sallan juma'a aka daura auran ku" * HALYSAAH 28... Khaleesat ta kwala wani karan da ya gigita Ummanta da Mama Salame, Umma ta mike da sauri tana kallonta a kidime, haka ma Mama Salame da tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, menene haka Khaleesah?" kishiyoyin Umma duk suka yo dakin a guje su ma don Khaleesat bata fasa ihun da take kwalawa ba cikin tashin hankali take cewa "Wallahi bana son shi bazan iya zaman aure da shi ba, na shiga uku na lalace, don Allah Umma ku min rai ku rufa min asiri, wallahi bana son sa" Umma dai sake baki tayi tana kallon Khaleesat tashin hankali karara a fuskarta gashi ta kasa cewa komai, daya daga kishiyoyin Umma da ake kira Mama Shatu tana gyara zaninta da ya kusa kwancewa saboda gudun da suka yi tace "Ji wani gulma da kinibibi? Shi Abdul din ne da ya daukeki ya kai ki kasan turai karatu yayi ta kashe kudadensa ne baki so yau? A ajiye batun ubanki a gefe, ke abinda ya kashe maki yau ko kaf kasar da uwarki ta baro za a siyar za a iya biyansa aka ce maki?" Ita ma daya Co-wive din da suke kira Mama Zubaida tace "A'a rainin wayo mana Shatu, gwara ai a rena mana hankali, don uwarta kasuwa ne nan da zata cika mana gida da ƙuwa, wannan ai iskanci ne da walakanci" Khaleesat bata fasa kuka da ihun da take a dakin Ummanta ba tana surutai ita kanta bata san takamaiman abinda take cewa ba tsabar tashin hankali, Kanninta Noor da Islam kuwa har sun fara kuka su ma a dakin, kan kace me har makota sun fara tururuwan shigowa gidan, aka tsaya cirko cirko bakin kofar dakin Ummanta ana salallami, Mahaifinta ne Malam Ali ya shigo gidan yana zazzare ido, shi ma ya karaso da sauri yana tambayar abinda ke faruwa a gidan, Mama Shatu ta tabe baki tace "Wai er da ta fi kowa ce ta sauka yau daga Amurka shine uwar ke sanar mata ai an daura aurensu da shi wanda ya kai ta waje karatu har ta dena ganin kowa da gashi, shine fa ta cika anguwa da ihu da koke koke wai ita bata son auren bazata zauna da shi ba, ga jama'a na ta shigowa an zata gobara muke, wannan ai tsabar sangarci da iya shege ne" Juyawa Malam Ali yayi ya nufi gun da ake ajiye itacen girki da sauri ya suri daya ya dawo ya nufo dakin Umma yana cewa "Ina take..." Matan makota dake tsakar gidan suka hau basa hakuri suna don Allah ya kyaleta, yaki sauraron kowa yana zazzare ido, Khaleesat na hangosa ta tafi bayan Ummanta da gudu tana kuka ta rungumeta, kanninta ma suka yi bayan Umma gaba daya suna kuka, Mama Salame ta tsaya tayi bake bake gabansa tace "Haba haba, haba Malam Ali, meye haka kake kokarin yi?" Yace "Salame ki bar ni dai inci malfar ubanta a wajen, mu zata tona ma asiri? Ni zata ja ma sabon bala'i da fitinan da ya girmeni?" Mama Salame tace "A'a wallahi baza ka doketa da wannan rafkeken icen ba ita ba jaka ba, mu je waje Malam Ali" Ita dai Umma kanta na kasa bata ce komai ba, haka Mama Salame ta samu ta tasa keyarsa ya fita daga dakin tana biye da shi, Mama Zubaida ta rike haɓa tace "Ikon Allah, mu muke ganin kinibibi iri iri a gidan nan, to in aka bibiya wani ta kyallara ido ta gani a Amurkan shine zata tona ma uban asirinsa da ke rufe, da can menene yasa ta hakura zata aurensa? Sai ranan da aka daura aure ta nemi tara mana mutan anguwa tace bata san zance ba? Yau ni nake ganin iskanci, to ta tsotsi nonon buzuwa ba dole ta iya makirci da kissa ba" Ita dai Khaleesat kuka kawai take a jikin Ummanta siblings dinta na kusa da ita suna taya ta, Mama Salame ta sake labulen dakin Umma duk don matan dake tsaye bakin kofar su kama gabansu, Umma ta juya tana kallon Khaleesat gaba daya ta kasa cewa komai, zamewa kasa Khaleesat tayi ta hade kanta da gwiwa tana kuka kamar ranta zai fita tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace" a sanyaye Umma ta tafi gefen katifar dakin ta zauna ta kasa cewa komai. Karfe biyun dare Umma na zaune kan darduma da carbi a hannunta, Khaleesat ta tsallake kanninta ta fito daga cikin net din da take kwance bayan ta tuna ko isha'i bata yi ba, tunda Mama Salame ta daura mata net tace ta shiga ta kwanta wajen karfe sha daya take kwance duk da ba bacci take ba, don ko bacci barawo bata gani ba, amma tayi shiru cikin net din tunani iri iri na yawo a kanta, gaba daya ta ji kamar hawayenta ma ya kafe, har a lkcn babu maganar da ya hadata da Ummanta, tana jin jiri da zazzabi ta nufi kofa zata fita ta dauro alwala, Umma dai ta bi ta da kallo, bayan ta dauro alwalan ta dawo ta saka hijab dinta ta tada sallah, bayan ta idar tayi nafila raka'a biyu, tana zaune kan darduman ta jingina da bango tayi nisa tunanin da take, gani take kamar a mafarki ake sanar mata an daura mata aure da Abdul amma ta ki farkawa daga mummunan baccin nan har yanzu, muryar Ummanta yaji ta kirata a hankali, Khaleesat ta juya ta kalleta amma ta kasa amsawa, Umma ta mike ta koma kusa da ita ta zauna tana kallonta, cikin sanyin murya tace "Me ya faru kuma tsakaninki da Abdul din Khaleesat? Wani abun ya kara maki? Me yasa kika ce baki son auren?" Khaleesat ta fashe da kuka a hankali tace "Umma wallahi bana son sa, bazan iya zama da shi ba, in aka ce za a kai ni gidansa zan iya mutuwa wallahi, don Allah Umma ku taimakeni ku yi min rai" Umma ta kasa ce mata komai hawaye ya cika idonta ta fara gogewa da hijab dinta, Khaleesat ta daura kanta kan kafadar Ummanta tana kuka me tsuma zuciya tace "Don Allah ku taimakeni Umma, bazan iya ba wallahi" Umma ta rungumeta tana patting bayanta ita ma hawayen na sauka idonta amma bata iya ta ce mata komai ba, they sat there for almost 40 mins, jin tana sauke numfashi a hankali Umma ta gane bacci tayi, a haka Umma ta zauna wajen Khaleesat na jikinta don bata son tashinta har kusan lokacin sallahn asuba. Da safe wajen karfe tara Umma ta shigo dakinta rike da cup din kunu da kosai a roba, ta karasa kusa da Khaleesat dake kwance gefen katifarta ta ajiye mata sannan ta zauna cikin kwantar da murya tace "Ta so ki ci ko kadan ne Khaleesat" Khaleesat dai kallon cup din kunun kawai take, lkci daya hawaye ya cika idonta, Umma dai ta sunkuyar da kai, Islam ce ta shigo dakin rike da paracetamol da Umma ta aiketa ta siyo ma yayar tata, ta zauna kusa da Umma tace "Umma ga maganin na siyo ma Aunty" Umma ta amsa ta ajiye a gefenta tace "Tashi ki je ki karasa min aikin da na sa ki" Islam dake kallon Khaleesat ta mike a hankali ta fita daga dakin, Umma ta maida dubanta kan Khaleesat tace "So kike ki sa ma kanki wani ciwon ne Khaleesat nima ki sa min damuwa? Ki tashi ko kunun ne ki sha" Khaleesat ta girgiza mata kai cikin rawan murya tace "Ni bazan iya sha ba Umma" a sanyaye Umma tace "Toh ya kike son in maki Khaleesat?" Umma ta kasa ci gaba hawaye ya fara sauka idonta ta dafe kanta, kuka kawai Khaleesat take tana kallon Ummanta, Umma ta dake tana share idonta tace "Ko wajen Nenne zaki sai ki gaya mata ki ji abinda zata ce, ni kin san babu abinda zan iya yi akan lamarin nan Khaleesat" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, Umma ta mike a sanyaye ta fita daga dakin don juye mata ruwan wankan da ta dora mata a kan wuta yana ta tafasa, a haka ta ta dawo ta samu ta lallabata ta ɗan sha kunun sannan ta tafi waje yin wanka, kafin ta fito har Umma ta fiddo mata kayan da zata sa tayi tagumi tana jiranta, karfin hali kawai Khaleesat take amma ji take kamar zata iya collapse at anytime, bayan ta shirya Umma tace "Amma bana son yan gidan nan su san inda zaki, kar su gaya ma Malam" Khaleesat ta jinginar da kanta da bango, a hankali tace "Umma bazan iya zuwa ni kadai ba don Allah ki rakani" Umma tayi shiru, can tace "To zan fita in shiga gidansu Er Lami in jira ki a can, bana son su ga mun fita tare, bayan na fita da minti goma kema sai ki fito" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata, Umma ta mike ta dau hijab dinta ta saka sannan ta dora nikab ta fita daga dakin, Su Mama Shatu da Mama Zubaida suna ta girka abincin siyarwansu da yaransu za su fita talla da shi, tace masu zata shiga makota sannan ta fita, duk suka bi ta da kallo sun tabe baki, Mama Shatu tace "Ma ji ma gani dai, a sanda ake mana fafa an tura 'ya kasar waje ga namu yaran a zube ai babu bakin cikin da ba a kuntsa mana ba" Mama Zubaida tace "Sun gana tattatse ɗan mutane rana daya su fito su ce basu san zance ba, ke ina kika taɓa ganin anyi haka? Ai na so Malam ya rarrade shegiya jiya da daddare, to dai ba kanta kadai zata ja ma babban magana ba, har shi Malam din" Duk Khaleesat na jin su, ita dai tana zaune ta jinginar da kanta da bango tana sauke numfashi a hankali, bayan minti goma da fitar Ummanta ta tashi da kyar ta fiddo gogaggen Hijab dinta ta saka sannan ta dora Nikab ta fita daga dakin, tunda ta fito suke kallonta, a haka ta nufi hanyar fita daga tsakar gidan tana ji kamar iska zai kadata ta fadi. Gidan da Ummanta tace zata jirata ta nufa, ta samu Ummanta a tsakar gida tana jiranta yan gidan ma duk basa nan, Umma ta taso suka fita daga gidan, tafiyar kusan minti sha biyar ne zuwa gidan Nenne daga gidansu, Nenne ta ajiye tsintsiyar hannunta tace "Dawowa yayi da ita daga inda take karatun don an daura aure?" Umma ta zauna kan tabarman tsakar gidan ta cire Nikab din fuskarta ta gaida Nenne, Khaleesat ta zauna gefen Ummanta, Nenne ta amsa tace "Ai dama nace ko da ta dawo sai ta huta an kintsa ta kafin ayi maganar wata tarewa tunda yace baya bukatar taron komai, amma baza mu dau yarinya haka kawai ace an je kai ta ba" Umma dai tayi shiru bata ce komai ba, a hankali Khaleesat ta cire Nikab din fuskarta ta ajiye, Nenne ta ɗan duka tana kallonta tace "Lapiya naga idanuwanta sun kumbura haka, me ke faruwa?" Umma ta sauke ajiyar zuciya ta kasa cewa komai, A fusace Nenne tace "Magana nake ku ka min shiru fa? Meye haka aka shigo min da ita da kumburarrun ido" Cikin rawan murya Khaleesat tace "Nenne ni bana son sa, bana son auren..." Nenne ta saki baki tace "Baki son auren kuma?" Khaleesat ta gyada mata kai hawaye wasu na bin wasu a kuncinta, Nenne ta nemi waje ta zauna tace "Atoh dai, ni dama shegen bai taɓa kwanta min ba, amma abun dubawa a nan shine na isa da Alin? Ashe ma ba er banza bace ni a gunsa kenan" Nenne ta mike ta shiga dakinta ba a dau lokaci ba ta fito ta dire wani babban ledan hannunta sannan ta bude tace "Kun dai ga duk wata shegiyar kyautarsa da yake kawo min ban taɓa amfani da ko daya ba duk na tara masa kayansa waje daya, ga atamfofinsa nan da turarurruka da tarkace, ba ruwana ban yi amfani da su ba, ke ma Zahra'u inda abunsa da kika san ya taɓa baki ki tattaro su waje daya, shi Ali ina ma yayi amfani da nasa shi ya sani, sai ya shiga kasuwa da wuri wuri" Ita dai Umma tayi shiru bata ce komai ba, Khaleesat kuwa kuka take a hankali, Cikin sanyin murya Umma tace "Kin mance abinda ke kasa ne Nenne, ai yanzu ba maganar wai abinda ya bamu bane damuwar" Nenne tace "Yo ina ruwana da abinda ke ƙasa, ko ina ruwan yarinya da abinda ke kasa? Sai a ma jikata auren dole kike nufi kenan? Ni fa tun asali katon mutumin nan bai min ba sam, ayi mutum ba fara'a ya shigo maka sandan sandan ya fita gansan gansan? A duba fa wannan lamari, da kyar kaga murmushinsa kamar rikakken ɗan ta'adda da aka kusa yi ma preedom, yo wannan uban kudi na ubansa wa ma yasan ko ta'addancin suke da garkuwa da jama'a, hatta ruwan gidana gansamemen mutumin nan bai taɓa sha ba, yanda na ajiye masa haka yake barin min tsiyata bai san yarana mata ruwan gora suke siya min ba ya zata durawa nake, haka zai zauna maka kamar sarki yayi ta danna waya ga gidan er banza ya shigo, to ban isa da Ali ba kannensa mata ma basu isa da shi ba, shi kawai ta kansa yake a rayuwar nan baya duba makomar er da ya haifa a cikinsa, ko dan yaga yaran rakacaa an haifa masa ne ba kwantrol oho, gashi ba jin maganar yayyin uban nasa zai yi ba balle ince ku je ku samesu, in kuma muka ce mu tafi mu kai rahotu gidan yan sanda daga karshe mu za a kulle, to ni Ramatu ya zan yi? Amma dai ba komai zan aika a kira min Alin anjima, hatta batun daurin auren sai jiya da za a daura muke samun labari" A hankali Umma tace "Shi ma Malam din shekaranjiya da yamma suka kirasa suka sanar masa ga abinda suke so za ayi" Nenne tace "Tirrr, duk sun rainamu sun mayar da mu yan iska kawai, na tabbata shi kansa Alin bai taɓa rokon Awdul din naira biyar ba balle uban Awdul" Umma ta girgiza kai tace "Bai taɓa ba kam, jarabawa ce kawai Allah ya dora mana babu yanda mu ka iya" Nenne tace "A'a har da dai iskanci, ku baku da baki? ke da er taki baza ku iya kwatar en cin ku ba, ita kadai ce mace a gidan? Tun asali dama kin maida kanki gantalalliya a gidan" Umma dai tayi shiru, Nenne tace "Ko kuma kawai ku tafi gida zan daidaici lkcn da zai koma gida da magariba in taho gidan" Umma tace "Toh shikenan Nenne" a haka Khaleesat da Ummanta suka bar gidan bayan Nenne ta dama mata fura da nono ta tilastata ta sha. Khaleesat na kwance dakin Ummanta wajen karfe shidda na yamma, har zuwa sannan ta kasa cin komai tun bayan furan da ta sha gidan Nenne, tun da suka dawo gida take karatun qur'ani don ta rasa me ke mata dadi a duniyar kawai bata son tayi ta daga ma Ummanta hankali yasa ta hakura da kuka sai na zuci kawai da take yi, gaba daya taji duniyar yayi mata zafi, da ta tuna wai fa ita matar aure ce yanzu kuma matar Abdul, sai taji dama kawai Allah ya dau ranta ta huta, bayan taji she is exhausted da karatun qur'anin da take tayi shine ta kwanta gefen katifar Ummanta, tayi nisa tunanin da take jin hawaye na taruwa idonta ta mike zaune tana kallon Ummanta dake gyara kayan su Islam a dakin tace "Umma ina wayarki?" Umma ta kalleta tace "Ko sati ba ayi ba na nemeta na rasa an dauke a gidan nan" Khaleesat tayi shiru tana kallon Ummanta, sai kuma ta jawo handbag dinta a hankali ta bude ta ciro wayar da Jay ya bata duk da babu SIM card a ciki, she just want to do something that will keep distracting her from her worries, har zata shiga game sai kuma ta fasa ta shiga gallery din wayar, ta ɗan yi jim na few seconds kafin ta bude hotunan, a hankali take flipping tana kallon each and every image of him and AJ, sai a sannan ta lura da kaman da suke yi even though it's not obvious, wani hotansu tare ta tsura ma ido ganinsu cikin shiga ta alfarma irin ta sarauta, ita dai tana ta kallon hoton babu ko kiftawa, sai kuma tayi flipping zuwa next image, haka ta dinga ganin ire iren hotunan, wani taga Jay shi kadai wani taga Ajay shi kadai, ko kuma ta gansu tare, with horses and so many things related to gidan sarauta, kashe wayar tayi a hankali ta mayar cikin jakarta ta ajiye jin muryan Babanta ya shigo gidan, ya ɗaga labulen dakin Ummanta yana kallonta yace "Ki fita ga Abdul can ya zo yanxu" Sosai gaban Khaleesat ya fadi ta dinga kallon Babanta bata ko kiftawa, Umma ta juya ta kallesa tace "Ta fita kuma Malam? Dama ana haka? Ai ina ga ba sai ya zo ba sai ya jira har zuwa sanda zata tare ko" Malam Ali da ya bude baki yana kallonta yace "Wato dai duk wani salon dauko min magana kun iya shi Zahra'u, in ya zo ta fita sai aka yi yaya? Addini ne ya haramta hakan ko kuwa shirmen ku? Kuma da kike batun tariya ko gobe yace yana bukatar ta tare mu muna da ja ne dama?" Umma tace "Ai ko muna da ja Malam, tunda baza mu dau yarinya haka kawai mu kai ta dakin miji ba, duka duka ma yaushe ta dawo kasar" Khaleesat ta fashe da matsanancin kuka tana jin kamar zuciyarta zai fashe ta huta, Babanta da ya bude baki yana kallonta yace "Ni kike neman tona ma asiri ko ko ya kike so inyi? Sabon magana za ku ja min ke da uwarki kenan? In ma ba yanzu za a tare ba tunda ya zo ai sai ki fita ku gaisa tunda ba haramun bane, in kun gaisa sai ki dawo cikin gida" Khaleesat taki cewa komai sai kuka take, Ya daka mata tsawa yace "Kar ki ga ina lallabaki don uwarki, zaki tashi ki fita ko sai na rarrade ki da icce" Khaleesat na kuka ta sauka daga kan gadon, Umma da hawaye ya cika idonta ta kauda kanta, Khaleesat ta dau Hijab dinta ta saka ta fita daga dakin tana kuka sosai, Kishiyoyin ummanta dake zaune tsakar gida duk suna sauraron abinda ke faruwa sai tabe baki suke, ganin Malam Ali ya bi bayan Khaleesat, Mama Shatu tace "To rakata wajen nasa zaka yi ne Malam?" Sai kuma ya juyo da sauri yace "Au to" Ya nufi ɗan karamin dakinsa dake tsakar gidan, Mama Zubaida ta tabe baki tace "Ma ji ma gani dai" Khaleesat na fita kofar gida hawaye na sauka idonta taga motarsa wanda ke dauke da tinted glass yayi parking dai dai inda su AJ suka tsaya jiya, ko saukowa bai yi daga cikin motar ba, hawaye na bin fuskarta ta tafi ta tsaya kusa da motar taki budewa kuma tasan yana kallonta, after almost 5 mins taga ya sauke glass din motar yace "Ni zan sauko in same ki?" Ita dai taki kallonsa, kuma taki cewa komai, after few seconds ta bude gaban motar a hankali ta shiga amma ta ki kulle motar, yace "Sauron unguwan ku zaki cika min a motata, are you in ur right senses?" A hankali ta ja motar har sannan taki yarda ta kallesa ta kulle, gabanta sai faduwa yake don jin muryarsa take kamar ana tsira mata allura a kunne, Lokaci daya ta juya da sauri tana zaro ido ganin ya zuge glass din ya tada motar ya kara volume din sautin da yake ji sannan ya ja motar, a rikice ta fara kokarin budewa motar taji a kulle gam, ta kwala wani azababben kara tace "Na shiga uku na lalace, don girman Allah kayi hakuri ka rufa min asiri ina zaka kai ni? Ka bude min in sauka...." Ko kallonta bai yi ba fuskarsa babu yabo babu fallasa yake driving dinsa idonsa na kan hanyar dake gabansa, ta rikosa da hannu biyu cikin gigicewa tana masa magiyan ya bude mata motar, bai yi wata wata ba ya sauke mata wani lafiyayyen back hand slap a fuska, sai da taji dumm na few seconds, lkci daya jin ta da ganinta ya dauke na ɗan lokaci, duk da haka bata sake sa daga rikon da tayi masa ba tana kururuwan ya bude mata motar, ya fincikota ya jefar kan kujeran motar cikin kaushin murya yace "Kika sake taɓa ni sai na wanka maki wani marin" Lokaci daya duk jikin Khaleesat ya mutu saboda shock, ta dinga sauke numfashi da kyar idonta na ganin dishi dishi daga marin da yayi mata tana kallonsa, shi dai driving dinsa kawai yake fuskarsa babu yabo babu fallasa...... * HALYSAAH 29 Sai da Khaleesat taga sun bar unguwansu gaba daya sannan reality yayi hitting dinta ta kara fahimtar me Abdul ke da niyyar yi, she felt so helpless at this point, ta jinginar da kanta jikin kujeran motar hawaye masu zafi na sauka idonta ta kasa cewa komai, shi dai driving dinsa kawai yake bai ko kalleta ba, ganin tafiya kawai yake ta juya tana son ko hakuri ne ta bude baki ta basa amma tsoron kar ya sake marinta yasa ta kasa don babu alamar rahama a fuskarsa, ta rufe fuskarta da hijab din jikinta hawaye wasu na bin wani a idonta, tsabar tashin hankali da firgicin da ta shiga a wannan moment din kilan da za a duba jininta za a ga ya hau, bayan tafiyar kusan minti talatin taji ya tsaya cak, da sauri ta sauke Hijab dinta zuciyarta na bugawa tana kalle kallen inda suke, taga dai dai wani eatry ya tsaya, ita dai kallonsa take har sannan hawaye bai daina sauka idonta ba, ya sauka daga motar without looking at her ya kulle, ta bi sa da kallo har taga ya shiga gidan cin abincin, ta fashe da matsanancin kuka tana waige waigen wajen cikin tashin hankali, babban wajen cin abinci ne sosai, ga mutane suna ta kai kawo a gurin, glass din motar ta fara bubbugawa da hannunta amma taga nobody is noticing her, ta fara kalle kallen cikin motar taga bunch of keys da ya ajiye ta dauka da sauri ta fara bubbuga glass din motar da shi da karfi, hakan ya ja attention din wani mutumi da ya fito daga cikin eatry din zai shiga motarsa dake kusa da inda Abdul yayi parking, ita dai bata fasa bubbuga glass din ba tana kuka sosai tana cewa don girman Allah ya taimaketa, da alama baya ganin cikin motar saboda tinted glass din, ya zaga ta gaban motar yana duba ciki, ta dinga kuka tana cewa don Allah ya taimaketa, ba ta damu ko yana jin abinda take cewa ba ko baya ji ita dai kawai ya taimaketa, mutumin ya tafi ya taho da wani security dake wajen, dai dai nan wani soja da ya fito eatry din zai shiga motarsa shi ma ya karasa gun motar kan kace me attention din jama'an dake gurin gaba daya ya dawo kan motar Abdul, Khaleesat bata fasa kukan da take ba duk da ta samu relieve ganin mutanen da suka zagaye motar wasu na kokarin mata magana suna haska cikin motar da fitila, mutane duk suka tsaya aka yi cirko cirko a kusa da motar, ita dai kuka me sauti kawai take kamar ranta zai fita, babu wanda bazai ce sato ta aka yi a lkcn ba, bayan wasu mintuna Abdul ya fito daga Eatry din rike da abinda ya siyo, yana zuwa inda yayi parking yaga jama'a jikin motar ya tsaya yana kallon ikon Allah, Security din dake tsaye wajen don yaga sanda Abdul yayi parking ya shiga eatry din, ya kalli sojan dake tsaye yace "Ga me motar nan ya fito" Da wani expression Abdul yace "What happened?" Sojan yace "Bude motar ta sauko Malam" Abdul yace "Ban gane in bude mota ta sauko ba, matata ce a ciki" Sojan yace "Ai bamu mu sa ka ba, mota kawai zaka bude ta sauko, ba wani abun tashin hankali bane ai" Nan jama'an wajen suka dinga cewa ya bude motar suna hayaniya, Abdul ya bude motarsa da Key din hannunsa daga inda yake tsaye, Khaleesat na jin alamar yayi unlocking din motar ta bude ta sauko da sauri tana kuka, Sojan ne ya fara mata magana yana nuna mata Abdul yace "Waye wannan?" Ta fashe da matsanancin kuka muryarta na rawa tace "Ni ban san shi ba" Kallonta Abdul ya dinga yi da mamaki babu ko kiftawa, hayaniya sosai mutanen wajen suka hau yi sojan na kokarin calming dinsu, Sai kuma ya sake kallon Khaleesat yace "Baki san shi ba? To garin yaya kika shiga motarsa?" Tana shessheka tace "Kawai dauko ni yayi a unguwanmu wallahi, ni ban san shi ba" Tuni matasa yan zaman kashe wandon dake wajen suka fusata suka zagaye Abdul suna dure duren ashar suna kokarin fara mazgarsa, gaban Eatry din ya cika da jama'a an zo kallo wasu har sun fara video, with the intervention of the soldier and the security men da wasu responsible mutanen dake wajen aka saka Abdul cikin motar Sojan don tsaf sun kula matasan za su yi aika aika ne a wajen, wannan opportunity din Khaleesat tayi using cikin dubara ta sulale cikin jama'ar wajen without letting anyone to notice her don gaba daya hankalin mutane ya koma kan Abdul a wajen, a haka ta samu ta tsallaka titi ko waigawa bata yi ta afka wani layi, nan ma tayi ta tafiya da sauri da sauri gabanta na faduwa, duk inda taga alamar hanya ce haka ta dinga bi ba tare da tasan inda zata ba, tafiyar kusan minti arba'in tayi a kafa hawaye na zuba idonta, ko sanin unguwan da take bata yi ba, daga karshe tsabar yanda ciwon kai ya matsa mata ga jiri dake ta kwasarta ya sa ta samu gaban wani gida ta zauna ta hade kanta da gwiwa tana shesshekan kuka, tana ta zaune for almost 10 mins wani mutumi dake ɗan nesa da ita yana zaune kofar gidansu ya mike ya nufota, don tun da ta shigo layin ta zauna ya ganta, sallama yayi mata ta dago kanta a tsorace, yace "Baiwar Allah lafiya dai ko?" Ta girgiza masa kai da kyar tana goge idonta tace "Bana jin dadi ne, kuma gida zan je" Yace "Ikon Allah, to ina ne gidan naku?" Without second thought tace "Hotoro" Yace "Hotoro? To bari in samo maki adaidaita sahu sai ya kai ki" Ta gyada masa kai cikin rawan murya tace "Nagode" Ya juya ya bar wajen, bayan wani minti goman sai gashi ya dawo cikin adaidaita sahu bayan yaje har bakin titi ya samo mata adaidaita sahun, ya sauko daga ciki yana kallonta yace "Toh ga adaidaita sahun na samo maki Hajiya" Tace "Nagode" Ta mike da kyar ta dafa adaidata sahun sannan ta shiga ciki, mutumin ya ciro wayarsa ya mika mata yana kallonta yace "Ki saka min lambarki sai inji ko kin isa gida lafiya" Ta girgiza masa kai a hankali tace "Matar aure ce" Mutumin yace "Ohh, na gane to, Allah ya tsare Hajiya, Allah ya baki lafiya, na biya sa kudinsa ba sai kin basa ba" Ta gyada masa kai tace "Nagode, Allah ya saka da alkhairi" yace "Ameen ya Allah" a haka mai adaidaita sahun ya bar layin. Har suka isa hotoro Khaleesat bata san sun iso ba, sai da me adaidaita sahu ya ankarar da ita, dai dai kofar gidan Gaje ta sa ya tsaya, ta sauka tayi masa godiya ta shige cikin gidan, nan gaban Gaje dake zaune tsakar gida ta zuba tana kuka kamar zata shide, Gaje tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, Khaleesah? Me ya faru? daga ina kike haka?" Da kyar Gaje ta lallashi Khaleesat tayi shiru bayan lokaci me tsayi, sannan ta fara gaya mata abinda ya faru, Gaje ta saki salati a rikice tace "Mun shiga uku mun lalace, yanzu gidan yan sanda suka tafi da Awdul din kenan?" Cikin kuka Khaleesat tace "Ban sani ba nima" Gaje tace "To kuwa zaman gidan nan bai kama ki ba Khaleesah, yasan bayan gidanku baki da inda zaki taho a kano da ya wuce gidana ko gidan Nenne, wannan fa ba karamin kess bane, Awdul na zuwa nan ya ganki sai ya zata da hadin bakina kika yi abinda kika yi, ya sa yan sanda su kulleni in shiga uku" Cikin kuka Khaleesat tace "Toh ya zanyi yanzu Baaba Gaje?" Gaje ta mike ta figi gyalenta a igiya tace "Ta shi mu je" Jikin Khaleesat na rawa ta mike ta bi Gaje suka fita daga gidan, da kafa suka tafi gidan kawar Aunty Farida da ake ce ma Maman Fu'ad, bayan sun shiga gidan Gaje tayi mata bayanin duk abinda ke faruwa, Maman Fu'ad tunda ta rike haɓa har gaje ta gama bada labari bata iya tace komai ba, Gaje tace "Don haka ki rufa mana asiri Sadiyah ta kwana gidanki zuwa gobe a ga abinda hali zai yi" Maman Fu'ad ta sauke ajiyar zuciya ta kalli Khaleesat, gwalo ido tayi ganin jinin da ya kwanta idonta tace "Me ya samu idonki?" A hankali Khaleesat tace "Marina yayi" Maman Fu'ad ta saki salati tace "Mari?? Har sai da jini ya kwanta maki a ido? ga lebenki ma a fashe? A'a gaskiya tsinanne ne wannan mutumi" Gaje ta rike haɓa tana kallon idon Khaleesat sai kuma ta fashe da kuka tace "Yanzu wannan har mijin aure ne in ba don Ali ya cuceki ba, dubi fa tafin hannunsa a fuskarta?" Maman Fu'ad tace "Da kyar ma in baya shaye shaye wannan, gaskiya duk yanda za ayi a raba auren nan domin ceto yarinyar nan daga halaka, yanxun nan zan kira farida kuwa" Gaje ta rufe bakinta da sauri tace "Ki kirata kice mata me? Rufa mana asiri ba wanda yasan tana nan, ina me tabbatar maki kilan yanzu an tafi da Awdul din police station, kinga ai dole ya kai yan sandan gidansu Khaleesat don wanke kansa su tabbatar matarsa ce, in kuma yayi haka ai za a bazama nemanta ne a gari" Maman Fu'ad tace "Ba komai Gaje, ki tafi kawai ki kyaleta a nan kar su je can gidan naki baki nan" Gaje ta mike da sauri tace "Don Allah ki bata ruwan zafi in kina da shi tayi wanka" Maman Fu'ad tace "Kar ki ji komai Gaje" A haka Gaje ta bar gidan, yanda Khaleesat taga daren jiya wannan daren ma haka ta gansa, ga ciwon kai, ga ciwon ido, ga zazzabi duk ta rasa inda zata sa kanta taji dadi, she don't even know who to speak to at this point. Washegari karfe tara Gaje ta shigo gidan, tun daga bakin kofa ta fara ba Maman Fu'ad labarin abinda ke faruwa tace "Sadiyah wajen karfe goma suka zo nemanta a gidana wallahi jiya har da shi Awdul din, ni dai jikina sai rawa yake don tare yake da yan sanda, yanxu haka daga can Mariri nake, uwarta na can hankalinta a tashe ko bacci bata yi ba sai koke koke, uban kuma yace da hadin bakin uwar Khaleesat ta gudu, babu kalan tijaran da Awdul bai yi ba jiya, keee abun dai babu kyau, ni dai hankalina ya tashi sosai, ina tsoron kar a gano ni na ajiyeta Awdul ya hadani da hukuma, shine na zo kawai ta shirya tayi hakuri ta koma gida duk abinda Allah yayi dai dai ne" Khaleesat dake jin duk abinda Gaje ke cewa ta fashe da matsanancin kuka tace "Don girman Allah kar ki ce masu ina nan Baaba Gaje, wallahi har duka zai iya min" Maman Fu'ad dai na tsaye da atamfar mutane da zata yanka ta hau kan keke ta kasa cewa komai sai zazzare ido take, ita ma tsoro take kar daga karshe ace ai a gidanta aka boye Khaleesat, ta ina zata fara ma Baban Fu'ad bayani in aka zo tafiya da ita gashi bai gari, Gaje tace "Toh ya kike so inyi Khaleesah, Awdul fa ya maida maganar nan babban magana wallahi, wai kin tozartasa a cikin mutane jiya kin sa an tafi caji opis da shi, ba ki da kowa da zai tsaya maki a lamarin nan sai Allah, Malam Ali na can kamar zai haukace shi ma ya saka uwarki a gaba sai ta fito dake" Khaleesat ta hade kanta da gwiwa tana shesshekan kukan, Gaje ta make hannun Fu'ad dake ta jan yakunannen gyalenta sannan ta ja kujeran tsugunno ta zauna ta rafka uban tagumi tace "Ni dai ban san kuma yanda zan maki ba Khaleesah, ina talaka da ni Awdul yasa a daureni wa zai cece ni, sai ma Kinga kallon da yake min jiya kamar bai yarda da ni ba" Khaleesat ta dago da kyar tana kallon Baaba Gaje hawaye na sauka idonta, Baaba Gaje dai zai zazzare ido take tace "Ni ban ma yarda bai sa CID unguwar nan su kula da shige da fice na ba, yanxu hka sai da na zaga kamar zan je Yan kaba sannan na taho gidan nan" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "Don Allah Baaba Gaje ki min alfarman dauko min jakana a can gidanmu" Baaba Gaje ta gwalo ido tace "Wani jakar?" Khaleesat tace "Karamin jakata, akwai wayata a ciki zanyi amfani da shi" Baaba Gaje tace "Um um Khaleesat, ta yaya zan dauko jaka ana gani na da rana tsaka?" Khaleesat ta girgiza mata kai tace "Karamin jaka ne bai da girma, ko a gyalenki zaki iya boyewa don girman Allah ki rufa min asiri ki taimakeni Baba Gaje ki dauko min, har da kudi cikin jakan, zaki ga jakar kusa da akwatina a gefen katifar Umman mu" Maman Fu'ad dai sai baza ido take taji Khaleesat zata bar gidanta amma shiru bata ji ba, can dai tace "To ke ina kika nufa daga gidan nan yanzu?" Khaleesat na share hawayenta a hankali tace "Idan ta dauko min jakar zan san inda zan je in sha Allah" Maman Fu'ad ta sauke boyayyen ajiyar zuciya, faridan ma bazata kira ba kar daga karshe a gane ita ta ajiye Khaleesat a gidanta ta shiga uku, Da kyar Baba Gaje ta yarda zuwa Mariri dauko jakan don duk a tsorace take, shi ma sai da Maman Fu'ad ta saka baki tunda taji ance in dai aka dauko jaka to za a bar gidanta, shi sa tayi ta lallaba Gaje taje Mariri dauko jakar, bayan kusan awa daya sai ga Gaje da jakar ta kudundunosa a gyalenta, Khaleesat ta amsa jakar ta bude ta ciro wayar Jay dake ciki, ta ga dollars din da ya bata suna ciki har sannan, Call log ta shiga sai kuma ta kalli Maman Fu'ad tace "Don Allah ki ara min wayarki bani da Sim card a nawa" Maman Fu'ad tace "Ai ko babu kati, tunda ga wayar Gaje bari in bada dari biyu a siyo sai ki saka a nata wayar ki kira" Nan duk dubara Maman Fu'ad tayi kar a ga Khaleesat tayi kira da wayarta idan bincike yayi bincike, Gaje ta mika ma Khaleesat wayarta ta fita ta amso mata katin dari biyun da Maman Fu'ad ta dauko ta bada, Khaleesat na saka katin ta fara dialing number Jay, ta kira yafi sau biyar sai dai kiran ya dawo mata alamar bai je ba, bata hakura ba still tayi ta kira baya shiga bata san ko katin ne yayi kadan ba kuma Number sa na Nigeria yake using a can din ma, wasu sabbin hawayen suka fara sauka idonta ta sake shiga call log din wayar tana scrolling slowly, number AJ ta gani shi ma Nigeria Line dinsa, ta ɗan yi jim tana kallon number, sai kuma tayi dialing tana share hawayen dake zuba idonta, ringing ya fara yi har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa, sai da ya kusa katsewa sannan yayi picking, muryarta na rawa tace "Good Afternoon" Shiru yayi, kafin yace "Wacece?" Ta sauke idonta tace "Ni ce" Yace "Ke wa?" Da kyar tace "Plss i want to speak to you" Kawai ta fashe da kuka uncontrollably, shiru yayi for almost 15 seconds, can yace "What happened?" Tana kuka tace "I need to speak to you pls" Ya kara yin wani shirun, can yace "Where are you?" Tace "Hotoro" He still kept quiet for some seconds kafin yace "Address" Katse wayar Khaleesat tayi ta tambayi Maman Fu'ad address din unguwan, Maman Fu'ad ta gaya mata sannan ta tura masa ta message, Gaje dake zaune kan kujera tace "Wanene wannan din da kika kira?" Ita dai Khaleesat tayi shiru wasu hawayen na taruwa idonta, Baba Gaje tace "Gashi idon naki sai kara ja yake yi, wallahi makantar da ke kawai yayi niyyar yi matsiyacin nan" Bayan kusan 35 mins wayar Gaje ya fara ring, Gaje ta mika ma Khaleesat da sauri tace "Ko wanda kika kira ne?" Khaleesat ta amsa tana kallon wayar taga AJ ne ke kira, dagawa tayi yace "I am outside" Khaleesat ta ajiye wayar sannan ta kalli Maman Fu'ad tace "Aunty don Allah kina da Nikab?" Maman Fu'ad tace "Yaushe rabona da Nikab, bani da shi yanzu kam" Khaleesat ta mike tana rike da handbag dinta da wayar Jay ta fita daga gidan, not far away from the house yayi parking, yana jingine jikin motar ya rungume hannunsa looking at a different direction, tana tafiya a hankali ta nufesa tana kallonsa, tana isowa kusa da shi ya juya jin Footstep, ya gyara tsayuwarsa ya dinga kallon idonta babu ko kiftawa, she tried her best na ganin bata fashe da kukan da ya taho mata ba amma ta kasa daurewa ta hade kanta da jikin motar ta fara kuka har da shessheka. *Thanks for ur patient, and thank you all for checking up on me* *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* kema kına cikin matan da kullum sedai su bawa miji abinci?? Ko kema kullum lunchbox na yaranki shinkafa ce? Sarari yummy treat ta sauqaqamiki Frozen snacks are always available a wajenmu Samosa Spring rolls Meatpie ( to fry) Duk yawan yanda kikeso hajiyata xaki samu Ga kuma sallah ta matso This year kibar wanna cincin din ki canjamai da samosa, Cup cake, Spring rolls, Doughnuts, Meat pie, sannan akwai frozen, fried ko kuma samosa wraps din @2800👌🏻 Kawai fillings dinki xaki hada ki nade ki soya Nation wide delivery 09014996620 https://wa.me/message/VBRYP3DYFYNME1 HALYSAAH 30 Ajay bai ce mata komai ba sai da tayi kukan me isarta don kanta tayi shiru, tana share idonta ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake har sannan, Calmly yace "He did all this to you?" Kai ta gyada masa wasu hawayen na taruwa idonta, yayi shiru for a while kamar me nazari, sai kuma yace "Ɗan kano ne?" Nan ma ta gyada masa kai, yace "A ina yake a kano?" Muryarta na rawa tace "I don't really know" Zai yi magana Baba Gaje ta leko kofar gidan kamar munafuka tana zazzare ido, Ajay ya ɗan sauke kansa ya gaisheta bayan sun hada ido da ita, fitowa tayi da sauri tana kalle kallen Unguwan tace "Lafiya lau ɗan nan, wallahi yarinyar nan tana cikin mummunan masifa, bata da kowa sai Allah, ta dawo daga turai ta tarar an daura mata aure da lafcecen yaron nan ɗan iska, dama kuma duk mun san ɗan iska ne muke kauda kai tunda bamu da yanda za mu yi, ashe bai ma yi shawara da ita ba kansa tsaye ya taho ya samu iyayen da ya raina suka daura aure shekaranjiya, to tunda tace bata son auren in dai ba tsinannen mutumi ba ai sai ya kyaleta ga mata kaca kaca a duniya, wani mugun kuduri ne a ransa haka da yasa aka daura auren a gaggauce ko shiri babu? dubi fa abinda ya mata a fuska daga ya dannata a mota taki bin sa, yanxu haka duk ya baza CID a unguwan nan ana nemanta, sai kaga tijaran da yaje ya ma iyayen nata jiya da daddare, shi sa ka gan mu duk a tsorace" Tun da ta fara magana Ajay ke kallonta ko kiftawa baya yi, mamaki ne sosai kwance a fuskarsa, can ya kalli Khaleesat dake kuka kamar Baaba Gaje na dada tunzurata, ya sake kallon Gaje yace "Aure kuma Mama?" Gaje tace "Wallahi da gantalallun igiyoyinsa har uku a kanta yanxu haka, tun jiya ta gudo nan bayan ta samu ta tsere da kyar daga hannunsa" Gaje ta fashe da kuka tana matsar kwalla da gyalenta tace "Wallahi bata da kowa sai Allah, iyayen basu da bakin magana, basu da ta cewa, ni kuma ba kowa bace makociyarsu ce mun yi zaman Mariri tare kuma ni talaka ce, ni ko taimaka mata ne kayi ka kai ta wajen masu kare hakkin ɗan Adam ta kai masu kukanta su kwato mata hakkinta da ake neman tauyewa" Har sannan Ajay ya kasa cewa komai, can ya bude gaban motarsa yana kallon Khaleesat, Baaba Gaje ta fara tura ta ciki tace "Maza shiga ku je ya kai ki ofishinsu, in ma rike ki za su yi su rikeki ki zauna har sai sun bi maki hakkin ki, amma kar ki ce nasan komai, kar ma ki saka ni a maganar" Khaleesat dai kuka kawai take ta shiga motar, Baba Gaje ta amshi wayarta dake hannunta ta kulle motar gbamm tace "Maza ku je" Ajay dai ya zaga ya bude driver seat ya shiga, Da sauri Baaba Gaje ta koma gate din Maman Fu'ad kamar ba daga kusa da motar ta taho ba, ta makale tana kallonsu har suka fita daga layin, driving kawai AJ yake idonsa a kan titi, gaba daya he look speechlesss, tunda ya kalleta sau daya bai sake kallonta ba, ita dai Khaleesat ta rufe fuskarta da Hijab dinta saboda hasken rana dake damun idonta kuma tana tsoron kar ace su hadu da Abdul dan motar babu Tint, har sannan bata daina kukan tashin hankalin da take ba, after driving for 20 mins AJ ya kalli wayarsa dake vibrate, Number Jay ne ke kiransa, hakan ya sa ya rage tafiyar da yake ya gangara gefen titi yayi parking sannan ya dau wayar yayi picking ya kai kunne a hankali yace "Jay" Khaleesat ta zame hijab dinta daga fuska jin sunan da ya kira ta juya ta kallesa, Calmly taji yace "I am cool" tambayarsa Jay yayi ko ya bar Kano, AJ yace "Am still around, when are you leaving Maryland?" After few seconds AJ yace "Alright, we will talk later" Daga haka ya katse wayar ya ajiye ya jinginar da kansa jikin kujerar motar ya kafe titi da ido for almost 2 mins, can ya sake daukar wayarsa don duba available flight to Abuja ranan, yaga jirgin karfe uku kuma saura just few seats, National ID card dinta da passport dake motarsa tun ranan da suka dawo US da drivern su na Lagos ya amsa a wajenta don mata booking ticket to kano, ticket ya siya mata immediately na zuwa Abuja sannan ya ajiye wayar, Aunty na nan gidansu na kano sun zo biki shi sa ma bazai fara kai ta can gidan ba, juyawa Khaleesat tayi da kyar ta kallesa tana dafe kanta pleadingly tace "Kanwar Ummata tana Lagos, don girman Allah ka taimakeni i want to go to her plss" Shi dai kallonta kawai yake, Calmly yace "Where in Lagos?" Tace "Zan kira in tambayeta, amma bani da numberta ne" Ya ga alamar gaba daya she is confuse and in fear, yace "Ta yaya zaki kirata baki da numberta?" Wayarsa ta dauka da sauri ta shiga call logs dinsa tana duba number Baaba Gaje, dialing tayi yana fara ring Baaba Gaje ta daga, da sauri Khaleesat tace "Baaba Gaje don Allah number Aunty Farida za a duba a wayarki sai a turo ta wannan layin" Baba Gaje tace "Har kun je wajen kare hakkin ɗan Adam din?" Khaleesat tace "Ki dai turo min don Allah yanxu Baaba" Baaba Gaje tace "Toh bari in je makota kin san ban san kan wayar ba ai" Khaleesat ta gyada kai da sauri tace "To ina jira" Katse wayar tayi ta jinginar da kanta jikin kujera tana sauke numfashi, wani dishi dishi take gani tsabar kuka, Shi dai Ajay idonsa na kan titi alamar dai kansa ya gama kullewa, ya kalli agogon wrist dinsa yaga karfe biyu ya gota, driving motar ya ci gaba da yi da tunani iri iri a ransa ya nufi wani eatry ya sauka ya shiga ciki, Khaleesat ta dinga bin haraban wajen da kallo sai kuma ta rufe fuskarta da Hijab dinta da sauri zuciyarta na bugawa, incident din jiya ne kawai ke dawo mata a kai as if she is hallucinating, sai taga kamar yanzu incident din ke faruwa yanda Abdul yayi parking ya fita daga mota ya shiga eatry, kan kace me ko ina na jikinta ya fara rawa taji kamar numfashinta zai dauke, ba a dau lokaci ba Ajay ya fito daga gidan cin abincin da leda a hannunsa, yana shiga motar ya ajiye ledan da sauri yana kallonta yace "Me ya faru??" Ta dago kanta hawaye caba caba a fuskarta, sai kuma ta kamo hannunsa gam tace "I just want to leave here plss, don Allah mu bar nan" Gaba daya ta dawo kamar warce ta zauce, ya fara bin area din da kallo tunaninsa ko Abdul din ta gani, can ya sake kallonta bayan ya zauna cikin motar, cikin nutsuwa yace "Look, stay calm.... You are safe" Ya gyara mata kujeran motar a hankali ta yanda zata ɗan kwanta yana kallonta, sai da ya jira for almost 10 mins yaga ta ɗan nutsu tana sauke numfashi a hankali, lkci lkci yake kallon agogonsa saboda flight din da yayi booking, after a while ya ɗan duba fuskarta yaga kamar ta fara bacci, tada motar yayi ya bar wajen, still sai da ya kara tsayawa a pharmacy ya siya mata magunguna, ko kashe motar bai yi ba don kar ta ma san yayi parking, har yaje ya dawo kuma bacci take, ya ja motar ya dau hanyar airport hoping jirgin bazai tashi kafin su isa ba, suna isa airport din bayan yayi parking yaga saura minti sha biyar kawai jirgin ya tashi kamar yanda suka sa a ticket, tapping din kujeran motar yayi gently don har lkcn bacci Khaleesat take, a tsorace ta farka kamar yanda tayi daxu a eatry tana ganinsa kuma tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya, ya bude ledan abincin da ya siya ya ciro mata takeaway din ya bata yace "Take a little before ur flight..." Ba musu ta amshi abincin tana kallonsa a hankali tace "Lagos din zan je?" Yace "In kin je zaki gani" Sai da ya hade mata rai sannan ta ci abincin cokali uku da kyar tana hadiyewa kamar magani, ya bude drugs dinta ya bata ta amsa ta sha da ruwan goran hannunta, without looking at her ya mika mata wayarsa yace "Saka min number mutumin nan" Zaro ido tayi tana kallonsa, yace "Ko bakya ji na ne?" Kamar zata yi kuka tace "Kiransa zaka yi?" Yace "Amsa ki sa min number sa nace" Hannunta na rawa ta amshi wayar ta saka masa lambar Abdul don tana da shi a kanta, ya amshi wayar yana kallon number sannan ya ajiye wayar yace "Dama an mashi alkawarin aurenki ne?" Ta sunkuyar da kanta cikin sanyin murya tace "Um, tun shekara hudu da suka wuce" Shiru Ajay yayi yana kallonta, but because of how cautious he is with time kar tayi missing flight dinta kawai ya ciro Eye drop din da ya siya mata ya mika mata ta diga a idonta, tsoro ya sa ta kasa digawa don bata san wani kalan azaba zata ji ba, daga karshe ya fixge eye drop din babu yabo babu fallasa ya diga mata a cikin idon, tuni ya sauka daga motar yana jiran in ta gama kururuwan da take ta sauko, daga karshe ta sauko daga cikin motar tana rufe idon da Hijab dinta, dayan wayarsa ya mika mata wanda ticket dinta ke ciki, daga ita sai handbag din ta da wayarsa ta nufi cikin airport din tana waige waige kamar iska zai kadeta ta fadi, kana ganinta kasan ba dai dai ta ke ba, she is traumatized and stressed, tsoron Abdul kuma ya gama shigarta sosai, shi dai yana tsaye jikin motarsa yana kallonta har ya ga shigarta cikin airport din, komawa cikin motarsa yayi yana duba full name din Abdul ta true caller, wani number yayi dialing yana fara ring aka daga yace "Zan turo maka wata number yanxu, ina son kasa a bincika min location dinsa a cikin garin kano, i will be waiting for feedback" Bayan ya katse wayar ya ajiye ya jinginar da kansa da kujeran motar, yana nan zaune har bayan 20 mins just to be sure bata yi missing flight dinta ba kafin ya bar airport din, Khaleesat ta dinga bin cikin jirgin da kallo kamar idanuwanta za su fito jin anyi announcing za su tashi zuwa garin Abuja, Abuja kuma? Ita wa ta sani a Abuja? Hawaye ne ya cika idonta ta dinga waige waigen cikin jirgin, me yasa ya mata booking ticket din Abuja. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 31 Khaleesat na zaune hall din da jama'a ke jiran Luggages dinsu a Arrival, duk da bata da kayan da zata jira amma rashin sanin inda ta nufa yasa ta zauna wajen tana bin kowa da kallo, tun 15 mins ago jirginsu ya sauka Abuja, daurewa kawai take don wani bacci take ji tare da gajiya, vibration taji a jakarta dake cinyarta alamar ana kiran waya, a hankali ta bude jakar ta ciro wayar da AJ ya bata tana kallon screen din, har ya katse bata daga ba don number kawai ta gani ba ayi saving ba bata san ko ta daga ba ko kar ta daga, kiran wayar da ake ta yi continuously ne yasa tayi picking tayi shiru tana sauraron me magana taji namiji ne, ta amsa sallaman da yayi mata, sannan yayi introducing kansa ya sanar mata shi ne ya zo daukanta Airport, a hankali Khaleesat tace "Ohk" Mikewa tayi ta fita daga Arrival din tana kalle kallen inda yace mata yake a Airport din, sai ga shi ya nufota bayan ya gane ita ya zo dauka, gaisheta yayi da ladabi yace "Babu kaya ko Hajiya?" Khaleesat ta gyada masa kai kawai, yace "Bismillah, Motar na can nayi parking" Tana biye da shi suka isa inda motar yake, ya bude mata back seat ta shiga ya kulle sannan ya zaga ya shiga driver seat, Ita dai Khaleesat ji tayi kawai yana sanar mata sun iso, bata san for how long suka yi tafiyar ba don bacci ne ya dauketa throughout the journey, gyara zama tayi tana kalle kallen compound din gidan da suke ciki, ta kalli Drivern da ya bude mata back seat, ta sauko a hankali tace "Nagode" Gida ne babba irin na zamani, tana biye da shi ya kai ta har zuwa Entrance din shiga babban parlon gidan ya danna bell, ba a dau lokaci ba aka bude kofar wata budurwa ce warce bazata wuce ta ba ta gani tsaye, da ladabi Drivern yace "Bakuwar da na dauko Airport ce Hajiya" Yarinyar ta ɗan yi murmushi ta koma gefe tana kallon Khaleesat tace "Sannu da zuwa sister, come in" Khaleesat ta shiga parlon yarinyar ta kullo kofar tana nuna mata kujera ta zauna, bayan Khaleesat ta zauna yarinyar na kallonta tace "I am Inteesar" Khaleesat ta daga idanuwanta ta kalleta tace "Sunana Khaleesat" Yarinyar tace "Welcome Khaleesat, bari in ma Ammin mu magana" Daga haka ta juya ta bar parlon, after a while sai ga ta sun shigo parlon da wata dattijuwa that is in her middle 50, zamowa kasa Khaleesat tayi a hankali tana gaisheta, da fara'a matar da ake kira da Ammi ta dagota tace "A'a, koma kiyi zamanki kan kujera diyata" Khaleesat ta koma ta zauna kan kujeran, Matar ta zauna kusa da ita tace "Sannu da zuwa, ya hanya?" Khaleesat tace "Alhmdlh, ina yini" Ammi tace "Lafiya lau, ya kika baro mutan gidan?" Khaleesat tace "Suna lafiya lau" Ammi tace "Ai na zata tare da Yariman ku ke, ashe ke kadai ce" Ita dai Khaleesat ta sunkuyar da kanta tayi shiru tana wasa da gefen hijab dinta, Ammi ta kalli Inteesar tace "Inteesar ki kai ta daki ta huta" Inteesar tace "Ohk" Tare suka tafi dakin Khaleesat na biye da ita, Ammi ta bi su da kallo. Wajen karfe takwas na dare Khaleesat na zaune daki tare da Inteesar da ta mayar da ita Television, ita dai a hankali take cin fruit salad din gabanta, tun zuwanta gidan in dai ta kalli Inteesar by mistake zata ga kallonta kawai take, da sun hada ido kuma sai Inteesar ta mata murmushi, Khaleesat wasn't bothered da kallon don farkon haduwarsu da Sophie haka ita ma take mata, tayi ta kallonta a makaranta ko gajiya bata yi kuma da sun hada ido sai ta mata murmushi, bayan sun zama best of friends ne Sophie ke gaya mata she is soo beautiful shi yasa bata gajiya da kallonta, sai bayan sun zama kawaye Sophie ta dena mata maganar kyanta, kuma dama da wuya taje waje bata ga mutane na kallonta ba, ba maza ba hatta yan uwanta mata haka suke kallonta, muryar Inteesar taji a hankali tace "You are Beautiful Khaleesat" Khaleesat ta ɗan kalleta sai kuma ta mayar mata da murmushin da take mata kawai, Inteesar tace "Sosai fa" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "And you too Inteesar" Inteesar tayi dariya tace "A'a gaskiya ba kamarki ba, ni dai ina son mu zama frnds in baza ki damu ba, Ya Prince yace gobe zaki tafi Lagos da safe, don Allah ki bani numberki mu dinga zumunci ta waya, probably baza ki sake dawowa gidanmu ba" Sosai Khaleesat taji wani relieve ya zo mata bayan taji Inteesar tace zata tafi Lagos da safe, dama gaba daya hankalinta yayi gun kanwar Ummanta, Allah ya gani daurewa kawai take amma ita kadai tasan me take ji both mentally and physically, tana cikin tashin hankali sosai but she is trying her best to act normal, Khaleesat tace "Ohk amma nayi misplacing wayana ban yi welcome back, idan nayi zan amshi lambarki gun sa" Inteesar tace "Ohk to ba damuwa, amma zaki dade a lagos ne in kin je?" Khaleesat tace "Zan ɗan yi kwana biyu a can in sha Allah" Inteesar tace "Akwai sisterna dake aure can, idan baza su dawo gida for New year ba in sha Allah zan je Lagos din so that i will meet with you there" Murmushi Khaleesat tayi tace "Toh shikenan Allah ya kai mu lafiya" Inteesar ta tashi ta bude press ta dauko mata kayan baccinta don dakinta ta kawo Khaleesat, bayan ta ajiye kayan gefen gado tace "You can change to this idan kinyi wanka, i will be back later" Khaleesat tace "Alright, thank you so much" Bayan few minutes da fitan Inteesar Khaleesat ta tashi a hankali ta tafi bandaki, da ta tuna auren Abdul dake kanta tashin hankalinta ninkuwa yake, sai da ta ci kukanta me isarta sannan tayi wanka ta fito daga bandakin, ta gama saka kayan da Inteesar ta bata kenan tana kokarin daure gashinta sai ga ta ta shigo dakin, Inteesar ta wara ido tace "Waow is all that ur hair Khaleesat?" Khaleesat dai ta mata murmushin karfin hali tana ci gaba da daure gashinta, Inteesar that was looking at the hair with fascination tace "Bari in baki Hair net" Hair net dinta ta dauko ta ba Khaleesat, Khaleesat ta amsa tace "Nagode sosai" Washegari karfe tara da rabi na safe Khaleesat ta gama shiryawa tana jiran Drivern gidan, kayan Inteesar ne jikinta da yake yanayin jikinsu daya babu me cewa ba kayanta bane, tana zaune gefen gadon Inteesar duk da Hijab ne har kasa jikinta amma sanyi take ji sosai, ga AC dake dakin a kashe amma she is shivering, tun da ta tashi da asuba tasan she is not feeling okay, breakfast din ma da kyar ta sha shayi kawai, ko irish din bata ci ba balle bread, she is trying all possible best to look alright don kar ayi cancelling tafiyarta zuwa lagos yau, Mai aikin gidan ce ta Kwankwasa kofa ta sanar mata driver yana jiran ta, Khaleesat ta tashi da kyar ta dau handbag dinta ta fita daga dakin zuwa parlor, nan ta tarar da Ammi zaune, Khaleesat ta karasa ta duka kusa da ita tana mata godiya don sosai suka sake mata kamar da can sun taba saninta, daga karshe dai Inteesar ta bi su har Airport don rakiya, haka kawai jininta ya hadu da Khaleesat, ita kanta Khaleesat don bata cikin nutsuwarta ne amma she so much appreciate Inteesar's care toward her, a haka dai suka rabu kamar sun jima da sanin juna, Khaleesat ta shiga cikin airport din ta amshi boarding pass dinta don Ajay ya tura mata ticket ta Email din wayar da ya bata hade da hoton National ID dinta da yayi snapping tun karfe bakwai na safe, bayan ta amshi boarding pass dinta ta nufi Departure Lounge. Karfe sha biyu saura suka sauka garin Lagos, Khaleesat ta sauka a jirgi da taimakon wata mata don zazzabi ne sosai ya rufeta but she is still pretending to be fine, a haka suka fito Airport din daga Arrival matar na tambayarta za a zo daukanta ne ko Taxi xata hau, Kafin Khaleesat tace komai ta hango wani kamar AJ tsaye jikin wata mota yana danna wayarsa, sai da ta kifta ido ta bude to be sure he is the one she is seeing, ta kalli matar kusa da ita da kyar ta sanar mata yayanta ya zo daukanta, a haka suka rabu da matar, Khaleesat ta nufi inda ta hango Ajay, sae da ta iso kusa da motar ya daga kai ya kalleta, ta sunkuyar da kai a hankali tace "Ina yini" Calmly yace "Ina wayar da na baki?" Jakar hannunta ta nuna masa tace "Yana ciki, na sa silent ne" Driver seat ya bude ya shiga sannan ya bude mata daya side din motar, zagawa tayi ta shiga ta jinginar da kanta ta lumshe ido, ya tada motar suka bar Airport din, Google map yayi ta using after almost 45 mins ride Khaleesat ta fara gane inda za su, amma kuma sae ko ina yayi mata sabo a area din ko don she is not stabilize ne bata dai sani ba, ta juya ta kallesa shi dai driving dinsa kawai yake with the assistant of his google map, at last suka shigo wani unguwa yayi parking ya dau wayarsa yayi dialing number, muryar Aunty Farida taji bayan anyi picking, Khaleesat taji kamar an yaye mata ƙaso tamanin cikin damuwarta jin muryar kanwar Ummanta, bayan few minutes sae ga ta ta fito daga cikin wani gate, tun da AJ ya hangota daga nesa ya fahimci da ita yake waya don kana ganinta ka ga Khaleesat, yayi driving din motar har zuwa dai dai kofar gidan da ta fito, yana parking Khaleesat ta bude motar da sauri ta sauka da sauran last strength dinta ta nufi Aunty Farida ta fada jikita, Aunty Farida ta rikota da sauri kafin ta kai kasa, wata makociyarta ce ta taimaka mata suka rike Khaleesat suka shiga da ita cikin gidan, shi dai AJ na tsaye kusa da motarsa yana kallonsu har suka shiga ciki, sai kuma ya jingina da motarsa yana kallon yara dake wasa few houses away, wayarsa ya ciro jin yana ringing ganin me kiransa ya daga yace "Ya ake ciki?" Daga daya bangaren mutumin yace "Ranka shi dade sai daxu ya kunna wayar tasa, an kuma duba location din nasa yana cikin garin Abuja yanxu haka" AJ yayi shiru kafin yace "Ohk, i will get back to you nagode" Daga haka ya katse wayar ya mayar aljihunsa, sai ga Aunty Farida ta fito daga cikin gidan, yayi ƙasa da kansa ya gaisheta, ta amsa cikin sanyin murya tace "Sannu da kokari fa, Allah ya saka da alkhairi, mu shiga ciki sai mu yi magana ko" Bai ce mata komai ba ya bi bayanta zuwa cikin compound din, Compound ne me dauke da apartment uku self contain each, AJ ya tsaya daga balcony din apartment din bai shiga ba har sai da Aunty Farida ta kara lekowo ta masa magana sannan ya cire takalmansa ya shiga parlon ya zauna saman kujera yana kallon Khaleesat da ta juya baya kan 3 seater din da take kwance, Aunty Farida ta tafi kitchen dauko masa ruwa, ya ciro wayarsa yana dannawa absentmindedly, Sai ga Aunty Farida ta fito kitchen ta ajiye masa ruwan a kusa da shi sannan ta zauna, da damuwa tace "Sannu da kokari Junaid, Allah ya saka da alkhairi, mun gode sosai" AJ ya daga kansa ya kalleta yace "Amma dai kince bai san inda kike a lagos ba ko Aunty?" Aunty Farida tace "Gaskiya bai san nan gidan ba, tsohon gidan da na baro ne dai ya sani, shi ma wani lokaci ne da ta zo Lagos dubani bani da lafiya, ta zo da kwana uku sai ga shi shima ya zo, to yau wata hudu kenan da barina wancan Unguwan na dawo nan" Ajay dai yayi shiru idonsa a kasa, Aunty Farida tace "Kuma ba unguwa daya bane, shi wancan Unguwan da na baro a Ojota ne, daga can zuwa nan ma tafiya ce me zaman kansa, ba kuma wanda yasan nan na dawo" Ajay yace "Toh shikenan, jikinta da zafi ne?" Aunty Farida tace "Ehh na ji da zafi sosai gaskiya, makociyata da ta rike min ita muka shigo yanzu nurse ce, tace zata rubuta min magunguna in siyo mata" Ajay yace "Ohk, bari zan fita yanzu sai in siyo magunguna da allurai da drip ayi mata karin ruwa" Aunty Farida tace "To Allah ya saka da alkhairi, amma baka sha ko ruwa ba Junaid" Ajay ya ɗan yi murmushi yace "Bari in je in dawo dai" A haka ya fita daga parlon ya tafi pharmacy ya harhado mata magunguna da drip da allurai. Wata mace ce warce bazata wuce shekaru hamsin da bakwai ba zaune wani kantamemen parlor cikin isa, mai aikinta na duke gabanta tana yanke mata kumbar kafafuwanta, cikin fada take cewa "Banda ma naci irin naka dama ina kai ina er matsiyata? Er talakawa? Wanda cin yau da kyar na gobe da kyar, ai kai ba class dinta bane ta ko ina, you just stoop ur self so low Abdul, babu wanda ya isa da kai babu wanda zai baka shawara ka dauka, na rasa irin wannan taurin kai naka, tun asali i am against you marrying that poor wretched girl, kuma har gobe ba wai nayi na'am bane kawai bani da yanda zanyi da kai ne Babana, baka jin maganata ko na ubanka balle na yayarka, yanxu ina amfanin kaskantar da kai da matsiyaciyar tayi cikin talakawa yan uwanta a gaban gidan cin abinci, abu har police station, da mutuncinka da iliminka a maka haka? In zaka dau shawarata yanzu gwara kawai ka saketa case ya dawo sabo fil, uban me zaka ci da ita kuma bayan wannan abun da ta maka a idon duniya? Idan yarinya kake so ni duk inda zan shiga zan je in samar maka yarinya karama da ta fi ta komai kuma er gidan arziki ba tsiya ba, kai ko Nijar din ne ma ni sai in shirya inje da kaina in samo maka wata buzuwar er gidan arziki ba talakawa ba, kai ga ma er wata kawata shuwa Arab yanda kaga ita wannan da makale ma ita ma haka take tass da ita, ga gashi, sannan su ba talakawa bane" Wata matashiya ce er shekara 39 dake zaune parlon ita ma ta juya da sauri ta kalli warce ke magana tace "Momy ban gane abinda kike nufi ba? Wai nufinki ya saketa kenan?" A fusace Momyn tace "Toh uban me zai ci da ita idan bai saketa ba Meema? Er talakawa ce fa, a kanta aka fara kyau a duniya ne da bazai rabu da ita ba?" Warce ta kira da Meema ta girgiza kai tace "A'a wallahi Momy, ai idan ya rabu da ita yanzu ma ita da iyayenta ne suka ci riba, duk uban hidimar da yayi mata sai kice ya saketa daga karshe ko tausayinsa ba ki ji ba Momy? Ae wallahi bata isa ya saketa ba, ko don mu kuntata mata yanda ta kuntata ma Abdul baza mu yi fatan ya saketa ba, dole sai ta shigo gidan nan, balle shi ba mahaukaci bane da zae saketan, yarinyar da ya tura har America karatu duk don dai ta zama presentable cikin mutane kar a mana dariya daga karshe ta saka masa da wannan walakanci da tijara haka?" Abdul dake zaune parlon shi ma duk yana sauraronsu ya mike yace "In har aka ga na saketa to bana numfashi ne a duniya, kuma duk inda ma take zata dawo hannuna nan ba da jimawa ba kuwa, a nan ne zata gwammaci bata taɓa sanina a rayuwarta ba, i will make life a living hell for her" Momy ta tabe baki tace "Shi dama talaka ai bai gaji abun arziki ba, shi yasa babu ruwana da su ko da wasa, hanyar jirgi daban ta mota daban, kai ne da jajibe jajibenka kasa ubanka ya tafka asaran kusan miliyan dari akan matsiyaciyar yarinyar nan" Tuni Abdul ya fice daga parlon, Meema na kallon uwarsu tace "Ai ki ma dena maganar asaran miliyan dari Momy, don yanxu babu wannan zancen asaran nake ji" Momy dai ta tabe baki tana kallon me aikinta tace "Ke kar fa ki yanka ni inyi mugun bata maki rai yanzu, ya zaki dinga gaftare min naman yatsu" Hakuri mai aikin ta hau bata. Wajen karfe biyar na yamma Khaleesat ta ɗan kishingida a 3 seater, hannunta rike da bowl din pepper soup din da Aunty Farida tayi mata, gaba daya ta kasa shan pepper soup din Offals din, don jinsa take kamar magani a bakinta gashi har sannan jikinta babu kwari ga ciwon kai, ta kalli drip din dake hannunta taga ko quarter bai yi ba amma har ta gaji ta rasa inda zata sa kanta taji dadi, tun da AJ ya kawo magungunan da drip ya ajiye ya bar gidan har sannan bai dawo ba, ga abincinsa Aunty Farida ta zuba a cooler ta ajiye a tray tun daxu tana jiransa, tambayoyi ne da yawa ke yawo a zuciyar Aunty Farida tana son tambayar Khaleesat ko shine ya taɓa biya mata jirgi kwanaki da Umma bata da lafiya amma ganin yanayin da Khaleesat ke ciki ta bar duk tambayoyin nan a zuciyarta, Aunty Farida ta kalli Khaleesat tace "Ki daure ko kadan ne ki sha, ko in dama maki custard?" Khaleesat ta girgiza mata kai, dai dai nan aka kwankwasa kofar parlon, Aunty Farida ta mike ta yafa gyalenta sannan ta tafi ta bude kofar ta koma gefe, da sallama Ajay ya shigo parlon yana kallon Aunty Farida yace "Tare da brother dina muke" Aunty Farida tace "To ku shigo mana" a hankali Khaleesat ta gyara zamanta tana kallon Jay babu ko kiftawa, ganinsa ta dinga yi kamar a mafarki, Jay ya sauke kansa ya gaida Aunty Farida ta amsa da fara'a, sannan ya juya yana kallon Khaleesat shi ma babu ko kiftawa, lkci daya hawaye ya cika idonta tana kallonsa, walking slowly ya karasa har cikin parlon ya duka gabanta yana kallonta, a hankali yace "Are you feeling better now Housemate?" Da sauri ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta, and truly she felt better immediately, shi dai AJ na tsaye yana kallonsu, haka Aunty farida da ta koma one sitter a sanyaye ta zauna, Jay yayi kasa da murya still looking at her yace "Kiyi hakuri, everything will be okay soon in sha Allah, i promise you" Ta gyada masa kai da sauri with so much hope from his assurance, yana kallon bowl din hannunta Softly yace "Take ur soup" Ba musu ta dau spoon din ta fara shan pepper soup din a hankali, Aunty Farida ta kalli Ajay tace "Baka zauna ba Junaid" Ajay ya sauke kansa ya karasa 2 seater ya zauna, Aunty Farida ta share hawayen da ya cika idonta, da kyar tace "Mu ma duk ba da son ran mu bane abubuwan nan ke faruwa haka ba, ba mu da yanda za mu yi ne kawai, amma babu nagartattun iyayen da za su dau er su su ba Abdul aure" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Alhamdulillah! Shin kunada labarin MG’s Beauty Lounge zai buɗe a ranar Litinin, 2nd June 2025 – daidai lokacin Sallah!😍 ‘Yan mata da mata masu son kyau a Kaduna, lokaci yayi da za ku haskaka a wannan Sallah! MG’s Beauty Lounge ya buɗe da kwalliya, tsafta da ƙamshi irin na sarauniyar zamani! Ga abin da zaki samu idan kika ziyarce mu: Gyaran gashi da kitson zamani Kwalliyar Sallah mai ɗaukar ido Wanke ƙafafu da pedicure mai sanyaya rai Kayan gyaran fata na gaske Lalle mai kyau da salo na zamani Tura-turai, humra, incense da ƙamshi masu daɗi Shirin amare da na musamman Ba kawai gyara muke ba – kulawa ce ta musamman ga kowace sarauniya. Zo ki ji daɗin wanke ƙafa, lalle, kwalliya, ki saya kayan kyau da ƙamshi – komai a wuri guda mai kyau. Adireshi: Block 21, Nnamdi Azikiwe by Makarfi Road, bayan gidan Indomie, kusa da Sorera Restaurant, Kinkinau, Kaduna. Tambaya/Booking: WhatsApp: 08062991549 Kira: 09016108092 / 08064532391 Ki zo ki gani da idonki – ki ji daɗin sauyin MG’s Beauty Lounge. Bi mu a IG & TikTok: @MGsBeautyLounge HALYSAAH 32 Sai da Jay yaga Khaleesat ta ci pepper soup din me ɗan yawa sannan ya mike ya koma kusa da Ajay ya zauna, After a while Ajay yayi breaking din silence din da ya ziyarci parlon yace "Iya daukar nauyin karatun ta kawai yayi Aunty?" Aunty Farida zata yi magana wayarta ya fara ring, dauka tayi ganin Umma ce ke kiranta ta wayar makociyarsu Sha'awa, ta mike ta tafi dakinta don daga wayar, Ajay dai kallon Khaleesat yake kamar yanda Jay ke kallonta don har ta shanye pepper soup din, ta ajiye bowl din kasa tana kokarin disconnecting drip din hannunta ta yanda zata bar cannula din kawai, Jay ya mike yana kallonta yace "What happened? Do u want to ease ur self" Da kyar tana girgiza masa kai tace "I think i want throw up" Ya karasa cikin hanzari yayi disconnecting din mata, ta tashi ta wuce bandakin Aunty Farida da sauri tana toshe bakinta, sai ga Aunty Farida ta fito daga daki, ta kalli inda Khaleesat ke zaune ganin bata nan ta kalli kofar bandaki, zaunawa kan kujera tayi a sanyaye tana kallonsu tayi kasa da murya tace "Yanzu yayata ta kirani wai an zo an tafi da mahaifin Khaleesat" Da mamaki Jay da Ajay ke kallonta, Ajay yace "Kamar yaya kenan?" A sanyaye Aunty Farida tace "Baban Abdul din ne yasa aka je aka tafi da shi" Daga Ajay har Jay kallonta suke with confusion da kuma mamaki, fitowar Khaleesat daga bandaki ya sa Aunty Farida tayi shiru bata sake cewa komai ba, bayan Khaleesat ta kwanta kan 3 sitter din Aunty Farida ta juya tana kallonta tace "Ko zaki shiga daki a maida maki drip din?" Khaleesat ta gyada mata kai don ita ma ta gaji da kwanciyar kujeran, Aunty Farida ta mike tace "Bari in ma makociyata magana sai ta sa maki a daki" Daga haka ta fita daga parlon, after some minutes sai ga ta ta dawo da Neighbor dinta Bayerabiya, Khaleesat ta tashi ta koma dakin Aunty Farida, Bayerabiyar ta bi ta ciki ta sa mata drip din, ita dai Aunty Farida na zaune parlor tayi nisa tunanin da take har makociyarta ta fito ta tafi, Aunty Farida ta kalli su Ajay a hankali tace "To abinda yayata ta kirani ta gaya min kenan" Ajay yace "So suke a biya su kudin makarantar da ya dinga biya mata?" Aunty Farida ta girgiza kai tace "Ai ba iya kudin makaranta bane Junaid" Ajay yayi shiru yana kallonta, Jay yace "Bayan makaranta akwai wani abu na kudi da ya hadasu ne?" Aunty Farida tace "Kwarai kuwa.... Shekarun baya Malam Ali wanda shi ne mahaifin Khaleesat dreban babban mota ne, babu garin da baya zuwa da kaya a babban mota a fadin Nigeria, kuma motar tasa ce iyaka idan kana da lodi ya kai maka kayan ka har inda kake so sannan ka biyasa, har Nijar ya sha shiga da kaya daga nan Nigeria ta haka ma ya hadu da yayata Aunty Zahra'u warce ita ce mahaifiyar Khaleesat, don mu yan Nijar ne mahaifinmu har yanzu yana nan da ransa mahaifiyarmu ce dai Allah yayi ma rasuwa shekarun baya, to bayan ya auri yayata ya kawota Kano Nigeria ya ajiyeta cikin matansa biyu, bayan en watanni da auren shine na dawo wajen yayata tunda bata da kowa a Nigeria bata san kowa ba, nan rikona ya dawo hannunta a lkcn ina da shekara goma, tsangwama da kyara babu irin wanda ban sha ba a wajen kishiyoyin yayata, gashi bata iya ce masu komai tunda ita ma ba barin ta suka yi ba, mace ce me hakuri da kauda kai, in zanyi magana ma sai ta hanani, a haka ta samu makaranta ta saka ni tunda a can kasarmu ina karatu aka daukoni aka kawo mata, sai da tayi shekara biyar a gidan sannan Allah ya bata Khaleesat, Mahaifin Khaleesat na da rufin asirinsa sosai don haka bamu rasa komai a gidan ba sai zaman lafiya da kwanciyar hankali daga kishiyoyinta wani lokacin har da uwar mijin, jifa jifa mu kan kai ziyara Nijar gun iyayenmu da yan uwa da abokan arziki, bayan shekaru 12 da auro yayata a lkcn Khaleesat na da shekara bakwai sai abokan Mijin yayata da yan uwa suka dinga zugasa akan ya shiga siyasa ya nemi wani babban mukami zai samu tunda yana da jama'a sosai, kuma ba laifi yayi karatunsa, matansa ma suka dinga zugasa akan ya fito takara, yayata tayi kokarin ganin ta hanasa tunda bai rasa komai ba a sana'arsa ta dreban mota amma ya ki, haka nan ya daga babban motarsa ya siyar har da sabon gidan da ya fara ginawa a nan Ɗan Ladi na sidi, ya daga duk en kadarorinsa ya siyar ya shiga siyasa gadan gadan, duk matansa sai da ya biya masu Hajji suka tafi da mahaifiyarsa, ya kuma canza ma ko wacce kayan daki, ya ba kowa kudi a hannu, kusan mutane goma sha biyu ya biya ma Hajji a lkcn, banda matasan anguwa da ya dinga biya ma kudin makaranta, yayi ta facaka da kudi a karshe dai ya zo ya fadi zabe, duk wa enda suka dinga zugasa suka juya masa baya, Allah ya rufa masa asiri bai amshi bashin banki da wani abokinsa ke ta zugasa ya amsa ba kasancewar da zaben ya gabato bashi da kudi kuma a hannu, bayan faduwarsa zabe aka shiga yanayi na babu a gidan, cin yau da kyar na gobe da kyar ga yayata na da cikin yan biyu, dama gidan da yake haya me tsada tuni ya saki bayan kudin hayan sun kare muka dawo mariri gidan gadonsa da ya bari a walakance don saura kadan ya kyautar lokacin da yake campaign sai gashi gidan ya mana amfani ya rufa mana asiri, makaranta me tsada da yaran gidan ke zuwa duk ya ciresu suka dawo gida suka zauna babu karatu, iyayen basu yi dubaran mayar da su na gwamnati ba, duk muka shiga mawuyacin hali a gidan, sai sanda ya samu mota yake lodin kaya ya kai a biyasa, sanda babu mota kuma sai dai kowa ta ciyar da kanta a gidan, yana kuma fin wata da watanni bai samu ko da karamar mota ba, duk ka zo kofar gida zaka gansa a zaune babu abun yi shi ma duk ya fita hayyacinsa, tuni yayata ta siyar da kayan dakinta ta fara sana'a ina taimaka mata, ta kuma saka Khaleesat a makarantar da zata iya biya don Khaleesat ta taso da kwazo da hazaka ga ta yarinya ce me shiga rai ko don kalan fatarta, don a unguwan ma gidan buzaye ake kiran gidanmu, hatta Mahaifinta kiri kiri yake nuna yafi sonta a cikin sauran yaransa wanda hakan ya ja mata tsana da kyara a gun matansa da yan uwanta, ko sanda yake da mota a hannu tsaraba na musamman yake ma Khaleesat ko da bazai yi ma uwarta ba, ana haka yayata ashe duk cinikin da nake sai ta kwasa ta ba mijinta a boye ban sani ba, ga dai matansa duk da hali na babu da aka shiga a gidan basu bar yayata ba, kullum cikin hada mata tuggu da makirci ake wajen miji da uwarsa, cikin wannan yanayi yayata ta haifi yan biyunta wanda haihuwan da tayi na karshe kenan a gidan, a lkcn matsaloli har sun fi na da, jarin yayata ya karye kuma babu wani abu da zata siyar ta tada jarin, ga jegon yan biyu tana yi ga yunwa wani lkcn sai makota ke zubo abinci a kawo mata, iyayenmu a can Nijar ba masu karfi ba balle su taimaka mana, a haka na bi wata kawata zuwa nan garin Lagos tana siyar da abinci, kafin nan fa nayi aure har na fito, duka auren bai cika shekara daya ba, na auri wani abokin mahaifin Khaleesat, karayar arziki na samun Malam Ali na dinga fuskantar matsaloli gun mutumin da matansa uku wanda daga karshe ya sakeni dama ba saboda Allah yayi auren ba saboda kalan fata ta yayi, ina nan Lagos nake tallafa ma yayata da 'ya yanta uku, don bana son karatun Khaleesat ya tsaya duk da ta samu Foundation sosai sbda makarantar da ubanta ya sa ta ma a sanda yake da rufin asirinsa yafi na sauran yan uwanta tsada, na zo Lagos da yan shekaru yayata ta kirani wataran wai gashi an ba Baban Khaleesat babban mota har zai kai kaya kudu, matsaloli sun fara warwarewa tunda har an biyasa kudin kai kayan kuma kudade masu tsoka gashi har ya siya kayan abinci masu yawa ya ajiye a gida, tace in Maza in dawo gida kawai dama ita hankalinta ba a kwance yake da zamana a lagos ina sana'a ba, a haka ta takurani har sai da na dawo Kano, a sannan Khaleesat na da shekaru sha shidda tana kuma gab da gama secondary don da wuri aka sakata a makaranta, na dawo da wasu kwanaki ranan muna zaune tsakar gida da yamma sai ga mahaifin Khaleesat an shigo mana da shi ranga ranga ko motsin kirki bai yi, wanda duk gaba daya mun zata yana hanyar kudu har ya kusa Lagos, ga dai shi babu ko kwarzanen ciwo a jikinsa kuma wa enda suka kawosa suka ce ai daga asibiti ma aka taho da shi a can wajajen garin yarbawa, sannan kwanansa uku a asibiti aka sallamosa wasu mutane da suka shaidasa tunda dreba ne suka biya kudi aka sako sa a mota aka dawo da shi Kano, sosai hankalinmu yayi mugun tashi a wannan lokacin, sae da Malam Ali yayi kwana biyu a gida ana ta addu'a da neman taimako kafin ya farfado gaba daya har yana iya magana, nan fa yake sanar mana barayi ne suka kwace Trailer da kayan mutane a ciki bayan sun shaka masa wani farin abu, tashin hankalin da duk muka shiga bazai misaltu ba a lokacin, daga Trailern har kayan cikin trailern ya doshi miliyan dari da tamanin" Shiru Aunty Farida tayi tana goge hawayen dake zuba idonta, Jay that was shock ya kalli Ajay dake kallon Aunty Farida babu ko kiftawa jin zunzurutun amount din da ta kira, Aunty Farida na share idonta ta ci gaba tace "A ranan yan sanda sun kusa goma suka zo a motoci, a haka aka sa ma mahaifin Khaleesat ankwa ana jan sa kamar barawo aka fita da shi yaransa da matansa na kururuwa suna ihu, Khaleesat kadai ce bata motsa daga inda take zaune da littafi a hannunta ba sai hawaye kawai, duk aka cika kofar gidanmu babu masaka tsinke kai kace barawon gaske aka zo dauka, mun shiga tashin hankalin da baya faduwa a wannan rana, kuma duk mutanen da yayi ta biya ma Hajji a sanda yake da hali, da kuma mutanen da ya taimaka ma aka rasa wanda zai bi yaga inda ma aka kai sa, ashe daga kano Abuja aka nufa da shi, bayan dogon binkice aka gano trailern an yasar a wani gari an kuma juye duk kayan cikin trailern, dama me trailer daban, me kaya daban, adadin kayan cikin trailern kuma zai yi na miliyan dari, to ba kowa bane me kayan cikin trailern nan illa mahaifin Abdul, sam ba a yarda babu sa hannun Mahaifin Khaleesat a juye kayan cikin trailern ba, dama kuma yan unguwa na jin haushin ya samu lodi me yawa haka ya tafi kai kayan shi kadai ko yaron mota bai dauka ba, kuma ko wani dreba an san sa da yaron mota daya ko biyu, nan aka yi ta zuga baban Abdul akan kar ya yarda wai dama planning Baban Khaleesat yayi don ya taɓa yi ma wani mutum haka da dadewa yace barayi sun kwace kaya a hanya sai yafewa mutumin yayi, kuma wai don yaga Alhaji Musa wato mahaifin Abdul me kudi ne sosai shi yasa zai cucesa yace an sace kaya tunda yanxu ta kare masa bai da komai, kuma wallahi sharri ne ba haka Baban Khaleesat yake ba, bai cin kayan wani baya taɓa abu in ba nasa bane, beside bai taɓa sanin Baban Abdul ke da kayan ba sai da iftila'in ya faru sannan yaga me kayan, shi dai kawai ance masa ga Lodi zai kai lagos ya kuma amince tunda sana'ar sa kenan kuma kullum fatan samun Lodi yake, ko da babu zugin yan anguwa baban Abdul bai yi kama da mutumin da zai iya yafe kudinsa ba don kana ganinsa kasan bashi da mutunci bashi da kirki, sai da Mahaifin Khaleesat yayi wata uku bamu sa shi a idonmu ba kafin aka dawo da shi kano duk ya rame yayi baki ya dawo kamar ba shi ba, da kyar aka bari muka gansa a fursin da aka ajiyesa na nan kano, ranan duk bamu yi bacci ba bayan mun dawo gida, yayata ta shiga tashin hankali mara misaltuwa don tun dauke mahaifin Khaleesat dama ta fara alalan siyarwa don mu rufa ma kanmu asiri saboda ɗan jarin da nake da shi nima duk ya karye bani da komai, kafin ma a dawo da mahaifin Khaleesat kano sau uku muna zuwa gidan Alhaji Musa a Nassarawa GRA domin mu basa hakuri ko zai dubi halin da muke ciki ya taimaka a sake mana Baban Khaleesat amma duk aka mana koran kare, na farko masu gadi ne suka kore mu, na biyu Matarsa ranan ta rako baƙinta ta gan mu tayi mana cin mutunci ni da yayata da Baaba Gaje ta sa aka kore mu, na uku kuma ɗan cikinsa Abdul wanda dama shi kadai ne namiji a 'ya yansa, ana haka aka shiga kotu ko lauya baban Khaleesat bashi da tunda bamu da halin daukan Lauya, rana na farko da aka kawo Malam Ali kotu daga prison ni da Khaleesat da kishiyar yayata Mama Shatu ce muka je kotun don sauraron karan, to a ranan Abdul yaje kotun shi ma a matsayin daya daga lauyoyin mahaifinsa ashe shi ma Lauya ne, sarai na ganesa da na gansa a kotun don ranan karshe da muka je gidansu har ce ma masu gadi yayi in muka sake dawowa su rike mu yan sanda ne za su zo su tafi da mu, zaman kotu da akayi a wannan rana babu wani positive outcome da ke nuni da cewar da nasara a case din, kwata kwata babu alamun nasara tunda Malam Ali ba kowa bane, kuma ba shi da kowa bai da komi, bashi da wanda zai tsaya masa, haka aka dage shari'ar zuwa wani watan shi kuma za a maidasa prison cikin motar da ta kawosa ko belinsa anki badawa, Khaleesat ta dinga kuka sosai a haraban kotun tana kallon yanda aka shigar da babanta motar prison, nima ina rungume da ita ina hawaye, wanda wannan ne ya ja hankalin Abdul da fitowarsa daga kotun kenan zuwa kanta, ba shi ba hatta sauran jama'an wajen kallonta suke, Alhaji Musa babban mutum ne kuma me kudi wannan yasa har da yan jaridu a haraban kotun, wani ɗan jarida ya nufo mu yana tambayar me za mu iya cewa game da zaman da aka yi yau a kotu, budan bakin Khaleesat cikin kuka sai cewa tayi Allah ya saka ma babanta sharrin da aka masa, ina tunanin a nan ne Abdul ya fahimci er gidan wanda suke ƙara ce Khaleesat, duka duka shekarunta sha shidda a sannan amma duk wanda ya kalleta sai ya sake kallonta, ranan ma tsautsayi yasa ta fito babu Nikab duk da ba a shiga da Nikab amma duk inda zata bata fita babu Nikab, in ma bata sa ba uwarta zata tilastata ta saka, hatta nima bana fita babu shi haka Mahaifiyarta saboda bakin jama'a, kun ji inda Abdul ya fara ganin Khaleesat, a sannan kuma kawai motarsa ya shiga, sai wani Lauya me zaman kansa ya nufo mu, ya ja mu gefe yana kokarin calming din Khaleesat, nan ya tambayeni me ya faru, me ya kawo mu kotu, nayi briefing din masa komai nima ina kuka, ya tambayeni zuwa yaushe aka daga karan, na sanar masa, yace to in basa lambata in sha Allah anjima zai kirani yaga abinda za ayi akan case din kuma mu kwantar da hankalinmu, ko wayar bani da shi a sannan, instead sai na basa Address din unguwanmu Mariri, ita dai kishiyar yayata na zaune karkashin bishiya tayi tagumi, a haka muka bar kotu ranan rai babu dadi muka koma gida, bayan kwana biyu ranan da yamma wajen karfe shidda muna zaune tsakar gida ko wacce na fafutukar abinda zata dora ta ciyar da kanta da yaranta, don yanzu kowa takai takai a gidan, kishiyoyin yayata har sun sake 'ya yan su maza kanana suna fita almajiranci suna ciyar da kansu, matan kuma a dora masu talla su tafi can bakin kasuwa, yayata dama ina taimaka mata muna sana'a a gida, kudin waec din Khaleesat ne dai muka kasa hadawa gashi saura kwanaki kadan a fara, kamar daga sama sai ga Mahaifin Khaleesat ya shigo gidan kamar an jefosa, Khaleesat ce ta fara ganinsa ta tafi da gudu ta rungumesa, duk muka mike tsaye a tsorace muna kallon ikon Allah baki bude, yayata tayi karfin halin tunkararsa tana tambayarsa daga ina yake haka, kar dai gudowa yayi daga gidan yari, Baban Khaleesat yace kawai shi dai ce masa aka yi an bada belinsa daxu da rana, sai gashi kuma aka daukosa aka kawo har gida aka ajiyesa, tsabar mamaki duk muka kasa cewa komai a tsakar gidan, yayata ta kama hannunsa hawaye cike idonta ta kai sa dakinsa don shi ma duk a firgice yake kana ganinsa kasan ba karamin wahala ya sha ba, sai a sannan yaran gidan suka fara ihu suna murnan dawowan mahaifinsu suna ta tsalle tsalle, sauran matan duk suka bi bayan yayata zuwa dakin Baban Khaleesat" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Alhamdulillah! Shin kunada labarin MG’s Beauty Lounge zai buɗe a ranar Litinin, 2nd June 2025 – daidai lokacin Sallah!😍 ‘Yan mata da mata masu son kyau a Kaduna, lokaci yayi da za ku haskaka a wannan Sallah! MG’s Beauty Lounge ya buɗe da kwalliya, tsafta da ƙamshi irin na sarauniyar zamani! Ga abin da zaki samu idan kika ziyarce mu: Gyaran gashi da kitson zamani Kwalliyar Sallah mai ɗaukar ido Wanke ƙafafu da pedicure mai sanyaya rai Kayan gyaran fata na gaske Lalle mai kyau da salo na zamani Tura-turai, humra, incense da ƙamshi masu daɗi Shirin amare da na musamman Ba kawai gyara muke ba – kulawa ce ta musamman ga kowace sarauniya. Zo ki ji daɗin wanke ƙafa, lalle, kwalliya, ki saya kayan kyau da ƙamshi – komai a wuri guda mai kyau. Adireshi: Block 21, Nnamdi Azikiwe by Makarfi Road, bayan gidan Indomie, kusa da Sorera Restaurant, Kinkinau, Kaduna. Tambaya/Booking: WhatsApp: 08062991549 Kira: 09016108092 / 08064532391 Ki zo ki gani da idonki – ki ji daɗin sauyin MG’s Beauty Lounge. Bi mu a IG & TikTok: @MGsBeautyLounge *Gaisuwa da fatan alkhairi zuwa ga me kasuwar garin Dutse Hajiya Aunty Zahrah da Hajjaju Sadiya Chamo Ex in-law, Hajiya Nafeesah Mom twins da Ummu Zainab Maman Ramla, Aunty Maryam Dan Ladi nasidi kema na gaisheki da katon murya, Hajiya Zainurah Boss Lady, Hajiya Jumare da Hajiya Asmy me kayan amare, Oum Nabeelah, Mardiyyah, Uwar Janan, Halysah Garba😂 i hail you all with respect yan Palace* Manyan Membobin _❤‍🩹Khaleesat's Citadel_❤‍🩹 *Su Meenah parrot🐔, Oum Noor, Nafeesah Jawwad, Rukayya, Fidomashi, Siyam, M manal, Mrs Barrister, Shanono Esq, Ummilos, Na'imatu, Zulaiha, Ummu Abdrhm, Khaleesat Haiydar is saying a big thank you to you all for ur support always, Allah ya bar min ku*🥰 HALYSAAH 33 Aunty Farida ta numfasa a hankali tace "Da yake Abdul shi kadai ne namiji gun mahaifinsa, mahaifin ya dauki son duniya ya dora masa kuma bai jin maganar kowa sai nasa, duk abinda Abdul yake so shi mahaifinsa ke so, bayan yaga Khaleesat a kotu babu tantama zuwa yayi ya samu uban ya nuna yana sonta zai kuma aureta, wannan dalili yasa babu bata lokaci suka janye kara a kotu suka bar maganar miliyan dari da sharadin Malam Ali zai ba Abdul auren er sa Khaleesat, mu dai har yau bamu san ko da wata yarjejeniya da aka yi a kotun ba ko babu, mun dai san an janye kara kawai kuma duk muka yi farin ciki sosai da hakan, burin mu kawai Malam Ali ya dawo gare mu ko da bazai tsinana mu da komai ba amma mu dinga ganinsa a tare da mu a matsayin kantangar gida, balle duk mun san yayi ma iyalansa hidima dai dai gwargwado ya kuma kyautata masu yanda ya kamata, jarabawa ce kawai ta fada masa, bana mantawa Khaleesat ta shiga damuwa sosai a lkcn tana ta koke koke wai ita bata son Abdul tun ma bata san kalansa ba bata gansa ba tace bata sonsa bazata iya aurensa ba, mu kam idonmu duk ya rufe da son ganin an wanke Malam Ali daga laifin da ake zarginsa da shi, ni da uwarta muka yi ta bata baki muna kwantar mata da hankali muka ce ko tafi son a maida mahaifinta prison ne, ko don mahaifinta bazata hakura ba ta amince da bukatar Abdul na son aurenta don case din ya mutu gaba daya, gashi tun bayan dawowar Malam Ali yayi ta rashin lafiya ko kudin kai sa asibiti babu, duba da hakan ne ma yasa muka yi ta karfafa ma Khaleesat gwiwa muna bata baki, a haka dai muka samu muka lallabata ta fara hakura, nan kishiyoyin Ummanta suka fito da baƙin cikinsu da hassada a fili tunda su ma ai suna da 'ya ya mata sa'annin Khaleesat da ma wa enda suka girmeta amma shine Abdul zai ce sai Khaleesat, nan fa duk suka hau gaba sosai da yayata saboda ɗan mai kudi ya ga Khaleesat yace yana so, ranan farko da Abdul ya fara zuwa unguwan cewa yayi shi bazai shigo da motarsa layin ba ta fito bakin titi ta samesa, gashi daga gidan zuwa bakin titi akwai tafiya sosai, haka nan uwar ta lallabata ta shirya ta saka nikab dinta kannenta biyu suka rakata har bakin titin ta samesa, a ranan kuma ya bata babban waya ya kuma hadata da dubu hamsin, ba ma ita ta amsa ba don nuna masa tayi bata so shine ya ba kannenta yayi tafiyarsa, da kudin aka samu aka biya mata waec dinta tunda ba mu da yanda za mu yi, a kaf tarihi ban taɓa jin wanda yake neman yarinya da isa da gadara da walakanci kamar Abdul ba, for almost 2 months in Abdul zai zo unguwan mu sai dai dole ta fito titi ta samesa shi bazai shiga layin da motarsa ba, watarana ne ya kira bata da lafiya shine da ya tashi zuwa dubata da yamma ya shigo layin a karo na farko tunda ya fara zuwa gurin ta, daga nan kuma ya dena cewa ta fito bakin titi in ya zo sai dai ya karasa ciki da motarsa, ya kai ya kawo har cikin gida yana shigowa, tun a wannan lokacin Abdul baya raga ma Khaleesat, fadan yau daban na gobe daban, bashi da fahimta bashi da uxuri, ga nuna isa da gadara abinda yace yake so dole shi zata yi, haka nan yarinyar nan ke hakuri da halinsa duk don saboda mahaifinta, rana daddaya ne baya sa ta kuka, sai dai ni da uwarta mu yi ta bata hakuri muna ganin duk me sauki ne tunda har yana sonta kuma yaji zai aureta ya zauna da ita wataran zata canza sa da kanta, ni dai a sanda na fara sarewa da lamarin Abdul jikina yayi sanyi shine watarana da ya daga hannu ya mareta har sai da shatin yatsunsa ya kwanta fuskarta, mu dai har yau bata gaya mana me tayi masa da yayi mata haka ba don a cikin motarsa hakan ya faru, nan jikin uwarta ma ya fara sanyi kan lamarin har ta samu Mai gidanta ta gaya masa amma Malam Ali yayi ta kakkarewa har da cewa duk wanda ma ya kara tada maganar Allah ya isa, ana haka har ya biya mata jamb ya kai ta da kansa ta zana don fara jami'a tunda waec dinta ya fito kuma sakamakonta yayi kyau sosai, kawai rana daya kwatsam ubansa ya kira mahaifinta wai ga abinda Abdul yace yake so, wato zai tura Khaleesat Amurka tayi karatu a can, duk kawaicin da yayata take wannan karan sai da ta nuna bata amince da hakan ba, don ana ta bin su a yanda suke so ba hakan ke nufin bamu da ta cewa akan lamarin Khaleesat ba, ba Yayata ba har kakar Khaleesat Nenne ta nuna rashin amincewarta a wannan bukatar tasu, babu ta yanda za a dau yarinya karama haka da ko mallakan hankalinta bata gama yi ba ace za a tura ta har Amurka da sunan karatu, in haka ne kawai a daura auren mana sai ya kai ta duk inda ma zai kai ta tayi karatu, in ko ba haka ba babu inda er ta zata je da sunan karatu sai dai duk abinda zai faru ya faru, a nan dai laifin Mahaifin Khaleesat ne da ya dau tsoron duniya ya dora ma Abdul da mahaifinsa ba kuma tsoron komai ba sai tsoron kar su sake maidasa inda ya baro wato prison, dama tunda ya baro can ya dawo gashi nan gashin nan dai kamar ya ɗan samu matsala a kwakwalwarsa, yau lafiya gobe akasin haka, ya dawo kamar ba Malam Ali ba, a lokacin duk ya gigice yayi ta bala'i wai ina ne ba a tura yaro karatu a zamanin yanxu, yarinya me shekara sha bakwai ce za ace ma yarinya, inda yake shiga ba nan yake fita ba, hakan ya zame masu bacin rai sosai da mahaifiyar Khaleesat har sai da ta bar gidan ta koma gidan Mahaifiyarsa warce ita ma yaki sauraronta, haka nan Malam Ali ya dau Khaleesat ya damka ma Abdul ba tare da amincewar uwarta ba ya kai ta karatu Amurka, Shiru Aunty Farida tayi tana kallon su Ajay dake kallonta duk suna sauraronta, a hankali tace "Tun daga sannan shi yake sponsoring komai nata a Amurka, cin ta da shan ta, da suturanta komai dai shi ne, sai san da ya ga dama ne yake bari ta zo hutu Nigeria, mu tsakaninmu da ita dama sai sanda muka ganta ko kuma muyi magana ta WhatsApp, gashi yaki a daura auren nasu wai sai ta gama karatun wanda wnn ne ke kara daga mana hankali, a haka ake ta rayuwar bamu da kwanciyar hankali, a ko da yaushe fatanmu shine ayi ayi auren don duk wasu iyaye nagari baza a same su da kwanciyar hankali ba ace yau er su budurwa bata gabansu, kusan kullum sai uwarta ta zubda hawaye kan wannan lamari sanadiyar hakan har sai da hawan jini ya kamata, ace bata da iko da er ta sai dai abinda Abdul da ubansa suka tsara gashi mai gidanta ya dau tsoron duniya ya dora masu sai jan sa suke kamar rakumi da akala.... ko wata biyu ba ayi ba ranan yayata ta kirani take sanar min sun kawo kudin auren Khaleesat, duk muka yi farin ciki sosai da hakan, muka yi fatan Allah ya sa hakan alkhairi ne a rayuwar Khaleesat tunda mu ma mun fi son ayi auren kowa ma ya huta, kawai ranan juma'an nan da ta wuce sai ga kiran yayata wai an daura auren Khaleesat da Abdul, nace mata ban gane ba, Khaleesat din ta dawo ne? Sannan dama ana daura aure haka ba shiri? Nan take gaya min ai mahaifin Abdul din ne ya kira Baban Khaleesat da yamma likis yace ga bukatarsu gobe juma'a, babu bata lokaci kuma aka daura auren kamar yanda suka bukata washegarin, nace mata to shikenan Allah sa hakan shine mafi alkhairi, zuwa satin da za a shiga zan shigo kanon tunda tace Khaleesat din ma na Amurka bata dawo ba, ban kuma san komai dake faruwa ba sai ranan Lahadi da kirani, mun yi waya da kai babu dadewa sai ga yayata ma ta kirani tana kuka" Ajay ya sauke idonsa kasa, Calmly yace "Amma dai baki ce mata tana nan ba har yanxu ko?" Aunty Farida ta girgiza kai tace "Ai tunda muka yi waya kace kar in nuna ma kowa nasan inda take wallahi ban nuna ma yayata nasan komai ba, ita kanta har yanxu bata san inda Khaleesat take ba, Nasan Baaba Gaje bazata gaya mata ba ita ma" Ajay ya sauke ajiyar zuciya yace "Shikenan, yanxun ma kar ki nuna tana wajenki, in sha Allah za mu ga yanda za ayi, in ma kudin baban nasa da abinda ya kashe mata na makaranta za a mayar masu wannan ba matsala bane in sha Allah" Aunty Farida ta gwalo ido jin abinda yace, ko dai bai ji amount din da ta kira bane da kyau, a hankali tace "Kudaden ne da yawa ai Junaid, miliyan dari fa banda abinda zai ce ya kashe mata na makaranta da bamu sani ba" Ajay yace "Bazai dai ce ya kashe mata sama da miliyan dari a makarantar ba, mu ma duk makarantar muke ai, in ma yace haka miliyan dari biyu ba abu bane da muke fatan zai gagara a mayar masu, so kawai kar ki ce ma kowa tana wajenki, we will see how things will go in sha Allah" Ita dai Aunty Farida tsabar yanda jikinta yayi sanyi ta kasa cewa komai, dama tun da ya sakko daga mota jiya taga kalansa take ta kallonsa tana mamakin inda Khaleesat ta samo shi, hatta wanda ya kira ɗan uwansa bata ga yayi kalar tsiya ba shima, Shi dai Jay yayi shiru bai ce komai ba idonsa akan buhun shinkafa biyu da babban jarkan man gyada da carton din taliya dake parlon Aunty Farida, kana gani kasan food vendor ce, Ajay ya mike yana kallon Jay alamar ya tashi su tafi, Jay ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yana kallon Aunty Farida a hankali yace "Bacci take ne?" Ajay ya wani kallesa sai kuma yayi ficewarsa daga parlon, Aunty Farida ta mike tace "Bari in duba ta" Dakinta ta nufa Jay ya bi ta da kallo, after few seconds sai ga ta ta fito tana kallonsa tace "Ehh bacci take" Yace "Ohk, amma Drip din na raguwa kuwa?" Aunty Farida tace "Eh yana sauka" Mikewa yayi yace "Toh shikenan, sai anjima Aunty, kilan zuwa gobe da safe in sha Allah za mu shigo" Aunty Farida ta ɗan yi murmushi tace "Toh Allah ya kai mu Jawwad, mun gode sosai" Murmushin ya mayar mata ya nufi kofa, har ya fita ya sake juyowa yace "Amma Aunty ki ɗan dinga duba drip din idan ya kare sai kiyi ma makociyar taki magana ta cire" Aunty Farida tace "Ina sha Allah, mun gode Jawwad" Daga haka ya fita daga parlon ya nufi kofar gida, cikin mota ya tadda Junaid har ya tada mota, ya karasa ya bude front seat ya shiga ya zauna ya jinginar da kansa da kujeran motar ya lumshe ido ya bude, saukansa kenan daga America ko hutawa bai yi ba balle ya ci abinci, yayi wanka kawai suka taho gidan Aunty Farida da Ajay, har suka isa gidan Cousin sister din parent dinsu dake Banana Island babu wanda yace komai a cikin motar, it's almost 7pm tsabar traffic din Lagos da ya rike su a hanya, bayan Ajay yayi parking Jay ya sauka daga motar ya nufi entrance din shiga gidan Ajay na biye da shi, a parlor suka tarar da Hajiya Fatima warce suke kira da Ummi, ta amsa gaisuwar da suka mata ta bi su da kallo, Ajay dai ya nufi sama, Tana kallon Jay tace "Baka ci abincin da aka ajiye maka ba Jawwad, ina ma ku ka je haka sai yanxu ku ke dawowa?" Jay ya shafa kansa a hankali yace "Wajen wani abokinmu" Daga haka shi ma ya wuce sama, ta bi sa da kallo. Wajen karfe tara na dare Ajay ya gama saka pajamas dinsa, Jay ya ajiye mug din tea dake hannunsa yana kallonsa Calmly yace "So now what is ur suggestion Ajay, gaba daya kai na ya kulle akan issue din nan, that guy have evil in mind shi yasa ya saka aka daura auren tun bata dawo ba, he have a different plan, abinda kayi masa a USA na ransa har yanzu.... He married her immediately just to deal with her, I don't think he still loves her, he married her to take revenge" Ajay yace "Dama ai ba saboda Allah ya sa aka daura auren ba, akwai abinda yake nufi da hakan, ashe ma karamin ɗan iska ne shi ban sani ba tun da bai yarda da kansa ba, da ya yarda da kansa bazai dinga kashe waya ba" Jay yace "Kamar ya?" Ajay yace "Na karbi numbersa na sa a duba min location dinsa, his location was showing Abuja on Sunday, tun sunday din har zuwa yau bai sake kunna wayarsa ba, kuma baya location din da aka gansa bayan na sa an je can" Jay ya bude baki yana kallonsa, can yace "Ban gane ka sa an je can ba, what are you trying to do? Plss ni bana son wannan dabancin naka Ajay, ni na zata fa ka shiryu, is that why u were busy shouting ku hadu a Nigeria on that very day? No pls ka girmi haka yanxu Prince, why spare ur precious time for a tout like him, don ni wallahi kallon tout nake ma gayen, sannan kar ka manta barrister ne shi kamar yanda kanwar mamarta ta gaya mana, definitely yasan plan dinka a kansa da yasa ka dage ku hadu a Naija, kaga bazai bar wayarsa a kunne ba kuwa" Ajay yace "Ai sai dai bai kunna wayarsa ba amma wallahi duk sai ya janye batancin da yayi min a parlon nan ranan, ya zata ana zagina a tafi scot free? I will so deal with him" Jay ya tabe baki yace "Yanxu dai that aside, meye abun yi" a takaice Ajay yace "Abun yi kawai a makasa a kotu ya fadi duk abinda ya kashe a biyasa ya saketa taje tayi rayuwarta, cause in har ta zauna zaman aure da mutumin nan zai iya kasheta har lahira, don prisoner zai mayar da ita kawai" Jay yayi shiru at first, can yace "But Ajay bamu san ko anyi a rubuce kan cewar an basa aurenta a madadin kudin da mahaifinta zai biya mahaifin Abdul din ba, sannan gayen nan Barrister ne, kana ganin zai bari ayi wannan yarjejeniyar babu sa hannu or anything of such ta bangaren shari'a?" Ajay yace "Su na ma iyayenta kallon talakawa marasu galihu da basu da wani say shine za su tsaya wani yarjejeniya? Ai masu arziki ke yarjejeniya, bayan sun san har a tashi duniya iyayen nata ba samun hanyar biyan miliyoyin kudin nan za su yi ba? Ai hankalinsu da tunani ma bazai je kan wata yarjejeniya ba cause they just assume sun samu yarinyar sun gama kuma ba wani abu da zai gifta ya hana hakan, so now we are taking this case to court, da bakinta zata ce ma alkali bata auren a kotu, iyaka ace ta biyasa abinda ya kashe mata na karatu sannan tayi masa wani auren ba shikenan ba" Jay yayi murmushi yace "Case din babanta da shi mahaifin Abdul din fa?" Ajay yace "We will reach der also" Jay yace "I just hope the agreement isn't in written form, but before mu je kotu nawa ne a account din ka Ajay?" Dariyar da Ajay bai yi niyya ba yayi yana shafa kansa, can ya kallesa yace "Why are you asking me that silly question Jay?" Jay yayi murmushi yace "Let me know first cause the money in my bank account isn't more than that amount" Ajay yace "200M?" Jay yace "Ban sani ba" Dariya sosai Ajay yayi yace "Na raina capacity dinka Bruh, meye kuma 200M a account dinka? Na zata account dinka ya doshi 1 Billion yanxu, Ohhh i remember baka wasa da investing fa, sannan kai Momy's boy ne har account din Momy ajiye kudi kake, Allah sa 200M din ma baya account dinta" Jay yaki tanka sa, Ajay yace "Kasan me, yanxu 600M or more ya kamata ace mun ajiye aside for this case cause I don't trust that stupid guy zai iya tripling kudin a kotu, i will get some more money from dad, Billah i am doing all this for the sake of humanity not because of that little brat, in don ta ita ne bazan yi ba, infact in don ta ita ne ba ruwana a case din ma" Jay dai danna wayarsa kawai yake bai ce komai ba don hankalinsa gaba daya yayi kan drip din da aka sa ma Khaleesat, yasan zuwa yanxu dai ya ci ya kare. Abdul na zaune gidan wani cin abinci tare da abokansa biyu da ke sauraronsa, Abdul yayi sipping energy drink din gabansa ya ajiye ya ci gaba da magana yace "I am still trying to gather more informations about the guy, kuma duk inda take yanxu da taimakon guy din taje can don bata da kowa a cikin garin kano or anywhere da zata je sai wajen sa, all of a sudden fa kawai naga yarinya ta canza attitude tana min wani sabon kalan raini, at first na zata naughty frnd din nan nata Safiyyah ce ke zugata duk da ita ma sai nayi maganinta don nasan da hadin bakinta a abubuwan nan da ke faruwa, i will fish her out too, ashe wai er ficiciyar yarinyar nan maza take kulawa a kasar suke bata liver take min raini, Billah sai na kauda gayen nan a doron kasa this is a promise i am making, sai dai uwarsa ta haifi wani, zai san gonata ya shiga sannan zai san bai daki banza ba, ba a dukana a ci gaba da rayuwa lafiya, he said we should meet in Nigeria ko? nasan yanxu shi ma yana bibiyan inda zai sameni, i don't want to be taken unaware shi yasa nake kashe wayata don nasan definitely zata basa lambata, idan na gama shirya masa tuggu zan bude wayar yayi tracking dina ya zo ya sameni inda nake, wallahil Azeem sai na kawar da shi kuma babu abinda zai faru, ita kuma duk inda take zata shigo hannuna nan ba da jimawa ba kuwa, sai dai in ban cika Abdallah Musa ba" Abokinsa Aminu yace "Toh kai baka ga fuskar guy din bane?" Abdul yayi wani murmushi yace "Ai ni yanxu ban damu da naga fuskarsa ko ban gani ba, burina in ga na aika sa barzahu, kun yankar mana ticket din da nace?" Aminu yace "But ta yaya zaka samu informations din wanda baka taba sani ba, baka da lambarsa ba, baka san komai kansa ba, baka san wanene shi ba, baka ma san inda yake a Nigeria ba ko kuma wanda ya san sa, How will that be possible Abdul?" Abdul yayi wani irin murmushi yana bubbuga kafarsa da kasa a hankali, sai kuma ya karyar da kai yace "Na zata you will be among people that will never underate my capacity and intelligence Aminu, ai ina da lambar wayarta ko? Kuma ni nayi mata registering sim card din, toh abokina dake aiki a kamfanin network din sim da take amfani na ba phone number dinta ya duba min duk calls dinta ya kuma turo min numbers din da take waya da su frequently a America, he just sent them to me few minutes ago" Yana kai wa nan ya mike yana wani murmushi yace "Let go" Dariya kawai abokan nasa ke yi, suka tashi duk suka fita daga eatry din. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* ur evidence of payment via 07087865788 Alhamdulillah! Shin kunada labarin MG’s Beauty Lounge zai buɗe a ranar Litinin, 2nd June 2025 – daidai lokacin Sallah!😍 ‘Yan mata da mata masu son kyau a Kaduna, lokaci yayi da za ku haskaka a wannan Sallah! MG’s Beauty Lounge ya buɗe da kwalliya, tsafta da ƙamshi irin na sarauniyar zamani! Ga abin da zaki samu idan kika ziyarce mu: Gyaran gashi da kitson zamani Kwalliyar Sallah mai ɗaukar ido Wanke ƙafafu da pedicure mai sanyaya rai Kayan gyaran fata na gaske Lalle mai kyau da salo na zamani Tura-turai, humra, incense da ƙamshi masu daɗi Shirin amare da na musamman Ba kawai gyara muke ba – kulawa ce ta musamman ga kowace sarauniya. Zo ki ji daɗin wanke ƙafa, lalle, kwalliya, ki saya kayan kyau da ƙamshi – komai a wuri guda mai kyau. Adireshi: Block 21, Nnamdi Azikiwe by Makarfi Road, bayan gidan Indomie, kusa da Sorera Restaurant, Kinkinau, Kaduna. Tambaya/Booking: WhatsApp: 08062991549 Kira: 09016108092 / 08064532391 Ki zo ki gani da idonki – ki ji daɗin sauyin MG’s Beauty Lounge. Bi mu a IG & TikTok: @MGsBeautyLounge HALYSAAH 34 Wajen karfe goma na dare Khaleesat na zaune dakin Aunty Farida da fruits a gabanta ta kasa sha, ita dai Aunty Farida na zaune opposite dinta ta zuba mata ido don har ta gaji da ce mata ta sha fruit din, ga abinci ma taki ci, tun tuni makociyar Aunty Farida ta shigo ta cire mata drip din bayan ya kare, ta daga kai ta kalli Aunty Farida a hankali tace "Aunty su Housemate dina sun tafi ne?" Aunty Farida tace "Waye kuma Housemate din ki?" Khaleesat ta sauke idonta tayi shiru, Aunty Farida tace "Junaid din ne Housemate din ki?" Khaleesat ta girgiza mata kai tace "Wanda suka zo tare" Aunty Farida tace "Ohk, tun daxu ai suka tafi kina bacci, ta yaya ya zama Housemate din ki?" Khaleesat na juya fruits din gabanta a hankali da fork tace "Gida daya muke da shi a America" Aunty Farida ta ɗan buda ido da confusion tace "Gida daya kuma? Kamar yaya? Amma ba kin ce makociyarki mace bace?" Khaleesat tace "Eh daga baya ta tashi daga apartment din, shi ne shi ya dawo gidan" Aunty Farida tace "Ikon Allah, shi kuma Junaid din a ina kika san shi?" Khaleesat tace "Cousin brothers ne ai, dalilin Housemate dina na san shi" Aunty Farida ta kafe ta da ido, Khaleesat ta sauke kanta bata boye ma Aunty Farida duk abun da ya faru tun daga dawowar Housemate apartment dinta, yanda ya biya mata kudin jirgi to and fro ta dawo Nigeria ta duba Umma, irin zaman da suka yi da shi da kirkin da yayi ta mata, har zuwa lkcn da Abdul ya zo kasar a karo na biyu da kuma abinda ya faru tsakaninsa da Ajay, da yanda suka maidata gidansu har ta gama Exams, babu abinda ta boye ma Aunty Farida hawaye na zuba idonta, Aunty Farida ta kasa cewa komai sai kallonta kawai take jiki a sanyaye, after almost a minute Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya tayi tagumi don she is just speechless bata san ma me zata ce ba, amma ta fahimci wani abu a labarin da Khaleesat ta bata..... Washegari wajen karfe goma na safe Jay ya bude kofar dakin Ajay ya samesa tsaye yana buttoning din shirt dinsa ya gama shiryawa, Jay ya jingina da jikin kofar dakin ya rungume hannu yana kallonsa calmly yace "You know what Ajay?" Ajay ya dau face cap dinsa ya saka, yana kokarin daura agogonsa a hannu yace "All ears" Jay yace "I think we shouldn't say anything to Abba akan kudin da muka yi magana jiya" Sai a sannan Ajay ya juya ya kallesa yace "Why?" Jay yace "Kasan zai yi querying dinmu about what we are using that huge amount of money for, i think gwara in amshi kudi wajen Mamina kawai, cause you know i can't lie to Abba idan yayi insisting akan abinda za mu yi da kudi haka, zan iya gaya masa me za muyi da kudin if he insist" Ajay ya masa wani kallo daga sama har kasa yace "Sannu saint, ita Mamin ce bazata yi querying dinka akan me zaka yi da huge sum of money din ba?" Jay yace "Yeah, but i know how to convince her" Ajay yayi wani murmushi yace "Mamin ce zaka yi convincing, i see" Bai jira amsar da Jay zai basa ba ya dau makullin mota da wayar sa ya bi gefensa ya fice daga dakin ya sauka downstairs, Jay ya bi sa da kallo, after a while ya jawo kofar dakin ya kulle sannan ya bi bayansa, Ummi dake zaune parlor ta bi su da kallo ganin alamar fita za su yi tace "Ina kuma za ku da safen nan?" Without looking at her a takaice Ajay yace "Bar beach" Ummi tace "Dama ana zuwa Bar beach da safe?" Ajay yace "Eh" daga haka ya fice daga parlon, Ummi ta kalli Jay tace "Wai Beach za ku?" Jay ya ɗan sosa kansa yace "A'a sai da yamma, yanxu dai kawai yawo za mu yi a gari" Ummi ta tabe baki tace "Ai shikenan, traffic ma kadai ya isheku, Mami ma suna hanya yau in sha Allah, sun ma kusa sauka" Jay ya sauke kansa yace "Eh haka tace min" Ummi tace "To sai kun dawo" Jay yace "Allah ya sa" Daga haka ya fita daga parlon, ya tarar da Ajay a mota yana jiransa, yana shiga motar Ajay yace "Ko ina ruwanta da inda za mu, ni bana son sa ido a rayuwata, shi yasa bana sauka gidanta a garin nan, i hate what i don't like" Jay yace "Ikon Allah, what's wrong with her asking us where we are going?" Ajay yace "That's very wrong, we are not kids da zata dinga tambayar mu inda za mu idan za mu fita, ko Abba baya controlling din mu yanda matar nan take yi, i don't think i am going back to that house zan je in kama hotel kawai" Jay ya girgiza kai yace "Kai fa matsala ne da kai kamar gidan haya, ni ban ga wani abu ba don ta tambayemu inda za mu da safe, it's normal ai" Ajay ya kallesa yace "To ni ba kai bane da ake controlling yanda aka ga dama a family, kai da kaga za ka iya sai ayi ta controlling dinka Jawwad" Jay bai sake ce masa komai ba, Ajay ya ja motar suka fice daga gidan. Da sallama Safiyyah ta daga buhun dake makale kofar shiga compound din gidansu Khaleesat, Mama Shatu da Mama Zubaida ne tsakar gida ko wacce na zaune bakin murhunta ana girka abincin talla hayakin icce duk ya cika ko ina na gidan, Mama Zubaida sai mita take an siyo masu jikakken icce, gaishesu Safiyyah tayi suka amsa ana mata wani kallo kasa kasa, Safiyyah ta tsaya suka gaisa da Labiba dake wanke robobin da za a zuba abincin siyarwa, sannan ta nufi dakinsu Khaleesat ta daga labulen ta shiga da sallama, zaune ta tarar da Umma ta jingina da bango hannunta rike da carbi ga kawarta Mama salame da wata Zaliha makociyarsu sai Sha'awa ita ma makociyarsu zaune dakin ko wanne yayi jigum, zaunawa Safiyyah tayi tana kallon Umma ko gaisheta bata yi ba ganin yanayinta tace "Umma baki da lafiya ne?" Umma tayi karfin halin cewa "Sannu da zuwa Safiyyah" Safiyyah ta gaisheta sannan ta gaida sauran mutanen dake dakin, ta sake maida dubanta kan Umma kan tace komai Mama Salame da ta san kawar Khaleesat ce ita tayi kasa da murya tace "Tsakaninki da Allah Sapiya baki san inda kawarki Khaleesah take ba?" Safiyyah ta zaro ido tace "Kamar yaya Mama?" Sha'awa ta gyara zama tace "Ae tun ranan asabar rabon da a saka Khaleesat a ido, daga ta dawo kasar waje ta tarar an daura mata aure da audallah washegari Asabar aka nemeta aka rasa, babu inda ba a shiga neman Khaleesah ba amma babu ita babu labarinta, jiya jiya yan sanda suka zo suka tafi da Malam Ali" Safiyyah da ta shiga wani shock jin wai an daura ma Khaleesat aure da Abdul ta ajiye jakarta a gefe ta dafe kirji tace "Wani Abdul din aka daura mata aure da?" Sha'awa na gyara barkakken zaninta tace "Audullah saurayinta dai da kika sani, ranan juma'an nan da ta wuce aka daura masu aure, tana dirowa kasar aka sanar mata shine ta gudu har yau babu ita babu labarinta, gashi an tafi da Malam Ali an kullesa" Safiyyah tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mikewa tayi tsaye ba tare da tasan tayi hakan ba tsabar shock din da ta shiga maganganun Sha'awa na yawo a kanta, hawaye ne ya cika idonta tana girgiza kai ta kasa cewa komai, ina jin bayan Khaleesat da tayi bakin cikin auren da aka daura mata da Abdul idan aka cire su Jay babu wanda yayi bakin ciki kuma irin Safiyyah, don ji tayi kamar an aza mata katon dutse a kirji tsabar bakin cikin wannan labarin, kawai ta fashe da kuka cike da tausayin kawarta, Abdul fa?? Housemate din Khaleesat ne ya fado mata a rai, nan Safiyyah ta dinga rera masu kuka kamar ita ce Khaleesat din, muryar Nenne suka ji a tsakar gida tana kunduma ma su Mama Shatu da Mama Zubaida zagi tana cewa "Wato har sararin kunna rubabbun murhun ku kuka samu a gidan nan baku dubi bala'in da ake ciki ba, ai in dai ɗa ne kowa ma ya haifa wallahi, yanda ku ke nuna halin ko in kula da abinda ya samu ɗa na ku ma dai kun haifi 'ya yan nan naga, shegu masu fararen kafafuwa tunda ɗa na ya auro ku yake shiga bala'i sinka sinka a duniya amma saboda baku da imani da tausayi ko wacce ta zauna bakin shegen murhun ta" Mama Zubaida ta kauda kai tana tabe baki tayi kasa da murya tace "Sai kuma yunwa ta kashe mu saboda yan sanda sun zo sun dauki Malam" Ita dai Mama Shatu sai juya miyarta take kar ya kone taki ko kallon inda Nenne take, Nenne na huci ta nufi dakin Umma ta dage labulen tana kallon cikin dakin tace "Saka dogon hijabi da rike carbi ba shine mafitarki ba Zahra'u, duk inda kika tura yarinyar nan waya kawai zaki buga masu ki ce ta dawo tun lamari bai lalace mana gaba daya ba, in ko ba haka ba wallahi sai a wanke daya daga kanninta a ba ma Awdul din tunda abinda yayi ta shi yayi su, in jar fata da gashi irin ta buzaye ne su ma duk suna da shi, babu abinda zata gwada masu sai shekaru tunda ta basu shekaru bakwai, don bazan zuba ido a karo na biyu ɗa na ya koma fursin ya tagayyara ba, Allah kadai yasan nawa na kashe wajen shige shige har Allah ya bamu mafita a wancan lokacin da aka kullesa, tun asali bata san bata son Awdul din ba sai bayan da ya kashe mata uban dukiya da bazai lissafu ba? Wace masifa ku ke son ja ma ɗa na ke da er ki a garin kano? Shi kadai fa ya rage min namiji sai mata, wallahi ki fito da ita Zahra'u in ya so su riketa a sake min ɗa na, nasan har da hadin bakin makirar tsohuwar can Gaje, yanxu kuma zan kama hanya in tafi Hotoron duk inda ku ka boye Khaleesah sai kun fito da ita baza ku kara ja min salalan tsiya ba, sha'awa taso ki rakani gidan tsohuwar banzan can Gaje" Da sauri Sha'awa ta mike ta figi baƙin gyalenta ta fita daga dakin ta bi bayan Nenne dake huci suka fita daga compound din gidan, Mama Zubaida da Mama Shatu suka saki guda a tare bayan Nenne ta fita, Mama Shatu ta kyalkyale da dariya tace "Ana yi muna hura murhu, ma ga dai karshen wannan dirama me dadin kallo a gidan nan, su buzuwa sai a koma dajin da aka shiga aka nemo maganin farin jini ayi ma Malam bayanin lamari ya kwabe, ba dai 'ya yanmu bane munana masu baƙin jini, maji ma gani dai" Umma dake jin duk abinda suke cewa ta jinginar da kanta da bango hawaye na sauka idonta Mama Salame na bata hakuri, Safiyyah dai jingina tayi daga bango a inda take tsaye hawaye na zuba idonta ita ma, ganin abun take kamar a mafarki wai an daura auren Khaleesat da Abdul, to amma ina Khaleesat zata tafi tun ranan Saturday ita da tasan Khaleesat ko kawaye bata da su a kano, Housemate ne ya fado mata, ta dau jakarta da sauri tana share hawayenta ta fita daga dakin Umma, Umma ta bi ta da kallo hawaye masu zafi na bin idonta daga ranan asabar zuwa yau har ta rame, ko abinci bata iya ci ta kira Aunty Farida yafi a kirga akan ta zo gareta ko zata ji saukin radadin da take ji a zuciyarta, Mama Zubaida da Mama Shatu suka bi Safiyyah da wani kallo suna tabe baki har ta fita daga compound din, Mama Zubaida ta matsa kusa da Mama Shatu da yake murhunsu kusa da kusa yake, tayi kasa da murya tace "Kin ga ki hakura da dafa waken nan da kika ce don gaskiya zai bata mana lokaci ga waje da nisa, gwara mu je a kara kada hankalinta taji ta tsanesa da auren kuma taki dawowa, in ya kama a kadata ta shiga duniya duk sai mu ce ayi, kudi ne dai zai yi kuka ba wani abu ba, kinga daga karshe in ma Labiba ko Lamisah duk wanda yace a basa duk daya ne a wajen mu babu banbanci, babu abinda zata gwada masu sai farin fata da uban gashi kamar na doki, in idanuwa ne su ma suna da shi, sannan suna da hancinsu dai dai gwargwado, tun asali kece kika yi ta makon fiddo kudi da ba a kai ga haka ba ma wallahi" Mama Zubaida ma tayi kasa da murya tace "Wallahi ban taba zaton aikin mutumin na ci haka ba Shatu, kinsan Malaman Jabu sun yi yawa yanzu sai dai ka kai masu kudinka su yi cefanen gidansu, shi sa kika ga ina ta ja da baya naki sakin kudi dama jarina ba jarin arziki ba, kinsan tun bayan rasuwar Malamin nan da yayi mana aiki kan Parida naki sakewa da Malamai don asaran kudi kawai mutum yake shi din dai ne malami gangariya amma mutuwa ta dauke mana shi kwatsam, gashi har yau duk uban kyan parida babu mashinshini tana can tana tuwo tuwo a Legas tana aiko ma yayar kudi kuma in sha Allahu a haka zata kare ga dai kyan da diri da komai amma babu mashinshini, to in anyi duniya don manzon Allah haka Khaleesar ma zata kare, amma yanxu tunda muka samu sabon Malamin nan naga aiki da cikawa kema kin san fiddo kudi bazai kara min wahala ba, ba gashi har na sa an amso min adashina ba daxu, in sha Allah sai mun karkato da hankalin Abdul kan 'ya yan mu, ko Labisah ko Labibah, ba dai kyau suke takama da shi ba wai su buzaye, to wallahi sai dai su ga ana aure....." Shiru Mama Zubaida tayi ganin Salame ta fito daga dakin Umma ta ci gaba da juya miyarta with serious face, Safiyyah na fita kofar gida ta ciro wayarta a jaka don tana da number Housemate, tayi dialing numbersa gabanta na faduwa tana hoping yasan whereabout din Khaleesat, jin Khaleesat take a ranta kamar er uwarta ta jini, she can't imagine halin da take ciki yanxu, yana fara ring Jay dake mota tare da Ajay ya daga wayar ganin Safiyyah ke kiransa yayi picking ya kai kunne calmly yace "How are you Safiyyah?" Da kyar Safiyyah tace "I am fine, ina kwana?" Yace "Lafiya lau, kin dawo Nigeria kenan?" Ta gyada kai da kyar tace "Pls tambaya nake son in maka Ya Jawwad" Jay yace "Ina jin ki Safiyyah" Safiyyah tace "Don Allah kasan whereabout din Khaleesat, wai tun Saturday ta bar gida har yanxu ba a san inda take ba, yanxun nan na zo gidansu nake samun labarin" Hawaye na zuba idonta ta kare maganar, a hankali Jay yace "Halysaah?" Lkci daya Ajay ya juya ya kallesa, sai kuma ya fixge wayar ya katse ya ajiye, Jay dai kallonsa kawai yake, can yace "Kawarta ce fa" Ajay yace "And so? Assignment din announcing whereabout dinta aka baka ne? Me yasa baka da sirri ne kai?" Jay yace "But it's nothing, kawarta ce kuma tana sonta sosai, nasan bazata gaya ma kowa komai ba" Ajay ya dau wayar jin ya fara ringing, yayi rejecting call din Safiyyah sannan ya saka wayar a silent ya zura a aljihunsa yace "Dama ka saba tona ma mutane asiri kayi ruining plan dinsu ai" Jay yace "Bani wayata malam" Calmly Ajay yace "Bazan bayar ba" Dai dai sanda Ajay yayi parking a kofar gidan Aunty Farida ya kashe motar ya sauka ya bar Jay a ciki. Nenne na isa kofar gidan Gaje tare da Sha'awa er rakiyarta suka ga yan sanda biyu kofar gidan Gaje da motarsu, ga yan unguwa sun tsaya cirko cirko ana salallami, Nenne ta ja burki inda take tsaye tana gwaggwale ido sai ga wata er sanda ta kado keyar Gaje sun fito daga cikin gidan, Gaje na rusa kuka cikin rudewa take cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wallahi ban san inda take ba tsakanina da Allahn da ya halicce ni, in nasan inda take Allah ya tsine min albarka, Al-qur'anin Allah babu abinda na hada da ita ba dangin iya ba na Baba haduwar gidan duniya ne kawai, don manzon rahama ku min rai ban hada komai da ita ba" Er sandar tace "Amma ai an ganta ta shigo gidan ki ranan asabar da daddare, iya gaskiyar ki kadai ne zai cece ki a wannan case din aki kai ki furson, in kuma kika ce zaki ci gaba da karya zaki ga illar karya kuwa" Cikin tashin hankali zufa na keto ma Gaje ta ko ina tace "Wallahi zan fada gaskiya ku tsaya ku saurareni, tsakanina da Allah ta zo gidana da daddare wajen karfe goma tace in rufa mata asiri amma bata gaya min abinda ke faruwa ba, ni kuma da na tashi sai na kai ta gidan wata er dakina Sadiyah Chamo, Sadiyah ce ta bata mafaka a gidanta ta kwana, kashegari kuwa ta kira wani gingimemen mutumi a wayarta ya zo da katuwar motarsa ya dauketa suka tafi inda ban sani ba, idan na maku karya a wannan zance kada Allah yayi min rahama" Er sandar tace "Ina gidan Sadiyar yake?" Jiki na rawa Baba Gaje ta nuna hanyar gidan Maman Fu'ad, er sandar tace "Shiga mota mu je ki nuna mana gidan" Gaje ta rushe da kuka tana cewa "Na shiga uku na lalace ni Al-haqqatu na ja ma kaina masifa a garin kano" Bayan mota aka bude ma Gaje tana kuka ta shiga er sandar ta dago mata yakunannen gyalenta dake jan kasa ta dora kan cinyarta sannan ta shiga bayan motar ita ma, tuni Nenne ta juya sum sum tun ba a lura da ita ba ta shige wani layi, sai juyawa sha'awa tayi taga gefenta wayam babu Nenne..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Alhamdulillah! Shin kunada labarin MG’s Beauty Lounge zai buɗe a ranar Litinin, 2nd June 2025 – daidai lokacin Sallah!😍 ‘Yan mata da mata masu son kyau a Kaduna, lokaci yayi da za ku haskaka a wannan Sallah! MG’s Beauty Lounge ya buɗe da kwalliya, tsafta da ƙamshi irin na sarauniyar zamani! Ga abin da zaki samu idan kika ziyarce mu: Gyaran gashi da kitson zamani Kwalliyar Sallah mai ɗaukar ido Wanke ƙafafu da pedicure mai sanyaya rai Kayan gyaran fata na gaske Lalle mai kyau da salo na zamani Tura-turai, humra, incense da ƙamshi masu daɗi Shirin amare da na musamman Ba kawai gyara muke ba – kulawa ce ta musamman ga kowace sarauniya. Zo ki ji daɗin wanke ƙafa, lalle, kwalliya, ki saya kayan kyau da ƙamshi – komai a wuri guda mai kyau. Adireshi: Block 21, Nnamdi Azikiwe by Makarfi Road, bayan gidan Indomie, kusa da Sorera Restaurant, Kinkinau, Kaduna. Tambaya/Booking: WhatsApp: 08062991549 Kira: 09016108092 / 08064532391 Ki zo ki gani da idonki – ki ji daɗin sauyin MG’s Beauty Lounge. Bi mu a IG & TikTok: @MGsBeautyLounge HALYSAAH 35 A hankali Khaleesat ta ɗan bude curtain din dakin Aunty Farida tana leko cikin parlon ta hada ido da su gaba daya, sauke idonta tayi ta shigo parlon walking slowly ta tafi ta zauna kan kujera kanta a kasa, tun da taji sallama ta tashi ta tafi dakin Aunty Farida don saka Hijab dinta, gaishesu tayi still not looking at them, Jay ne kawai ya amsa yana kalllonta calmly yace "How are you feeling now Housemate?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa a hankali tace "I am much better now" Kallon Ajay tayi suna hada ido ta sunkuyar da kanta tace "Ina yini?" Yana danna wayarsa yace "Fine" Aunty Farida ta shigo parlon daga kitchen ta ajiye masu tray din Can drink da ruwa da taje dauko masu, sannan ta zauna kan kujera tana kara gaishesu, Jay yace "Ya me jiki" Aunty Farida tace "Da sauki, abinci ne dai bata ci har yanxu" Jay ya daga kai ya kalli Khaleesat, sauke idonta tayi ta dau plate din abincin da Aunty Farida ta zuba mata not long ago, ta bude murfin ta ajiye sannan ta dau spoon ta fara cin abincin a hankali, Aunty Farida na kallonsu tace "Bari in kawo maku abinci" Ajay ya kalli Jay, Jay yace "A'a mun yi breakfast Aunty, mun gode" Aunty Farida tace "To ai rana tayi yanzu" Bata jira taji me zai ce ba ta tafi kitchen zata zubo masu abincin, ita dai Khaleesat a hankali take cin abincin hannunta, mikewa Ajay yayi, Jay ya sa hannu a aljihunsa ya ciro wayarsa, Ajay yace "Zan yi waya a waje" Daga haka ya fita daga parlon kafin Aunty Farida ta fito daga kitchen, Jay yayi murmushi bai dai ce komai ba, bude wayarsa yayi yaga miss calls din Safiyyah har shidda, yayi dialing number dinta ya saka handsfree, yana fara ring Safiyyah ta daga kamar jira take, yayi kasa da murya yace "Can you hear me Safiyyah?" Tace "Ina jin ka, plss ba a san inda Khaleesat take bane tun ranan asabar, kuma ni nasan bata da inda zata je a garin kano" Yace "Where are you at now?" Da sauri tace "Nima a kano nake ai, jiya da yamma na dawo daga Maryland shi ne na zo gidansu yau nake samun labari she is away from home tun ranan Saturday after receiving the news of her marriage with Abdul, wai Abdul fa aka daura mata aure da" Safiyya na kai wa nan ta fashe da kuka, Jay yace "I mean are you at home or where?" Cikin kuka tace "A'a yanxu na baro gidansu, ina bakin titi ma haka, i am just confuse, Khaleesat bata da kawaye bata zuwa ko ina, i don't know where she will be now, i am disturb don Allah in kasan inda take kar ka boye min plss Ya Jawwad trust me" Calmly yace "Look, this should be confidential Safiyyah, i trust you are saying nothing to anybody about this...." Da sauri Safiyyah tace "Na rantse babu wanda zan ce ma komai Ya Jawwad, trust me, i am also not in support of the fruitless marriage" Jay yace "Ohk, here is ur frnd speak to her....." Mikewa yayi ya mika ma Khaleesat wayar, ta amshi wayar tana kallon screen din dama tun jiya take wishing ace Sophie na kusa da ita ko ba komai zata dinga Consoling dinta tana karfafa mata gwiwa da bata assurance, lkci daya hawaye ya cika idonta cikin rawan murya tace "Sophie" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Khaleesat, i am so happy you are safe and sound, dama fatana kenan, plss kina ina haka yanxu in taho don Allah" Khaleesat ta girgiza mata kai cikin sanyin murya tace "Bana kano Sophie" Da mamaki Safiyya tace "To kina ina?" Khaleesat ta daga kai ta kalli Housemate dinta dake kallonta, sauke idonta tayi da kyar tace "Ina Lagos" Safiyyah tace "Lagos wajen wa? Ko wajen Aunty Farida?" Khaleesat tace "Um" Safiyyah tace "Amma Umma bata san kina nan ba" a hankali Khaleesat tace "Bata sani ba" Safiyya ta sauke wani ajiyar zuciyar tace "Pls kar ki tada hankalinki kinji kawata, i know ur Housemate won't allow u do that, kuma in sha Allah babu zaman aure tsakaninki da Abdul don bai yi deserving din ki ba, i can't imagine what he will turn you into, in Allah ya yarda bazai ci nasara akan ki ba, Allah zai raba auren cikin gaggawa, shi kadai yasan mugun Intention din dake ransa akan ki shi yasa yayi haka, amma Allah ya fi sa" Khaleesat dai gyada mata kai kawai take hawaye na sauka idonta ta kasa cewa komai, Housemate dinta ya mike ya nufeta ya amshi wayar a hannunta ya koma ya zauna yace "Safiyyah" A sanyaye Safiyyah tace "Na'am Ya Jawwad, Please kawata bata da wanda zai tsaya mata akan issue din nan, ba da intention me kyau ya saka aka daura auren ba wallahi, mugu ne azzalumi, har abusing dinta yana yi" Jay dake sauraronta yace "In sha Allah we will try our very best ki taya mu da addu'a" Safiyyah tace "In sha Allah, but how can i be reaching her?" Yace "Don't you have her aunt's number" Safiyyah tace "Sure ina da shi, i will be calling her ta wayar Aunty Farida" Jay yace "Keep this confidential pls Safiyyah" Safiyyah tace "Trust me Ya Jawwad, i now have rest of mind knowing my frnd is safe" Da haka suka yi sallama ya ajiye wayar, Khaleesat ta ajiye plate din abincin hannunta don ta kasa ci, iya spoon uku kawai ta iya yi, tuni Aunty Farida har ta ajiye ma Jay abincin da ta zubo ta nemi waje ta zauna, sai da ta jira suka gama waya da Safiyyah sannan ta kallesa tace "Ina Junaid din ga abincin na zuba maku" Jay yace "Aunty bamu dade da cin abinci ba da gaske" Aunty Farida tace "Ai ko in baku ci ba bazan ji dadi ba, haka jiya ku ka bar min abincin ku ka ki ci, yanxu fa karfe biyu da rabi ake nema kuma breakfast kace kawai ku ka yi" Jay dai murmushi kawai yake, can yace "Toh zan ci Aunty" Tace "To ko kai fa, ina Junaid din kayi masa magana ya shigo ku ci" Jay na shafa kansa yace "Ai shi ya ci snacks a mota bazai ci abincin ba na sani, bai fiye cin abinci da rana ba" Aunty Farida tace "Ikon Allah to saboda me?" Jay yace "Haka yake, iya breakfast da Dinner kawai yake yi" Aunty Farida tace "Iko sai Allah" Jay na kallon abincin da Khaleesat ta rage ya mike ya dauko yace "Zan ci wannan kar mu bata abincin Aunty" Aunty Farida tace "Don Allah ka ajiye ka debi abinci ga plate nan Jawwad" Yace "Aunty wannan fa ya isheni ba iya cinyewa zan yi ba ma" Spoon din ya dauka ya fara cin abincin, Khaleesat dai kallonsa kawai take, Aunty Farida tace "Ai shikenan" Karfe uku da yan mintuna Ajay da Jay suka bar gidan, Jay ne ke driving din idonsa akan titi yace "To ya ku ka yi da Lauyan?" Ajay yace "He said we should meet in kano" Jay ya ɗan kallesa yace "Zuwa gobe kenan?" Ajay yace "Sure, tomorrow in the morning za mu tafi kano" Jay bai sake cewa komai ba har suka isa gida, yau dai traffic din da ɗan sauki, bayan Jay yayi parking ya juya yana kallon Ajay yace "Please since gobe za mu tafi kano ka bar maganar hotel da kace zaka koma" Ajay yace "Ai matar ne ta fiye takura da sa ido" Jay yayi dariya bai dai ce masa komai ba suka sauka zuwa cikin gidan, Ummi na zaune parlon Hadeeyah na kwance kusa da ita da daura kanta a saman cinyar Ummin, ba tare da Ajay ya kalleta ba ya gaisheta a takaice zai wuce sama Hadeeyah ta gaishesa ya amsa yana haura stairs, Jay ya zauna parlon ya gaida Ummi ta amsa tace "Sai yanxu? Ko dai ba Bar beach din ku ka je ba?" Jay ya ɗan buda ido yace "Mun fasa" Yana magana ne yana kallon Hadeeyah da ta hade rai tana danna wayarta kamar bata gansa ba, Ummi ta kalleta tace "Ke baki ga yayanki bane" Hadeeyah na ci gaba da danna wayarta tace "Oh, ok, Good evening" Jay yace "Ya hanya?" Tace "Lafiya lau" Ummi na kallonsa tace "Mami tana sama" Jay ya mike yace "Ohk" Sama ya wuce, Hadeeyah ta bi sa da kallon gefen ido har ya fara hawa stairs, bayan ya tafi Ummi na kallon Hadeeyah tace "Fadan ku ka sake yi kenan?" Hadeeyah ta ɗan yatsine fuska taki cewa komai tana danna wayarta, Ummi ta kyabe baki tace "Kun fi kusa dai" Jay na bude kofar dakin da yasan Maminsa na ciki ya sameta zaune tana waya, ya karasa ya zauna kusa da ita yana kallonta yayi mata side hug ya jinginar da kansa a shoulder dinta a hankali yace "Mami" Mami tayi ma warce suke wayar sallama ta ajiye wayar hannunta tana kallonsa tace "Ina ka je tun safe Son? I was thinking zaka zo airport kayi picking din mu" Jay ya ɗan kalleta yace "Karfe nawa ku ka iso Mami?" Tace "Karfe sha daya da rabi na safe" Jay yace "Mun fita ne da Ajay, Ummi bata gaya maki ba" Mami tace "Kaga da ubansa ne zai sauka Lagos duk abinda yake yi barin sa zai yi ya tafi ya taro sa, amma kai uwarka ta sauka Lagos ya ja ka kun tafi gantali" Jay bai ce mata komai ba, Mami na kallonsa tace "Duk karatun ne yasa ka fada haka? Are you okay?" Jay yace "Stress din tafiyar da nayi zuwa Nigeria ne" Mami tace "Nasan shi zai zugaka ku dawo Nigeria kar ka biyo min ta UK" Jay ya ɗan hade rai yace "Ya fa riga ni dawowa Nigeria Mami, ni ba jiya na dawo ba, shi kuma ai tun last week yake Nigeria" Mami ta tabe baki bata ce komai ba, Jay ya mike ya nufi kofa yace "Zan je inyi wanka" Mami tace "Dama gobe ka shirya mu tafi Bauchi ban san gantalin da yake jan ka ku ke yi a Lagos ba, kai da ko ance ka sauka Lagos baka taba yarda sai gashi saboda Junaid na lagos kai ma ka zauna a lagos, to gobe za mu tafi Bauchi kuma Hadeeyah ma a can zata yi hutu" Jay ya juya ya kalleta yace "Mami ni ban gama abinda nake yi ba, kawai ku yi tafiyar ku" Bai jira me zata ce ba ya fice daga dakin. Wajen karfe biyar da rabi Jay da Ajay suka sauko downstairs, dakin dake kasa suka nufa don Mami na ciki tare da wata bakuwarta warce suka hadu da dadewa a Saudia suna zumunci sun zama kaman en uwa, jin Mami ta shigo Lagos sai matar ta taho gidan gaida Mami tunda ita ma a Lagos din take, Ajay ya zauna kan 1 sitter dake dakin ya gaida Mami sannan ya gaida frnd dinta, Jay ma ya zauna ya gaida kawar Maminsa, matar me suna Hajiya Batula ta amsa da fara'a tana kallonsu sai kuma ta kalli Mami tace "Wanne ne son din naki a ciki Hajiya?" Mami tayi pointing Jay tace "That is my son" Matar na kallon Jay tace "Maa sha Allah, ai kuwa ga kama na gani" Shi dai Ajay danna wayarsa kawai yake bai dago kansa ba, Jay ya mike yace "Mami za mu je Gym ne" Mami ta kallesa tace "Da yamman nan ga uban traffic din Lagos ne zaka je Gym?" Jay yace "Ai ba nisa Gym din" Hajiya Batula tace "Nan Area din ma ai da Gym ba sai sun je da nisa ba" Jay ya kalli Ajay yace "Mu je" Mikewa Ajay yayi ya nufi kofa Jay ya bi bayansa suka fice daga dakin, Hajiya Batula tace "Amma ɗan uwansa ne wannan din ai ko, naga suna yanayi sosai" Mami tace "Eh Cousin dinsa ne" Hajiya Batula tayi kasa da murya tace "Ko dai shi ne ɗan sarkin dai?" Mami ta tabe baki tace "Shi ne" Hajiya Batula tace "Ya sunansa?" Mami tace "Sunansu daya Ahmad amma Junaid ake kiransa" Hajiya Batula tace "Ikon Allah, shi kam Jawwad babu ruwansa..." Cike da takaici Mami tace "Ni babban bakin cikina yanda har yanxu Jawwad bai san ciwon kansa ba, hakan na ci min tuwo a kwarya wallahi, controlling dinsa kawai yake yana bin sa, ko a America din ma Junaid din ne ke juyasa" Hajiya Batula tace "A'a gaskiya bai san ciwon kansa ba naga alama, shi ko kishi baya yi, kuma gaskiya Mai martaba ya nuna son kansa a fili karara nada ɗan sa da yayi Yarima me jiran gado a maimakon Jawwad, ina ce Jawwad din ya girmi ɗan sa?" Mami tace "Ya basa watanni har uku" Hajiya Batula ta rike haɓa tace "Amma in tambayeki mana Fulani, bayan rasuwan mahaifin Jawwad wato me martaba Sarki Ahmadu Yusuf shi brother din nasa wanda shi ne sarkin yanxu bai nemi rikon Jawwad a gabansa ba?" Mami tayi shiru, can tace "Cikin Jawwad na da wata bakwai mahaifinsa me martaba ya rasu aka nada kaninsa wato mahaifin Junaid, dama su uku ne gun babansu Sarki Yusuf Ibrahim, daga Mahaifin Jawwad wanda shi ne babba sai Mahaifin Junaid sannan Maimuna warce nake gidanta yanxu suna kiranta da Ummi...." Hajiya Batula tace "Ikon Allah, to amma...." Shigowar Ummi dakin ne yasa Hajiya Batula tayi saurin canza topic din tace "Yanxu goben za ki koma Bauchi kenan Hajiya?" Mami tace "In sha Allah" Ummi ta ajiye plate din hannunta tace "Sannun ku, gashi nan kaza na tsaya gasa maku" Hajiya Batula na murmushi tace "Allah sarki, sannu da aiki" Ummi tace "Bari in kawo maku drinks din, a can parlor mai aikin ta ajiye" Daga haka ta fita daga dakin, Mami tace "Da ma kin ci gaba da maganar ki, ita ma ai bata so Junaid din da aka nada Yarima me jiran gado ba" Hajiya Batula tace "To ke sai kika zuba ido aka yi hakan Fulani? In uban Jawwad din bai mutu ba a ina kanin nasa zai samu har yayi sarauta? Kuma shine bazai yi kara ya nada ɗan yayansa da ya mutu ya bar masa sarautan Yarima me jiran gado ba sai ya nada ɗan cikin sa?" Mami tayi wani murmushi tace "Ni fa ko a jikina hakan da aka yi, Jawwad is doing fine beside shi mulki ma baya gabansa, as far as my son is okay, i think da a nada sa Yarima da kar a nadasa duk daya..." Hajiya Batula tace "To halan Junaid din kadai sarkin ya haifa?" Mami tace "Wani Junaid? Amaryarsa da suke kira da Aunty na da ɗa me shekara 29, ita in son samu ne ma a nada ɗan ta Yariman ai" Hajiya Batula ta rike haɓa tana kallon Mami. Ajay yayi parking kenan bayan sun dawo gida wajen karfe bakwai na dare ya kalli Jay zai yi magana wayarsa ya fara ring, ya dauka yana duba me kiransa ganin number wani abokinsu ne da kamar bazai yi picking ba kawai sai kuma ya daga ya kai kunne, after few seconds of listening to what the frnd was saying ya zaro ido yace "What???" Kallonsa Jay yayi da sauri don intonation din da yayi using ya nuna ba lafiya ba, Da kyar Ajay ya cire wayar a kunnensa yana kallon Jay dake kallonsa shi ma babu ko kiftawa, Nan da nan Jay yaji hankalinsa ya tashi don babu inda mind dinsa yaje immediately sai gun Khaleesat, Ya fixge wayar hannun Ajay yace "What's happening plss?" Ajay ya kasa cewa komai tsabar yanda ya girgiza, Jay ya shiga call logs din wayar da sauri yaga Adams abokinsu ne ya kira nan yaji hankalinsa ya ɗan kwanta don yasan ba abu bane da ya shafi Khaleesat, dialing number yayi amma har ya gama ring ba a daga ba, a hankali Ajay yace "Salim aka harba" Jay bai san sanda ya ajiye wayar hannunsa ba yace "What? Harbi kuma? Is he dead?" Ajay ya dau wayarsa shi ma ya kara dialing number Adams amma har ya katse bai daga ba, available flight to kano ya fara dubawa immediately..... _Barka da sallah everyone, Allah Ubangiji ya maimaita mana Ameen, ina nan ina baza ido ina jiran goron sallah na🙄_ *Next update sai bayan an gama suyan nama*😁 *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 36 Washegari sai da rana Ajay da Jay suka samu ganin Salem a hospital din da aka yi admitting dinsa, iya kafadarsa ne kadai aka nannada ma bandage alamar a nan aka harbesa amma duk kamanninsa ya canza alamar ya ci duka ba na wasa ba, Jay ya zauna kujeran dake kusa da gadon yana kallon Salem that was in pain yace "Hasbunallah, How did this happen Salem?" Shi dai Ajay na tsaye ya rungume hannu shi ma yana kallon Salem ganin yanda aka canza masa kama, ya ma kasa cewa komai, Salem dake kishingide jikin pillow da kyar don ko iya motsa kafadarsa daya baya yi ga duk jikinsa yayi tsami yayi karfin halin cewa "Ban san su ba suka yi attacking dina" Jay yace "Har gida suka same ka?" Salem ya girgiza kai yace "I stayed out late yesterday in wudil naje gurin wani abokina, he insisted i stay till the next day amma saboda ina da abun da zanyi washegari da safe a kano sai naki kwana a garin muka yi sallama da shi, bayan na kusa unguwan da nake da zama sai na lura da wata mota na biye dani a baya amma ban yi tunanin komai ba na zata ya shigo layin ne bai san hanya ba shine yake bi na ko nima fita zanyi daga unguwan mun fita tare, bayan na shigo layin mu babu kowa saboda dare yayi tun kan ma in sauko daga motata in shiga gida in bude gate sai nake ma motar alama da hannu ya tafi gaba zai samu hanya, sai kawai matukin motar ya fito ya nufo ni, duk da haka ban wani damu ba na zata direction zai tambayeni, na tsaya har ya iso dai dai gabana ban ankara ba kawai sai jin saukan naushi nayi ta ko ina a fuskata ina kokarin defending kai na sai sauran mutane ukun dake cikin motar suka fito su ma suka hau dukana ta ko ina at the same time they were asking me about a girl i know nothing about, wai inyi providing dinta ko su kashe ni" Da wani expression Jay ke kallonsa, sai kuma ya mike da sauri ya dafa gadon da Salem yake kai yace "A girl?" Salem ya gyada kai da kyar yace "Wai Khaleesat, ni ban ma taba jin sunan ba wallahi, suka yi ta dukana wai sai na fadi inda take ko su harbeni" A tare Ajay da Jay suka kalli juna, Salem yace "Kashe ni suka yi niyyar yi banda Allah ya rufa min asiri kururuwan da nake yi wani soja dake kusa da gidanmu ya fito da bindiga, da wani makocina da ya fito da adda, kafin makota na su fito ne suka min harbi har biyu daya ya sameni a kafada daya kuma bai sameni ba ya sami gate, sojan da makoci na suna fitowa suka shige motarsu suka tsere, ni wallahi ban taba jin sunan yarinyar da suka ambata ba ma" Aunties din Salem biyu ne suka shigo ward din da sallama, Ajay ya gaida su sannan ya fita daga ward din ya tafi haraban asibitin ya zauna, after almost 10 mins Jay ma ya fito, inda Ajay ke zaune ya nufa ya zauna bai dai ce masa komai ba, Ajay yayi breaking silence din yace "He is tracking me, ni yake nema ba Salem ba, but tana da number Salem a wayarta ne?" Jay ya sauke wani ajiyar zuciya yace "Yawanci shi take kira ya bani waya if there is anything she wants to tell me, ko number ka ma ai Salem ne ya tura mata, instead cewa zaka yi he is tracking the both of us tunda nima ta kira layina ai ranan, but how did he get Salem's line?" Ajay yayi murmushi yace "Definitely layinta ya sa a duba masa numbers din wa enda take waya da, and he is using that to track us" Jay ya mike yace "We need to take down our sim card AJ, decidedly zai samu information mun shigo kano since we are in his list, sannan i think before anything ya kamata mu fara fighting for her innocent father's release tunda ita Halysaah yanxu bai san inda take ba and she is safe where she is, but the Man needs help" Ajay yace "No, i don't think she is safe with her aunt, although aunt din tace bai san inda ta koma ba amma as far as yana da number wayarta zai iya sakawa ayi tracing din inda take ita ma" Jay ya juya yana kallonsa yayi shiru, he just realize of course hakan zai iya faruwa cause ya daina underrating Abdul yanxu, Jay ya sauke wani ajiyar zuciya yace "That guy is something else Ajay, duk wata salon mugunta ya sani adding it to his career skills, ina jin kawai a duba mana if there is flight zuwa Niger republic a biya masu kawai su tafi can da aunt dinta har zuwa sanda za mu gama da Case din dad dinta, in the other hand shi kuma mun yi sue dinsa requesting for divorce for her" Ajay yayi shiru, can yace "But what if she is needed in court?" Jay yace "For now her lawyer will represent her, in ma an bukace ta a court we will sort that out" Jay yace "I think that's cool, amma ya kamata mu je gidan su gun mahaifiyarta" Ajay dai kallonsa kawai yake, can yace "Is that necessary?" Jay yace "Of course, kasan aunt dinta tace mana the mother is not medically fit, kada wannan damuwar yayi weighing dinta down" Ajay yace "Sai mu je a matsayin su wa?" jay ya mike yace "Human right" Abdul na tsaye rike da takardan da mahaifiyar sa ta mika masa daga shigowar sa parlor idonsa na kan takardar yana karanta content din jiki, Meema yayarsa ma na zaune parlon tana kallonsa fuskarta dauke da bacin rai karara, wani murmushi Abdul yayi ya cukuikuye takardar ya jefar kan kujera, Mahaifiyar sa dake ta kallonsa ta tabe baki tace "To yanxu menene amfanin wannan tozarcin da kaskantar da kai da ake yi? Sam kace kai baza ka ji maganata ka dau shawara ta ba Abdallah?" Meema ta katse ta tana kallonta a fusace tace "Haba Momy ta yaya kike son ya ji maganarki bayan uban kudin da ya kashe ma tsinanniyar shegiyar yarinyar? Ai jin maganar ki ba nasa bane wallahi, kuma don an kawo masa sammaci ba shi ke nufin ya hakura zai saketa ba, kotu ce kawai za a shiga ayi ta gwabzawa, kuma in sha Allahu duk inda kafafuwana za su shiga sai na shigar da su don Abdallah yayi nasara a wannan case din, bazan taɓa bari a tozarta min kanina ba ga mari ga tsinka jaka bazai taɓa yiwuwa ba wallahi, alamar koma waye ya zugata ta yarda aka yi karansa zai iya biyan ko nawa aka ce ya biya a kotu, kai jama'a amma yarinyar nan anyi babbar er iska butulu, dama ni tun asali ban goyi bayan da yace zai kai yarinyar nan Amurka ba ina jiye masa tsoron kar idonta ya bude, to gashi nan bayan karatun har da karuwanci ta dinga yi da manyan kasar nan tunda gashi har ta samu wanda zai tsaya mata da lauya ya biya makudan kudin da aka kashe mata kilan yace har da miliyan 100 da ubanta ya salwantar, abun arziki dai bai amshe mu ba a family din nan, ban ga laifin ki da baki son talakawa ba Momy, shi yasa nima bana son su na tsane su" Momy dai girgiza kafa kawai take tsabar takaici da bakin ciki ta kasa cewa komai, Meema ta kalli Abdul daka safa da marwa a parlon yana ɗan murmushi tace "Ka kwantar da hankalin ka Abdul, as far as ina numfashi kuma uwar mu na numfashi ko don ka rama duk abinda yarinyar nan tayi maka za mu shiga mu fita har sai kotu ta baka ita, in sun san wata ai basu san wata ba, koma waye ke taka mata baya daga karshe kashe kudadensa kawai zai yi a banza don sai ta shigo gidan nan mun ci ubanta da izinin Allah, banda kaddara me ma zaka yi da er gagurumin barawo kuma makaryaci, daga basa dukiya ya kai Lagos yace an kwace mota" Sama Abdul ya wuce kamar zai tashi sama, Momy ta bi sa da kallo cikin bacin rai tace "Kai Allah Ubangiji ya tsine ma mutanen nan albarka, yanda suka sa ɗa na a damuwa Allah ya saka duk zuri'arsu a damuwa, ita kuma yarinya Allah ya kasheta ma duk mu huta, tun da lamarin nan ya faru ko abincin kirki Abdallah yaki ya zauna ya ci a gidan nan, in ya fita tun safe sai dare muke ganinsa gaba daya ba shi da sukuni akan er talakawa, wannan wani irin iftila'i ne ya same mu" Meema tace "Tashi tsaye kawai za mu yi ayi abinda ya kamata Momy, gidan nan ai kamar ta shigo sa ne in sha Allahu, da bakinta zata ce ita ta hakura a kai ta gidan mijinta kawai, kuma ta shigo nan ta same mu muna jiranta" Daga haka Meema ta mike ta bi bayan Abdallah. Jay na zaune tare da Ajay a office din lauyansu suna sauraron sa, lauyan yace "He is trying to re-litigate a case already resolved in court, don an riga an rufe case din a kotu tunda yace ya yafe, har lauyoyinsa sun yi filing notice of discontinuance kuma kotu tayi approving sannan ta kulle case din ta yi releasing debtor dinsu from any further liability, but like seriously ban san wani irin lauya bane ɗan sa, don har da written confirmation of debt forgiveness da suka yi a kotu duk yana nan, why let them arrest the man again? Ko dai ɗan nasa bai gaya masa consequences din hakan da yayi bane cause this is pure abuse of process and malicious prosecution" Jay yace "To yanxu meye abun yi Barrister?" Lawyern ya ajiye pen din hannunsa yace "Za mu yi Filing motion to dismiss the already forgiven case, and we will plead abuse of process, sannan muyi Raising estopped from pursuing the debt again in near future, just that za mu yi presenting documentation of the original debt forgiveness and court records to the court, wannan ma ai sun yi breaching court order ne kuma hakan laifi ne me zaman kansa" Ajay yace "That is because suna ganin ba shi da wanda zai tsaya masa ko shekara nawa zai yi a kulle, his family have no voice to do so, that was why the breached the court order for their selfish interest" Lauyan yace "Babu matsala in sha Allah za mu shigar da kara kotu, and the man will be bailed out while the case is going on, they will even have to pay him damages...." Bayan la'asar Ajay yayi parking a kofar gidansu Khaleesat, dai dai inda yayi parking ranan da suka yi dropping dinta da daddare, a bayansu kuma wata mota ce ita ma tayi parking, Guard uku ne suka fito daga cikin motar dukkansu suka yi tsaye jikin motar da suka sauka, shi dai Jay kallon unguwan kawai yake, Ajay ya bude mota ya sauka, ya jingina da motar ya rungume hannunsa, Jay ma ya sauko sannan ya zagayo inda Ajay yake tsaye yace "Where is the house?" Ba tare da Ajay ya kallesa ba yace "Gashi nan kana kallo" Jay ya kalli gidan dake opposite dinsu, wani almajiri ne ya zo wucewa Ajay ya kirasa, yaron ya taho da sauri Ajay yace "Shiga cikin gidan can kace ana sallama da Maman...." Sai kuma ya kalli Jay alamar ya fadi sunan, Jay na kallon almajirin yace "Kace ana sallama da Maman Halysaah" Almajirin yace "Toh" Da sauri ya nufi gidan, Ajay yace "Meye kuma Halysaah? How is that even a name? In zaka kira sunanta na asali kawai ka kira" Jay na kallonsa yace "Meye sunan nata na asali?" Ajay bai kallesa ba har sannan yace "Ka fi ni sani ai, tunda ka fi kusa da ita" Jay ya ɗan yi murmushi bai sake ce masa komai ba, Nenne ce ta leko kofar gidan tana zazzare ido kuma bata yarda ta fito waje ba, tana yin ido hudu da su Jay sannan ga wasu samudawa da ta gani har uku tsaye jikin wata motar ta juya ta koma cikin gidan da sauri har tana tuntube, sai ga Mama Zubaida tana gyara gyalenta da ta yafa akan daurin kirjin da tayi, Mama Shatu na bayanta tana kokarin saka hijabinta ta bai bai, tsaye duk suka yi daga cikin gidan suna leko su Ajay da samudawan dake jikin mota a tsaye, Mama Shatu tayi karfin halin cewa "Ina wuninku?" Jay ne ya karasa har inda suke tsaye, shi dai Ajay na rungume da hannunsa yana kallon ikon Allah, Jay ya gaishesu duk suka amsa kamar munafukai suna gwale ido, Jay yayi kasa da kai yace "Mahaifiyar Halysaah mu ke son gani" Da sauri Mama Zubaida tace "A'a to ku shigo mana, Bismillan ku ai tana ciki, fakewa kawai suka yi da cewar bazata iya fitowa ba bata da lafiya, lafiyarta lauz ku shiga har dakin ku sameta" Duk tunaninsu an zo tafiya da Umma ne kamar yanda aka zo aka tafi da Malam Ali, Jay ya juya ya kalli Ajay dake jin duk conversation din su daga inda yake tsaye, ko ba a gaya masa ba yasan stepmom din Khaleesat ne matan, ya kulle motarsa yana kallon wa enda ke tsaye jikin mota yayi masu alamar da cewar za su fito in 5 mins sannan ya karasa har inda Jay ke tsaye yana jiransa su shiga gidan, su Mama Zubaida kuwa har sun koma tsakar gidan sun tsaya cirko cirko suna jiran su ga yanda za a shigo a fitar da Umma, da hannu suka nuna ma Jay da Ajay hanyar dakin Umma, Jay ne yayi sallama bakin kofar dakin, shi dai Ajay na tsaye a gefe yana kallon white t-shirt dinsa to be sure ruwan taɓon da yayi gaja gaja a compound din bai fallatsar masa a jiki ba, Mama Shatu da Mama Zubaida a tsakar compound din suke zubar da duk wani ruwan da suka yi aiki haka ma yaransu, sun maida compound din kamar na mahaukata, gashi simintin da aka masa duk ya dagargaje ya kusa komawa kasa, shi yasa in suka zubar da ruwa sai ya cabe, kudaje sai safa da marwa suke ta ko ina, ga kwanuka gaja gaja, igiyoyin gidan kuwa duk an rataye kaya, Ajay na ganin Jay ya shiga dakin Umma shi ma ya shiga ciki da sallama, dukawa Jay yayi daga bakin kofar ya gaida Umma da Maman Salame dake dakin, Ajay ma yayi hakan ya gaishe su, ganin haka Maman Salame ta tashi da sauri ta shimfida masu darduma a kan ledan dakin tana masu sannu da zuwa, duk tunaninta ita ma zuwa aka yi za a tafi da Umma amma sai bata ga alamar hakan a tattare da su ba duba da yanda suka yi gaisuwa cikin girmamawa, Jay ne kawai ya zauna kan darduman Ajay kuwa ya kasa zama ga wani zafi da yake ji a duk jikinsa, ya ciro handkerchief dinsa yana goge zufan goshinsa, Mama Salame ta dau mafici ta mika masa, ya ɗan yi murmushi ya amsa yace "Nagode" Mama Salame ta dage labulen dakin tana cewa "Yau mun fi sati biyu basu kawo wutan ba, ance tiranspoma tayi bindiga" Nenne dake makale kofar bandaki rike da buta ta dinga leka dakin Umma bayan Maman Salame ta daga labulen, haka su Mama Zubaida da suka ji shiru ba a taso keyar Umma an fito da ita ba, Jay na kallon Umma dake zaune don ko ba a gaya masa ba yasan ita ce mahaifiyar Khaleesat duba da kalan fatarta sannan babu ta inda Khaleesat ta bar ta, ba karamin kama Khaleesat ke yi da mahaifiyarta ba a nan ta samo asalin kyanta, Yayi kasa da murya yace "Ya jikin Umma?" Cikin sanyin murya Umma tace "Alhamdulillah da sauki" Ajay ma yayi mata ya jiki ta amsa tana kallonsu gaba daya don jira kawai take taji me ke tafe da su, in ma cewa za su yi tafiya suka zo yi da ita dama a shirye take tunda hijab dinta na jikinta, shiru ne ya biyo baya a dakin, don Jay bai san ta inda zai fara introducing kansa ba ma, haka ma Ajay da yayi shiru zafi na neman hallaka sa, after few seconds Ajay yayi karfin halin breaking silence din a hankali yace "Makaranta daya mu ke tare da Jidderh a can America, so kawarta ta sanar mana abinda ke faruwa shi ne muka nemi ta bamu address mu zo nan duba ki" Sosai hankalin Mama Salame ya kwanta jin abinda Ajay yace, Mama Salame tace "Allah yayi maku albarka, kuma mun ji dadi mun kuma gode da zuwan da ku ka yi" Jay ya kwantar da murya yace "Kiyi hakuri Umma kuma ki kwantar da hankalinki, muna tabbatar maki in sha Allah komai zai wuce nan ba da dadewa ba, don za ayi duk abinda ya kamata, mahaifinta ma in sha Allahu za mu yi abinda ya dace a sakesa a yan kwanakin nan, ita kanta Halysaah zata dawo gida in sha Allah" Maman Salame ta daga hannu sama cike da farin ciki tace "Alhamdulillah ya Allah, gaskiya mun ji dadin jin hakan daga gare ku, don bamu da wanda zai tsaya mana sai Allah, Alhamdulillah" Ita dai Umma kanta na kasa hawaye na zuba idonta, Ajay yace "Zuwa gobe da safe in sha Allah za mu shigo" Mama Salame tace "To Allah Ubangiji ya kai mu goben lafiya, mun gode, mun gode" Mikewa Ajay yayi ya kara yi ma Umma sallama sannan ya fita daga dakin kar yayi suffocate, heat wan finish prince, don in akwai abinda baya shiri da shine zafi, baya son zafi ko yaya yake, Nenne na ganin Ajay ya fito daga dakin Umma ta sake komawa cikin bandaki da sauri, su Mama Zubaida da Mama Shatu suka bi sa da kallo har ya fita daga compound din, to su waye wannan kuma su da suka baza ido da kunne su ga an fito da Umma tana kuka, bayan fitar Ajay da few minutes sai ga almajirai suna shigowa gidan da buhun shinkafa biyu, carton din taliya biyu, carton din indomie biyu, manyan gallon na manja da mangyada, da carton din maggi duk kuma aka dinga dire su a kofar dakin Umma, daga Nenne har su Mama Zubaida haka suka saki baki suna kallon ikon Allah, Maman Salame ta taso zuwa bakin kofa tana kallon kayan abincin da mamaki tace "Ikon Allah, har da uban hidima haka??" Jay ya ajiye ma Umma 100k yace "Gashi Umma ayi cefane da wannan, in sha Allah gobe za mu shigo da izinin Allah" Bai jira cewar Umma that was speechless and shock ba ga hawayen dake sauka idonta kawai ya fita daga dakin..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* *Hmm don't even know where to start from🥺 Khaleesat's Citadel ku sani Billah ina yinku 💯 Nagode Nagode da abun arziki, Allah Ubangiji ya bar mu tare, Allah ya kara maku arziki ta yanda bakwa zato, Allah ya raya maku zuri'a ya baku zaman lafiya da mazajenku, wa enda basu da auren cikin ku Allah ya fiddo maku da mazaje na gari, yanda ku ka faranta min yau ku ma Allah ya faranta maku, thank you soo much Meenah parrot for bringing about the idea and the wonderful Souls that supported it, Allah ya kara mana hakurin zama da juna yan Citadel dina😍* HALYSAAH 37 Jay na fitowa dakin Umma, Nenne dake tsaye tsakar gida bayan ta fahimci ba yan sanda bane ta rushe da matsanancin kuka ta nemi er kujera ta zauna tana kallonsa tace "Da wannan uban kudaden da ku ka kashe na siyo kayayyakin abincin nan ai da belin ɗa na ku ka yi, wallahi maraya ne ba shi da kowa, in ba wani ikon Allah ba sai dai ya rube a can, wancan karan ni kadai nasan wahalan da na sha na ganin an sako sa, babu inda kafata bata shiga ba wallahi, na dinga bi gida gida ina neman taimakon kudi" Jay ya kwantar da murya yace "In sha Allah za mu yi bakin kokarin mu na ganin an sako sa kaka, ki kwantar da hankalin ki" Nenne na matsar kwalla da gefen haɓar zaninta tace "Ɗan nan ina hankalina zai kwanta ɗa na na can furson? In dai daga gidan radio da talabijin ku ke ni dai na amince ku zo ku dau muryata da fuskata in nemi taimakon al'ummar musulmai ku watsa ni duniya ta gan ni ina jawabi, kilan gwamna ma in ya gani yaji tausayina ya saka baki a sakar min ɗa na" Jay yace "Ba sai anyi haka ba Kaka, ina tabbatar maki nan ba da dadewa ba zai dawo gida in sha Allah" Nenne tace "To daga ina ku ke? Ko dai kungiyar kare haƙƙin en Adam ne" Jay ya ɗan yi shiru, Mama Zubaida da Mama Shatu dai sun yi cirko cirko a tsakar gida suna gwale ido suna kallon Jay, Jay yace "Makarantar mu daya da Halysaah a can Amurka, shi ne muka samu labarin abinda ya faru mu ka zo" Nenne ta mike da sauri tace "To ai yau kusan sati daya kenan ana neman ta ko sama ko kasa, wallahi bamu san inda take ba, ita uwar ta na daki tana jimamin ta, ni kuma ina nan ina jimamin ɗa na, haka muka raba abun, amma tun da yarinyar nan ta samu labarin daurin aurenta da annoban nan Awdul ta shiga duniya, wallahi bakina da nata tace min bata son sa bazata iya auren sa ba, tun da uwata ta haifeni ban taɓa ganin inda ake auren dole ba" Nenne na kai wa nan ta fasa sabon kuka, Jay dai ya ma rasa abinda zai ce mata, beside baya ma son yayi magana gaban su Mama Zubaida da suka wangale kunnuwa suna saurare, kawai ya saka hannu a aljihunsa ya ciro dubu ashirin din da yayi saura, yaje har gaban Nenne ya mika mata da ladabi yace "Ga wannan Kaka, in sha Allah za mu shigo gobe" Nenne ta daga hannu da sauri tace "A'a, gwara ku hada kawai ku kai furson a sako min ɗa na, don yafi min ko wani kudi a duniya" Jay yayi murmushi yace "Ki amsa kaka, na maki alkawarin za a sako sa nan ba da dadewa ba in sha Allah" Nenne ta amshi kudin da hannu bibbiyu tana sa masa albarka cikin rawan murya tace "In ma Allah ya sa kun zo gobe ba ku sameni a nan ba ku sa a raka ku gidana babu nisa daga nan" Yana murmushi yace "In sha Allah Kaka" Daga haka yayi mata sallama sannan ya fita daga gidan su Mama Zubaida suka bi sa da kallo babu fara'a ko wacce da abinda ke yawo a ranta, Nenne ta kulle kudin a habar zaninta ta soke tace "Dama gobe da asuban fari zan je gun Malam Na ta'ala, Allah ya sa in samu kwale kwalen da zai tsallakar da ni da sassafe" Dakin Umma ta nufa tace "To ke Salame kike ko wa? Ki fito mana ki shigar mata da dukiyar nan dake bakin kofa kar a faki ido a sungume mata wani abun, kayan abinci ai dukiya ce me zaman kanta a yanxu, Allah kadai yasan dubu dari nawa suka kashe wajen siyo kayan abincin nan...." Maman Salame ta fito daga dakin Umma ta fara shigar da kayan abincin ciki, Mama Shatu ta shige dakinta fuska a murtuke, Mama Zubaida ma ta tabe baki ta shige nata dakin ta sako tsumman labulenta dake rataye da kyauren dakin. Jay na fita waje ya tarar da Ajay cikin mota yana zaune a kujera me zaman banza ya kwantar da seat din kujeran idonsa a lumshe, Jay ya bude driver seat ya shiga yana kallon Ajay jin yanda ya kure AC din motar gaba daya, Ajay ya gyara zamansa yana kallonsa, Jay dai yayi murmushi ya fara driving motar Ajay ya nuna masa hanyar da suka bi suka fita ranan da yayi dropping Khaleesat, motar dake bayan su ma ya bi su, Ajay sai sake kare ma unguwan kallo yake with distress har suka isa main road, bayan sun hau saman titi ya kalli Jay yace "In za a samu gida ko na 30M zuwa 50M ne a siya pls su bar wannan vicinity din" Jay yace "I think that will be okay idan anyi releasing mai gidan but not now" Ajay yace "Duk daya ne Bruh, plss kayi ma Salisu magana a fara duba gidan daga yau zuwa gobe, that house isn't healthy for a living thing, ta yaya me rai zai dinga rayuwa a gida irin wannan? This is so pathetic, or am i exaggerating pls?" Jay yace "But haka kawai baza mu yanke decision without the release of the head of the House ba, so kake mu kara triggering saurayin nata bayan har yanxu ba mu yi achieving ko abu daya ba, we are following everything step by step Ajay, we will reach der in sha Allah" Ajay bai sake cewa komai ba, amma da gaske hankalin sa ya tashi kwarai ganin condition din cikin gidan most especially the compound, in ba dole ba shi kam babu abinda zai sake kai sa gidan nan, it's not about the house structure or where it's located but the hygiene of the house, sai kace cikin prison, ji yake kamar har ya kamu da cholera don har wani zazzabi zazzabi ya fara ji, ya kai hannu ya rage Ac din motar, shi dai Jay driving dinsa kawai yake. Washegari da yamma haka nan suka sake komawa gidan bayan Lauyan su yayi requesting su tambayi matan Malam Ali ko da akwai wani written debt forgiveness document kuma original one din da kotu ta bashi bayan masu karansa sun janye karar, cause in dai babu takardun to sai dai ayi case din biyan bashin da yake bin Alhaji Musa amma ba dai su yi karan sa ba, Bayan Ajay yayi parking ya juya yana kallon Jay yace "Zan jira ka" Er dariya Jay yayi yace "Toh ai da baka biyo ni ba kayi zaman ka a gida kawai" Bai jira cewar Ajay ba ya sauka daga cikin motar ya nufi cikin gidan, yau ma dai kamar jiya ba su kadai suka zo unguwan ba don securities da suka biyo su har sun fi na jiya tunda basu san ko Abdul na da Spy a unguwan ba, infact bazai ma rasa ba, definitely za a basa labarin wasu sun zo gidan su Khaleesat jiya, so they are not loosing guard by any means, and they are never going to let him take them unaware, A takaice Jay ya gaida Kishiyoyin Umma dake zaune tsakar gidan sun yi rashe rashe da su, yau ko murhu basu kunna ba don dawowar su kenan daga wajen Malamai, tun asuban fari suka bar gida sai yanxu suke dawowa, duk suka bi Jay da kallo, Jay dai yana tafe yana kallon Islam da Noor dake ma Umma wanke wanke a tsakar gidan don ko ba a gaya masa ba yasan siblings din Khaleesat ne duba da pheomelanin din su, a tare suka gaishesa ya sakar masu murmushi yace "How are you?" Murmushin kawai suka yi basu ce masa komai ba Islam na wanke wanke Noor na mata dauraya, Jay ya isa har kofar dakin Umma yayi sallama, Umma da ta gama gyara dakinta kenan ta saka turaren wuta na tsinke ta amsa sallaman sa, a kullum in zaka shigo dakin Umma a haka zaka tarar da shi fes fes, duk da ba komai bane a dakinta don ta siyar da komai nata amma kullum a gyara zaka same dakin da turaren tsinke, Jay ya shiga dakin Umma na kallonsa tace "Sannu da zuwa" Tabarma ta dauko ta shimfida masa don bata yi tunanin zai dawo yau kamar yanda yace mata jiya ba, Jay ya zauna yana murmushi ya gaisheta, Umma ta zauna kan dardumanta ta amsa gaisuwar sa, har a sannan zaka ga damuwar dake tare da ita alamar karfin hali kawai take, sai kuma ta mike tace "Bari in kawo maka ruwa" Ruwa ta debo masa a cup din stainless ta karaso ta ajiye masa a gabansa sannan ta koma ta zauna, yace "Nagode Umma" Ɗan murmushi kawai tayi, Mama Zubaida da Mama Shatu suka yi tsit a tsakar gida ko wacce ta kasa kunne ko zata ji abinda ake cewa a dakin Umma, Ajay ne ya shigo gidan duk suka zuba masa na mujiya, sau daya ya kallesu ya dauke kai ya nufi dakin Umma, yau dai tsakar gidan a bushe yake bai yi gaja gaja da ruwa ba da yake basu yi girkin siyarwa ba, Islam na tsaye bakin kofar dakin Umma bayan ta shiga da kayan wanke wanken da suka yi da twin sis dinta, Ita kuma Noor na share inda suka yi wanke wanke, Idan Ajay ya kalli Noor sai ya kalli Islam, ya amsa gaisuwar da Noor ke masa tana rike da tsintsiya, yana isa bakin kofar dakin Umma ya ja dogon hancin Islam don ita ce ke mugun kama da Khaleesat har bakinsu iri daya ne, murmushi tayi tana kallonsa yace "How are you?" Ta sauke idonta bata ce komai ba yanda dai Khaleesat ke yi, da sallama ya shiga dakin Umma, Jay ya daga kai yana kallonsu don bai yi tunanin zai shigo ba, Umma ta amsa sallamansa, ya zauna daga gefen Jay sannan ya gaisheta, Umma ta amsa da murmushin karfin hali tana masa sannu da zuwa, after some seconds Jay ya fara magana a hankali yace "Umma akwai wasu takardu na yarjejeniyar kotu na yafiyan bashin da aka yi ma Mai gidan nan, Allah yasa kun san in da takardun suke ana bukatarsu ne" Umma tayi shiru, can tace "To, amma wallahi ban sani ba sai dai ko a duba dakinsa ko suna nan" Jay yace "Eh a duba Umma, Allah ya sa a gani" Umma tace "Ameen" Mikewa Umma tayi ta fita daga dakin, Mama Zubaida da Mama Shatu suka bi ta da kallo har ta shiga dakin Malam Ali, after almost 8 mins sai ga Umma ta fito da wasu takardu wanda bata san ko na menene ba dai zata kai masu su duba ko akwai wanda ake nema a ciki, a haka ta wuce Kishiyoyinta da idanuwansa duk ke kanta, ta koma dakinta ta mika ma Jay takardun sannan ta koma kan dardumanta ta zauna, Jay ya dinga duba takardun daya bayan daya, yaga har da takardun makarantar Malam Ali, ashe har Degree garesa a Agriculture, kafin nan kuma sai da yayi diploma, yana ta dai duba tulin takardun har daga karshe yaga wasu takardun da yake saka rai na yarjejeniyar yafiyar da aka yi ma Malam Ali a kotu na biyan bashin Mahaifin Abdul ne, ya mika ma Ajay shi ma ya amsa yana duba takardun, Jay ya kalli Umma yace "Ina jin wannan ne takardun da muke nema" Umma tace "To Alhamdulillah" Jay yace "To za mu koma, duk yanda ake ciki za mu dawo in sha Allah" A hankali Umma tace "To Allah ya saka da alkhairi, amma sai dai akwai wata uwar dakina da bata ji ba bata gani ba yan sanda suka tafi da ita shekaranjiya har yanxu ba a ma san wani caji ofis din aka kai ta ba" Ajay dake kallonta yace "Ko Baabar nan ta Hotoro?" Cike da karfin hali Umma tace "Ita, wallahi bata ji ba bata gani ba aka je aka tafi da ita" Ajay yayi shiru yana kara mamakin stupidity din Abdul, he don't think that guy is okay in anyway, after some seconds ya kalli Umma a hankali yace "Za mu bincika inda aka kai ta mu yi bailing dinta in sha Allah" Umma ta share hawayen da ya kawo idonta ta kasa cewa komai, Jay yace "Ki kwantar da hankalin ki Umma, in sha Allah komai zai wuce da izinin Allah" Cikin rawan murya Umma tace "Allah ya sa" Jay ya kalli Ajay, tsabar tausayin Umma kawai yaga gwara su gaya mata gaskiyar inda Khaleesat take ko zata ɗan samu sukuni a ranta, Jay ya sauke idonsa a hankali yace "Sannan Umma akwai maganar da zan gaya maki yanxu, amma don Allah kar ki gaya ma kowa har zuwa sanda za mu gama abinda muke" Ajay ya juya ya wani kallesa don har ya gano maganar da Jay zai gaya ma Umma, Umma na share idonta tace "To in sha Allah" a hankali Jay yace "Halysaah na Lagos, amma don Allah ba ma son kowa yasan hakan Umma, ko makusantan ki kar ki gaya ma tukun....." Umma da zuciyarta ke bugawa tace "Lagos kuma? Wajen wa a Lagos?" Jay yace "Tana wajen sister din ki ne, amma mun ce mata kar ta nuna maki tana wajenta har sai sanda komai ya dai daita, shi yasa ma har yanxu bata gaya maki ba" Umma tayi shiru, amma fa ji tayi wani nutsuwa ya zo mata, lkci daya kuma taji hankalinta ya kwanta kamar an yaye mata kashi saba'in na damuwar da take ciki, Umma tace "In sha Allahu babu wanda zai ji hakan daga gare ni, yanda ku ka tsaya mana ku ma Allah Ubangiji ya tsaya maku haka, Allah ya saka maku da alkhairi..." Umma ta kasa ci gaba hawaye masu zafi na sauka idonta, A haka Ajay da Jay suka fita daga dakin Umma za su koma Office din lauya din su da takardun hoping shi ne kotu zata bukata, yau ma dai Ajay ji yayi kamar zafi zai kashesa a dakin Umma amma haka ya dinga daurewa har suka fita daga dakin sannan ya ciro handkerchief dinsa yana goge zufan da yayi, ya kalli Islam dake zaune bakin kofar dakin Umma da takardan makaranta a hannunta alamar karatu take, Noor kuma na hura gawayi a can gefe, ya saka hannu a aljihu ya ciro kudaden da bai san ko nawa bane ya mika ma Islam yana kallonta yace "Ku raba ke da er uwarki" Islam taki amsan kudin, ya hade rai yace "C'mon collect it" Jay dake kallonta shi ma ya sakar mata murmushi yace "Karba mana cutie" Islam ta kalli Noor amma still taki amsan kudin, Ajay ya zare mata ido yace "Kee, amsa nace" A hankali ta kai hannu ta amshi kudin, Ajay da Jay suka fita daga compound din, Kishiyoyin Umma suka dinga kallon uban kudin da aka ba Islam kamar idanuwansu za su fito ko kiftawan kirki basa yi, Islam ta tashi ta shiga dakin Umma da kudin a hannunta, Mama Zubaida ta mike ta ma Mama Shatu alamar su shiga daki, duk suka shiga dakin Mama Shatu sannan suka sake labule, Mama Zubaida ta rike haba tace "Anya kuwa Shatu baza mu san yanda za mu yi Abdul ya samu labarin abinda ke faruwa a gidan nan ba? Ni wallahi ban yarda wa ennan samarin basu san inda Khaleesat take ba, kina fa ganinsu kin ga 'ya yan masu kudi, dubi suturan da suka sa wa, ji motocinsu, sannan kalli fatarsu kalan ta yan hutu, in fa muka yi sake Shatu bakin ciki ne zai kashe mu a gidan nan muna ji muna gani" Mama Shatu tace "Ke ma dai wallahi kin fiye gaggawa, sai kace kin manta me Malamin yace mana, duka duka ba yau muka kai masa kudin ba, to mu zuba ido ya fara aiki mana tukun" Mama Zubaida tace "Duk da haka dai gwara mu ma mu dinga yin namu ta bayan fage Shatu, kada mu sakankance mu bar malami da aiki shi kadai, ya kamata tun wuri mu san yanda za mu yi mu ankarar da Abdul abinda ke faruwa a gidan nan, don gaskiya na sha jinin jikina da wa ennan zaratan samarin, ke ki ga tulin kudin da suka ba Islam, sannan kalli uban kayan abincin da suka jibge jiya daga karshe don walakanci aka biyo mu da kwano uku uku da taliya bibbiyu da man gyada da manja, sai maggi leda bibbiyu ga mayunwata, ke kiji wai yau Zahra'u ce da tsam mana kayan abincin da aka jibge mata, bayan haka Allah kadai yasan nawa suka bata a daki tunda ba gaya mana zata yi ba, ga Nenne ma a gaban mu aka bata rafar kudi yan dubu dubu, anya bamu shiga uku ba Shatu? Ni fa jikina yayi sanyi hankalina ya tashi, meye hadin su da Khaleesat din da har suke wannan hidima haka a kanta, mu ga 'ya yanmu a zube har yau babu mataya sai talla suke, ni fa wallahi ko tsirara zan yi yawo gwara inyi da dai Zahra'u da zuri'arta su ji dadi a duniya" Mama Shatu tace "Yanxu dai Gwaska za mu samu ya raka mu gidan su Abdul din tunda yace yasan gidan uban sa, nasan Abdul din zai taka ma yan iskan burki har ma ya bamu makudan kudi fallasa asirin abinda ke faruwa da mu ka yi" Mama Zubaida tace "Atoh dai tun wuri my gaya masa abinda ke faruwa, zuba ido ba namu bane wallahi, amma sai dai jibi kenan za mu je gidansu Abdul din don Gwaska ya tafi dambatta daxu uwarsa ke gaya min yaje kai kaya can" Mama Shatu tace "Ai jibin kamar gobe ne, kin ga gobe dama mu gama girkin mu da wuri mu tafi inda wannan matar ta mana kwatance daxu a gidan Malam" The next day wajen karfe biyar da rabi na yamma Sha'awa tayi sallama bakin kofar dakin Umma dake yi ma yan biyun ta gyaran gashi, babu kowa gidan don duk yan matan gidan basu dawo talla ba, kananun yaran kuma sun tafi gantali, tun Sha'awa bata shigo dakin Umma ba take cewa "Umma yanxu Ladingo ke sanar min an sako Gaje, wai daxu taje unguwan taga ana ta shiga gidan yi mata jaje" Umma ta sake gashin Noor ta mike da sauri tace "Da gaske Sha'awa?" Sha'awa tace "Wallahi kuwa Ladingo bazata min karya ba Umma, tace Gaje dai ta dawo gida ga yan unguwa na ta tururuwan shiga yi mata jaje tun daxu" Umma ta jawo Hijab dinta tace "To bari in je gidan Allah ya sa da gaske ne dai" Sha'awa tace "Da ina da kudin mota ai da mun je tare Umma, kusan kwanan ta biyar fa a kulle, don ma akwai kanwarta da zata kula da jikokinta tunda uwarsu na can Libiya ta tafi aikatau, ubansu kuma yayi watsi da su, banda haka da yaya makomar jikokin nan nata fisabilillahi?" Umma bata tanka ta ba ta gama saka hijab dinta ta daura nikab ta dau purse zata fita, Noor da Islam suka marairaice wai za su bi ta, ganin in ta tafi su kadai zata bari a gida yasa tace su saka hijab gaba daya, haka nan duk suka saka Hijab suka fita daga dakin Umma na biye da su, kusan kullum sai Umma taje gidan Gaje sau biyu ta duba ko ta dawo amma sai taga akasin haka sai dai ta samu kanwarta Iya a gidan, jiki a sanyaye take juyawa ta koma gida don Iya na ganinta take fara masifar ita ta saka er uwarta a uku, Umma zata fita gidan tare da yan biyunta sai ga su Mama Shatu da Mama Zubaida sun shigo wujiga wujiga da su, kana ganin fuskokinsu kasan a gajiye suke likis, ga wuyan hijabinsu duk yayi jagab da zufa, kafafuwarsu kuwa kamar wa enda suka dawo daga gona, Umma dai tayi masu sannu da zuwa kawai ta fita daga gidan su Islam na biye da ita, ai ko tana isa gidan Gaje taga da gaske an sako Gaje, Gaje na ganin Umma tayi kamar bata taɓa saninta ba a duniya, yanda take amsa gaisuwa da jajen masu shigo mata haka ta amsa ma Umma kamar ranan ta fara ganinta, ita dai Umma na zaune tayi shiru ta ma rasa me zata ce, su Islam na zaune gefenta, Gaje bata sake kallon direction dinta da yaranta ba, duk wanda ya shigo haka take sanar masa yanda Maman Fu'ad ta ci amanarta tace ma yan sanda ita bata taɓa ganinta ba ma balle wata Khaleesat, In tayi bayanin sai ta rushe da kuka tace "Ban taɓa tunanin Sadiyah zata min butulci haka ba duk alakar da ke tsakanin mu wai bata taɓa gani ba, kaji tsoron Allah kaji tsoron mutumin yau kawai, duk kyautata ma yarinyar nan da nake amma ta barni ni kadai raina a cikin matsalar da na tsoma kaina" Ita dai Umma tayi tagumi tana sauraron duk abinda Gaje ke cewa. _Thanks sooo much for the birthday wishes everyone, Allah ya saka da alkhairi_ *As usual yau akwai discount na littafin Halysaah daga yanxu har zuwa gobe karfe goma na safe, the book will be 300 naira, via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah, ur evidence through 07087865788* Thank you sooo much everyone. Gaisuwa da fatan alkhairi zuwa ga Deejah me sana'ar lamurje da ganja, tare da Aunty Amzaj Maman mara Jidda da Damsalele, Uwata Zeenariya kema an gaisheki da babban murya tare da Hajiya Safiyyah Usman me kantin kayan yara😁 Aneesah Zero zero da Ummi matar mijin uwar gida ku ma na gaisheku da siririn murya, Barrister Inna da 'ya ta Uwar Annur da Hajiya Sadiya Uwar Hanan kuma duk na gaisheku da fatan alkhairi, Hajiya Sadiya Chamo au banda ke🙄, Mom Asas, Maman Faruk me data, da Sis Aisha Dalhat ga kuma Maman Aisha da Hajiya Bilkisu duk Khaleesat na maku fatan alheri 💖 HALYSAAH 38 Sai bayan da aka yi sallan Magrib Umma ta bar gidan Baaba Gaje da yan biyun ta, kuma har ta bar gidan Gaje bata nuna ta taɓa saninta ba don casually ma take amsa mata kamar yanda take ma kowa da ya shigo mata jaje, Umma dai a sanyaye ta baro gidan, tana isa gida taga mutane tsattsaye a kofar gida kowa da abinda ke fitowa bakinsa, sosai taji gabanta ya fadi gashi ta kasa fahimtar akan me ake ta surutu haka, can dai ta dubi wata makociyarsu dake tsaye wajen tace "Munnira me ke faruwa?" Munnira tace "Wallahi Umman su Khaleesah nima fitowa ta kenan da naji hayaniyar tayi yawa, amma wai kamar wasu mutane ne da ba a san ko su waye ba suka shiga gidan naku suka yi aika aika, ance a katuwar mota suka zo...." Umma ta kasa cewa komai tana kallonta, da kyar take jan kafa tana rike da su Islam ta shiga gidan har sannan gabanta bai daina faduwa ba, Su Mama Shatu da Mama Zubaida ta gani tsaye da 'ya yan su duk sun yi cirko cirko a tsakar gidan da makota ana ta maida magana, tsakar gidan dai cike yake da jama'a kowa na fadin albarkacin bakinsa, Umma ta dake tace "Wai me ke faruwa ne a gidan?" Mama Zubaida ta wani kalleta a walakance tace "Ina kuwa za mu san me ke faruwa tunda mu dai muna zazzaune sai ga wasu kattin gardawa sun kusa goma babu annuri a tare da su sun shigo mana gida da makamai suna tambayar dakin Malam, basu tsaya iya dakin Malam ba hatta sauran dakunan gidan nan sai da suka shiga..." Sai a sannan Umma ta lura da bakin kofar shiga dakin Malam Ali, gaba daya yayi kaca kaca da takardun da ta mayar daxu bayan su Jay sun dau wanda za su dauka, har kayan cikin dakin sai da aka watso su waje har da er katifarsa da akwatin kayan sakawan sa da butar alwalansa, Umma ta juya tana bin tsakar gidan da kallo taga har dakinta an fito da kaya an yi watsi da su waje, da kyar Umma ta karasa kofar dakin Malam Ali ta leka ciki taga basu bar komai ba, dama ba wasu abun kirki ke cikin dakin ba, can ta juya tana kallon Kishiyoyinta amma ta ma rasa me zata ce, Mama Shatu ta kyabe baki tace "Ni takaicina dakunan mu da suka shiga wai ina takardun da Malam ya ba mu ajiya, ni ko nace mu muka san wasu takardu mu da bamu yi karatu ba ta yaya Malam zai bamu takardu mu ajiye ai sai dai ko ya ba er sa da aka kai turai karatu daga karshe tayi ma wanda ya kai ta karatun butulci wai bata son sa kuma, amma ina mu ina ajiyar takardu mu da muke jahilai" Umma bata tanka ta ba ta duka tana tattara takardun dake watse bakin kofar su Islam suka je suna tayata, a haka duk ta maida kayan Malam Ali cikin dakinsa, su Mama Zubaida sai hararanta suke, can Mama Shatu ta kyabe baki tace "Mu dai mun san ko ma wani takarda suke nema bazai wuce yana da alaka da er ki ba kilan kotu za a shiga, tun da kika haifi yarinyar nan muke shiga jarabawa munana a gidan nan, ko kuma muce tunda aka auro ki, mu da bamu san wani talauci ba balle wahalar rayuwa, daga auro ki karayar arzikin da ba a taɓa yin irinsa a tarihi ba ya samu Malam, sannan gashi sanadin er da kika haifo ga abinda ya samu Malam a karo na biyu, daga ke har 'ya yanki babu wani abun alkhairi a tare da ku sai masifa, ina ma Malam zai yada kwallon mangwaro ya huta mu ma mu huta ki tattara ki koma can kasar ku ki auri buzu ɗan uwanki" Sha'awa dake tsakar gidan wanda tana daga cikin mutanen farko da suka shigo bayan Mama Zubaida da Mama Shatu sun kurma ihu, amma fa sai da gardawan suka fita sannan suka samu bakin ihun neman agaji su da yaransu, Sha'awa tace "Haba Mama Shatu, wannan wani irin magana ce kike yi haka don kin ga Ummansu Khaleesah bata tanka ku a gidan nan, wannan ai cin fuska ne, kar fa wataran ku kureta ayi dauki ba dadi a gidan nan, don mai hakuri bai iya fushi ba wallahi" Wani zagi Mama Shatu ta kundumo mata a fusace, Sha'awa ta rama tace "Wallahi ba dai ubana ba, sai ko in naki uban me gyaran keke dake kabari" Ganin fada na kokarin kaurewa a tsakar gidan Umma da wasu mata suka fitar da sha'awa dake kunduma ma Mama Shatu zagi ta uwa ta uba, ga su Labeebah na kokarin dambe da Sha'awa dake zagar masu uwa su ma duk aka rirrike su, a haka dai aka fitar da Sha'awa dake gyara daurin zaninta da ya kusa faduwa gashi babu komai kasan zanin, tana huci take cewa "Shegu en kutumar uba masu bin bokaye, ko jiya sai da aka bani labarin kun je wajen wani boka na kuma san warce ta raka ku, kun ga kuwa Umman Khaleesah ta fi ku ko a wajen Allah tunda bata san hanyar zuwa gun Malamai ba" A haka dai aka fitar da Sha'awa daga gidan, Umma dai jiki a sanyaye ta tafi kofar dakinta ta tarar su Islam suna ta maida kayan cikin dakin da aka watso waje bayan sun kunna er fitilar dake ba dakin hasken, Noor na kallon Umma tace "Umma kinga babu kayan abincin a inda suke" Umma ta kalli inda Maman Salame ta ajiye mata kayayyakin abincin da su Jay suka kawo taga wayam, tsayawa tayi tana kallon wajen babu ko kiftawa tsabar mamaki yasa ta kasa cewa komai, muryar Nenne taji a tsakar gidan cikin fushi tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, meye haka aka cika gidan nan kamar ana taron farin ciki? Ku yan unguwan nan tsabar munafurci da gulma bakwa tashi shigowa sai iftila'i ya faru sannan ku bi ku cika ma mutane gida ko wacce da warin jikinta, farin cikin iftila'in ku ke ko menene haka? Doo Allah duk ku fita ku ba mutane waje mu ji da daya, ai ba kanmu farau ba, en iska kawai magulmata" Rai bace ta nufi dakin Umma hannunta rike da jarkar manja daya hannun kuma rike da tocilan ta, ta tsaya daga bakin kofa tace "Zahra'u me suka dauka a dakin Alin da suka zo?" Umma da ta zauna gefen katifar ta tace "Shigowa ta kenan nima Nenne, na je gidan Baaba Gaje an sakota daxu da yamma" Nenne ta kalli kayan da su Islam ke shigarwa daki tace "Har dakin naki suka shiga ne? To ni Usama ce min yayi iya dakin Ali suka shiga suka watso kayan ciki, ke kuma wa ya watso naki tsummokaran waje?" Mama Shatu tace "To shi da ya sulale ya gudu ya bar gidan ta yaya zai ce iya dakin Malam suka shiga? Ai babu dakin da basu shiga ba a gidan nan yau, mu ma duk mayar da namu kayan mu ka yi, hatta babban jarkan mangyada da na siya jiya sun dauke, iya shi suka dauka a dakina, Ita kuwa Zubaida kwashin adashin da aka kawo mata suka dauke" Nenne ta fara matsar kwalla cikin rawan murya tace "Lallai na ga abinda ya isheni bai ishi Ubangijina ba, to yan fashi Awdul din ya aiko mana wannan karan? Don dai duk mun san yafi karfin wani kudin adashin da bai taka kara ya karya ba balle wata jarkan mangyada, Allah mun gode maka da wannan rantsattsiyar jarabawan da mu ke ciki mun gode maka Allah, Alhamdulillahi ya Allah, Ina ga in ba tattarawa muka yi muka hakura da zaman birni mu koma kauye gaba daya ba muna cikin mummunan hatsari a Mariri gashi ba mu da gata, kar wataran cikin dare mun saki baki muna bacci su babbake mu, su babbake banza tunda babu me tsaya mana" Ita dai Umma tayi shiru bata ce komai ba, Nenne na kallonta tace "Su kuma samarin da suka sha uban fararen kaya suka zo mana nan suna kwambo dama yaudarar mu suka zo yi bamu sani ba, sun zo nan sun gama cika mana baki sai gashi tunda suka karkade wandonsu suka fita bamu sake ganin keyar su ba, to ina amfanin karya? har da ce min za a saki Ali kwanan nan ashe duk yan iskan gari ne makaryata bamu sani ba" Umma dai kallon Nenne kawai take, Nenne ta mika ma Islam jarkan manjan hannunta tace "Ba ruwana, wahalan da nake ta sha kan Ali ko shi ya halittoni duniya ai sai haka, kai kenan kullum ayi ta garkame ka kamar kasungumin barawo, sai kace wanda yayi ma Allah wani saɓon da bamu sani ba, saura kadan kwale kwalen da na hau jiya zan je nema masa taimako ya kife da mu banda Allah ya tsare, to ina dalili bayan ba shi kadai na haifa ba, in ya kasheni sauran su yi yaya? ke ungo amsa ki mika ma uwarki ta tsiyaya min manja, nawa ya kare" Islam tace "To ai an kwashe kayan abincin gaba daya Nenne" Nenne ta gwalo ido tana kallon direction din da aka ajiye kayan abincin taga wayam, bude baki tayi tana kallon Umma tace "Zahra'u ina kayan abincin? Ko kasuwa ki ka kai kika siyar? Fatarar taki ta kai haka Zahra'u?" Umma tace "Saboda me zan kai kayan abinci kasuwa in siyar Nenne, daga zuwa gidan Baaba Gaje in dawo nima na tarar an kwashe kayan abincin" Nenne ta ajiye jarkan hannunta a kidime ta saki salati tana tafe hannu tace "Baki kulle dakin bane Zahra'u?" Umma tace "In zan fita ai ina sa ma dakina kwado, to fasa kwadon aka yi, ga makullin ma a jakata" Nenne ta juya ta fita daga dakin dai dai shigowar Usama wani almajirin Malam Ali dake tare da shi tun yana da arzikinsa, kuma har yanxu dai yana tare da shi, Nenne na haska sa da tocila tace "Yauwa Usama kace iya wani daki mutanen suka shiga a gidan nan?" Usama yace "Iya dakin Alhaji kawai suka shiga" Nenne bata sake cewa komai ba ta nufi dakin Mama Zubaida don yafi kusa da ita, tana dage labulen dakin ta fara haske hasken tocila, sai kuma ta duka karkashin gadon karfen dake dakin ta hango carton din indomie biyu an tura su can ciki, ta kwalo ma Usama kira ya karaso da sauri tana haska masa karkashin gadon tace "shiga ka jawo min kwalayen taliyar yaran can" Ai ko ya shiga ya kwaso su ya fito da su, Nenne ta shiga cikin dakin tana duba bayan kyaure nan ma taga Babban jarkan man gyada ta sa Usama ya fiddo waje, ta gama duba dubenta a dakin bata ga wani kayan abincin ba sannan ta nufi dakin Mama Shatu, a bayan kyaure taga buhun shinkafa daya da quarter an lullube da zani, ta kwalo ma Usama kira shi ma ta saka ya kinkimo su ya fitar waje, a dakin Mama Shatu still taga kwalayen taliya da na maggi da jarkan manja duk ta sa Usama ya fiddo su waje, Nenne na kallonsa tace "Kwashe su ka mayar dakin Zahra'u Usama" Yace "To Nenne" Sai a sannan Nenne ta juya tana kallon su Mama Shatu da suka yi wuki wuki da ido ko wacce na kokarin diban ruwan alwala a buta, Nenne tace "An dai yi asara duniya da lahira, barayin banza barayin wofi, tirrr da halin ku, wato ga sabon jarin kayan abinci kun samu ko, tunda Zahra'un ta maida kanta er wahala warce bata san ciwon kanta ba, da ban ce a tsam min manja ba shiru zata yi maganar ta bi rariya ta bar ku da haram, ko zama da ku kadai ya isa ya dinga jefa Ali a masifa iri iri, ai ba kyau zama da jahilai shine kawai bai gane ba" Daga haka ta juya ta koma dakin Umma. Khaleesat na bakin pampon dake compound din Aunty Farida tana wanke wanke, ita kadai ce a gidan gaba daya don duk sauran tenant dake gidan sun fita aiki, Aunty Farida kuma ta tafi kasuwa, juyawa Khaleesat tayi jin an bude gate, ta mike tsaye tana kallonsa, murmushi ya sakar mata ya rufe gate din ya karaso cikin compound din shi ma yana kallonta, ta sauke idonta a hankali tace "Sannu da zuwa" Yace "Good morning Halysaah" Ɗan murmushi tayi ta sunkuyar da kai ta gaishesa sannan ta juya ta tafi ta bude masa kofar shiga parlon Aunty Farida tana kallonsa, yace "Aunty fa? ina ta kiran wayarta no response" Khaleesat tace "Eh ta bar wayar a gida ne ta tafi kasuwa" Ya kalli plastic chair dake veranda din Aunty Farida yace "Let me seat here ba sai na shiga ba, i just came to check on you" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "I really appreciate Housemate" Yace "To ki zauna mana" Ta kalli second chair din dake wajen sannan ta zauna, sake gaishesa tayi da ladabi tana kallonsa, yace "Lafiya lau Halysaah, how is ur body?" Tana wasa da gefen karamin veil din jikinta tace "Naji sauki" Yace "To amma naga kin rame, baki cin abinci ne?" Tayi shiru, yace "Baki ci ko?" Ta ɗan yi murmushi tace "Ina ɗan ci kadan" shiru ne ya biyo baya for almost 30 seconds, ta ɗan daga kai ta kallesa taga kansa a kasa, ajiyar zuciya ya sauke calmly yace "Everything will be alright soon in sha Allah Housemate" Nan da nan hawaye ya cika idonta, da kyar tace "But i don't know my mom's condition, i am really worried" Jay yace "Don't worry, Umma tasan kina nan, mun je can gidanku da Ajay, i assure you everything is fine back home do not worry ur self pls, yanxu dai we are working on clearing ur dad first before anything, soon in sha Allah he will be free from the debt" Hawaye na sauka idonta tace "To amma ni bazan iya zama da Abdul ba tsoron sa nake wallahi, kawai torturing dina zai yi yayi revenging abinda nayi masa, i am afraid" Jay yace "Do not be Housemate, we won't allow that happen in sha Allah, we will go to any extent na ganin hakan bai faru ba" Khaleesat dai tayi shiru tana share hawayen idonta, after some seconds yace "Baki tambayi Ajay ba?" Ta daga kai tace "Na zata tare ku ke yana waje" Jay yace "Not at all yana kano, bai ma san nayi tafiya ba, i took an early morning flight, zuwa 12 noon kuma zan koma kano in sha Allah, i just came to check on you" Khaleesat na kallonsa cikin sanyin murya tace "Nagode sosai, kuma naji dadi" Ya kalli agogon wrist dinsa dake nuna karfe sha daya saura yace "I will be leaving for the airport now kar inyi missing flight dina, kafin Ajay yayi noticing i am not home ya fara damuna da kira" Khaleesat tace "Ko ruwa baka sha ba, ko in kawo maka shayi? Kilan ma baka yi breakfast ba ko?" Da damuwa tayi tambayar tana kallonsa, Yace "No i am okay Housemate" Wayarsa ne ya fara ring ya ciro yana kallon screen din yayi murmushi sannan ya nuna mata screen din taga Ajayn ne ke kiransa, mayar da wayar yayi aljihunsa sannan ya fiddo 100k ya mika mata yace "In case you need anything Halysaah" ta girgiza masa kai tace "A'a Nagode, bana bukatar komai wallahi" Mikewa yayi ya ajiye mata kudin a kafarta ya fita daga balcony din yace "Take care of ur self Housemate, idan na sake samun lkci ko zuwa nan da few days ne zan dawo in sha Allah, my regards to Aunty Farida" Khaleesat ta mike tana kallonsa ta kasa ce masa komai wasu sabbin hawayen suka cika idonta, ya daga mata hannu kawai ya nufi gate don bai ma son ganin hawayen nata, tana kallonsa har ya fita sannan ya rufo gate din, parlon Aunty Farida ta shiga ta zauna kan kujera ta rufe fuskarta tana rera kuka tana shessheka..... Bayan few weeks na zirga zirga a cikin garin kano, da kuma zuwa court lauyan su Jay yayi Succeeding na amsan Bail din Malam Ali, afterward suna sa ran kotu tayi dismissing claim din Alhaji Musa saboda previous debt forgiveness dake kasa, a kuma yi masa imposing monetary sactions for abuse of process, all this weeks Jay da Ajay where so cautious of der movement in kano and they were at alert In case of necessity ko kadan basu ba Abdul chance din yi masu ba zata ba cause sun san bazai rasa informant a unguwan ba, ranan da suka yi dropping din Malam Ali a gida bayan kotu ta bada bail dinsa farin ciki gun iyalinsa da wasu yan unguwan ba a cewa komai barin ma Umma, sai shigowa gidan ake ana taya sa farin ciki, shi ko Malam Ali har kasa ya duka cikin ladabi yana gode ma Jay da Ajay, shi dai Ajay ya juya ya koma jikin motarsa ya tsaya ya rungume hannu, ga motar escort dinsu a bayan motar tasa, Jay har ya gaji da ce ma Malam Ali ya dena masu godiya, Calmly yace "Don Allah Baba ka dena mana godiya, mu saboda Allah muka yi..." Malam Ali na gyada kai yace "To... to...to wannan gaskiya ne, Allah Ubangiji ya maku albarka, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya kara daukaka, Nagode Nagode" Duk a birkice yake godiyan, Mama Shatu ta dauko tabarma ta shimfida tace "Taho ka zauna ka huta ko zaka dawo seti Malam, naga duk a firgice kake" Nenne ce ta shigo unguwan bayan wani almajiri yaje har gidanta ya sanar mata Malam Ali ya dawo, mayafin nata ma a baibai ta yafa ga dankwali da ta kima a kan mayafin tana hade hanya ta taho gidan ɗan nata, bata kula da Ajay a kofar gidan ba ta shige ciki da sauri, Ajay ya ciro wayarsa dake vibrate a aljihunsa yana duba me kiran sa, gyara tsayuwarsa yayi yana kallon screen din wayar babu ko kiftawa ganin Aunty Farida ke kiransa, haka kawai yaji zuciyarsa ta harba don Aunty Farida bata kiransa all this while, in ma da wani abu shi ne ke kiranta, ya kalli Jay da ya fito daga cikin gidansu Khaleesat, har sannan ya kasa daga kiran Aunty Farida. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Akwai wani abu da yake iya faɗakar da tunani tun daga nesa... Wani ƙamshi da yake sa zuciya bugawa da sauri... Wani ɗanɗano mai narkar da zuciyar masoyi... Wannan shi ne ƙamshin *Scent Palace* *Scent Palace*, da ke cikin birnin Gombe, shine gidan turaruka na musamman da ke kawo muku turaruka masu inganci daga cikin gida da waje masu ɗorewa, masu daɗin shaƙa, kuma masu burgewa Idan kina son turare da zai saka masoyinki ya ƙara zurfafa soyayyarsa gare ki ko kuma turare da zai sanya ki zama abar misali a wajen jama’a to *Scent Palace* shine mafita. Abubuwan da muke da su sun haɗa da: Turaren jiki (body spray/perfume) na mata da maza Turaren gida da ɗaki Turaren mota Turaren wuta na gargajiya da zamani Eid Gift Boxes an tanada musamman domin ku da masoyanku Me yasa *Scent Palace*? ✔ Ingantattun turaruka daga ƙasashen waje ✔ Farashi mai sauƙi da rangwamen Sallah ✔ Kyaututtuka da aka shirya cikin kwali na alfarma ✔ Nationwide delivery *Scent Palace* ba kawai turare ba ne ƙamshi ne da ke ƙarfafa soyayya, daɗi, da kima Tuntube mu yau don odar ki: 📍 Gombe 📞 08038888936 Instagram/Facebook/WhatsApp:08038888936,08154812224 *Scent Palace* Ƙamshin da ke bayyanar da ƙima! Ƙamshi ba wai kawai ƙamshi ba magana ce ta zuciya HALYSAAH 39 Jay ya karasa har inda Ajay ke tsaye yace "I think we can take our leave now, nan da friday sai a basa makullin sabon gidan, we just hope he will accept it" Shi dai Ajay bai ce masa komai ba don bai ma san me yake cewa ba, ganin yanayinsa Jay yace "Hey Bruh, are you alright?" Jin Ajay bai basa amsa ba ya kalli wayar hannunsa that was still vibrating yace "Who is calling you?" Ajay ya sake kallon screen din sannan yayi picking dab da kira na biyu zai katse, kunne ya kai wayar yayi shiru yana sauraron yaji abinda Aunty Farida zata ce, muryar Khaleesat yaji a hankali tace "Good evening, Plss can i speak to my Housemate?" At first shiru Ajay yayi, can babu yabo babu fallasa yace "About?" Khaleesat ta girgiza kai murya can kasa tace "Ba komai, kawai dai ina son zan masa magana ne" Jay dai kallon Ajay kawai yake don bai san da wanda yake wayan ba, a takaice Ajay yace "Don't you have his digit?" Bai jira cewarta ba ya katse wayar ya mayar aljihu, Jay yace "Who is that?" Banza Ajay yayi masa ya bude driver seat ya shiga ya tada motar fuskarsa a daure, Jay ya daga shoulder sannan ya zaga ya shiga gaban motar shi ma bai sake kulasa ba, Ajay ya ja motar suka bar anguwan motar dake bayansu na biye da su. Bayan sallahn magariba Malam Ali na zaune tsakar gida tare da Nenne da duk matansa sai yaran gidan gaba daya, Nenne ce kadai zaune kan kujera er tsugunno, sauran duk kan tabarma suke a zaune kowa na jiran jin dalilin zaunar da su da Nenne tayi, Umma dai na kusa da bakin kofar dakinta da su Islam da Noor a jikinta, Nenne tayi gyaran murya tace "Da farko dai nayi farin ciki ainun da dawowan ɗa na daga furson a karo na biyu, ina kuma rokon Allah ya sa iya bakin wahalarsa kenan sannan muna fatan yayi zuwan karshe furson, wa ennan samari da suka zo suka tsaya mana kuma har suka kubuto da Ali Allah Ubangiji ya masu albarka don da farko na zata makaryata ne kawai en neman suna, duk da dama inda naje ance min za a roki Allah ya kubutar da ɗa na, nafi tunanin ma rokon Allahn da aka yi ne kawai hakan ta faru ba wai don samarin nan ba, mun dai gode koma ya ya ne, sannan shawaran da zan bada shi ne muyi bulaguro mu koma kauye gaba dayanmu na en shekaru kafin komai ya lafa, mu ma hankalinmu zai fi kwanciya da hakan don Alhaji Musa da tsinannen ɗan sa ba barin mu za su yi mu zauna lafiya ba, duk da kotu ta wanke Ali amma Allah kadai yasan wani sharrin za su billo da shi don mutane ne wa enda babu Allah a ransu, wallahi sai su iya sa wa duk a kona mu cikin dare muna bacci, kunga ance zaman lafiya yafi zama ɗan sarki shi sa cikin rufin asiri mu tattara komatsanmu ko zuwa gobe da magariba ne Ali ya mana shatan katuwar tirela mu koma kauyen mu" Mama Zubaida da Mama Shatu da suka saki baki suna kallon Nenne kusan a tare suka ce "Kauye kuma Nenne?" Nenne na kallonsu da kyau tace "Kwarai kuwa kauye, don dama can ne asalinmu, na gaji da tsallaka kogi cikin kwale kwale zuwa nema ma Ali taimako wataran inje in kife, gwara tun da sauran mutuncinmu mu bar garin nan" Mama Zubaida na girgiza kai tace "Inaaa, ai bazata saɓu ba gaskiya, sai dai ni a bar ni a nan in ci gaba da kasuwancina ina rufa ma kaina da 'ya ya na asiri, akan matsalar da buzuwar matarsa da er ta suka jawo baza a cucemu a mayar da mu riga ba, bazai ma taɓa yiwuwa bane gaskiya" Mama Shatu ta cafke tace "Sai dai ya tattara matarsa da 'ya yanta su kuma kauye Nenne, amma mu kam muna nan tunda ba mu da 'ya yanmu muka jawo magana ba, dama mu ke ciyar da kan mu balle mu ji tsoron zamu rasa abinci" A fusace Nenne tace "A yaushe ku ka fara ciyar da kan naku munafukan Allah? ba sai bayan da ku ka tsiyacesa da fararen kafafuwan ku ba tukun? Ai ko Alhamdulillah kowa zai ma Ali shaidan kula da bautata ma iyalinsa banda jarabawan shegun mata da Allah ya hadasa da, ku ne nan ku ka ja masa karayar arziki, dama ance min dukkanin ku babu alkhairi a tare da shi gwara ma Zahra'u, wallahi ce min aka yi in dai zai rabu da ke da Zubaida to arzikinsa zai dawo kaca kaca har fin na ɗa, Zahra'u ce kadai matarsa ta arziki aka ce min, da zai ji ta nawa ma duk ya sallameku in ga inda za ku koma idan ba kauyen ba, ke Zubaida kin manta kauyen da uwarki da ubanki suke sai sati sati ake kawo ruwan pampo? Kin manta ko wutar lantarki ba a ja maku har yau a kauyen ba? Kauyen da muka je na dawo ina ta amai da gudawa amma har kina da bakin kushe namu kauyen da babu abinda babu? To wani ɗan iskan ne ma yace Rano kauye ce tukunna? Sannan ke shatu baza ma a kira garin iyayenki da kauye ba sai dai ace daji, haka nan muka dawo kano maguzawan mayu suka kamani da kyar aka samo kaina ba don Allah yayi da sauran shan ruwana a duniya da tuni na rasu wallahi" Shi dai Malam Ali yayi tagumi yayi shiru bai ce komai ba don tun kan Nenne ta kawo wnn shawara dama yake jin gwara ya koma garinsu don bai san da me Alhaji Musa da ɗan sa za su billo ba kuma, shi dai bai yarda kotu zata wankesa akan kudaden nan masu yawa ba gani kawai yake dadin baki su Ajay suke masa, Nenne tace "Yau ga samun waje kai, ita Zahra'u me yasa bata kushe shawarata ba sai ku masu fararen kafa, ko da yake ita ta guduwan er ta da ta shiga duniya ma take, mu bar ta taji da wannan ma" Mama Shatu tace "Wace er ta? Ai wallahi ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba Zahra'u tasan inda er ta take, mu dai ne kawai aka rena ma wayo aka raina mana hankali" Mama Zubaida tace "To ai ba ma sai kin rantse ba Shatu, kwarai kuwa Zahra'u tasan inda Khaleesat take" Nenne dai sai kallon Umma da ko kallon kishiyoyin nata bata yi ba take, a hankali Nenne tace "Lallai biri yayi kama da mutum, na kuma yarda da maganarku don Zahra'u da na sani da har yanzu tana nan kan darduma sanye da dogon hijabi tana rike da carbi tana kuka ba dare ba rana duk ta fita hayyacin ta, kawarta Uwar Salame da makociyarku sha'awa me daddawa su yi ta shigowa suna dannarta su zazzauna kusa da ita kamar me takaba, amma ina lura da ita yau kusan sati uku kenan tana ta harkar gabanta kamar babu abinda ya faru, nima dai ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba tasan inda Khaleesah take" Malam Ali ya gyara zama yana kallon Umma cikin lallami yace "Kiyi ma girman Allah Zahra'u ke da er ki ku rufa min asiri yanda Allah ya rufa maku, duk inda er nan ta tafi kiyi masu waya ta dawo ta amshi auren mijinta hannu bibbiyu, dama Allah ya riga ya kaddara Abdul ne mijinta mu din banza ne za mu canza hakan? don girman Allah ta rufa min asiri, ina cikin tashin hankali har yanxu wallahi don ban san kuma da me Alhaji Musa da ɗan sa za su dawo min ba, rufin asirina shi ne na damka masu Khaleesah kawai, in har suka kasheni wallahi banza kawai za su kashe tunda ba galihu ne da ni ba, tunda aka maida ni furson din nan nake rashin lafiya me tsanani, yanzu haka maganar da nake yi kirjina kamar an aza min katuwar dutse, ku yi min rai ke da er ki" Kamar zai yi kuka ya kare maganar, Nenne na matsar kwallan da babu tace "In wani abu ya same ka dama da Zahra'u da er ta zan yi kuka wallahi, don su ke kokarin salwantar min da kai ta karfi da yaji" Umma da hawaye ya cika idonta tace "To wai ta yaya zan san inda Khaleesah take ni ba waya ba balle ku yi tunanin tana kirana? Ko kun ga ina zuwa wani waje daga cikin dakina ne?" Mama Zubaida tace "Na rantse da wanda raina ke hannunsa Zahra'u kinsan inda makirar er ki take, don haka sai dai ki rena ma wani hankali amma ba mu ba, duk abinda ya samu mijinmu dama har karshen duniya mun yi ta ja ma ke da 'ya yanki Allah ya isa kenan, banda samun waje ita Khaleesah har tana da ta cewa da har zata bude baki tace bazata zauna da Abdul ba? Da me tafi Abdul din banda rufa mata asiri da yayi zai aureta? Mutumin da ya maida ta fess ya maida ta mutum ya kashe mata dukiya babu adadi don butulci da samun waje tace ita bata son sa kuma a ina aka taɓa tafka wannan iskancin? Wallahi ba a samu wanda zai ci ubanta bane shi yasa ta samu waje da yawa" Umma tace "Tun da har kuke tunanin nasan inda take kuma baza ku rasa sanin inda take ba ai, kilan ma za ku fi ni sani, don haka sai ku je ku fito da ita ku kai ta gidan Abdul din" Umma na kai wa nan ta mike ta shige dakinta, Mama Shatu tayi kasa da murya tace "Al-qur'an tasan inda take, da bata san inda take ba wallahi da har yau bata dena koke koke ba kilan har sai tayi rashin lafiya, kuma ni na ma fi zargin tana wajen kanwarta ne a garin Legas wallahi, in da ba haka ba ai da tuni mun ga Farida a gidan nan kamar an jefota amma gashi kusan sati uku har yau shiru Farida bata zo ba" Mama Zubaida tace "Ahaf ai mu ba yara bane" shi dai Malam Ali sai zazzare ido yake, Nenne tayi kasa da murya tace "Gaskiya na yarda da maganarku, don nima ina ta mamakin me yasa har yau farida bata zo ba, ita da ko tari yayarta tayi zata hawo mota ta kamo hanyar kano, amma ace an rasa Khaleesah yau sati uku shiru bata kamo hanya ba, ai da alamar tambaya" Malam Ali ya share zufar goshinsa duk da sanyin da ake shi ma yayi kasa da murya yace "To yanxu meye shawara? Ko ni zan shirya in tafi Lagos din ne?" Sosai hankalin Umma dake tsaye bakin kofarta daga cikin daki ya tashi don duk tana jin abinda suke cewa, Mama Zubaida tayi kasa da murya tace "Ai ban ma yarda da shiga dakin da tayi ba kilan er uwar zata kira, ko da yake bata da waya, kawai ina ga a gaya ma...." Mama Shatu ta ɗan tsunguli Mama Zubaida alamar tayi shiru, lkci daya Mama Zubaida tayi tsit, Nenne ta mike tana kallon Malam Ali tace "Mu je daga gefe mu yi shawara Ali" Mikewa Malam Ali yayi ya nufi can hanyar fita daga compound din Nenne na biye da shi, Mama Shatu ta mike tayi ma Mama Zubaida alamar su shiga ciki, suna shiga daki Mama Shatu tace "Ke ya muna neman maganar auren nan ya rushe gaba daya ko zai hakura yace a basa Labeebah ko Lamisah amma kike basu shawaran su je Lagos?" Mama Zubaida tace "Wallahi gaba daya na sha'afa kinsan kwakwalwar tawa, kuma kece kika kawo maganar Khaleesah, tun asali ma bai kamata mu ce komai ba gashi yanxu mun karkato da hankalinsu zuwa Lagos, sai fa Malam ya iya shiryawa ya kama hanyar Lagos wallahi" Mama Shatu tayi shiru, can tace "Ai ko in yaje lagos din nan shikenan tsarinmu ya lalace don taso keyarta zai yi su dawo kano ya mika ma Abdul ita, kinga shikenan mun tashi a tutar babu mun kai ma malamai kudadenmu a banza, tunda duk mun san Abdul din na sonta kuma hannu bibbiyu zai amsheta su fara rayuwar aure" Mama Zubaida tace "Toh kuwa ina ga da kaina zan kira Farida ince mata in har tasan Khaleesah na wajenta to tayi maza maza su bar gidan don Malam zai kama hanyar lagos tare da Abdul" Mama Shatu tace "A'a bari in shiga dakin Zahra'u in gaya mata hakan, tunda ga Nenne da Malam can sun kebe bamu san maganar da suke ba" Bata jira cewar Mama Zubaida ba ta fita zuwa dakin Umma, Zaune ta tarar da Umma bakin katifarta abun duniya ya isheta gashi babu waya hannunta, kuma in tace ta fita daga gidan ta amshi waya a makota tasan dole za a zargeta, kuma daxu da safe suka yi waya da farida ta wayar Mama Salame take sanar mata jibi za su Nijar da Khaleesat, Mama Shatu na kallon Umma tayi kasa da murya tace "Zahra'u, ga 1can Nenne da Malam suna shirya yanda za a tafi legas wajen Farida gobe da asubar fari, in dai kinsan Khaleesah na wajenta wallahi kiyi maza ki buga mata waya su bar gidan su tafi wani wajen, a ajiye batun kishi a gefe abinda baza ka so ma danka ba kar ka so ma ɗan wani, don duk mun san Abdul ba mutumin kwarai bane, kuma a zamanin nan an dena auren dole, mu ma ba a mana dole ba don haka baza mu yi ma 'ya yan mu ba" Mama Shatu na kai wa nan ta juya ta fice daga dakin, Umma ta mike gabanta na faduwa ta ɗan leka tsakar gidan taga Nenne da Malam Ali tsaye a can lokon tsakar gidan suna magana kasa kasa.... Jay ya fito daga kitchen hannunsa rike da mug din shayi yana juyawa a hankali, Step Mom din Ajay ce zaune parlon cikin shiga ta alfarma, a ranan ta sauka gidan tare da jakadiyarta sun dawo daga kaduna, Jakadiyarta na dinning area tana yanka mata fruit, Jay ya tsaya dai dai inda yake don bata san ya fito daga kitchen din ba, da wani kallon tsana kawai yaga take bin Ajay dake haurawa sama hannunsa rike da laptop dinsa, after few seconds Jay ya ci gaba da juya shayin hannunsa yana kallonta, tana jin sound din cokali ta juya da sauri tana ɗan murmushi ta hau canza channel din TV, shi dai Jay ya karasa cikin parlon bai sake kallonta ba, Jakadiyarta ta taho ta ajiye mata fruit din da ta gama yankawa cikin ladabi take sanar mata ga kayan marmarin, Cike da isa Aunty ta dau Apple ta fara ci, ta ɗan kalli Jay ganin sama zai wuce shi ma tace "Gobe Abbanku zai shigo wani taro" Jay yace "Mun yi waya da shi" Daga haka shi ma ya wuce sama, ta wani taɓe baki ta bi sa da kallo, Jakadiyar da ta zube gefenta cikin girmamawa tayi kasa da murya tace "Ranki shi dade, Allah ya ja zamaninki, daxu bayan saukan mu gidan nan na jiyo mana wani labari, Allah ya sa zaki yi maraba da wannan labarin" A takaice Aunty tace "Labari akan me?" Jakadiyar ta gyara zama murya can kasa tace "Akan Yarima" Aunty ta ajiye Apple din hannunta ta ba jakadiyar gaba daya attention dinta tace "Me kika jiyo?" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 40 Har mahaifin Abdul ya gama bambamin da yake yi a parlon Momy kamar zai ari baki bata ce masa komai ba illa rungume hannu da ta yi tana zaune kan kujera tana girgiza kafa fuskarta babu fara'a, Meemah dake zaune parlon ita ma dai bata ce komai ba fuska a murtuke, Alhaji Musa yayi bala'in sa me isarsa sannan ya juya zai bar parlon a fusace, sai kuma ya sake dawowa yana huci yace "Ina wawan Abdallan yake? Ina yake yaga abinda rashin tunaninsa da rashin daukan shawarar sa ya ja min" Momy ta tabe baki ita ma cike da takaici tace "Ai Alhaji yau kwana uku curr rabonsa ma da gidan gaba daya, kuma ba a samun sa a waya, ya kashe wayar" Rai bace Alhaji Musa yace "Duk shi ya ja min wannan bala'i ina zamana, wa yace masa dama ana harkar arziki da talaka? Sam ai ba a shige ma talaka duk yanda yake kuwa, tun asali zuri'ar da yake son in hada da wancan barawon mutumi ba wai nayi na'am da hakan bane, kawai bani da yanda zan yi da Abdallah ne" Momy ta gyara zama zuciyarta na tafarfasa tace "Atoh dai, har na gaji da nanata wannan sentence din da kayi Alhaji, ai ba a abun arziki da talaka don tun asali dama a tsiyace ya zo duniya kuma a tsiyace zai koma, kana zaman zaman ka gashi Abdullah ya ja maka asaran makudan kudi har da su taran kotu, wai kai da aka zalunta kai ne kuma da biyan tara saboda rashin adalci, ai Abdul bai kyauta mana bai duba mana ba, ace shi bazai dau maganata a matsayina na uwarsa ba? Babu yanda banyi discouraging dinsa kan tsinanniyar yarinyar nan ba na nuna masa ba ajinsa bace yaki saurarata wallahi, kyanta ne kawai ya rudesa wato kyan ɗan maciji, har tayin er aminiyata nayi masa amma firr yaron nan yaki, to ga dai abinda ya ja mana" Meemah tace "Ni duk ba wannan ba Momy, kawai so nake in san wasu 'ya yan shegun ne suka tsaya mata haka har suka maida case din kotu? Sannan ga auren ma suna kokarin kotu ta rabasa ta karfi da yaji, kun ga kenan mun tashi a tutar babu, kuma babu tantama duk yanda aka yi ma su suka boye yarinyar, su waye en iskan nan ne?" Alhaji Musa na safa da marwa a parlon yace "Don kotu ta kori karar nan ba shi ke nufin na bar wannan mutumi da ya salwantar min da dukiya ba, mu zuba mu gani da shi, sai na lahira ya fi sa jin dadi wallahi" Daga haka ya bar parlon kamar zai tashi sama, Momy ta sauke wani ajiyar zuciyar takaici tana girgiza kai tace "Abdallah bai duba mana ba wallahi, ya kaskantar da mu a idon duniya kawai, wai yau talaka ne ya ci nasara a kan mu a kotu, this is a big slap to us, kuma ko uban menene dalilinsa na dinga kashe waya ba a samun sa oho? Ni taran da aka ci Alhaji ne ma yafi ƙona min rai wallahi, ga mari ga tsinka jaka, ki sake kiran wayarsa kiji ko zai shiga" Meemah tace "Baza fa a samesa a waya ba Momy, mu da ganin Abdallah sai ya cika burin dake ransa kema ai kin san halinsa, gwara ma ki saka ma ranki salama mu bi sa da addu'a kawai" Momy ta kalleta tace "Wato kin san inda yake kenan?" Meemah tace "Ke dai kawai ki bi sa da addu'a Allah ya basa nasaran abinda ya saka a gaba Momy, amma shegiyar yarinyar nan ai kamar ta shigo gidan nan ne babu me hana hakan, don baza mu yi biyu babu ba" Momy ta tabe baki tace "Har ga Allah ni so nayi kawai ya hakura da er matsiyatan nan Meemah, kada tsautsayi ma yasa a hada iri da ita mu shiga uku, hada iri da talaka ai ci baya ne Meemah, don ni har cikin raina naki jinin talaka wallahi balle in hada zuri'a da su" Meemah tace "To ai dama bama fatan a hada iri da ita Momy, personally bazan ma bar hakan ya faru ba trust me, kawai ta shigo gidan ta gane Allah daya ne, ke kuma ki fara masa fafutukar wani auren da wuri wuri" Momy dai tayi shiru, can ta tabe baki tace "Allah ya sa ya saurareni to" Meemah tace "Haba dai zai saurareki, da kaina zan masa magana, a samar masa yarinya dai dai class dinsa" Momy tace "To ai shikenan, yanxu tracing din matsiyaciyar yarinyar ya sa a masa kenan?" Meemah tace "Ko ma dai menene mu dai mu zuba ido mu bi sa da addu'a kawai Momy" Mikewa Momy tayi tace "Bari in je in lallaba babanku, na dade ban ga ransa ya baci irin haka ba, haba ai abun da bacin rai, wai ace talaka yayi nasara akan ka a kotu bayan kai ne me gaskiya ai abun da ciwo" Daga haka ta wuce sama, Meemah ta dau wayarta tayi dailing number da take samun Abdul da shi ta tashi ta shiga dakin dake parlon. Da asuba ko sallah ba ayi Malam Ali ya fito da er jakar da yake tafiya da shi bayan ya mulke jikinsa da basilin saboda sanyin da ake, bin dakunan matan nasa yayi duk ya kwankwasa masu kofa, Mama Zubaida da Mama Shatu suka fito suna kallonsa da mamaki suka ce "Lafiya Malam?" Mama Zubaida tace "Ko tafiya kauyen ne ya taso?" Shi dai bai tanka su ba ya dinga goge takalminsa da yayi ƙura, Umma ce karshen fitowa ita ma ta tsaya tana kallonsa ta kasa cewa komai don tasan manufarsa, ko baccin kirki bata yi ba daren jiya tsabar yanda hankalinta ya tashi, Nenne ce ta shigo gidan yafe da zaninta tana ganin Malam Ali tace "Yauwa ko sallah kar ka jira kayi idan kaje tashar kayi a can Ali, ga er soyayyiyar nama da gurasa na kullo maka ka ci a hanya" Mama Shatu tace "Tafiya zai yi ne Nenne?" Nenne tace "Babu ruwan ku, ku dai ku yi masa fatan Allah ya kiyaye hanya" Malam Ali ya amshi kullin nama da gurasan da Nenne ke mika masa, yana kallon matan nasa yace "Toh sai Allah yayi min dawowa" Mama Shatu tace "To ai shikenan, Allah Ubangiji ya tsare Malam" Mama Zubaida ma tace "Allah ya tsare duk da muna da hakkin ka sanar mana inda zaka je da asuban fari Malam" Nenne tace "Bazai sanar ba Zubaida, uban me sanin inda za shi zai kara maki?" Mama Zubaida ta juya ta koma daki, Mama Shatu ma ta tabe baki ta koma dakinta, Nenne ta kalli Umma tace "Wato ke ce isasshiyar da bazata yi masa Allah ya kiyaye ba ko Zahra'u" Shi dai Malam Ali tuni har ya fice daga gidan, Nenne na nuna Umma tace "Mugun abun ku zai kare maku da ke da er ki wallahi, babu wanda ya isa ya salwantar min da ɗa na lokacinsa bai yi ba" Daga haka ta bi bayan Malam Ali da sauri zata rakasa bakin titi ya samu adaidaita sahun da zai kai sa tasha. That same day bayan an idar da sallahn asuba Jay ya shigo parlorn Mai martaba da sleepy face ta dalilin kiran da yayi masa, ganin irin zaman da Abba yayi kamar yana fadarsa ya gane serious issue Abban zai yi discussing da su kenan, ya kalli Ajay dake parlon zaune shi ma alamar kiran sa Abban yayi, Aunty ma na zaune parlon, Jay ya sauke kansa ya karasa kusa da Ajay ya zauna kasan lallausan carpet din parlon, dabi'ar Abba ne sai ya iya minti biyar zuwa goma kamar me nazari kafin ya fara magana in ya tara ku, Jay ya sunkuyar da kansa ya lumshe ido, Ajay ya ɗan kallesa sanin sai ya iya bacci a haka, ai ko yaga baccin yake, Ajay ya ɗan tunkudesa da elbow dinsa, Jay ya bude ido da sauri yana gyara zama, shi dai Abba kallonsu kawai yake, At last Abba yayi gyaran murya cikin nutsuwa yace "First of.... Ina son sanin zaman me ku ke har yanxu a garin nan baku karasa gida ba?" Duk suka yi shiru babu wanda yace komai kansu a kasa, Calmy Abba yace "Ohk take ur time, amma kuyi kokari ku je gida kafin hutun ku ya kare, Secondly.... maganar da nayi da ku a Maryland naji babu wanda yace min komai a kai har yanxu, ga lokacin da na baku ya cika, nayi maku uxurin mantuwa shi yasa nake tunatar da ku yanxu..." Nan ma duk suka yi shiru babu wanda yace komai, shi ma Abban yayi shiru yana kallonsu yana jiran amsa a duk sanda suka shirya, sun san shirun da Mai martaba yayi amsarsu yake kira ko da zai dau 10min ko fin haka ma kafin su basa amsan he won't mind zai jira su patiently, sanin halin Abban nasa yasa Ajay ya daga kai, Softly yace "Ayi hakuri ranka shi dade ba mantawa muka yi ba, in sha Allah we are working on that very soon" Mai martaba yace "Is that so?" Ajay ya sauke kansa don kalman Abba na nufin bai gamsu da abinda yace ba kenan, Shi dai Jay yaki dago kai, a hankali Ajay yace "A gafarce mu a ɗan kara mana lokaci Abba..." Aunty da har ta fahimci maganar da ake ta ɗan yi gyaran murya ta nemi permission din magana gun Mai martaba, ya gyada mata kai alamar ta fadi abinda zata fada, cikin nutsuwa tace "In na fahimci maganar da ake ranka shi dade, magana ce akan su fito da matan aure duba da yanda shekarunsu ke gaba ba baya ba, wannan magana kuma ba sabuwar magana bace don an fi shekara 3 ana yin ta amma babu wani progress, a takaice basa daukar maganar da muhimmanci, to amma dai ina ga ka ɗan sha'afa ne ur Highness, don shi Jawwad ai akwai maganar sa da Hadeeyah a kasa duk da ba wai maganar tayi karfi bane kuma wannan hadi, hadi ne me kyau da zai kara karfafa zumunci don mahaifiyar Hadeeyah jininka ce kuma ita ta kawo wannan shawara duk da Fulani wato mahaifiyar Jawwad uwar dakinta ce tun asali, shi kuma Junaid a yanda na lura da shi zai fi maraba da zabin ka garesa duba da nature dinsa da rashin choice dinsa, don haka shi Jawwad a tsaida maganar sa da Hadeeyah kawai ina ga hakan zai fi, shi kuma Yarima i think we should get him a princess from neighbouring states, ko ni zan iya jagorantar hakan don arranged marriage zai fi suiting dinsa duba da nature dinsa, kuma ina son a bar komai a hannuna ranka shi dade..." Ajay ya daga kai ya kalleta zai yi magana mai martaba ya dakatar da shi, Ajay ya sauke kansa, Speaking Calmly Mai martaba dake kallon Ajay da Jay yace "Za ku iya tafiya, Allah yayi maku albarka" Sai a sannan Jawwad ya dago kai ya kalli Aunty dake ɗan murmushi ganin Mai martaba yayi na'am da shawaranta, tuni Ajay har yayi disappearing daga parlorn fuska a murtuke, Jay ya mike shi ma ya bi bayan Ajay yana tafiya a hankali, bai taɓa sanin baya son Hadeeyah da aure ba sai yau da Aunty ke bada shawaran a tsaida ranan aurensu da ita, yasan kuma duk abinda Aunty tace kamar Abba ya aikata hakan ya gama ne, kawai yaji hankalinsa yayi mugun tashi yaji wani zufa na keto masa, dakinsa ya shige ya kulle da makulli ya jingina da kofar ya lumshe ido zuciyarsa na bugawa, Ajay na shiga dakinsa shi ma ya kulle da makulli ya zauna gefen gado ya dafe kansa da hannu biyu, this is not the first time da Aunty ke kasalanda akan duk abinda ya shafesa gashi Abbansa baya basa listening ears ko me Aunty tace masa kawai haka za ayi abun nan komin munin abun, at this point he felt he is of no importance to his father, he felt dejected, and it's been like this for so many years, he have no one to stand for him, a hankali ya juya yana kallon wayarsa dake vibrate, Number Aunty Farida ya gani a gaban screen din wayar, ya kalli agogo yaga karfe shidda da minti biyar na safe, request din Khaleesat na jiya da ta kirasa ya tuna, hakan yasa har kiran ya katse bai daga ba knowing she might be the one calling, kiran ya sake shigowa ya kalli screen din nan ma bai daga ba har ya katse, sau hudu kiran na shigowa continuously, hakan yasa ya maida attention dinsa kan wayar ya ɗan yi jim with different thought running his mind, ganin kiran ya katse an sake kira making it the 5th time of calling yasa ya dau wayar ya daga ya kai kunne yayi shiru waiting to hear who is on the line, a hankali ya mike jin abinda Aunty Farida ke ce masa ta wayar, bai san sanda ya zame wayar daga kunnensa ba rate din heartbeat dinsa na karuwa, da sauri ya nufi kofarsa ya bude ya fice daga dakin ya murda kofar dakin Jay yaji a kulle, knocking ya dinga yi non stop kafin Jay ya bude kofar da mamaki yana kallonsa yace "What is it?" Ajay ya shiga dakin yana shafa gashin kansa da wani expression yace "He tracked her to Lagos" Still Jay yayi a inda yake tsaye ko kwakkwaran motsi baya yi yana kallon Ajay, Ajay ya ja numfashi sannan ya zauna kan kujeran dakin ya lumshe idanuwansa ya jinginar da kansa jikin kujeran trying to calm himself, Jay was speechless and shock at the same time, da kyar ya ja kafa ya zauna gefen gadonsa ya dafe kansa da yaji yayi masa nauyi, kamar an tsikare Ajay ya mike yace "Book us ticket to Lagos" Daga haka ya fice daga dakin. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Akwai wani abu da yake iya faɗakar da tunani tun daga nesa... Wani ƙamshi da yake sa zuciya bugawa da sauri... Wani ɗanɗano mai narkar da zuciyar masoyi... Wannan shi ne ƙamshin *Scent Palace* *Scent Palace*, da ke cikin birnin Gombe, shine gidan turaruka na musamman da ke kawo muku turaruka masu inganci daga cikin gida da waje masu ɗorewa, masu daɗin shaƙa, kuma masu burgewa Idan kina son turare da zai saka masoyinki ya ƙara zurfafa soyayyarsa gare ki ko kuma turare da zai sanya ki zama abar misali a wajen jama’a to *Scent Palace* shine mafita. Abubuwan da muke da su sun haɗa da: Turaren jiki (body spray/perfume) na mata da maza Turaren gida da ɗaki Turaren mota Turaren wuta na gargajiya da zamani Eid Gift Boxes an tanada musamman domin ku da masoyanku Me yasa *Scent Palace*? ✔ Ingantattun turaruka daga ƙasashen waje ✔ Farashi mai sauƙi da rangwamen Sallah ✔ Kyaututtuka da aka shirya cikin kwali na alfarma ✔ Nationwide delivery *Scent Palace* ba kawai turare ba ne ƙamshi ne da ke ƙarfafa soyayya, daɗi, da kima Tuntube mu yau don odar ki: 📍 Gombe 📞 08038888936 Instagram/Facebook/WhatsApp:08038888936,08154812224 *Scent Palace* Ƙamshin da ke bayyanar da ƙima! Ƙamshi ba wai kawai ƙamshi ba magana ce ta zuciya HALYSAAH 41 Aunty Farida ta share hawayen da yaki tsaya mata tana kallonsu Ajay da kyar tace "Wallahi ban san ko har su nawa bane a motar, ban ma san ya motar take ba tunda ina cikin gida sanda abun ya faru, yaran makota dake diban ruwa a bakin rijiyar tare da ita ne suke cewa kawai suna diban ruwa sai ga motar ta shigo street din, wasu mutane suka sauka a motar suka ja ta zuwa cikin motar suka tafi da ita, a sannan an idar da sallahn subahi kenan kun ga gari bai waye ba ai" Ajay was speechless, bai taɓa zama confuse haka a rayuwar sa ba don ya ma rasa abun cewa, likewise Jay dake jingine jikin mota tun da suka iso unguwan dama shi bai ce komai ba, Ajay ya daga kai after some seconds ya kalli Aunty Farida a hankali yace "Amma yana da number ki ne Aunty?" Aunty Farida tace "Ba shi da wannan number tawa gaskiya sai tsohon layi na, kwanaki Maman Khaleesat tayi rashin lafiya sai na tafi kano dubata to a hanya na yar da wayata, da na zo kano sai na siya sabon layi kafin inyi welcome back din tsohon layin, to har yanxu ban yi welcome back din ba" Ajay yayi shiru yana nazari, Aunty Farida na hawaye tace "Tsautsayi yasa ta fita deban ruwan yau, amma tunda ta xo wallahi ni ke diban ruwana bana barin ta dibar min tunda har yanxu gata nan ne dai bata dawo dai dai ba, wani lkcn ma da daddare idan na dawo kasuwa nake yi tunda ana wahalar ruwa a season din nan don yawanci rijiyoyi kafewa suke yi sai ana bari ruwan na taruwa sannan a diba, gashi ba a samun wuta balle a samu ruwan pampo, a jiyan nayi girki me yawa ne na wani biki duk sai na gaji ban deba ruwan da daddare ba, da na tashi kuma sai nake jin zazzabi, kun ji dalilin fitarta ta debo mana ruwa kenan" Ajay ya jingina da motarsa ya lumshe ido ya bude, gaba daya ƙansa ya gama kullewa, bai yi zaton Abdul ya wuce yanda yayi zatonsa ba, the guy is really something else ko wani salon tactics na mugunta ya san sa gashi har yau yaki kunna wayarsa balle a san inda yake, ko by mistake baya kunna layin, shi dai Jay dama bai taɓa underrating Abdul ba dai dai da rana daya duba da irin actions din da ya dinga portraying, kawai dai tracing din Halysaah har zuwa Lagos is the least thing da yayi zaton Abdul zai yi, tunda bashi da access da Aunt dinta, but like seriously how did he even find his way, bayan bashi da active line din Aunty Farida sannan bai san unguwan da take ba, ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya yana tunanin ta inda za su fara billo ma wannan lamari, tunda dai babu ta yanda za su ce yayi kidnapping Halysaah da ke a matsayin matarsa ta sunna. Khaleesat na zaune at the far end of the large room ta hade kanta da gwiwa, zuwa sannan ta hakura da kukan da take don ba ma ta da strength din kukan amma tana jin zuciyarta na mata zafi ga wani azababben ciwon kan da take ji da kishin ruwa da ya dameta, tafi awa sha biyu zaune a dakin ba ci ba sha, don tunda aka shigo da ita har zuwa sannan babu wanda ya sake zuwa dakin, infact bata ji motsin kowa a gidan ba alamar ita kadai ce a ciki, bandakin dake cikin dakin take shiga tayi alwala ta fito tayi sallah duk da ba sanin lokaci tayi ba kawai tana amfani da instinct dinta ne, at this point in time tasan bata da wani sauran gata sai wajen Allah, domin kuwa tasan Abdallah ne kawai zai sa a zo ayi mata irin wannan daukan, wasu hawaye masu zafi suka zubo idonta tana tausayin rayuwarta, all she could remember vividly was that tana bakin rijiyan dake kusa da gidansu Aunty Farida tana diban ruwa wasu mutane biyu suka zo a mota, lokaci daya kuma suka yi leading dinta zuwa motar tasu, at first turje masu tayi ta fara kokarin raising alarm tana ihu, yaran dake bakin rijiyan duk suka gudu suka shige gidajensu, tana kururuwa daya mutumin ya rufe fuskarta da wani Handkerchief da sauri, taji ta shaƙi wani abu kamar dust, lkci daya kuma ya cire handkerchief din a fuskarta, daga nan kuma ko kokarin ihun bata sake yi ba cause she became weak, ita dai tasan all through the ride she was conscious but not fully, gashi ta kasa tabuka komai don duk jikinta ya mutu, kanta yayi mata nauyi idonta suka dinga juya mata.... Da sauri Khaleesat ta dago kanta ta mike tsaye jin ana ƙoƙarin bude kofar dakin ta waje da makulli, gabanta ya dinga bugawa da karfi idonta na kan kofar har ya bude ya shigo, she wasn't expecting anyone but him dama, ta sauke kanta bayan sun hada ido, wasu sabbin hawayen suka fara zuba idonta, muryarsa taji ya daki kunnenta cike da isa da gadara yace "Har yanxu Body guards din naki basu biyo bayanki bane? Ai yaci ace sun iso zuwa yanxu don naga It's almost 12 hours now, how comes basu zo cecen ki ba duk capacity din su" Sai a sannan Khaleesat ta daga kai ta kallesa cikin rawar murya tace "Ka ji tsoron Allah...." Kasa ci gaba tayi ta fashe da matsanancin kukan takaici, shi dai yana tsaye yana kallonta da wani murmushin mugunta kwance fuskarsa, ta dago kai da sauri jin yana takowa har zuwa inda take tsaye, mannewa tayi da bango tana jin kamar bangon ya tsage kawai ta shige gabanta na bugawa da karfi, sai da ya zo dab da ita cikin kwantar da murya yace "Me kika ce?" Ta girgiza masa kai da kyar gabanta na ci gaba da faduwa muryarta na rawa tace "Kaji tsoron Allah Ya Abdul, kaji tsoron...." Bata rufe baki ba taji saukan lafiyayyen mari a fuskarta wanda sai da taga taurari, ta dafe kuncinta tana kallonsa babu ko kiftawa, cikin husky voice dinsa yace "You still have the guts to repeat what u just said saboda baki da kunya ko? Ni zaki gaya ma in ji tsoron Allah? To tsoronki zan ji ko tsoron uban ki dake Mariri idan ban ji tsoron Allah ba?" Da kyar Khaleesat ta dake tace "Ka zageni amma kar ka sake zagar min uba" Still bata rufe baki ba ya sake sauke mata wani wawan marin a other side of her face, this time around sai da dakin ya juya mata don ba marin wasa yayi mata ba, ya fixgota yana mata wani irin kallon da ya gigitata don tuni idonsa yayi jajur yana huci yace "Ina magana kina mayar min how dare you poor wretched girl?" Ta fashe da matsanancin kuka tana jin dama Allah ya dau ranta kawai ta huta a wannan lokacin, zata durkusa kasa ya hadeta da bango yace "Yau ina body Guards din naki dake goya maki baya kina min iskanci? Tell me where they are today? Da aurena a kanki kike hulda da wasu banzayen gardawa saboda ke jahila ce warce bata san me take ba" Tana kuka sosai bata san sanda tace "To wai ana aure dole ne dama Abdul? Nace bana son auren, bana son ka, gwara kawai ka kasheni duk mu huta" Da karfi ya bugata da bango har sai da taji numfashinta ya dauke na few seconds, yana mata wani mugun kallo yana huci yace "Dama ke baki san aurena wajibi ne a gare ki ba ko kina so ko ba kya so? Dama shi ubanki bai gaya maki hakan ba ko mantawa kika yi saboda kin fara bin maza? Wallahil Azeem kin ji rantsuwar musulmi ko? Duk ranan da kika sake yunkurin guduwa ko kuma yin wani silly act to rayukan twin siblings din ki za su zama fansar aurena idan kika kuskura kika min jakanci, ko kina so ko baki so lallai dole ki zauna da ni ko kuma in salwantar da ran kanninki i am promising you this Billahil Azeem, kuma babu abinda zai faru don tamkar na kashe banza ne daga ke har iyayenki babu abinda za ku yi, su kansu Body guards din naki ba kyalesu nayi ba don sai na dau revenge din intruding da suka yi a sabgata, i will teach them a lesson kina ji kuma kina gani" Khaleesat ta kasa cewa komai don sama sama kawai take jin numfashinta kalmansa na cewa zai salwantar mata da siblings dinta ya sa jikinta ya fara rawa, ya juya cike da isa ya tafi ya bude closet din dakin wanda duk kananun shegun kaya ne yace "All this are your wears, in kin yi sallah kin shirya ki zo ki sameni a dakina which is 3 rooms away from this, ina jiranki at exactly 7pm and this is just 6:30pm" Yana kai wa nan ya fice daga dakin yana rike da key din dakin, a hankali Khaleesat ta sulale kasa tana sauke numfashi tana jin wani abu ya tsaya mata cak a zuciya, gashi ba ta ma da strength din da zata yi kuka sosai ko zata ji relieve don tun jiya rabonta da abinci, she was just weak and helpless, ga idonta da taji ya fara ciwo saboda marin da yayi mata don dama ba warkewa idon yayi gaba daya ba lkci lkci tana jin yana damunta, tsoro da fargaban kada ya sake dawowa dakin yayi mata fiye da abinda yayi mata yasa Khaleesat tayi karfin halin mikewa da ɗan sauran strength din ta da ya rage tana tafiya da kyar ta shiga bandakin dake cikin dakin ta tara ruwan pampo tana sha ko zata ji saukin abinda take ji a zuciyarta, bayan ta sha ruwan ta dinga kallon fuskarta da yayi ja ta madubi, a hankali ta zame kasan bandakin ta jingina da tile din bangon hawaye masu zafi na zarya a fuskarta, tafi minti goma a haka lokaci daya ta yunkura ta mike bayan ta tuna time din da ya bata kar ya sake dawowa, she wish akwai makulli a jikin kofar bandakin don da kulle bathroom din kawai zata yi in ma mutuwa ne tayi a haka don yafi mata kasancewa da Abdul, cikin rashin kuzari ta cire hijab dinta da kayan baccin dake jikinta ta fara wanka da shower gel din dake bandakin, komai na bukatar mace akwai a banɗakin everything is just set, after a while ta gama wankan ta wanke bakinta ta fito sanye da dogon hijab dinta with different thoughts running her mind, tunda ya bar kofar dakin a bude ko dai ta samu ta lallaba ta fita and find a way for her self, duk da tasan Abdul will never be that stupid da zai bar kofa a bude har ta samu ta fita, infact in ma ta fita daga building din gidan tasan definitely akwai mai gadi a bakin gate kuma babu ta yanda zai bar ta ta fita, kilan ma Abdul din ya sanar masa in zata fita kar ya bude mata gate, but still ita dai burinta ta samu ko daki me makulli ne ta shige ciki ta kulle kofar sannan ta bar key din a jiki yanda ko spare key idan aka saka za a bude kofar bazai budu ba sbda key din da ta bari a jiki, da wannan tunanin ta nufi kofa gabanta na faduwa ta bude kofar dakin a hankali zata fita suka kusa cin karo da shi, rikicewa tayi ta juya da sauri zata bar bakin kofar ya fixgota, bakinta na rawa tace "I am very thirsty" fuskarsa babu wani rahama yace "Follow me" Bata iya ta masa musu ba tunda taga kiris yake jira ya mareta a ko da yaushe, at every slight opportunity marin ta kawai yake, tana biye da shi zuciyarta na bugawa suka shigo Main parlor din gidan, karshen haduwa gidan ya hadu amma ita ko lura da hakan bata yi ba don ta kanta kawai take, tana biye da shi ya kai ta har kitchen din gidan, ya juya ya kalleta a takaice yace "Gashi nan ki dafa abinda zaki ci don bani da time din fita in siya maki komai tunda kina da hannun girki, after that ki dafa min lipton ki kai min dakin da nace" Ita dai Khaleesat na rakube jikin kofar kitchen din gaba daya hankalinta baya jikinta, taga yayi ficewarsa ya bar mata kitchen din, ta bi sa da kallo har ta dena ganinsa, ta zame kasa ta hade kanta da gwiwa cikin rawan murya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace" ta kusa minti biyar a haka kafin ta yunkura ta mike tana goge hawayen da yaki tsaya mata, tana tafiya a hankali ta nufi kofar parlon ta murda taji a kulle kuma babu makullin a jiki she wasn't surprise don tasan dole zai kulle gidan, haka duk sai da ta bi dakunan dake gidan ta murda su taji a kulle kuma babu makullansu a jiki, a sanyaye hawaye na bin fuskarta ta koma kitchen din, duk da rabonta da abinci tun jiya amma ko yunwan bata ji tsabar tashin hankali, kawai jikinta ne yayi weak taji strength dinta duk ya kare, wnn yasa ta ɗan hada shayi kadan a cup zata sha, shi ma dai ta kasa sha don bata da appetite, haka nan ta zubar ta dau black tea din da yace ta dafa masa ta fito daga kitchen din, dai dai san da ya shigo parlon, sunkuyar da kai tayi rate din heartbeat dinta na karuwa cause he is just wearing short and singlet, cike da karfin hali tace "Ga tea din" Babu yabo babu fallasa taji yace "A nan nace ki bani tea?" Ita dai bata ce komai ba amma kana ganinta kasan a mugun tsorace take, tana hade hanya ta nufi inda yace ta kai masa shayin yana biye da ita a baya, da ace tashin hankali da fargaba na kashe mutum ya ci ace ya kashe Khaleesat a wnn moment din, a bakin kofar dakin ta tsaya cikin rawan murya tace "Ga tea din" Wani tsawan da ya kidimata yayi mata don bata ma san sanda ta shige dakin ba ta je ta ajiye masa Mug din tea din a kasa tana waige waige, ya shigo dakin ya tura kofar fuska a daure yace "Cire Hijab din nan, kuma yau ya zama first and the very last day da zaki min yawo da Hijab a gida" Ta durkusa kasa ta fashe masa da kukan tashin hankali tana kallonsa, ya mata tsawa yace "Are you daft?" Cikin kuka tace "Wallahi sallah nake son inyi ne kayi hakuri" Darduma ya nuna mata a takaice yace "Je kiyi" Jiki na rawa ta mike ta tafi kan darduman ta fara sallah jikinta na rawa, tayi raka'a ya fi sha biyar ita kanta bata sani ba, kawai daga bayanta taji ya fixge hijab din, tun bai karasa cirewa ba ta fara kokuwa da shi ta rike hijab din gam tana kiran Ummanta cikin rikicewa, amma da yayi mata wani riko da hannu daya sai da ta gane Allah daya ne, don ko kwakkwaran motsi kasawa tayi, tana ji tana gani ya fixge hijab din ya jefar da ita kan gado rokonsa ta dinga yi da duk kalman da ya fito bakinta tana cewa "Ina rokon ka da girman Allah kayi hakuri Yaya Abdul, don Allah ka min rai kayi hakuri, in kana yi ma darajan iyayenka kayi hakuri, wallahi ban gama sallan da nake ba...." Ya gama kare mata kallo at the same time yana surveying every bit of her beautiful and breathe taking body, komai yayi masa yanda ya kamata, ashe asalin kyanta na boye all this while bai sani ba, yayi tarayya da mata iri iri amma bai taɓa ganin mace that is so beautiful while naked kamar ta ba, iya haskenta kadai ya isa ya rikita mutum, tuni idanuwansa suka sauya launi ya cire singlet dinsa yana kallonta kasa kasa yace "In ma kika yi taurin kai kece a wahale don that isn't stopping me in anyway Baby gal, just relax and i won't be rough" Kara gigicewa Khaleesat tayi tana rokonsa at the same time tana kokarin sauka daga kan gadon ya fixgota ya mayar da ita saman gadon yana kallonta cikin husky voice dinsa yace "Do not allow me give you a dirty slap...." Bata ma san me yake cewa ba still zata sake sauka taji ya danneta kan gadon, roughly ya fara exploring dinta kamar ya samu er hannu.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 42 Ko minti uku Abdul bai yi da fara taɓa ta ba Khaleesat taga ya koma gefe lkci daya, da sauri ta mike tana komawa baya har sannan bata dena kukan da take tana basa hakuri ba cikin rikicewa, after some seconds ya juya ya kalleta da rinannun idonsa, suna hada ido ta kara rikicewa muryarta na rawa cikin kuka take cewa "Don girman Allah kayi hakuri, i am begging you please kayi hakuri" Ya jefa mata wani kallo ya mike kamar zai tashi sama ya nufi kofa ya fice daga dakin, ganin hakan tayi kamar a mafarki ta kasa ko kwakkwaran motsi, kamar ance ta sauke kanta taga jinin da ya ɓata farin zanin gadon da take kai, ta dinga komawa baya a hankali tana kallon jinin babu ko kiftawa zuciyarta na bugawa at the same time, and she realize daga jikinta yake fita, lokaci daya ta tuna rabonta da period tun a Maryland almost a month and some days, from nowhere taji relieve ya zo mata, ta jingina da jikin gadon hawaye masu zafi na sauka idonta, tafi minti biyar a hakan ganin zata ci gaba da soiling zanin gadon ta sauka ta dau hijab dinta ta rungume, har sannan jikinta bai daina rawa ba, tana ta tsaye a dakin tana tunanin yanda zata yi, ta kalli kafarta jin period din yana gangaro mata, ajiye hijab dinta tayi ta shiga bandakin da ke cikin dakin, after few minutes ta fito ta dau hijab dinta ta saka, tana kallon zanin gadon da ya baci ta fara ƙoƙarin cirewa a hankali har ta cire gaba daya, bude kofar dakin taji anyi ta mike tsaye da sauri zuciyarta na bugawa tana kallonsa, ya wani harareta yace "What are you using that for?" Bakinta na rawa tace "A'a wankesa zan yi ne" Yace "Ajiye bana so, zo ki fitar min a daki" Ta sunkuyar da kanta babu musu ta ajiye zanin gadon a gefen gado ta nufi kofa a tsorace kamar munafuka, amma ta kasa bin gefensa ta fita daga dakin saboda fargaba, gashi he is blocking the way, ta fi 30 seconds tsaye zuciyarta na bugawa ta kasa fita, shi dai kallonta kawai yake babu yabo babu fallasa, da kyar tace "Zan wuce" Ganin kallon da yake mata bata sake cewa komai ba haka nan ta raɓa ta gefensa ta fita daga dakin, kallon inda ta tsaya yake don nan din ma dai sai da tayi staining dinsa da jini, ita dai tuni har ta shige dakin da aka fara ajiyeta ta tafi bandaki da sauri tana jin maranta na kullewa, ita da ko ciwon mara bata yi sai dai wani lkcn tayi ciwon baya ko kafafuwanta su rike shi ma kawai na 'yan awanni ne, ta samu dai ta wanke jikinta ta fito tana dukawa sbda ciwon da take ji a mara, a haka ta bude closet din da ya nuna mata tana duba ko zata ga pad, amma taga babu alamarsa, ta fara tunanin yanda zata yi gashi tana jin alamar saukan period din nata a jikinta, ita ko da kyalle ne idan ta samu zata iya manage da shi, amma duk dube dubenta bata ga alamar akwai kyalle ko dankwali a closet din ba, duk kananun kaya ne, she was so confuse and in pain at the same time, ta rasa yanda zata yi, sai da tayi sahu ya fi a kirga zuwa bandaki ta wanke jikinta ta sake fitowa, kuma a haka ba heavy flow take ba a ranan farko, ko zama ta kasa yi ciwon mara ya addabeta, hawaye ya fara sauka idonta ta karasa kusa da gadon dakin ta durkusa ta daura kanta saman gadon ta lumshe ido trying to endure the pain she is feeling, tafi 20 mins a haka taji budewar kofar dakin, da sauri ta dago kanta daga gefen gadon har sannan tana duke, ta kallesa gabanta na faduwa, ya shigo dakin ya ajiye ledan hannunsa yana mata kallon sama har kasa a takaice yace "Me ye ma'anar hakan?" Muryarta na rawa tace "I am having cramps" Yace "Yaushe kika fara cramps? Is this also among ur lies?" Ta sunkuyar da kanta wasu sabbin hawayen na sauka idonta, yace "Bazan sake fita gidan nan da daddaren nan ba saboda ke, after all mate din ki ne ke enduring labor pain" Ita dai bata ce masa komai ba har ya fita daga dakin, sai a sannan ta dago kanta with tears rolling down her face, ta kalli ledan da ya ajiye, rarrafawa tayi zuwa gun ledan ta bude taga Sanitary pad ne, daya ledan kuma abinci ne da ya siyo mata a eatry da bottle water, ta daure ta mike tsaye da kyar bayan ta cire pad daya ta bude closet ta dau sabon underwear dake ciki ta tafi bandaki, bayan ta gyara jikinta ta wanke hijab dinta da yayi staining a bandakin sannan ta fito, rigan bacci wanda ya ɗan fi sauran mutunci ta dauka ta saka, ya saukar mata har kusa da gwiwa, kasa cin abincin da ya siyo mata tayi, haka nan ta bude ruwan goran ta sha sannan ta dau pillow ta ajiye a kasan dakin ta dau duvet din saman gado ta kwanta tana jin ciwon cikinta na tsananta, ita rabonta da ciwon mara tun ranan farko da ta fara period, haka nan hawaye yayi ta zuba idonta, har ta samu bacci ya dauketa taji budewar kofa, taki bude idonta tayi lamo a inda take bugun zuciyarta na tsananta, ya zagayo har inda take ya duka gabanta, hannu ya kai forehead dinta hakan yasa ta bude ido da sauri, magani ya mika mata da ruwa a hannunsa ta sauke idonta sannan ta daure ta mike zaune ta amshi maganin da ruwan hannunsa ta sha, ajiye sauran ruwan tayi a gefenta har sannan ta kasa kallon idonsa, taji yace "Meye da gadon da baki hau ba?" Kai kawai ta girgiza masa yace "Get on the bed now" Tashi tayi ta koma gefen gadon ta zauna, kana ganinta kasan a tsorace take, ya dau pillow da duvet din ya ajiye mata saman gadon, kwanciya tayi ta lulluba da duvet din ta kulle idonta, tana ji ya fita ya kullo mata dakin, ta bude idonta da sauri taga ya kashe mata wutan dakin, hawaye taji na gangarowa ta gefen idonta, gradually taji ciwon maran ya fara subsiding after almost an hour of taking the drug he gave her, daga nan kuma bata san sanda bacci me nauyi ya dauketa ba, wajen karfe ukun asuba yunwa ta farkar da ita, ta mike zaune tana bin dakin da kallo har wani rawa jikinta yake saboda yunwa don rabonta da abinci tun shekaranjiya ga kuma maganin da ta sha babu komai a cikinta, zamowa tayi daga kan gadon tana laluba ledan abincin da ya kawo mata taga ya dauke, rasa yanda zata yi tayi, tana ta zaune a haka kawai taji ya bude kofar dakin hannunsa rike da wayarsa da ya kunna fitila, shigowansa na uku kenan zuwa dakin amma duk bata sani ba tana bacci, haskata yayi da wayarsa ya karaso cikin dakin ya kunna switch din fitila, ita dai ta sunkuyar da kanta kamar munafuka tana jin zuciyarta na throbbing, yace "Me kike yi a nan?" Sai a sannan ta daga kai da kyar ta marairaice amma bata ce komai ba, ya daure fuska yace "Nace me kike yi a nan?" Da kyar tace "I am hungry" Yace "Me yasa baki ci abincin da na kawo maki jiya ba?" A hankali tace "Na kasa ci" Juyawa yayi ya fita daga dakin, ta lallaba ta koma saman gadon ta kwanta tayi lamo, after almost 10 mins sai gashi ya dawo dakin da abincin bayan yayi microwaving din mata, nan kan bedside drawer ya ajiye mata abincin da ruwan gora, bata jira yace mata komai ba ta mike zaune tana sunkuyar da kai kamar mara gaskiya ta kai hannu ta dau abincin, shi dai yana tsaye yana kallonta, a hankali ta fara cin abincin har sai da ta ci rabi sannan ta kallesa cike da karfin hali tace "Na koshi" Yace "Cinye sa" Bata masa musu ba ta ci gaba da cin abinci har sai da ta cinye, amma fa da kyar ta dinga turawa, ta ajiye plate din a saman beside drawer, juyawa yayi ya fice bayan ya kashe wutan dakin, Khaleesat ta koma ta kwanta tayi lamo kan pillow, ta ma rasa wani tunani zata yi at this point, ta goge hawayen da taji yana gangaro mata, ba ita ta koma bacci ba sai da aka yi sallan asuba. Wajen karfe bakwai na safe ta fito daga wanka daure da towel tana tafiya a hankali ta bude closet din dakin tana tunanin abinda zata saka, kana kallon fuskarta kasan tana cikin damuwa me tsanani, fargabanta yanxu idan ta gama period ya kenan? Ta ina zata fara nema ma kanta solution yanxu, what next? ta fashe da kuka a hankali tana jin kirjinta na mata zafi, ta jingina da closet din tayi kukanta me isanta tana tausayin rayuwarta, daga karshe ta goge hawayenta a sanyaye ta dau wata riga wanda har kasa ne amma it's transparent, ajiyewa tayi gefen gado ta cire hair net din dake kanta tun shekaranjiya, tana tafiya a hankali ta karasa gaban madubin dakin, turarurruka iri iri ne da mayuka, da man kai, ta dau turaren jiki kadan ta shafa sannan ta shafa ma kanta man gashi don tana barin sa ya kara kwana daya a haka bata shafa mai ba duk tangling zai yi barin dama cukuikuyesa kawai tayi cikin Hair net din Aunty Farida, ita ma Aunty Farida haka gashinta yake, infact dukkansu har Umma da su Islam duk texture din gashinsu daya, tana cikin shafa ma gashinta oil aka bude kofar dakin, still tayi a inda take gabanta ya fara faduwa, taki yarda ta kalli direction dinsa, da kyar ta ajiye oil din hannunta ta dau Hair net zata mayar da gashinta ciki, taga ya amshe net din a hannunta ya juyo da ita yana kallonta, ta sunkuyar da kanta kirjinta na heaving shi dai kallonta kawai yake, short ne kadai jikinsa shi ma da alamar he just took his bath, ya jawota jikinsa ya daura goshinsa saman gashinta at the same time yana shafa dogon baƙin gashinta a hankalin, Khaleesat ta runtse ido zuciyarta na bugawa, murya can kasa taji yace "Why did u change ur mind abou me? It's all my fault right?" Jin bata ce komai ba ya dago kanta yana kallonta, kawai jin bakinsa tayi a nata bayan ya lumshe idanuwansa, tsoron turje masa take yi don bata san me zai biyo baya ba idan tayi hakan, jikinta ya dinga rawa kamar me zazzabi hawaye na sauka idonta tana girgiza masa kai amma ta kasa cewa komai kar ya mareta kamar yanda ya saba, a haka ya ja ta zuwa saman gadon dakin yana sarrafata, he made sure he romanced her deeply to the extent that sai da ya birkice mata kamar ba shi ba, daga karshe kuma ya kyaleta kar ya kasa controlling kansa gashi tana period, amma fa sosai ya iya kai zuciyarsa nesa kafin ya kyaleta ya koma can edge din gadon yayi rub da ciki tare da lumshe idonsa, everything about Khaleesat is just perfect for a Man, laushin jikinta kadai ya isa ya kara gigita mutum, Khaleesat ta koma daya side din gadon a hankali take kukan takaici faduwar gabanta ya tsananta, juyawa yayi ya kalleta after some minutes yaga yanda dogon gashinta ya rufe duk fuskarta tana kuka, sai kuma ta zamo a hankali daga saman gadon ta kife kanta da jikin gadon tana shessheka, ji tayi ya dafata ta juyo a firgice tana komawa baya don bata san sanda ya zagayo ba, ya sa hannu biyu ya maida duk gashinta zuwa gefen fuskarta yana kallonta, tuni ta daina kukan da take saboda tsoro, ta sunkuyar da kanta kirjinta na heaving, jawota yayi jikinsa ya rungumeta ya lumshe ido, ita dai tayi tsit tsabar firgici, a haka ta dinga jin bugun zuciyarsa tana jikinsa, they were like that for 3 mins daga karshe taga ya mike a hankali ya fita daga dakin ta bi sa da kallo tana share sabbin hawayen dake sauko mata a fuska, throughout ranan haka Khaleesat tayi ta zama a daki sai dai ya kawo mata abinci, da ta tuno abubuwan da Abdul yayi mata daxu sai ta firgita, sai ya zama kamar tana hallucinating ne, hakan ya dinga sa mata ciwon kai taji kamar zazzabi zai rufeta, saura kadan panic attack ya kamata a dakin banda Allah ya takaita mata, gaba daya yanxu tunanin menene makomar rayuwarta take, shikenan haka zata hakura tayi zaman aure da Abdul ta ci gaba da shanye duk bakin cikin da zai kunsa mata a zaman aurensu bata da me tsaya mata tunda shi din mijinta ne? Did she even have a way out with the way things turn out to be all of a sudden? Is this going to be the beginning of a new era a rayuwarta? Shikenan irin rabuwar da zata yi da su Housemate dinta kenan? Kilan ma ba lallai ta sake ganinsu ba a rayuwarta? Shikenan haka Abdul zai ci gaba da caging dinta a gidansa ga threatening din kashe mata siblings da yayi idan taki zama da shi? Duk wa ennan tunanin suka sa ta dinga kuka tana tausayin sabuwar rayuwar da take kokarin fadawa, don tasan Abdul na gane ta gama period bazai daga mata kafa ba and that is the end of her, kuma shikenan dole ta zauna tayi zaman aure da shi ko da yankan naman jikinta zai dinga yi kuwa don azabtarwa, tunda Ummanta ta haifeta tana jin bata taɓa shiga irin wannan tashin hankalin da take ciki ba a wannan lokacin, tana jin alamar zai shigo dakin take goge fuskarta ta langwabe a zuwan ciwon ciki take.... Cikin wannan yanayin Khaleesat tayi kwana uku a gidan tare da Abdul, a wannan kwanaki ukun kuwa duk da halin da take ciki a haka yake sakawa taje tayi masu girki a kitchen wai shi baya son abincin restaurant, Khaleesat bata taɓa fatan kar period dinta ya dauke ba kamar irin wannan lokacin, she wish she will keep on flowing continuously like the woman with the issue of blood amma tasan dole ya dauke nan da kwana biyu don bata wuce 5 days in tana period, sosai hankalinta ke kara tashi idan ta tuna hakan, yau tunda gari ya waye tayi wanka ta saka pad take kwance kan gado saboda azababben ciwon kan da take, all these pass days bata wani samun baccin kirki da daddare tsabar damuwar da ta saka ma kanta da tunane tunane, daga karshe dai haka ta daure ta fita zuwa kitchen da kyar don dora breakfast kafin ya fito daga dakinsa kamar yanda yayi mata umarni 2 days back, tana fita parlor ta leka compound din gidan taga babu motarsa alamar ya fita, ta murda kofar parlon taji a kulle kamar yanda tayi tunani, Zaunawa tayi kan kujera ta dafe kanta hawaye masu zafi na zuba idonta, after a while ta mike tana shesshekan kuka ta wuce kitchen din, tana cikin hada breakfast taji alamar shigowar motarsa gidan, after a while aka bude kofar parlon, ƙasa kunne tayi jin kamar muryar mace take ji a parlor, can kuma taji tsit, ita dai ta ci gaba da abinda take yi jiki babu kuzari har ta gama ta tsaftace kitchen din sannan ta juya zata fito ta kusa cin karo da wata mace in her late 30's zata shigo kitchen din, daga sama har kasa matar dake tsaye kofar kitchen din take mata wani irin kallo da za a iya kira da kallon kaskanci, ita dai Khaleesat tunda ta kalleta sau daya ta sunkuyar da kanta ita kanta bata san sanda ta gaisheta ba don duk ta rude gashi kuma taga suna kama da Abdul duk da bai taɓa nuna mata wani nasa ko da a hoto ba, a walakance matar tace "Da ban kwana ba zaki gan ni munafukar Allah, Er gidan matsiyata ma ci amana.... A gidan ubanki kika san ni da zaki gaisheni?" Sai a sannan Khaleesat ta sake daga kai tana kallonta da mamaki cause kalmomin matar kawai a bazata suka zo mata, bata san sanda tace "Ki zageni amma banda iyayena...." Bude baki Meema tayi da mamaki tana kallonta ganin guts dinta, kafin tace komai Khaleesat ta bi gefenta zata fice daga kitchen din wanda saura kiris ta bangajeta wajen fitan, cikin zafin nama da bacin rai Meema ta fincikota ta dawo da ita gabanta sannan ta sauke mata wani wawan mari ta shakota tana kokarin kai ta kasa ta nakadi banza, Khaleesat ta kwala wani kara, dai dai isowan Abdul wajen, lkci daya yanayinsa ya canza don a kan idonsa yayar tasa ta sauke ma Khaleesat mari sannan ta shakota tana kokarin dukanta, cikin daga murya yace "Zo ki fita ki bar min gidana Amina, how dare you? Me tayi maki zaki mareta haka? Baki da hankali ne? Get out of my house pls, fita ki bani waje" Sake baki Meema tayi tana kallonsa babu ko kiftawa, cikin zafin nama ya tafi ya bude kofar parlon kirjinsa na sama da kasa yace "Ki fita nace Amina kar in rama mata" Cikin karfin hali Meema ta dafe kirjinta da hannu daya tace "Abdallah ni kake cewa in fita a gidanka?" Ya jefar da wayar hannunsa yana huci ya nufeta kamar zai kai mata duka cikin daga murya yace "Na ce ki fita din ko gidanki ne? Get out of this house before i loose my control Amina, gerrout" Ita dai Khaleesat makalewa tayi jikin kofa jikinta na rawa, sum sum sum Meemah ta karasa ta dau handbag da karamin travelling bag dinta don dama daga airport yaje ya daukota saukanta garin kenan, ta nufi kofar fita parlon sannan ta juya tana kallonsa da mamaki tace "Abdallah ni kake daga ma murya kake cewa in fita in bar gidanka akan wancan matsiyaciyar? Har kake ikirarin zaka kai min hannu? Ni din Abdallah?" Da karfi yace "Duk nayi, fitaa ki bar min gidana malama" Fita tayi daga parlon ya bi bayanta kamar zai tashi sama ya tafi ya bude mata gate din gidan, ta fita yayi banging gate dinsa ya kulle, har ya dawo parlon Khaleesat na makale jikin kofa ita tsabar yanda ta tsorata ma ko digon hawayen marin da Meemah tayi mata babu a idonta, ya karasa kitchen din yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi, sai a sannan taji hawaye ya fara zuba idonta. *Sorry for keeping u waiting* *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* _Assalamu Alaikum yan mata da matan Oga ina me maku albishir da cewa Han-Ash skin beauty ta zo maku da kayan gyaran jiki iri iri wanda zai mayar da fatarki kamar Madara ta yanda duk inda kika shiga sai an kalleki, ki sai mayukan da zesa fatar ki tayi kyau, muna kuma maraba da siyan daya ko sari, i am assuring you that duk wani product dinmu is tested and trusted, ga kuma arha, for more information contact Han Ash via +234 803 810 3096_ HALYSAAH 43 Juyawa Abdul yayi ya fice daga kitchen din ba tare da yace mata komai ba ya dau wayarsa ya nufi dakinsa, Khaleesat ta bi sa da kallo tana goge hawayen dake zuba idonta har ta dena hango sa, jingina tayi da kofar kitchen din ta kai hannunta fuskarta dai dai inda Meemah ta mareta don sai a sannan ta fara jin zafin marin, fashewa tayi da kuka tayi me isarta kafin ta fito daga kitchen din tana tafiya a hankali ta tafi ta zauna kan 1 seater dake parlorn tana share hawayen da yaki tsaya mata, abubuwan da Abdul yayi ma Meemah ne suka dinga dawo mata a kai don hakan yayi mugun shock dinta, but she just don't want to believe senior sister dinsa yayi harrassing haka har da koranta, to ko dai ita ce Aunty Aminan da suke ce ma Meemah don taga sosai suke kama da ita, tana ta zaune parlon bayan wani lokaci sai gashi ya fito daga dakinsa, sunkuyar da kanta tayi tana wasa da fingers dinta, ya karaso cikin parlon yace "Kin yi breakfast din ne?" Da Authoritative voice yayi tambayar yana kallonta, hakan yasa ta ɗan rikice kamar mara gaskiya ta girgiza masa kai with fear all over her face, sai kuma ta mike da sauri ta nufi kitchen ya bi ta da kallo har ta shiga ciki, shayi rabin cup ta hada sannan debi Irish kadan a plate don tension yasa ta rasa appetite dinta gaba daya , sai kuma ta tuna shi ma bata basa breakfast din ba, tunanin ko ta kai masa parlor ta fara yi don a kwanaki ukun nan Bedroom dinsa take kai masa breakfast din kamar yanda ya umarce ta, kamar munafuka ta makale jikin kofar kitchen din tana kallonsa tana son tambayarsa ko ta kawo masa breakfast din nasa parlorn amma ta kasa don bata san me zai ce ba kar yayi mata masifa, wayarsa kawai yake dannawa bai ma san tana wajen ba, juyawa tayi a hankali ta koma kitchen din a sanyaye ta hada masa breakfast din ta fito da shi parlor, jikin kujera ta tsaya a hankali tace "Ga breakfast din nan" Daga kai yayi ya kalleta, gabanta ya dinga faduwa ta sauke idonta daga kallonsa, jin bai ce komai ba yasa ta karasa har gabansa ta duka ta ajiye masa breakfast din, yace "Ke ina naki?" Taki barin su hada ido tace "Yana kitchen" Yace "Dauko" Mikewa tayi ta tafi ta dauko nata ta dawo tana kallonsa, yace "Ajiye ki ci a nan" Bata masa musu ba kanta a kasa ta zauna gefensa da ya nuna mata ta fara tuttura irish din kamar dole tana satan kallonsa ta gefen idonta, a hankali taga ya jawota jikinsa taji gabanta yayi mugun faduwa, calmly yace "I am a monster to you right?" Da sauri ta girgiza masa kai zuciyarta na bugawa, yace "Gashi nan, kin maida ni dodonki" Ita kanta bata san sanda hawaye ya cika idonta ba, yayi kasa da murya yana zame hulan kanta yace "Now tell me what u want from me, tell me what's on ur mind.... amma before then ki sani bazan taɓa rabuwa da ke ba saboda ina son ki Khaleesat, rabuwa dake will be the last thing i will do on earth no matter what, You know i love you genuinely from onset, i loved you wholeheartedly and i gave u the best of everything I could, i loved you even before you become the woman you are today, i love you since when u were just a 15 year old teenager tun baki girma ba, yea i know about my flaws but loving you is all that matters, not in the sense that abubuwan da nake yi are right, i am obsessed with you Baby, may be you can change me in ur own way...." Khaleesat ta rufe idonta tana jin kamar ta fashe da kuka, jin kalamansa take kamar ana soka mata mashi a kirji, Ya dora forehead dinsa a nata murya can kasa yace "Why not give me a chance and forgive my flaws Khaleesat?" Bude idonta tayi hawaye suka hau zarya a idonta, har cikin ranta taji bata son jin maganganun da yake mata, a hankali yace "Forgive me, i know i wronged you in all ways, but don't forget ina sonki, ina kuma sonki ne saboda Allah, they are many beautiful ladies out der buh i chose you Khaleesat" Lokaci daya gaba daya tunaninta ya tafi kan Housemate dinta, kasa daurewa tayi ta fashe da matsanancin kuka, ya daura kanta a saman shoulder dinsa patting her softly, ta dinga kuka kamar an aikota, shi dai bai ce mata komai ba, sai da tayi kukan me isarta sannan ta hakura don kanta tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya, ya daga kanta yana kallonta taki yarda su hada ido, breakfast dinta ya ajiye mata a kusa da ita, ba musu ta fara ci a hankali da tunani iri iri a ranta, muryarsa taji ya daki dodon kunnenta "Yaushe zaki gama period?" Gabanta yayi mugun faduwa, ta ajiye cup din shayin dake hannunta ba tare da ta kallesa ba, a hankali tace "Ai ban dade da farawa ba" Yace "Yau kwana hudu da farawan ki" Da kyar ta dake tace "A'a, uku ne.... first day din ai bana yi sosai..." Yace "Saura kwana nawa ki gama kenan?" Sosai gabanta ke bugawa, ta sunkuyar da kanta cike da karfin hali tace "Kilan nan da kwana uku ko hudu" Jin bai ce komai ba ta daga kai a ɗan tsorace ta kallesa, taga kallonta yake without blinking, sauke idonta tayi tana wasa da karamin cokalin dake cikin mug din shayinta, ya dauke shayin ya mayar gefe, taga ya kai hannu shoulder dinta zai sauke siririn hannun rigar dake jikinta, sosai hankalinta ya tashi amma bata ce masa komai ba gabanta na ci gaba da faduwa, ya sauke rigan gaba daya yana kallon bare chest dinta, hawaye ne ya cika idonta taki yarda su hada ido, can dai tayi karfin hali muryarta na rawa tace "Toh baka sha shayin ka ba zai huce" Yayi kasa da murya yace "Wa ennan zan sha... " Momy ce tsaye parlor tana kallon Meemah dake rusa kukan bakin ciki uwa er yarinya, ga trolley dinta a gefenta, bacin rai ne karara kwance fuskar Momy da idanuwanta suka ƙankance tana huci, mai aikin gidan ce ta shigo parlon rike da bowl din pepper soup din da tayi ma Momy, cikin ladabi ta risina tace "Hajiya ga farfesun nan ya kammala" a fusace Momy ta figi throw pillow ta jefa mata tace "Don ubanki wuce ki ban waje ke da farfesun, baki ga magana nake bane zaki shigo min parlor kai tsaye, yau ga jahilar mata kai" a tsorace mai aikin ta juya da sauri ta bar parlon ta koma kitchen ta kullo kofar, Momy tace "Na kusa daina daukan tsinannun masu aikin nan don sun isheni haka kuma, na kori wancan shegiyar da ta shigo min parlor da yan uwan Alhaji da suka zo daga kauye babu izinina yanxu kuma an kawo min wannan jakar da ko kwana biyu bata yi ba ta fara nuna halayyan dabbobi" Ita dai Meemah kuka kawai take tana fyace hancinta da handkerchief, tsabar kuka idonta har sun suntume, Momy ta kara kankance idanuwanta tana kallon Meemah tace "Shi Abdallahn ne yayi maki haka Meemah?" Meemah ta hadiye wani abu da ya tokare mata wuya don bakin ciki tace "Momy da kin ga tijaran da Abdallah yayi min akan yarinyar nan ko, hmmm, ki bari kawai Momy, Momy kare bazai ci abinda Abdul yayi min ba, bayan zagi da cin mutunci wai ni ya kora a gidansa, kora irin ta walakanci" Momy ta zauna kan kujera with disbelief, duk da AC dake aiki a parlorn sai zufa take yi dama ga ta narkekiya, tana gyara zama tace "Ko dai ya sha wani abu ne Meemah??" Cikin rawan murya Meemah tace "Babu abinda ya sha wallahi Momy don lafiyan Allah ya dauko ni a airport muna ta hira, tare fa da ni duk aka yi tracking yarinyar nan tunda akwai wani tsohon saurayina wanda aikinsa kenan, amma wai yau akanta Abdallah zai min irin wannan tijara haka tun ba aje ko ina ba, duka duka fa kwananta yau hudu da shiga hannunsa, amma ya rufe ido ya zazzageni ya ci min mutunci ya koreni" Momy tayi wani murmushin takaici tana girgiza kafa tace "Kin ga abinda nake ta gudu kika kasa ganewa kenan ai ko? Dama ance duk abinda babba ya hango yaro ko uban me zai hau bazai taɓa hangowa ba wallahi, ba ya kwana da ita ba dole ki ga abinda yafi haka ai, babu yanda banyi in lalata batun auren nan ya hakura ba amma sam Meemah kika ki bani hadin kai ki ka koma bayan Abdallah, har da bin wasu malamanki da basu taka kara sun karya ba duk don yarinyar ta shigo hannunsa, to ai ta shigo kuma kin ga abinda ya biyo baya daga shigowarta, to wallahi zai kai ya kawo wataran Abdallah yace bai san mu ba akan yarinyar nan, ni na haifesa ba wani ya haifar min shi ba sarai nasan abinda zai iya aikatawa" Meemah ta dinga kallon Momy babu ko kiftawa don ita sai yanxu ta kara fahimtar dalilin Abdul nayi mata irin wannan mugun tijara kan yarinyar da yake ta ikirarin zai koya ma lesson idan ta shigo hannunsa, sarai kuwa ya kwana da ita dole ya birkice haka ya haukace kanta, dama buzaye da aka sani da mugayen asiri, Meemah tayi wani murmushin takaici tace "To kuwa yanda nayi ruwa nayi tsaki har sai da yarinyar nan ta shiga hannunsa to haka zan yi har sai ya rabu da ita a kwanan kuwa ba da jimawa ba" Momy ta kwado ma sabuwar me aikinta kira, matar ta taho a guje har sai da tsantsin tiles ya kwasheta sbda ruwan dake kafarta sai ga ta a kasa timmm, A fusace Momy tace "Wallahi tallahi kika kuskura kika illata min tiles sai na cire cikin kudin albashinki, yau naga er iskar mata kawai, kullum na kiraki sai kin azabtar min da tiles saboda kauyanci? Wannan wace irin mata Adama ta kawo min haka da sunan me aiki?" Har kasa mai aikin ta zube tana ba Momy hakuri, cikin tsawa Momy tace "Miko min wayata dallah ki fita ki bamu waje, er kauyen banza" Mai aikin ta kalli wayar dake kan center table dab da inda Momy ke zaune, ta karasa da sauri ta dau wayar ta mika ma Momy, Momy ta warce, mai aikin ta bar parlon, Momy ta mika ma Meemah wayar tace "Dubo min lambar Godiya, glasses dina yana daki" Meemah ta amshi wayar ta dubo number aminiyar Momy sannan tayi dialing ta mika mata, a kashe suka ji wayar, Momy tace "Tayi tafiya me muhimmanci kenan, bari zuwa anjima in sake kiranta" Meemah da kanta ya gama kullewa tace "Tabddi jam, lallai nayi babban kuskuren da ban taɓa yin irinsa ba Momy, sai ma fa kinga kayan dake jikinta da naje gidan, tana kitchen tana soye soye" Momy dai tayi shiru tana girgiza kafa don bakin ciki da takaici, can tace "Dauko min gyale da jaka a daki, ina zaman zamana kin janyo min kashe kudin da banyi budgeting ba Meemah, duk ke kika ja min wannan masifa da kika ki jin maganata wallahi, in hada iri da matsiyata akan wani dalili? A farko dai na hakura na zuba masa ido da yaki jin maganata, amma yanxu kuwa wallahi sae ya rabu da yarinyar nan, babu dalilin da zai sa in hada zuri'a da ita, ga kuma rashin adalcin da aka yi ma Alhaji ga asara ga biyan tara" Tashi Meemah tayi ta tafi dauko ma Momy gyalenta da handbag, all this while dama ita ke ta shiga malamai don Khaleesat ta shiga hannun Abdul Momy ko bin ta kanta bata yi tunda dama ba son auren take ba, Momy na ficewa daga gidan da driver dinta Meemah ta tafi dakinta da wayarta tayi dialing number Malamin da tasa yayi mata aiki. Runtse ido Khaleesat tayi bayan taji duk maganganun da Abdul yayi, yana rungume da ita saman gadonsa kamar zai maidata jikinsa, it's past 8pm na dare, jin taki cewa komai s hankali yace "Khaleesat" Bude idonta tayi wasu hawaye masu zafi suka silalo fuskarta tace "Um" Yace "Say something" Still tayi shiru hawaye na zuba idonta don bata ma san me zata ce masa ba at this point, ya dago kanta yana kallonta yayi kasa da murya yace "Say something pls" Da kyar muryarta na rawa tace "Ban san me zan ce ba" Yace "Say anything" Shesshekan kuka ta fara yi masa tana jin zafi a zuciyarta, me kuma yake son ta ce masa, tunda yace bazai taɓa rabuwa da ita ba ko me zai faru, meaning dole ko tana so ko bata so haka zata ci gaba da rayuwa da shi a matsayin mijinta, so me yake son ta ce, ta dai dake da kyar har sannan muryarta na rawa tace "Kawai alfarma daya zan nema wajenka" Murya can kasa yace "Say it Khaleesat" Tayi karfin halin cewa "I don't want you to hurt anyone because of me...." Kasa ci gaba tayi tana kuka a hankali, ya dinga kallonta don sarai yasan su wa take nufi, Calmly yace "Ohk u mean ur Body Guards that sue me?" Ita dai kuka kawai take, Ya ɗan yi wani murmushi yace "I don't think i will leave dem cause they started everything first, they intruded in what wasn't der business, basu baki labarin harbin da aka yi ma wani dake da alaka da su ba, I mean Salem..." Khaleesat ta daga kai da sauri ta kallesa hawaye na sauka idonta gabanta na faduwa, lkci daya ta tuna sanda Aunty Farida ke sanar mata Ajay yace mata an harbi wani abokinsu a kano, yana wani murmushi yace "To su ma ana nan ana targeting din su, amma in kince in kyalesu i will do that under 2 condition..." Khaleesat dai kallonsa kawai take ta kasa cewa komai duk jikinta yayi sanyi, yace "The first condition is that.... zaki yi magana ta waya da su ki gaya masu ke za ki zauna da mijin ki they should back off, sannan ki gaya masu su janye karan da suka kai kotu..." Bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba, ya dinga kallonta sai kuma yayi murmushi yace "Baza ki yi ba kenan?" Muryarta na rawa tace "Ban ce bazan yi ba" Wayarsa ya dauko ya mika mata yana kallonta, da kyar tace "Bani da number ai" Yace "Amma aunt dinki na da shi ai... Call her and ask her to send you the number" Ta girgiza masa kai tana jin kamar numfashinta zai dauke sbda rikicewan da tayi bayan ya fadi conditions dinsa, cikin kuka tace "Bani da numberta offhand" Yace "Ni ina da shi, i will call her now sai ki gaya mata ta turo maki number daya daga cikinsu, and mind you kada ki kuskura ki ce mata komai, number kawai zaki yi requesting ta turo maki" Ta fashe masa da kuka sosai tace "Why are you doing this plss Ya Abdul" Yace "Ohk, i will revenge and nothing is gonna stop me, i promise you this, shi abokinsu da aka harba ai yayi surviving, i hope they survive too....." Tana kuka sosai tace "No plsss..." Wayar ya dauka yayi dialing number din Aunty Farida yana fara ringing ya mika mata yana kallonta. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* _Assalamu Alaikum yan mata da matan Oga ina me maku albishir da cewa Han-Ash skin beauty ta zo maku da kayan gyaran jiki iri iri wanda zai mayar da fatarki kamar Madara ta yanda duk inda kika shiga sai an kalleki, ki sai mayukan da zesa fatar ki tayi kyau, muna kuma maraba da siyan daya ko sari, i am assuring you that duk wani product dinmu is tested and trusted, ga kuma arha, for more information contact Han Ash via +234 803 810 3096_ HALYSAAH 44 Har Aunty Farida ta ɗaga kiran Khaleesat bata amshi wayar da Abdul ke mika mata ba hawaye na zuba idonta, lkci daya ya hade rai yana mata wani irin kallo, babu shiri ta amshi wayar hannunta na rawa, a sanyaye tace "Aunty" Cikin rikicewa Aunty Farida tace "Khaleesat?" Khaleesat ta sauke idonta tayi shiru, hankali tashe Aunty Farida tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Khaleesat kina ji na? Don Allah kiyi magana, Hello Khaleesat" Khaleesat ta kasa ce mata komai hawaye masu zafi na sauka idonta, kiris ya rage ta fashe mata da matsanancin kuka a wannan lokacin, Abdul ya fixge wayar yayi a hannunta ya katse yana mata wani mugun kallon da ya tsorata ta sosai yace "Are you daring me?" ta fashe masa da kukan da take dannewa tana girgiza masa kai, a fusace yace "Ohk then, since abinda kika zabar masu kenan to ina me tabbatar maki zan aikata hakan nan ba da jimawa ba kuwa, sannan bayan nayi zan sanar maki, don bani da imanin kyale duk wani mahalukin da yace zai shiga hurumina, i don't mind sending that person to his early grave, and mind you.... i will so deal with them yanda in their next life baza su kara shisshigi akan abinda bai shafesu ba, if you think i am bragging watch and see, bani da conscience...." Khaleesat ta girgiza masa kai cikin karfin hali tace "Duk ba sai ka masu komai ba, zan yi abinda kace" Wayar ta amsa a hannunsa ta cire a Flight mode din da ya saka sannan ta sake dialing number Aunty Farida, yana fara ringing Aunty Farida ta daga da sauri tace "Khaleesat, kina ji na Khaleesat?? Hello" Khaleesat ta dake ta hadiye sauran kukanta cike da karfin hali tace "Na'am Aunty" Cikin tashin hankali Aunty Farida tace "Kina ina Khaleesat?" A hankali Khaleesat ta daga kai ta kalli Abdul taga ya wani murtuke fuska yana kallonta kamar bai taɓa fara'a ba a rayuwarsa, ta sunkuyar da kanta wasu sabbin hawayen na zubo mata cikin sanyin murya tace "Aunty Number Ahmad za ki turo min yanxu plss" Aunty Farida da duk ta rude tace "Ahmad kuma Khaleesat? Wanene Ahmad? Kina ina ne yanxu?" Shi dai Abdul wani devilish look kawai yake mata, tayi kasa da murya tace "Aunty Number Junaid zaki turo min" Da sauri Aunty Farida tace "To bari in turo maki yanxun nan" Katse kiran Aunty Farida tayi cikin rawan jiki ta tura ma Khaleesat number Ajay, number na shigowa Abdul ya amshe wayar a hannunta yana kallon number for almost 5 seconds, can yayi wani murmushi ya mayar mata da wayar, cike da isa yace "Kirasa ki gaya masa abinda nayi instructing din ki" It took Khaleesat almost 30 seconds kafin ta iya dialing number Ajay, shi ma saboda irin kallon da Abdul ke mata ne, exactly irin kallon da yake mata in zai gaura mata mari, cikin muryarsa dake tsoratata taji yace "Kika kuskura kika yi magana da wata muryar da ba normal voice dinki ba zaki sha mamaki wallahi, and immediately he picks just go straight to ur point, do not give him a breathing space to say anything to you, go straight and tell him kin hakura zaki zauna da mijinki, kin ji me nace maki?" Ita dai bata ce masa komai ba hawayen takaici na zuba idonta, sai da kiran ya kusa katsewa Ajay ya daga, ta ɗan kalli Abdul da bai fasa mata wani irin kallo ba, da kyar ta daure tace "Hello, good evening....." Mikewa Ajay yayi jin muryarta, bata jira ya gama processing ba ta ci gaba a hankali tace "Dama ina son in ce maka ni na hakura zan zauna da mijina, and i appreciate all what you've done for me kai da Yaya Jawwad, thank you so much" Ajay ya juya ya kalli Jay da shigowar sa dakin kenan, as if counting his words yace "Come again!" Yana fadin haka ya saka wayar a handsfree sannan ya nufi Jawwad yana kallonsa, Khaleesat ta kalli Abdul, sai kuma ta sunkuyar da kanta tace "Cewa nayi ni na hakura yanxu, zan zauna da mijina, and thank you for all what you've done for me...." Wasu sabbin hawaye suka hau zarya a fuskarta tana ji kamar ta fashe da kukan dake cin ta, Abdul ya fixge wayar a hannunta ya katse sannan ya kashe wayar gaba daya, Ajay ya kalli Jay that looks speechless and shock at the same time, lkci daya ya jefar da wayarsa saman gado, cikin nutsuwa yace "Nayi da na sanin bata lokacina akan yarinyar nan, i regret wasting my very precious time...." Jay ya ma rasa me zai ce, walking slowly ya karasa gaban window din dakin yana kallon Ajay that was boiling from inside, a hankali yace "Look Ajay, i think those words are not coming from her heart, sakata yayi ta fadi hakan pls mu yi mata uzuri, she is forced to say all what she said, ba mu san situation din da take ciki ba let consider that plss" Ajay ya masa wani kallo yace "Billah na cire hannuna a lamarinta kaji na rantse Jay, i have nothing to do with her case again, after all i was just doing it just for the sake of humanity not because of her, ko kasheta yake ya kamata ta gaya mana haka? Mu zata dauka for granted? Beside she spoke confidently meaning she is okay with what he asked her to say, i am leaving this state first thing tomorrow morning, so unfortunate i waste my time on the brat, don taga mun yi stooping kan mu so low shi yasa ta dauke mu for granted" Yana kai wa nan ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, Jay ya lumshe ido ya bude don bai san me zai sake ce masa ba da zai sa ya sauraresa, kuma tunda har ya rantse magana ta kare, ya zare hannunsa kenan babu abinda zai sa ya sake involving kansa, zaunawa yayi gefen gado ya dafe kansa da yaji ya masa nauyi, at the same time letting out a sigh, kalmomin Khaleesat ne suka dinga dawo masa kai, he felt really disappointed in her too, but can kasan zuciyarsa tausayinta ne ya mamayesa ya kuma yi mata uxuri, ya rasa menene yasa shi shiga yanayin da ya shiga a wnn lkcin, da kyar dai daga karshe ya mike ya fita daga dakin yana tafiya a hankali. Daren ranan nan Khaleesat bata yi baccin awa biyu ba cikakke, da bacci barawo ya saceta zata farka a firgice, bata taɓa jin abu ya tsaya mata a rai irin abinda Abdul ya sa tayi ma su Housemate dinta ya tsaya mata ba, gashi ko digon hawaye yaki fita idonta, her heart is just heavy, but did she have a choice? In bata yi hakan ba yayi ma su Housemate dinta wani mugun abu ai bazata taɓa yafe ma kanta ba, tunda har yake ikirarin ba shi da imani babu abinda bazai iya aikatawa ba, tasan kuma sarai zai iya aikatawa din, tunanin sabuwar rayuwar da take kokarin fadawa take, is she going to survive this at all? Is this not going to be her end? A ranta taji kilan lokacin mutuwarta ne ke tinkarota, sai a sannan taji hawaye masu zafi for the first time a idonta, ta kai hannu a hankali tana sharewa ta juya tana kallon Abdul dake baccinsa hankali kwance, dai dai nan alarm din wayarsa ya kada, ta juya da sauri tayi backing dinsa tana goge hawayen da ya fara zubo mata sosai, after some seconds taji alamar ya tashi yana karanto addu'an tashi bacci, ita dai hawaye kawai take, sai da taji yayi sallah ya fita daga dakin sannan ta mike zaune tana kuka a hankali. Nenne ta bude hannu tana kallon su Aunty Farida cikin nutsuwa tace "To kun ga ai baza mu shiga hurumin Allah ba, ko akwai me tsaurin idon da zai shiga a cikin ku? Allah Ubangiji ne kadai yasan daliliin da ya maidata hannun mijinta cikin ruwan sanyi babu tashin hankali, to don me za mu shiga hurumin da ba namu ba? A'a gaskiya banda ni tunda ni dai nasan wanene Allah, kuma shi kadai yasan hikimarsa ta yin hakan, da yasan Khaleesah zata cutu hannun Awdul da bazai fara basa sa'ar sungumeta ba don bamu fi sa sani ba, ko ba komai ɗa na zai samu kwanciyar hankali ya ci gaba da sabgogin rayuwarsa kamar ko wani ɗan adam, mu mun yarda da kaddara mummuna ko kyakkyawa tunda mu musulmai ne, kuma duk abinda Allah yayi mu din banza za mu ce don me, domin haka nake cewa Allah ya bata zaman lafiya da mijinta, ɗan halayyarsa da yake yi mara kyau Allah ya gyara sa ya dena, ai babu wanda bai da taɓon wani mugun abu a rayuwar nan, in sun dawo kano mu kuma sai mu je ganin daki mu sa albarka, duk sanda ya bar ta ta zo ta gaida mu a Mariri sai ta zo bakinta alekum, shi kuma Ali Allah ya sa karshen wahalarsa kenan a duniya" Wani irin kallo Aunty Farida ke ma Nenne zuciyarta na tafarfasa, Umma dai kanta na sunkuye bata ce komai ba amma ita kadai tasan abinda take ji a zuciyarta, Mama Zubaida tace "Amma dai Nenne ai ya kamata a bibiyi halin da take ciki, an taɓa tarewa haka kawai a zo a sungumi yarinya a mota da asuba ba a san ko shi din ne ba ko ba shi ba amma duk a rasa me bibiyar hakan, wannan ai abun dubawa ne, tun da mu dai har yanzu bai ce mana shi ya dauketa ba" Nenne tace "To er bakin ciki, shi din ne ya sungumeta ba kowa ba aniyarki ta bi ki, kuma ai halaliyarsa ya sunguma ba wata ba, duk wanda ya sake cewa zai bada shawara a wannan lamari idan ban sa Ali ya sallamesa ba shegiya uwata da ubana suka haifeni, kwata kwata bakwa neman ma ɗa na sauki a rayuwar nan, burin ku kawai tashin hankali ya kashe Ali ku huta ni kuma in shiga uku, ita uwar da ta tsugunna ta haifi yarinyar bata da bakin magana sai ke me baki kamar ta dorinar ruwa?" Mikewa Mama Zubaida tayi ta shige dakinta, Mama Shatu ta kyabe baki tace "To Allah ya kyauta, in ya dawo mana da gawar ta ai sai mu zauna mu yi zaman makoki ba shikenan ba" Nenne tace "Sai dai ki ga gawar er ki Labeebah amma ba Khaleesah ba, kuma bakin cikin da ku ka kasa boyewa ne zai kashe ku ke da Zubaida" Mikewa Umma tayi hawaye cike idonta ta shiga dakinta, Nenne ta kyabe baki ta mike tana kallon Aunty Farida tace "In Ali ya dawo ki ce masa nace ya zo ya amshi tuwo da miyar taushe zan ajiye masa, wallahi wata guda zan yi ina masa girki ya marmaro" Daga haka ta fice daga gidan, Aunty Farida tayi tagumi hawaye cike idonta. Meemah ta shigo parlon Momy ta zauna tana ɗan murmushi, ta jira har Momy ta gama wayar da take yi da aminiyarta godiya sannan tace "Momy na samesa a waya" Da sauri Momy tace "Ya daga kuma?" Meemah tace "Eh ya daga bayan yaga text din da na tura masa kenan" Momy na gyara zama tace "Toh Alhamdulillahi nagode ma Allah, sai yace maki me?" Meemah tace "Kema kinsan dole zai taho ai, amma tsorona daya kada ya kira Daddy kuma ya daga waya yace masa ba haka ba" Momy tayi wani murmushi tace "Bazai daga ba, tunda na riga na gaya masa abinda ke faruwa ai" Meemah ta sauke ajiyar zuciya tace "Alhamdulillah, in ya samu flight yau za mu iya ganinsu a gidan nan" Momy tace "Me zai hana ya samu jirgi, ai da sauran lokaci dole zai samu" Mai aikin Momy ce tayi sallama tana makale jikin kofar parlon duk da a bude yake amma bata shiga ba, hannunta rike da tray me dauke da plate din gasasshen kaza da lemon kwali biyu, Meemah ce ta amsa sallaman tana mata wani kallo tace "Tun da kika ga kofa a bude ba sai ki shigo ba, kin wani raɓe jikin kofa kamar munafuka, don Allah ki dena wannan kauyancin yana damun mu a gidan nan" Momy ta hade rai tana kallonta har ta karaso ta ajiye plate din, cikin ladabi tace "Ga kazar ta kammala Hajiya" Momy tace "Kalan Hijabin nan naki na daga min hankali a gidan nan, kar ki sake saka min shi, in yar wa zaki yi to ki yar bana son shi kwata kwata yayi kalar talauci" Mai aikin ta dukar da kai tace "Toh Hajiya in sha Allah bazan sake sa shi ba, kiyi hakuri" Fita tayi daga parlon da sauri, Momy ta dau plate din tulin kazar da aka ajiye mata ta fara ci tana cewa "Ai dama tunda aka ce min zai taho da ita hankali na ya kwanta, don dama taho da ita shi ne me wuyan...." Meemah tayi murmushi ita ma ta dau yankan kaza daya tana ci tace "I trust you Momy" Khaleesat ta saka Hijab dinta har kasa tana harhada wasu daga kananun kayan dake cikin closet din dakin kamar yanda Abdul ya umarceta tayi, absentmindedly take aikin don tayi nisa a tunanin da take, bude kofar dakin yayi ya shigo, ita dai bata juya ba tana ci gaba da abinda ya sakata, ya karasa har bayanta ya tsaya, taki juyowa gabanta na faduwa, juyo da ita yayi yana kallonta ta sunkuyar da kanta, yace "Me ya sa baki son ki saki ranki har yanxu? Always looking worried" A hankali ta daga kanta ta kallesa amma bata ce komai ba, yace "Kin gama hada kayan ne?" Girgiza masa kai tayi, yace "To gama" ta juya ta ci gaba da abinda take, shi dai yana tsaye yana kallonta, pad ta dauko a karshe zata saka cikin karamin trolley din yace "What are you using that for? Ba yau zaki gama ba?" Taki kallonsa zuciyarta na bugawa tace "Amma ban gama ba ai" Bata jira me zai ce ba ta saka a akwatin sannan ta kulle ta mike tsaye, kamo hannunta biyu yayi yana kallon cikin idonta, speaking slowly yace "Promise me you won't act silly har mu isa kano Khaleesat" Ta rasa dalilin da hawaye ya cika idonta, shi dai kallonta kawai yake, after some seconds yace "If you try anything silly, zaki yi matukar mamakin abinda zan yi, i promise you" Da kyar tace "Toh, amma plss ina son inyi waya da Safiyyah, i am missing her" Yace "Baza ki yi waya da Safiyyah ba, amma idan muka isa kano zan fara kai ki gidanku ki gaishesu sannan mu tafi gidanmu" Ita dai bata ce komai ba hawaye na zuba idonta, a haka suka bar gidan zuwa airport tunda yana da hoton National ID dinta a wayarsa. Da yamma suka sauka garin kano, driver din gidansu har ya iso airport din yana jiransa, Drivern ya bude ma Khaleesat back seat bayan ya gaisheta, kanta a kasa ta shiga motar, kana ganinta kasan tana cikin damuwa sosai gashi ta kara zagbewa gaba daya, Abdul ya shiga ta daya side din, sannan drivern ya shiga motar ya tada suka bar airport din, sai bayan da suka fita daga cikin airport Abdul ya gaya ma drivern inda zai fara kai su, sun yi nisa sosai da tafiyar Abdul ya juya ya kalli Khaleesat da tayi nisa cikin tunanin da take, hannunta ya saka cikin nasa wanda hakan ya dawo da ita reality, ta ɗan kallesa, yayi kasa da murya yace "Are you hungry?" Girgiza masa kai tayi, ya jawota zuwa jikinsa yana kallonta, ita dai bata ce masa komai ba zuciyarta na bugawa, a haka suka isa Mariri wajen karfe biyar da rabi na yamma, Drivern na parking daga opposite din gidansu Khaleesat Abdul ya bude motar ya sauka, jiki a sanyaye Khaleesat ta sauka daga motar, ta ma rasa ko farin ciki zata yi ko akasin haka ganinta a kofar gidansu, Abdul ya bi ta da kallo har ta shiga cikin gidan sai a sannan hawaye suka cicciko mata ido, Noor ce ta fara hangota tana hura gawayi ta taso da gudu ta rungumeta, sai a sannan sauran en gidan duk suka juya suna kallon Khaleesat, Umma dake zaune bakin kofar dakinta ita ma ta dinga kallonta, Mama Zubaida da Mama Shatu suka taɓe baki suna kallon juna, Aunty Farida dake gyara dakin Umma ta fito da sauri jin sunan wanda Noor ta kira, Khaleesat ta tafi ta rungumeta ta fashe da matsanancin kuka, Farin ciki wajen Aunty Farida ba a cewa komai don duk tunanin su Ajay ne suka dawo da ita gida, sallaman Abdul yasa duk suka juya suna kallon hanyar shigowa gidan da mamaki, nan da nan fara'ar Aunty Farida ya bace, su Mama Shatu ne kawai suka amsa masa sallaman, ya karaso cikin compound din, Aunty Farida ta saki Khaleesat ta tafi ta zauna kusa da Umma fuskarta babu yabo babu fallasa, Mama Zubaida ta mike da sauri ta shimfida masa tabarma ita da Mama Shatu na masa sannu da zuwa, ya zauna kan tabarman yana kallon Umma ya gaisheta, Umma ta amsa tace "Sannu da zuwa" Aunty Farida ta mike ta shige dakin Umma, Abdul ya gaida su Mama Zubaida dake ta washe baki, duk suka amsa da fara'a, Ita dai Khaleesat na durkushe kusa da Ummanta kanta a kasa, Abdul ya kalli Umma yace "Baba baya nan ne" Umma tayi karfin halin cewa "Eh bai dawo ba" Ko rufe baki bata yi ba sai ga Malam Ali ya shigo gidan da rabin buhun dankalin Hausa a hannunsa, ajiyewa yayi ganin Abdul da Khaleesat, yace "A'aa, ikon Allah, baki mu ka yi yau a gidan" Abdul ya tashi ya tafi har inda Malam Ali ke tsaye ya gaishesa, Malam Ali ya amsa yana kame kame, ya tafi da sauri ya dauko tabarma ya kara shimfida ma Abdul yace "Yi zaman ka a nan, bari in zubo mana ruwa a buta lokacin Magariba yayi" Da sauri ya tafi ya dauko butoci biyu ya tafi zai debo ruwan, Umma ta mike ta shige dakinta, Khaleesat ta bi bayanta, Nenne ce ta shigo gidan da sallama tace "Allah me hikima, sannunku da zuwa Awdul" Abdul ya gaisheta, ta jawo kujera ta zauna tana facing dinsa tace "Lafiya lau wallahi, ya iyayen naka, ina kokarin daura sanwa kenan sai ga wani almajiri da gudu ya zo ya sanar min ai kun zo, kasan ɗan albarka ne almajirin nan duk wani abu da ke faruwa a gidan Ali kamar kiftawan ido yake rugowa ya sanar min, ni kuma in ina da er dabino kwara uku in basa la'ada, nayi farin cikin ganin ka wallahi, ina matar taka, in ji tare ku ke?" Yace "Tare mu ke" Sai ga Malam Ali da ruwa a butoci yace "Ai ina jin tana dakin uwarta" Nenne tace "Kai kuma lafiya? ina zaka da butocin ruwa ko karfe shidda bai yi ba?" Malam Ali yace "Au? To to bari a ajiye, na zata magariba ta yi" Da sauri ya koma ya ajiye butocin ya dawo, Nenne tayi kasa da murya tana kallon Abdul tace "To Awdallah, ka dubi girman Allah ka rike amanar da muka baka, yanxu kai ne uwarta kai ne ubanta, duk ta kuskure maka ka kawota wajena ni zan san yanda zan yi da ita, kuma albarkacin auren da ya shiga tsakaninka da jikata ka kara ba Mahaifinka hakuri ya yafe ma Malam Ali komai ya wuce a wajensa don girman Allah, don yanxu kam duk mun zama daya tunda ga aure har ya shiga tsakani, Allah Ubangijin ya baku zaman lafiya ya kauda duk wata fitina ya kawo zuri'a dayyaba" Abdul yace "In sha Allah Kaka" Nenne na murmushi tace "To madallah, gashi ko tuwon dare ban yi ba balle in zubo maka" Yace "Ba komai, can gidanmu za mu wuce yanxu yamma tayi" Nenne tace "Gaskiya kam, bari in fito maka da ita ku tafi, go slown hanyar nan bata da kyau" Tashi Nenne tayi ta nufi dakin Umma, kuka kawai Khaleesat take Umma tayi tagumi tana kallonta ta ma rasa abun cewa amma daurewa kawai take ita ma hawayen bai zubo mata ba, don bakin ciki Aunty Farida na jingine jikin bangon dakin ita ma ta kasa cewa komai, a haka Nenne ta shigo dakin ta same su, taɓe baki tayi tace "Ta so ki fita mijinki na waje na jiranki" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba tana kuka kamar ranta zai fita, Nenne tayi kasa da murya tace "Wato a yanda kanwar uwarki ke zube ba mashinshini shekara da shekaru haka kema kike son ki zauna mana tunda kyau kawai gare ku amma babu farin jini, banda samun waje ki samu miji zankadede kamar Awdul amma son zuci irin taki da na uwarki da kanwarta bazai sa ku yi farin ciki da hakan ba, in a baya Awdul ɗan iska ne dama Allah ya taɓa halittar da bai shiryar ba in yayi niyya? Daga yanda Awdul ke magana a kintse na gane ya shiryu wallahi, to ko kawota da yayi ta gaishemu kadai ya isa mu shaida shiriyarsa, wallahi ku dinga jin tsoron Allahn da ya halicce ku, duk wanda burinsa ya raba aure to tsinuwar Allah ne zai tabbata a garesa, kuma in sha Allahu Khaleesat tayi aure kenan mutuwa kadai ne zai rabata da mijinta tunda duk mun san yana sonta, tashi ki fita gun mijinki ku tafi munafuka kawai, duk da can baki san baki son shi ba sai da ya aika ki kasar turawa idonki ya bude a can" Cikin kuka Khaleesat tace "Ni wallahi bana son sa, bana son sa, bazan iya zama da shi ba" Nenne tace "Aikin banza, to uban me ya rage kuma bayan ya kwana da ke? Ai duk rashin son da kike masa dole ki zauna da shi tunda ya kwana dake yau kusan satin ki daya a gidansa ba kuma ajiye ki zai yi yana kallo kamar hoto ba tunda shi ba ɗan iska bane, kuma gidan Ali ba Obalande bane da za a tara masa fararen zawara har biyu a gida, Farida ma kadai ta ishemu, tashi ki fita ki bani waje ko in tafi in kira maki Ali yanxun nan ya fitar min da ke, tun da uwata ta haifeni ban taɓa ganin er da bata son kwanciyar hankalin ubanta ba sai ke" Umma ta share hawayen dake zuba idonta tana kallon Khaleesat tace "Ta shi ki je Khaleesah, Allah ya maki albarka, Allah kuma ya baku zaman lafiya" Mikewa Khaleesat tayi tana kuka sosai ta fita daga dakin Ummanta, Nenne tace "Atoh dai, iya addu'ar da za mu yi mata kenan a matsayin mu na rikakkun musulmai, tun da muka ga haka to Allah ne kadai ya san hikimarsa nayin hakan, kuma dama an gaya min aurenta da Awdul aure ne me kyan gaske in har zata kwantar da hankalinta, gashi mun shaida yana son ta, kuma ta dalilinta arzikin ubanta duk zai dawo har ma ya fi na da, wallahi haka aka ce min, kawai dai babba ba a son yayi ta surutu ne shi sa nake jan bakina nayi shiru" Har suka bar gidan da Abdul hawaye ne kawai ke zuba idon Khaleesat, dubu talatin ya ba kishiyoyin ummanta ko wacce 15k, ya ba Islam 50k, Nenne ya bata 20k, Malam Ali kuwa bai amsa kudinsa ba sai ajiye masa Abdul yayi kan tabarman dake bakin kofar dakinsa, babban tashin hankalin Khaleesat yanxu period dinta da ya dauke, don kafin su taho kano a dari dari tayi sallahn Azahar kar ya shigo ya ganta, tasan yau dai ƙaryar ta ya kare kawai, a haka suka iso gidansu Abdul bayan sallan magrib, Driver na shiga babban compound din da mota Khaleesat taji gabanta ya tsananta faduwa, bayan yayi parking a space din parking Abdul ya sauko daga motar yana kallonta, da kyar ta iya saukowa daga motar zuciyarta na bugawa sosai wanda ita kanta bata san dalilin hakan ba all of a sudden, ya fara tafiya tana bin sa har suka isa entrance din shiga parlorn gidan.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* _Assalamu Alaikum yan mata da matan Oga ina me maku albishir da cewa Han-Ash skin beauty ta zo maku da kayan gyaran jiki iri iri wanda zai mayar da fatarki kamar Madara ta yanda duk inda kika shiga sai an kalleki, ki sai mayukan da zesa fatar ki tayi kyau, muna kuma maraba da siyan daya ko sari, i am assuring you that duk wani product dinmu is tested and trusted, ga kuma arha, for more information contact Han Ash via +234 803 810 3096_ 45 Khaleesat na tafiya a hankali ta shiga parlon tana karanto addu'o'i a ranta don irin faduwar da gabanta yake yi isn't normal, ga tsikar jikinta sai tashi yake, she was so uncomfortable and restless at the same time, Abdul ya kulle kofar parlon ya kalli mahaifiyarsa dake zaune cikin parlor ita da kanwarta Aunty karima da Meemah, ko wannensu da bowl cike da farfesun kayan ciki a hannu, Khaleesat ta sunkuyar da kanta ganin gaba dayansu zubo mata ido suka yi suna kallonta fuskarsu babu yabo babu fallasa, amma kana kallon kwayar idanuwansa babu abinda zaka gani sai tsantsan kiyayyarta, da kyar ta karasa tsakar parlon kamar zata harde ta fadi, ta duka kasa cikin sanyin murya ta gaishesu gaba daya, instead Momy sai ta dauke kai tana kallon Abdul tace "Flight din sai na dare ka samu kenan Babana, bayan tun sassafe Meemah tayi maka text" Aunty Karima ta hau kwalo ma mai aiki kira ta zo ta karo mata farfesu, Abdul bai ce ma Momy komai ba ganin babu wanda ya amsa gaisuwar Khaleesat cikinsu ya kalleta yace "Ta shi mu je" Khaleesat ta ɗaga kai ta kallesa amma bata tashi ba ga zuciyarta sai bugawa yake, Momy tace "Ta tashi ku je ina? Wacece ita din tukunna?" A takaice yace "Matata ce" Aunty Karima ta gyara zama da mamaki tace "Ikon Allah, ita ce er gidan barawon da yayi ma Alhaji sata har na miliyan dari kenan?" Meemah tace "Kwarai kuwa gashi kin gane ma idonki, ita ce dai er matsiyatan da Abdul ya makale ma saboda rashin sanin darajan mahaifinsa bai dubi rashin kirkin da aka yi ma Daddy a kotu akan hakkinsa ba ya koma ma yarinyar, dama yawon ta zube uwarta ta shigo yi Nigeria shi ne ta hadu da ubanta bayan sun yi watsewarsu ya aureta...." Katse ta Abdul yayi a fusace yace "Idan kika ci gaba da voicing gibberish zaki sha mamakin abinda zan maki a nan Amina, bridle ur tongue" Aunty Karima ta bude baki da mamaki tace "Amina kai tsaye? Ko ka fara shaye shaye ne Abdul? Akan shegiyar yarinyar nan kake nema kayi ma yayarka rashin kunya?" Abdul ya kalleta yace "Kar ki sake sako min baki tunda ba dake nake ba, stay out of anything that concerns me, Momy ce dolen ki ba ni ba" Momy tayi wani murmushi tace "Rabu da su Babana, take her inside ta huta, sannunku da zuwa" Tana fadin haka ta tashi ta taho kusa da Khaleesat ta dafa ta tace "Welcome my daughter, ku je sama kin ji" Da kyar Khaleesat ta mike tsaye duk jikinta a sanyaye ta bi bayan Abdul, Momy ta koma ta zauna ta bi ta da kallon gefen ido, har ta ga sun haura sama sannan ta kalli su Meemah tayi kasa da murya tace "Sam baku da hankali baku da tunani, haka muka yi da ku daxu?" Meemah da ke huci tace "Ni matsala ta kinsan ban iya pretending bane Momy, wallahi ban iya ba ko nace zan yi" A fusace Momy tace "To in kin san ruguza min plan za ki yi ki ja min asara to tun wuri ki tattara ki tafi gidan Suwaiba bana son hauka, duk ba ke kika ja mana wannan bala'i ba? da sa hannun ki fa abubuwan nan suka faru, ai wallahi sati daya yayi ma yarinyar nan yawa a gidan nan in dai ni na haifi Abdallah, don haka duk wanda bazai iya abinda nace yayi ba to ya bar gidan nan kawai kar ya ja min asara" Aunty Karima tace "Toh Momy kar kuma fa yace zai koma can gidansa da ita, kin san babu me sa shi babu me hanasa idan yayi niyyar yin abu" Momy tace "Ku dai ku zuba min ido kawai ku ga ikon Allah, ance maku ni mahaukaciya ce warce bata san abinda take yi ba irin ku? Ai ni ba yarinya bace nasan me nake yi" Mikewa Momy tayi tana tafiya gansan gansan ta nufi staircase, Meemah ta kyabe baki tace "Wallahi ji naki zuciyata bazata iya wani pretending ba akan shegiyar yarinyar nan me kamar sadaka yalla, ban taɓa jin tsanar mutum a duniya irin yanda na tsaneta ba, Abdul bai taɓa min kalan tijaran da yayi min akan ta ba, kuma fa a gabanta yayi min haka tana ji tana kallo" Aunty Karima ta sauke ajiyar zuciya tace "Nima ba gashi yayi min ba Meemah, fatan mu kawai komai ya zo karshe cikin gaggawa, mu yi yanda Momy tace kawai" Khaleesat ta dinga bin dakin da Abdul ya kawota da kallo wanda babu tantama dakinsa ne, a hankali ta zauna saman kujeran dakin tana kallonsa yana cire agogon wrist dinsa alamar zai shiga bandaki yayi alwala, abinda aka yi mata a parlor ne kawai ke yawo a kanta, tayi nisa tunanin da take yi sai gashi ya fito daga bandakin yana kallonta yace "Shiga kiyi alwala" Sosai gabanta ya fadi ta daga kai tana kallonsa, ta dake tace "Ai ban gama ba" Wani tsawan da ya gigitata ya daka mata, yana mata wani mugun kallo yace "Kar ki raina min hankali, is it going to take u forever to finish ur period? Karya kike yi kin gama" Tsabar yanda ta tsorata jikinta har bari yake ta ma rasa me zata ce masa, yace "Idan na dawo masallaci i will check for my self" Daga haka ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, hawaye ya fara zarya a idonta, wannan moment din take ta tsoro gashi ya zo kuma babu yanda ta iya, shesshekan kuka ta fara yi cikin tashin hankali, bayan ya fita da kamar minti biyu taji an bude kofar dakin, ta juya da sauri gabanta na faduwa, Momy ce ta shigo dakin ta sakar mata murmushi ta nufota tace "Ya sunanki daughter? Mu sai yace mana Khaleesat, ni dai nace Khaleesat ai ba sunan yanka bane" Khaleesat ta sauke idonta zuciyarta na bugawa a hankali tace "Sunana Hauwa" Momy tace "Maa sha Allah, ashe uwata ce, welcome to the family my dear, taso mu je kiyi sallah" Khaleesat felt a bit relieve da gesture din Momy toward her, ta mike tsaye Momy ta kama hannunta suka fita daga dakin, can bangarenta ta tafi da ita har cikin Bedroom dinta sannan ta nuna mata bandakin dake dakinta tace "Ki shiga ciki kiyi alwala, amma kafin nan let's do a mother and daughter talk first my dear" Khaleesat ta daga kai tana kallon Momy, Momy ta nuna mata kan kujera tana mata murmushi tace "Get sitted Mamana" Khaleesat ta zauna kan 2 seater dake dakin Momy ta zauna gefenta tana facing dinta tace "Kar ki boye min komai mamata, ki daukeni tamkar mahaifiyarki, ki gaya min gaskiya wani abu ya shiga tsakaninku da Abdul ne tun bayan da ya dauke ki?" Sosai Khaleesat taji tambayar yayi mata nauyi a kai, hakan yasa ta kasa kallon Momy ta sunkuyar da kanta kawai, Momy ta kwantar da murya tace "Akwai dalilin da ya sa nake tambayarki haka ne Mamana, kar ki ji kunya ki boye min komai, open up to me" Girgiza mata kai kawai Khaleesat tayi ba tare da ta bari sun hada ido ba, Momy ta kamo hannunta tace "Kar fa ki ji kunyata ki boye min komai mamana, gaskiya zaki gaya min" a hankali Khaleesat tace "Gaskiya na gaya maki Momy" Momy ta dinga kallonta kamar dai bata yarda ba, can tace "To saboda me? Anya kuwa gaskiya kike gaya min Mamana?" Khaleesat bata dago kanta ba tace "Period nake yi ne" Momy tace "Toh kin gama yanxu?" A hankali Khaleesat tace "Daxu na gama" Momy ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace "To naji dadin jin hakan mamana, don nasan irin daukan da Abdul ya tafi ya maki bayan dawowar ki daga makaranta, hakan bai ba iyayenki daman yi maki duk abubuwan da ya kamata su maki ba a matsayinki na budurwa kafin ki tare gidan mijinki, basu samu daman yi maki shirin xuwa gidan miji ba, amma tunda ya kawo ki nan in sha Allah zan maki duk abinda ya kamata diyata...." Ita dai Khaleesat tayi shiru har sannan bata dago kanta ba, Momy ta mike tace "Ta shi mu je bandaki ki ga...." Khaleesat ta mike tsaye ta bi bayan Momy har zuwa bandakinta, Momy ta nuna mata wani babban flask tace "Kin ga wannan flask din? To zaki dinga tsiyayan ruwan ciki ki sirka da ruwan zafi a pampo ki dinga tsarki da shi" Momy ta dauko wasu ɓakakken sabulai dake nannade a leda ta mika mata tace "Sabulan nan su ma tsarki zaki dinga yi da ko wannensu, in kin yi sai ki ajiyesa inda kika ga na dauko yanzu don naki ne" Momy ta nuna mata wani roba dake rufe a bandakin shi ma tace "Wannan ma diba zaki yi kiyi tsarki da shi, kin ji?" A hankali Khaleesat tace "Toh Momy" Momy ta dauko wani kwalba dake boye a cikin bandakin, Khaleesat dai bin ta kawai take da kallo ta bude flask din ta tuttule abinda ke cikin kwalban, sannan ta mike tace "Yauwa mamana, duk ki tabbatar kinyi amfani da su yanda nace, sai kiyi alwala ki fito" A hankali Khaleesat tace "Toh Momy" Daga haka Momy ta fito daga bandakinta ta shimfida ma Khaleesat darduma, sannan ta zaune kan kujera ta jirata har ta fito daga bandakin, Momy ta mike ta nuna mata darduman tace "In kin idar da sallan kar ki fito, kiyi zamanki zan kawo maki abinci" Khaleesat tace "To Momy" Daga haka Momy ta fita daga dakin ta kulle da key ta tafi da makullin tana ɗan murmushi, a corridor ta hadu da Abdul ya taho daga dakinsa bayan ya shiga bai ga Khaleesat a ciki ba, Momy tace "Har ka dawo masallacin Babana?" Yace "Na dawo, tana ina ne Momy?" Momy ta ja kunnensa tace "Yanxu abinda kayi ma yayarka ya kamata Babana? Kasan ta fa wani lokacin ba hankali ya ishi yayar taka ba, da sai kayi hakuri ka kyaleta da halinta kawai" Ya hade rai yace "Dukanta fa take kokarin yi Momy? A ina ta san ta ko kuma me tayi mata da zata zageta kuma ta nemi ta doketa??" Momy ta kama hannunsa suka shiga dakin baƙin dake kusa da su tana kallonsa tace "Ai na mata fada sosai Babana, yanxu ma haushin abinda kayi mata ne yasa tayi abinda tayi a parlor amma kayi hakuri kaji Babana" Yace "Naji, ina Khaleesat din take?" Momy tace "Bazan fa baka matar ka ba sai zuwa jibi in ma zaka cire ido a kanta ka cire, tun da baka bari iyayenta sun gyarata yanda ya kamata ba to ni zan gyarata" With confusion Abdul yace "Gyarata kamar yaya Momy?" Momy tace "Ka taɓa ganin inda aka dau mace budurwa aka kai ta gidan miji haka nan? To fin karfin iyayenta da kayi kuma suna shakkar ka shi yasa suka baka ita haka babu yanda suka iya maka, amma a al'adar mu ta Hausa babu inda ake yin haka, ni kuma kaga bazan baka ita ba sai nayi mata duk abinda ya kamata na gyarata, in kuma rashin kunya zaka yi min to yi Babana, Khaleesah dai bazan baka ita ba sai zuwa nan da jibi in sha Allah, zan mata duk abinda ya kamata a matsayin ta na 'ya ta" Abdul ya kasa cewa komai yana kallon Momynsa, Momy tace "Mu je ka ci abinci" Bata jira cewarsa ba ta fita daga dakin, bin bayanta yayi ya fita amma duk tsaurin idonsa sai yaji nauyin ce ma uwar tasa komai, haka nan Momy ta dauko masa abincinsa da ta hada masa da kanta ta jera masa su a dinning sannan ta koma kitchen zata hada abincin Khaleesat, Abdul ya zauna kujeran dining amma ya kasa cin abincin, shi fa bai yi niyyar ma kwana gidan da Khaleesat ba don irin burin da ya ci a kanta yau ai sai Allah, nan da nan yaji ransa ya baci, ya mike ya shiga kitchen ya samu Momy ta sa mai aikinta ta jera ma Khaleesat abinci a tray, don irin abin da ta hada mata har ya fi na Abdul, Momy na kallon mai aikin tace "Tafi ki kai mata bangarena ki jirani ina zuwa" Mai aikin ta fita daga kitchen din da tray din, Abdul na kallon Momy a fusace yace "Toh wai menene yasa Meemah zata ce min Daddy ba shi da lafiya critically bayan ma ashe baya kasar?" Momy tace "To ai ganin likita yaje a Amurka, ko bai gaya maka bane? Karfe hudu na yamma jirginsu ya tashi, shi yasa kaji nake cewa baka taho da wuri ba don duk zatona zaka tarar da shi" Abdul yayi shiru yana kallon Momy, Momy tace "Ni dai bari in je wajen diyata, kar ka wani huce kan Meemah don ba ita ta hanaka matarka ba" Daga haka Momy ta bar sa tsaye a kitchen din, tsaye ta tarar da Mai aikinta a bangarenta tana jiranta don kofar a kulle yake, Momy ta bude mata suka shiga ciki, Mai aikin ta ajiye abincin gaban Khaleesat, Momy na kallon mai aikin wanda ranan ne ranan farkon da ta shigo mata daki tace "Toh fita ki ban waje...." Mai aikin ta fita da sauri ta kullo kofar, Momy tayi murmushi tana kallon Khaleesat tace "Ga abinci nan Mamata" Momy ta tafi ta dauko handbag dinta ciro wani kulli ta dawo kusa da Khaleesat ta bude kullin ta barbada mata abinda ke ciki a farfesun kayan cikin dake cike a bowl tace "Maza ki shanye har romon kin ji" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata, Momy ta tafi ta zauna kan kujera tana murmushi ta dau remote ta kunna TV din dakin, a hankali Khaleesat ke shan farfesun tunani iri iri na yawo a kanta, to yanxu kenan hakuri kawai zata yi da auren Abdul, since gaba daya family dinta sun nuna sun yi accepting auren, sannan ga Mum dinsa ma ta ga tana sonta, kilan zaman aure da Abdul a kaddarar rayuwarta yake, she should just accept it with good faith, most important of all gashi mahaifiyarsa na sonta, his sister won't be an issue tunda mamansa na sonta, kawai ta saka ma ranta salama ta amshi auren tunda haka Allah ya kaddara mata, Housemate dinta ne ya fado mata, lkci daya taji hawaye ya cika idonta, da sauri ta sunkuyar da kai kar Momy ta gani cikin dubura ta dinga goge hawayen tana jin wasu masu zafi na sakkowa, sai da Momy ta tabbatar ta ci abincin sosai, sannan ta umarceta da taje tayi wanka ta tabbatar ta sake tsarki da duk abubuwan da ta nuna mata a bandaki, kafin Khaleesat ta fito Momy ta dauko mata kayan bacci da inner wears, Khaleesat ta shirya tayi sallan isha'i, Momy bata tashi barin dakin ba sai kusan karfe tara da rabi, bayan ta sa Khaleesat ta kwanta kan gadonta sannan ta kashe mata wutan dakin ta bata remote din Ac a kusa da ita, tayi mata sai da safe ta fita daga dakin, har ta kulle kofar ta sake budewa ta shiga tana kallon Khaleesat tace "Ko tashi kika yi zaki kama ruwa cikin dare kiyi tsarki da abubuwan nan fa Mamana kar ki manta" Khaleesat tace "Toh Momy" Momy ta kara mata sai da safe sannan ta fita ta kulle kofar da makulli ta sauka downstairs, Abdul kadai ne zaune parlor yana kallon kwallo amma kana ganinsa kasan ransa a bace yake, Momy tana kallonsa tace "Sai da safe Babana" Ciki ciki ya amsa mata, ta juya ta koma sama zuwa dakin da su Meemah suke, duk suka dinga kallon Momy bayan ta shigo, Aunty Karima tace "Ya dai Momy duk ta yi?" Momy tayi wani murmushi tace "Tun yaushe kuma" Meemah tace "Alhamdulillahi, shi Abdul din fa?" Momy tace "Shi ai dama a miyar shinkafa aka ce na zuba masa maganin, sai ruwan lipton, na kori mai aikin taje bakin pampo tayi wanke wanke shine na samu duk na zuba masa nasa" Meemah tayi murmushin mugunta tana gyara zama sanin Momy bata bin malaman banza, kai in malami yace zai amshi kasa da 1M a wajenta ma bata yarda da ingancin aikinsa ba, inda ake aikin da gaske take zuwa, ko da kuwa miliyan biyar zata kashe bata kyashi don tasan aiki na gaske ake mata. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* _Assalamu Alaikum yan mata da matan Oga ina me maku albishir da cewa Han-Ash skin beauty ta zo maku da kayan gyaran jiki iri iri wanda zai mayar da fatarki kamar Madara ta yanda duk inda kika shiga sai an kalleki, ki sai mayukan da zesa fatar ki tayi kyau, muna kuma maraba da siyan daya ko sari, i am assuring you that duk wani product dinmu is tested and trusted, ga kuma arha, for more information contact Han Ash via +234 803 810 3096_ We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 46 Washegari da safe bayan Khaleesat ta shirya cikin tsadadden Abayan da Momy ta bata, Momy ta gama hada mata shayin da take yi cikin cup tace "To zo kiyi breakfast din kar ya huce Mamana" Khaleesat bata ce komai ba ta karasa ta zauna kan darduman da aka jera mata breakfast din, Momy tayi murmushi tace "Idan farfesun bai isheki ba sai ki bude warmer ki ƙara, dankalin ma akwai saura a warmer in bai ishe ki ba" Ita dai Khaleesat kai kawai ta gyada mata, tana juya shayin gabanta a hankali da spoon din ciki, Momy ta koma kan kujera ta zauna tana kallonta tace "Duk da ma ina lura jiya baki wani ci abincin da aka kawo maki da yawa ba, ko maganin cin abinci zan sa a samo maki mamana" Khaleesat tayi murmushin karfin hali bata dai ce komai ba ta dau shayin tana kallon ciki, sai tayi tunanin lipton din ne kilan ya fashe a cikin ruwan shayin, sipping din shayin tayi kadan ta ajiye sannan ta fara cin irish din, Momy dai kallonta kawai take kasa kasa, Bude kofar dakin aka yi Momy ta juya, ganin Abdul tace "Sai yanxu ka tashi Babana" Bai ce mata komai ba ya karasa ya zauna saman kujera, Khaleesat ta ɗan kallesa taga kallonta yake, sauke idonta tayi a hankali tace "Ina kwana" Ya kauda kai yace "Lafiya" Momy tace "Ka tashi kaje kayi breakfast din ka" Yace "Momy za mu je shopping ne, bata zo da kaya ko daya ba" Momy na kallonsa tace "To wanda ka gani a jikinta yanxu kai ka siyo mata?" Shiru Abdul yayi yana kallon Momy, Momy tace "To har na tura ma Meemah kudi su je su yi mata siyayya ita da Karima tunda kai baka da ƙara" Mikewa Abdul yayi ya nufi kofa ya fice daga dakin, Momy ta bi sa da kallon gefen ido, sai da Momy taga Khaleesat ta gama cin abinda zata ci na breakfast din sannan ta mike ta fita ta kira mai aikinta ta fitar da sauran abubuwan da Khaleesat ta rage, bayan mai aikin ta fita Momy ta bude bayan labulenta ta dauko wani karamin jarka ta kawo ma Khaleesat tace "Wannan tsumi ne Mamana, daga yanxu har zuwa dare nake son ki shanyesa gaba daya" Ita dai Khaleesat kallon jarkan take, Momy tace "Kin ji ai ko?" Khaleesat ta gyada mata kai tace "Toh Momy" Momy ta dauka ta mayar bayan labule sannan tace "In zaki yi kallo sai ki kunna TV abun ki, bari in je zanyi bakuwa ban san ko ta iso ba" Khaleesat tace "Toh" Momy ta fita daga dakin ta kulle da makulli tana rike da makullin ta sauka downstairs don aminiyarta godiya ta kirata ta sanar mata tana hanya, tana shigowa parlor taga Abdul zaune dinning area da breakfast din da Khaleesat ta rage a gabansa, da karfi Momy ta kwala masa kira, ya juya yana kallonta, ta karasa wajen da mugun sauri tace "Banda abun ka ba ga naka a kitchen ba Abdul me zaka yi da wanda aka rage? Ko har kaci wannan din ne?" Abdul dake kallonta yace "Ban ci ba, amma menene idan na ci?" Momy ta kwalo ma mai aikinta kira, Mai aikin ta taho da sauri Momy ta kunduma mata wani ashar tace "Nan nace ki ajiye sauran abincin er iska kawai er neman jidali? Me yasa ke dakikiya ce? Wallahi zan kore ki fa a gidana na gaji da maganar da kike sa ni kamar kanwar uwarki, yau ga shegiyar mata kawai" Abdul ya kalli Momy yace "Ni fa nace ta kawo min nan, beside what is wrong with the food da bazan ci ba?" Momy ta mata tsawa tace "Dauka ki wuce ki ban waje guntuwar banza kawai" Mai aikin na ba Momy hakuri ta dauke jiki na rawa ta tafi kitchen da breakfast din, Momy ta kalli Abdul dake kallonta, yace "I want to understand meye da abincin da bazan ci ba Momy?" A takaice Momy tace "Kayan gyaran mata mana? Ko kai na mace ne?" Bata jira cewarsa ba ta bar wajen ta shige kitchen ya bi ta da kallo, Tuttular da shayin tayi a sink sannan ta juye sauran irish din da kwai da farfesun duk ta cakudesu waje daya tace "Gasu nan ki kai ma karnuka, in kuma kwadayin ki ya ja ki kika ci ke kika jiyo" Mai aikin ta risina ta amsa tace "Toh Hajiya" Sai da Momy ta jirata har ta dawo bayan ta kai ma karnukan can cage dinsu sannan Momy ta dau breakfast din Abdul ta kai masa kan dining din tace "Ga naka nan" Daga haka ta juya ta bar wajen, dai dai shigowar Godiya gidan, da fara'a Momy ke mata sannu da zuwa Abdul ya dauke kai kamar bai ganta ba don ya tsani matar with passion, tun asali dama baya gaida ta, Haka Momy ta ja ta zuwa sama tana cewa "Mu je ki ga surkar tawa ku gaisa" Da ido Abdul ya bi su har suka haura sama, Momy na isa kofar dakinta ta bude da makulli suka shiga, Khaleesat dake gyara gadon Momy ta mike tsaye tana kallonsu, Momy na murmushi ta kalli godiya tace "Kin ganta" Da fara'a sosai Godiya tace "Maa sha Allah, ai ko ga ta kamar balarabiya Maa sha Allah, sannu amarya, ya sunanki?" Momy na murmushi tace "Sunan Baabata gareta, Hauwa sunanta" Khaleesat ta zame kasa ta sauke idonta ta gaida Godiya, Godiya ta karasa kusa da ita ta dafata tare da ɗagota ta zaunar da ita gefen gadon Momy tace "Lafiya lau diyata, ya bakunta?" Khaleesat bata ce komai ba kuma bata dago kanta ba, Momy na kallon Khaleesat tace "Kin sha tsumin da nace ki sha kuwa?" Khaleesat ta gyada mata kai tace "Na sha" Momy tace "To maa sha Allah, Allah ya maki albarka Mamana, zuwa anjima sai ki kara sha kin ji" Khaleesat tace "To" Bayan few minutes Momy da Godiya suka fita dakin, Momy ta sake kulle kofar da makulli sannan ta cire makullin suka tafi wani daki dake sama, bayan sun shiga Momy ta kulle kofar tana kallon Godiya tayi murmushi tace "Duk tayi amfani da abubuwan babu gardama godiya, iya na jarkan nan ne kawai ya rage yanzu" Godiya ta zauna gefen gado tace "To madallah, shi ma Abdul din duk kinyi yanda aka ce kiyi da na sa?" Momy tace "Kwarai kuwa" Godiya tayi wani murmushi ta bude handbag dinta ta ciro wani babban laya bakikirin da shi ga er karamar kwado a jiki ta mika ma Momy tace "To aikin karshe kenan wannan Hajiya, Malam ya ce ki samu inda kika san baza a taɓa tono sa ba ki binne a cikin gidan nan" Momy ta zauna gefenta tana murmushi ta amshi layan tace "To laya nawa na binne gidan nan ba a tono ba godiya, ai wannan karamin aiki ne a wajena don ba sabon abu bane" Godiya tace "Yauwa, bayan kin binne Malam yace ki basa yarinyar kawai, wallahi yace min in har ta wuce sati biyu Abdul bai rabu da ita ba to bazata wuce sati biyar ba a gidansa" Fara'ar fuskar Momy ya bace tace "Har sati biyar Godiya? Ni da yace min sati daya kacal a waya" Godiya tace "Halan bai gaya maki irin abubuwan dake ƙan dan ki bane? Da yaya ma aka samo kansa har asirin nan yayi tasiri? Ai abubuwan ƙan Abdul sun fi karfin wani asirin wallahi kiji in gaya maki" Momy ta sauke ajiyar zuciya tace "An taɓa gaya min haka da dadewa wallahi, don ni akwai malamin da yace min ma yanda asiri ke cin ubansa shi sai an wahala asiri zai ci sa" Godiya tace "To wallahi Malam sai da ya tura masa aljanu don ma ki ji Hajiya, aikin nan sai da Malam ya hada da wasu malaman don aiki ne me wahalan gaske yace min wallahi" Momy tace "To ni fargabana kada fa in mika masa yarinya ace asirin nan bai ci ba abinda muke gudu ya afku mu shiga uku Godiya" Godiya tace "Sai kace yau Malam ya fara maki aiki? Ai da aikin bai yi ba kinsan bazai boye mana ba, sai dai ya kara mana lokaci yayi wani sabon aikin fa, dama yace in na yarinyar ya ci shine zai sa na Abdul din ma yayi tasiri sosai" Momy tace "Haka ya ce kam" Godiya tace "Don haka zuwa gobe ki basa ita kawai su tafi an gama aiki sai jiran result, kuma ina me tabbatar maki zaki sha mamaki" Momy na murmushi tace "Toh shikenan godiya, nagode sosai, zan tura masa cikon dubu dari biyar dinsa anjima" Da yammacin ranan bayan Momy taga Abdul ya fita gidan tayi maza ta aiki mai aikinta kasuwa saboda tayi amfani da daman ta haƙa rami a garden din gidan ta binne layan da Godiya ta kawo mata, bayan mai aikin ta tafi Momy ta zaga zuwa garden din gidan ta samu spot me kyau ta fara haƙa rami da wuka, bayan ta haka yayi zurfi yanda take so sannan ta jefa layan ta mayar da ƙasan wajen ta dau wani dutse ta dora dai dai wajen don kada a ga alamar an tono kasa, tap ta bude don wanke hannunta da wuƙan da tayi using, Khaleesat ta karasa bakin window din dakin Momy jin ƙaran bude ruwan pampo, in ta gaji da zaman dakin dama jikin window take zuwa ta tsaya tana kallon waje, ta tsaya jikin window din tana ta kallon Momy dake ta wanke hannunta bayan ta wanke wuƙan, bayan ta gama ta kara komawa kusa da dutsen tana seta sa da kyau ta yanda ko da wasa baza a ga tonannen ƙasa ba, sai kuma ta mike ta fara tsinko doddoya dake Garden din, sannan tayi using wuƙan hannunta ta yanki pumpkin leaves isasshe bayan ta gama ta bar garden din tana rike da ganyayyakin hannunta, babu abinda Khaleesat ta kawo a kai don tunaninta ganye Momy taje diba a garden din, Momy na kai ganyayyakin kitchen sai ga su Meemah sun dawo daga shopping din da ta aikesu su yi ma Khaleesat, dariya Momy ta dinga yi a parlor ganin wasu shegun abayoyi masu saukin kudi da suka kwaso ma Khaleesat irin wanda ake dinkawa a kano, ga wasu shegun dogayen riguna su ma masu arha, hatta inner wears da suka siyo duk very low quality ones ne, babu wani abu na arziki da suka siyo ma Khaleesat, Momy na ci gaba da dariya tace "Duk maida su cikin ledojin kawai na yafe ganin wannan tarkace haka karima, amma baku da kirki yaran nan" Aunty Karima na dariya ta maida kayan cikin leda ta kulle tace "Su ne dai dai er talakawa ai Momy, da so kika yi ki ga abayan dubu hamsin zuwa sama? Ai ita Meemah ma en gwanjo ta so mu je muyi selecting mata kawai" Dariya kawai Momy take, ita kuwa Meemah danna wayarta kawai take don duk wani abu da ya shafi Khaleesat ko kadan baya bata dariya, she just can't wait taga irin rabuwan da Abdul zai yi da Khaleesat don shine babban abinda ke gabanta yanxu. Wajen karfe takwas da rabi Momy na zaune parlor da Abdul tana ta yi masa hira, shi dai wayarsa kawai yake dannawa baya responding kamar ma bai san me take cewa ba, Momy ta kwalo ma mai aikinta kira, Mai aikin ta taho da gudu tace "Na'am Hajiya?" Momy tace "Zaki ga Kankana da na yanka a kitchen ki dauko ki kai ma Mamata a sama" Mai aikin tace "To Hajiya" Juyawa tayi ta koma kitchen sai ga ta ta dawo rike da bowl din kankanan tana kallon Momy cikin ladabi tace "Amma Hajiya dakin a kulle yake" Momy tace "A'a a bude yake tun daxu, ki je ki kai mata" Bayan mai aikin ta tafi ta kai water melon din ta dawo ta tafi kitchen ta ci gaba da aikin da take, Momy ta dau wayarta tace "Bari in inyi waya da Alhaji, daxu na ga kiransa ina kitchen wallahi" Shi dai Abdul bai ce mata komai ba har ta shiga dakin dake downstairs ya bi ta da kallo... Bayan minti biyu ya mike ya nufi stairs direct ya tafi bangaren Momy, yana bude kofar dakin Khaleesat dake zaune saman darduma bayan ta idar da sallah ta gama duk addu'o'in da zata yi ta juya ta kalli kofar, sosai gabanta ya fadi bayan sun hada ido da Abdul, ya karasa cikin dakin babu yabo babu fallasa yace "Ta shi mu je shopping...." Khaleesat da gabanta ke faduwa ta nuna masa ledan da Momy ta kawo mata daxu duk da bata duba kayan ciki ba cikin sanyin murya tace "Ai Momy ta sa an min shopping din, ka gan su can ma" Ya hade rai yace "Kee... Get up nace, i am not asking for ur opinion" Ta sauke idonta ta mike tsaye da kyar ta dauke darduman tana linkewa, sosai taji hankalinta ya tashi, a ranta ta dinga addu'an Allah ya kawo Momy dakin immediately, fixge darduman hannunta yayi ganin it's taking her a whole eternity to fold, ya ajiyesa saman kujera sannan ya kama hannunta suka nufi kofa fuskarsa a daure suka fita daga dakin, Khaleesat dai bin sa kawai take a tsorace, downstairs suka sauka har sannan yana rike da hannunta, babu kowa a parlorn sai mai aiki dake goge goge a dining area, ya dau makullin motarsa da ya bari kan center table, Khaleesat ta marairaice masa cikin rawan murya tace "Ya Abdul Momy fa bata sani ba, kar ta shiga dakinta taga bana nan, kaga babu dadi haka" Wani kallon da yayi mata yasa tayi shiru zuciyarta na bugawa, bata sake gigin ce masa komai ba har suka fita parlorn gidan zuwa parking space, Khaleesat taji hawaye ya cika idonta bayan ya sa ta shiga motarsa ya shiga driver seat, mai gadi ya bude masa gate ya fice gidan da motar. Momy ta fito parlor tana kallon Mai aikinta tace "Naji kamar fitar mota, waye ya fita?" mai aikin tace "Alhaji karami ne ya fita" Momy tace "Shi da wa?" Mai aikin tace "Shi da matarsa" Shiru Momy tayi don bata yi tunanin zai ce zai tafi da Khaleesat yau ba, don so tayi taga yanda za su kwashe, shi yasa ma ta basa hint din dakinta a bude yake, ta zata can din kawai zai bi ta ko kuma ya kai ta dakinsa, Momy ta sauke ajiyar zuciya, ganin mai aikinta sai kallonta take ta hade rai tace "Lafiya kike kallona haka munafuka?" Da sauri mai aikin ta juya ta bar wajen, Momy ta juya ta koma daki amma fa zuciyarta ya kasa nutsuwa sam sam, gani take kamar Abdul zai yi tarayya da Khaleesat, duk da malaminta bai taɓa mata aiki bata ga result me kyau ba amma a wnn case din sai take ɗari ɗari kada abinda suke gudu yaje ya afku dama ga Godiya tace aikin me wahala ne, ai kuwa da ta shiga uku ta lalace, number Godiya tayi dialing ta zauna gefen gado tana jiran tayi picking. Hawaye kawai Khaleesat take tana dafa shayin da Abdul ya sa ta dafo masa a kitchen, ita ta ma riga tayi give up yau don bata da wani dubaran da ya rage mata in ba so take ta fusata Abdul ya doketa ba, she will just accept her kadr with good faith, gwara tayi accepting dinsa kawai a mijinta tunda haka Allah ya kaddara mata, goge hawayenta tayi tana tafiya a hankali ta tafi kai masa lipton din dakinsa, tana bude kofar ya ajiye wayar hannunsa yana kallonta, kanta a kasa ta karasa har inda yake ta duka ta ajiye masa black tea din, ta mike zata bar wajen ya jawota ya zaunar da ita gefensa yana kallonta, ita dai bata bari sun hada ido ba zuciyarta na wani irin bugawa, ya dago kanta suka hada ido, sauke rigar baccin jikinta yayi slowly yana kallonta babu ko kiftawa, ta sunkuyar da kanta bugun zuciyarta ya tsananta sosai, tana ji tana gani ya cire duk abinda ke jikinta yana kare ma each and every part of her body kallo, bata sake yarda sun hada ido ba, a hankali ya kwantar da ita, ta runtse idonta da sauri jikinta na rawa ganin inda yake kokarin kai bakinsa, after some seconds Khaleesat ta bude idonta a hankali tana kallonsa jin bai yi abinda yayi niyya ba, taga wani wajen daban yake kallo babu ko kiftawa, after some seconds ta ga ya mike ya nufi kofa ya bude, fuska daure yake kallonta babu yabo babu fallasa yace "I need my privacy....." Khaleesat ta mike zaune da kyar tana kallonsa, lokaci daya jikinta yayi sanyi, ta jawo Hijab dinta da ya cire tun zuwansu gidan ta saka sannan ta dau kayan baccinta ta nufi kofa, bata bari ta hada ido da shi ba ta fita daga dakin taji ya kulle kofar da makulli, juyawa Khaleesat tayi tana kallon kofar..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 47 Da Asuba Khaleesat na zaune kan gado ta dafe kanta da yayi mata nauyi sosai, tun karfe uku da rabi bacci ya kaurace mata, bayan tayi sallahn nafila ta kai ma Allah kukanta shine take ta zaune saman gado tana tunanin rayuwarta, in 3 weeks time za su yi resuming school wanda shekarar su na karshe kenan za su shiga a makarantar but unfortunately tasan baza a koma da ita ba, ko kadan bata saka ran zata koma John Hopkins ba dama, but it's really hurtful don duk shekarun da tayi a makaranta zai tashi a banza kenan, ta goge hawayen da ya gangaro mata jin ana kiran sallan asuba ta sauka daga saman gadon, sai da ta dafa bango sbda juya mata da kanta ke yi, tun da ta tashi daxu take jin jikinta kamar ba ita ba, she can't even understand how she is feeling, sai da ta koma ta zauna na yan mintuna sannan ta tashi tana tafiya slowly ta wuce bandaki, wanke bakinta tayi sannan ta dauro alwala ta fito daga bandakin, bayan ta idar da raka'atanil fajr tayi sallan asuba, har karfe bakwai na safe Khaleesat na zaune kan darduma duk da ta idar da azkar din ta, in tayi wannan tunanin tayi wancan a haka dai har ta mike daga karshe tana tafiya a hankali ta nufi kofa ta bude ta fita daga dakin, bata karasa parlon ba ta tsaya tana kallon Abdul dake kwance saman 3 seater idonsa a lumshe yana sauraron karatun qur'ani ta wayarsa dake gefensa, duk tunaninta bacci yake ganin yanda ya lumshe ido, har zata juya ta koma dakinta taga ya bude ido yana kallonta, ta sauke idonta ta karasa cikin parlon tana tafiya a hankali ta duka kusa da shi cikin sanyin murya tace "Ina kwana" Yace "Lafiya" Bata sake cewa komai ba kanta a kasa, after some seconds ta mike zata bar wajen, calmly yace "I need breakfast, ban ci abinci da daddare ba" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma tace "Toh...." Juyawa tayi ta nufi kitchen don ganin me zata girka, doya da kwai tayi deciding tayi don shi tagani available a kitchen din, wajen karfe takwas ta gama komai ta kai har gabansa a parlon ta durkusa ta ajiye, ganin bread a kan dining table ta mike ta tafi ta dauko sannan ta dawo ta ajiye masa tana kallonsa a hankali tace "Gashi na gama, in hada maka shayin?" Without looking at her yana danna wayarsa daga kwancen da yake yace "Ohk" Hada shayin tayi bayan ta gama ta koma gefe tana kallonsa a hankali tace "Na gama" Ajiye wayarsa yayi ya sauko daga saman kujeran, shayin ya dauka yana sha, ba tare da ya kalleta ba yace "Ke ina naki shayin?" Shiru tayi bata ce komai ba, jin tayi shiru ya daga kai ya kalleta, sunkuyar da kanta tayi, sai kuma ta mike ta nufi kitchen, ba a dau lokaci ba sai ga ta ta dawo da cup da tea spoon, ta duka kasa ta fara hada shayin nata, ya kalli madaran da ta zuba a shayinta ya dau wani spoon ya kara mata madaran, ita dai bata bari sun hada ido ba, a plate daya ya dibar masu doyan ya fara ci, ita dai juya shayinta kawai take a hankali, after some minutes ganin bata fara cin doyan ba ya daga kai ya kalleta yace "Ko a baki za a baki?" Ta ɗan yi murmushin karfin hali ta dau fork ta fara cin doyan a hankali, da ta kallesa sai su hada ido, kana ganinta kasan she is not comfortable a wajen don ya riga ya sa mata tsoronsa a zuciya, daga karshe ta ajiye fork din hannunta a kan tray, ya daga kai ya kalleta, a hankali tace "Na koshi" Bai ce mata komai ba, ta koma gefe tana shan shayinta slowly, after a while Abdul ya mike ya koma saman kujera, ta tashi ta dau sauran abincin ta kai kitchen, sai da ta wanke utensils da suka yi using sannan ta fito daga kitchen din, magana take son yi masa amma tana tsoro, ya kalleta tayi saurin sunkuyar da kai kamar munafuka tana wasa da yatsunta, yace "Me ya faru?" Ta karasa ta duka daga gefensa a hankali tace "Dama pls ina son zan yi magana da Safiyyah, ka taimaka ka kira min ita ta wayarka" A takaice yace "Bazan kirata ba, kanwar baabarki ce Safiyyar?" Sosai jikin Khaleesat yayi sanyi, ta sunkuyar da kanta tayi shiru bata ce komai ba, yace "Tafi ki bani waje" A hankali ta mike a sanyaye ta wuce dakinta, goge hawayen da ya taru idonta tayi ta zauna gefen gado, after a while ta share hawayen da ya ki tsaya mata ta mike ta cire hijab din jikinta ta linke ta ajiye sannan ta shiga bandaki, brush tayi sannan tayi wanka, ganin abubuwan wanke gashi a bathroom din ta wanke gashinta ta tsane da karamin towel sannan ta dau wani towel din ta daura ta fito, tana tsaye gaban madubi tana shafa man gashi taji an bude kofar dakin, da sauri ta juya gabanta ya fadi sosai ganinsa, kana ganinsa kasan daga wanka ya fito shi ma, cikin dubara ta gyara daurin towel dinta tana jin zuciyarta na bugawa ta ci gaba da oiling gashinta, ya karaso har inda take tsaye ya tsaya a bayanta yana kallonta ta madubi, ita dai ta kasa dago idonta tana jin saukan numfashinsa a bayanta, ta ajiye oil din hannunta a hankali don duk ta daburce, shi dai yana tsaye dab da ita yana kallonta ta madubi, ya kai hannu zai yi loosening din towel din kirjinta, juyowa take son yi da sauri kamar zata yi kuka cause bazata iya ganin kanta ta madubi a yanda yake ganinta ba, yaki barin ta juyo hakan yasa ta runtse idonta zuciyarta na bugawa, bai fasa kallonta ta madubin ba har ya cire towel din jikinta ya jefar saman gado, he kept his eyes glued to her cause he just can't stop admiring her bare body any time he set his eyes on her, gaba daya taki yarda ta bude idonta, bata ankara ba kawai sai jin su tayi a saman gado, bata san sanda ta bude ido ba ta fashe da kuka tana turasa a tsorace ganin yau kai tsaye kawai far mata yake kokarin yi babu bata lokaci, ita kanta bata san inda ta samu courage din turasa ba duk da tsoronsa da take, da mamaki yake kallonta yana sauke numfashi, ganin kiciniyar sauka take yi daga saman gadon tana kuka, cikin kakkausan murya yace "I will give u a dirty slap" Danneta yayi yanda ko motsin kirki bazata iya ba balle tace zata sauka daga saman gadon, ta dinga masa kururuwa tana kokarin kwatar kanta don bata taɓa tsorata ta gigice da lamarin nan ba irin yau, duk yanda Abdul ya so cimma burinsa a wnn moment din hakan ya faskara, kawai ya tuna ita ba irin matan da ya saba mu'amala dasu bane, he couldn't have his way no matter how hard he tried, he was so confuse as at how intact she is even though he knows she is a virgin, hakan yasa ya fara romancing dinta roughly to make his way more slickier, cause he was determined in fulfilling his mission today, wani wawan marin da yayi resetting dinta back to default ya sauketa mata don duk da yanda ya danneta she is still struggling so hard to free her self under him, Khaleesat taji kamar numfashinta na yi mata gardama, at this moment tasan babu me kwatar ta hannunsa sai Allah, she was so weak and in severe pain hakan bai hanata struggling ba cikin kuka take cewa "Don girman Allah ka rufa min asiri Abdul, wallahi mutuwa zan yi bazan iya ba, it's soo painful...." Ya kara sauke mata wani marin cause he is seriously trying to find his way by all means, Gaba daya Abdul komawa yayi kamar bai taɓa tarayya da mace ba a wnn lkcn, ya koma kamar Amateur da ta mance inda zai bi, duk wani dubaransa was fortile, he was really frustrated and vexed, Ganin how helpless she was ga numfashinta na neman daukewa ya rungumeta gam jikinsa yana kallon fuskarta da tafin hannunsa ya kwanta ta dalilin marin da yayi mata, lumshe ido yayi yana sauke numfashi kamar wanda yayi tsere, saukan hawayenta ya dinga ji a kirjinsa ya lumshe idonsa zuciyarsa na bugawa, after almost a minute yayi kasa da murya da kyar, yana shafa dogon gashinta yace "I am sorry Khaleesat, i am sorry" Ita dai hawaye kawai take tana sauke ajiyar zuciya, tana jin wani azaba in between her, they were like this for almost 5 mins, Abdul ya saketa ya koma can karshen gadon ya dafe kansa dake sara masa, ga wani azababben ciwon mara da yake ji, da kyar ya mike ya dafa bango na ɗan lokaci kafin ya nufi kofa ya fice daga dakin, Khaleesat ta takure cikin duvet tana sauke ajiyar zuciya hawaye wasu na bin wani a idonta, bata san lkcn da baccin wahala ya dauketa ba a haka. Karfe sha biyu saura taji hannu a forehead dinta, bude idonta da suka kumbura tayi a hankali don sosai kanta yayi mata nauyi, suna hada ido ta sauke idonta, Calmly yace "Ta shi ki shirya mu tafi shopping" Da kyar ta mike zaune tana kara rufe jikinta da duvet, sai kuma ta fara jawo towel din da ya cire mata daxu, shi dai bai ce mata komai ba yana kallonta, har cikin ransa he felt bad ganin yatsunsa kwance a fuskarta, cikin dubara ta daura towel din sannan ta mike tsaye lkci daya ta duka kasa da sauri tana runtse ido, yana kallonta yace "What?" Lokaci daya hawaye ya idonta, cikin rawan murya tace "Bazan iya ba, zafi nake ji sosai" Ya hade rai yace "Zafin me?" Ta kasa kallonsa hawaye na sauka idonta, yace "Me na maki da za ki ji zafi?" Ita dai bata dago kanta ba gabanta na faduwa, mikewa yayi ya fice daga dakin ta bi sa da kallo, after a while Khaleesat taji fitar motar sa a gidan, ba karamin daurewa Khaleesat tayi ba ta tafi bandaki, sai da tayi sit bath sosai sannan taji ta samu sukuni, tayi wanka ta dauro alwala ta fito. Karfe biyu saura tana tafiya a hankali tana dingishi ta fito parlor, ledan kayan da Momy ta bata ta gani a parlon, ta karasa ta bude ledan sai a sannan taga irin kayan da su Meemah suka siyo mata, a hankali ta daure ledan ta dau kayan walking slowly ta koma dakinta da su ta ajiye ta dawo parlon ta tafi kitchen don daura girki... Momy dake zaune parlor tana kallon Meemah da wani expression tace "Bacci fa kika ce Meemah??" Meemah ta ajiye gyalen jikinta tace "Wallahi kuwa Momy" Momy tace "To baccin me take wajen karfe sha dayan safe??" Meemah tace "In kin tambayeni in tambayi wa?" Momy ta gyara zama tace "Toh baki tafi dakin kin dubo ba?" Meemah tace "In lafiyarta qlau ai kinsan taso ta zai yi ta fito ta gaisheni barin ma da nace masa kin bani sako in bata, sai ce min yayi magani ta sha tana bacci" a hankali Momy tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Meemah tayi wani murmushi tace "Kinsan Allah Momy, kawai jikina ni tun asali ya bani ba lallai irin wannan asirin yayi tasiri lokaci daya ba, bance bazai yi tasiri ba amma sai ya gama moreta tukun, kin ga in rabo ya shiga kafin nan kuma ai mun shiga uku mun lalace, hada iri da talaka ya tabbata" a fusace Momy tace "Ke dai a rayuwarki baki taɓa furta alkhairi sai sharri Amina? Asirin kusan miliyan biyun kike ce min ba lallai yayi tasiri ba? Ko kina hauka ne?" Meemah tace "A'a ni bance bazai yi tasiri ba Momy, cewa nayi..." Momy ta dakatar da ita rai bace tace "Bana son ki sake saka min mugun bakin ki a lamarina, ki tashi ki ban waje kar in yi mummunan bata maki rai wallahii" Mikewa Meemah tayi ta kyabe baki tace "Shi Abdul din da duk mun san yanda idonsa ke kan mata ne kike tunanin zai bar yarinyar nan su kwana gida daya babu abinda ya shiga tsakaninsu?" Wani zagi Momy ta kunduma mata tace "Baza ki tafi ki ban waje ba, me mugun alkaba'i kawai, duk ba ke kika ja mana wannan bala'i ba?" Meemah na tabe baki tayi tafiyarta sama, Mikewa Momy tayi ta fara zaga parlor tana jin zufa na keto mata duk da Ac dake kunne, sai kuma ta dau wayarta ta wuce sama da sauri. Wajen karfe hudu da rabi Abdul ya dawo gida, Khaleesat ta idar da sallah tana zaune kan darduma ya shigo dakin ya ajiye shopping bags din hannunsa, ta mike a hankali tana kallonsa tace "Sannu da zuwa" Yace "Ki duba ko akwai abinda ba a siya ba" Tana kallon bags din ta karasa inda ya ajiyesu tana duba tsadaddun Abayan da ya siya mata kala kala, da takalma da handbags, irin dai quality din da yake siya mata a baya, duk wani abu da zata bukata sai da ya siyo mata, har da tsadaddun turaruka iri iri da man gashi, da na shafawa, kallon lube din da ta ciro a siyayyan ta dinga yi don at first tayi zaton na shafawa a fuska ne, sosai gabanta ya faɗi ta ɗan kallesa taga kallonta yake, da sauri ta dauke kai zata ci gaba da ciro sauran abubuwan da ya siyo ya mika mata hannu alamar ta basa lubricant din, ta mika masa ba tare da ta bari sun hada ido ba, juyawa yayi ya dau ledan kayan da Meemah ta kawo daxu ya fitar da shi daga dakin, a hankali Khaleesat ta zauna gefen gado nan da nan hawaye ya cika idonta, bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba tana tuna azaban da ta sha daxu. Wajen karfe takwas da rabi na dare Khaleesat ta gama dafa ma Abdul tea din da ya sa ta ta dafa masa, gaba daya tun daga sanda ya dawo har zuwa yanxu bata da sukuni a gidan, tana sanye da hijab ta karasa har inda yake zaune a dakinsa yana karatun Alqur'ani, ta durkusa ta ajiye masa shayin, zata mike ya jawota jikinsa bayan ya rufe qur'anin, yayi kissing goshinta yana kokarin cire mata hijab din har dai ya cire, lkci daya jikinta ya fara rawa tana son kwace kanta, ƙin saketa yayi ya riketa gam, tun tana ganin abun kamar wasa tunda a zaune yake, har sai da ta gansu saman gado ya rabata da komai na jikinta sannan idonta yayi clear, ihun da ta dinga masa tana kuka tana kokuwa da shi bai sa ya fasa abinda yake yi ba, upon yayi using lube da ya siyo amma kamar daxu yanxun ma dai bai iya yayi mata komai ba, after a while ya sake ta, fuskarsa a daure yace "Fita" Ta sauka kan gadon da sauri ta dau hijab dinta ta saka ta fice daga dakin jikinta na rawa, zaunawa yayi gefen gado ya rike kansa da yayi masa nauyi yana sara masa. Throughout washegari Abdul bai bi ta kanta ba a gidan, ta dai gaishesa da safe ya amsa babu yabo babu fallasa, amma hatta breakfast da tayi bai ci ba balle lunch, sosai taji guilty conscience na damunta don tana tsoron kamun Allah, tunda tayi karatun addini tasan kuma meye aure, amma yanxu ita kanta tasan ba intentionally bane taki basa hadin kai, kasa daurewa tayi wajen karfe uku na rana jiki a sanyaye ta samesa a parlor ta durkusa daga gefensa a hankali tace "Don Allah Ya Abdul kayi hakuri idan nayi maka laifi" Shiru tayi don ita kanta tasan she sounds stupid, Babu yabo babu fallasa yace "Laifin me?" Ta sauke idonta ta kasa cewa komai, Yace "Ohk kinsan ma abinca kike yi kenan" Ta girgiza masa kai da sauri, kallonta kawai yake don duk yau ji yayi kamar an dauke masa sha'awarta, unlike before da ko me zata yi feeling din nan nata dai na nan a ransa, kawai ji yayi baya ma son ganinta kawai, Calmly yace "Tashi ki bani waje" A hankali ta mike ta bar parlon. Da daddare bayan magrib yana kwance parlor ya kunna karatun Alkur'ani ta wayarsa yana saurare, tun da Khaleesat ta fito zata je daukan abinci a kitchen ya bi ta da kallo, har ta fito daga kitchen din ta wuce dakinta da abincin, ya mike zaune, after a while sai ga ta ta sake fitowa ta kai plate din kitchen, hijab ne har kasa a jikinta, still da ta fito haka ya bi ta da kallo, ita dai ta gefen ido kawai take kallonsa har ta koma dakinta, Bayan isha'i ya bude kofar dakinta, sosai ta tsorata ganinsa, suna hada ido ta sunkuyar da kanta don dama zaune take kan darduma ta idar da sallah, Yace "Make me a cup of tea" A hankali tace "Toh" Jiki a sanyaye ta tashi taje ta dafo masa tea din ta kai masa dakinsa, haka kawai gabanta ya dinga faduwa ganin kallon da yake mata, ta dai ajiye cup din tea din sannan ta fita ta koma dakinta ta kashe wuta ta kwanta ta shige cikin duvet, banda faduwa babu abinda gabanta yake yi, har ta fara bacci ta ji ana cire duvet din jikinta ta mike zaune a tsorace tana kallonsa kamar zata yi kuka don ya kunna dim light a dakin, yace "Nan wai wayo kika yi kika zo kika kwanta da wuri?" Sunkuyar da kanta tayi zuciyarta na bugawa bata ce masa komai ba, ya xauna gefenta ya jawota jikinsa a hankali, yayi kasa da murya yace "Kar ki manta you are my wife legally Khaleesat, why are you making everything seems hard for us both?" Kuka ta fara yi a hankali, yana magana kamar me rada yace "You just have to stay calm and relax plss, i promise i won't hurt you Khaleesat, the lube will help, jiya kin ki sakin jiki shi yasa bai yi ba" Khaleesat dai kukan tashin hankali kawai take bata ce masa komai ba tana kallon lube din da ya ajiye saman gado, kwantar da ita yayi taking off her nighty ya fara bi da ita gently kamar yanda yace, duk yanda Khaleesat ta saka ma ranta yau dai zata daure kawai tayi hakuri yayi abinda zai yi amma yana fara taɓata ta fara masa kuka da karfi tana turjewa, tsabar feelings dinta da yake ji yau duk bai ma san tana yi ba, banda lallabata da bata hakuri babu abinda yake yi yana bi da ita a hankali, don burinsa kawai yayi accomplishing mission dinsa yau ya maida ta mace, amma me? even with the help of so much lube hakan yayi seeming impossible, magiya ya dinga yi mata kamar zai mata kuka yake rokonta she should let him pls don gani yake kawai don taki sakin jiki ne, sosai yake rokonta as if his life depend on what he is trying to do, ita banda kukan azaba babu abinda take tana kokarin kwace kanta tana turasa da duk sauran karfinta, mari ya sauke mata a fusace ya shakota yana huci yace "Is all this among ur plan??" Kasa magana tayi saboda shaƙeta da yayi da karfi, ya wani turata har sai da ta fadi kasan dakin, yana huci ya sauka daga saman gadon ya nufeta yace "Ni xaki raina ma hankali? Ni zaki dinga dauka for granted?" Cikin kuka tana komawa baya ta dinga cewa "Don girman Allah kayi hakuri, wallahi bani bace Ya Abdul, nima ban san me yasa haka ba" Ya dagota da karfi yana kallonta da idanuwansa da suka yi jajir yana wani irin numfashi yace "Saboda kin saka a ranki baki son aurena baki son zama da ni shi yasa baza ki bani hakkina ba?" Jikinta na rawa ta dinga girgiza masa kai tace "Wallahi a'a, don girman Allah kayi hakuri...." Wurgata yayi da karfi har sai da ta buga da bango, ya juya ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, ƙasa motsi Khaleesat tayi tana ganin duk dakin na juya mata, yana fita dakin da minti goma taji fitar motarsa a gidan, kuka Khaleesat ta dinga yi sosai ko ina na jikinta na mata ciwo a dakin, ta fi awa daya kwance inda ya wurgata, ji take kamar bazata iya tashi ba ga azaban da take ji a ƙasanta, da kyar ta rarrafa zuwa bandaki daga karshe, bayan ta gyara jikinta ta fito ta kwanta nan kasan dakin tana kuka a hankali ga wani azababben ciwo da kanta yake mata, tashi zaune tayi ta jingina da gado tana tunanin what exactly will be the problem, don ita ta riga tayi give up din Abdul a matsayin mijinta, ko dai tana da wani ciwo ne da bata sani ba a wajen, if not ko yanda yayi using lube din nan should have been enough, to ko ce masa zata yi su je asibiti don ya dena zargin hanasa take yi, bazata so Allah ya kamata da laifin hana mijinta kanta ba, hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta, she wish zai bata listening ears ya saurareta yasan she is not doing this purposely, sai wajen karfe daya da rabi na dare taji shigowar motar Abdul, gabanta ya dinga faduwa tana kwance kasan dakin har taji alamar ya shiga dakinsa, mikewa tayi da kyar ta saka hijab dinta tana dingishi ta fita daga dakinta, tsaye tayi tana kallon kofar dakinsa gabanta na faduwa don bata san me zai ce zai mata ba idan ta shiga dakin, daga karshe tayi shahada ta bude a hankali ta shiga gabanta na faduwa, wanka taji alamar yake yi a bandaki, ta dinga kallon wrist watch dinsa da wayoyinsa da sauran ledan Prophylactic dake ajiye gefen gadon, sosai jikinta yayi sanyi ta dinga kallon prophylactic din, taji hawaye masu zafi na sauka idonta, bayan few seconds ta juya a hankali ta fita daga dakin, wasu sabbin hawaye na sauka idonta ta koma dakinta ta kwanta saman gado tana shesshekan kuka. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 48 Wajen karfe bakwai Khaleesat ta fito daga dakinta tana tafiya a hankali, duk da zazzabin da ta tashi da shi yau haka nan ta daure ta fito, tana hangosa kwance kan kujera yana danna wayarsa sai da gabanta ya fadi sosai, ta sauke kanta ta karasa har inda yake kwance ta durkusa cikin sanyin murya ta gaishesa, wayarsa kawai yake dannawa yaki kallon direction dinta balle ya amsa gaisuwarta fuskarsa a daure, bayan kusan minti daya ta mike jiki a sanyaye ta juya ta wuce kitchen, hawaye taji ya cika idonta ta kai hannu tana gogewa sannan ta fara preparing breakfast, bayan kusan minti arba'in ta fito daga kitchen din zata tambayesa ko ta kawo masa breakfast din yanxu duk da yanda gabanta ke faduwa, amma sai bata gansa a parlon ba, hakan yasa ta juya ta koma kitchen din ta dauko breakfast din ta kai dinning table ta ajiye, zata tafi dakinta kenan sai gashi ya fito daga nasa dakin har ya shirya alamar wanka yayi, tana kallonsa a hankali tace "Na gama preparing breakfast din" Banza yayi mata ya wuce ta, ta bi sa da kallo har ya shiga parlor, a sanyaye ta bude kofar dakinta ta shiga hawaye na taruwa idonta, ta zauna gefen gado tana goge hawayen a hankali, lamo tayi kan pillow tana shesshekan kuka, tunani iri iri ne ke mata yawo a rai, me ke faruwa da ita ne? Ko tana da wani ciwo ne da bata sani ba, who is she going to talk to about this? Hawaye taji na zubo mata sosai, how is she going to explain to Abdul that this isn't her fault? Ta yaya zata fahimtar da shi ya gane? Tafi awa daya kwance tana saƙe saƙe a ranta, a hankali ta mike zaune jin alamar fitar motarsa daga gidan, da kyar ta mike daga karshe ta tafi parlor tana tafiya a hankali, dinning area ta nufa ta duba taga bai taɓa komai ba a breakfast din da ta ajiye masa, ta juya a sanyaye ta koma parlor ta zauna ta jinginar da kanta da kujera hawaye na sauka idonta, after a while ta tashi da kyar ta fara gyara gidan sannan ta hada shayi ta dawo parlorn ta zauna amma ta kasa sha saboda damuwa, daga karshe kawai ta koma dakinta. Wajen karfe uku taji ya dawo gidan, ita dai tana ta zaune dakinta bata fita ba, bayan kusan minti biyar ya bude kofar dakin nata, kallo daya yayi mata yace "You have Visitors" Daga haka ya juya ya bar wajen, tayi jim tana tunanin su waye visitors din, mikewa tayi ta dau veil din Abayan dake jikinta ta rufe kanta sannan ta fito parlor tana tafiya a hankali, buda ido tayi ganin Aunty Farida da Nenne da step mothers dinta zaune a parlor, da gudu ta tafi ta fada kan Aunty Farida ta rungumeta cike da farin cikin ganinta, Nenne ta hade rai tana kara hakikancewa kan kujera tana kallon TV da aka kunna a parlon, Aunty Farida ta dago kan Khaleesat tana kallonta ganin yanda ta rame, a hankali tace "Ya kike Khaleesat?" Khaleesat ta sauke idonta cikin sanyin murya tace "Lafiya lau Aunty, Ummana fa? Me yasa baku zo da su Islam ba?" Aunty Farida tayi kasa da murya tace "Ke baki gaida su Nenne ba" Sai a sannan Khaleesat ta tuna da sauran mutanen parlon, zamowa ƙasa tayi a hankali tana kallon Nenne tace "Ina yini Nenne?" Nenne tace "Akan me zaki ce min ina wuni ni da nake er banza mara mutunci a idonki? Ita Faridar da kika makalewa kina shigewa jikinta da an biye ta tata da bata kashe auren nan har lahira ba? Da an biye ta Farida da Zahra'u idan kin ganki a wannan gida haka Allah ya tsine min albarka, to sai me don kin gan ni kin kauda kai kinyi kamar baki ganni ba da sauran matan ubanki? Ai babu komai" Khaleesat ta hade rai ta gaida su Mama Shatu dake zaune fuska duk babu walwala suka amsa mata babu yabo babu fallasa suna kare mata kallo, Nenne ta gyara zama cikin bacin rai tace "Banda matan ubanki da suka takura aje a san inda kike a ga halin da kike ciki sannan ni da na amshi sabon lambar Awdul wajen Farida nayi ta doka masa kira har yaje ya dauko mu ya kawo mu kin zata akwai wanda zaki gani a gidan nan ne? Ita farida Allah Allah take ta koma Legas ta ci gaba da tuwo tuwonta a can, uwarki kuma ba sanin ciwonki tayi ba balle ta samar mana hanyar zuwa ganin halin da kike ciki, amma me? haka nan albarkacin Ali nace dole dole sai naje naga halin da kike ciki, haka nan na uzura ma Awdul da kira yaje ya dauko mu, kuma Alhamdulillahi ga ki nan har wani haske kika kara alamar kina cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya da mijin ki, to meye zaki yi kamar baki taɓa sanin mu ba daga abun arziki dai" Mama Zubaida tace "To ai sai a zaga damu cikin gidan mu sa albarka tunda Allah bai yi mu za mu kawo amarya ba" Nenne tace "A'a, ba bin kwakkwafi da tsegumi ya kawo mu ba kaman en iska, tunda dai yarinya na cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya dama mu hakan ne kadai fatan mu, don haka babu me shiga mata ko ina a gidanta, in ma ce maku aka yi ku yi hakan don wata mugun manufa taku to baza ayi ba, don ni ban yarda da yanda ku ka dage sai an zo gidan Khaleesah ba tunda ni ba yarinya bace, dama kuma Ali yace ko minti sha biyar kar mu yi, da mun samu ganinta mu kamo hanya mu dawo tunda mu ba iyayen banza bane" Mikewa Khaleesat tayi ta tafi kitchen ta bude fridge ta dauko ruwa da drinks ta daura kan tray ta kai masu parlorn ta ajiye, ita dai Aunty Farida sai bin ta da kallo take don kana kallon fuskarta tasan akwai damuwa, gashi tana son kebewa suyi magana da ita amma tana gudun fitinar Nenne, Nenne na kallon Farida tace "Karfe nawa yanxu?" Farida tace "Uku da minti goma" Nenne na gyara mayafinta tana kallon Khaleesat tace "Toh kitchen za ki kai ni mu gana ko kuwa? in mun gama magana sai kije ki ce masa za mu koma ba zama muka zo yi masa ba" Aunty Farida ta dake ta mike tace "Kafin nan bari in ɗan yi magana da ita Nenne" Nenne ta kalleta da sauri tace "Ai ba kashe aure ya kawo mu ba Farida, in baza kiyi mata magana a gabanmu gaba daya ba to ki rike maganar ki kawai don ba alkhairi bane, haka kawai baza ki ja yarinya ki keɓe da ita ki kitsa mata tsiya da salon kashe aurenta ba" Aunty Farida ta dinga kallon Nenne, Nenne ta mike tana rike da babban jakarta tana kallon Khaleesat tace "Kai ni kitchen din" Khaleesat taji kamar tayi kuka bayan Nenne ta hana Aunty Farida tayi mata magana, rai babu dadi ta nufi kitchen Nenne na biye da ita a baya bayan ta jaddada ma farida a kunne kar ta bari su Mama Zubaida su shiga ko ina na gidan, su Mama Shatu da Mama Zubaida sai tabe baki suke, Nenne ta tura kofar kitchen din bayan sun shiga, tana kare ma kitchen din kallo tace "Maa sha Allahu kai kaji waje sai kace daki uku a hade, kuma iya girki kawai ake yi a nan?" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, Nenne ta zauna kasan tiles din kitchen din ta zuge jakarta tana kallon Khaleesat tace "To kin tsaya min kerere a kai" Dukawa Khaleesat tayi a gabanta tana kallonta, Nenne ta fito da wasu kulle kulle har ƙashi biyar, ta dinga kwancesu daya bayan daya cikin nutsuwa, murya can kasa tace "Kin ga wannan?" Khaleesat dai kallon kullin da Nenne ke nuna mata kawai take, Nenne na magana a hankali kamar tana tsoron wani ya ji tace "Cikin ruwan wanka zaki dinga diba kadan kadan kina zubawa kiyi wanka, duk wani mugun abu da mutum zai maki ko kuma yayi maki to da izinin Allah zai koma kansa da zuri'arsa, sharrin zai lalace na har abada, Wnn kuma a kunu zaki dinga zubawa ki sha kayanki ke kadai, wannan girki zaki dinga yi maku da shi gaba daya ku ci, ba wani mugun abu bane kawai saboda zaman lafiyanku da kwanciyar hankalin ku babu kuma ɗan iskan da zai iya shiga tsakaninki da mijin ki, sai ki ga kanku ya hadu kuna ma juna nutsattsen soyayya bakwa son laifin juna, wnn na hayaki ne shima duk wani mugun abu idan an maki zai karye ya koma kan me shi da izinin Allah, da kyar aka tsam min wallahi, kin dai gansa ɗan mitsitsi ko Ali ban dibar ma ba tunda naga bashi da yawa na kawo maki ba don halin ki ba, wannan na karshen shi kuma na sha ne da wanka, in kinyi wankan sai ki kada shi ko cikin ruwan shayi ne ki dinga shan abun ki" Ita dai Khaleesat tayi shiru tana ta kallon abubuwan da Nenne ke mata bayaninsu sinka sinka cikin nutsuwa, Nenne ta gyara zama fuskarta a daure tace "Wallahi in kika sa nayi asaran lokacina da en kudadena kika ki amfani da wannan abubuwan da na shiga kauyuka takanas na samo maki to in na maki Allah ya isa sai ya bi ki tunda ni ba baiwar buzuwar uwarki bace, duk ita ya kamata ta maki wannan abun amma gantalalliyar bazata yi ba, dama kuma sari nasan ke da ita bakwa amfani da duk wani abun taimako da nake baku, wani lkcn matsalarku ce ma ke shafan ɗa na yayi ta wahala a duniya, to wannan in ma kinki yi wallahi kanki kika cuta don dangin Awdul ba mutanen arziki bane duk mun sani, kuma ba lallai su barki ki zauna lafiya a gidan mijin ki ba barin yanda suka dau ƙaran tsana suka dora ma ubanki saboda shi talaka ne, to ni dai gashi nan albarkacin ubanki na maki wannan wahala, haka nan na shiga wani kauye duk mayu na fito da kyar, to ya rage naki kiyi ko kar ki yi, in ma baki yi ba Allah ya isa" Khaleesat dake kallonta tace "Toh in ya gan su sai in gaya masa na menene su?" Nenne ta saki baki tana kallonta, a fusace tace "Ke dai sokuwa ce mahaukaciya, to uban wa yace maki a gabansa za ki yi? Yau naga bala'i, wannan wace irin shashashar yarinya ce? dama ba sai ya fita ba zaki yi maza kiyi duk abinda zaki yi kafin ya dawo? Ni da ban yi boko ba ma nafi ki hankali da wayo? wannan wace irin jaraba ce Zahra'u ta haifar ma Ali? To ki kwasa ki nuna masa tunda baki da seti" Khaleesat ta wani hade rai ta kauda kai, Nenne tayi kasa da murya tace "Ae sai ya fita duk zaki yi komai cikin sirri, yanxu boyewa zaki yi inda ko da wasa bazae gani ba" Khaleesat tace "Toh ae zae ji warin hayakin kuma, sannan ni bama ni da abun yin turaren wutan ai" Nenne tace "To dama ai shegen a gantale ya dauko ki bai bari duk mun shirya maki turaren wuta ba da sauran abubuwan da ake kai mata da su gidan miji, yanxu dai nasan shi zai maida mu gida ina da manyan robobin turaren wuta har biyu da na ajiye maki zan basa turaren da kasko ince ya tsaya gun masu siyar da gawayi a bakin hanya ya siya maki ko leda uku ne ya taho maki da shi, sai ki dinga hurawa a kaskon tunda ga AC a parlon nan da nan zai kama maki in kika hura" Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba, Nenne tace "To shikenan ki maida ni mahaukaciya ina kokarin taimakon rayuwarki" Khaleesat tace "Na ji" Nenne tace "Yauwa to, yanxu gasu nan maza ki je ki boye inda bazai gan su ba kwata kwata" Khaleesat ta amsa ta nemi waje a nan kitchen din ta boye, Nenne tace "Yauwa to haka ake yi, yanxu maza tafi ki ce masa zamu tafi kar ya ga mun zaune masa a gida, dama ni wnn abubuwan yasa nayi ta doka masa kira yau kwana uku kenan, har Allah yayi ya zo ya dauke mu" Mikewa Khaleesat tayi ta fita daga kitchen din Nenne na biye da ita murya can kasa tace "Ko ruwan gidansa mu dai bamu sha ba balle yace" Khaleesat na tafiya a hankali ta nufi dakin Abdul, knocking tayi tana jiran ya amsa, after almost a minute ya bude kofar, ta sunkuyar da kanta tace "Za su tafi" juyawa yayi ya koma dakinsa, hakan yasa ta dawo parlor, Nenne na kallonta tace "Kin gaya masa?" Kai ta gyada mata ta tafi kusa da Aunty Farida ta zauna a kasa, Su Mama Shatu kana ganin fuskokinsu kaga bakin ciki da hasadda karara a kwance, bayan kusan minti biyar Abdul ya fito daga dakinsa yana murmushi yace "Har za ku koma Kaka?" Nenne tace "Wallahi kuwa Awdul, ai dama ba zama za mu yi ba, ni dai nayi farin cikin ganin jikata cikin kwanciyar hankali dama duk haka muke so" Shi dai bai ce komai ba, Nenne ta mike tace "Don haka yanxu sai ka maida mu gida kawai" Abdul yace "Toh naga ko abinci bata baku ba ai" Nenne tace "A'a mu muka hanata don duk a koshe mu ke, ruwan ma in ka lura ai bamu sha ba" Shi dai murmushi kawai yayi, a haka Nenne ta kada keyarsu Mama Zubaida da Mama Shatu suka fita daga parlon, Ita dai Khaleesat na biye da su duk jikinta a sanyaye, Aunty Farida ce last din fita a parlorn, tana kallon Khaleesat tayi kasa da murya tace "Za ki ga sako na ajiye maki bayan throw pillow din kujeran da na zauna, kar ki damu kafin in koma lagos zan samu lokaci in zo ni kadai kin ji?" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata, Bayan Abdul ya bude motarsa ya kalli Khaleesat da duk jikinta yayi sanyi ganin su Aunty Farida za su tafi, yace "Mu je sai mu yi dropping din su mu dawo" Nenne dake kokarin shiga bayan mota ta dakata tace "Toh ai babu waje a motar, a ina zaka dora ta Awdul?" Aunty Farida tace "Sai ta shiga gaban motar Nenne ni in koma baya" Nenne tace "A'a babu ruwana wallahi, a irin narka narkan jiki na Shatu da Zubaida mu uku ma ya muka kare a baya balle kin shigo cikinmu Farida? Ko dai a cinyar su zasu dora ki?" Shi dai Abdul murmushi kawai yayi, Khaleesat tace "Toh ni sai in zauna a bayan" A fusace Nenne tace "To ke dole sai kin bi mu ne kamar en matan amare? Kawai don na zo gidanki sai in koma gida da ciwon jiki? ni wallahi in da matsi a mota ma bana shiga, da mun sani da bamu taho da Zubaida ba don duk ita ta cika waje..." Abdul ya kalli Khaleesat yace "Don't worry, ki koma ciki kawai" Hawaye ne ya cika idonta tana kallonsa, Aunty Farida ta yi ma Nenne wani kallo ta shige gaban motar, Nenne ta kyabe baki ta shiga bayan motar tana hararansu Zubaida da su ma duk suka shiga motar kuma babu warce tayi gigin gogan jikin Nenne a cikin motar, Nenne tace "To duk ku sauka Khaleesah ta fara shigowa ta dawo kusa da ni tunda ba wani auki gareta ba, ku ne abun tsoron dama" Babu musu duk suka sake sauka daga motar suka koma gefe, Nenne na kallon Khaleesat tace "Ba sai kin yi kuka ba, shigo ki matso kusa da ni mu ga adadin wajen da zai rage, in ya kama wata sai ta hau adaidaita sahu" Khaleesat ta goge idonta ta karasa ta shiga cikin motar ta matsa kusa da Nenne, space din da ya rage a motar tsaf zai dauke su Mama Zubaida, Nenne ta tabe baki tayi kasa da murya tace "Duk fa wari suke, in Farida ta shigo nan ai jikina za su rakube in ta shakan wari su cuce ni, in de ba kusa dani Faridan zata dawo ba, kuma Zubaida duk ta fi warin, banda akwai turare da AC a motarsa ai da mun ji kunya" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba su Mama Zubaida suka shigo motar Nenne na yatsine yatsine, a haka suka bar gidan. Sai kusan karfe biyar suka isa Mariri, bayan Abdul yayi parking dai dai kofar gidansu Khaleesat Nenne ta bude motar ta sauka tare da Khaleesat, su Mama Zubaida ma duk suka sauka da Aunty Farida suna ma Abdul godiya sannan suka shiga cikin gida, Nenne na gyara gyalenta tace "To Allah yayi maka albarka Awdul mun gode, amma dai zan yi maza in karasa gida akwai sakon Khaleesat da zan dauko in bata tunda Allah ya kawo ku ta tafi da kayanta kawai" Yana zaune driver seat ba tare da ya juya ba yace "Toh Kaka" Tana kallon Khaleesat tace "Mu je ki taho da sakon" Khaleesat bata ce komai ba ta fara bin Nenne zuwa gidanta, bayan sun yi nisa Nenne tace "Ai kinga shegen bai ce bari ya karasa gidan nawa da mu a motar ba, gaba daya baya ganin mutuncin gidana dama" Ita dai Khaleesat tayi kamar bata ji me tace ba, har suka isa gidan Nenne Khaleesat na gaisawa da mutanen anguwan, Nenne tace "Munafukai, sun yi mamakin ganin ki haka ai, kinsan duk ca aka yi kin shiga duniya kin gudu, sai daga baya kuma aka ji kina gidan mijin ki" Murmushi kawai Khaleesat tayi, bayan sun shiga gidan Nenne ta dauko turaren wutan ta saka su a katon leda da kasko biyu sannan suka fito, suna isa kofar gidansu Khaleesat Nenne ta saka ledan a bayan motar Abdul tana cewa "Kaga har mun dawo Awdul, dama turaren wutan ne ba wani abu ba, don haka ku yi maza ku tafi kar Magariba ya tarar da ku a hanya" Yace "To Kaka" Khaleesat na kallonsa tace "Zan shiga in gaida Ummata" Bata jira cewarsa ba ta shiga cikin gidansu ya bi ta da kallo, ko minti uku bata yi da shiga dakin Ummanta ba sai ga Nenne, tana tsaye bakin kofar dakin bayan ta dage labule tace "Abun kuma ba hauka bane ai, taso ki fita yana jiran ki..." Khaleesat ta daga kai tana kallon Nenne, Nenne tace "Ae sai yayi mana kallon mutanen banza marasu hankali, taso nace ki fita kar ki ja mana reni" Umma na kallon Khaleesat tace "Ku je Khaleesat, kin ga yamma tayi" Fuska a daure Khaleesat ta mike ta fita daga dakin, Nenne ta rakata har bakin motar Abdul, tana shiga gaban motar yayi ma Nenne sallama ya ja motarsa ya bar wajen, har suka isa gida ana kiraye kirayen magrib bai ce mata ba, ita ma bata ce masa komai ba, bayan yayi parking ya sauka motar ita ma ta sauka, tana tafiya a hankali ta bi bayansa suka shiga gidan, Kitchen ya shiga direct, har zata wuce dakinta ta tuna sakon da Aunty Farida tace ta bar mata kan kujera, ta karasa inda Aunty Farida ta zauna ta dauke throw pillow din wajen ta dinga kallon Dollars din dake ajiye da wayoyi biyu, daukan 1000 dollars din tayi wanda Jay ne ya bata da zata dawo Nigeria, ta dau wayoyin biyu, daya na Ajay daya na Jay, lkci daya jikinta yayi sanyi hawaye suka cika idonta, muryar Abdul taji a kanta yace "What's that?" Da sauri ta boye hannunta a baya tana kallonsa tsabar yanda ta gigice. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 49 Abdul ya zagayowa ya tsaya gabanta yana kallonta ya mika mata hannu yace "Give me what you are hiding" Sosai gabanta ya fadi tana kallonsa ta kasa cewa komai, tsawan da ya gigitata ya daka mata yana mata wani kallo, lkci daya hawaye ya cika idonta ta mika masa wayoyin da kudin hannunta, amsan su yayi yana kallon su, ta sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa, Calmly yace "Who gave you this?" Kasa dago kanta tayi hawaye na zuba idonta tana jiran jin saukan mari at anytime, juyawa yayi ya bar wajen ya nufi dakinsa yana rike da wayar da dollars din, Khaleesat ta bi sa da kallo har ya shiga dakin, taji kafafuwanta sun kasa daukanta tsabar yanda ta tsorata, da kyar ta karasa ta zauna gefen kujera tana jin bugun zuciyarta na karuwa, tana goge hawayen dake sauka idonta.... Abdul na shiga dakinsa ya zauna gefen gado ya ajiye dollars din yana jujjuya wayoyin hannunsa ganin iri daya ne with different colors, kuma duk a mace suke babu caji, Exactly irin second phone din da yake using ne, ya mike ya tafi yayi plugging din wayar Jay da chargern sa, sannan ya koma ya dau kudaden ya kiraga yaga 1k dollar ne, ya ajiye su saman gadon yana kallonsu, jin za a tada sallah a masallaci ya shiga bathroom dinsa, bayan ya fito zai tafi masallaci ya kulle Bedroom din nasa da makulli, har sannan Khaleesat na zaune parlor ta kasa motsi a inda take zaune, tana ganinsa ta mike tsaye a tsorace tana kallonsa, ko kallonta bai yi ba ya nufi kofa ya fita daga parlon, a sanyaye ta tafi dakinta hawaye na sauka idonta zata je tayi alwala ita ma. Abdul na dawowa masallaci bayan ya bude dakinsa ya shiga ya dau wayar Jay ganin har yayi caji ya kunna kansa, ya cire wayar jikin chargern ya dauko wayar Ajay ya jona, sannan ya koma gefen gado yana duba wayar tunda babu lock jiki, gani yayi ba Sim card a wayar, ya dai ci gaba da dube dubensa, babu inda bai shiga ba a cikin wayar yana bincike but bai ga komai ba don babu any form of Media a wayar, messages ma ko daya bai gani ba, bayan ya shiga Email yaga Business class flight ticket da Jay ya siya mata da zata dawo Nigeria, ya dinga kallon Ticket din for almost 30 seconds, sosai fa yayi mamaki ba kadan ba, fita yayi daga Email din ya shiga Gallery din wayar hoping zai samu hoto a ciki, a nan ne ya ga Hotunan Jay, wanda duk yawanci tare zaka gansu da Ajay, Zooming pic din Jay yayi yana kallonsa with full concentration, sai kuma ya koma kan Ajay shi ma ya dinga kallonsa baya ko kiftawa, at once ya gane da shi ne suka samu Encounter a Amurka, but sai ya ga Ajay looks familiar, where did he know him from? mikewa yayi da sauri ya dauko wayarsa ya shiga Instagram dinsa yayi Searching sunan da yake tunanin ya san sa da shi a Instagram, amma sai yaga account dinsa is locked, komawa yayi ya zauna ya kasa dena kallon hoton Ajay babu ko kiftawa, can ya kara duba hoton Jay yayi Zooming dinsa yana kallo, kawai bai san me yasa yaji yafi jin tsanar Jay ma akan Ajay, mikewa yayi ya dauko wayar Ajay don har ya ɗan yi caji, babu lock a wayar hakan ya sa ya shiga, nan yaga Ticket da aka siya mata from Kano to Lagos, iya shi kadai ya gani a wayar babu hotuna, babu WhatsApp, babu komai, hatta sim card babu a wayar, fita yayi daga dakinsa ya tafi dakin Khaleesat ya sameta tana sallah, tun da taga yanda ya tsaya mata a bakin kofa taki idar da sallan da take yi da wuri kamar me Tuhajjud, muryarsa taji cikin tsawa yace "Idan baki sallame sallan nan da kike yi continuously ba zaki ga abinda zai faru yanxu" Sosai jikinta yayi sanyi, haka nan ta daure ta sallame sallan tana ji kamar bango ya tsage ta fice daga dakin tsabar tsoronsa, duk da yanda gabanta ke faduwa haka ta hade rai taki kallon direction dinsa barin da ta ga both wayar Jay da Ajay a hannunsa, ya karaso cikin dakin yana mata wani kallo cikin daga murya yace "Wayoyin su wanene wannan??" Still taki kallonsa, wani tsawa yayi mata yace "Are you stupid? Are you Mad? Ina maki magana kina kallon wani direction din daban?" Sai a sannan ta kallesa, har sannan fuskarta a daure yak, amma Allah ya gani daurewa kawai take, yace "I am asking you whose phones are this?" A takaice tace "My Housemate and his Brother....." Ya dinga kallonta babu ko kiftawa, she just realized she said her Housemate to him, ta kallesa a sanyaye, ganin kallonta yake yi baya ko kiftawa, ta sauke idonta a hankali tace "I mean...." Ya girgiza kai yace "No, you mean ur Housemate, dama Housemate dinki ne ranan da na je kika min karya? Dama gida daya ku ke tare da wannan katon banzan da na gani?" Gani tayi shiru fa ba nata bane, don shirun nata duka kawai zai ja mata, in ma maganar tayi ba hakan zai hana ya doketa ba in yayi niyya, ta wani hade rai duk da mugun faduwan da gabanta ke yi, a takaice tace "Eh, he is my Housemate, Nancy moved out of the apartment shi ne shi ya shigo, and i have no choice but to live with him, tunda bana son in dinga bothering dinka da Expenses, kuma naga in just few months za mu yi hutu, dama nufina idan mun yi hutu sai in ce maka ka canza min wani apartment din since a sannan ne zaka yi renewing house rent dina" Kallonta kawai Abdul yake yi babu ko kiftawa, ita dai ta kasa kallonsa gabanta na faduwa tana expecting ta ji saukan mari at anytime a cheek dinta, Calmly yace "So, shi ne kike zaune gida daya da shi ku ke rayuwa, ku yi sharing same kitchen, same parlor and same corridor, if coincidentally kin fito daki shi ma ya fito sai ku kusa karo da juna ko? Ki fito babu hijab ya gan ki haka, ki fesa turare ki zo ki wucesa yana jin kamshi, in ma ya kama ki zauna ku yi hira da shi, in kinyi girki ya diba ya ci" Sai a sannan Khaleesat ta kallesa tace "I don't mind if you believe me or not... But shi baya kwana gidan, karatu kawai yake zuwa yi ya tafi don suna da gidansu a Amurka" Abdul ya dinga kallonta, sai a sannan ya tuna abubuwa masu tsadan da ya dinga gani a kitchen sanda yaje, tun daga kan bottle water, cikin nutsuwa yace "Shi ne dalilin da ya sa kika fara min wasu stupid attitude kenan? Kin samu wanda yake siya maki duk abinda kike so a gidan har ma ya ɗebe maki kewa, To bari ki ji, ko duk jikina kunnuwa ne bazan taɓa yarda babu wani intimacy da ya hada ki da shi, ke kika san me kike basa da yasa yake siya maki abubuwa masu tsada yake ajiye maki a kitchen, sannan har ya cire kusan 5000 dollars ya siya maki Business class ticket kawai don ki dawo Nigeria...." Nan da nan hawaye ya cika idon Khaleesat, ta mike tsaye tana kallonsa tace "Ko me zaka fada bazan ce maka ba haka bane, amma put this at the back of ur mind, ba kowa ke da halin son taɓa warce ba muharramarsa ba kamar ka, kuma shi bai dau kudin Business class ticket wata tsiya ba shi yasa ya siya min, akwai difference sosai between you and him" Kallonta Abdul ya dinga yi da mugun mamaki, bata ankara ba sai jin saukan tagwayen mari tayi a fuskarta, ta fashe da kuka tace "Iya mari kawai?? ka kasheni mana ka huta kawai Abdul...." Ya fizgota da karfi yana huci yana kallonta da idanuwansa da suka yi jajir yace "Ni kike comparing da wani ɗan iska matsiyaci can??" Cikin kuka tace "May be if i do that you will change ur terrible ways, he made me realize i am dating a monster because of his kind attitude toward me, babu komai tsakanina da shi amma shi din mutum ne me kirki da sanin darajan ɗan Adam da sanin ya kamata, he always make sure i am fine, baya barina da damuwa komin kankantar sa, kuma ko da kuskure bai taɓa saɓa min ba a duk zaman mu da shi a America, kyawawan halayyarsa da irin yanda yake interacting yasa naji i am fed up with ur attitude, all this made me realize you are enslaving me ba sona kake ba, why not treat me the way he is treating me idan har sona kake da gaske? Bani da daraja da mutunci a idon ka, kullum cikin duka da cin mutunci nake a wajenka tun sanda baka aureni ba, iyayena ma basu da mutunci a wajen ka, to menene yasa baza kayi releasing dina zuwa inda za a ga mutuncina da na iyayena ba kuma a san darajata? Is it my father's fault da kaddarar sa ta zo a yanda take? Ku kan ku kun san bai ci kudin mahaifinka ba, bai salwantar masa da kayansa don son rai ba, ba ku tunanin ko ba ta sanadin mahaifina ba sai kun yi asaran kudaden nan tunda ku ma a kaddarar ku hakan take? Kuma meye zaka daga min hankali a kan su bayan kace baza ka sakeni ba kuma kowa yasan igiyar auren nan a hannun ka yake? Duk cikin rashin lissafin naka ne yasa kake kishi da su bayan ka ri ga ka aureni??" Turata yayi har sai da ta bugu sosai da bango sannan ya juya ya fice daga dakin kamar zai tashi sama. Wajen karfe dayan dare Khaleesat dake kwance taji an bude kofar dakinta, da kyar ta bude idonta da yayi mata nauyi tsabar kuka da ciwon kai, tana ta kwance a yanda take bata juya ba duk da bata ga ya kunna wutan dakin ba, duvet din jikinta ya sauke kasa ya jawota kusa da shi yayi kasa da murya yace "Kinsan da igiyata a kanki kike da effrontery din kawo min maganar wani katon banza can har kike comparing dinsa da ni? What wrong have i commit to you da kike ganin shi yana da halayya masu kyau wanda ni bani da shi" Khaleesat taji zuciyarta na mata wani zafi jin useless question din da yake tambayarta, tayi kamar bacci take taki motsawa, yayi kasa da murya yace "Khaleesat..." Still tayi kamar bata jin sa, duk da idonta a rufe yake she could feel the tears accumulating in her eyes, kiranta ya sake yi a hankali jin bata amsa masa ba ya juyota zuwa jikinsa yana kallonta cikin duhun, ya dora goshinsa kan nata yayi kasa da murya yace "But you know i love you so much Khaleesat, da bana son ki bazan yi wasting shekaru kusan biyar a kanki ba, i gave you the best of everything i can kema kin sani" Bata san sanda ta turasa ba tsabar wani tsanarsa da take ji a rai jin abinda yake cewa, ta mike zaune muryarta na rawa tace "Duk saboda kana sona kake dukana kake marina kamar jaka? Shi ma duk cikin so ne? Plss ka koma ka fahimci menene kalmar so...." Sauka ta fara kokarin yi daga kan gadon tana shesshekan kuka, ya rikota da sauri yaki barinta ta sauka, ta fashe da matsanancin kuka sosai tana jin zuciyarta na mata zafi saboda bakin ciki, ya rungumeta gam a jikinsa, a hankali yace "Kiyi hakuri, amma Allah ya sani ina son ki, in ma baki yarda ba i owe you no explanation tunda Allah shi ya sani, kuma today should be ur first and last warning Khaleesat.... I mean in ur life do not ever ever dare compare me with any stupid guy born of a woman, kar ki sake kawo min zancen wani ɗan iska ko shi wanene a kunne na, sannan bazan yi taking zaman da ku ka yi tare da shi and whosoever da kuma alakar ku personal ba because you are my wife now, duk wannan ya zama pass and shi ne looser, kuma har abada babu wata alaƙa da zai sake hada ki da shi don ubansa har duniya ta nade kuwa, ba wai ban ji zafin alakar da kika yi creating da su a America bane a raina, fadin zafin da naji ma is just an understatement wallahi, amma considering the fact that you are my wife yasa nayi letting bygone to be bygone, so let me keep using that to calm my self kar in masu abinda ke raina...." Wani mugun tsanarsa ne ke karuwa a ran Khaleesat jin kalmomin da ke fitowa bakinsa, wasu hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta tana tausayin kanta da irin monster din da Allah ya bata as miji, kokarin kwace kanta take yi a jikinsa zata sauka daga kan gadon yaki saketa yace "Ohk bokare min za kiyi don ina baki hakuri? But i said i am sorry, and i promise i won't hurt you again, na dena dukan ki...." Ƙin ce masa komai tayi tana kuka a hankali, ya kwantar da ita kirjinsa yana shafa gashinta a hankali yace "Billah ina son ki Khaleesat, duk abinda kika ga ina maki saboda ina son ki ne, but kin ki bani hakkina saboda ke akwai wani plan din a xuciyarki, probably ma su suka koya maki haka" Daga kai Khaleesat tayi ta kallesa tsabar bakin ciki bata san sanda tace "Ai ba kowa ne bashi da aikin yi kamar ka ba" Shiru yayi yana kallonta babu ko kiftawa, ita kanta shirun tayi gabanta na faduwa don bata san sanda kalman ya fito bakinta ba, Instead sai ji tayi yayi kasa da murya kamar me rada yace "Where is the Lubricant?" Sosai gabanta ya fadi jin abinda yace, yana rungume da ita jikinsa ya bude bedside drawer kamar yasan nan din ta ajiye kuwa, ya laluba ya dauko, shesshekan kuka ta fara yi zuciyarta na bugawa, yayi kasa da murya yace "Kinsan tsinuwar Allah kike tara ma kanki kuwa?" Cikin kuka tace "To ai ba ni bace" Yace "To waye?" Muryarta na rawa tace "Wallahi ban sani ba" Cikin kwantar da murya yace "Promise me today will be different plss Baby" Ta kasa cewa komai hawaye masu zafi na sauka idonta ga faduwan da gabanta yake yi, gently ya fara cire kayan baccin jikinta yana kallon kwayar idonta cikin duhun dakin, a wannan dare Abdul bai yi bacci ba tsabar bacin rai, sai dai bai hantareta ba bai zageta ba, bai kuma doketa ba, haka ya mike ya fice kawai ya bar mata dakinta ya koma nasa, ya shiga bandaki ya sakar ma kansa ruwan sanyi duk da mugun sanyin da ake a garin, bayan ya fito ya saka Pajamas dinsa ya kunna karatun qur'ani a wayarsa ya kwanta amma ko rintsawa bai yi ba har asuba. Tunda Khaleesat ta idar da sallan asuba take zaune kan darduma bayan ta gama azkar dinta, gaba daya jikinta a sanyaye yake, zuwa yanxu kam sosai lamarin nan ya fara bata tsoro, ko baccin kirki bata yi ba daren jiya tsabar yanda abun ya tsaya mata a rai, kawai tayi deciding tayi amfani da abubuwan da Nenne ta kawo mata zuwa anjima, sai da gari ya waye sosai sannan ta mike tana tafiya a hankali ta fita daga dakin zuwa parlor, sosai gabanta ya fadi ganinsa zaune a parlon da cup din shayi a gabansa, ta sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa ta tafi ta durkusa ɗan nesa da shi a hankali tace "Ina kwana" Maimakon ya amsa sai ji tayi yace "Meye nake perceiving a cikin kitchen kamar maganin gargajiya?" Khaleesat ta daga kai ta kallesa, shi ma kallonta yake fuskarsa babu yabo babu fallasa, rasa me zata ce masa tayi tana wasa da fingers dinta, a fusace yace "Bakya ji na ne?" Bakinta na rawa da kyar tace "Nenne ce ta kawo min" A takaice yace "Na menene?" Ta sauke idonta tace "Magani ne kawai, dama ta saba bani in dinga amfani da shi a gida" Mikewa yayi yace "Mu je ki bani su" Ta shi tayi kamar munafuka ta nufi kitchen din ya bi bayanta, ita kanta taji kamshin itatuwan da ta shiga kitchen din, ta bude inda ta ajiyesu ta dauko, ya mika hannu, ta karasa ta basa, yace "Ba a min amfani da irin wa ennan abubuwan a gida" Kai kawai ta gyada masa, fuska daure yace "Kin ji me nace maki? Kar ki sake amsa idan ta baki" A hankali tace "Na ji" Juyawa yayi ya fice daga kitchen din ya koma parlor ya zauna, ya ajiyesu nan kasan tiles, tana fitowa daga kitchen yace "Get ready za mu fita, kuma kar ki bata min lokaci" Cikin sanyin murya tace "Toh" Dakinta ta tafi, bayan kusan minti talatin sai ga ta ta fito cikin shiri, dai dai nan shi ma ya fito daga dakinsa rike da wayarsa da car key, yana gaba tana biye da shi suka shigo parlor, ya dau ledan magungunan da Nenne ta kawo mata ya nufi kofar fita daga parlon ita dai tana biye da shi a baya, a booth dinsa ya saka ledan magungunan, sannan ya zaga zuwa driver seat, ita ma ta shiga front seat, bayan ya gama warming motar ya fita daga gidan. A sanyaye Khaleesat ta fito daga Office din Dr Mariya with different thoughts running her mind, ta ɗan juya ta kalli Abdul da ke bayanta shi ma ya fito office din likitan, ƙin kallonta yayi, hakan ya sa ta ci gaba da tafiyarta slowly, sai ga Dr Mariya ita ma ta fito daga Office din zata masu rakiya zuwa parking space, hira suke yi kawai da Abdul suna tafiya a tare, ita dai Khaleesat na can gabansu, har dai suka fita daga reception din hospital din suka karasa parking space, Dr Mariya na kallonta tana murmushi tace "To amarya plss inji labari opposite of this kin ji? There is nothing wrong with you, In kinyi amfani da duk shawararin da na baki komai zai tafi dai dai in sha Allahu, hakuri kawai za ki yi it's always like that dama, Allah Ubangiji ya bada zaman lafiya, in dai na samu lokaci zan zo har gida mu gaisa" a hankali Khaleesat tace "To Nagode Aunty, Allah ya kawo ki lafiya" Dr Mariya na murmushi tace "Ameen" Sai kuma ta kalli Abdul tace "To Barrister ku gaida gida, ina kuma tabbatar maka in sha Allah matsalar ta zo karshe tunda kaga mun dade ina magana da ita, kuma hopefully ta dau duk abinda nace mata" Yace "Thanks for your time Dr" Zagawa yayi ya shiga driver seat, Khaleesat kuma ta shiga front seat, ya tada motar suka bar hospital din, har suka yi nisa bai ce mata komai ba, ita ma dae shiru tayi tana ta tunane tunane, sae da taga unguwan da suka shigo tayi realizing gidansu ya kawosu, bayan yayi parking ya sauka motar, ita ma ta sauka, booth ya tafi ya bude ya ciro ledan da Nenne ta kawo mata, da mamaki tana kallonsa tace "Ina zaka kai wannan?" A takaice yace "Momy zan kai ma, naga tana dealing da irin abubuwan nan, she can use it if she want, ke dai baza kiyi amfani da su ba a gidana" Khaleesat ta marairaice masa tace "Noo pls, ni dai gwara kayi disposing dinsu don Allah" Fuska daure yace "Bazan yi disposing din su ba" Bata san dama haushinta ne fal zuciyarsa ba bayan Dr Mariya ta dubata ta tabbatar masa lafiyarta qlau babu wani abu da yake hindering passage dinsa, everything is normal, kawai hadin kai taki basa, Khaleesat ta sunkuyar da kai a sanyaye bata sake cewa komai ba, ya nufi entrance din gidan nasu, tana tafiya a hankali ta bi bayansa har suka shiga parlorn gidan, da mamaki Momy ke kallonsu tace "A'a, daga ina ku ke da safen nan, sannun ku da zuwa" Abdul ya zauna ya gaisheta, ta amsa tana kallon Khaleesat da ta zauna kasan carpet tana gaisheta, Momy ta amsa da fara'a sosai fuskarta tana welcoming dinta, Momy na kallon Abdul tace "Amma ba daga gida ku ke ba ko" Yace "Eh, daga asibiti mu ke" Da mamaki Momy tace "Asibiti kuma, waye ba lafiya?" A takaice yace "Bata ji dadi bane, amma da sauki" Momy na kallon Khaleesat tana murmushin karfin hali tace "Allah sarki, sannu Mamana, Allah ya kara lafiya" Sai kuma ta kalli Abdul tace "Ko wajen Dr Mariya ku ka je?" Yace "Eh" Mikewa yayi ya ajiye mata ledan magungunan kusa da ita yace "Kakarta ce ta kawo mata wnn jiya, ni kuma kin san bana son irin abubuwan nan na gargajiya shi ne na kawo ko zaki yi amfani da su ke" Momy tayi kuri da ido tana kallon ledan da mamaki, sai kuma ta dauka ta bude da sauri, lkci daya ta saita kanta tana murmushin karfin hali tace "Allah sarki, ai kam nasan halin ka baka san itatuwa, zan ko yi amfani da su dama nawa sun kare tas" Ita dai Khaleesat kasa dago kanta tayi, Momy was shock har cikin ranta amma tayi karfin hali take wayancewa, can ta kalli Khaleesat tace "Amma baki fara amfani da su ba ko" Khaleesat ta girgiza kai ba tare da ta kalli Momy ba tace "A'a jiya ta kawo min banyi amfani da komai ba" Momy tace "To to, hakan yayi" Ta kalli Abdul tace "In dai an samu wasu a dinga kawo min kawai" Mikewa yayi yace "Za mu koma Momy" Momy tace "Da wuri haka? To wai ka koma aiki ne?" Yace "Ban koma ba tukun" Momy tace "Toh shikenan, Allah ya tsare nima in sha Allahu ina nan shigowa in kawo mata turarrukan wuta da na jiki" Shi dai bai ce komai ba ya nufi kofa, Khaleesat ta mike tana yi ma Momy sallama, Momy duk fa a rude take ta gyada mata kai kamar kadangariya tace "To Mamata, sai na shigo, ku gaida gida, maza bi sa ku tafi" Daga haka Khaleesat ta bi bayan Abdul da har ya fita daga parlon, Momy ta dau wayarta har tana tuntube ta shiga dakin dake downstairs ta fara kiran Dr Mariya don family Dr dinsu ce for long, Dr Mariya na dagawa suka gaisa da Momy cikin fara'a, Momy tace "Yanxu Abdul ya zo min da matarsa yace daga asibiti suke, naga duk ba shi da walwala nasan yana da zurfin ciki bazai gaya min ko menene ba, shi ne na kira inji lafiya dai ko Dr? Ko juna biyu gareta? kinsan dama yace bai son haihuwa da wuri, in dai juna biyu ne da ita gwara in yi dubara in dawo da ita wajena don ni dai ina son ganin jikana, kar yaje ya bata wani abu da zai lalata cikin taje ta sha" Dr Mariya tayi dariya sosai, bata boye ma Momy komai ba tayi mata bayanin dalilin zuwansu Asibiti, Momy ta sauke wani irin ajiyar zuciya ba tare da tasan tayi hakan ba, sai kuma ta bige da cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, kinsan yarinya ce fa, duka duka Allah yasa tayi shekara ashirin, har da yarinta abun nata dae" Dr Mariya tace "Wallahi nima haka nace masa don dae in kwantar masa da hankali kar ya dinga jin haushinta, amma shekara ashirin ai ba yarinya bace Hajiya, aka ma er shekara sha biyar aure ta zauna balle er shekara ashirin, ni dai na bata shawarwari Allah ya sa tayi amfani da shi, kar tun yana hakuri da ita hakurinsa ya kare a fara samun matsala gaskiya" Murmushi kawai Momy take tana Allah Allah su gama waya da Mariya ta kira Godiya, daga karshe Momy tace "To Allah ya sa ta dau shawaran naki Dr, kuma zan yi ma yayarsa magana ita ma taje gidan anjima ta kara nutsar da ita in sha Allahu" A haka Momy suka yi sallama da likitan, Momy tayi wani dariya tana girgiza kai sannan ta fara dialing number Godiya, aikin miliyan biyu ai ba wasa bane, sun dade suna waya da Godiya a waya, daga bisanni suka yi sallama, Momy na ta murmushi ita kadai bayan Godiya ta sake jadadda mata Malamin yace lokacin ma da ya dibar masu za ayi sakin baza a kai haka ba, don gab ake da yin sakin cikin kwanan nan kuwa, Meemah da ta shigo dakin ta tarar Momy na waya ta zauna duk tana sauraron conversation dinsu har suka yi sallama tace "To shikenan Momy yanxu haka zai saketa ba mu ci ubanta ba na huce haushin abinda yayi min a kanta?" Momy tace "Ke wa ke ta wani cin ubanta? Ance maki shi ne a gabana sai kace wata yarinya? Ni dai in na samu Abdul ya rabu da ita an gama min komai, kuma hakan kadai ne a gabana yanxu ba shashanci irin naki ba, ke kinsan menene hada iri da talaka kuwa? Ke kiji matsiyaciyar kakarta har ta fara shige shigen malamai tana kawo mata asiri banda Allah yasa Abdul din ya gani, to karyarsu ta sha karya wallahi, cikin kwanan nan zai kora masu ita bayan ya saketa" Mikewa Meemah tayi ta fita daga dakin don kwata kwata ba haka ta so ba ita, so kawai tayi a bar ta tayi ma Khaleesat dukan mutuwa ko zata jin sanyin abinda Abdul yayi mata a kanta. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 50 Bayan Khaleesat sun koma gida tayi wanka sannan ta canza kaya tayi sallan azahar ta fito ta dora lunch a kitchen, tana ta zaune parlor bayan ta gama hada komai na girkin tayi tagumi tayi nisa tunanin da take bata san sanda ya fito daga dakinsa ba, ya karaso parlon yana kallonta yace "Burden din mutane nawa ne a kanki da kike tagumi haka" Juyawa tayi ta kallesa tana gyara zamanta amma bata ce masa komai ba, tunda suka dawo gidan sai yanxu yake mata magana bayan ya gama cika da batsewan sa kenan, Yace "I am asking you" Shiru tayi still bata ce komai ba, ya zauna kan kujeran dake facing dinta yace "Mutane nawa kike ciyarwa da kike tunanin yanda za ki yi?" Bata san sanda tayi murmushi ba tana wasa da fingers dinta, kamar bazata ce komai ba, sai dai a hankali tace "Ba ina son zan yi magana da frnd dita Sophie ba kace bazan yi ba" Yana kallonta yace "Kiyi magana da ita ki ce mata me?" A hankali tace "Babu komai, i am just missing her kawai" Wayarsa dake hannunsa ya cire ma lock sannan ya mika mata yace "Speak to her in my front" Amsan wayar tayi ta shiga contact dinsa ta duba number Safiyyah sannan tayi dialing, yana kallonta yace "Sa a handsfree" Ba musu Khaleesat ta saka kiran a Handsfree, yana fara ring Safiyyah ta daga, a hankali Khaleesat tace "Sophie" Safiyyah tace "Omg Khaleesat? Wallahi I've been expecting your call for so long kawata amma shiruu, Ya Allah, number Abdul din ne wannan?" Khaleesat ta ɗan kalli Abdul da ya kafeta da ido tace "Um, nasa ne" Lkci daya har Safiyyah ta gane wayar a handsfree yake sanin wanene Abdul, a hankali tace "Ohk then, ki gaida min shi sosai pls, but can i come over in gan ki if he will permit that pls?" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "I will speak to him about it" Safiyyah tace "Alright dear, take care of ur self, i will be waiting for ur feedback" Khaleesat tace "In sha Allah" a haka suka yi sallama, safiyyah ta kalli wata aunt dinta dake kusa da ita cike da bakin ciki tace "Wallahi nasan yana gefenta shi yasa ban tofa nawa ba, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Her marriage and Abdul is the worst thing that have happened to me last year, yanxu shikenan ta zama matarsa duk guje mata hakan da na dinga yi, ba irin addu'an da ban sa ta akan Allah ya rabata da Abdul ba, nayi ta mata sha'awan Housemate dinta amma Allah ya riga ya kaddara Abdul ne mijinta, dubi yanda take min magana kina jin muryarta kinsan tana cikin damuwa da matsin rayuwa, gashi karshen watan nan za mu koma school ban kuma ga alamar zai bar ta taci gaba ba" Safiyyah ta fara matsar kwallan bakin ciki, ita dai tana jin babu wanda ya kai ta bakin ciki da auren Khaleesat da Abdul, Abdul ya amshi wayarsa da Khaleesat ke mika masa bayan tayi sallama da Sophie, a hankali tace "Thank you" ajiye wayar yayi yace "Sai hankalin ki ya kwanta yanxu tunda kin yi magana da kanwar Baabarki ko" Cikin sanyin murya tace "Plss ina neman favour din ka barta ta zo wajena don Allah, i am missing her so much" A takaice yace "Baza ta zo ba, in barta ta zo ta ji dadin zuga ki kamar yanda ta saba? you think i don't know saboda tasan wayar a Handsfree yake shi yasa tayi composing words dinta without saying anything silly yanxu, duk ba ita bace ta fara ruining tunanin ki, very stupid girl" Khaleesat dai kallonsa kawai take hawaye cike idon ta, kawai tayi deciding tayi masa maganar abinda ya tsaya mata a rai all this while, hoping Allah zai sa yayi considering din request din nata, cike da karfin hali tace "Amma don Allah Yaya Abdul kar kace bazan koma makaranta ba, we are resuming end of this month kuma kasan wannan shekaran kadai ya rage min plss kar ka bari inyi asaran shekarun da nayi a baya, kayi considering expenses din karatun plss, in kuma zai yiwu kawai a min transfer ba lallai sai can kasar ba..." Hawaye na sauka idonta ta kare maganar tana kallonsa, ya mike yace "You think i am stupid da zan bari ki kara komawa America ki ci gaba da karatu? to ai kai ki can ma da nayi tun farko i deeply regret doing so, nayi da na sanin kai ki karatu America da har ya bude maki ido, kuma tunda ba kudin ki ko kudin wani naki aka kashe ba all this past years ina ruwanki da asaran da za ayi? How is the lost going to affect you da kike nagging akan expenses din? Ina ce kudina ne sai ko kudin mahaifina? So babu ruwanki, na gwammace inyi asaran duk abinda na kashe maki da dai ki koma kasar nan, kuma kika kuskura kika sake kawo min maganar karatu sai nayi mummunan saɓa maki wallahi, kuma bari kiji, common University din kasar nan ma baza ki yi ba balle na wata kasar don babu inda aka ce lallai lallai sai kinyi karatu, at first nayi tunanin kina da kamun kai da nutsuwa ne shi yasa confidently na kai ki America, amma sai kika tafi kina rayuwa da wani ƙaton ɗan iska a gida daya without my knowledge, ya kai ya kawo ko kudi na tura maki sai kiyi kamar baki gani ba for days tunda kin samu ɗan iskan dake siya maki abubuwa, not even one guy, kattin maza har biyu kika je kina mu'amala da su a can, ko wanne kuma ke kika san abinda kike basa da yake kashe maki kudi, so ko da kuskure kika sake kawo min maganar karatu wallahi sai na maki abinda har ki koma ga Allah baza ki manta ba" Yana kai wa nan ya dau wayarsa ya fice daga parlon kamar zai tashi sama, Khaleesat ta bi sa da kallo hawaye masu zafi na sauka idonta. Har dare Khaleesat na dakinta abun duniya ya taru ya mata yawa, wajen karfe sha biyun dare har ta fara bacci taji an bude kofar dakinfa, a hankali ta bude idonta, wutan dakin taga ya kunna sai kuma ya kashe, ita dai tana kwance bata juyo ba, ya karaso inda take kwance ya cire duvet din jikinta ya cire hulan kanta yana shafa dogon gashinta ya kai fuskarsa kusa da nata murya can kasa yace "You gave me Neither lunch Nor dinner today, saboda kinfi karfin a gaya maki gaskiya ko?" Ita dai bata ce komai ba duk da tana jin sa, dagota yayi zaune ya rungumeta yace "Then let me have you since you are not giving me what u cook" Bai jira abinda zata ce ba ya fara kissing dinta, Sosai Abdul ya bata lokaci wajen romancing dinta irin yanda yasan zai gigita ta, in ba ita ba ma babu warce ya taɓa romancing har haka, ko lube din bai dauko ba yau don baya ganin zasu bukace sa ma, a wannan moment din Frustration dinsa yafi na kullum don sosai ya kai zuciyarsa nesa bai kai mata hannu ba, yana wani irin huci ya fixgota da karfi yace "Why are you doing this to me Khaleesat? Why are you frustrating me?" Kasa ce masa komai tayi jikinta na rawa hawaye na zuba idonta, ta gaji da ce masa ita bata san abinda ke faruwa ba, cikin daga murya jikinsa na rawa yace "Ki bani amsa? Me na maki kike wahal dani kike cutata haka?" Khaleesat dai ta kasa ce masa komai jikinta na rawa don tsoron magana ma take ya gaggaura mata mari, yana wani irin huci ya turata yace "Ki jika abun ki ki sha" Yana fadin haka ya sauka daga saman gadon ya saka Pajamas dinsa ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, Khaleesat dai ta jawo duvet ta rufe jikinta har sannan zuciyarta na bugawa ta fashe da matsanancin kuka, bayan kusan minti goma taji fitar motarsa a gidan gaba daya. Da yammacin ranan Momy na parlonta da Godiya sai ga Abdul ya shigo kamar an hankado sa, Momy na kallonsa tace "A'a Babana, sannu da zuwa" Juyawa yayi ya fice daga parlon ganin Godiya, Momy ta ɗan zaro ido tana kallon Godiya sai kuma ta mike da sauri ta tafi kusa da kofar ta bude tana leka corridor taga bangaren Abbansa ya tafi, ita ta dade bata gansa cikin irin wannan yanayin ba ma, ta kulle kofar ta dawo tana kallon godiya tace "Anya Godiya Malamin nan ba maye bane kuwa, kin ga dama yace Abdul zai zo yau gashi kuma ya zo din kamar an jefosa" Godiya tayi wani dariya tace "Ke ma dai wallahi sai kace yau Danger ya taɓa maki aiki da zaki yi mamaki? Yanxu dai sai ki tashi kije ki dora masa girkin da ya fi so da maganin" Momy tace "Ikon Allah, in dai kana da kudin ka zaka ga aiki da cikawa kawai, yanxu ki dubi yanda ya shigo mana a firgice kamar mara lafiya" Godiya tace "Ina kuwa lafiya dama an hanasa angwancewa da amarya, sai kace baki san maza in suka kwallafa rai kan wannan lamari ba" Suka kwashe da dariya gaba daya har da kyakyatawa, Momy tace "Toh yanxu zan tura cikon aikin nan na karshe, yaushe zaki koma wajensa mu je tare in masa godiya" Godiya tace "Nan da kwana uku in sha Allah, kin ga bari in tashi in tafi mai gidana na hanyar dawowa yau" Momy tace "Haka fa kika ce, toh shikenan sai mun yi waya dai kawai" A haka Momy ta raka Godiya har gun motar ta sannan ta dawo cikin gidan ranta fari ƙal, bangaren Alhaji ta nufa ta tarar da Abdul kwance a parlor idonsa a lumshe, zaunawa tayi gefensa tana kallonsa cikin kwantar da murya tace "Babana baka da lafiya ne?" A takaice yace "Hutawa nake yi Momy, i need privacy pls" Momy tace "Toh shikenan, bari in sa a daura maka favorite din ka, ina Mamata fa?" Shiru yayi yaki ba Momy amsa, Momy ta mike ta nufi kofa ta fita daga dakin ta kullo kofar, sai a sannan tayi wani murmushi ta koma bangarenta zata dau maganin da Godiya ta kawo mata wanda zata zuba a cikin girkin abinda Abdul ya fi so, sai da ta kori mai aikinta can compound sannan ta fara girka masa Pounded yam da Vegetable soup, cikin miyan ta zazzage duk maganin da kyauta ta kawo har kala uku, wajen karfe bakwai ta gama ta dau abincin ta kai masa dining table ta ajiye, dama iya cin sa kawai ta girka wato malmala daya kuma ba babba ba, miyar ma ɗan tsut yanda zai cinye gaba daya, sai bayan isha Abdul ya ci abincin da Momy tayi masa, ya bar ma mai aiki ta kwashe sannan ya wuce sama zuwa dakinsa, Momy ta fito dakin Meemah kenan ta bi sa da kallo har ya shiga dakinsa sannan ta bi bayansa, tana shiga dakin tace "Wai lafiya Babana? Ko dai akwai wani matsalan da kake boye min ne" a takaice yace "Ba komai, zan shiga wanka" Yana fadin haka ya fara cire kayan jikinsa, Momy tace "To ka ci abincin?" Yace "Na ci" Momy na murmushi tace "You like it?" Yace "Miyan yayi dadi, but it's little" Tana murmushi tace "To maa sha Allah, amma ai ya isheka dai" Yace "Ya isa" Tace "Toh je kayi wankan ka nima bari inje in ci abinci" Fita tayi daga dakin ya shiga bandaki, Momy na zaune parlonta tana cin farfesu dake cike cikin bowl din hannunta Abdul ya shigo, kallonsa tayi ganin yanda ya shirya sai zuba azababben kamshi yake, tace "Har zaka tafi Babana" Yace "Eh, sai da safe" Tace "To ko in zuba maka farfesun ka kai ma Mamata" A takaice yace "A'a ni ba gida zan kwana ba" Momy tayi murmushi tace "To Allah ya tsare Babana" Yace "Ameen" Daga haka ya fita daga gidan. The next 10 days a gidan Abdul was a living hell for Khaleesat, gaba daya Abdul ya sauya mata a gidan ya dawo kamar wani monster, dukanta da yace ya dena sai dai bai samu slightest opportunity din yin hakan ba, kawai ya maida ta punching bag dinsa a gidan barin in ya zo gareta bai samu biyan bukata ba, kuma bai fasa zuwa mata da bukatar tasa ba amma as usual sai dai kawai ya doketa ya fita bai cimma burinsa ba, kwata kwata ya dena cin abincin gidan, ya dena kwana sai sanda ya ga dama, duk wani ingredients din girki ya dena siyowa sai dai tayi ta cin indomie, hatta bottle water ma da ya kare yaki siyowa, kuma ko Satchet water yaki siya ya ajiye, sai dai ta sha ruwan pampo, gaba daya Khaleesat ta fita hayyacinta a gidan ta dawo kamar ba Khaleesat ba, ga karyewa da gashinta ya dinga yi sosai saboda tsananin damuwa, kana ganinta kasan tana cikin jarabawan rayuwa, bata da aiki sai kuka sai kuma addu'a da sallan dare, gaba daya ta maida duk lamarinta ga Allah, kullum haka take kwana ta tashi da zazzabi amma ina taga fuskar ce masa bata da lafiya, sai dai tayi ta daurewa a haka, in ma ta gaya masa don ya zagi iyayenta ba komai bane a wajensa, in zazzaɓin ya rufeta sai dai ta kwanta har sai sanda zata ji dama dama sannan ta daure ta tashi. Ranan Friday tana dakinta a kwance ko breakfast bata yi ba har kusan karfe sha biyu da rabi, zuwa yanxu ta gaji da cin indomie da ma tana da dakakken yaji sai ta dinga yin ko shinkafa da mai da yaji ne amma babu, indomie duk ya fita a kanta bata iya ci ko ta dafa, gashi haka take dafasa babu yaji balle albasa, bude kofar dakin nata yayi ta mike zaune da sauri tana kallonsa gabanta na faduwa, kamar zai fasa mata dodon kunne taji yace "Ina Cufflinks din da na bari a parlor shekaranjiya?" Sauka tayi daga kan gado, ita dai ta gyara parlon ta goge ko ina jiya da yau amma bata ga wani Cufflinks dinsa ba, a hankali tace "Toh bari in duba a parlon" Wani mugun kallo yake mata hakan yasa ta raɓa tabi ta gefensa ta fita daga dakin zuciyarta na bugawa ta tafi parlor tana dudduba Cufflinks din, da alama masallaci zai je don yin sallan juma'a, babu ta yanda za ace iya Cufflinks din da yake tambayarta yake da shi a gidan, amma sbda neman hanyar da zai musguna mata yake shi yasa zai saka ta gaba ta fito da abinda bata gani ba, kuma rabonsa da gidan tun shekaranjiyan, tana cikin dube dube a parlon shi kuma yana tsaye fuskarsa a murtuke alamar he is loosing his patient aka bude kofar parlon, Momy ce ta shigo da Cousin sis din Alhaji Musa, warce suke kira da Ummu, Yau kwanan Ummu uku a Nigeria daga Dubai inda take aure da yaranta duk a can, kuma a yau zata koma Dubai shi ne ta sa a kawota ta ga matar Abdul kafin a kai ta airport, duk da Abdul yaje ya gaisheta san da ta zo, Khaleesat da duk a rude take ta kalli Abdul a hankali tace "Wallahi ban gansa ba da nake gyaran parlorn jiya da yau, kilan ka sha'afa ko a daki ka bar su ne ka manta" Bata rufe baki ba ya sauke mata wani gigitattcen mari yana huci ya fixgota yace "Ni zaki gaya ma a daki na bar su?" Ta dafe kuncinta hawaye cike idonta tana girgiza masa kai, nan da nan fuskarta yayi ja, ko minding uwar sa da Cousin sis din Babansa da suka shigo parlon bai yi ba, duk suka yi cirko cirko baki bude suna kallon ikon Allah, cikin tsawa yace "Baza ki fito min da shi ba sai na maki dukan tsiya a nan?" Tana shesshekan kuka tace "Nace maka ni ban ga wani links din ka ba wallahi...." Bata rufe baki ba ya sake sauke mata wani wawan marin, Momy da taji ranta yayi fari tass cikin kwantar da murya tace "Subhanallahi, Babana ka bi a hankali, hakuri ake Babana" Ummu ta jefar da handbag dinta kan kujera ta nufesa cikin bacin rai tace "Abdallah?? kana hauka ne kake marin mace haka don uban ka?" Momy ta wani hade rai tana kallon Ummu, Abdul yaki ko kallon Ummu dake masa magana, ya wani haure Khaleesat a mugun fusace har sai da ta fadi kasa, Wani Mari Ummu ta sauke masa a fuska, cikin fushi tace "Ashe kai jahili ne shashasha ban sani ba?" Juyowa yayi yana kallon Ummu da mamaki baya ko kiftawa, Momy ta dinga huci tana kallon Ummu ita ma, nan da nan idanuwanta suka kankance don bacin dai, tunda ta haifi Abdul bata taɓa marinsa ba haka ma ubansa sai gashi yau an maresa a gabanta, Abdul dake kallon Ummu kamar me counting din words dinsa yace "Ummu akan wannan jakar yarinyar kika mareni??" Ummu tace "Na mare ka din, zaka rama ne? Wawa kawai mahaukaci ka saka yarinya karama haka a gaba kana duka? Tarbiyar da aka maka kenan? In na san abinda zan zo in tarar a gidan ka kenan uban me zai kawo ni?" Abdul da idanuwansa suka sauya launi ya kalli Khaleesat yace "Ki je... na sake ki" Yana fadin haka ya dau makullin motarsa ya fice daga parlon kamar zai tashi sama, Khaleesat ta bi sa da kallo babu ko kiftawa kamar bata fahimci abinda yace ba, Momy ta sauke wani bayanannen ajiyar zuciya tace "To Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah" Sai kuma ta kalli Ummu tace "Ke kuma Muhusina kin ci darajar Musa banda haka da babu uban da zai hanani rama ma ɗa na marin da kika masa don tunda na haifesa ban taɓa marinsa ba haka ma ubansa, kuma Abdul yayi min dai dai hukuncin da ya dauka, dama me ake da auren er gidan talakawa er gidan matsiyata? Ai ba class din mu bace ita, kuma duk bama goyon bayan wannan tsinannen auren, kawai irin wannan rana muke ta jira gashi Allah ya kawo mu cikin ruwan sanyi, Alhamdulillah Allah na gode maka, Allah na gode maka, yau zan yi bacci cikin farin ciki da kwanciyar hankali burina ya cika, effort dina kuma bai tashi a banza ba" Momy na kai wa nan ta nufi kofa tana tafiya gansan gansan farin ciki fal a ranta mara misaltuwa tana murmushi ta bude kofar parlon, Khaleesat ta bi Momy da kallo with shock ko kwakkwaran motsi ta kasa tsabar mamaki, maganganun Momy suka dinga yawo a kanta kamar a mafarki, Ummu ta zauna gefen kujera ta dafe kanta tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Sai a sannan Khaleesat taji hawaye masu zafi na silalowa fuskarta, ta mike tana tafiya a hankali ta tafi daki ta dauko hijab dinta har kasa ta fito.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 51 Khaleesat na fitowa parlor suka hada ido da Ummu dake kokarin kiran Alhaji Musa da wayarta cikin bacin rai, sunkuyar da kai Khaleesat tayi tana goge hawayen dake ta zuba idonta, Ummu tace "Zo ki zauna tukunna diyata" Khaleesat tayi shiru bata ce mata komai ba don har cikin ranta bata ji zata iya zama a parlon ba kamar yanda Ummu ta umarceta, amma kar tayi disrespecting matar duba da tsaya mata da tayi sanda Abdul ke ci mata mutunci yasa kawai ta duka kasan carpet kanta a kasa, Sau uku Ummu na kiran wayar Dad din Abdul, daga karshe ya daga kiran, cikin fushi ta fara koro masa abubuwan da ta zo gidan Abdul ta tarar da kuma abinda Abdul ya aikata daga karshe, Alhaji Musa dake ta sauraronta ya jira har ta gama, sannan yayi gyaran murya yace "Ai ina ganin Muhusina wannan ba issue bane da zaki shigar da kanki farat daya, ke da ba ma a kasar kike ba zuwa kawai kika yi, i don't think it's proper kiyi involving kanki sama ta ka, it's not done that way, alright? kuma tunda kika ga ya saketa definitely yana ganin hakan shi ne dai dai so meye zaki damu kanki, ko mu iyayensa we are not in the rightful place to question his act, okay? decision dinsa ne, so just stay out of what u know nothing about Muhusina, ba naji kin ce flight din karfe biyu gare ki ba? Ko kin daga tafiyar taki ne?" Kasa cewa komai Ummu tayi tsabar mamaki, kana ganinta kasan she is speechless, ita dai Khaleesat kanta na kasa don ba handsfree Ummu ta saka wayar ba balle ta san abinda Dad din Abdul ke cewa, a hankali Ummu tayi ending call din ta ajiye wayar a gefen kujera don ba ma ta da amsan da zata ba ɗan uwan nata, sosai jikinta yayi sanyi, yanxu dama Family din Alhaji Musa basu canza ba daga yanda ta san su tun tale tale, don ita sai tayi shekara aru aru ba a ganta a Nigeria ba in ba muhimmin abu bane ya kawo ta, Momy ce ta bude kofar parlon fuskarta a murtuke, ashe all this while tana kofar gida tana jiran ganin Khaleesat ta fito ta bar gidan amma shiru shiru bata ga ta fito ba, Momy na kallon Khaleesat tace "In dai ba gidan ubanki bane ko na uwarki nan din tunda har ya furta ya sake ki ai kya fito ki kama gabanki, ko zaman ubanki kike yi har yanxu? Da wani abinda kika zo gidan da shi ne kika yi waya a zo da mota a kwashe maki ko yaya?" Ummu ta kalli Momy tana girgiza kai cike da takaici tace "Ki ji tsoron Allah Hajiya, ki ji tsoron haduwar ki da Allah, ke ma fa kina da yaran nan mata...." A mugun fusace Momy ta karaso cikin parlon ta dakatar da ita tana nunata da ɗan yatsa tace "Kin ga wannan family issue ne ki cire bakin ki a abinda bai shafeki ba Muhusina don ke bare ce a wannan ɓangaren, kuma ba ke kika haifar min Abdul din ba da kike neman cusa kai abinda ya shafi rayuwarsa, who are you to even interfere? Ko Musa kin zata ya isa ya hana Abdul abinda yayi niyyar zai yi ne? To wallahi ki cire bakin ki da idonki akan abinda ya shafi zuri'ata, 'ya ya mata kuma dama ko wani shege ya haifa ai, meye a ciki" Momy na kai wa nan ta kalli Khaleesat cikin daga murya tace "Baza ki tashi ki san inda dare yayi maki ba ko sai na kira su Meemah sun fitar min da ke daga gidan nan??" Mikewa Khaleesat tayi bata bari sun hada ido da Momy ba ta nufi kofa tana tafiya a hankali, Ummu ta kasa cewa komai tana kallon Momy tana girgiza kai, sai da Khaleesat ta fita daga compound din gidan gaba daya sannan ta fara share hawayen dake sauka idonta, tunanin yanda zata koma gida bata da ko sisi ta fara yi, tafiya me nisa tayi har ta iso titin da zata samu abun hawa, daga karshe bayan jiran kusan minti sha biyar ta samu wani adaidaita sahun da zai kai ta Mariri a dubu biyu da dari biyar, in taje gida sai ta basa kudinsa, har Khaleesat ta isa gida hawaye ya ki tsaya mata a ido, ita kanta bata san yanda take ji a ranta ba game da abinda Abdul yayi mata, farin ciki take ko akasin haka har sannan ta kasa ganewa a zuciyarta, but she was deeply hurt and pained, daurewa kawai take kar ta fashe da kuka a adaidaita sahun, bayan ya tsaya dai dai kofar gidansu ta sauka tace "Za a kawo maka kudin yanxu, nagode" Daga haka ta shiga cikin gidansu, a tsakar gida ta tarar da kishiyoyin Ummanta sun gama abincin siyarwansu na yamma yara za su fita da shi talla, ta gaishesu ba tare da ta bari sun hada ido da su ba direct ta nufi dakin Ummanta, duk suka bi ta da kallo, Aunty Farida da fitowar ta daga bandaki kenan zata yi alwala don lokacin sallan La'asar yayi ta ajiye butan hannunta ta bi Khaleesat da kallo ita ma duk da Khaleesat bata ganta ba, Khaleesat na shiga dakin Ummanta ta fada jikinta ta fashe da kuka a hankali, Kasa cewa komai Umma tayi tana kallonta da mamaki, sai ga Aunty Farida ta shigo dakin ita ma, sosai gabanta ya fadi ta tsaya nan bakin kofa tana kallon Khaleesat, da kyar Umma ta dago kanta cike da karfin hali tace "Me ya faru?" Khaleesat ta kasa cewa komai tana kuka sosai, Umma da nan da nan ita ma hawaye ya cika idonta ta rungumeta bata sake ce mata komai ba ta bar ta tayi kukan me isarta, cikin sanyin jiki Aunty Farida ta karasa cikin dakin ta zauna gefen katifa tayi shiru, Umma ta goge idonta tana patting Khaleesat a baya a hankali trying to calm her amma bata hanata kukan da take ba, sun fi minti biyar a haka sai ga Mama Zubaida ta dage labulen dakin tace "To ɗan sahu dai na ta jira a mika masa kudinsa a kofar gida" Magana take amma idonta na kan Khaleesat da Umma, tsabar gulma yaron makota me adaidaita sahun ya aiko cikin gidan amma tayi karaf ta mike bayan yaron ya sanar masu ta nufo dakin Umma taki barin yaron ya karasa, don tun shigowar Khaleesat suka baza kunnuwa ko za su ji wata magana amma shiruu basu ji ko tari ba a dakin Umma, Aunty Farida ta dau handbag dinta ta fita daga dakin ta sake labulen daga hannun Mama Zubaida dake rike da shi, sannan ta fita zuwa gun mai adaidaita sahun, sai a sannan Umma ta iya daga kan Khaleesat, suna hada ido Khaleesat ta sauke jajayen idanuwanta, Umma tayi karfin halin cewa "Me ya faru Jiddah?" Khaleesat ta sauke idonta wasu hawayen na zuba idonta tace "Yace ya sakeni" Hawayen dake makale idon Umma ya zubo tana kallon Khaleesat babu ko kiftawa, Khaleesat ta rufe fuskarta jikin Umma ta fara wani sabon kukan, Umma ta rungumeta sosai, cikin rawan murya tace "Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi a gare ki, kiyi hakuri kin ji?" Kai kawai Khaleesat ke gyada mata tana shesshekan kuka, a haka Aunty Farida ta dawo dakin ta same su, Aunty Farida ta zauna gefen Umma tana kallonsu, Da kyar Umma ta kalleta tace "Wai sakin ta yayi" Ƙasa cewa komai Aunty Farida tayi tsabar yanda ta girgiza, ta dinga kallon Umma babu ko kiftawa, nan da nan ita ma hawaye ya cika idonta, after a while ta goge hawayen dake zuba idonta ta fita ta dau buta tayi alwalanta ta dawo ta tada sallah, Umma ta dago Khaleesat da tayi shiru a jikinta, sai taga bacci take, Khaleesat ta bude ido a hankali, Umma tace "Kin yi sallah ne?" Girgiza mata kai Khaleesat tayi, Umma tace "Ki je kiyi alwala kiyi sallah" Khaleesat ta mike tana tafiya a hankali ta fita daga dakin. Khaleesat na idar da sallah Aunty Farida na kallonta tace "A zubo maki abinci?" Khaleesat ta girgiza mata kai cikin sanyin murya tace "Na koshi" Daga haka ta mike ta hau saman gadon Ummanta ta kwanta, nan da nan bacci me nauyi ya dauketa, daga Umma har Aunty Farida babu wanda ya iya cewa komai a dakin, suna ta zaune har kusan karfe shidda, ita dai Aunty Farida tana rike da Al-qur'ani tana karatu silently a ranta, su Islam suka dawo hadda wanda suke zuwa har ranan friday, Umma ta sa su je su hura gawayi su dora girki, muryar Nenne suka ji a tsakar gida tana cewa "To Zubaida sai ki dau na annabawa don kin tafka asara lafiyayye yau, almajirai na mugun wasa suka hamɓare Suwaiba tallan da kika dora mata ya kife a kasa, su kuma suka tsere, sanin azaban da zaki mata ta taho ta sameni tana kuka kamar ranta zai fita, yanzu haka tana can gidana nace tayi zamanta, ga robobin tallan da faranti nasa an kwaso maki kayanki, ko roba daya bata siyar ba suka hambare farantin" Mama Shatu ta saki salati tana kallon Mama Zubaida da ta nemi waje ta zauna jin abinda Nenne ke cewa, Nenne ta kwashe da dariya har da kyakyatawa tace "Yaran layi kuwa duk suka wawushe abincin da ya zube a kasa suka loda ma cikin su" Daga haka ta nufi dakin Umma ta dage labulen tace "Zahra'u kina da er kuka ko kubewa ki tsam inje in ƙada miya" Umma bata yarda sun hada ido da Nenne ba tace "To bari in duba maki, Ina wuni" Nenne tayi mitsi mitsi da ido tace "Wacece wancan kuma a kwance kan katifarki?" Umma dai bata ce komai ba ta tashi zata dauko ma Nenne kubewa busasshe, Aunty Farida ta gaida Nenne ba tare da ta kalleta ba, Nenne na kallon Khaleesat tace "Wai wa nake gani kamar Khaleesah a kwance?" Aunty Farida ta ajiye Qur'anin hannunta still bata kalli Nenne ba tace "Ita ce" Nenne ta shigo dakin tace "Wato ni dai shikenan kun nuna mata banda matsayi da har zata shigo unguwan nan ta karasa gidana ta gaisheni ko? In ma bata je ta gaisheni don Allah ba ai sai tayi don ubanta Ali tunda ni na haifesa har ya haifeta" Daga Umma har Aunty Farida babu wanda yace ma Nenne komai, Nenne tace "Mijin ne ya kawota? Shi ma ai shegen ne tunda ba karasawa yake yi gidana ya gaisheni ba, banda kaddara a ina za mu san sa har mu aura masa Khaleesat mutumin da baya ganin mutuncin mu, kana masa magana yana amsa maka cikin gadara da yanga wai shi ɗan Alhaji Musa, waye bai san satan da ubansa ya zabga a gwamnati ba kafin ya koma kasuwanci, ko don muna kauda kai?" A takaice Aunty Farida tace "To sakin ta yayi..." Nenne ta juya ta kalli Aunty Farida na en sakwanni, can tace "Ban ji me kika ce ba Parida?" Aunty Farida da har hawaye ya kawo idonta tace "Sakinta Abdul din yayi" Nenne ta kasa motsi a inda take tsaye, a hankali tace "Sakin aure ko sakin me?" Aunty Farida dai bata tanka ta ba, ita dai Khaleesat na kwance tayi backing din Nenne bayan surutunta ya tasheta daga baccin da take, Nenne ta saki wani salati muryarta na rawa tace "Wato dai ɗan nawa ne ba a son a ga ya zauna lafiya a gidan duniya kamar yanda kowa yake zaune" Fita tayi ta koma tsakar gida ta rushe da kuka sosai tace "Allah ya isa tsakanina da Zahra'u da er ta, babban burin su a duniya su ga Ali ya tagayyara, babban burinsu su ga Ali cikin mawuyacin hali cikin tashin hankali, banda haka ko dukanta da zaginta Awdul ke yi a gidan bazata hakura ta zauna ba albarkacin ubanta? Shi ne har zata amshi sakin da yayi mata hannu bibbiyu ta dawo mana gidan nan domin shari'arsu da Ali ya dawo sabo?" Mama Zubaida da Mama Shatu tuni suka mike tsaye jin abinda Nenne ke cewa, cikin kuka Nenne tace "Ban taɓa ganin er da burinta taga ubanta a walakance ba, kun ga ai ta dawo taga yanda za ayi da uban nata ko furson din za a mayar da shi ko hukuncin rataya za a yanke masa, ni dai na shiga uku na lalace, Allah ya hada Ali da mata da 'ya yan da basa tausayinsa kuma su za su yi ajalinsa, yanxu in Khaleesat er arziki ce da yace ya saketa ba sai tace babu inda zata je ba tunda bautar Allah take??" Malam Ali ne ya shigo gidan da er taliyar Hausa da ya siyo cikin Bacco bag, Nenne na ganinsa ta rushe da sabon kuka tace "Wallahi ta kashe auren ta dawo taga yanda za su yi da kai Ali" Malam Ali ya tsaya yana kallon Nenne, Nenne na fyace majina tace "Ga ta can dakin uwar a kwance tana jiran taga da wace motar za a zo a kwashe ka, dama wallahi tun da muka je gidan da parida nasan za a samu babban matsala don babu alkhairi a ran Parida, kuma in bata yi hankali ba daga ita har Zahra'un sai dai su koma kasar su, duk wanda baya son kwanciyar hankalin ɗa na to kwanciyar hankalina ne baya so wallahi" Malam Ali dai ya nemi tabarma ya zauna ya kasa cewa komai, Mama Zubaida tace "Ikon Allah, kuma abinda ya faru kenan ni Zubaida? Aure wata daya da yan kwanaki amma har an yi saki? Yanxu zawarawa har biyu garemu a gidan nan kenan?" A fusace Nenne tace "Ta zauna tayi ma uban wa zawarci a gida? Ai ko taki ko ta so sai naje na ba Awdul hakuri ya maidata dakinta don kaf zuri'armu babu wanda ya taɓa zawarci sai in mutuwa mijin yayi, to ko bakin halinta bai isa ya sa ya korota ba bai shirya ba, Khaleesah ce duk wani mummunan bakar maganar da ya zo bakinta take yaɓa ma mutum, ko kuma in ka gaya mata abinda bai gamsheta ba tayi maka wani kallon walakanci da kaskanci da tula tulan idanuwanta, wani lkcn kana mata magana tayi maka banza wannan duk mun san halinta ne ba wai sharri ba, ga nukurci kamar er sarkin kutare, to ai ba ko wani namiji bane zai dau wannan, don haka zan je in basa hakuri ya dubi girman Allah ya maidata dakinta..." Mama Shatu tace "Toh ko samun sa kika yi ai sai yayi niyya zai maidata Nenne, in zai iya ai bazai fara sakin ta ba" Wani zagi Nenne ta kundumo mata a fusace, dai dai nan aka rafka sallama a kofar gida, Malam Ali ya mike tsaye yana kallon hanyar fita gidan, Nenne tayi tsit zufa na keto mata, can ta fara kuka a hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, Zahra'u dai bata zo mana pamily da alkhairi ba, kun ga har an zo tafiya da shi" Mama Zubaida ce ta yafa gyale ta nufi hanyar fita daga compound din, wani mota taga anyi parking a kofar gidan, mutumin dake tsaye kusa da motan ya nufota yana kallonta, Mama Zubaida ta gaishesa har da risinawarta, ya amsa yace "Mai gidan na ciki kuwa?" Mama Zubaida tace "To Allah ya sa dai lafiya Malam" Mutumin yace "Eh to, ni Dreban Alhaji Musa ne, an bani sako ne in kawo ma mai gidan" Mama Zubaida tace "To ni mai dakinsa ce, ni ce uwar gidansa, ko zan iya karba in mika masa, don baya jin dadi ne" Mutumin yace "To ba damuwa" Hannu yasa a aljihu ya ciro Envelope ya mika mata, ta amsa yayi mata sallama ya koma zai shiga mota, Mama Zubaida ta koma gidan tana juya takardan ita kanta sai da gabanta ya fadi don irin wannan in an kawo ai sammaci yake nufi, Nenne na ganin Envelope din hannun Mama Zubaida ta rushe da matsanancin kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, shi kenan Ali a haka zai kare kenan ni Zainabu? wani takardan kotun aka sake kawo masa kenan?" Malam Ali ya amshi Envelope din hannun Mama Zubaida ya yage ya ciro takardan ciki ya warware, "Ni Abdallah Musa, na saki er ku Hauwa saki daya, biyu, uku" content din dake jikin takardan kenan, Shatu ta amshi takardan hannunsa tun da tayi karatun primary, tana duba takardan ta karanto abinda ke jiki amma fa da kyar tana in ina, Nenne ta tsaida kukan da take bayan taji Shatu ta karanto rubutun jikin takardan tace "Ji tsinanne la'ananne matsiyaci? saki har uku kamar warce ta kashe ubansa ko uwarsa? To Allah Ubangiji ya tsine masa albarka, dama banda kaddara uban me Khaleesat zata ci da ɗan barawon Gwamnati? ubansa barawon gwamnati shi kuma ɗan daba, Ai mu wannan sakin abun farin ciki ne a gare mu gaba daya tunda ba na'am muka yi da auren ba, kuma ko yau Khaleesat ta fita sai ta samu mijin nuna ma tsara da ya fi sa komai wallahi, bakin cikinmu daya zawara da ya maida ta, dama kullum da fargaban aurenta da shegen nake don har raina bana son sa babu yanda na iya ne kawai, banda jarabawa wasu iyayen kwarai ne za su dau er su su ba tsinanne irin Awdul? Khaleesah sai dai kawai tayi hakuri don cuta kam Ali ya cuceta, ya cuci Rayuwarta, don duk shi ya ja mata wannan masifa, da suka ce maka er ka suke so bayan an fito da kai furson in kai uba na gari ne sai ka cije kace sam baka yarda ba sai dai a maida ka furson din ka mutu a can, amma saboda tsoron azaban duniya ba na lahira ba ka zabi ka sadaukar da erka don samu encin kanka, to gashi nan bayan ya rabata da budurcinta ya sako mana ita, dama auren sha'awa kawai yayi da ita, Allah ya isa bamu yafe masa ba wallahi" Nenne na kai wa nan ta fashe da kuka ta jawo kujera er tsugunno ta zauna tana rera kuka sai kuma tace "To yanxu ko zuwa za muyi mu basu hakuri ya dubi girman Allah ya maidata tunda malamai sun ce saki uku a madadin daya yake" Wajen karfe goma na dare Aunty Farida ta zauna gefen Khaleesat dake zaune da cup din kunun da Umma ta dama mata tunda ta kasa cin abinci, Aunty Farida tace "Baki shanye kunun bane?" Khaleesat ta dau cup din ta ci gaba da shan kunun a hankali, Aunty Farida tayi shiru bata sake cewa komai ba tana kallon buhun abubuwan da ita da Umma suka hada zata kai ma Khaleesat gobe, don da gobe zata je wajenta, tun daga dakakken yaji, kubewa busasshe, kuka, kanwa, su citta da kanumfari, gyadar miyar, har da garin danwake da sauran abubuwa da yawa duk su ne a cikin buhun, ga turaren wuta da suka siya mata masu kyau, Aunty Farida ta sauke boyayyen ajiyar zuciya ta kalli Khaleesat da ta kasa shanye kunun hannunta, a hankali ta jawota jikinta, soothingly tace "Kiyi hakuri Daughter, Allah yasa hakan shi ne mafi alkhairi gare mu baki daya, kar ki saka komai a ranki kin ji?" Khaleesat ta gyada mata kai, Aunty Farida bata sake ce mata komai ba don ita bata ma son ta tambayi abinda ya hadasu don mayar da maganar bacin rai kawai zai kara masu, Ita dai Umma na zaune kan darduma Islam na bacci a jikinta, Maman Salame ce tayi sallama ta shigo dakin tana kallon Umma tace "Wani labari ne wannan nake ji a garin nan Zahra'u?" Umma dai tayi shiru tana kallonta, Maman Salame ta zauna kan tabarma tana kallon Aunty Farida da Khaleesat dake gefenta tace "Farida" Aunty Farida ta ɗan yi murmushi tace "Ina yini Maman Salame" Maman Salame tace "Wai da gaske ne? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Aunty Farida tace "A ina kika ji Maman Salame?" Maman Salame tace "Ga labari nan ya baza Mariri? Dawowata daga Wudul kenan kusan mutane biyar suke gaya min haka a hanya tun ban karasa gida ba, wallahi buhun hannuna kawai na ajiye bayan na shiga gida na yo nan" Aunty Farida tace "To Allah ya sa mu dace" Maman Salame tana kallon Khaleesat cike da tausayinta tace "Garin yaya haka Khaleesah?" Khaleesat ta sauke idanuwanta bata ce komai ba, Maman Salame tace "To Allah Ubangiji ya sa hakan shi ne mafi alkhairi gare mu baki daya, in kuma auren bai kare ba Allah ya kaddara za ki koma sai ki ga an koma" Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya tace "Ai saki uku ne Maman Salame" Maman Salame ta kasa cewa komai tana kallon Aunty Farida, kana ganinta kasan sosai jikinta yayi sanyi, ita dai Umma babu abinda tace a dakin, bayan kusan minti goma Maman Salame ta mike a sanyaye tace "Toh Allah ya sa mu dace, Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi gare mu duka, sai na shigo da safe in sha Allah" Umma tayi mata sallama, Maman Salame ta fita daga dakin rai babu dadi, sarai Umma tasan kishiyoyinta ne suka baza labarin a garin, don ko Nenne bazata gaya ma kowa wannan labarin ba ita da ta tsani tonan asiri, Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya don exactly tunanin da Umma take yi ita ma shi ne a ranta, Khaleesat ta kalli Aunty Farida a hankali tace "Aunty kina da number Safiyyah?" Aunty Farida tace "Ina da shi" Khaleesat tace "Ina son zan kirata ne" Aunty Farida tace "Babu kati a wayar, kuma yanxu dare yayi, ki bari gobe da safe sai kiyi magana da ita" Khaleesat ta gyada mata kai sannan ta mike tayi kwanciyarta saman gadon Umma, yaron Mama Shatu ne yayi sallama bakin kofar dakin Umma ya daga labulan yace "Wai Babanmu yace Khaleesat ta je" Umma da Aunty Farida dai sai kallon yaron suke, ya juya ya bar bakin kofar, Khaleesat ta mike zaune bayan taji abinda step brother dinta yace, tun dawowarta gidan ita ko haduwa da baban nata bata yi ba, ta sauka daga saman gadon tana gyara hulan kanta ta fita daga dakin Umma ta bi ta da kallo taji hawaye na taruwa idonta, Khaleesat na tafiya a hankali ta karasa har bakin kofar Babanta don yana zaune kan tabarma shi kadai a bakin kofar nasa, dukawa tayi daga gefen tabarman ta sunkuyar da kanta cikin sanyin murya ta gaishesa, maimakon ya amsa sai taji a hankali yace "Kiyi hakuri Jiddah, i failed you as a father, i caused you all this, but everything happened because I am a nobody, everything happened because...." Shirun da taji yayi ya sa ta daga kai ta kallesa taga hawaye a idonsa, bata san sanda ta fashe da kuka ba, yace "I am sorry for failing you daughter, albarkacin biyayyan da kika min baza ki taɓe ba in sha Allah, my wish for you since u were born was to give you the best of everything i could amma Allah bai nufa hakan ba kaddara ta fada min...." *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Read my book "HALYSAAH" on ArewaBooks, Platform available: "app only" :: https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 HALYSAAH 52 Washegari da safe har karfe goma saura Khaleesat bata tashi baccin da take ba, daga Umma har Aunty Farida babu wanda ya tasheta don duk sun san bata yi wani baccin kirki ba daren jiya, daga wayewar gari zuwa lokacin mutanen da suka shigo dakin Umma yi mata Allah ya kyauta da abinda ya faru sun fi goma, don gaba daya labarin ya gama bazuwa garin, Aunty Farida ta kalli Umma bayan wata makociyarsu da ta shigo jajen ita ma ta fita, a fusace tace "Don Allah ki dena tanka masu Umma, ki nuna ke baki ma san jajen uban me suka shigo yi maki ba, wallahi banda ke in ban ci kaza kazan mace ba ta sake shigo mana dakin nan ace ba ni ba, wannan ai iskanci ne" Umma tace "To ya kike son inyi Farida? kinga ai muna mutunci sosai da su shine har ya sa suke shigowa, duk warce kika ga ta shigo dakin nan to muna mutunci sosai ne da ita, kin ga ai bazan masu rashin mutunci ko wani abu ba, wanda ya yaɗa labarin a garin ai shine vabvan munafuki ba wanda ya shigo jajenta maka ba, kuma naga dai ba kan Khaleesat farau ba mutuwar aure" Aunty Farida ta mike tace "Ban taɓa ganin inda ake shigo ma mutum jajen mutuwar aure ba sai a garin nan, kuma wannan ba komai bane banda salon gulma da munafurci" Daga haka ta fice daga dakin zata duba ruwan zafin da ta dora kan wuta, Umma ta kalli Khaleesat da tayi backing dinsu tana bacci, ta kai hannu ta dafata, tayi kasa da murya tace "Har yanxu baccin dai Khaleesat?" Juyowa Khaleesat tayi tana murza ido, sai kuma ta mike zaune, Umma na kallonta tace "Jiya da daddare baki ci abun kirki ba, ki je ki wanke baki ki zo ki karya, ga wainar shinkafa na sa an amso maki tun daxu, kar ya huce" Khaleesat ta jawo hijab dinta ta saka sannan ta sauka daga kan gadon, ta tafi gun akwatinta da ta dawo da shi daga America ta duƙa ta bude jakar ta ciro Shower gel dinta da sponge, sai toothpaste da Brush, Umma dai kallonta kawai take har ta mike zata fita daga dakin Umma tace "Tunda wanka za kiyi kice Farida ta juye maki ruwan zafin, tana waje" Khaleesat tace "To Umma" Daga haka ta fita daga dakin Umma ta bi ta da ido, Khaleesat bata ko kalli inda kishiyoyin Ummanta suke ba da dukun dukun din zannuwan jikinsu kamar masu yin kuli kuli, ta jira Aunty Farida ta juye mata ruwan zafi a bucket ta surka mata sannan ta kai mata har bandaki, bayan ta shiga wankan Aunty Farida ta dora wani ruwan ta koma dakin Umma, Mama Zubaida ta taɓe baki tana murmushi ta kalli Mama Shatu tace "To kuma yanxu ko da uban me za ayi mana takama?" Mama Shatu ta kwashe da dariya tace "In kin tambayeni in tambayi wa? Ba ke kike kokwanton maganar Malam ba da yace auren karkari ayi wata daya ya sakota, to kin dai ga kwalliya ta biya kudin sabulu, sai ki dena cewa kinyi asaran kudin ki, ji yanda hankalinki ya tashi ranan da muka je gidan da Nenne kin ga katon gida ta shiga dakin can ta fito ta shiga wancan ta fito kin zata watayawa take a gidan, ni dama ina kallon kwayar idonta nasan ubanta take ci a gidan, sam ban ga alamar kwanciyar hankali ba don duk a firgice na ganta" Mama Shatu ta sauke ajiyar zuciya ta rike haɓa tace "Ohhh.... Ba karatu a Amurka, ba Miji, ga zawarci, wannan asara da yawa take ni Aisha, wannan shi ne ga koshi ga kwanan yunwa, an ga samu an ga rashi, ina Zahra'u zata saka ranta ta ji dadi" Mama Zubaida tace "Ke baki ga haka ya korota daga ita sai kayan jikinta ba, ko er jakar hannu da ake saka waya fa bata taho da shi ba, dama a haka ya dauketa, kuma kinga ko tsinke ba a kai mata ba dama" Duk suke kwashe da dariya har da kyakyatawa, Mama Shatu tace "Sai a dawo a ci gaba da alalan da aka watsar, don ita kanta Faridan Allah ya sa ɗan zaman da ta dawo suka yi ba a cinye jarin nata ba, nan nan a gabanmu aka yi ta hade haden garin ɗanwake da su kuka da kubewa za a kai ma Khaleesat ashe ashe korota zai yi, ni anjima ma zan shiga a tsam min garin danwaken don naga da yawa suka yi" Tana dariya ta kare maganar, Mama Zubaida tace "Ae wallahi ko tsirara zan yi na gwammace inyi da dai Zahra'u taji dadi da 'ya yanta, in ke kin manta irin cin ƙashin da Malam ya dinga mana bayan ya aurota ni ban manta ba, duk muka zama bora a gidan nan, baya ganin kowa sai Zahra'u tunda da asirinsu na buzaye ta shigo gidan, banda dai dama tun asali idonmu ya bude da Malamai ai da tuni ya sake mu tun bai samu karayar arziki ba, hatta kayan dakin da ya siya mata sai da na zaga na koma kasuwa na tambaya aka ce min nata duk yafi namu tsada, gashi yaranta su ne 'ya yan so barin Khaleesat din nan ai mun sha bakin ciki iri iri Shatu, Ita fa har Umra tayi sannan ga Hajji, mu kuwa iya Hajji kawai muka je mu ka yi tsabar ya maida mu 'yan iska" Mama Shatu ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Ki bar tuna min wannan takaicin Zubaida, banda a tsaye muke ai da wani labarin ake yanxu ba wannan ba, haka mu ma muka yi ta hadata da Malam da taimakon asiri, amma shegiyar bata yi zuciya ta koma kasar su ba da ya fara cin ubanta a gidan, in sha Allahu yanxu ta fara ganin bala'i ita da zuri'arta su da jin dadi ko farin ciki har abada, hatta yan biyun nan ya kamata mu fara miƙa sunansu yanxu kar lokaci ya kure, don naga wani farin jinin jama'a da suke da shi, duk inda suka shiga sai an tankasu ayi ta nan nan da su" Shigowar Nenne gidan yasa suka yi shiru, duk suka gaisheta ta amsa ba tare da ta kallesu ba ta nufi dakin Umma da er ledanta a hannu, duk suka taɓe baki suna bin ta da kallo har ta shiga dakin, Umma da Aunty Farida suka gaida Nenne bayan ta shigo dakin, Nenne ta amsa bayan ta ajiye ledan hannunta tace "Ina Khaleesar take?" Aunty Farida tace "Ta shiga wanka" Nenne tace "Atoh dai, dama ina zata tsaya bakin cikin shege ya kasheta, harkar gabanta kawai zata ci gaba da yi kamar babu abinda ya faru, da auren wannan gansamemen mutumin da rashin aurensa ai duk daya, kuma mu muka cusa mata shi ba sonsa take ba wallahi, yanxu banda ni da ku waye yasan tayi wani gantalallen aure ko da wani ya fito yana son ta, banda dai gulma tayi ma jama'ar Mariri katutu, ai kawai ce ma Ali zan yi ya siyar da gidan nan da nawa gidan mu koma ko Rijiyar Lemo ne" Dukawa tayi ta kwance ledan da ta ajiye tace "Gashi nan, kasuwa na aiki almajirina ya siyo min kayan ciki me kyau nayi mata farfesu ta sha ta mance abinda ya dameta, saki ai ba kanta farau ba, mu ma duk ai an taɓa sakin mu, uban Ali saki nawa ne bai min ba, sai da igiya daya ya rage mana sannan muka nutsu muka zauna har mutuwa ta raba" Wata mata ce tayi sallama bakin kofar dakin Umma, Umma ta amsa mata, matar ta shigo tana gyara yakunannen gyalenta, ganin Nenne ta duka har kasa ta gaisheta, Nenne ta amsa tana rufe farfesun da ta kawo ma Khaleesat kar matar ta barbade farfesun da gyalenta, Bayan matar sun gaisa da Umma tace "Ashe abinda ya faru kenan Ummansu Khaleesah?" Nenne ta juya ta kalleta tace "Me ya faru?" Matar ta langwabar da kai cikin rashin jin dadi tace "Mutuwan auren Khaleesah Nenne" Nenne ta mike tsaye tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, mutuwar auren wace Khaleesar? A ina kika ji auren Khaleesah ya mutu? Na shiga uku na lalace, wato matan Mariri baza ku canza halin ku na tsugudidi ba ko? To daga ke har wanda ya gaya maki kun ci kaza kazan ku yan iska kawai shegu, tashi ki fita ki ba mu waje, sai dai ki ga mutuwar aure a dakin ki ko na uwar ki, kaji min mata dai munafuka, uban mutuwan auren Khaleesah, fita ki bamu waje" Da sauri matar ta fita daga dakin ta saka takalmi wari da wari ta bar bakin kofar, Nenne na huci ta kalli Umma tace "Ke kuma Las spika ki ka dauka kike shelan an saki Khaleesah?" Aunty Farida ta tabe baki tace "Ina fa Nenne, mu ma kawai gani muka yi ana ta shigo mana tun da gari ya waye, wai an zo Jaje, wa enda suka fitar da labarin ai su ne babban munafukai" Nenne na share zufan goshinta tace "Shatu da Zubaida kenan, babu me fitar da zancen nan sai su" Tana kai wa nan ta fice daga dakin, kafin ta fito dama su Mama Shatu duk sun shige dakunan su da sauri bayan sun ji abinda Nenne tayi ma matar da ta fita daga gidan, nan tsakar gida Nenne ta tsaya babu abinda ta manta bata gaya masu ba, zagi kam sun sha har sun gode Allah, Allah ya isa shima tayi masu kwando kwando, daga karshe tace "Kuma in har Ali ya dawo gidan nan anjima bai dau matakin fitar masa da sirrin gida da ku ka yi ba wallahi sai dai ya zaba ko ni ko ku, da dai in zauna da surkai magulmata munafukai gwara in sallame ma duniya Ali in shi bazai sallama maku ba, to ai ita Khaleesar ta samu mashinshini har tayi auren ta fito, ku kuma da naku 'ya yan ke zube kaman gwanjo babu mataya fa? Dama nace ma Ali in har bazai bada su sadaka ba to ni a dena nuna su ace jikokina don kunya nake ji, ko kuma in tattara in bar masa Maririn in har bazai samar ma narka narkan 'ya yanku mafita ba, yanxu in na Jera da Labeebah ba sai ace ita ta haifeni ba, sannan kwata kwata basa wuni a gidan nan ban san inda suke zuwa ba, sai mutum ya shigo sau dari bai gan su sau biyu ba" Khaleesat ta fito daga bandaki tana rike da Shower gel dinta ta nufi dakin Umma, Nenne ta bi ta a baya tana cewa "Kin fito Khaleesah, mu je ga farfesu can na maki" Sai da suka shiga dakin sannan Khaleesat ta gaida Nenne, Nenne ta amsa tace "Kar fa ki ce zaki sa damuwar shegen a ranki kin ji? Allah ne ya dubemu ya rabu dake cikin aminci bai maki wata illa ba, dama kuma ance min uwarsa har tsafi take yi, kinga hada zuri'a da irin wannan mutane ai abun tsoro ne, kar ki saka komai a ranki, rabuwan shi ne mafi alkhairi a gare ki dama an gaya min" Khaleesat dai ta zauna gefen gadon Umma tana shafa cream dinta, Nenne na kallon Umma tace "Ke kuma duk wanda ya shigo maki jaje baki koresa ba Allah ya isa kema, ai mutum daya na shigowa kika rufe ido kika koresa komawa zai yi ya sanar ma sauran, shikenan babu wanda zai sake shigo maki, ni kin ga tafiyata inje in nemi abinda zan ci da rana" Daga haka ta fice daga dakin. Bayan Azahar Khaleesat na zaune kan darduma da qur'ani a gabanta tana karantawa a zuci, sai ga Safiyyah ta shigo dakin Umma da sallama, Khaleesat ta rufe Al-qur'anin ta daga kai tana kallonta tana murmushi, ji tayi kamar all her worries are gone ganin Safiyyah, Safiyyah ta ajiye handbag dinta ta zauna edge din katifar dakin tana kallon Khaleesat a sanyaye, gaba daya ta kasa ce mata komai, Khaleesat ta mayar da Al-qur'anin Aunty Farida gefe sannan ta mike ta koma kusa da Safiyyah ta zauna tana kallonta har sannan murmushin fuskarta bai ɓace ba tace "I miss you so much" Hawaye ne ya zubo ma Safiyyah a ido don kawai ta kasa daure hakan, Khaleesat ta sauke idonta kasa, sai ga hawayen ita ma a idonta, rabonta da zubda hawaye tun jiya a gaban Abbanta, bayan kuma ta shigo ta kwanta bata sake yarda tayi kuka ba duk da kusan yanda taga rana haka taga daren ga zafin da zuciyarta ya dinga mata, Safiyyah ta rungumeta tace "It's fine Khaleesat, Allah ya saka maki abinda yayi maki" Khaleesat ta gyada mata kai kawai, Safiyyah ta goge idonta don taga alamar kukan da take ne yasa Khaleesat kuka, Safiyyah ta dago kanta tana kallonta tace "Su Umma fa?" Khaleesat tace "Sun je gaisuwa ne anyi rasuwa dazu a unguwan" Safiyyah tace "Allah sarki, Allah ya ji ƙan musulmi" Khaleesat tace "Ameen, ya su Mama fa?" Safiyyah tace "Duk suna lafiya lau, tace in gaisheki, bayan mun gama waya daxu tace in kira mata ke, na sake kiran wayar Aunty Farida naji a kashe" Khaleesat tace "Ehh babu caji ne, ta bada a kai mata wajen caji" Safiyyah tayi shiru, bata son yi ma Khaleesat maganar da zai kara sa taji ciwo a ranta, amma duk da haka calmly tace "Saki nawa yayi maki?" Khaleesat ta buda manyan idanuwanta tace "Kawai ce min yayi ya sakeni" Safiyyah taji bakin cikin ba saki uku yayi mata ba, don ita ba kukan bakin cikin sakin da yayi take ba, a'a bakin cikin mayar mata kawa bazawara da yayi ne babban bakin ciki da takaicinta shi ne yasa har ta zubda hawaye, a gida ma kukan da tayi kenan don taji ciwon abun sosai, Khaleesat ta kalli inda Aunty Farida ta ajiye Envelope din da Drivern gidan su Abdul ya kawo tace "Ga ma can takardan ya aiko" Safiyyah ta juya ta kalli Envelope din, mikewa tayi ta dauko ta dawo ta zauna ta ciro takardan ciki, ita dai Khaleesat kallonta kawai take don har sannan bata duba abinda ke jikin takardan ba, daga Aunty Farida har Umma babu wanda yace mata saki uku ne, jiya kuma da Nenne ke ta hayaniya a tsakar gida bayan an kawo takardan Khaleesat na kwance duk bata san abinda ake ba don abubuwan da suka dameta daban, Safiyyah ta kalli Khaleesat da sauri tace "Saki uku ne ai a takardan" Khaleesat ta amshi takardan a hankali tana dubawa, after some seconds ta kalli Safiyyah tace "Wannan ai ba rubutun sa bane" Safiyyah ta hade rai tace "Do we care?? Ba dai shi aka kawo mana ba, kinga ai da shi za mu yi aiki, don da kika ce saki daya ne sai da gabana yayi mummunan faduwa don matsiyacin zai iya dawowa yace ya maida ke mu shiga uku, amma tunda ga takarda an rubuta saki uku a jiki shikenan an wuce wajen, Alhamdulillah" Khaleesat dai kallon Safiyyah kawai take, Safiyyah ta ajiye takardan ita ma tana kallonta, can a hankali Safiyyah tace "I don't understand you Khaleesat, ko dai bakin ciki da sakin da Abdul yayi maki ki ke? Kin yi give up kan cewa zaki zauna zaman har abada da shi ne? Pls let me know first so that i will watch my words" Khaleesat tayi murmushin takaici tace "Dukan yau daban, na gobe daban, zagi, hantara cin mutunci, living with hunger...." Kasa ci gaba Khaleesat tayi ta fashe da matsanancin kuka tana girgiza kai, Safiyyah ta rungumeta tace "Allah ya saka maki, Allah ya saka maki cikin gaggawa, in sha Allahu sai yaga karshensa tun ba aje da nisa ba, in sha Allah sai hakkin ki yayi tormenting dinsa har karshen rayuwarsa, komin lalacewan gidanku baza a doke ki ba balle a zage ki ko a hantare ki, uwa uba a bar ki da yunwa, In anyi duniya don manzon Allah sai Allah ya nuna ma Abdul iyakansa, wato punching bag ya mayar dake a gidan, kalli yanda kika rame kalanki ya disashe kamar ba ke ba, dubi yanda duk kika fita hayyacin ki, wallahi hakkin ki bazai taɓa barin Abdul ba, ki kwantar da hankalinki ki cire ko wani damuwa a ranki ki dau hakan a kaddarar rayuwarki" Kai kawai Khaleesat ke gyada mata hawaye masu zafi na zuba idonta, Sosai Safiyyah ta dinga bata words of encouragement tana kwantar mata da hankali, har Khaleesat taji sanyi sosai a ranta, taji ta samu relieve din abubuwan da suka tunkushe mata a rai tun jiya, a haka Umma da Aunty Farida suka dawo suka samesu, Umma ta ajiye masu ɗanwaken da ta siyo a makota sanin Khaleesat na son ɗanwake, ba laifi Khaleesat ta ci ɗanwaken me yawa tare da Safiyyah, dama duk yau ta kasa cin komai, ko farfesun da Nenne ta kawo mata kaɗan ta iya ci, amma sai ga shi ta ci ɗanwaken sosai, sai kusan karfe shidda na yamma Safiyyah ta bar gidan, with the relieve that tayi consoling kawarta tunda gashi har tana dariya ta baro ta, sallan magrib kawai Safiyyah tayi ta jawo wayarta tayi dialing number Housemate, wanda rabon su yi magana tun sanda ya gaya mata abinda Khaleesat tayi masu shi da Ajay. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Read my book "HALYSAAH" on ArewaBooks, Platform available: "app only" :: https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 09017242889 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** HALYSAAH 53 Jay na zaune dakinsa wajen karfe tara na dare yana rike da mug din coffee da yake ta stirring for almost 5 minutes now ya kasa sha, ya daga kai jin an bude kofar dakin, Ajay ne ya shigo ya nufi inda Laptop dinsa yake, shi dai Jay kawai bin sa yayi da ido har ya kunna laptop din ya duka yana dube dube a cikinsa, after almost 2 minute ba tare da Ajay ya kallesa ba yace "Resend me those files u sent yesterday via Email" Jay bai ce masa komai ba, hakan yasa Ajay ya juya yana kallonsa, mikewa yayi ya nufesa, ya cire masa head warmer din kansa ya saka a nasa kan yace "Hey is everything Okay? Me yasa baka fito ka ci abinci ba?" Jay ya mike ya fixge Head warmer dinsa sannan ya koma ya zauna yace "Kai dai ba ka ci ba, cire min Jacket dina Ajay, I can't remember dashing you the Jacket...." Ajay na gyara Jacket din jikinsa ya koma ya ci gaba da abinda yake yi a laptop din Jay, after a while Jay ya ajiye Mug din hannunsa, speaking slowly yace "I spoke to Safiyyah not long ago" Ajay ya kallesa yace "Wacece haka?" Jay yace "My Housemate's friend" Banza Ajay yayi masa ya ci gaba da duba abinda yake yi a laptop, calmly Jay yace "And she...." Ajay ya dakatar da shi sounding pissed off yace "Plss Jay, i am not interested, do not provoke me this night, banda file da nake nema a laptop dinka baza ma ka gan ni a dakin ka da daddaren nan ba" Jay ya mike yace "Whether you are interested or not, Safiyyah ta gaya min gayen ya saki Halysaah" Ajay ya juya ya kalli Jay babu ko kiftawa, after some seconds ya maida idonsa kan laptop din gabansa sai dai bai ci gaba da operating laptop din ba, Jay ya karasa kusa da window din dakinsa ya bude drape din ya rungume hannunsa yana kallon tiny snow din dake zuba kasa, Ajay yace "What did you expect? Were you expecting less? He's satiated his craving, and that is all that he is after, yayi satisfying Lust dinsa" Yana kai wa nan ya rufe Laptop din kawai ya nufi kofa ya fice daga dakin, shi dai Jay da ido ya bi sa kawai, can ya sauke wani ajiyar zuciya ya karasa ya rufe kofarsa da Ajay ya bari a bude. Khaleesat na zaune gaban Coal pot wajen karfe sha biyun rana tana ta fifita gawayin da ta hura zata dora girkin rana at the same time tana gyara waken farantin dake cinyanta, Ummanta ce zata dora girkin don Aunty Farida ta fita kasuwa shi ne ta amshi girkin tace zata yi, shinkafa da wake da mai da yaji ne za su yi da rana, babu kowa a gidan sai ita da Umma don su Mama Zubaida da Mama Shatu sun tafi gidan biki ko girkin siyarwa basu yi ba ranan, Umma ma gidan Nenne take shirin zata je ta kai mata kubewan da ta tambayeta ranan friday, ɗaga kai Khaleesat tayi jin sallaman Safiyyah a compound din su, ta dinga kallonta bata ko kiftawa don bata ce mata zata dawo yau ba, Safiyyah tayi murmushi ta karasa har inda take sannan ta dau kujeran tsugunno da ta gani a tsakar gidan ta zauna tana kallon Khaleesat tace "Sannu da aiki" Khaleesat ta ɗan bude ido tana murmushi tace "You didn't tell me you were coming today Safiyyah" Safiyyah tace "Eh nima ban zata zan zo yau ba, dama ranan Monday ko Tuesday nace maki zan dawo ai" Umma ce ta fito daga dakinta, Safiyyah ta gaisheta da ladabi, Umma ta amsa da fara'a tace "Ya su maman ku?" Safiyyah tace "Sun ce in gaishe ku Umma" Umma tace "Allah sarki, to ina amsawa, bari in je gidan Nenne in dawo yanxu" Safiyyah tace "To sai kin dawo Umma" A haka Umma ta fita daga gidan, Khaleesat ta dora ruwan girkin ta ajiye waken da ta gyara sannan suka shiga dakin Umma da Safiyyah, Safiyyah na kallonta tace "Don Allah ki daure ki dinga cin abinci Khaleesat, kin ga yanda kika rame kamar ba ke ba kuwa" Murmushi kawai Khaleesat tayi tace "To ni dama kiba gareni Sophie?" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Even though, yanxu raman tayi yawa wallahi, ji fa sai idanuwa da dogon hanci kawai" Dariya kawai Khaleesat tayi bata ce mata komai ba, Safiyyah na kallonta tace "Ba dadewa zan yi yau ba Khaleesat, aikoni aka yi wajen ki" Da mamaki Khaleesat ta dinga kallonta, sai kuma tace "Wajena kuma? Wa ya aiko ki" a hankali Safiyyah tace "Ur Housemate" Sosai gaban Khaleesat ya fadi ta dinga kallon Safiyyah babu ko kiftawa zuciyarta na bugawa, Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya ta kamo hannunta tace "Sai dai kiyi hakuri, ni dai na gaya masa abinda ya faru, And...." Sai kuma Safiyyah tayi shiru, Ita dai Khaleesat kallonta kawai take don ta kasa cewa komai tana jin hawaye na taruwa gradually a idonta, a hankali Safiyyah tace "He sent me money for ur flight ticket back to America, and you tuition fee for this semester, ya ce zai samar maki wani apartment din for the one year that is remaining for us...." Hawayen dake makale idon Khaleesat ya zubo, ta kasa ce ma Safiyyah komai, bata san sanda ta fashe da kuka ba sosai, ita dai Safiyyah tayi shiru tana kallonta cause she wasn't expecting less, sai da Khaleesat tayi kukanta me isarta sannan tana girgiza kai muryarta na rawa tace "I don't think za a bari in koma in ci gaba da karatu Sophie" Safiyyah tace "Ban gane ba? Saboda me baza a bar ki ba?" Khaleesat na goge idonta da kyar tace "Saboda Abdul ma da aka bari ya kai ni karatu babu yanda za mu yi ne hakan ta faru, we had no choice then, dalilin haka har sai da Ummata ta samu hawan jini, kin ga yanxu kuwa ai babu wani hujjan da zai sa a sake barin wani ya ci gaba da sponsoring dina a wata kasar" Safiyyah tace "I don't understand Khaleesat, yanxu me kike nufi? So kike kiyi asaran shekarun da kika yi a makarantar kenan?" Hawaye na zuba idon Khaleesat ta girgiza mata kai tace "A'a Sophie, but iyayena za su ji tsoron sake yarda wani ya dau dawainiyata try to understand me" Safiyyah tace "Zan jira har Umma ta dawo daga gidan Nenne in mata magana, ke kam bani da sauran magana dake, cause haushi zaki ci gaba da bani idan na biyeki, banda haka ta yaya ga dama ta samu amma kina neman misusing opportunity din, did you even know what you are saying?shekara daya kacal fa ya rage maki Khaleesat? Dropout kike son ki zama ko me? Ai wani abun mutum ba shi yake bargaining ma kansa hakan ba, you never bargained for all this Khaleesat, situation ne kawai, kina tunanin har a tashi duniya akwai ranan da Yaya Jawwad zai bude baki yace ai ya dau nauyinki a makaranta? Kina ganin Jawwad yayi kama da mutumin da zai maki gori wataran? Ai wallahi daga shi har Cousin dinsa sun girmi hakan, they are too classy for that, Kin zata kowa mahaukaci ne mara aikin yi kamar Abdul? Haba wallahi har kin bata min rai, ban taɓa tunanin zaki nemi kiyi turning down din offer dinsa ba, shi fa taimako kawai yayi saboda yana da halin yin hakan, duba da kin kusa gamawa kuma yasan duk abinda ya sameki, amma sbda rashin tunani irin naki kina neman gwalesa, i was thinking zaman da kika yi da Abdul zai sa ki ɗan canza wasu tunaninki marasu ma'ana, ko kuma in ce Childish tunani" Ita dai Khaleesat hawaye kawai take sosai ta kasa ce ma Safiyyah komai, tasan duk bayanin da zata mata bazata taɓa fahimtar ta ba, Safiyyah ta ciro wayarta ta fara dannawa bata sake ce ma Khaleesat komai ba don da gaske ta ɓata mata rai, after a while Khaleesat ta mike zata je ta wanke wake ta zuba a ruwan da to dora kan wuta, bayan ta gama wanke waken ta zuba ta rufe tukunyar tayi tagumi tana zaune gaban Coal pot din, a haka Umma ta shigo gidan ta sameta, Khaleesat ta sauke hannunta daga tagumin da tayi tana kallon Umma da ta nufota, tace "Umma kin dawo" Umma tace "Na dawo, ina Safiyyar?" Khaleesat tace "Tana ciki" Umma tace "Shi ne kika bar ta ita kadai" Khaleesat tace "Yanxu na fito in zuba wake ne" Aunty Farida ce ta shigo gidan da abubuwan da ta siyo a kasuwa, Umma tayi welcoming dinta sannan ta karasa dakinta ta shiga ciki da sallama, Safiyyah ta amsa tana mata sannu da zuwa, Umma ta cire Nikab da hijab dinta ta linke tace "Bata baki ko ruwa ba?" Safiyyah tayi murmushi tace "Umma ni ke nake jira ma tafiya zan yi" Umma ta zauna tana kallonta tace "To gani Safiyyah, lafiya dai ko?" Safiyyah tace "Lafiya lau Umma" Kafin Safiyyah ta ce komai Aunty Farida ta shigo dakin, Safiyyah ta gaisheta tana murmushi, Aunty Farida ta ajiye kayan hannunta tana amsa gaisuwan Safiyyah da fara'a, Umma dai kallon Safiyyah take tana jiran jin abinda zata ce, Babu bata lokaci Safiyyah ta fara yi ma Umma bayanin duk yanda suka yi da Housemate din Khaleesat, ita dai Aunty Farida na tsaye ita ma tana sauraron bayanin Safiyyah, Umma ta ɗan yi murmushi bayan Safiyyah tayi shiru tace "Allah sarki, mun gode sosai da kulawan sa, amma dai ki maida masa kudinsa Safiyyah, don ko babanta ma bana jin zai yarda, Abdul ma da ya kai ta karatun ba mu da yanda muka iya ne Safiyyah, Allah ya amfana abinda ta samu" Safiyyah was speechless, Aunty Farida ta dinga kallon Umma jin abinda tace, can tace "Allah ya amfana abinda aka samu kuma Umma? Shikenan fa tayi asaran karatun gaba daya idan bata karasa ba, kamar ka fara gini ne fa ya ruguje har kasa ya rage Foundation, ai kin ga kuwa baza kace Allah amfana abinda aka samu ba" Umma ta kalli Aunty Farida tace "Farida kin fi kowa sanin ban taɓa goyon bayan fitar Khaleesat karatu waje ba tun asali, daga ni har mahaifinta babu yanda muka iya ne, don haka Khaleesat bazata koma Amurka da sunan karasa karatu ba, ashe ma bamu dau darasin abinda ya faru a baya ba kenan" Aunty Farida bata sake ce ma Umma komai ba ta hau fiddo abubuwan da ta siyo a kasuwa, Ita ma Safiyyah tayi shiru don bata ma san me zata ce ba, Umma na kallon Safiyyah tace "Ki masa godiya kawai ki mayar masa da kudinsa Safiyyah, Allah ya dubi niyyarsa na alkhairi ya saka masa, ba wai ni kadai ba, hatta Mahaifinta ma ba yarda zai yi ba Safiyyah, cutar da ita da muka yi da farko ma da muna da wani dubaran da baza ayi haka ba, kin ga in mu iyayen arziki ne ai baza mu yarda ayi na biyu ba" Aunty Farida ta mike tace "To shi Umma ce maki yayi da wata manufa zai biya mata kudin karatun har kike tunanin za ayi na biyu? Shi fa Abdul duk abinda yayi yana da manufar yin hakan duk mun sani, ba haka kawai ya dauketa ya kai ta karatu ba...." Umma ta dakatar da ita tace "Ban ce shi wannan bawan Allahn yana da wata manufa ba amma dai kam Khaleesat bazata koma Amurka ba Farida" Aunty Farida bata sake tanka Umma ba ta fitar da albasan da ta siyo zata je ta shanya a bakin kofa, Safiyyah ta sauke boyayyen ajiyar zuciya a hankali tace "Toh shikenan Umma, ni zan koma gida, dama abinda ya kawo ni kenan" Umma tace "To ki gaida mutanen gidan Safiyyah mun gode kwarai, shi ma ki yi masa godiya don Allah" Safiyyah tace "To Umma" Jiki a sanyaye ta mike ta fita daga dakin, Aunty Farida ta dau hijab dinta da ta rataye a igiya tayi ma Safiyyah alamar su je waje, ita dai Khaleesat na zaune inda take bata tashi ba don duk taji conversation din Safiyyah da Ummanta, Aunty Farida na fita kofar gida da Safiyyah tace "Safiyyah kar ki yarda ki gaya masa abinda Umma ta ce, ki bari Babanta in ya dawo anjima zan samesa in yi masa magana" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya cikin sanyin murya tace "To Aunty, don Allah ki yi convincing dinsa shi ma, It will be very sad idan aka ce bata karasa karatun nan ba, shekara daya fa kawai ya rage mana" Aunty Farida tace "In sha Allah zan yi bakin kokarina, kuma Khaleesat zata ci gaba da karatun ta" Safiyyah tace "To Aunty, gobe da safe zan kira ki sai inji yanda ku ka yi da Baba" Aunty Farida tace "To babu damuwa, ki gaida gida" a haka suka rabu Aunty Farida ta juya ta koma cikin gida... Khaleesat ta gama girkin da take bayan ta kashe gawayin tayi alwala ta shiga dakin Ummanta, tana idar da sallah ta kwanta, gaba daya taji damuwarta ya dawo sabo fil maganar Housemate dinta da Safiyyah ta kawo mata, Umma na kallonta tace "Baza ki ci abincin bane yanxu?" Khaleesat ta girgiza mata kai tace "Sai anjima" Ita dai Aunty Farida linke kayan su Islam take don tun bayan tafiyar Safiyyah bata ce ma Umma komai kan maganar da Safiyyah ta kawo ba sanin Umma bazata taɓa fahimta ba. Bayan Magrib Aunty Farida ta samu Malam Ali yana zaune kofar dakinsa, bayan sun gaisa yace "Amma ba Lagos kika zo gaya min zaki koma ba Farida?" Murmushi kawai Aunty Farida tayi don in akwai abinda ya tsana zamanta Lagos yayi fadan har ya gaji, ta kauda tambayar da yake mata tace "Magana na zo mu yi kan Khaleesat" Yayi shiru kamar bazai ce komai ba, sai kuma yace "To ina sauraron ki" Cikin nutsuwa Aunty Farida ta sanar masa batun da Safiyyah ta zo da shi daxu da rana, Malam Ali ya girgiza kai yace "Ashe ban daddara ba kenan Farida, na yi tunanin duk mun dau darasi kan abinda ya faru wanda duk nafi kowa laifi a ciki...." Aunty Farida ta kwantar da murya tace "Ae wancan issue din da wannan ba daya bane Malam, shi fa Abdul da isa da gadara ya turata karatu Amurka kuma babu yanda muka iya haka duk muka sallama masa domin zaman lafiyanmu da naka, Abdul da manufarsa na tura ta karatu, shi ko wannan bawan Allahn babu wata manufa a ransa, saboda Allah zai biya mata ta karasa karatun kar tayi asaran shekarun da tayi, iya shekara daya fa ya rage mata Malam, ka san muhimmancin karatun nan balle ka kushe komawarta America ta karasa, in kowa zai kalubalanci haka ai banda kai Malam, don Allah ka duba wannan lamari, kuma shi wannan bawan Allahn da ya ce zai dau nauyin shekara dayan da ya rage mata su ne fa suka dau maka lauya har aka wanke ka a kotu aka kashe maganar bashin ka da Baban Abdul...." Malam Ali yayi murmushi yace "Ai nayi appreciating hakan da suka min kuma kullum ina saka su a addu'ata, amma babu zancen komawar Jiddah America karatu Farida, kiyi hakuri a bar batun nan gaba dayanta, we shouldn't be a bad parent for the second time saboda son abun duniya, tayi hakuri in Allah ya hore min sai in biya mata tayi Jamb ta nemi ko BUK ko Northwest, duka duka shekarunta nawa suke? Ai lokaci bai kure mata na karatu ba Farida, kuma ko aro ne zan nema in biya mata in sha Allah, don haka bana son a sake tada zancen ci gaba da karatun ta a America" Aunty Farida tayi shiru bata sake cewa komai ba, after a while tace "To shikenan, Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi" Yace "Ameen" Mikewa tayi ta bar wajen rai babu dadi. Washegari wajen karfe tara Aunty Farida ta gama shirin da take, Umma dake kallonta tace "Ina za ki ne?" Aunty Farida na dora Nikab dinta kan Hijabin jikinta tace "Ba nace maki zan je gidan Abida ba shekaranjiya" Umma tace "Shi ne zaki mata sammako?" Aunty Farida tace "Jiya tace min bata da lafiya ne, kuma ina son in dawo da wuri in wanke kai na" Umma ta tabe baki tace "To sai kin dawo" Ita dai Khaleesat juya kokon gabanta take a hankali tana sha ga dumamen tuwo shi ma a gabanta, da kyar take shan kokon, dumamen kuwa ta kasa ci, dama jiya da daddare ma bata wani ci tuwon ba, Aunty Farida tayi ma Umma sallama ta fita daga dakin. Nenne na gyara daurin dankwalinta tayi kasa da murya tace "To ke banda abun ki ai Zahra'u Jahila ce Parida, matar da har yau bata da wayewa kanta a murfi yake kamar matar kauye, ita ta wani san maki muhimmancin karatu kina ganin mata haka kara zube, gashi sai yanda kazaman kishiyoyi suka yi da ita sun mayar da ita Bora? Ai bari ki ji Parida, Zahra'u a yanxu dai ita daga tuwo sai bautan Allah kawai ta saka a gaba, babu ruwanta da wani ci gaba na duniya ko kyale kyalin duniya, ta riga ta amince ta kare rayuwar ta a haka in dai zata ci tuwo tayi bautar Allah, shi yasa kullum zaki ganta rike da carbi a kuturin dakinta da ko Ceiling din arziki babu, ni bana ma jin Zahra'u na yi ma Ali addu'an Allah ya dawo masa da arzikinsa don in tayi hakan gani zata yi kamar ta butulce ma Allah, duk tunaninta fa haka Allah ya so ganinsu cikin baƙin talauci, gani zata yi in tayi ta ma Allah magiyan ya yaye masu talauci kamar butulci tayi bata gode da ni'imarsa ba tunda tana samun tuwo ta ci, to irin tunanin yayarki kenan Parida, in ba haka ba ta yaya zaki dinga yi ma er cikinki bakin cikin karasa karatu ta taimake ku a rayuwa ta cire ku daga kangin talauci? shikenan kuma don kai jahili ne sai ka rasa sanin abinda ya kamata? Har wani kwambo fa take da jahilcin ta da rashin wayewa, ki bar ni da su kawai zan yi maganinsu daga Alin har Zahra'un, da can uban me yasa suka bari aka kai ta Amurkan in har da tsoron Allah a lamarinsu daga ita har Alin? Wato sai yanxu suka zama iyayen kirki masu tsoron Allah ko? To zan yi maganinsu gaba daya, in dai karatu ne kamar Khaleesah taje Amurka ta karasa in har ina numfashi, Allah ya kai mu anjima da yamma, Alin ai zai dawo daga zaman kashe wandon da yake yi a kasuwa, zan je har gidan in samesa inji ko na tauye masa karatunsa duk da talauci na, in de ni na amince taje to ko wani ɗan iska ma kar ya amince" Nenne na kai wa nan ta mike ta jawo kofar dakinta ta kulle da kwado, sannan ta dau mayafinta sabo dake rataye saman igiya ta yafa, ta dau handbag dinta ta saka makullin kofar a ciki, ta zura takalmanta ta nufi kofar fita daga gidan tana taku dai dai don sabuwar atamfa ce a jikinta, Aunty Farida ta bi ta da kallon mamaki tace "Wai fita zaki yi ne Nenne?" Ba tare da Nenne ta juyo ba tace "To me zan maki, anguwa har uku zan je yau da kika gan ni, bazan zauna a banza ki bata min lokaci ba, in ba gulma ba ganinki nake yi a gidana, ni dai in kin gama zaman kin fito ki ja min kyauren gidana kar almajirai su shiga su min sata" Daga haka Nenne ta fice daga gidan, murmushi Aunty Farida tayi ta mike ta nannade mata tabarmanta ta ajiye sannan ta daura nikab dinta, bin bayanta tayi da sauri don jadadda mata kar tace ita ta zo ta gaya mata maganar don tasan tsaf sai yayarta ta kullace ta. _Assalamu Alaikum yan mata da matan Oga ina me maku albishir da cewa Han-Ash skin beauty ta zo maku da kayan gyaran jiki iri iri wanda zai mayar da fatarki kamar Madara ta yanda duk inda kika shiga sai an kalleki, ki sai mayukan da zesa fatar ki tayi kyau, muna kuma maraba da siyan daya ko sari, i am assuring you that duk wani product dinmu is tested and trusted, ga kuma arha, for more information contact Han Ash via 0902 469 2720_ *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Read my book "HALYSAAH" on ArewaBooks, Platform available: "app only" :: https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 HALYSAAH 54 Wajen karfe shidda na yamma Khaleesat na zaune bakin kofar dakin Ummanta tana yanka mata alaiyahu a cikin roba, stepsisters dinta Labeebah da Lamisah na can zaune su ma daga bakin kofar dakin Mama Shatu da kawayensu sai hira suke suna shewa duk sun cika tsakar gidan kai kace gidan biki ne, Mama Shatu da Mama Zubaida su ma suna tsakar gidan don da su ake hiran da kawayen 'ya yan nasu, magana daya biyu sai su kwashe da dariya, yawanci kuma duk habaici suke jefa ma Umma da Khaleesat, ita dai Umma tana zaune gaban Coal pot tana kwashe tuwon masara da ta gama tukawa, Aunty Farida kuma ta tafi Hotoro tun bayan la'asar da su Noor, Nenne ce ta shigo gidan rataye da jakarta a kafada, lkci daya gidan yayi tsit, a takaice Nenne ta amsa gaisuwan da su Mama Zubaida da Lamisah da kawayensu ke yi mata ta nufi gun Umma tace "Zahra'u Alin ya dawo ko be dawo ba?" Umma ta gaida Nenne sannan tace "A'a bai dawo ba tukun Nenne, sannu da zuwa" Nenne tace "Kin gan ni nan daga Sheka nake daga can na tafi Ɗan Agundi, ni ce har Na'ibawa yau, tun safe na bar gida sai yanxu nake dawowa 'yan adaidaita sahun kano dai sauransu yawo da bindiga kawai...." Murmushi kawai Umma tayi tana ci gaba da kwashe tuwon da take yi, Nenne ta jawo kujera ta zauna tace "Gidan Katime me Aya na tafi a Sheka, in gaya maki me Aya dai kafafuwanta sun mutu murus Zahra'u, ko tashi bata iya yi, babu yanda ban yi da matar nan ta rage cin nama ba amma taga kamar bakin ciki nake mata don mijina baya kawo min, to yau ni da ban ci nama ba gani da kafafuwana biyu rass, ita kuwa duk sun mutu, wai tana ganina ina taku dai dai na shigo gidan sai ta fashe da kuka, ni dai bata ban tausayi ba wallahi, sai kinga yanda take mana fafa da nama lokacin, kullum kya ji kamshin tafashen nama a gidanta, mu sai dai mu watsa er daddawa a miya" Umma na girgiza kai tace "To Allah Ubangiji ya bata lafiya" Nenne tace "Ba batun Allah ya bata lafiya ba, ai duk kafafuwan sun rube, da kyar in baza ace za a yanke mata su ba tunda ko motsa su bata iya yi " Su Mama Zubaida gaba daya kunnuwansa na kan labarin da Nenne ke ba Umma, Malam Ali ne ya shigo gidan da sallama, Nenne ta juya tana kallonsa, can ta mike ta nufesa tace "Yanxu Ali baza ka hakura da fita kasuwar nan ba tun da ba wani abu kake yi a can ba sai zama cikin rana da iska? Ka dubi yanda duk kayi bakikirin kamar baka taɓa haske ba a rayuwarka Ali, tunda ba aikin fari gareka ba balle baƙi a kasuwar ka hakura da zuwa mana" Gaisheta kawai yayi ya dau buta zai debi ruwa ya fita waje ya zauna ya jira Magariba, Nenne ta tabe baki tace "To wajen kai da matar ka Zahra'u na xo" Umma ta juya tana kallon Nenne jin abinda tace, Shi ma ya tsaya yace "To lafiya dai ko?" Nenne tace "A ina lafiyar take, ba sai kun nemi zaman lafiyar za a zauna lafiya ba, labari na samu wai masu kare hakkin 'yan Adam sun zo gidan nan sun ce za su ci gaba da daukar nauyin karatun Khaleesat a Amurka saboda tausayin abinda tsinannen mutumin nan Awdul yayi mata, to amma wai saboda kai da Zahra'u yan bakin ciki ne sai ku ka gwalesu ku ka koresu, da wanne ku ke son yarinyar ta ji fisabilillahi? Da mayar da ita bazawara da aka yi tana da karancin shekaru ko kuma da asaran karatun ta da kuke kokarin yi mata? In ita Zahra'u jahila ce bata yi karatun boko ba kai ma Jahili ne Ali? Ina ne ban shiga nayi aikatau ba don kayi karatu? To wallahi ko karshen bangon duniya ne sai Khaleesat ta koma ta karasa karatun ta tunda har aka ce za a dau nauyinta babu ko sisin ku, to ina ma ku ka ga ko sisin" Malam Ali dake ta kallon uwar tasa yace "A ina kika ji wannan zancen Nenne?" Nenne tace "Labarin duniya na buya ne dama? Ina zaune yan Mariri suka zo suka tsegunta min har unguwan da naje yau...." Mama Shatu ta kalli Mama Zubaida da ta saki baki tana sauraron Nenne, Mama Zubaida ta kasa daurewa ta gyara zama cikin kwantar da murya tace "Amma Nenne na farkon ma ba a wanye lafiya ba shi ne za a sake na biyu? Dama gashi duk garin nan kallon makwaita masu son abun duniya kawai ake mana, ko ina sai zaginmu ake tun da aka samu labarin sakin walakancin da aka yi ma Khaleesat, ana ta cewa ubanta ne ya ja mata, A rayuwar nan yanxu fa in ba iyayenka ne za su yi maka dawainiya ba duk wanda yace zai dau dawainiyar ka sama ta ka to da wani abu da yake hangen zai samu a gare ka ne, Khaleesat fa 'ya mace take ba namiji ba Nenne, kuma ba komai ke rudar maza akanta ba sai kyanta da kalan fatar ta sun ga buzuwa, shi kenan saboda son abun duniya sai a zuba ido har sai yarinyar nan ta lalace tukunna, Abdul ya gama nasa ya samu abinda yake so ya sako mana ita sai kuma yanxu ace ga wani ma ya zo wai zai ci gaba da daukar nauyinta? Haba sam batun nan babu tsari a cikinta, shikenan ita kuma haka ta zama kamar Tasi...." Nenne ta kundumo wani zagi tace "Toh duk wanda ya fasa fadin abinda ke ransa akan Khaleesah Allah ya tsine masa albarka, kuma in de karatu ne kamar tayi ta gama sai dai bakin ciki ya kashe duk wani shege wallahi, ko ma ina za a kai ta a kai ta ni na amince ta je, ai ita tasan tarbiyyar da muka yi mata in ma ta gantalar da tarbiyar ita da Allah, kuma gobe gobe zan sa a kira min baƙar kawar tata ta zo in gaya mata uban Khaleesah ya amince koma waye zai dau nauyinta ya dauka, taje can ta ci gaba da karatun ta, ai gwara tayi nesa da mu ko bakin cikin dake damunta a rai zai ragu, mu kanmu in tana ganinmu takaici da bakin ciki take don ba mu da wani babanci da Awdul a wajenta tunda mu muka ja mata komai, gwara ta koma ta gama karatunta ta dawo da kwalinta don bazata tashi a tutar babu ba, shi kansa Awdul din yana samun labari an samu wanda ya maidata Amurka ta ci gaba da karatu sai bakin ciki ya kusa kashe shegen, a nan kuma zai san ba a banza Khaleesah take ba farin jininta ya shahara" Nenne na huci ta juya ta kalli Umma tace "Ke kuma Zahra'u halan tallan alalen ki ke da niyyar dora mata da kike mata bakin cikin komawa ta karasa karatun? To kamar yanda kike takama kina da iko da ita nima haka tunda ni na haifi ubanta, ban ga shegen da ya isa yace bazata koma ta karasa karatun ta ba" Ita dai Umma bata ce ma Nenne komai ba, Malam Ali dai na tsaye rike da buta a hannunsa yana kallon uwarsa, can dai yace "Amma dai Nenne sam babu tsari ace mun sake barin yarinyar nan ta bar kasar nan da sunan wani zai dau nauyinta bayan duk abinda ya faru, me kike son jama'an gari su ce a kaina? Sannan nace duk sanda na samu kudi zan nema mata Jami'ar garin nan tayi, ba wasu shekaru gareta ba balle ace lokaci zai kure mata" Nenne ta kallesa da sauri tace "A gidan uban wa zaka samu kudin? Mutanen garin in sun fasa fadin abinda za su fada a kanka Allah ya tsine masu albarka, kai bari kaji Ali bana bukatar ra'ayinka ko shawararka a yanxu saboda kai ma sanda ka bi ra'ayinka ka yarje ma Awdul ya kai ta kasar waje babu wanda ka saurara ko kaji shawaransa, don haka ni ma yanzu wallahi bazan saurare ka ba Amurka ne sai Khaleesat ta koma ta karasa abinda ta fara in sha Allahu, in kuma nuna ma duniya zaka yi ni er banza ce a gareka to Bismillah" Kofar gida kawai Malam Ali ya fita da butansa a hannu, Nenne ta kalli Khaleesat tace "Maza ki hada akwatinki ki tsaya cikin shiri, in sun biya maki kudin jirgin ki kama gabanki kije kiyi abinda zai taimaki rayuwarki, zama gidan nan kadai ya ishi mutum ya fada cikin mummunan damuwa, gida kamar na 'yan sansanin gudun hijira, ga lafta laftan mata suna yawo suna doyi a cikinsa, ai ko mutum matsiyaci ne ya kasance dai yana da tsaftarsa dai dai gwargwado, amma gidan nan ga talauci ga kazanta, ina bawa zai iya rayuwa a nan idan ba dole ba" Nenne na kai wa nan ta kama hanya tayi tafiyarta, Khaleesat ta daga kai ta kalli Umma da ta bi Nenne da kallo, Mama Shatu ta mike tana kallon Umma tace "Muddin kika ce baza ki bude baki kiyi magana ba to kina ji kina gani za a mayar maki da er ki karuwa Zahra'u, wata birkitacciyar tsohuwa can kamar Nenne ce zata yanke ma er da kika haifa hukuncin abinda ya shafi rayuwarta? Ita ta tsugunna ta haifar maki er? Mu meyasa ba a mana iko akan namu yaran ba? Saboda an san baza mu dauka ba mu ba yan iska bane, to kuwa wallahi Nenne na dab da kai ki ta baro ki, mata me tabin ƙwaƙwalwa zaki yarda ta yanke hukunci akan 'er ki? ai in ita Khaleesar ta bude baki tace bazata je ba babu uban da zai tilastata ta je wallahi, waye bai san Nenne da kwadayi da son abun duniya ba kamar tayi sata?" Muryar Nenne suka ji ashe tana makale bata tafi ba tana jiran jin abinda za a ce, Nenne ta dinga kwalo ma Malam Ali kira, sai gashi ya shigo da sauri yana kallonta yace "Lafiya Nenne? Ai magana ta wuce yanda kika ce haka za ayi" Mama Shatu tayi wuri wuri da ido daga inda take tsaye, Mama Zubaida ta mike ta lallaba ta dau kwandon kwanon wanke wankenta ta shige daki ta sako labule, Nenne ta rushe da matsanancin kuka tana kallon Malam Ali tace "Ali yau sai dai ka zaba ko ni ko Shatu a gidan nan, kawai ka zaba ko ni ko ita, ni Shatu zata kalla ta kira me tabin ƙwaƙwalwa wato mahaukaciya er macukule? Ni zata ce ma me kwadayi da son abun duniya? Tunda nake me na taɓa zuwa gun almajirin ubanta dake bara a bakin danja nace ya bani? Me na taɓa rokon uwarta me shanyayyen kafa? Bata san ina labe ban tafi ba duk ina jin abinda take cewa, cin mutunci da zagi sai wanda ta manta ne bata min ba Ali, har tana gaya ma Zahra'u ni na haifar mata er da zan yanke mata hukunci akan ta? Me nayi ma Shatu da har zata yi mugayen kalamai haka a kai na? Naga dai kullum ci gabanka da na iyalan ka shi ne burina, fadi tashi babu wanda bana yi akan kai da iyalinka, amma daga karshe sai zagi da cin mutunci ya biyo baya, tsofe tsofe da ni Shatu tace min me son abun duniya?" Kuka sosai Nenne take tana share idonta da gyalen jikinta, Malam Ali na kallon Mama Shatu da tayi tsuru tsuru yace "Shatu ki tafi gida, sai na neme ki" Mama Shatu ta gwalo ido tace "Ban gane in tafi gida ba Malam, wani gidan zan tafi?" Malam Ali yace "Gidan iyayenki, ki je na sake ki" Mama Shatu ta zabura tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ka sake ni fa kace Malam, na shiga uku na lalace" Labibah ta mike tana huci tace "Gaskiya Baba sai dai mu bi Baabarmu mu ma" Nenne tace "Shegiya ku bi ta mana, yunwar cikin ku kadai ma ya isheku ai" Malam Ali na kallon Mama Shatu dake rusa kuka yace "Kar in dawo in sameki a gidan nan" Daga haka ya fice daga gidan, Nenne ta bi bayansa tana goge idonta ita ma ta fita, sai a sannan Mama Zubaida ta fito tana salati tana kallon Mama Shatu dake kuka wiwi, Umma tsabar yanda jikinta yayi sanyi ta ma kasa cewa komai daga inda take zaune, Mama Zubaida na kallon Umma tace "Ke kam kinyi asara wallahi Zahra'u, ko wani bala'i ta dalilin ke da tsinannun 'ya yan ki yake faruwa a gidan nan, gashi yau saboda ke da er ki an saki Shatu, sam babu alkhairi a tare dake da zuri'ar ki Zahra'u" Umma ta juya tana kallon Mama Zubaida sai dai bata ce komai ba, Khaleesat ma ta daga kai tana kallonta, Mama Shatu na kuka sosai tace "Kuma in sha Allahu asirin da kike yi zai kare maki a gidan nan Zahra'u, yanda kika yi sanadiyyar tsinkewar igiyar aurena daya ke da er ki wallahi sai nayi sanadin naki igiyar kema, ko tsirara zan yi yawo kuwa, Ni saki daya aka min ke ukun gaba daya za a maki, kuma kamar Ali ya maida ni ne don yanxu na fara auren sa wallahi" Don mamaki Umma ta ma rasa abun ce masu ganin yanda suka juya zancen lokaci daya, yau ga fadan karfin hali tana gani kiri kiri, biyesu ma bata lokaci ne kawai a wajenta ga makota na jin su, tsam ta mike tayi shigewarta daki, Khaleesat ta mike ta bi bayanta. Washegari da sassafe Umma da Aunty Farida suka fito tsakar gida suka tarar da Mama Zubaida da Mama Shatu a tsaye suna jiran fitowarsu za a je ba Nenne hakuri, ko wanne da Hijab dinsa har kasa don sanyi ake sosai, duk abinda suka yi ma Umma jiya hakan bai sa tace bazata bi su zuwa gidan Nenne ba, Su ma din sun san ta dalilin Umman sai Nenne ta iya hakura ta sa Malam Ali ya maida Mama Shatu shi yasa Mama Zubaida da kanta ta samu Umma ko kunya babu tayi mata magana wajen karfe biyar din asuba, Mama Shatu dama a makota ta kwana ranan don sae da Nenne ta dawo ta korata har da watsi da en tsummokaran ta, sae kusan hudun asuba Shatu ta dawo gidan daga inda ta kwana, a haka duk suka kama hanya zuwa gidan Nenne da asuban. Ranan Thursday da safe Khaleesat na zaune dakin Umma tana kallon Aunty Farida dake ta jera mata kayanta da aka amso wajen guga a cikin akwati, ita dai Khaleesat har sannan ta rasa gane me take ji a ranta, farin ciki take ko akasin haka duk ta kasa ganewa, babban damuwarta yanxu bata san da idon da zata kalli Housemate dinta ba idan ta koma America, sannan gani take kamar babban burden kawai zata zame masa a can din tunda ita ba komai gare iyayenta da za su tallafa mata da shi ba idan ta koma, ɗan kudin dake account dinta ba wani kudin kirki bane kuma da shi ta siya sabon waya with new sim card, sai few abubuwan da tasan zata bukata a can kasar, sauran kudin dake account dinta ko dubu dari da hamsin bai karasa ba, duk wannan tunanin yasa take damuwa sosai a ranta, Aunty Farida ta daga kai tana kallonta kafin ta rufe zip din jakar tace "Baki manta komai ba dai ko?" Khaleesat ta gyada mata kai kawai, Aunty Farida tace "A Airport din za ku hadu da Safiyyah goben?" A hankali Khaleesat tace "Eh" Aunty Farida ta kulle zip din tace "Gwara ki saki ranki kiyi abinda ke gaban ki Khaleesat, ki cire duk wani damuwar dake ranki kar ki je ki samu matsala a karatun ki, shi kuma Jawwad Allah ya saka masa da mafificin alkhairi...." Khaleesat ta sauke idonta bata ce komai ba, lkci daya taji hawaye ya cika idonta, Aunty Farida ta mike ta dauko daya akwatin don hada few foodstuffs din da suka siyo mata da Umma wanda zata iya shiga Amurka da shi, a hankali Khaleesat tace "Toh Aunty ta yaya za a maida masa kudinsa dake account dina?" Aunty Farida ta daga kai ta kalleta, can tace "Kudin wa? Ko Abdul?" Khaleesat ta gyada mata kai, Aunty Farida ta saki baki, can tace "Wai dama har yanxu kudaden nan nasa na account din ki?" Khaleesat ta gyada mata kai, shiru Aunty Farida tayi kamar me nazari, after a while tace "Ki ci gaba da ajiye kudin kawai Khaleesat, duk sanda ya dawo ya bukaci kayansa sai a basa, ko Umma kar kiyi ma maganar kudin for now, bana son a samu delay a tafiyarki don yanxu sai su iya cewa sai an maida masa kudadensa, kuma hakan zai iya ja maki delay...." Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, Aunty Farida ta ci gaba da hada foodstuff din da take a akwati. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* _Assalamu Alaikum yan mata da matan Oga ina me maku albishir da cewa Han-Ash skin beauty ta zo maku da kayan gyaran jiki iri iri wanda zai mayar da fatarki kamar Madara ta yanda duk inda kika shiga sai an kalleki, ki sai mayukan da zesa fatar ki tayi kyau, muna kuma maraba da siyan daya ko sari, i am assuring you that duk wani product dinmu is tested and trusted, ga kuma arha, for more information contact Han Ash via 0902 469 2720_ We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 55 Wajen karfe uku na yamma Khaleesat na zaune bakin kofar dakin Umma Aunty Farida na combing din mata dogon gashinta bayan ta wanke mata shi da Shampoo da Conditioner, har wani sheki baƙin gashin nata yake yi bayan Aunty Farida ta shafa mata man gashi, tun daga wajen wanke gashin Aunty Farida ke ta mata fadan ta bar gashinta ya kakkarye saboda banzan da tayi da shi ta dena kula da shi, ita dai Khaleesat bata ce mata komai ba don har sannan basu san irin zaman da tayi a gidan Abdul ba, don ma abun ya tsaya iya kakkaryewan gashi, har bata son tuna experience dinta a gidan Abdul hakan yana traumatizing dinta, su Mama Zubaida da Mama Shatu dai na bakin murhu suna girka abincin siyarwansu na yamma, suna yi suna kuskus a bakin murhun, lkci lkci sai su kalli direction din su Khaleesat, ita dai Aunty Farida dama ko kallo basa isanta a gidan, a da dai ta biye su har dambe sun sha yi amma yanxu bata da wannan time din, kallon stark illiterates kawai take masu, wasu mata biyu ne suka shigo gidan babu ko sallama, sun yi shiga ta alfarma sun sha gwala-gwalai suna taku cikin isa, at the same time suna bin ko ina na gidan da kallo cike da kyama gashi dama su Mama Zubaida sun yi gaje gaje da ruwa a tsakar gidan ranan, Khaleesat ta dinga kallonsu haka Aunty Farida da ta ajiye comb din hannunta, Mama Zubaida ta mike tace "Sannun ku da zuwa ko dai batan hanya ku ka yi ne, in gidan Hajiya Samira matar Alhaji Bala ku ke nema can karshen layi za ku karasa sai ku yi tambaya a nuna maku gidan, amma ba nan bane" Momy ce ta shigo gidan tana tafiya gansan gansan da Drebanta a bayanta yana biye da ita, mayafin nata ma ko yafa shi bata yi ba, gashi ta sha wani tsadadden baƙin glass no respect, Khaleesat ta dinga kallonta babu ko kiftawa, lkci daya taji gabanta ya fadi sosai, ta juya ta kalli Aunty Farida, sai ga Meemah ita ma ta shigo gidan tana yatsine fuska, ita ko mayafin ma babu a hannunta, Aunty Farida ta dake tace "Bayin Allah lafiya? Daga ina haka, babu ko sallama" Daya daga matan da suka shigo da farko tana ma Aunty Farida wani matsiyacin kallo tace "Ba shi ya kawo mu ba, a irin wannan bolan za ayi maku sallama?" Umma ta fito daga dakinta don tana jin duk abinda ake cewa, tsaye tayi bakin kofa tana kallonsu, Mama Shatu da Mama Zubaida dai sai zazzare ido suke kamar wa enda suka yi ma sarki karya, Momy ta karaso har tsakiyar compound din tana tafiya cikin isa da gadara, fuskar nan nata babu ko digon mutunci tace "Zuwa nayi in ji ko shegiyar er ku tana da gadon Abdul ne, Ko kuma shi ma satan da ku ka yi ma ubansa kuke da niyyar za ku yi masa, in kuwa babu gado to yanxun nan ba sai anjima ba a maido mana kudadensa dake account din er ku..." Umma ta kalli Khaleesat nan da nan hankalin Umma ya tashi sosai, Aunty Farida tace "Ikon Allah, shi ne sai anyi wannan zuga haka kamar za ayi yaki?" Meemah ta matso har gaban Aunty Farida tana mata matsiyacin kallo tace "Yakin ne ai, ko kin ga alamar da sassauci muka zo? sanin halin familyn na ku na sata wanda ku ka gado a gun Malam me dattin hula ya sa mu ka yo tattaki a mayar mana da kudaden mu tun wuri, ai kowa yasan sata da cin amana shi ne tambarin gidan nan, don haka tun wuri ba a jiyo kan mu ba a maido mana Miliyan goman Abdul, kun zata bulus za ku ci ga banza ta fadi ko? To Sponsoring din matsiyaciyar er ku da ya dinga yi da kudinsa ma ai ba yafewa yayi ba sai kun biyasa a lahira wallahi, kawai babban farin cikin dake saka ni nishadi idan na tuno shi ne karewar da zata yi as dropout din John Hopkins university, don ko kaf zuri'arku za ku siyar baza ku samu kudin biya mata ta ci gaba da karatun a kasar Amurka ba, da yau ta gama John Hopkins sai bakin ciki ya kasheni, amma Alhamdulillah a dropout zata kare, Abdul kuma ya yar da kwallon mangwaro ya huta" A fusace Momy tace "Ke Meemah tsayuwa cikin kangon bolan nan ne ke burge ki da baza kiyi abinda ya kawo mu mu fita ba, ko so kike Cholera ya kama mu? Ina ke ina cacar baki a irin wannan gida" Aunty Farida tayi wani murmushi tana kallon Meemah tace "Sai dai kuwa bakin cikin nan ya kashe ki don kina ji kina gani Khaleesat zata gama karatu a makarantar da kike fada, Allah ya ji ƙan ki in Advance" Cikin tsawa Meemah tace "Keee, ki iya bakin ki, kar ki gan ni tsaye a wannan bolan gidan a gabanki kiyi zata ni sa'ar yin ki ce, don wallahi inda na bi da kafata ma baki isa ki bi ba har duniya ta nade, ni ba sa'ar ki bace ta ko wani angle, banda Abdul yayi downgrading dinmu ya kaskantar da darajan da Allah yayi mana ina mu ina hada hanya da matsiyata talakawa irin ku balle har aje ga auratayya? Ke ki duba irin wajen da ku ke rayuwa wanda ko karen gidanmu baza mu bari yayi rayuwa a cikin wannan hali ba, To wallahi ki iya bakin ki ni ba sa'ar yin ki bace, ba karamin aikina bane in sa a shafe babin ki a duniya" Tun kan Aunty Farida ta mayar ma da Meemah amsa Umma ta hanata, cikin fushi Aunty Farida tace "Kamar yaya in yi shiru Umma, gidanmu fa suka zo suka same mu kuma ki ce inyi shiru? ashe ma karyar arziki suke in don saboda miliyan goma za su yi wannan uban zugan kamar masu bibiyan miliyan 50 har su tsaya suna kumfar baki suna tada jijiyoyin wuya akan 10M, uban wani ya saka ya tura mata kudin a account dinta da har za su zo nan suna gaya ma mutane maganar banza, ko kuma rokonsa tayi ya saka mata kudin, su arzikin ma wallahi da gani taka haye suka yi, da can su ma matsiyata ne" Meemah ta mika ma Momy handbag dinta tana huci zata cakumo Aunty Farida, Momy ta dakatar da ita tace "Ke me ya kai ki, ki taɓa ta ki ce kin taɓa wa? Salon ta goga maki ƙashin tsiyarsu kike kokarin dambe da ita? Yanzu wannan har Class din damben ki ce in ba rashin wayo irin naki ba Meemah? Ai ba a dambe da talaka matsiyaci" Umma ta kalli Khaleesat tace "Ta yaya za ki fiddo kudaden a account din ki Khaleesat?" Khaleesat ta sauke idonta tace "Sai naje banki, bani da Atm card, kuma kudin bazai fita lokaci daya ba...." Momy na mata matsiyacin kallo tace "Sai ki tashi ki tafi bankin ai don wallahi kudaden nan baza su kwana a account din ki ba yau, da niyyar ki kin ci bulus tunda ubanki ne ya nema masa kudin ba" Khaleesat ta daga kai ta kalleta, ita har sannan ta kasa daina mamakin matar nan, kai tunda aka haifeta ma ita ba a taɓa shayar da ita ruwan mamaki yanda mahaifiyar Abdul ta shayar da ita ba, yau sati daya da sakin da Abdul yayi mata amma kullum in ta tashi sai ta zauna tayi mamakin uwarsa ganin abun take kamar Drama, ba ayi ranan da zai zo ya wuce da Momy bazata fado mata ba, bata taɓa san akwai mutane irin Momy a rayuwar nan ba, muryar Mama Zubaida taji tace "Ai ba zama zaki yi kina zazzare ido ba kamar barauniya, tashi za ki yi ki kama hanya ki tafi banki ki fiddo masu da kudadensu tunda ba gadon Abdul din gare ki ba kuma ba kudin tsohon ki bane, duk wani abu na rashin gaskiya dake da uwarki da kanwarta gaba ku ka basa ba baya ba, banda haka ta yaya za kuyi shiru da makuden kudadensa har Miliyan goma a account dinki? So ku ka yi ku danne kudin ko yaya? Don ma kun samu masu hakuri da kawaici da wasu ne idan ba a zo da motar yan sanda an tafi da ku ba ku ce bani ba, wannan ai rashin gaskiya ne da rashin tsoron Allah kiri kiri, duk kun yi mukus da bakin ku za ku cinye miliyan goma ga banza ta samu" Aunty Farida ta juya tana kallon Mama Zubaida, sai kuma ta nufeta tana cewa "Zubaida idan ban zubar maki da hakora a gidan nan yau ba ki ce bani ba, don kaza kazan ki akwai tsinannen da ya sako bakin ki? Uwarki muka yi ma rashin gaskiya ko ubanki?" Mama Zubaida tayi wani shewa tana tafe hannu tace "To yau kika saba Farida? Ai ke fitsararriya ce dama mara mutunci mara kunya shi yasa ga ki har yau duk kyan ki kin rasa mashinshini sai dai kiyi tuwo tuwo a garin legas kina hadawa da karuwanci, waye bai san wannan ba?" Aunty Farida zata cakumo Mama Zubaida Mama Shatu ta shige tsakaninsu tace "Ke yanxu Farida Zubaida sa'arki ce zaki dinga zaginta haka ta uwa ta uba don kawai tana kishiyar yayarki? Daga dai ta fadi gaskiya banda ɗan Adam baya son gaskiya?" Aunty Farida tayi wani wurgi da Mama Shatu sai ga ta a kasa timmm, tuni Mama Zubaida ta shige dakinta ta kulle kofarta da sakata tana cewa "Haka kawai ki shafa min bakin jini irin na ku? Allah ya sauwake in yi dambe dake Farida, ku je can ku ji da rashin sa'ar ku a rayuwa, ku kenan daga wannan iftila'in sai wannan bala'in, ko wani fitinar duniya a kan ku ya kare, daga wannan sai wannan, Allah kadai yasan laifin da ku ka tafka a kasar ku, kilan ma ta zina aka sami ke da yayar taki, ga bakin jini da rashin sa'ar ku ya shafi Malam ya talauce" Da kafa Aunty Farida ta hambare uban miyan da Mama Zubaida ke yi na abincin siyarwanta, miyar duk suka malale kasa, shinkafar ma dake cikin kwando ta kifar da shi a kasa tana zagin Mama Zubaida ta uwa ta uba, Mama Shatu ganin yanda aka yi watsi da kayan sana'an Mama Zubaida ya sa ta ja bakinta tayi shiru ta tafi gun nata miyan ta zauna tana cewa "Hakuri kawai za kiyi Farida, hakan ba dadi kam" Momy ta rike haɓa tace "Alhamdulillahi da na yi iya bakin kokarina na ganin ban hada iri da gayyar tsiya ba, ku kuga wannan tsiya haka kamar 'yar tasha, ga talauci ga tashanci, Abdul ya so ja mana abun fade a dangi Allah ya takaita min abun, kuma ba dai kun ce kudade na banki ba, to zuwa yau da daddare in ga alert din Miliyan goma, in kuwa ba haka ba gobe da sassafe za ku gan ni a gidan nan ba kuma zuwan lumana zan yi ba, ai shi ramin karya kurarre ne, kuma ko kwabo daya yayi ciwon kai a kudaden nan wallahi sai an daure er ku..." Momy na kai wa nan ta bude handbag dinta ta ciro takarda dauke da account details dinta ta jefa ma Khaleesat sannan ja tawagarta suka yi waje tana cewa "Haka kawai Meemah zata ja min bala'i ta hada ƙashi da wannan iri na fitina, irin tsiya, to kiyi dambe da ita ki ce kin yi dambe da wa? Kina ganin yarinya kamar mahaukaciya, A'a wallahi Allah ya maki tsari" A haka duk suka fita daga compound din, Khaleesat taji hawaye ya cika idonta, Umma komawa dakinta tayi tayi tagumi ranta ba dadi, ita kam ta gode Allah da jarabawa iri iri, daga wannan sai wannan, Khaleesat ta dau takardan da Momy ta jefa mata ta juya ta shiga dakin Umma hawaye na zuba idonta, Aunty Farida kuwa bata fasa zage su Mama Zubaida da Mama Shatu a tsakar gida ba, Mama Zubaida taki fitowa kuma taki tanka Aunty Farida, Mama Shatu kuwa tayi tsit kamar bata san da wa Aunty Farida take ba, daga karshe bayan Aunty Farida tayi masu wankin babban bargo ta shige dakin Umma tana huci, Umma ta daga kai tana kallonta tace "Yanxu ban isa ince ki bari ki bari ba Farida?" Aunty Farida ko tanka Umma bata yi ba ta dau Hijab dinta ta saka tana kallon Khaleesat tace "Ki tashi ki shirya mu tafi bankin" Mikewa Khaleesat tayi tana goge idonta ta dau hijab dinta ta saka, a haka suka kama hanyar banki da Aunty Farida, amma suna isa bankin suka tarar an tashi aiki sai ran Monday don karfe hudu har da rabi a lokacin, Aunty Farida na kallon Khaleesat bayan sun fito bankin tace "Goben karfe nawa ne tafiyar naku?" A hankali Khaleesat tace "Flight din karfe daya zuwa Abuja, daga Abuja kuma jirgin yamma ne" Aunty Farida tace "Kuma bazai yiwu a daga tafiyar ba Khaleesat? Kinga banki dole fa sai Monday idan Allah ya kai mu" Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba, ita kanta she is just confuse bata san yanda zata yi ba. A haka suka koma gida kusan karfe biyar da rabi, Umma na kallonsu tace "An tashi a banki ko?" Aunty Farida bata ce komai ba ta cire hijab dinta ta nemi waje ta zauna, Khaleesat ta zauna tana kallon Umma tace "Banki sai ranan litinin, sun tashi yau" Umma tayi shiru bata ce komai ba, can tace "Kema kin san bai amshi kudinsa ba me yasa zaki yi shiru har na sati daya Khaleesat? Yanxu da kinyi magana tun yaushe za a san yanda za ayi a cire kudin a mayar masa kayansa, yanxu rashin mutuncin da suka zo suka mana makota na ji ina amfanin sa?" Aunty Farida tace "A'a ta min maganan kudin fa ranan Alhamis, a lkcn ma tayi zaton yau ne tafiyar ashe gobe ne, kuma kema kinsan Khaleesat bazata taɓa ko biyar a kudin nan ba tunda ba nata bane, kawai dai dama matsiyata ne yan iska daga Abdul din har iyayensa" A hankali Khaleesat tace "In ma an cire kudin an basu bazan iya tafiya babu kudi a account din ba, don baza a bari in shiga kasar ba, they wilk see i am not financially capable idan babu kudi a account dina, shi yasa ma ya bar kudin a account din all this years" Aunty Farida tayi shiru don bata ma san me zata ce ba, haka ma Umma da ta rafka tagumi tun shigowarsu, after a while a hankali Umma tace "Ni tsorona kar su dawo goben da suka ce bamu san kuma da me za su zo mana ba" Aunty Farida ta mike tace "Sai su zo su amshi babu tunda su yan iska ne" Daga haka ta fice daga dakin, Khaleesat taji hawaye ya cika idonta, Umma na kallonta a hankali tace "Kiyi hakuri Jiddah, wataran duk hakan zai zama labari, Allah ya bamu ikon cin jarabawan mu, in ma kin koma makarantar in ma baki koma ba duk yanda Allah yayi dai dai ne" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata ta mike ta dau tsintsiya zata yi gyaran dakin Umma tana goge hawayen dake sauka idonta.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Read my book "HALYSAAH" on ArewaBooks, Platform available: "app only" :: https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 HALYSAAH 56 Khaleesat har ta fara bacci wajen karfe goma da rabi Aunty Farida ta tasheta tana mika mata sabuwar wayarta dake vibrate, mikewa tayi zaune tana gyara hulan kanta ta amshi wayar taga Safiyyah ce ke kiranta, ɗagawa tayi ta kai kunne, daga daya bangaren Safiyyah tace "Ko har kin fara bacci ne" Khaleesat tace "Um, da wuri na kwanta ne" Safiyyah tace "Ayya sorry for waking you up, dama Housemate din ki ne yace in tambayeki wani account zai maki funding, cause nasan definitely Abdul ya amshi kudinsa dake account din ki ko?" Khaleesat tayi shiru ta kasa ce ma Safiyyah komai, har sai da Safiyyah tace "Hello" a hankali Khaleesat tace "Ina jin ki Sophie" Safiyyah tace "To naji kin yi shiru" Khaleesat ta daga kai ta kalli Aunty Farida dake kallonta, goge hawayen dake makale idonta tayi cikin sanyin murya tace "Daxu Mom dinsa suka zo za su amshi kudin, ni kuma bazan iya transfer ba kuma bani da Atm card, shi ne ta ajiye min account number wai in tura masu kudin yau, and today is Friday, mun je banki sun tashi, yanxu tace zata dawo gobe da safe idan ban tura mata kudin ba" Safiyyah dake ta sauraron Khaleesat cikin bacin rai tace "Allah ya sauwake, ke kiji wani tsiya don girman Allah, akan miliyan tara ne ko goma uwar ta kamo hanyar gidan ku da kanta? Can you imagine fa? A'a gaskiya sai yanxu nake sake tabbatar da su Abdul were once poor in this life, all of a sudden kawai Allah ya basu arziki sama ta ka, nobody can change this my perspective wallahi, banda tsiya meye kuma miliyan Goma a irin yanda suke show casing arzikinsu, what is 10M to them? wannan ai abun kunya ne a garesu, Ke kuma maimakon ki kirani tun daxu ki gaya min shi ne kika yi shiru? Yanxu ba don Housemate dinki yayi reason cewar dole sai da sufficient fund a account dinki za ki iya tafiya ba da shiru zaki yi kenan sai gobe da za mu tafi ki gaya min? Allah ya sauwake, ita kuma uwar Abdul wallahi matsiyaciya ce er wahala, har ta iya kamo hanyar Mariri akan kudin da ba ita ta bada ba, in kin bibiya ma ɗan nata bai sani ba ta kamo hanya, ki min sending shegen account din nata da ta bar maki" Daga haka Safiyyah ta kashe wayarta, Khaleesat ta jawo handbag dinta tana goge hawayen da ya taru idonta, ta bude jakar ta ciro takardan account details din da Mom din Abdul ta bar mata, tura ma Safiyyah account din tayi ta message sannan ta mayar da jakar ta ajiye ta koma ta kwanta, ita dai Aunty Farida bata ce komai ba don duk ta fahimci conversation din nasu. Washegari Khaleesat na idar da sallan asuba kiran Safiyyah ya shigo wayarta, tayi picking call din ta kai kunne, a hankali tace "Good morning Safiyyah" Safiyyah tace "How was ur night?" Khaleesat tace "Alhamdulillah" Safiyyah tace "Na tashi yanzu naga Housemate dinki ya tura min receipt din 10M da ya tura a account din da kika turo min jiya, he sent the receipt via my WhatsApp, ba ki yi activating WhatsApp dinki ba da sai in tura maki ki tura masu, sai su san su ne matsiyata" Kasa cewa komai Khaleesat tayi hawaye ya fara sauka idonta, Safiyyah tace "Ko kuma bari in tura ma Aunty Farida receipt din kawai since she is on WhatsApp" Khaleesat ta gyada mata kai da kyar tace "Nagode" Safiyyah tace "Kuka kike yi ko? Kina da aiki, ni dai sai anjima, make sure ki fito gida da wuri kin san Flight dinmu zuwa Abuja karfe daya ne" Daga haka Safiyyah ta katse wayar, Umma na kallon Khaleesat tace "Wai me ya faru?" Khaleesat na share hawayen da yaki tsaya mata tace "Ta ce ya tura masu kudin ne, zata tura ma Aunty Farida receipt" Shiru Umma tayi ta rasa abun cewa, kana ganinta kasan jikinta yayi sanyi sosai, Aunty Farida dake zaune kan darduma tace "Allah Ubangiji ya saka masa da alkhairi ya kare sa sharrin masu sharri, Allah ya mayar masa da dubban abinda ya kashe maki, yanda ya rufa maki asiri Allah ya rufa masa shi ma" a hankali Umma tace "Ameen ya Allah" Mikewa Khaleesat tayi don dama ta gama azkar din da take yi, ta kwanta kan gadon Umma har sannan hawaye yaki dena sauka idonta. Da safe wajen karfe tara Aunty Farida na bude WhatsApp dinta taga Receipt din da Safiyyah ta tura mata, tana kallon Khaleesat tace "Yanxu ta ya za a tura masu receipt din su gani Khaleesat?" Umma tace "Ba kina da number Abdul din ba? Ki tura masa ta WhatsApp din kawai" Khaleesat dake cin wainar da Umma ta sa aka siyo mata ta daga kai ta kalli Umma, sai kuma ta girgiza kai a hankali tace "A'a Umma kar a tura masa, ba sun ce za su zo da safe ba, in sun zo sai a nuna masu receipt din" Umma tace "Saboda me? Ba kudinsa bane kuma shi ya aiko su karbar masa?" Aunty Farida ta kalli Umma tace "Suka aiko kansu dai Umma, don Abdul dai a yanda yake ji da kansa bazai ce a zo a amsar masa miliyan goma ba, dama sun san da kudin kuma kilan sun san bazai ce zai amsa ba shi yasa suka taho su amsa" Khaleesat tace "Shi yasa nace kar a tura masa receipt din, don nasan ba shi yace su zo ba" Umma tace "To ko ma dai yaya ne ai kudinsa ne, ni bana son su sake dawo mana nan su mana tijara makota na ji shi yasa nace a tura masa kawai, idan yaso sai yayi ma uwar tasa magana tunda zai ga a account dinta aka tura kudin ai, tonan asirin bai ishe mu bane da har za mu sake yarda su dawo gidan nan" a hankali Khaleesat tace "Umma ni bana son abinda zai sake hadamu magana da shi balle har yace zai dawo da wata magana kuma" Aunty Farida tace "Ya dawo da wani magana? Saboda ba shi da hankali zai dawo da wata maganar? Ai yanxu ba mu da abinda zai sake hadamu da shi da ya wuce kudin nan nasa, saki uku ya aiko maki balle ace zai dawo da wata magana" Khaleesat ta sauke idonta kamar bazata ce komai ba sai kuma cikin sanyin murya tace "Aunty ba fa shi ya aiko da takardan sakin nan ba, ba rubutunsa bane, iya saki daya yayi min" Daga Aunty Farida har Umma kallonta suka dinga yi, a hankali tace "Shi yasa bana son a tura masa receipt din balle har hankalinsa ya dawo kan mu..." Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya bayan kusan minti daya tace "To Allah ya kyauta, yanxu su suka rubuto takardan suka aiko kenan? To su dai suka sani Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi gare mu da ke baki daya, idan sun kwaso kafa sun sake dawowa sai a nuna masu receipt din" Umma dai bata ce komai ba don bata ma san me zata ce ba. Meemah na bacci Momy ta shigo dakinta wajen karfe goma na safe ta tasheta tana mika mata wayar hannunta, Meemah ta amshi wayar tana kallon screen din, sai kuma ta kalli Momy tace "Kudin suka sako?" Momy ta tabe baki tace "Gashi kuwa kina gani, nima yanxu naga alert din ashe tun daren jiya aka sako" Meemah tace "To a gidan uban wa ta samu ta turo bayan tace bata yin transfer kuma bata da Atm card" Momy tace "Ke baki ga sunan wanda ya turo kudin ba? Ai ba ita bace ta turo" Meemah ta kara kallon wayar da kyau taga sunan namiji, taɓe baki tayi tace "To wai ke Momy da nake ce maki iskancinta ta dinga yi da maza a Amurka kin zata wasa nake? Ai ba abun mamaki bane don kin ga ta samu wanda ya turo miliyan goman, harkar iskancinta kawai ta dinga yi a Amurka da 'ya yan masu kudi, kuma karya take babu miliyan goman nan a account dinta wallahi, to dai gashi nan daya daga farkanta ya turo kudin nan take" Momy tace "Oho dai koma wa ya turo kudin ta matse masu can, ni dai ba na amshi kudin ɗa na ba, da ban yi haka ba har a tashi duniya in dai Abdul ne wallahi bazai yi maganar kudin nan ba, kin ga da shikenan sun ci bulus, to ni da na haifesa ba asararriya bace da zan yarda ya bar masu makudan kudaden nan" Meemah tace "Wallahi Momy ni so nayi mu ce sai sun biya kudin sponsoring dinta da Abdul yayi, ke kinsan nawa Abdul ya kashe akan yarinyar nan kuwa? Wallahi idan na fara maki lissafi sai kin rike baki don mamaki, kudade ne ba na wasa ba da, duk kanta dukiyarsa ya dinga tafiya kamar kin masa baki, yaushe rabon kiji Abdul ya siya wani asset nasa ya ajiye? Tun da ya hadu da tsinanniyar yarinyar nan ya dena yi ma kansa komai sai dai yayi mata, ranan a gabana ya siya mata Abaya har biyu ko wanne dubu dari da hamsin, nayi masa magana ya nemi ya min rashin kunya cikin jama'a, handbag din nan shegiya sai Abdul ya siya mata na dubu kusan dari har fin haka, komai designer yake siya mata, suturu kam yayi mata ba iyaka, to wai ko monthly allowance da yake tura mata a kasar Amurka in kika ji sai hankalin ki ya tashi, uwa uba a zo kan kudin makarantar ta da House rent" Momy tayi mitsi mitsi da ido cikin bacin rai tace "Don Allah ki bar wannan maganar don raina baci yake Meemah, su je kawai Allah ya isa, ni da nake uwarsa ma sai ya ga dama yake siya min abu, to yanxu ko ce masu muka yi su biya a ina suka ga kudin biya Meemah? Ko gidan da suke ciki suka ce za su siyar wallahi karkari yayi dubu dari biyar, kai ni dubu dari biyar din ma bazan siya wannan kangon ba wallahi, kin ga kuwa gwara a bar zancen kawai, baki ji yanda raina ya baci ba wallahi, kawai Allah ya isa zan ta ja masu a kan uban kudin da Abdul ya kashe ma yarinyar kuma ba wai don bani da kudin maka su kotu ba...." Meemah tace "Ko kuma mu je duk mu kwaso kayan da ya dinga siya mata da jakunkuna masu tsada" Momy tace "Ki ci uwar me da su? Kema dai wallahi, shekara 38 ban san yaushe zaki yi hankali ba Meemah, Allah ya isan dai shi ne dai dai su, don babu abinda za mu ci da kayanta, tunda muka samu miliyan goman ma ai mun gode Allah" Meemah ta tabe baki ta koma ta kwanta tace "Kuma kin san wani abu Momy, da Abdul yana kasar nan har yanxu zai fa iya waiwayanta idan asirin ya sakesa, don wallahi masifaffen so yake ma shegiyar ke har yanxu baki gane ba, ji fa kafin su bar kasar yanda ko magana baya yi ma mutane a gidan nan, kullum zaka gansa babu walwala" Momy ta hade rai tace "Ni kuma ga er iska sai in sakankance har asiri ya sakesa ko? Ai da gangan na sa uban ya tafi da shi business trip din da za shi china, da biyu na takura uban su tafi tare don naga take takensa, ga sabon tijaran da na lura zai fara mana, kuma ko ba komai ai kinga za su dade a can kan su dawo, ni kuma kafin nan na sa anyi aiki sosai ya mance da wata shegiya wai ita Khaleesat a duniyar nan, sai kuma in tanadar masa mata er gidan mutunci, yana dawowa sai biki kawai" Meemah tace "Da dai yafi kam, yana dawowa yayi aure, ki sama masa yarinya dai dai class dinsa ba er talakawar da ya nace ma ba, ni wallahi ban zata talaucin iyayen yarinyar nan ya kai haka ba, har muka dawo gida na kasa cire view din gidan a idona, wannan ko karen gidanmu aka ajiye a gidan nan ai sai yayi rashin lafiya a bar mu da kashe makudan kudi zuwa veterinary balle ace mutum, to yanxu da bai rabu da ita ba haka wataran abu zai kama ki kwashi kawayenki da abokan business aje gidansu yarinyar? Misali ace ubanta ko uwarta wani ya mutu, haka za a kwasa aje masu gaisuwa wannan gidan?" Momy tace "Ai Abdul ya so ja min abun kunyan da bazai taɓa goguwa ba, ya so tona min asiri a idon duniya amma Allah ya rufa min asiri ya takaita abun, da irin rainin da Abdul zai ja min sai Allah wallahi, to ni dai tunda na samu aka rabu lafiya ai sai su bi wani sarkin kuma" Meemah tayi dariya tace "Kuma da bai saketa ba fa sai ya iya canza masu wani gidan don ba hankali garesa ba, tunda don yayi ta ma shegiyar yarinyar bauta Allah ya halitto sa" Wani shegen kallo Momy tayi mata sannan ta juya ta fita daga dakin. Khaleesat na durkushe gaban Umma dake mata addu'an Allah ya kai ta lafiya, ya bata sa'an karatun ta, ita dai Khaleesat kanta na kasa duk jikinta a sanyaye, a hankali Umma tace "Ki kula da kanki don Allah, duk da na yarda dake Jiddah amma ki kara taka tsantsan, kar ki mance tarbiyar da muka maki, kuma ki rike addu'a da azkar, Allah ya kare min ke ya tsare ki duk inda zaki shiga..." Nenne ce ta bude labulen dakin a fusace tace "Yau naga jaraba wajen Zahra'u, sai me motar yayi zuciya ya ja motarsa ya wuce ne ko yaya? Duk daren jiya da wayewar garin yau baki sakata gaba da duk wani zancen da zaki mata ba sai yanxu da motar da zai kai ta iyapot ya iso, haba Zahra'u ya ki ke haka ne? Ko dai maidata ciki za kiyi?" Aunty Farida ta wani kalle Nenne tace "To kyauta zai kai ta airport din da bazai jira ba, naga dai kudi zata basa Nenne" Nenne tace "Ai ba motar ubanta bane da zata shanya sa a rana don zata basa kudi, kuma shi ba boyi boyinta bane da zai ta tsayuwa yana jiranta a rana kamar ɗan iska, tunanin ku kenan 'yan Adam, don zaka ba mutum kudi sai aka ce ka walakantasa? Ka ki darajasa?" Aunty Farida taki tanka Nenne, Umma na kallon Khaleesat tace "Tashi ki je Jiddah, Allah ya tsare ya kai ku lafiya" A hankali Khaleesat tace "Ameen Umma" Daga haka ta mike ta dau handbag dinta don duk an fitar da akwatunan ta kofar gida, Nenne na kallon Umma tace "In ji dai duk an saka mata doya da dankalin da na kawo mata a akwatin nata?" Da sauri Aunty Farida tace "An saka komai" Nenne tace "Wake da su albasa da garin masara da na alkama fa?" Aunty Farida tace "Har su an sa" Nenne tace "To mu je" Khaleesat ta bi bayan Nenne suka fita daga dakin, Aunty Farida ta kara tura doya da dankalin da Nenne ta kawo da su garin alkama da Masara a bayan kyaure ta boye yanda Nenne bazata gani ba ko ta dawo dakin, daga nan ta bi bayan su, kasa daurewa Umma tayi ta mike ita ma ta fita, su Mama Zubaida da Mama Shatu na tsaye tsakar gida duk suka bi Khaleesat da kallo, Kana ganin fuskokinsu kasan babu farin cikin komawa Amurka da Khaleesat zata yi, Yaron Mama Zubaida ya nufo Khaleesat da gudu yana mika mata kudin hannunsa yace "Wai gashi inji Ummanmu da Mama Shatu ki sha ruwa a hanya" Nenne ta karbe kudin a hannun yaron ta kirga taga dubu biyu ne, sokesa tayi jikin haɓar zaninta tace "Ta gode" Daga haka ta kalli Khaleesat tace "Mu je" Khaleesat tayi ma kishiyoyin ummanta sallama sannan ta bi bayan Nenne suka fita daga gidan Aunty Farida na biye da su, a kofar gidan Khaleesat ta kara sallama da Babanta don bai fita kasuwa ba ranan yana jiran tafiyarta, kasa hada ido tayi da shi yana mata addu'a da fatan alkhairi, Nenne ta bude mata bayan motar tace "Ni dai shiga don Allah, tun jiya basu san da addu'an su ba sai yau da kike sauri salon jirgi ya tafi ya bar ki" Khaleesat ta shiga motar Nenne ta kulle, haka kawai Khaleesat taji hawaye ya cika idonta, ta daga masu hannu kawai sannan drivern ya ja motar suka bar kofar gidan. Ko da Khaleesat ta isa airport ta tarar Safiyyah na ta jiranta don tun daxu ta iso airport din, Khaleesat ta amshi boarding pass dinta suka nufi Departure Lounge, bayan minti ashirin jirginsu ya tashi zuwa garin Abuja, inda a nan za su hau jirgin da zai kai su kasar America. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 57 Tun da suka sauka Amurka wajen karfe hudu na asuba gaba daya walwalar Khaleesat ya bace, ta dawo so silent kamar mara lafiya, cikin rashin kuzari ta dinga yin komai har suka gama da custom da Immigration, Safiyyah na kallonta tace "Wai duk sanyin ne yasa kika dawo haka? Naga mood din ki ya canza all of a sudden, are you okay?" Khaleesat tayi murmushin karfin hali ta girgiza mata kai kawai tana gyara Jacket din jikinta don tun a kasar da suka yi transit duk suka saka Jacket din su saboda sanyi, Safiyyah na kallon wayar hannunta ganin kiran Mustapha for the 4th time tace "Shi kuma wannan daga sauka ko kashe jirgin ba ayi ba ya fara doka min kira kamar jira yake, kilan kewan fadan da muke yi da matarsa kullum yake yi, bai san i came fully ready for her ba, don this time around bazan sake tolerating nonsense dinta ba wallahi" Khaleesat dai murmushi kawai tayi bata ce mata komai ba har suka fita daga Arrivals, Safiyyah tace "I don't want us to stress ur Housemate, naga message dinsa tun muna Abuja yana tambayar karfe nawa za mu taso kuma a ina za mu yi transit, kilan da na gaya masa zai iya estimating time din da za mu iso ya zo yayi picking din mu daga airport cikin azababben sanyin nan da ake, shi yasa kawai ban masa reply ba kar muyi inconveniencing dinsa" Khaleesat ce ta fara hango Ya Mustapha tsaye jikin motarsa kafin Safiyyah ma ta gansa tayi kasa da murya tace "Sai kin ga yanda ya addabi Dad din mu wai an koma makaranta naki dawowa, sai kace zaman jin dadi nake yi a gidansa da shegiyar matar nan tasa" Khaleesat ce ta fara gaida Mustapha bayan ya iso inda suke tsaye, ya amsa da fara'a yace "Ya hanya Khaleesah?" Khaleesat tace "Alhamdulillah" Safiyyah ma ta gaishesa ya amsa sannan suka nufi motar sa gaba daya, ya amshi trolley dinsu ya saka a booth din motar yace "Kun ji sanyin America ko, don ma yau babu snow" Khaleesat dai tayi murmushi, Safiyyah ta bude mata back seat tana kallonta, Khaleesat ta shiga sannan Safiyyah ta zaga ta bude gaban motar ta shiga ita ma, Mustapha ya tada motar bayan sun bar Airport din ya kalli Safiyyah yace "Amma dai Khaleesat won't be going to her apartment now, zai fi kyau mu je can gidana idan ta huta sai ta koma Apartment dinta anytime she is ready" Safiyyah tace "Dama gidan ka zaka kai mu gaba daya mana, cikin sanyin nan ta ina zata je ta fara gyaran apartment dinta ga gajiyar hanya" Ko da wasa Safiyyah bata ba Mustapha labarin abinda ya faru da Khaleesat ba, ita dai Khaleesat tayi shiru a bayan motar tana tunanin another new life that she is going to begin in America with her burden on people's shoulder, shikenan ita kuma daga wannan ya dau responsibility dinta sai wannan ya dauka, sosai tunanin nan ke kara kashe mata jiki, gashi rayuwar America ba dai tsada ba, kawai tasan takura Housemate dinta zata yi da burden dinta, a haka suka isa gidan Mustapha da tunani iri iri a ranta, bin unguwan ta dinga yi da kallo don bata san unguwan ba, sati biyu da fara exams dinsu Last semester Safiyyah ke gaya mata Mustapha ya amshi wani apartment da ya fi wanda suke ciki girma za su tashi a gidan da suke, ita dai har suka bar America bata san gidan da suka koma ba, bayan Mustapha yayi parking suka sauka a motar Safiyyah ta bar sa da shigo masu da kayansu ta kama hannun Khaleesat zuwa cikin gidan, ita dai Khaleesat bin ta kawai take, upon yanda ta tsani duk abinda zai hadata da gidan Mustapha saboda matarsa sai gashi yau saboda rashin option da choice ya sa ta amince da zuwa gidansa babu ko musu, zaune suka tarar da matarsa a parlor ta sha uban rigan sanyi ga daurin dankwalin ture kaga tsiya da tayi da zaninta, sosai jikin Khaleesat yayi sanyi ta rakube jikin kujera tana kallonta ta gaisheta, amma matar nan ta dinga kallon TV tana cin popcorn kamar bata ji Khaleesat ba, Safiyyah dama ko kallonta bata yi ba ta nufi hanyar dakinta ta murda taji a kulle kuma babu makulli a jikin kofar, tsaye tayi fuskarta babu yabo babu fallasa tana jiran Mustapha ya shigo gidan, bayan yan sakwanni sai gashi ya shigo parlon da akwatuna biyu, Safiyyah tace "Yaya ina makullin dakina?" Ya karasa ya murda kofar yaji a kulle, ya dawo parlor yana kallon Surayya yace "Surayya ina makullin dakin can yake?" Sai a sannan Surayya ta juya ta wani kallesa tana ci gaba da cin popcorn din hannunta tace "Makullin daki? Ban gane Makullin daki ba, Ajiyar makulli aka bani da za a tambayeni?" Safiyyah dake ta kallon Ya Mustapha tana huci tace "Kai dama yaya da ka wani ishi Daddy da kira cewar mun koma makaranta in dawo a saman roofing din gidan nan kake da niyyar ajiyeni tunda gashi an dauke makullin dakin an boye? Wannan ai iskanci ne da walakanci, mutum yayi dogon tafiya haka ya dawo kuma yaga an dauke masa makullin daki?" Mustapha ya karasa kusa da Surayya da sauri yace "Ke Surayya ko dai Aslam yana wasa ya cire Makullin dakin ne a jikin kofar?" Surayya taki ko kallonsa, Safiyyah ta wani tsuke fuska tace "Aslam ne tsayinsa zai kai har ya cire makulli a kofar daki? Ai sai dai Uwar Aslam, kuma Allah ya so ban bar komai da za a sace min a dakin ba sai takardu, tunda an saba min satan dama" Mikewa Surayya tayi tana mata wani tsinannen kallo tace "Keeee, in kina cin kasa ki kiyayi ta shuri, wallahi ki iya bakin ki don ni ba sa'ar ki bace ki kiyaye ni, in kika yi wasa za ki sha mamakina yanxun nan" Safiyyah tayi wani dariya tana tafe hannu tace "Osheyy ancient of days, ashe dai ke ba sa'a ta bace, ai sai yau kike gaya min nake ji, kuma in kin fasa bani mamaki sunanki ba Surayya ba, shege ka fasa tsakanin ni da ke" Fada Mustapha ya fara yi yana cewa "Meye haka? Ko kuna hauka ne? Wannan wani irin iskanci ne? A gaban nawa ku ke wannan rashin hankalin?" Magana yake yi at the same time yana kai kawo yana dube duben makullin dakin Safiyyah a parlon, Ita dai Khaleesat na rakube jikin kujera taji kanta har ya fara mata wani azababben ciwo, banda rashin option me zai kawota gidan nan ita kam, tunanin hakan yasa ta ji hawaye ya cika idonta, Safiyyah sai girgiza kafa take tana hararan Surayyah da ta koma ta zauna tana cin Popcorn dinta tana gyara daurin ture kaga tsiyan dake kanta tana kara cokarosa gaba, Mustapha ya karasa inda Aslam ke kwance yana bacci a parlon ya fara tashinsa yana tambayarsa makullin dakin Safiyyah, yaron da ko shekara biyu bai karasa ba, a fusace Surayya tace "Wallahi kar ka tada min yarona Mustapha, shi yasan maka wani makulli da zaka tashesa yana bacci" Mustapha ya juya ya kalleta yace "Surayya in ke kika dauke makullin nan ki fito da shi bana son rainin hankali" Surayya ta wani hararesa tace "Kar ka bata min rai this early morning, in dau makulli inyi uwar me da shi? Plss do not provoke me Mustapha" Tana kai wa nan ta mike ta figi yaronta dake bacci ta nufi dakin ta da shi, Mustapha ya kasa cewa komai ya bi ta da kallo yana rike da waist dinsa, can ya juya ya kalli Safiyyah dake masa wani mugun harara kamar zata kwadesa, karasawa yayi kusa da ita yace "Look Safiyyah...." Katse sa tayi a fusace tace "Babu abinda zaka gaya min Yaya, Don't tell me anything, dama don matarka ta min wannan walakancin ya sa ka dage sai na dawo an koma makaranta, wallahi ni dai Daddy zan kira a samar min wani gidan da zan zauna in karasa final year dina kawai in peace, don bazan iya zama da wannan devil wife dinka a gida daya ba" Kamar zata yi kuka ta kare maganar, Mustapha bai iya yace mata komai ba, can dai ya nufi hanyar dakinsa don daki uku ne a gidan, yana shiga dakin ya dau duk abinda zai bukata ya fito da shi parlor ya ajiye yana kallon Safiyyah yace "Ga bedroom dina can ku shiga" Safiyyah na jin haka ta figi hannun Khaleesat zuwa dakin nasa, da sauri Surayya ta fito daga dakinta don bata kulle kofar dakin ba saboda ta dinga jin abinda za ace a parlon, tana kallonsa da wani irin mamaki tace "Ban gane ga Bedroom dinka can su shiga ba Mustapha, turakar namu za su shiga kake nufi ko me?" Safiyyah ta kwashe da wani dariya har da kyakyatawa ta ja Khaleesat suka shiga dakin sannan tayi banging kofar ta kulle, Surayyah zata yi magana Mustapha ya ɗaga mata hannu fuska a murtuke alamar baya son jin komai sannan ya fice daga parlon zai shigo da sauran akwatunan su Safiyyah, Khaleesat da duk jikinta yayi sanyi ta dinga kallon Safiyyah tace "Haba Sophie, this isn't proper mana, why not mu zauna a parlor har san da za a ga makullin dakin naki, dakinsu ne wannan fa" Safiyyah ta mata wani kallo tace "Ai ba kowa ne ɗan iska mara zuciya kamar ki ba Khaleesat, kuma wallahi ina dakin nan babu inda zan je har sai ranan da ta fito min da makullin dakina...." Khaleesat ta kasa cewa komai don da gaske she is shock, sai ga Mustapha yayi knocking kofar dakin sannan ya ajiye masu hand luggage dinsu yace "Me za ku ci yanxu?" Safiyyah na zaune gefen gadonsa fuskarta babu walwala irin ita an bata mata din nan tace "Kawai shayi da cookies kafin gari ya waye" Yace "Ohk" Juyawa yayi ya fita daga dakin ya kullo masu kofa, har sannan Surayyah na tsaye inda take a parlor ta kasa motsin kirki, ta bi sa da kallo har ya shiga kitchen zai hado masu shayin, bata san sanda ta fashe da kuka ba tana rufe bakinta ta nufi dakinta da sauri, Mustapha ya dawo dakin nasa da Cup din shayi biyu da cookies ya ajiye masu ya fita.... Khaleesat na idar da sallan Asuba ta kwanta kasan carpet din dakin Mustapha don dakin da dumi saboda room heater dake kunne, amma hakan bai hanata dinga jin sanyi ba saboda wankan da tayi, babu yanda Safiyyah bata yi da ita ta kwanta saman gado ba amma Khaleesat taki tace kasan carpet din ya isheta, wayar Safiyyah ya fara ring, ta mike ta dauko handbag dinta ta ciro wayar, kallon Khaleesat tayi tace "Housemate dinki ne ke kira" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, Safiyyah ta zauna gefen gado sannan tayi picking call din tayi masa sallama tare da gaishesa, daga daya bangaren yace "How are you, naga baki yi replying message da na maki ba tun jiya" Safiyyah tace "Kawai bana son inyi stressing dinka ne probably kace zaka zo picking din mu a airport" Yace "Kuna ina yanxu?" Safiyyah tace "Muna gidan yayana, ga Housemate din ka nan, let me give her the phone...." Calmly yace "Ohk..." Safiyyah ta mike ta tafi inda Khaleesat ke kwance ta durkusa tana mika mata wayar, Khaleesat ta kasa amsan wayar, har sai da Safiyyah ta kai mata wayar kunne, daga daya bangaren Khaleesat taji yace "Halysaah...." Kasa ce masa komai tayi, lokaci daya taji hawaye masu zafi sun fara sauka idonta, a hankali yace "Can you hear me?" Muryarta na rawa da kyar tace "Uhm" Shiru yayi, after some seconds yace "I will come over later in sha Allah" Ta gyada masa kai kamar yana ganinta, kashe wayarsa yayi, ta ajiye wayar wasu hawayen na sauko mata, ita dai Safiyyah bata ce mata komai ba. Karfe takwas na safe Safiyyah ta fito daga dakin Yaya Mustapha zata je kitchen ta duba menene available da zata girka masu ita da Khaleesat, ga mamakinta sai taga an ajiye makullin dakinta kan Centre table din parlon, dariya ma abun ya bata, ta karasa ta dauki makullin sannan ta koma dakin ya Mustapha da sauri ta kulle kofar, dariya ta dinga babbakawa Khaleesat na kallonta, tana nuna ma Khaleesat makullin hannunta tace "Kin ga er iskar ta ajiye min makullin kan Centre table saboda taga na tare dakin mijinta, ashe karamar er iska ce ita ban sani ba? ai wallahi boyewa zan yi inyi kamar ban gani ba don ni kam naga dakin zama..." Safiyyah na fadin haka ta bude zip din akwatin ta ta cusa makullin ciki, Khaleesat dake ta kallonta ta girgiza kai tace "Don Allah tunda har ta ajiye maki makullin kiyi hakuri mu koma dakin ki Sophie" Safiyyah tace "Wallahi bazan koma ba for now, next time in ance ta boye min makulli bazata boye ba, ba tace ita er iska bace ni kuma zan nuna mata er daba ce ni, ina nan dakin sai naga abinda ya ture ma buzu nadi" Murmushi kawai Khaleesat tayi bata ce komai ba, Safiyyah ta kyalkyale da dariya tace "To ni ba na manta ke buzuwa bace" Khaleesat tace "A'a ni bafillatana ce, babana bafillatani ne" Safiyyah tace "To Umma fa?" Murmushi kawai Khaleesat tayi bata ce mata komai ba, Safiyyah ta nemi waje ta zauna tace "Ke kiji rashin kunya kiri kiri ta ajiye min makulli kan Centre table da taga ba sarki sai Allah, to da menene nufinta da ta boye makullin in koma garage da zama ko me?" Knocking kofar dakin aka yi Safiyyah ta mike ta bude taga Mustapha tsaye ya shirya alamar zai fita aiki yace "Zaki fito ki yi maku breakfast ne?" Safiyyah tace "Har yanxu duk jikina ciwo yake min wallahi Yaya" Yace "Toh bari ayi maku order" Ta gefen ido Safiyyah ke kallon Surayya da ta fito parlon daga dakinta idonta akan Centre table wato tana duba makullin da ta ajiye, Surayyah ta kalli Mustapha tayi mitsi mitsi da ido tace "Mustapha bayan Aslam ya tashi bacci na tambayesa makullin shi ne ya dauko min wani toy dinsa ashe ciki ya zura, na samu da kyar na ciro makullin sannan na fito na ajiye mata kan Centre table 30 minutes ago, to kaga dai yanxu babu makullin kan Centre table din sannan bata fito daga dakin ka ba, me hakan ke nufi??" Mustapha ya kalli kan Centre table din, can ya kalli Safiyyah da ta hade rai tana rike da waist dinta yace "Safiyyah kin dau makullin ne?" Safiyyah ta wani kallesa tace "Ban gane na dau makullin ba Yaya" Cikin daga murya Surayyah tace "Wallahi in baki fito min daga dakin miji ke da shegiyar kawarki ba duk abinda na maku ku kuka ja ma kan ku a gidan nan" Safiyyah tayi wani dariya tana tafe hannu tace "Toh ni kuma dakin yayana ne, ita kuma Khaleesat dakin yayan kawarta ne, kin ga kuwa baki isa ki ce mu fito ba bayan bamu da wani dakin da za mu zauna in mun fito" Rungume hannu Mustapha yayi yana kallonsu ya kasa cewa komai, Surayya ta yo kan Safiyyah a fusace Mustapha ya tareta yace "Kee baki da hankali ne??" Safiyyah tayi wani shewa tace "Ka kyaleta dai ta zo ta taɓa ni zan nuna mata da sabon dabanci na dawo daga Nigeria, wallahi sai na tuge mata gashin kanta gaba dayansa, ta zo ta taɓa ni ta ga ikon Allah" Khaleesat dai tayi tagumi duk jikinta a sanyaye tana jin su, Surayyah ta fashe da kuka tace "Wallahi Mustapha zan bar maka gidan nan kai da Safiyyah ku zauna don bazan ci gaba da zama da matsiyaciyar ba a gida daya, sai dai ka zaba ko ni ko ita a gidan nan" Safiyyah tace "Ke din banza, minti nawa ne ya canza ki amma ni bazai taɓa canza ni ba tunda jininsa ce ni, ke kuwa tsaf zai iya sakin ki ya auro wata" Surayya tayi wani kukan kura zata cafko Safiyyah, Mustapha yayi saurin riketa ya ja ta zuwa dakinta yana masifa kamar zai ari baki, Safiyyah ta koma daki ta dinga babbaka dariya har da rike ciki, Khaleesat dai sai kallonta take ta kasa cewa komai, after a while Mustapha ya sake knocking dakin, Safiyyah ta fito ta wani kauda fuska tana jiran jin abinda zai ce, nan ya fara lallabata yana cewa "Pls Safiyyah in dai kin san kin dau makullin kiyi hakuri ki kyaleta ki koma dakin ki, don ni zaki yi ai ba don ita ba, kin ga i am almost late for work, don Allah in kin dau makullin kiyi hakuri ko koma dakin ki" Safiyyah taki cewa komai tana girgiza kafa daya, haka ya dinga lallabata daga karshe ta kallesa tace "Na ji, amma wallahi ka ja mata kunne da kyau ta fita sabgata a gidan nan idan ba haka ba za mu yi batattciya da ita, don jahilci zan dinga nuna mata iri iri wallahi" Mustapha yace "Na ji, i will talk to her" Juyawa Safiyya tayi ta koma dakin, shi dai ya koma parlor ya tsaya yana jiran yaga fitowar Safiyyah. Khaleesat felt relieve bayan sun koma dakin Safiyyah, sai sannan ne ma ta samu bacci ya dauketa don kasa bacci tayi a dakin Mustapha. Wajen karfe uku da rabi na yammacin ranan Safiyya ta dau wayarta dake ringing sai kuma ta kalli Khaleesat tace "Housemate din ki ne, kilan ya zo ne, tun daxu yace in tura masa location ta WhatsApp" Tana fadin haka tayi picking call din ta kai kunne tare da yi masa sallama, after few seconds tace "Ohk to" Daga haka ta katse wayar tana kallon Khaleesat tace "Yana waje" Ita dai Khaleesat ta kasa dago kanta ga wani faduwa da gabanta yayi. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 58 Safiyyah ta gama saka Jacket dinta da neck warmer tana kallon Khaleesat da ta kasa tashi daga inda take zaune tace "C'mon Khaleesat, yana fa waje yana jira, and the weather is very cold outside, don Allah ki tashi mu je" Da kyar Khaleesat ta tashi tana jin bugun zuciyarta na tsananta ta dau Veil din Abayan jikinta ta yafa kanta a hankali, gaba daya jikinta a sanyaye yake don bata san ta yaya zata fara hada ido da Jay ba, Safiyyah na kallonta tace "Baza ki saka rigar sanyin ki ba?" Khaleesat ta girgiza mata kai kawai, Safiyyah tace "Saboda room heater ne fa yasa kike jin kamar ba sanyi sosai a garin, amma wallahi azababben sanyi ake a waje idan kika fita" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba don bata ma san me Safiyyah ke cewa ba, duk tunaninta ita dai da wani idon zata kalli Housemate dinta, Safiyyah ta tabe baki ganin Khaleesat taki tanka mata kamar ma bata san me take cewa ba, Safiyyah ta nufi kofa Khaleesat ta bi bayanta tana tafiya a hankali kamar mara lafiya, a haka suka fito parlor, Safiyyah bata ko kalli Surayyah dake zaune parlor tana ba yaronta abinci ba ta nufi kofar fita, ita dai Khaleesat na bin ta a baya walking slowly fuskarta dauke da damuwa, Surayyah ta bi su da wani shegen kallo har suka fita daga parlon, Khaleesat na hada ido da Housemate dinta dake jingine da motarsa ya rungume hannunsa taji wani kuka na neman taho mata from no where, amma ta dake ta sunkuyar da kanta tana biye da Safiyyah har suka iso dai dai inda yake tsaye, sau daya ya kalli Khaleesat ya dauke idonsa ya mayar kan Safiyyah dake gaishesa, ya amsa gaisuwanta da murmushi fuskar sa yace "Ya hanya?" Safiyyah tace "Hanya Alhamdulillah" Ita dai Khaleesat gefe ta koma ta tsaya har sannan ta kasa hada ido da shi tana wasa da veil dinta, nan kuma daurewa kawai take kar ta fashe da kukan dake cin ta, bayan sun gama gaisawa da Safiyyah, ya juya ya kalli Khaleesat for the second time, calmly yace "Housemate" Kamar jira take ta fashe masa da kuka sosai, ya sauke idonsa yayi shiru, after some seconds... walking slowly ya karasa har inda take tsaye yayi kasa da murya yana kallonta yace "Ina Jacket din ki?" Ta kasa cewa komai tana kuka a hankali tana girgiza masa kai, cire tsadadden rigar sanyin jikinsa yayi yana kallonta ya zaga ta bayanta yace "Wear this, the weather is cold" Ta gyada masa kai kawai wasu hawayen na sauka idonta ta amshi Jacket din nasa ta saka, lokaci daya kamshin turarensa da ta dade bata ji ba ya cikata ta ko ina ga kuma warmth din jikinsa from the Jacket, ji tayi kamar an yaye mata duk wani damuwar dake tunkushe a ranta, Ita dai Safiyyah na tsaye tana kallonsu, har cikin ranta take jin tausayin Khaleesat don tana jin ta ne kamar er uwarta ta jinin, Jay ya cire neck warmer din wuyansa ya daura mata kan Jacket din, ita dai Khaleesat ta kasa barin su hada ido, taji daddaden kamshin turarensa na kara mata wani irin nutsuwa da relieve, Ya juya ya kalli Safiyyah yace "Za mu je tare da ke can apartment din nata yanxu ko?" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ohk, let me get her luggages" Daga haka ta juya ta koma cikin gida, ya bude ma Khaleesat gaban motarsa yana kallonta, ita dai ta kasa hada ido da shi wasu hawayen na taruwa idonta ta shiga motar ya kulle gently, after some minutes Safiyyah ta fito da akwatin Khaleesat guda biyu ya bude booth ya saka a ciki, Safiyyah tace "Let me get the rest" Daga haka ta juya ta koma cikin gidan ta dauko sauran kayan su ma ya amsa ya saka a booth, Safiyyah ta shiga back seat sannan ya zaga ya bude driver seat ya shiga, the ride was so silent ga snow da aka fara yi, after almost 20 minutes suka iso sabon Apartment din da Jay yayi renting ma Khaleesat, parking yayi a garage din apartment din yayi shiru, sai kuma ya jinginar da kansa da driver seat ya lumshe ido bayan ya tuna makullin apartment din na can gida ya bar sa, after some seconds ya ɗan shafa kansa yace "Sorry... i think na mance makullin apartment din a can gidanmu" Reverse ya fara yi bayan ya fita garage din ya dau hanyar gidansu, ita dai Safiyyah tayi murmushi kawai bata ce komai ba, dai dai sanda wayarta ya fara vibrate ta duba taga Mustapha ne ke kiranta, hade rai tayi, tayi silencing kiran sannan ta kife wayar a cinyarta, wato ya dawo yaga bata gida shi ne zai fara doka mata kira, Jay na isa gidansu yayi parking a waje ya juya ya kalli Khaleesat da tayi nisa tunanin da take, yace "Let me get the keys Housemate" Bata bari sun hada ido ba ta gyada masa kai kawai, ya bude motar zai fita, ta kalli snow din dake sauka sai kuma ta kallesa, da sauri ta fara kokarin cire Jacket dinsa dake jikinta tace "Should i give you the Jacket? Naga akwai sanyi" Ya juya ya kalleta, sai a sannan suka hada ido all this while, taji kamar kasa ya bude ta shige tayi saurin sauke idonta, ya ɗan yi murmushi yace "Don't worry, i will get another one idan na shiga gida yanxu" Daga haka ya sauka daga motar ya shiga gidansu. Bayan kusan minti goma sai ga shi ya fito daga cikin gidan yana sanye da wata rigar sanyin, Khaleesat dai kallonsa kawai take, ganin ya tsaya bakin gate din gidan nasu yana kallon direction daban yasa ta kalli direction din da yake kallo, sunkuyar da kai tayi bayan ta hango Ajay yana tahowa tare da katon karensa Legend yana rike da Leash din karen, Safiyyah tayi kasa da murya tace "That is Ajay, and ya kamata ki gaishesa gaskiya Khaleesat" Khaleesat ta ɗan kalli Safiyyah, a hankali tace "Baza ki gane ba Sophie wallahi kunya nake ji" Safiyyah tace "To ya za ki yi? Dole dai haka zaki ajiye kunyan ki sauka ki gaishe sa, ni dai nasan baxai taɓa barin Jay yayi duk wannan hidimar da yayi maki shi kadai ba, tunda kan su a hade yake, nasan dole Jay zai yi shawara da shi before anything, Kuma tare za su yi komai..." Khaleesat ta kasa cewa komai amma har cikin ranta she is so ashame of speaking to him, har yau maganganun da Abdul yasa tayi masa ta waya na yawo a kanta, Safiyyah ta hade rai ganin Ajay ya kusa inda Jay ke tsaye tace "Pls Buckle up kiyi abinda ya dace Khaleesat, ni na tsani wannan halin kauyancin da kike yi wallahi, to meye a ciki gaishesa fa kawai zaki yi, ai ko ba komai kokarin da shi ma yayi maki ya kamata ki gaishe sa, abinda ya faru ya riga ya faru so forget that and do the needful" Jiki a sanyaye Khaleesat ta kai hannu zata bude motar, amma Ajay ko kallon inda suke bai yi ba ya wuce Jay dake tsaye yana jiransa yayi shigewarsa cikin gida, Jay ya bi bayansa, a sanyaye Khaleesat ta fasa bude motar ta juya tana kallon Safiyyah, Safiyyah ta sauke wani ajiyar zuciya tace "He is still angry at what you did to them, nasan zai huce definitely" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, after some minutes sai ga Jay ya fito daga cikin gidan ya bude driver seat ya shiga yace "Sorry for keeping u waiting, makullin apartment din na aljihun jacket dina ne, and Ajay wore the Jacket out for a walk" Safiyyah na murmushi tace "It's fine" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, wajen karfe biyar da rabi suka iso sabon Apartment din, ya kashe motar yana kallon Khaleesat a hankali yace "This is ur new apartment Housemate, i hope you will love it" Daga haka ya bude motar ya sauka, Safiyyah ma ta sauka tana kallon gidan tana murmushi don sama da kasa ne, Khaleesat ta goge hawayen dake makale idonta sannan ta sauka daga motar, bude masu kofar apartment din Jay yayi ya jira suka fara shiga sannan shi ma ya shiga, yayi switching din light din parlon da Heater, Safiyyah na murmushi tana bin parlon da kallo ganin yafi na tsohon Apartment din girma tace "Waow, this is soo beautiful" Jay ya zauna kan kujera yana duba wayarsa dake vibrate alamar kira, Safiyyah ta bude kofar da ta gani a parlor taga kitchen ne, ita dai Khaleesat na tsaye bayan kujera tana kallon Jay ta kasa cewa komai, Safiyyah ta fito daga kitchen din ta nufi sama zata duba dakunan gidan, after some seconds Jay ya gama sending message din da yake a wayarsa ya juya suka hada ido da Khaleesat, sauke idonta tayi tana wasa da gefen Veil dinta, Calmly yace "Housemate" Da kyar tace "Um" Ya mike ya dawo gabanta ya tsaya yana kallonta, a hankali yace "You like the new apartment?" Ta gyada masa kai tana kokarin ganin bata fashe da kuka ba, bai sake ce mata komai ba don yana kallon fuskarta yasan kuka zata fara masa, Safiyyah ce ta sauko downstairs tace "Ya Jawwad wallahi gida yayi kyau Maa sha Allah, Allah Ubangiji ya saka da alkhairi yasa kafi haka, my frnd is really grateful ba ma ta da bakin yi maka godiya shi yasa nake magana on behalf of her, mun gode sosai, Allah Ubangiji ya kare ka da sharrin mahassada, thank you so much Housemate we are really grateful" Ɗan murmushi yayi bai ce mata komai ba, Khaleesat ta goge hawayen da taji ya silalo idonta, Safiyyah tace "Toh ni zan tafi yanxu, yayana sai doka min kira yake, ya kirani yafi sau goma ban dauka ba" Jay yace "Ohk, to bari in yi dropping din ki" Da sauri Safiyyah tace "A'a wallahi ba sai ka ba kanka wahala ba Yaya Jawwad, har nayi order din Lyft gashi nan zuwa" Yace "Ohk then, my regards to everyone back home Safiyyah" Safiyyah na murmushi tace "In sha Allah" Sai kuma ta kalli Khaleesat tace "Toh mu je ki rakani kawata" ta kama hannun Khaleesat suka fita daga parlon, suna barin apartment din Safiyyah ta kalleta tace "If you like kar ki dena wannan kukan ki bude baki kiyi masa godiya sosai, shi yasa ma nace ki rakani don nasan halinki in kika fara kuka ba lallai ki masa godiya ba, in mutum yayi kukan sau daya ba shikenan sai ya rungumi kaddara ba yayi abinda ya kamata yayi move on, amma ke kiyi ta kuka kamar me takaba, i understand you are lost of words amma kiyi composing kanki kiyi appreciating dinsa plss, wallahi ban taɓa ganin mutum with kind heart like Jawwad ba, kuma shi tsakani da Allah yake abun sa ba don komai ba" Khaleesat ta fashe da kuka muryarta na rawa tace "I don't know where to begin Safiyyah, ban san ta inda zan fara masa godiya ba, i am just confuse" Safiyyah ta rungumeta tana patting bayanta a hankali tace "I understand Khaleesat, i understand you, nasan you are confuse, but just start from anywhere, tell him anything that means appreciation zai fahimce ki" Khaleesat ta gyada mata kai hawaye masu zafi na sauka idonta, a haka Lyft din Safiyyah ya karaso, Khaleesat ta kamo hannunta da kyar tace "Thank you for everything Safiyyah, thank you for always being by my side through thick and thin, thank you for being supportive, nagode Allah ya saka da alkhairi" Tana magana hawaye na zuba idonta, Safiyyah ta hade rai tace "C'mon Khaleesat, ni kar ki sake min godiya, don na dauke ki tamkar sister din da bani da ita ne, i care so much about you" Safiyyah ta zame hannunta ta bude bayan motar ta shiga ta kulle kofar sannan ta daga ma Khaleesat hannu, kai kawai Khaleesat ta gyada mata tana share hawayen da yaki tsaya mata sannan ta juya tana tafiya a hankali ta koma Apartment din, tana bude kofar parlon Jay ya juya ya kalleta sai kuma ya ci gaba da danna wayarsa, walking slowly ta nufesa har inda yake zaune ta durkusa kasa tana kallonsa, Kafin tace komai ya dakatar da ita ba tare da ya kalleta ba yana magana softly yace "I don't want ur thanks Khaleesat, bana bukata, ba don ki gode min nayi duk abinda nayi ba, nayi ne saboda Allah, nayi ne saboda kinyi deserving in yi maki, so bana bukatar godiyan ki pls, instead ki gode ma Allah" Khaleesat ta kasa cewa komai kanta a kasa hawaye na zuba idonta daurewa kawai take kar ta fashe masa da kuka, ya mike yace "Let me show you round the house before i leave" Tana goge fuskarta ta mike ta fara bin sa tana tafiya a hankali, kitchen ya fara kai ta, ita dai tana tsaye daga bakin kofa take bin kitchen din da kallo, hatta foodstuff duk ya siya mata, fridge din kitchen din ma was fully stocked up, ga cookies kala kala a kitchen din saboda yasan tana son cookies, ta kasa daurewa bata san sanda ta kamo hannunsa ba muryarta na rawa tace "Ban san ta inda zan fara maka godiya ba...." Ya ɗan bude ido cause he never saw that coming, lkci daya yayi saurin janye hannunsa daga nata, yana murmushin karfin hali yana komawa baya ba tare da ya bari sun hada ido ba yace "Nace maki bana bukatar godiyan ki, let me show you other places" Daga haka ya fita daga kitchen din, ta jingina da kofar kitchen din bayan ya fita tana kuka a hankali, sai da tayi me isarta sannan ta fito daga kitchen din tana jan kafa da kyar, tsaye ta gansa dai dai staircase yana danna wayarsa alamar ita yake jira, yana ganin ta fito daga kitchen din ya mayar da wayar aljihunsa ba tare da ya kalleta ba yace "The rooms are upstairs" Sai da ta karaso har inda yake sannan ya fara haura stairs din ta bi bayansa, ya fara nuna mata spare rooms guda biyu, sannan ya bude kofar nata dakin, calmly yace "Ur room" Ita dai tana tsaye bakin kofa tana kallon dakin babu ko kiftawa, ba abinda babu cikin dakin nan na comfortability, duvets ma manya hudu duk sababbi cikin case dinsu ta gani a dakin, the room look so beautiful sai wani sparkling yake, a hankali ta juya ta kallesa ya sauke idonsa bai dai ce mata komai ba, sai kuma ya juya ya bar bakin kofar dakin ya sauka downstairs ta bi sa da kallo, jingina tayi da kofar dakin for almost 5 mins tana kallon cikin dakin, a hankali ta juya ta bar bakin kofar dakin ta fara sauka downstairs cikin rashin kuzari, tsaye ta gansa bakin kofar fita daga parlon, yana ganin ta sauko yace "I will take my leave now Halysaah, amma dai sai jibi zaki shiga school, cause i see you look stressed" Ta gyada masa kai a hankali, yace "Ohk, here are the apartment key" Ta karasa ta karbi bunch din makullan da yake mika mata, sai kuma ta kallesa tace "Baka cire spare key ba?" Yace "A'a ki ajiye su kawai a wajen ki" Ta gyada masa kai kawai bata ce komai ba, ya bude kofar parlon without looking at yace "Text me ur Skin care set via WhatsApp" Yana fadin haka ya fita daga parlon yace "Good night Halysaah" Tana kallo ya kulle kofar parlon, after some minutes ta ji alamar tafiyar motarsa. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Read my book "HALYSAAH" on ArewaBooks, Platform available: "app only" :: https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 59 Khaleesat ta dade rabon da tayi bacci peacefully babu abinda ke damunta a rai kamar yanda tayi daren jiya, bayan tayi sallan asuba ta sake komawa baccin don garin akwai sanyi sosai, karfe takwas da yan mintuna na safe vibration din wayarta ya tasheta daga baccin da take, ta jawo wayar a hankali tana duba me kiranta duk da tasan bazai wuce Safiyyah ba, ai ko taga ita ce, picking din kiran tayi ta kai kunne murya can kasa tace "Sophie" Safiyyah tace "Nasan kina nan kina bacci ko?" Khaleesat tace "Um, Good morning" Safiyyah tace "Morning, amma baza ki shigo school ba yau?" A hankali Khaleesat tace "Sai gobe in sha Allah" Safiyyah tace "To Allah ya kai mu, ni dai gani har na shigo school din, amma fa gobe akwai get together da za mu yi na manta ban gaya maki ba, just few of us, ba mu wuce mu sha biyar ba duka, the time is 5pm prompt" Khaleesat tace "Cikin sanyin nan za ku yi get together Sophie?" Safiyyah tace "So? Kin ga alamar sanyi na hindering daily activities din mutane a kasar nan ne in dai ba snow bane yayi mugun yawa? Beside ai ba a open space za ayi get together din ba, it will take place at one of our Course mate House" Khaleesat tace "Toh ai shikenan" Safiyyah tace "Ban gane ai shikenan ba, banda ke za ayi get together din kenan kike nufi?" Khaleesat tace "Kema kin san bana son gathering ko ya yake Sophie, me yasa kika yi tunanin har da ni za ayi bayan kinsan bazan je ba" Safiyyah tace "Plss for once ki zama Social or should i even say Civilised Khaleesat, ko ba komai idan kika zo za kiyi nishadi ki mance duk wani damuwar ki na Nigeria kiyi freshen up din ƙwaƙwalwar ki for this semester, amma kawai kiyi ta zaman gida ke kadai kullum kamar me wani cuta, kin ga wannan shekara dayan da ya rage mana so nake ki waye ki fara yin abubuwa irin na wayayyu ta yanda babu wanda zai raina ki babu wanda zai san daga wani irin background kika fito, yanxu fa ba da bane a gareki Khaleesat don ke kin ma tsallake matsayin da mu bamu zo ba ma, don haka use this last opportunity in USA ki zama wise ta yanda babu shegen da zai raina ki" Khaleesat dai idonta a lumshe yake don har ta ci gaba da baccin ta, Safiyyah tace "Hello" Khaleesat ta bude ido da kyar tace "We will talk later Sophie" Safiyyah tace "Tun da ina gaya maki gaskiya ba dole kice we will talk later ba, kuma ko kin ki ko kin so sai mun je get together din nan da ke don yanxu ba da bane" Daga haka ta katse wayar ta, Khaleesat ta gyara kwanciyarta ta rufa da duvet zata ci gaba da bacci, ita kanta tasan bashin baccin da bata yi a Nigeria ne take biya.... Sai kusan karfe uku na rana Khaleesat ta tashi daga bacci, bayan tayi wanka tayi sallan azahar ta sauka parlor don yunwa take ji sosai, kunna heater din parlon tayi don parlon yayi sanyi kamar fridge, ta karasa ta tsaya jikin window din parlon ta daga labule tana kallon beautiful Neighborhood din ta, ko ina fari tas saboda snow din da aka yi sosai daren jiya da bai gama narkewa ba, after some minutes ta sake drape din windan a hankali ta nufi kitchen, shayi ta hada ta debi cookies ta dawo parlorn ta zauna, bayan ta gama ta kai plate din da cup kitchen ta wanke sannan ta koma sama don harhada textbooks dinta da reading materials, gaba daya sauran kayanta na tsohon Apartment dinta duk ta gansu a dakin alamar Jay ne ya kwaso mata su daga old apartment din nata, ta gama hada kan reading materials dinta, ta fara gyara kayan sawanta a press din dakin kenan taji an danna bell din gidan, ta ɗan yi jim to be sure a apartment din take jin karan bell din, after some seconds ta fita daga dakinta ta sauka downstairs bayan an sake danna bell din, ta karasa har bakin kofar ta bude a hankali tana duba waye a bakin kofar, yana kallonta calmly yace "Good evening Halysaah" Ɗan murmushi tayi ta koma gefe don basa hanyar shigowa, yace "A'a kawai ki shirya, za mu je kiyi shopping abubuwan da kike bukata, i will wait for you inside in the car" Shiru Khaleesat tayi tana kallonsa, ganin zai koma motarsa tace "Amma ai ba abinda zan bukata yanxu, don naga akwai komai a gidan" Yace "For ur personal use Halysaah, beside ai babu cleaning agents a gidan, i forgot to get them..." Khaleesat ta sauke idonta bata ce komai ba, yace "I am waiting at the garage" Daga haka ya juya ya koma garage ta bi sa da kallo kafin ta rufe kofar ta juya ta nufi sama a sanyaye, bayan minti sha biyar ta sake saukowa downstairs tana sanye da jacket dinta, tana fita waje taji wani azababben sanyi duk da Jacket din jikinta, ta kulle gidan tana rike da makullin ta nufi motarsa, bude front seat din tayi ta shiga ta kulle, yace "Akwai sanyi ko?" Tana kara takurewa waje daya tace "Sosai, ni ban ma san akwai sanyi haka ba" Yayi murmushi ya kara dumin motarsa yace "Kina cikin gida da room heater ya za ayi ki san akwai sanyi" Murmushi tayi tana juya makullin hannunta ta ɗan kallesa a hankali tace "Ina yini?" Yace "Lafiya Halysaah, how was ur night?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Hope you are comfortable in the new house?" Ta gyada masa kai tana kallonsa, yace "Good to hear that..." Tada motar yayi suka bar garage din, bayan sun dan yi nisa da tafiyar a hankali tace "Yaya Junaid fa?" Sai a sannan ya kalleta yace "Ajay yana gida, he is under the weather, baya son irin season din nan" Tayi shiru bata ce komai ba, yace "Ya kika baro su Umma and Aunty Farida?" Tace "Mun yi chatting dasu jiya da daddare, Umma tace tana son ta maka magana if you are around" Yace "Ohk to idan mun koma gida sai in kira ta" Khaleesat bata sake cewa komai ba, jifa jifa dai take kallonsa, shi kam ya maida hankalinsa kan driving din da yake, Wani babban Shopping mall ya kai su, bayan yayi parking sun shiga ciki ya dau shopping cart yana turawa, zata amsa cart din a hannunsa yayi murmushi yace "No, don't worry Halysaah, i will do the wheeling and u do the shopping" Ta sauke idonta bata ce komai ba, gun cosmetics ya fara kai su yace "Ki dauki duk abinda kika san za ki bukata a nan Housemate..." Ta ɗaga kai ta kallesa, ya ɗan bude ido yace "Look Halysaah, i want you to be free and open with me, kar ki saka komai a ranki ko kiji nauyin tambayar wani abu da kika san kina da bukata, assuming i don't have the means ai bazan ce zan yi ba Halysaah, so feel free plss Housemate, haka jiya nace ki turo min Skin care set din ki ba ki turo ba, ni ina maki duk abinda nasan zan ma kanwata ne ko er uwa ta, so ki dau duk abinda kika san kina da bukata yanxu" Ita dai idonta na kasa bata ce komai ba, ya mika mata katin kudinsa yace "Ko in baki katin in jira ki a mota?" Ta ɗan kallesa sai kuma ta girgiza masa kai a hankali tana murmushin karfin hali tace "A'a" yace "Then shop all you need Housemate" Cikin sanyin murya tace "Ohk, Thank you so much" Shi dai murmushi kawai yayi bai ce mata komai ba, few abubuwan da tasan zata yi needing take dauka a wajen cosmetics din tana ajiyewa a cart din da yake tura mata, amma idan ta dau abu daya sai ya kara mata biyu a kan wanda ta dauka, ita dai sai dai ta kallesa, ta dau set din Cream din shafawanta da shower gel, nan ma yayi doubling mata su ya zuba a cart, a hankali tace "Ina da saura fa" Bai ce mata komai ba, ta ci gaba da tafiya, tana kallon pad amma ta kasa dauka kawai ta wuce, shi ma kuma bai ce mata komai ba yana wheeling cart din har dai suka gama da bangaren cosmetics, ya nufi gun cleaning agents tana biye da shi abaya, duk shi ya dinga daukan abubuwan da yasan zata bukata a gida, sai bayan minti talatin suka fito daga shopping mall din ya zuba duk abubuwan da suka siya a booth din motarsa, maimakon su nufi gida sai taga ya kai ta wani babban store din Africa yace "I didn't get much cooking ingredients for you cause i am not good at that, so mu shiga sai ki dau duk me zaki bukata na girki...." Ta kallesa tace "To ai ko fara amfani da wanda ka siya ban yi ba" Yace "I know, zan ɗan yi tafiya ne Housemate, so i want to be sure you have enough of everything" Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, yace "Mu je" Daga haka ya sauka daga motar, jiki a sanyaye ita ma ta sauka ta bi sa zuwa cikin store din, Spices din girki da su seasoning, albasa, irish, dankalin hausa, doya, eggs, all kind of peppers, tomatoes, da dai duk wani mahadin girki suka siya a store din, sannan ya kara mata frozen chicken da turkey, sai beef, bayan ya biya kudaden suka bar store din, yana driving Khaleesat ta kallesa cikin sanyin murya tace "Thank you so much, Allah ya sa kafi haka" Yayi murmushi kawai, sai kuma ya dau wayarsa dake vibrate yana dubawa, ganin Ajay ne ke kiransa yayi picking ya kai kunne yace "How are you feeling?" After some seconds ya ajiye wayar, Khaleesat tace "Is he sick?" Yace "Yeah, i told you he is under the weather" Khaleesat ta yi shiru, Jay ya kalleta yace "Ko mu je gidan ki dubasa?" Ta ɗan buda ido, sai kuma tayi murmushi a sanyaye tace "Bazai kulani ba ai" Jay yayi dariyar da bai yi niyya ba yace "Saboda me bazai kula ki ba?" Ta sauke idonta tace "Jiya ma da ka je dauko makulli ai yayi kamar bai gan mu ba a mota" Jay yace "Jiyan nan ma da ku ka gansa ba shi da lafiya, sai da nace kar ya fita yaki saurarana, bayan ya fita kuma aka fara snow" A hankali Khaleesat tace "To Allah ya basa lafiya" Jay yace "Mu je can gidan za ki gaishesa?" Tayi shiru don har zuciyarta tana fargaban kar ya shareta, Jay yace "A bari next time ko?" Ta sauke idonta a hankali tace "To mu je, amma idan bai kulani ba ai shikenan" Jay yayi murmushi yace "Idan bai kulaki ba kema sai ki sharesa" Khaleesat ta ɗan kallesa suka hada ido, murmushi tayi har sai da dimple dinta ya lotsa tana kallonsa, ya dauke idonsa ya maida dubansa kan titi yana ci gaba da driving dinsa gently. Kusan karfe biyar da rabi suka isa gidan, Jay yayi parking a compound ya kashe motarsa ya ɗan kalleta yace "I can see you are tensed?" Ɗan murmushi tayi tana wasa da fingers dinta bata ce komai ba, ya bude motar yace "To mu shiga" A hankali ta bude motar ita ma ta sauka, ta bi Jay da kallo har ya dau hanyar entrance din babban gidan nasu, ta bi bayansa tana tafiya slowly, bayan ya bude kofar parlon sai da ya jira har ta iso, ta sunkuyar da kanta ta shiga parlon sannan shi ma ya shiga, sosai gabanta ya fadi bayan wasu memory sun dawo mata, memory that is so disturbing to her, tana tafiya a hankali ta karasa har cikin parlon ta zauna kan kujeran da ta zauna ranan da Jay ya kawota gidan da daddare, ta daga kai ta kalli Reading Nook din da Ajay ya zauna a ranan da daddare, sauke idonta tayi tana wasa da fingers dinta, Jay ya karaso cikin parlon yana kallonta yace "Give me some minutes" Ta gyada masa kai ya nufi stairs ta bi sa da kallo har ya haura sama, Jay na tafiya sama ya karasa bangaren Ajay ya bude kofar gently yana kallon cikin dakin nasa wanda babu haske sosai don Drape din dakin very thick one ne saboda sanyi, Jay ya shiga ciki ya kunna dim light din dakin yana kallon Ajay, kwance yake saman gado yayi rub da ciki yana bacci, har wani hucin zafi dakin yake tsabar yanda ya kure room heater, Jay ya karasa kusa da gadon yana kallonsa, lallai yanxu ya kara tabbatar da bai da lafiya, Ajay ne har za a bude masa daki a kunna wuta a shigo bai sani ba, ai duk baccin da yake kana taɓa kofar dakinsa yake tashi tun kafin ka shigo masa, Jay ya juya ya fita daga dakin ya jawo kofar gently amma bai kulle ba, ya koma downstairs yana kallon Khaleesat yace "Mu je sama Housemate, yana bangarensa" Mikewa tayi tana kallonsa ta nufesa, Jay yace "And before i forget, kiyi masa godiya he paid for ur new apartment" Khaleesat tayi shiru tana kallonsa amma ta kasa cewa komai, jiki a sanyaye ta bi Jay suka haura sama zuwa bangaren Ajay, Jay ya tura kofar dakin Ajay gently ya shiga sannan ya kalleta yayi mata alamar ta shigo, ta dake tana tafiya a hankali ta shiga dakin, haka kawai taji gabanta na faduwa, dakin nan nasa dai ne da tayi kwanaki biyu a ciki sanda take gidan, kallo daya tayi ma Ajay dake kwance kan gadon sannan ta kalli Jay, Kan lallausan farin carpet din dakin ta durkusa, Jay ya nuna mata kujera alamar ta zauna ta girgiza masa kai kawai, kamar yanda ta san dakin har yanxu komai na cikinsa fari ne kal, ga wani irin kamshi da dakin yake, amma fa ji tayi tana jin zafi saboda room heater din da ya kure, Jay ya karasa har inda yake kwance ya duka yana kallon fuskarsa ya janye Head warmer din da ya ƙima a kai, calmly yace "Hey...." A hankali Ajay ya bude idonsa yana kallonsa, hade rai yayi cikin muryar bacci yace "Gerrout Jay, meye na shigo min Bedroom" Jay ya mike tsaye yana kallonsa yana murmushi yace "Kai baka shiga na mutane?" Ajay ya jawo pillow dake gefensa da kyar ya jefa masa yace "Gerrout Jawwad, i want to be alone, i think i am running temperature, i am feeling sleepy, can i speak to my dad? I want to speak to Ammi too" Jay yayi murmushi don yasan duk sumbatu yake kamar yanda ya saba in bashi da lafiya, Jay ya duka yana kallonsa yace "Should i get u a Cup of Coffee? And some drugs?" As if murmuring Ajay ya lumshe ido yace "Yess pls, but don't come back" Jay yace "To ta ina za a miko maka Coffee din?" Ajay bai bude ido ba yace "Drink it for me Jay" Jay yayi dariya yace "Ohk, amma an zo duba ka" Ajay ya bude idonsa da kyar yace "Don Allah ka fita, leave my room pls Jawwad" Sai kuma ya juya zai jawo wani pillown a fusace ya wurga ma Jay kawai suka hada ido da Khaleesat dake ta kallon ikon Allah, juyawa Ajay yayi da sauri ya kalli Jay amma tuni Jay ya nufi kofa trying not to laugh out loud ya fita daga dakin, Khaleesat ta bi Jay da kallo taji kamar ta tashi ta bi sa, Ajay ya kasa juyowa, yana kokarin tuna abubuwan da ya fada da Jay ya tashesa bacci..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 60 Khaleesat dai har sannan tana durkushe inda take a dakin ga gabanta sai faduwa yake, lkci lkci take satan kallon Ajay, bayan kusan minti biyu ya mike zaune daga kwancen da yake ya sauke kafafuwansa kasa yana facing bangare daban na dakin, he still can't recall all what he said to Jay bayan ya tashesa a bacci, after some seconds ya jawo head warmer dinsa ya saka, ya daure ya mike tsaye ya juya, hada ido suka yi ta sauke idonta a hankali, ya hade rai yace "What happened?" Girgiza kai tayi ba tare da ta kallesa ba tana wasa da farin carpet din da take durkushe tace "Kawai gaisheka na zo in yi ne" A takaice yace "Gaisheni for what? Do we have any agenda?" Sai a sannan ta daga kai ta ɗan kallesa tace "And i want to say thank you for the apartment you got me" Kofa ya nufa yace "Karya yake maki, meye hadina dake zan biya maki apartment, ki dai je ki masa godiya...." Bata san sanda ta bi sa da wani irin kallo ba har ya fice daga dakin, can ta wani murguda baki ta mike ta nufi kofa, har zata fita sai kuma ta tsaya bayan ta hango wani abu a gaban mirror din dakin nasa, tana tafiya slowly ta karasa har gaban madubin tana kallon Hair ribbon dinta dake ajiye, ta dau ribbon din tana jujjuyasa tana kallonsa, wanda da alama sanda tayi kwana biyu a dakin ne ta manta shi, kofa ta nufa ta fita daga dakin tana rike da ribbon din nata, tana isowa dai dai stairs ta hango Ajay downstairs yana tsaye gaban Jay sai bala'i yake masa kamar ubansa, Jay dai na zaune yana kallonsa keenly yana cin chocolate din hannunsa, can dai Jay yace "Where is ur rod Ahmad? Ka mance baka sakko da bulalan ba ai" Ajay na masa wani kallo yace "Seriously kar ka sake min haka bana so, i did all what i did because of you not her, kawai don kar burden yayi maka yawa nayi ba don komai ba, meye na zuwa kace mata ni na biya mata apartment? Did i send you message? Upon how i warned you not to tell her amma sai da kaje ka fada, to yanxu riban me ka ci da kaje kace mata na biya mata gida?" Jay yace "Ashe dai lafiyarka qlau all this while Junaid? Where did u get this strength from all of a sudden?" Khaleesat dai ta taɓe baki ta fara saukowa downstairs, tana saukowa Ajay ya nufi stairs din fuskarsa a daure zai koma sama, Jay ya bi sa da kallo yana cin chocolate din hannunsa, Khaleesat ma ta bi sa da kallo kafin ya haura sama tace "Sai anjima, and thank you for everything, Allah ya kara budi" Ya wani juya ya kalleta yace "Kee kar ki sake min godiya, ko kinga ina wasa da ke ne?" Kamar bazata ce komai ba sai kuma tace "Tunda kayi abinda zan maka godiya ai dole zan maka godiya, inda baka yi ba ai bazan maka godiyan ba, wishing you quickest recovery" Ɗan murmushi Jay yayi ya mike yace "It's getting dark, mu je inyi dropping din ki Housemate" a hankali Khaleesat tace "Ohk" daga haka ta bi bayan Housemate dinta ta bar Ajay tsaye bakin stairs din ya bi su da kallo har suka fita daga parlon.... Jay ya kalli ribbon din da take juyawa a hannunta bayan ya tada motarsa yace "Where did you get that from?" Ta kalli ribbon din tace "A dakinsa na gani" Jay yayi shiru yana kallon ribbon din, sai kuma yace "Kuma na ki ne?" Ta gyada masa kai tana kallonsa, ya amshi ribbon din yana kallo babu ko kiftawa, sai kuma yace "How did it get there?" A hankali tace "Sanda ka kai ni dakin nayi kwana biyu" Jay bai sake cewa komai ba ya mayar mata da ribbon din without looking at her, ya fara driving zai fita daga compound din nasu, bayan sun bar gidan calmly yace "Where did u see the ribbon in his room? Ko shi ya baki?" Ta girgiza kai tace "A'a, kawai hangosa nayi a gaban mirror din dakin" Jay yayi shiru bai sake cewa komai ba yana driving dinsa with calm, a haka har suka iso apartment din nata, bayan ya kashe motar ya sauka ita ma ta dau makullin apartment dinta ta sauka, Jay ya zaga ya bude booth zai fiddo shopping din da yayi mata, kawai bag din cosmetics dinta ya mika mata yace "Go with this, i will get the rest" ta ɗan duka ta amsa sannan ta nufi kofar apartment din ta bude ta shiga ta kunna wutan parlon, sai da Jay ya tabbatar ya ajiye mata duk siyayyan da suka yi a inda ya kamata a kitchen din, wanda zai zuba fridge duk ya zuba mata, sannan yayi tidying din ko ina a kitchen din, ita dai tana tsaye jikin kofa tana ta kallonsa, yana juyowa ta sauke idonta ta juya a hankali ta bar kofar kitchen din ta koma parlor, bayan ya fito parlor yana kallonta yace "Ki turo min account details din ki let me send you Money for transportation to school" Ita dai Khaleesat kallonsa kawai tayi bata ce komai ba, yace "I am waiting, zan tafi ne" Ta sauke idonta tace "Ai akwai kudi a account din" Yace "Halysaah" Ta daga idanunta ta kallesa, yace "Turo min details din ki yanxu" Shiru tayi tana kallonsa, sai kuma tace "Ai bani da number ka" Yace "Oh, na manta, ina wayar naki?" Tace "Yana sama" Yace "To dauko" Sama ta wuce ya bi ta da kallo, sai kuma ya dauke idonsa ya zauna kan kujera, after some minutes sai ga ta ta dawo parlon, ta karaso har gabansa ta mika masa wayar, ya amsa without looking at her yayi dialling numbersa a wayar sannan ya mika mata yace "Save it" Ta amshi wayar, ta ɗan yi jim kamar tana tunanin sunan da zata yi using tayi saving number nasa, after some seconds kawai ta saka My Housemate, ya mike yace "Turo min details din yanxu, zan tafi" Tura masa bank details din nata tayi, bayan yaga shigowar message din nata yace "Alright then zaki ga alert anjima, if there is anything just ping me via WhatsApp" a hankali tace "Ohk" Yace "Good night?" Sai da taga ya nufi kofa ta kasa daurewa cikin sanyin murya tace "Ka ce zaka yi tafiya?" Juyowa yayi ya kalleta yace "Sure Halysaah..." A hankali tace "Gobe zaka tafi?" Yace "Yeah that was my plan initially, but i think if Ajay is still sick zan yi postponing tafiyar zuwa Wednesday or Thursday" Khaleesat ta gyada masa kai, yace "Or is there anything Housemate?" Ta girgiza masa kai a hankali tace "Zaka dade ne?" Yace "I am going to UK, cousin sis dinmu ce bata da lafiya zan je in duba ta, idan naga she is much better zan koma Nigeria da ita" Khaleesat ta sauke idonta bata ce komai ba, after few seconds a hankali tace "Allah ya bata lafiya" Jay yace "Ameen, but do not worry Housemate, Ajay is around if there is anything nasan zai yi idan yaga bana nan" Khaleesat ta girgiza kai tace "A'a babu komai, i am okay, Allah ya kai ka lafiya" Jay yace "Ameen, amma idan ban tafi gobe ba we will meet in school in sha Allah" Kai kawai ta gyada masa, yayi mata murmushi yace "Good night" Tace "Thank you very much Housemate, Allah ya saka da alkhairi" Ya dora finger daya a lips dinsa yana kallonta da kyawawan idanunsa, sauke idonta tayi, ya juya ya fita daga parlon, ta karasa window din parlon ta tsaya tana kallonsa ta Drape har ya bar garage din da motarsa sannan ta sake drape din a hankali ta juya, after some minutes tana jan kafa ta karasa ta kulle kofar parlon. Washegari Khaleesat ta fito lecture Hall saboda message din da Jay yayi mata ya shigo school din yana jiranta, dama ba lectures suke ba suna tutorial na wani course dinsu ne kawai ta ce ma Safiyyah tana zuwa sannan ta fito, exact spot din da yake jiranta sanda take exam ta hango sa zaune, gaba daya attention dinsa na kan wayarsa da yake dannawa, yanda yayi keeping serious face ya fito da ainahin handsomeness dinsa, sam bashi da wata makusa, he is just the real definition of handsome, everything about him is just perfect, tun daga nesa Khaleesat take kallonsa bata yi realising ba sai ganinta tayi har ta iso inda yake zaune, ya daga kai ya kalleta, sai kuma ya mike ya mayar da wayarsa aljihu yace "Good Afternoon Halysaah" ta sunkuyar da kai tana ɗan murmushi don sai ta ganta er karama a kusa da shi, yace "Hope ba lectures ku ke ba?" Ta girgiza kai tace "A'a" Yace "Ohk, my flight is in 2 hours time in sha Allah" Ta daga kai tana kallonsa a sanyaye, suna hada ido ta sauke idonta tace "Ya Junaid yaji sauki kenan?" Jay yace "Yeah he is better, shi ne ma yace in tafi..." Khaleesat bata sake cewa komai ba, yace "Kin yi lunch ne?" Duk da bata yi ba ta gyada masa kai alamar tayi, yace "Ohk ke da Safiyyah?" Tace "Um" Yace "To shikenan, i came to tell you i am leaving, take care of ur self Housemate, kuma kiyi concentrating a karatun ki, if there is anything just ping me via WhatsApp" A hankali Khaleesat tace "Dadewa zaka yi kenan?" Yayi murmushi yace "Bazan dade ba in sha Allah, nasan dai daga can definitely za mu je Nigeria" Khaleesat ta kasa kallonsa don sai taji kamar hawaye na neman ciko mata a ido, ta dake tace "To shikenan, Allah ya kai ka lafiya, ya tsare" Yana kallonta yace "Ameen" Taki barin su hada ido tace "Muna karatu ne da su Safiyyah zan koma" Yace "Ohk" Tace "Sai anjima" Bata jira cewar sa ba ta juya zata bar wajen tun kan hawayen da ya cika idonta ya zubo, Calmly yace "Halysaah" kin juyowa tayi, ya zaga har gabanta ya tsaya yana kallonta, ta kasa kallonsa tana goge hawayen da ya fara zuba idonta, shiru yayi yana kallonta, after some seconds ya dauke idonsa a hankali yace "But you have Safiyyah here Housemate...." Ta gyada masa kai tana murmushin karfin hali, yace "In sha Allah bazan dade ba i promise" Nan ma dai kai kawai ta gyada masa, yace "Ko za ki rakani Airport din?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa, still tana murmushi ta girgiza masa kai, bai yi wani insisting ba bayan ya tuna Ajay ne zai yi dropping dinsa a airport din, dai dai nan wayarsa dake aljihunsa ya fara vibrate, ya ciro wayar yana duba me kiransa, ganin Ajay ne yayi picking ya kai kunne, after few seconds ya katse wayar yana kallonta yace "Mu je to ki rakani, our car is somewhere around here" Ta gyada masa kai suka fara tafiya gun motar, tun daga nisa ta hango Ajay dake tsaye jikin mota yana jiran Jay, wayarsa ce a hannunsa yana dannawa with his full attention, Khaleesat ta ɗan kalli Jay, sai a sannan taga kaman da suke yi da Ajay, Jay ya kalleta speaking slowly yace "Ko zaki koma daga nan?" A hankali tace "Ohk, Allah ya kiyaye hanya" Yace "Ameen" Kamar ance Ajay ya daga kai yayi ido huda da su, Jay ya dauke idonsa yana kallon Khaleesat yace "I will drop you a WhatsApp message idan na isa, just go" Ta gyada masa kai, ta ɗan kalli Ajay suka kara hada ido, sai kuma ta kasa tafiya, murya can kasa tace "Ko dai kawai mu je gun motar sai in gaishesa tunda ya gan mu?" Ba tare da Jay ya kalleta ba yace "Ohk" a haka suka karasa gun motar, Khaleesat na kallon Ajay da ya ci gaba da danna wayarsa tace "Ina yini?" Jay ya zaga ya bude front seat ya shiga ya kulle motar, ita dai tana tsaye don Ajay bai amsa gaisuwan ta ba bai kuma kalli inda take ba, after some seconds ya daga kai ya kalleta yace "Idan kika gaishe da Jay ya wadatar, ni ki dena gaisheni" Tana kallonsa tace "Saboda me" Ajiye wayarsa yayi yana kallonta da mamaki, can yace "Na fara wasa da ke ne?" Still tana kallonsa tace "To ai kar watarana kace bana gaishe ka shiyasa nake gaishe ka yanxu, once again thank you for the new apartment" Yace "I will slap you idan baki fita a gabana ba" Tayi masa wani kallo ta juya ta fara tafiya, ya bi ta da kallon mamaki, ta sake juyawa suka hada ido don kallonta kawai yake, ta zumbura baki tayi wucewarta, sai da ya dena hangota ya bude driver seat ya shiga ya fara balbale Jay da bala'i yana cewa "Ka ga ka dena hadani da yarinyar nan Jay, don na lura tun da taje ta san menene aure ta karo wani rashin kunya na musamman" Dakatar da shi Jay yayi fuska daure yace "Pls bana son hayaniya Junaid" Tada motar Ajay yayi ya fara driving, after some minutes ya juya ya kalli Jay yace "What happened? Wa ya bata maka rai?" Jay na danna wayarsa yace "Never Mind" Ajay bai sake ce masa komai ba ya ci gaba da driving din da yake. Murmushi Khaleesat tayi ta bude handbag dinta ta saka wayarta ta mike tace "Ai kuma sai kiyi, naga dai ba dole bane sai naje wani get together ko?" Safiyyah ta rike Abayan jikinta rai bace tace "Wallahi dole ne Khaleesat, wai don Allah me yasa kike haka ne? Me yasa kike da taurin kai haka? Sai yaushe zaki waye ki fara abu irin na mutane wayayyu? Wallahi na fara gajiya da halin ki, babu wanda ya isa ya baki shawara ki dauka kike nufi ko me?" Khaleesat tayi dariya tace "Yau nake ganin ikon Allah, duk saboda nace maki bazan bi ki ba? To naji zan je amma ni ko minti talatin bazan yi ba a wajen" Safiyyah da fuskarta ke daure har lokacin tace "Naji, mu tafi gidan naki mu shirya" Khaleesat tace "Meye da kayan jikina da bazan je da shi ba?" Safiyyah tace "A'a wallahi a gan ki tun safe da kaya anjima kuma a sake ganinki wajen get together da shi? Ni ma ga kayana da zan canza cikin jakan laptop dina, bari in mana order din Uber mu tafi gidan naki" Khaleesat dai ta tabe baki bata ce mata komai ba, Safiyyah ta gama order din ride din sannan ta mike har sannan tana rike da Khaleesat, Khaleesat tace "Ikon Allah, to ki sakeni mana ko guduwa zan yi?" Safiyyah tace "Na san maki?" Dariya kawai Khaleesat tayi a haka suka tafi inda za su jira Lyft dinsu, wajen karfe hudu suka isa apartment din Khaleesat, sai da suka yi sallan azahar sannan suka shirya, Safiyyah har da make up, Khaleesat dai ko powder bata yarda ta shafa ba, Safiyyah ta kyaleta da baƙin halinta don lallabata take kar ta canza mind dinta, a haka dai suka bar gidan wajen karfe biyar saura. Halysaah is 500, ur evidence via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah 07087865788 S-BORNO INCENSE AND MORE. Muna Saida turarukan wuta masu Kamshi dakuma kama gida, ba iya su kadai muka tsaya ba, muna saida kayyakin gyaran jiki wanda babu ruwanki da zuwa gyaran jiki zaki gyara jikin ki gida cikin sauk’i, idan kina son turaren kabbasa mai kama jiki da Kaya Hajiya ta kwantar da hankalin ki, ba Kaya kawai zai kama ba har kujerar da kika zauna sai ta kama Kamshi da yardar Allah, turarukanmu sune kamar haka. FARCE, HAWEE, GABGAB, DORUT AFTER PERIOD, KAJIJI, Halut oud, White oud, Qatari bakhoor, Sandal flakes Sandal sukkariya, Couscous, Nawwar , Sandal bange, Dollar, Wardrobe balls, SANDAL BALLS, COTTON INCENSE, HAIR INCENSE, CURTAINS INCENSE, BATH MIST, MOPPING MIST, MATAN MAIDUGURI, WHITE KHUMRAH, BROWN KHUMRAH, DUFR KHUMRAH, BLACK KHUMRAH, CHADIAN KULECCAM SUDANESE KULECCAM TOILET SPRAY ROOM SPRAY. BANGAREN GYARAN JIKI MUNADA READY TO USE DILKE, HALAWA, Dilka Soap. MUNA BADA SAYAN D’aya ko sari kan farashi mai rahusa, ina mai tabbatar miki babuke babu nadama sayan kayanmu, gidan ki yayi Kamshi, labulayenki suyi kanshi, hatta bangon gidan ki sai yayi kanshi, muna zuwa ko wani gari don yin gyaran jikin Amarya. 08093772168 Karku manta munada mayukan gashi masu Kara tsawon gashi zasu gyara miki gashi yayi laushi yayi tsantsi,Sannan yayi tsawo in two months. Muna tura kayan mu duk inda mutum yake, location dinmu Maiduguri ne. 08093772168 HALYSAAH 61 Tun da suka iso gidan Coursemate dinsu Clara da aka yi organizing Get together din Khaleesat ta nemi waje a parlon ta zauna tayi isolating kanta totally daga cikin mutane don sun tarar har an fara taron ana ta nishadi, yawanci duk turawa ne sai few Africans da kuma student from other Continent, simple girke girken turawa da snacks iri iri ne a parlon sai drinks with so many chocolate, sannan ga tea with cookies, tuni Safiyyah ta shige cikin Coursemate dinsu ana ta shagali dama duk ta saba da su unlike Khaleesat da ba kowa take hulda da shi a department din nasu ba, lokaci lokaci Khaleesat ke kallon Safiyyah don a rayuwa idan akwai abinda ke saka Safiyyah farin ciki da nishadi bai wuce Chilling da partying with friends ba, har mamakinta Khaleesat take ko gajiya da harkar party bata yi, tana son life sosai ba kadan ba, bata ki a gayyaceta wani partyn gobe ba tsaf zata je, Khaleesat dai wayarta kawai take dannawa tana yi tana kallon agogo don dama tace minti talatin kawai zata yi, sai ga Safiyyah ta nufo tana washe hakora da glass din wine ta mika mata tace "Haba Khaleesat ki tashi ki shiga cikin jama'a mana ayi shagali da ke, sai tambayata suke if you are okay, ke in baki kunyata mutum ba baki ji dadi ba, ni dai ga glass din wine na kawo maki" Khaleesat ta girgiza mata kai tace "A'a ni bazan sha ba, thank you" Safiyyah ta hade rai tace "Ke Non-alcoholic wine ne fa, sai kace ban san abinda nake ba, it's non alcoholic" Khaleesat tace "Na sani, kawai bana sha ne, kema kinsan drink ba wani damuna yayi ba" Safiyyah ta kyabe baki ta juya ta koma cikin yan ajin su, ba iya Coursemate dinsu kadai bane a wajen har da few masters student, wa enda suke Pursuing masters dinsu a course din da su Khaleesat ke Degree din sa, tun da Khaleesat suka shigo parlon dama ta lura da wani mutumi dake zaune shi ma yayi isolating kan sa a gefe yanda ita ma tayi, shi ma kuma wayarsa kawai yake ta dannawa da glass din wine a hannunsa, tana ganinsa ta gane bahaushe ne amma ta fuske a inda take a zaune, lokaci lokaci yake kallon direction dinta, kawai mistakenly ta daga kai suka hada ido da shi, ta maida kanta kasa tana danna wayarta with full concentration, mikewa yayi ya nufota har sannan yana rike da glass din wine, tana ganin alamar ya nufo inda take taki dago kanta har ya karaso wajenta, jingina yayi da bango daga gefen inda take zaune yana kallonta yace "Good evening" Ba tare da ta dago kanta ba a takaice tace "Ohk" Ya mayar da wayarsa aljihunsa yana kallonta yace "African?" Ta girgiza masa kai kawai, yace "But Safiyyah is your friend" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa a karon farko babu yabo babu fallasa tace "So???" Ya ɗan bude ido yana murmushi yace "Safiyyah that i know is from Africa, Nigeria precisely" A takaice tace "I don't know what you are talking about pls, because Safiyyah is my frnd doesn't mean we have to be from the same continent" Fuska daure ta kare maganar ta, calmly yace "Not at all, you sound provoked, sorry if u feel offended..." Mayar da wayarta tayi jaka with the intention of leaving the house gaba daya, sai ga Safiyyah ta nufo su da plate din cake a hannunta zata kawo mata, tana ganinsa tace "Ohh Aymaan, i didn't even notice you here, ashe ka zo" Ya gyada mata kai yace "Yeah, good evening Safiyyah" Tana murmushi tace "Evening Aymaan" Yace "Ya sunan kawar taki ne?" Safiyyah na murmushi tace "Ohh, her name is Khaleesat" Ya gyada kai yace "Ta ce min daga wani Continent din daban take not Africa, i saw she was sitted alone, shi ne na zo nan so we while away time together, but she took it personal, i think i wilk take my leave" Yana fadin haka yayi murmushi ya fara tafiya zuwa inda yake zaune, Safiyyah ta kalli Khaleesat tayi kasa da murya tace "Na shiga uku, yanxu kenan baza ki taɓa canzawa ba Khaleesat, ke baza ki koyi siyasa ba a rayuwar nan? Meye ne don ya zo ya sameki? kin zata cewa zai yi yana son ki? Ai shi kuma Aymaan ba haka yake ba, Masters dinsa ma yake shi yasa baza ki wani san sa a department din ba, he is the son of the Deputy governor of a state in Nigeria" Khaleesat ta wani kalleta tace "So??" Safiyyah tace "Maida wukar, nan da kika gansa ma ba lafiya garesa ba, chronic ciwon zuciya yake battling with, you think he have time for any relationship aside friendship? Beside iyayensa ma sun masa aure yana da mata haka da kika gansa, kawai don ya gan ki zaune shi ne ya zo to keep you company amma ba wani abu ba, kuma da aka yi inviting dinsa get together din ma yace bazai zo ba, nasan Nora ce ta takurasa ya xo, ita wai son sa take kamar zata yi yaya, ko me zai yi da baturiya, ke kuma ki sha kurumin ki ba cewa zai yi yana son ki ba he is Married..." Khaleesat dai bata ce komai ba, can ta kalli Aymaan din taga ya koma inda yake zaune yana danna wayarsa kawai sai taji wani iri a can kasar zuciyarta, sai take jin kamar bata kyauta ba yanda tayi shunning dinsa kamar jiransa take dama, Safiyyah ta tabe baki ta mika mata plate din cake din hannunta tace "Ni dai ga shi, kuma ki taso za mu yi hotuna, in shi ma din baza kiyi ba sai mu ji...." Khaleesat ta amshi plate din ta ajiye duk da ba ci zata yi ba amma kawai jaraban Safiyyah ne bata so yasa ta amsa. Haka nan Khaleesat babu yanda ta iya ta tashi za su yi hotuna da Coursemate dinta, yawancin su duk shakkar interacting da ita suke don ko murmushinta baka gani a department balle dariyarta, bata kuma kula kowa sai dai gaisuwa shi ma sama sama saboda Safiyyah, tunda Safiyyah kowa nata ne, yawanci duk hotunan da suka yi Ayman yana ciki shi ma kuma sai da aka je aka gayyatosa ya zo ayi pictures, daga karshe ya mika ma wani abokinsa wayarsa yace yayi masu hoto da Safiyyah, ita dai Khaleesat na tsaye gefe kamar bata ma san abinda suke yi ba nan kuwa slightest opportunity take nema da zata fita daga parlon ba tare da Safiyyah ta lura ba, abokin yayi masu hoto da Safiyyah tana washe hakora as usual, sosai kuma hoton yayi kyau, sai kuma ya mika ma Safiyyah wayar tasa yace "To yi min da kawarki, Khaleesat ko?" Safiyyah na murmushi ta amshi wayarsa da yake mika mata tace "Eh, her name is Khaleesat..." Komawa yayi kusa da Khaleesat ya tsaya yana kallonta yace "Let take a snap Khaleesat" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, amma da ba don abinda Safiyyah ta gaya mata a kansa ba da babu abinda zai sa ta tsaya wani yin hoto da shi, fuskarta babu yabo babu fallasa take kallon Safiyyah da ta saita waya zata masu hoton, Safiyyah ta wani kankance ido tana kallonta alamar ta saki ranta mana, kamar irin uwarta din nan haka tayi mitsi mitsi da ido tana kallonta, Khaleesat bata sanda tayi dariya ba don ba karamin dariya Safiyyah ta bata ba, Safiyyah tayi using wannan Opportunity din tayi snapping dinsu pictures kusan biyar tare da Aymaan, shi dai Aymaan kallon Khaleesat yake don bai zata tana dariya ba, abokansa biyu ma suka yi joining hoton, da wasu turawa, a haka Safiyyah ta gama masu pictures din ta mika masa wayarsa, yayi murmushi yace "Thank you Safiyyah" Safiyyah tace "Bari in sa maka numberna ka min sending pictures din pls" Ya bata wayar yace "Alright" Take away Safiyyah tayi ma Khaleesat ganin bata ci komai ba a wajen, Khaleesat dake ta kula da agogo tana ganin karfe bakwai da kusan rabi tayi ordering ride da zai maidata gida ba tare da Safiyyah ta sani ba, ride din na isowa cikin dubara tayi sneaking ta bar parlon without letting Safiyyah notice her. Wajen karfe goman dare sai bayan Khaleesat ta gama duk abinda zata yi tayi shirin kwanciya sannan ta bi miss calls din Safiyyah da tayi mata kusan hudu tun daxu, Safiyyah na dagawa tace "Sannu kin kyauta Khaleesat, da kince min zaki tafi ai ba hanaki zan yi ba, sai ma kilan in samar maki motar da zai maida ke gida, amma ba sai kin sulale kin tafi ba" Khaleesat tace "Uhm ke din ce baza ki hana ni ba?" Safiyyah tace "Ke kika jiyo kuma, da na sani ma da ban taho da ke ba wallahi, ba wani amfanin da zuwan ki yayi, Coursemate dinmu sai cewa suke me yasa kike haka baki da walwala ko kina battling da wani ciwo ne da yake sa kike haka" Khaleesat tayi dariya tace "To kun gama party din ko har yanzu kuna can kuna yi? Ko dai till dawn ne party din? Ya Mustapha bai yi ta kiran ki ba?" Safiyyah tace "Ban sani ba" Daga haka ta katse wayarta, Khaleesat tayi murmushi ta bude WhatsApp dinta, sosai gabanta ya fadi ganin message din Housemate dinta ya shigo, dama saboda shi ta kunna data ta shiga WhatsApp din nata, sai taga hoto ya turo mata kawai, ta kalli time din da ya turo ta ga tun karfe tara ya mata sending image din kuma iya shi kawai babu wani sako, ta shiga DM dinsa sai taga yana ma online, ta fara downloading hoton, lokaci daya ta mike zaune daga kwancen da take tana kallon hoton da ya turo mata babu ko kiftawa, ta cire duvet din jikinta tsabar yanda ta girgiza da wannan hoto, hoton da Safiyyah tayi mata da Aymaan ne tana dariya, ta kasa daina kallon hoton with confusion, to a ina yaga hoton nan? How did he get it? Wani kyau na musamman tayi a hoton saboda dariyar da take, shi kuma Aymaan dake gefenta ya kafeta da ido shi ma yana murmushi a hoton, ajiye wayar tayi don gaba daya kanta ya gama kullewa, to ko dai Safiyyah ta dora a status ne tunda yana da numberta, ko kuma yasan Aymaan ne? da sauri ta dau wayar tana kokarin duba status din Safiyyah, ai kuwa ta ga ita ce ta dora kusan duk pictures din da suka yi a get together din, hotunan da ta dora sun kusa 15 a status, sauka tayi daga WhatsApp din tayi dialing number Safiyyah yana fara ring ta daga, Khaleesat tace "Safiyyah me yasa zaki dora har da nawa hotunan a status din ki?" Safiyyah tace "Ban gane ba? Is there anything wrong don na dora hoton ki a status dina?" Khaleesat da taji ranta yayi mugun bace tace "Then why will u upload har da wanda muka yi da wannan mutumin nan?" Safiyyah tace "To fa" Sai kuma da sauri tace "Ohhh sorry wallahi na mance the situation on ground bari in je in goge Khaleesat, wallahi na manta" Khaleesat tace "Yanxu gashi Housemate dina ne ya min fowarding hoton wanda muka yi da mutumin fa" Cikin sanyin murya Safiyyah tace "Ni wallahi mancewa ma nake kina iddah ne, bari in je in goge yanxu, to amma dai ghost viewer ne Housemate din nan naki don ni bana ganin ya bude status dina kuma yana budewa wani lkcn... Let me go and delete them" Katse wayar Safiyyah tayi, Khaleesat taji kamar tayi kuka saboda bakin ciki da takaici, ita irin dariyar da tayi a hoton ne ma yafi kona mata rai, nan kuma ba a san Safiyyah ce ta bata dariya ba, can dai ta sake shiga WhatsApp ta shiga Dm din Housemate dinta taga yana online har sannan, ignoring hoton da ya turo mata tayi ta tura masa Good evening, hope ka isa lafiya? Har bayan minti goma bata ga yayi reply ba kuma yana online din, gaba daya duk jikinta yayi sanyi, after another 5 mins tayi deciding ta kirasa ta WhatsApp call, har call din ya katse bai daga ba, kuma tana ganinsa online, kashe datan ta tayi, ta ajiye wayar a sanyaye ta kwanta, amma ta kasa bacci har kusan karfe sha biyun dare, daga karshe ta mike zaune ta kara jawo wayar ta kunna data ta hau WhatsApp, har sannan taga bai mata reply ba kuma yayi uploading status din abun kwallo 30 minutes ago, taji hawaye ya cika idonta ta kashe datan ta ajiye wayar ta koma ta kwanta tana goge idonta. Washegari wajen karfe goma na safe Khaleesat ta gama shiryawa zata tafi school, duk da sai karfe biyu suke da lectures ranan amma taji gwara kawai ta tafi schl din, har sannan she is moody tun da ta bude WhatsApp dinta bayan da tayi sallan asuba taga har sannan bai mata reply ba bata sake hawa WhatsApp din ba, tana zaune parlor tana jiran Lyft din da tayi ordering, ta bude handbag dinta ta ciro wayarta ta kunna data ta shiga WhatsApp, bayan messages dinta sun gama shigowa still dai bai mata reply ba, ta bude voice note din Aunty Farida bayan ta saurari abinda ta ce mata, ta mayar mata da reply, WhatsApp call Aunty Farida tayi mata don tana online, ta daga bayan ta kara gaisheta daga daya bangaren Aunty Farida tace "To Khaleesat in Jawwad din shi baya nan ki hada mu da Junaid mana" A hankali Khaleesat tace "To ai ba wai muna haduwa bane a schl Aunty, inda nake daban inda suke daban" Aunty Farida tace "Ya naji muryarki haka, lafiya dai ko?" Khaleesat ta ɗan yi yake tace "Ba komai, kawai dai akwai sanyi ne kuma gashi zan fita school yanxu" Aunty Farida tace "Kuma rigunan sanyi biyu kawai ki tafi da shi ko?" A hankali Khaleesat tace "Eh, amma Ya Jawwad ya bani wani" Aunty Farida tace "Toh shikenan, ko Junaid din ne ki hada mu da shi, kinga ba dadi har yanzu bamu ce masu komai ba ba ayi masu godiya ba, kuma duk laifin ki ne, tun yaushe muke ta bin ki, Babanki ma sai da yayi magana daxu" Khaleesat tace "To zan hada ku idan mun hadu Aunty, Umma fa?" Aunty Farida tace "Umma tana lafiya" Khaleesat tace "To shikenan, zan tafi schl yanxu sai anjima" Aunty Farida tayi mata sallama, sannan Khaleesat tayi ending call din, status taga Housemate dinta yayi uploading tun karfe tara na safe, ta bude status din, kallon hoton dake status din ta dinga yi babu ko kiftawa don lkci daya ta ganeta, ta kalli caption din da yayi mata hoton, next photo din ma na yarinyar ne tare da shi kuma da alamar new pictures ne ba old ones ba, da har zata fita daga WhatsApp din sai kuma tayi screenshot din hotonsa da Hadeeyah, ta shiga DM dinsa taga yana ma online, sending masa hoton tayi sannan a kasa ta rubuta ur sick Cousin? After few minutes taga ya mata reply yace Halysaah... Bata mayar masa da reply ba, ta tafi zata duba last picture din status din nasa taga ya goge duk hotunan daga status din nasa, ajiye wayar tayi for almost 5 mins, can ta dauka zata fita daga WhatsApp din sai ga WhatsApp call dinsa ya shigo, har ya katse bata daga ba, daga karshe ta kashe data dinta ta saka wayar cikin handbag dinta. Har Khaleesat ta isa school bata san ta isa ba don gaba daya hankalinta baya jikinta, ta sauka daga Lyft din tana tafiya a hankali kamar mara lafiya, all through lectures dinsu na ranan kawai gata nan gata nan ne a hall, ko sanin abinda ake koyarwa ma bata yi ba, ta rasa menene ya tsaya mata a rai haka, bayan sun fito lectures din Safiyyah na kallonta tace "Wai har yanzu fushi kike akan hoton da na dora Khaleesat? Kin san fa bazan yi hakan da gan gan ba, don Allah kiyi hakuri, wallahi yayi escaping mind dina ne situation din dake at hand, ko fada Housemate din naki yayi maki ne?" Khaleesat ta girgiza kai trying to sound ok tace "A'a ni fa kaina ne ke min ciwo amma ba wani abu ba, gida ma nake son zan tafi yanxu" Shiru Safiyyah tayi trying to be sure of wanda take hangowa nesa da inda suke zaune, can ta kalli Khaleesat.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* S-BORNO INCENSE AND MORE. Muna Saida turarukan wuta masu Kamshi dakuma kama gida, ba iya su kadai muka tsaya ba, muna saida kayyakin gyaran jiki wanda babu ruwanki da zuwa gyaran jiki zaki gyara jikin ki gida cikin sauk’i, idan kina son turaren kabbasa mai kama jiki da Kaya Hajiya ta kwantar da hankalin ki, ba Kaya kawai zai kama ba har kujerar da kika zauna sai ta kama Kamshi da yardar Allah, turarukanmu sune kamar haka. FARCE HAWEE GABGAB DORUT AFTER PERIOD KAJIJI Halut oud White oud Nawwar, Sandal bange Dollar Wardrobe balls SANDAL BALLS COTTON INCENSE HAIR INCENSE CURTAINS INCENSE BATH MIST MOPPING MIST MATAN MAIDUGURI CHADIAN KULECCAM SUDANESE KULECCAM TOILET SPRAY ROOM SPRAY. BANGAREN GYARAN JIKI MUNADA READY TO USE DILKE, HALAWA, Dilka Soap. MUNA BADA SAYAN D’aya ko sari kan farashi mai rahusa, ina mai tabbatar miki babuke babu nadama sayan kayanmu, gidan ki yayi Kamshi, labulayenki suyi kanshi, hatta bangon gidan ki sai yayi kanshi, muna zuwa ko wani gari don yin gyaran jikin Amarya. 08093772168 Karku manta munada mayukan gashi masu Kara tsawon gashi zasu gyara miki gashi yayi laushi yayi tsantsi,Sannan yayi tsawo in two months. Muna tura kayan mu duk inda mutum yake, location dinmu Maiduguri ne. 08093772168 HALYSAAH 62 Sau daya Khaleesat ta kallesa ta dauke kai bayan tayi convincing kanta ba wajensu yake tahowa ba, Safiyyah tayi kasa da murya tace "Ni ban ma taɓa ganinsa a school din nan ba sai yau, gwara Housemate dinki shi dama ya saba zuwa ya same mu a nan sanda muke Exam, he is coming toward us fa" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba amma can kasan ranta ita ma tayi mugun mamakin ganinsa a department dinsu, how did he even know spot din da suke zama da Safiyyah, sai kawai tayi assuming hanya ce ta biyo da shi ta nan din, har ya iso inda suke zaune Khaleesat bata daga kai ba but she is surprise, Safiyyah na kallonsa tana murmushi tace "Good afternoon Ya Junaid" Ba tare da ya kalleta ba yana kallon different direction yace "Evening, can you excuse us... I want to have a word with ur Coursemate" Safiyyah dai bata fasa kallonsa ba tana gyada kai tace "Sure, why not...." Sai kuma ta dau jakanta ta mike tana kallon Khaleesat tace "Zan je wajensu Nora, if you are looking for me ina can..." Khaleesat ta gyada mata kai kawai, daga haka Safiyyah ta bar wajen, ita dai Khaleesat mamaki ma yasa ta kasa kallon Ajay dake tsaye kanta, he wants to have a word with her? To me zai ce mata da zai biyota har department din su, duk da under same faculty suke amma ko da wasa bata taɓa haduwa da shi a school ba in ba few days ago ba da suka shigo da Jay, ta kalli wayar da yake mika mata fuskarsa babu yabo babu fallasa, she was surprise, why is he giving her his phone? bata amshi wayar ba ta daga kai ta kallesa a karo na farko, ganin yanda ya daure fuska ya sa ta mika hannu ta amshi wayar tana kallon screen din, sosai gabanta ya fadi ganin hoton da suka yi da Aymaan jiya a get together, ta dinga kallon hoton babu ko kiftawa, gashi ba hoto daya ba ba kuma biyu ba, can ta kalli a ina yaga hoton sai taga a Instagram ne, bata san sanda ta gyara zama ba zuciyarta na bugawa sosai, Instagram kuma? Me ya kai hoton Instagram? ta shiga uku, ita da ko a screen din wayarta bata taɓa saka hotonta ba balle aje ga WhatsApp ko kuma facebook uwa uba Instagram, gaba daya hankalinta yayi mugun tashi ta kasa cewa komai, da kyar ta daga kai ta kallesa ta ga wani irin kallo yake mata, ta sauke idonta gabanta na ci gaba da faduwa ta kasa cewa komai, fixge wayarsa yayi daga hannunta yace "So you came back fully prepared to party in Baltimore Right? You came back to mingle with jobless guys following them to party up and down, Har kin ma mance abinda ya same ki, but wait... Baki taɓa zuwa islamiyya bane ko kuma kin je kin yi skipping classes? Ko kuma bayan mijin da kika ce a kyaleki kina son zama da shi ya sake ki baki zauna kin tambayi makusantan ki what next ba? Kawai saboda kina jin kanki on a different level yanxu shi yasa kika kama hanya kika tafi cikin kattin banza masu shaye shaye da sunan get together, har ki tsaya gefen wannan crook guy din ayi maku hoto kina dariya" Khaleesat ta kasa daurewa ta fashe da kukan da tun safe take son yi bata samu kwakkwaran reason din yin sa ba, shiru yayi yana kallonta irin kallon mamakin nan, after a minute ya zauna inda Safiyyah ta tashi amma bai ce mata komai ba, ita kuma bata fasa kukan da take ba kamar an aiko ta, tayi me isarta don kanta ta hakura ta fara goge idonta tana sauke ajiyar zuciya, sai a sannan ya kalleta yace "Ohk i understand, kin dawo America ne kiyi abinda ranki yake so ba kuma kya bukatar wani yace zai yi questioning din ki ko kuma yayi correcting din ki" Wani sabon kukan ta fara yi kamar ana tunzurata, ya mike trying to control himself yace "Get up" ganin taki tashi ya hade rai yace "Baza ki tashi ba?" A hankali ta mike tana ci gaba da goge hawayen dake zuba idonta tana shesshekan kuka, babu yabo babu fallasa yace "Mu je" Bata masa musu ba ta fara bin sa har sannan tana goge hawayen idonta, after almost 10 minutes walk suka iso inda yayi parking motarsa, yana bude motar ta daga kai ta kallesa a hankali tace "Ni ban ce ma Safiyyah zan tafi ba" Ya mata wani irin kallo yace "Baza ki ce mata ba, get in the car" Bata ce komai ba ta zaga ta bude gaban motar ta shiga, bata taɓa shiga motarsa a America ba sai ranan, har suka isa Apartment dinta babu abinda yace mata, bayan yayi parking without looking at her yace "Leave my car" Sauke idonta tayi, ta bude motar a hankali ta sauka ta kulle masa tana kallonsa tace "Don Allah tunda ka san sa kayi masa magana ya goge hotona a Instagram" Ya jefa mata wani kallo yace "Zan gaura maki mari, ni na hada ku nayi maku hoton da zan ce masa ya goge?" Daga haka yayi Reverse yayi zoom off daga Neighborhood din, wasu sabbin hawaye suka cika idonta ta juya tana tafiya a hankali ta nufi kofar apartment dinta ta bude ta shiga, zaunawa tayi a parlor ta fara tunanin to ko shi ma Housemate dinta ya ga hoton ne a Instagram bayan status din Safiyyah, bata taɓa jin haushin Safiyyah irin yau ba, Allah kadai yasan mutane nawa ne suka ga hoton nan daga jiya zuwa yau, ta goge idonta ta bude handbag dinta ta ciro wayarta ta fara kiran Safiyyah, yana fara ring Safiyyah ta daga tace "Ya tafi ne in fito?" Trying to be calm Khaleesat tace "Kin ga Safiyyah kije kiyi ma wannan mutumin magana ya cire hotona a Instagram, who does that? Ta yaya daga hoto zai je yayi posting a Instagram kamar mun san juna from anywhere da shi? Meye hadina da shi da zai min haka? Har wani dogon magana muka yi da shi da har zai dau hotona tare da shi yayi posting a Instagram dinsa?" Muryarta na rawa ta kare maganar, Safiyyah tace "Innalillahi, Instagram yayi posting hotunan? Kinsan ni ba wani damuwa da IG nayi ba, kuma fa Aymaan ban taɓa ganin yayi posting mace a Instagram ba, sai gashi yayi posting na ki, amma how did you know his Handle da har kika ga yayi posting din ku?" A fusace Khaleesat tace "Ina ruwana da wani handle dinsa, kawai daga haduwa ko maganar minti daya ban yi da mutum ba ya kama hotona yayi posting duk duniya su gani, is he even okay? Ko ba shi da hankali ne? To wallahi ki je kiyi masa magana ya goge min hotona" Safiyyah tace "Ni ma dai nayi mamaki gaskiya, wallahi ban taɓa ganin yayi posting mace ba sai gashi yayi posting din ki, kar dai shi yasa Ajay ya zo wajen ki yau? Don definitely za su iya sanin juna kilan ma suna following juna, kinsan akwai association na Nigeria student a makarantar mu dole ma za su sun san juna, ɗan Deputy governor ne fa Aymaan, he is also popular on IG" Takaici ya sa Khaleesat ta katse kiran ta jefar da wayarta kan kujera, wani mugun haushin Aymaan da Safiyyah ta dinga ji a ranta, da tana da numbersa babu abinda zai hanata kiransa ta gaggaya masa magana, ko an gaya masa ita irin wa ennan matan ne da har zai yi posting din ta duniya su gani, Abdul ne ya fado mata, nan da nan jikinta yayi mugun sanyi, don babu uban da ya kai sa zama active a Instagram gashi da uban followers, wa ma ya sani ko yasan Aymaan din, sosai taji hankalinta ya tashi ta jinginar da kanta da kujera wasu hawayen na zuba idonta, bata taɓa jin Safiyyah bata kyauta mata irin yau ba, da kyar ta mike ta dau jakarta da waya ta wuce sama. Meemah ce ta shigo dakin Momy tana mika mata wayar hannunta hankali tashe tace "Momy kin gane wacece wannan kuwa?" Momy ta ajiye bowl din farfesun hannunta ta amshi wayar tana kallon screen din, can ta kalli Meemah tace "Wannan ba er matsiyatan can bace? Khaleesat take ko wa" Meemah ta zauna gefen gado har sannan fuskarta dauke da tashin hankali tace "Ita ce Momy, ita da Aymaan" Momy ta ajiye wayar ta dau bowl din farfesunta ta ci gaba da ci tace "Waye kuma Aymaan?" Meemah tace "Aymaan din kuma kika manta yau Momy, Muhammad Aymaan ɗan mataimakin gwamna fa" Momy ta kalleta tace "Wai tsohon saurayin ki Muhammad?" Meemah ta hade rai tace "Tsohon saurayi fa kika ce Momy, Aymaan din ne tsohon saurayina?" Momy tace "To in ban ce maki tsohon saurayin ki ba ya zan ce, yaron da ba ɗaga kiranki yake ba yanxu, yaushe rabon ki da shi? kin ga kuwa ai sai in ce tsohon saurayin ki Meemah, dama ai a titin Instagram din ku ka hadu da shi, ba sai da na dinga hada maki da rokon Allah ba kika samu sassaucin son sa da kika dora ma kanki, dama su biyu zuciyarki ta makale ma da shi da wani ɗan sarki yake ko wa shi ma kullum sai kin isheni da zancensa bana ma tunanin kina da numbersa, duk samarin ki a Instagram din ku ke haduwa kuma a can ku ke rabuwa, ni na taɓa ganin wannan wahala" cike da damuwa Meemah tace "Wallahi mace ce ta shiga tsakaninmu da Aymaan Momy, amma ai ya so ni kamar ran sa, ki tuna har fa kano ya sha zuwa wajena" Momy ta tabe baki tace "Amma ai ba gidan ubanki yake zuwa ba sai dai yace ku hadu gidan cin abinci ko wani wajen, bai taɓa biyo ki yaga gidan ku ba, shekara kusan takwas ana abu daya in da gaske son naki yake me ya hanasa fitowa har yau, ni dama tun da Malam Tasi'u yace min bazai fa aureki ba na hakura da kashe kudina a iska, amma ai na kashe kudi kan wannan Aymaan din, bayan Malam Tasi'u ma akwai wani malamin da yace min mu hakura ba auren ki zai yi ba bata maki lokaci kawai yake, kuma uwarsa ma a tsaye take kyam" Meemah tace "Momy duk ba wannan ba, a ina yasan yarinyar nan har suka yi hoto tare? Kinsan shi ma a Amurka yake kuma makarantar su daya amma ya gama degree dinsa tuntuni in dai ba masters ya koma yi ba, kuma wnn hoton daga gani a Amurka aka yi sa" Momy tace "Atoh kika san ko tsohon hoto ne, dama ai kin ce iskanci ta dinga yi a Amurkan don haka ba abun mamaki bane don kin ga hotonsu tare, yanxu kuwa ai sai dai tayi karuwancinta da yan Mariri" Meemah dai ta kasa cewa komai amma kana ganinta kasan hankalinta ya tashi sosai, Momy ta kalleta tace "Ai kun ma fi shekara biyu baku yi waya da shi ba ko?" Meemah ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Yanxun ma ina ganin hoton na kirasa bai daga ba, amma ni abinda ya bani mamaki duk yanda yake da mace fa baya posting dinta ko a WhatsApp balle har Instagram" Momy tace "Ɗan wani gari ne ma?" Meemah tace "Gusau" Momy tace "Abdul ya san sa ne?" Meemah tace "Oho, shi wannan ana sanin cikinsa ne, ni ban san ko sun san juna ba, kuma ai Abdul bai san ni da Aymaan ba tunda kinga ba wai ya taɓa zuwa gidanmu bane Aymaan din, sai dai su san juna a Instagram amma ba a sarari ba" Meemah ta kara Zooming din hoton da kyau tana kallon tsadadden Abayan jikin Khaleesat ga wani kallo da Aymaan ya kafeta da shi, ita kuwa tana dariya with her beautiful set of teeth, Meemah ta fice daga wajen hoton ta sake dialing number Aymaan amma har ya katse bai daga ba, mikewa tayi ta nufi kofa, Momy ta tabe baki tace "To ke banda abunki me zai yi da er talakawa aka ce maki, in kin bibiya hoton ya dade, yanxu kuwa ina taga hanyar zuwa Amurka, ai uwarsa ma ta fi mu ƙin talakawa bari ki ji in gaya maki, a zamanin yanxu dai ko wani me kudi ya waye baya yarda ya hada zuri'a da talaka, yanxu kwarya tabi kwarya kawai, haka abun yake" Ita dai Meemah ta fice daga dakin tana sake dialing number Aymaan with confusion. Tana zaune usual spot din da suke zama a school tana jiran Safiyyah da taje kai ma wani coursemate dinsu laptop dinsa, tun daxu take zaune wajen tana danna wayar hannunta with full concentration, lkci daya ta dakata da abinda take yi a wayarta jin wani kamshin turaren da ta sani ya doki hancinta, waige waigen wajen ta fara yi suna hada ido bata san sanda ta saki wayar hannunta ba zuciyarta na bugawa tana kallonsa babu ko kiftawa, he was the least person she is expecting to see in her life, lkci daya taji wani courage ya zo mata ta dau wayarta fuskarta a daure ta mike da nufin barin wajen, ya fixgo gyalen jikinta yana kallonta da kyau yana murmushi yace "You think i will let you just like that Khaleesat? Har kin samu masu ci gaba da sponsoring din ki an dawo dake America, ga shi har ana hoto dake ana dora ki a Instagram, u snapped a picture together with Aymaan har yayi posting din ki duniya ta gani, ko wani ɗan iskan gaye kin sani a Amurka and they are all ready to go through any mile for you, to ki sani na maida aurenmu da ke, you are still my wife...." A firgice Khaleesat ta farka daga baccin da take ta mike zaune jikinta na rawa, tun da uwarta ta haifeta bata taɓa mummunan mafarki irin wannan ba, ta sauka daga saman gadonta har sannan jikinta na rawa, bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba tana ganin abun kamar ba mafarki bane gaske ne, ba karamin tashin hankali ta shiga ba ta fara karanto duk addu'an da ya zo bakinta tana kuka, duk yanda ta so ta samu nutsuwa hakan ya gagare ta, she was really shock, da kyar ta daure ta dauko wayarta ta kunna data hannunta na rawa, kawai taji she wants to speak with her Housemate, tana bude data taga Aunty Farida ta ajiye mata sako, ta shiga DM dinta taga hoton da suka yi da Aymaan ta turo mata tana tambayar wanene shi, kuma me yasa zata yi hoto da shi.... Tashin hankalin Khaleesat ya ninku akan wanda take ciki da, she was so confuse and shock, gashi jikinta sai rawa yake, a ina kuma Aunty Farida taga hoton nan, ta shiga uku, shikenan kilan Abdul ma zai gani kenan mafarkinta ya tabbata ya zamto gaskiya? Ta fashe da matsanancin kuka tana jin zuciyarta kamar zai fito tsabar tashin hankali, ko reply din Aunty Farida bata yi ba ta fita daga WhatsApp din ta fara dialing number Housemate dinta da sauri, ta kirasa har sau biyu bai daga ba, rasa yanda zata yi tayi tana kuka, can kawai ta fara dialing number Safiyyah har sannan jikinta bai dena rawa ba, yana fara ring Safiyyah tayi picking, cikin rawan murya Khaleesat tace "Safiyyah baki ce ma mutumin nan ya goge hotona a Instagram ba dama??" Safiyyah tace "A'a na masa message ta WhatsApp he is not online fa, na kuma kirasa bai yi picking ba, kuka kike yi ko me? Haba Khaleesat sai kace warce tayi wani mugun abu? Get together fa kawai muka je aka yi hoto ba wai club ba, kuma shigar ki ta mutunci kika yi fa, Aymaan kuma left a reasonable distance tsakanin ku balle ace ko manne maki yayi a jiki" Khaleesat taki bata amsa tace "Kina da number Ya Junaid pls?" Safiyyah tace "Eh kamar ta numbersa Jawwad yayi min fowarding receipt din 10M da aka tura ma su Maman Abdul" Da sauri Khaleesat tace "Don Allah ki turo min yanxun nan" Safiyyah tace "Ohk bari in duba, amma ni dai wallahi ban ga abun damuwa ba don kawai Aymaan ya daura hoton ki a Instagram, sanannen Celebrity ne shi fa, kawai don bama Instagram ne shi yasa baza mu sani ba, kuma kawai don dai kina Iddah ne da ace kin gama so what?? Ai kin isa ne yasa ya dora ki" Khaleesat ta katse wayarta don bata son ta gaya ma Safiyyah magana she is just controlling her self all this while, ba a dau lokaci ba sai ga Safiyyah tayi mata fowarding number Ajay, Khaleesat tayi dialing number da sauri, gaba daya zafi ta dinga ji duk da uban sanyin da ake har da snow, don Ajay na dropping dinta daxu babu dadewa aka fara snow shi ne har ta kwanta bacci tayi wnn mummunan mafarkin, sai da ta kira sau biyu sannan Ajay ya daga, ta kasa daurewa ta fashe masa da kuka muryarta na rawa tace "Don girman Allah idan kasan mutumin nan ka taimaka min kayi masa magana ya cire hotona a Instagram page dinsa, wallahi ni ban san sa ba pls talk to him" Tana kuka sosai ta kare maganar, Ajay dake sauraronta kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "Ni na ajiye ki a gefensa aka yi maku hoton da zan masa magana ya cire?" Ta kara fashe masa da matsanancin kuka tace "Na shiga uku, don Allah ni dai ka taimake ni wallahi ban san waye shi ba" Ajay ya ki cewa komai daga karshe ma ya katse wayarsa, ta mike ta koma kan gado ta dinga rera kuka, ita babban tashin hankalinta ace Abdul ya ga hoton nan, tsaf attention dinsa zai iya dawowa kanta kuma ba da good Intention zai dawo ba, tana rayuwarta low key gashi Safiyyah ta ja mata fitina, ji tayi kamar zazzabi na neman rufeta tsabar tashin hankali, ta kwanta saman gado tana sauke ajiyar zuciya hawaye wasu na bin wasu a fuskarta, ta kusa awa daya a haka daga karshe tayi karfin halin tashi ta tafi bandaki zata yi alwala don yin sallan magrib, ko da ta fito ta kasa yin sallan ta kwanta ta lulluba da duvet saboda rawan sanyin da take, ba karamin kidimar da ita wnn mafarkin da tayi yayi ba, after like 15 mins ta ji ana danna bell din gidan, ta mike zaune da sauri har lkcn tana rawan sanyi, gaba daya a tsorace take kamar mara gaskiya, after some minutes aka sake ringing bell din gidan, ta fara tunanin ko dai Housemate dinta ne ya dawo, tunanin hakan yasa ta daure ta sauka daga saman gadon ta fita daga dakin, har a sannan kuma snow bai dena zuba ba..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 63 Khaleesat na isa kofar parlon ta bude a hankali tana kallon wanda ke tsaye bakin kofar, sauke idonta tayi ta koma gefe ta tsaya, babu yabo babu fallasa yana kallonta yace "Me yasa kika kira wayana kina kuka kamar ni na aike ki? Why didn't you call Jay kiyi masa kukan sai ni?" Ta daga jajayen idanuwanta ta kallesa, ji tayi wasu hawayen sun cika idonta ta sunkuyar da kanta, after some seconds ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake, da kyar tace "Ni dai in ka san sa kayi masa magana he should delete my pictures off his phone plss, Aunty Farida ma fa sai da ta turo min hoton, ni kuma wallahi ban san sa ba" Yace "Baki san sa ba kika tsaya gefensa kina washe hakora ku ka yi hoto?" Ta fashe masa da kuka ta juya da sauri ta bar wajen ta koma cikin parlor ta kwanta kan kujera tana rera kuka, tsabar mamaki da haushi yasa ya kasa cewa komai ya bi ta da kallo, ya tsani unnecessary kukan mace a rayuwarsa, ya kuma lura bata da aiki sai kukan banza tun da ya santa a haka ya santa da kuka, how is Jay coping interacting with her this way, shi ba shi da irin wannan patient din, parlon ya shiga ya kulle kofar, ya saka hannunsa a aljihun Jacket din jikinsa cause he is already cold kawai ɗan tsayuwar da yayi a waje, ya karasa har inda ta kwanta take kukan ya hade rai yace "Don't you dare call my line again kina kuka, ni ban aikeki ki bi silly friend dinki zuwa party har ayi maku hoto da wani namiji ba, stop stressing me with ur troubles pls, i am not Jay" Ta dakatar da kukan da take ta wani kallesa ta hade rai tace "Ni ba party muka je ba, get together ne, ka dena cewa party" Wani kallo yayi mata, ta kauda kanta tana goge idonta, ya kalli Heater din parlon sai kuma ya tafi ya kunna, ta bi sa da kallo ganin ya nufi window din parlon ya bude drape din yana kallon snow dake sauka waje sosai, he was just imagining how he managed to get here in this snowstorm, mikewa tayi a hankali tayi wucewarta sama, ya juya ya bi ta da kallo. Wajen karfe takwas da rabi Khaleesat ta fito daga dakinta tana leka downstairs daga corridor din da take tsaye, taga yana zaune har sannan a parlon ya jinginar da kansa jikin kujera idonsa a lumshe, ta zata ma ya tafi, after some minutes ta sauko downstairs tana kallonsa, har sannan bai bude idonsa ba, tana tafiya a hankali ta nufi window tana duba waje taga it's still snowing outside, dawowa parlor tayi ta tafi kitchen, after a while ta fito da cup din tea biyu ta tafi har inda yake zaune ta tsaya tana kallonsa, a hankali tace "Ga shayi" Bude ido yayi, sai kuma ya gyara zama yace "Did i send you message?" Ta wani kallesa, sai kuma tace "To ai naga kamar sanyi kake ji tunda gashi ka kasa tafiya" Ya kalleta yace "Zan juye maki shayin a baki in baki matsa gabana ba, ba ke kika fito da ni cikin sanyin ba? Kin zata idan Jay yana nan zan saurare ki ne? Ai shine wahalalle dama" Tace "Ni ban fito da kai cikin sanyi ba, tunda ba cewa nayi ka zo ba ai, kawai kiranka nayi nace kace mutumin nan ya cire hotona a Instagram, amma ban ce ka zo ba" Kallonta ya dinga yi, at this point kamar he is lost of words, ta juya ta koma kitchen ta ajiye cup daya ta fito ta wuce sama tana rike da cup din nata shayin, still ya bi ta da kallo babu ko kiftawa, Khaleesat na gama shan tea din ta kwanta ta rufa da duvet ta lumshe ido tana addu'an Allah ya sa kar ta kara mafarkin da zai firgitata kamar daxu, kamar warce ta tuna abu ta bude idonta a hankali, ta jawo wayarta tana dubawa ko Housemate dinta ya biyo kiranta bata sani ba, amma sai taga bai biyo kiran ba, har ta ajiye wayar sai kuma ta sake dauka a hankali ta kunna data dinta tayi login WhatsApp, tun call din da yayi mata da safe bata daga ba bai kara mata magana ta WhatsApp din ba, and he uploaded a status not long ago, sauke idonta tayi ta kashe datan ta ajiye wayar ta gyara kwanciyarta, nan da nan mood dinta ya canza, duk yanda ta so tayi bacci kasawa tayi, sai juye juye take har kusan karfe sha dayan dare, mikewa zaune tayi daga karshe ta cire duvet din jikinta ta dau Jacket dinta ta saka sannan ta bude kofar parlon a hankali ta fita, tsaye tayi a corridor din sama tana kallon Ajay dake kwance kan 3 seater idonsa a lumshe don wutan parlon a kunne yake, ta fi minti biyu tsaye tana kallonsa, sai kuma ta juya ta koma dakinta ta dau one out of the new duvet Jay got for her, ta cire farin duvet din daga pack dinsa sannan ta fito daga dakinta ta sauka downstairs, tana tafiya a hankali ta isa har inda yake kwance, gida biyu ta linke soft duvet din ta rufa masa a jiki, ba wai hannunta ya taɓa sa bane but she could feel he is running temperature, tana rufa masa Duvet din ya cire daga jikinsa ya wurgar ba tare da ya bude ido ba yace "Gerrout Jay...." Sai kuma ya fara kokarin juyawa a kan kujeran sai ga shi a kasan carpet ya fadi timm, rufe bakinta tayi da sauri, ita kanta bata san meyasa dariya ya taho mata ba don da har jikinta yayi sanyi after noticing that he is running temperature, amma wannan reaction din nasa yayi mugun bata dariya, cikin magagi yake cewa "Bana son haka Jawwad, why are you stressing me, gerrout pls, i think i caught a cold, can you help increase the room heater before getting out" Sai kuma ya bude ido a hankali yana dafe kansa da yayi masa nauyi cause bai ji Jawwad na responding ba, ita dai kallonsa kawai take da mamaki, he look so shock ganinta, ya fara bin parlon da kallo, sai kuma ya kalleta ya hade rai yace "Kee, fita ki ban waje" Bata san sanda tayi dariya ba tace "Ai to bani na fadar da kai kasa ba, ni kawai bargo na kawo maka, and you heavily fell down on the Carpet" Ya kara daure fuska yace "Get out of my sight, am i a joke to you?" Ta wani juya kai, sai kuma ta nufi stairs tana waigansa har ta haura sama ta shiga dakinta, sai a sannan ta fara dariya tana mamaki shi kuma haka yake, har bayan minti talatin Khaleesat bata yi bacci ba tana dai zaune dakinta, after a while ta mike a hankali ta kara fita daga dakin nata tana leka downstairs, bata gansa kwance a parlon ba, hakan yasa ta fara saukowa downstairs, ta kalli duvet din da ya ajiye saman kujera da makullin gidan, sai kuma ta kalli bakin kofa ta karasa can ta murda kofar taji a kulle, window ta tafi tana leka Garage taga babu motarsa, ta dawo parlon ta dau makullin gidan tana kallo taga ya cire guda daya a ciki, she felt somehow ganin bashi da lafiya kuma still ya bar gidan a haka gashi snow din raguwa kawai yayi, ta fi minti biyu a tsaye after a while ta dau duvet din zata koma sama taji vibration din wayarsa, dube dube ta fara yi amma bata ga wayar kan kujera ba, daga karshe sai karkashin kujeran taga wayar, kilan sanda ya fadi daga kan kujeran shi ne wayar ya shige karkashin kujeran, screen din wayar ta dinga kallo ganin Jay ne ke kiransa, tayi silencing wayar ta wuce sama tana rike da wayar da duvet, sau uku Jay na kiran wayar, ita dai ta ajiye wayar gaban madubi tayi kwanciyarta. Washegari ta idar da sallan asuba bayan ta gama azkar dinta zata kwanta wayar Ajay ya fara vibrate gaban madubinta, ta dinga kallon wayar sai kuma ta karasa can tana duba screen din taga Jay ne still ke kiransa, ta juya ta koma saman gado tayi kwanciyarta, wajen karfe tara na safe ta gama shiri zata tafi school, tana tsaye gaban mirror din dakin tana kokarin daure gashinta sai ga Jay ya sake kiran wayar Ajay, ta dinga kallon wayar babu ko kiftawa sai kuma ta daga wayar ta sa handsfree bata ce komai ba, daga daya bangaren Jay yace "Why were you not picking ur calls Bruh, hope baka fita jiya ba cause naji anyi snow sosai, how are you doing?" Khaleesat dake sauraronsa ta sauke idonta tace "Good morning, he forgot his phone" Shiru Jay yayi daga daya bangaren for almost 10 seconds, can yace "Halysaah..." Tace "Good morning" Yace "Morning, where did he forget his phone?" Tace "In my apartment" Shiru Jay yayi bai ce komai ba, after some seconds a hankali yace "Ohk then" Daga haka ya katse wayar, Khaleesat ta dinga kallon screen din, sai kuma ta ajiye wayar tana kallonsa, sai bayan kusan minti daya ta iya ci gaba da gyara gashinta. Bayan Khaleesat ta gama abinda take ta saka wayar Ajay a jakarta zata tafi school da shi incase yaje zai amsa a department dinta, bata nuna ma Safiyyah komai ba da suka hadu a school duk da har sannan she is still very much angry at her, Safiyyah na kallonta tace "Yanxu dai sai hankalin ki ya kwanta don naje na duba na ga Aymaan ya cire hoton naku a account dinsa, ko wa yayi masa magana oho, ni kuma gashi bai min reply din WhatsApp message dina har yanzu ba" Khaleesat tace "Toh in ba dai he is irresponsible ba ta yaya zai dau hotona bai san ni ba yayi posting a account dinsa? Bai ma dau matarsa da muhimmanci ba in dai haka ne, who does that?" Safiyyah tace "Atoh, nima dai haka naji aka ce yana da mata amma ban sani ba ban kuma tabbatar ba" Khaleesat ta kalleta baki bude, Safiyyah tace "Wallahi kuwa, haka naji ana cewa, kuma wai yana da ciwon zuciya, ni dai bai min kama da me ciwon zuciya ba kuma ban ma yarda da wnn labari ba, kinsan yan mata na jin haushinsa saboda sai wanda ya ga dama yake kulawa shi yasa aka masa wannan sharrin, amma ki kalli mutum lafiyayye kamar sa a wani ce ciwon zuciya, gashi da son zuwa club" Khaleesat ta ma rasa abinda zata ce ma Safiyyah, kawai ta kauda kai don lamarin Sophie ya fara bata tsoro, the way she is saying it kamar bakinta da bakinsa suka yi magana ya gaya mata yana da ciwon zuciya kuma yana da mata, Safiyyah tace "Ni dai tashi mu je mu ci abinci yunwa nake ji, kilan ma haushin an sa shi ya cire hoton ne ya sa yayi banza da ni ta WhatsApp kuma na kirasa yaki picking, dama an masa shaidan girman kai and he is way too pompous of himself, bazai wuce Housemate dinki ya san sa ba shine yayi masa magana ya sauke hoton, dama ni fa sam gayen bai min ba ga wani jijji da kai da yake wai shi ɗan gidan Deputy sai kace ɗan vice president, deputy governors da ba a ma san da zamansu ba a Nigeria, gani yake yafi kowa a haka fa, kina kallon idonsa kinsan bazai rasa shan drugs ba" Khaleesat tace "Amma dai yanxu idan Abdul yaga hoton nan me kike tunani Safiyyah?" Safiyyah ta mike tace "Waye kuma Abdul? Pls mu je mu ga abinda za mu siya mu ci yunwa nake ji wallahi" Har Khaleesat ta bar school ranan bata ga Ajay ya zo amsar wayarsa ba, hakan kuma yasa taji a ranta he is sick. Mamaki abun ya ba Khaleesat ganin har ta dawo school Housemate dinta bai kirata ba ko kuma yayi mata magana ta WhatsApp, wayar Ajay ma bai sake kira ba, sai dad dinsa da ta ga ya kira wayar har sau biyu, da daddare taji zuciyarta ya kasa daurewa kawai tayi ma Housemate din nata magana via WhatsApp, ta gaishesa sannan ta tambayesa ya jikin cousin dinsa, after almost 15 minutes yayi mata reply da Alhamdulillah, daga nan kuma bai sake cewa komai ba, she was taken aback, haka nan ta ajiye wayarta kawai ta kwanta tana jin wani iri a zuciyarta. Bayan kwana biyu Khaleesat da Safiyyah suna zaune a wajen department dinsu, Khaleesat na yi mata explaining wani course dinsu da tace bata gane ba, Murya can kasa taji Safiyyah na cewa "Ji gantalallen Aymaan din can, he is coming toward us, kar ki dago kanki" Khaleesat bata dago kai ba, ta ci gaba da bayanin da take ma Safiyyah, har ya iso inda suke zaune, calmly yace "Good evening Safiyyah and Khaleesat" Safiyyah ta washe baki tace "Hi Aymaan, how are you doing ya kwana biyu?" Yace "Lafiya lau, ya karatu?" Safiyyah na washe hakora tace "Alhamdulillah, tun ranan bamu sake haduwa ba sai yau" Yana kallon Khaleesat yace "Good evening Khaleesat" Ba tare da Khaleesat ta kallesa ba fuskarta babu fara'a tace "Ohk" Ya kalli Safiyyah yace "Naga kamar kawar taki a fusace take" Safiyyah tayi dariya da iyakarsa fuskarta tace "Ai bata ji dadin abinda kayi mata bane, duk da na fahimtar da ita ba da wata manufa kayi hakan ba, kuma ta fahimta, ita tsoronta ma kar matarka ta ga hoton" Yana kallon Safiyyah yace "Ke kika min auren?" Safiyyah tayi dariya tace "To ai kaga za a sa maku ido kuma shi yasa ta damu" Yace "Ohk in nasan haka ne ai da bazan sauke hoton ba, don wani guy that is full of himself i think saurayinta ne ya sameni yayi min magana about it, yasan ni, na sansa a kasar nan amma ba mu taɓa ma juna magana ba, had i know ban cire hoton ba in ga abinda zai yi" Safiyyah ta kwantar da murya tace "Kaga Aymaan Khaleesat fa matar aure ce babu wani boye boye...." Aymaan yayi wani murmushi without letting Safiyyah to go further yace "Ban yarda ba, shi wanda ya min magana in cire hoton zan nuna masa ba aurenta yayi ba ai...." Khaleesat ta daga kai fuska daure tace "Pls delete my pictures off your phone Mr man, don ban san ka ba, ban hada komai da kai ba ban kuma ga dalilin da yasa zaka yi posting dina ba, no sane person will do such, plss take my pictures off ur phone matar aure ce ni" Tana kai wa nan ta tura ma Safiyyah Laptop dinta ta mike ta figi handbag dinta ta bar wajen ko waigawa bata yi ba, Aymaan ya bi ta da kallo yana ɗan murmushi, Safiyyah tayi tagumi don har ta gaji da ce ma Khaleesat ta koyi siyasa da iya zaman duniya, da faram faram ya kamata ta samu ta rabu lafiya da Aymaan amma ga abinda tayi, Aymaan ya gyada kai yace "We shall see then" Safiyyah ta kallesa tace "Kasan tana da aljanu ne fa Aymaan kuma abun har ya taɓa brain dinta, da sauki ma basu tashi a nan ba, don wallahi duka take kuma in ta fara famfala gudu da kyar ake kamota, shi sa kullum zaka ganta babu fara'a ni kadai nake iya zama da ita wallahi, wanda kuma yasa ka cire hoton ba saurayinta bane believe me..." Aymaan yayi wani murmushi yace "Nima su gareni, kin ga dai dai kenan" Daga haka ya juya ya bar wajen, Safiyyah ta kara rafka wani tagumi. Khaleesat na isa gida wajen karfe biyar zata bude kofa taji kofar a bude, ta kalli parking space taga babu mota a nan, tura kofar tayi a hankali ta shiga parlon, zaune ta gansa ya kunna TV yana kallon kwallo, ko juyowa bai yi ba har ta karasa cikin parlon tana kallonsa, ya mike without looking at her yace "Bani wayata" Tace "Ya jikin?" Sai a sannan ya kalleta yace "Nace maki bani da lafiya ne?" Tace "A'a kawai na gane idan baka da lafiya surutu that is not comprehensible kake yi a bacci....." Tana murmushi ta kare maganar tana kallonsa. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* HALYSAAH 64 Khaleesat ta bi sa da kallon gefen ido ganin ya nufi kofa, sai kuma ta juya tana kallonsa, fita ta ga zai yi daga parlon, da sauri tace "Ka jira in dauko maka wayar yana sama" Tuni ya fice daga parlon without looking at her, tafi minti biyu tsaye tana kallon kofar da mamaki, does this min yaji haushin abinda ta fada kenan? To ai ita ba da wata manufa ta fadi hakan ba, tana ta tsaye parlorn with surprise, can dai ta taɓe baki ta karasa ta zauna kan kujera ta bude handbag dinta ta ciro wayarta tana duba pdf da aka mata sending a school na wani course dinsu, after a while ta mike ta tafi sama don yin sallah ta canza kayan jikinta sannan ta dawo downstairs ta girka abinda zata ci, Khaleesat bata sauko downstairs din ba sai kusan karfe biyar da rabi na yamma don tana sallah bacci ya dauketa saboda sanyin garin, tana gyara hulan kanta bayan ta sauko kasa zata shiga kitchen taji anyi knocking kofar parlor at the same time aka murda kofar, juyawa tayi da sauri after realizing ashe a bude ta bar kofar bayan Ajay ya fita daxu, kallonsa ta dinga yi babu ko kiftawa kuma ko kwakkwaran motsi bata yi a inda take tsaye tsabar yanda ta tsorata, ya kullo kofar yana tsaye daga nan bakin kofar yana kallonta yana murmushi with calm yace "Good evening Khaleesat" Khaleesat ta sauke idonta gabanta na wani mugun faduwa, her common sense didn't give her the go Ahead to be rude or anything of such to him, can dai ta kallesa with calm in her voice tace "Why will you badge into my House just like this?" Ya ɗan yi murmushi yana sauke hulan jacket din jikinsa yace "That was because u left the door open..." Cikin kwantar da murya tace "But that doesn't warrant you to badge in" Ya daga hannu sama yace "My bad, sorry about that beautiful Khaleesat" Zaunawa tayi kan kujera bata sake cewa komai ba faduwar gabanta ya tsananta, yana bin apartment din da kallo keenly yace "Such a nice apartment, Communal living kike, ko ke kadai ce a duk apartment din nan?" Ba tare da ta kallesa ba calmly tace "Co-living" Ya karaso cikin parlon tayi masa kallon gefen ido gabanta na faduwa sosai, zaunawa yayi gefenta yana kallonta yace "Sorry i came unannounced, banyi tunanin kina da fahimta haka ba, na zo gidanki ba tare da izinin ki ba and u are not mad at me, i even badged in but u are still calm...." Khaleesat tayi murmushin karfin hali tace "It's fine... How did you get to know my apartment?" Yana gyara zama yana wani murmushi yace "Gane apartment din ki har wani wahala zai min a Baltimore ni da na damu dake?" Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, tasan babu tantama bayan ta fito school ne daxu ta hau Lyft shi ne ya biyota without her knowledge, bin parlon ya dinga yi da kallo yace "But seriously i really love this ur apartment, it's big and fine, ko ke da Safiyyah ku ke sharing?" Ta girgiza masa kai, can kasan zuciyarta kuwa tunanin next move din da zata dauka take yi, yana kallon sauran gashinta da basu gama shiga hulan kanta ba tunda tana cikin saka hulan ya shigo parlon, ya kai hannu zai taɓa gashin da mamaki yace "Are all this ur hair??" Da sauri ta matsa gefe tace "Noo, i won't welcome that" Ya buda ido yace "I am sorry Dear, you've got a beautiful soft black hair" Ita dai bata ce komai ba, Yana kallonta speaking calmly yace "Tell me more about ur self pls Khaleesat" Ta kirki murmushi tace "Kaga yanxu fita zanyi zan tafi supermarket in yi shopping, and it's almost late" Yayi er dariya yana kallonta da kyau yace "Duk salon korana ne wannan dear?" Tace "Not at all, assuming zan kore ka ai kana shigowa zance ka fitar min a gida, kawai zan je in yi siyayya ne yanxu don gobe ba da wuri zan dawo gida daga schl ba" A hankali yace "Alright, dress up sai mu je shopping din" Tayi karfin halin mikewa tsaye sai kuma ta kallesa tace "But plss respect my privacy, ka jira ni in sauko" Yayi wani murmushi yace "Baki da matsala my dear" Bata sake cewa komai ba ta nufi stairs har sannan gabanta na faduwa sosai, ga wani takaici da take ji a ranta don wata er doguwar riga ne kawai a jikinta that is not even cloth enough, a haka dai ta haura sama yana bin ta da kallo, tana shiga dakinta ta kulle dakin da makulli hawaye ya cika idonta ta tafi ta dau wayarta da sauri, number Housemate dinta tayi dialing bayan few seconds ya fara ring amma har ya katse bai daga ba, zaunawa tayi gefen gado tana goge hawayen dake sauka idonta tana tunanin yanda zata yi, bata sake dialing number Housemate dinta ba instead tayi dialing number Ajay, a cikin daya daga jakunkunan da take fita school taji vibration din wayar tasa, ajiye wayarta tayi ta daura kanta kan pillow ta fashe da kukan takaici, after some minutes ta mike tana goge hawayen da yaki tsaya mata, ta dau handbag din da wayar Ajay ke ciki, ta ciro wayar tana dubawa taga ya ma kusa shut down, cikin jakar da ta dawo da shi daga school ta saka wayar sannan ta dau nata wayar tayi ordering Uber, ta saka wayarta ma cikin jakar, ta canza kayan jikinta sannan ta saka hijab ta fito daga dakin ta kulle ta sauka downstairs, yana tsaye parlorn hannunsa rike da can drink da ya shiga kitchen dinta ya dauko a fridge yana sha, ya bi ta da kallo yace "The weather is cold outside dear, ina jacket din ki?" Without looking at him tace "I will be fine" Yace "Ohk then, mu tafi?" Tace "A'a zan ɗan yi abu a kitchen in fito tukunna" Yace "Ohk, take ur time" Kitchen dinta ta nufa ya bi ta da kallo har ta shiga ciki, kulle kofar tayi ta tsaya a kitchen din tana jiran Uber dinta at the same time zuciyarta na tafarfasa tana goge hawayen takaicin dake sauka idonta, after a while ta fito daga kitchen din without looking at him tace "Na gama" Mikewa yayi yana gyara jacket dinsa yace "You look cute dear, ko dai in baki jacket dina, its freaking cold outside fa" Tace "Kar ka damu" Daga haka ta nufi kofa ta fita, shi ma ya fito sannan ta kulle kofar da makulli, motarsa da yayi parking ya nufa yana nuna mata yace "There is my car" Ta kallesa tace "Ga Uber da nayi order can" Ya juya ya kalleta yace "Why? Cancel the order, da mota na zo ae" Tace "I can't cancel it" Bata sake sauraronsa ba ta nufi uber din without looking at him, ya bi ta da kallo with astonishment, dariya yayi yace "Whatt? Like seriously.... this little girl played me" jingina yayi da motarsa ya rufe baki yana murmushi yana kallonta yana gyada kai har ta shiga uber din, wato shi zata yi ma wayo, gaskiya tana da wayo, gyada kai yayi ya shiga motarsa ya tada sannan ya bi bayan uber din da ta shiga.... Khaleesat na lura da yanda yake bin uber din da ta shiga a baya, sai kusan karfe bakwai ta isa gidan, ta bude Uber din ta sauka ta nufi cikin gidan da sauri, sai gashi shima yayi parking, ko kashe motar bai yi ba ya sauka ya bi ta yana kiranta, amma tuni ta shiga gidan zuciyarta na bugawa, hakan yasa ya tsaya ya bi ta da kallo har sannan yana murmushi yana gyada kai, sai da ya kare ma babban gidan kallo sannan ya juya ya koma motarsa, Khaleesat tana hardewa ta isa har kofar shiga gidan tana jin gabanta na faduwa sosai don gani take kamar ya biyota har cikin gidan tunda ba juyawa tayi ba balle ta gani, bubbuga babban kofar parlon ta dinga yi hawaye cike idonta, amma shiru ba a bude ba, sai a sannan ta lura da madannin kararrawan gidan, ta danna da sauri hannunta na rawa, sau uku tana danna bell din kafin aka bude kofar after almost 5 minutes, ta fashe masa da matsanancin kuka tana kallonsa, Da mamaki yake kallonta daga sama har kasa yace "Me ya faru?" Taki ce masa komai tana rusa masa kuka, bai san sanda yayi mata tsawa ba sounding so apprehensive yace "Can't u speak out? Tell me what is it? Me ya faru?" Cikin kuka tace "He followed me to my apartment" Ya bude ido sosai yace "Who?" Tace "Wannan mutumin nan" Da mamaki yake kallonta babu ko kiftawa yace "Ur apartment?" Ta gyada masa kai hawaye na zuba idonta tace "Ya biyoni har nan gidan ma a cikin motarsa" Yace "Nan gidan??" Tace "Eh, yana waje ban san ko ya shigo ba ma...." Ya cire takalman kafarsa ya saka wasu dake bakin kofar sannan ya fito daga parlon ta bi sa da kallo tana goge hawayen idonta ta jingina da bango, Ajay na fita can waje ya dinga bin Neighborhood din nasu da kallo don babu alamar ko mota daya a waje, sannan kuma babu kowa cause the weather is sooo cold kuma gari yayi duhu, ya juya ya koma cikin gida, har ya iso entrance din shiga parlon kallonsa take, ya hade rai yace "Shiga ciki" A hankali ta juya ta shiga cikin parlon ta cire takalmanta ta karasa ciki ta zauna kan kujera har sannan gabanta bai dena faduwa ba, shi dai Ajay na tsaye bakin kofar parlon gaba daya mamakin Aymaan ya gama cikasa, har ya fara tunanin irin matakin da zai dauka kansa, lkci lkci Khaleesat take kallonsa, after some minutes ya karaso cikin parlon yana kallonta fuska daure yace "Ta yaya ya san apartment din ki har ya je?" Muryarta na rawa tace "Nima wallahi ban sani ba" Ya wani hade rai yace "Kee, kar ki kuskura ki min kuka a nan, don't stress me with your silly cry...." Ita dai bata ce komai ba, yace "Da ya je apartment din naki sai aka yi yaya?" A hankali tace "Ni na manta ban kulle kofar ba da ka tafi daxu, kawai da yayi knocking sau daya shine ya bude kofar ya shigo da yaji sa a bude, and i told him i am going out for shopping yace to zai kai ni, bayan mun fito sai naki shiga motarsa dama nayi ordering Uber, shi ne ya biyo bayan motar da na shiga har muka zo gidan nan" Ajay yace "Da ya je apartment din naki ur common sense bai gaya maki ki kira masa cops ba immediately, ni ranan saboda rashin kunya ba cewa kika yi zaki kira min 911 ba??" A hankali tace "To ba wayar yana sama ba, kuma ai mantawa nayi da cops, i was confuse" Jinginar da kanta tayi jikin kujera bata sake cewa komai ba cause she is already tired, a hankali ta jawo handbag dinta ta bude ta ciro wayarsa ta mika masa tana kallonsa, taga direction din da yake kallo daban yana nazari, ajiye wayar tayi a gefenta, after a while ya juya yana kallonta a takaice yace "Go upstairs" Ta ɗan bude ido tana kallonsa tace "Upstairs?" Ya mata wani kallo yace "Gidan za ki koma yaje ya same ki a can?" A hankali tace "A'a i tot za mu koma gidan tare" Yace "Sai ki zo ki daukeni mu tafi" Daga haka ya nufi stairs, ta wani bi sa da kallo, shi dai komai masifa, sai kuma ta zumburo baki ta kauda kai, har bayan awa daya Khaleesat bata ga ya sauko downstairs ba, tayi ta zama a parlon har ta gaji gashi bata yi sallah ba, bata ji alamar da workers ko daya a gidan ba cause everywhere is so silent, jinginar da kanta tayi da kujera don ta gaji ga wani ciwo da kanta yake mata and she is very hungry, ta lumshe ido tana zaune a haka bacci ya dauketa, cikin bacci taji muryarsa ta bude ido da sauri ta gyara zama, yana kallonta yace "Oh baki tafi saman ba?" Ta hade rai tace "To ni nasan inda zan je a saman?" Yace "Baki san inda Jay ya saba ajiye ki ba?" Kin cewa komai tayi, after some seconds ta daga kai ta kallesa taga hararanta yake, ta mike ta dau handbag dinta ta bar masa wayarsa a kan kujeran, juyawa yayi ya koma sama ta bi bayansa tana tafiya a hankali, tsaye ta gansa a corridor fuskarsa babu yabo babu fallasa, sau daya ta kallesa har zata tafi dakin da ta taba zama a gidan sai kuma ta saci kallonsa tace "Ina zan je?" Yace "Ban sani ba" Juyawa tayi ta dau hanyar bangarensa, ya bude baki da mamaki yana kallonta yace "Kee" kasa daurewa tayi har sai da tayi dariya don ba karamin dariya abun ya bata ba, ta dake tace "To ba kace inda Housemate dina ya ajiyeni ba, ae can zan je" Shi tsabar mamaki ma rasa abinda zai ce mata yayi, can yace "To tafi ki ga ikon Allah" Ta wani kallesa ta juya ta nufi dakin da ta zauna sanda take exam, tana shiga dakin ta kulle kofar, the room was neat amma kana gani kasan an dade ba a zauna a ciki ba, sosai dakin yayi sanyi kamar kankara, tayi dusting gefen gadon sannan ta zauna tana takurewa waje daya, bayan wani ɗan lokaci ta mike da sauri bayan ta tuna bata yi sallah ba, ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito, Heater din dakin ta kunna amma yaki yayi function, a haka dai ta tada sallah bayan ta idar tana zaune saman darduman taji knocking a kofar dakin, tana ta kallon kofar sai kuma ta mike ta tafi ta bude kofar tana kallonsa, a takaice yace "The workers in the house are yet to resume, you can go to the kitchen and sort ur self out, this is the only help i can render" Daga haka ya juya ya bar bakin kofar ta bi sa da kallo, sai kuma ta kulle kofar ta koma ta zauna ta takure waje daya don sanyi take ji sosai gashi bata zo da Jacket ba, duk da yunwan da take ji ta gwammace ta hakura don bazata iya zuwa kitchen ba, har ta kagu gari ya waye a san yanda za ayi da Aymaan ta koma gidanta, amma duk da haka ita dai ta tsorata da wannan apartment din ita kadai a cikinsa, mikewa tayi ta kwanta saman gadon bayan ta kakkabe, ta lulluba da second of the bedsheet don biyu ne a kai amma duk da haka sanyi ta dinga ji kamar bata rufa ba, a haka bacci ya dauketa, wajen karfe goma Ajay yayi knocking kofar dakin, ta bude idonta a hankali don restlessly take baccin saboda sanyi, still dai bata juya ba, ya shiga cikin dakin, ya nufi gun room heater din shi ma ya kunna yaga bai yi ba, ya fi minti daya tsaye dakin, sai kuma ya juya ya fita, dakin Jay ya nufa ya bude ya shiga ya dauko white duvet dinsa, sannan ya fito ya koma dakin da Khaleesat take, sai da ya fara duba tagogin dakin to be sure they are locked, sannan ya rufa mata duvet ya juya ya fita ya kullo kofar, kamshin turaren Jay ya cikata gaba daya, nan da nan ta nemi baccin da take yi ta rasa, and she felt so warm, a hankali ta jawo wayarta tana kallon call logs dinta don har sannan Jay bai biyo kiran da tayi masa ba a apartment dinta, ta kunna data dinta ta duba WhatsApp taga nan ma bai ajiye mata message ba, and she even saw him online, sauke idonta tayi, nan da nan taji hawaye na taruwa idonta ta fita daga WhatsApp din ta shiga contact dinta ta goge numbersa da tayi saving daga wayarta, sannan ta ajiye wayar ta rufe har kanta da duvet din tana kuka a hankali, wajen karfe sha daya saura ta zamo kasa a hankali ta dalilin sharp pain da take ji a abdomen dinta, tana durkushe for almost 10 mins daga karshe ta mike da kyar ta shiga bandaki, sosai gabanta ya fadi ganin period dinta ne, ta kasa fitowa daga bandakin, at last dai ta jawo kafa ta fito tana tafiya a hankali, to yanxu ya za ta yi, ta kalli white bedsheet da duvet din Jay dake saman gadon, ba wai ta fara flow sosai bane amma tasan dai hakan zai iya faruwa ko zuwa anjima, a hankali ta durkusa kasan dakin, bata ma damu da sanyin da take ji ba, ta jawo wayarta tana tunanin yanda zata yi, ko dai tayi order din Uber zuwa apartment din nata, amma dai tsoron komawa gidan kuma take, tana jin alamar saukan period din ta mike a hankali, duk jikinta a sanyaye ta nufi kofa ta bude ta fita, ta dade tsaye corridor kamar mara gaskiya daga karshe dai tayi gathering courage ta karasa har bangaren Ajay, tsaye tayi jikin kofarsa kamar tana tausayin kofar tayi knocking gently, Ajay dake danna wayarsa ya juya yana kallon kofar, ta sake knocking a hankali, ya mike zaune ya jingina da gadonsa ya ajiye wayarsa ya rungume hannu yana kallon kofar, idan yace bai gaji da yarinyar nan ba yayi ma Allah karya, daukar wayarsa yayi, yayi dialing number Jay fuska daure, after some seconds Jay ya daga, Ajay yace "Wai yaushe ma kace zaka dawo ne?" Jay yace "Gobe zan tafi Nigeria" Ajay yace "Na gaji da wannan brat din da ka bar ni da ita a kasar nan, you know i have anger issues, I can't tolerate her anymore wallahi..." Jay dake ta sauraronsa yace "To ka iya ajiyar ribbon for more than 2 months, me ribbon din ce baza ka iya ajiyewa under your watch ba?" Shiru Ajay yayi, Jay yace "Hang up pls, Mami tana kirana" Ajay ya kalli screen din wayarsa don daga can bangaren Jay ya katse wayar, ajiye wayar Ajay yayi idonsa akan screen din ko kiftawa baya yi, after almost a minute yace "What is he talking about, meye ma ribbon?" A hankali ya dau wayarsa ya shiga Google yayi typing ribbon..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa bello jidda* 07087865788 Read my book "HALYSAAH" on ArewaBooks, Platform available: "app only" :: https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 HALYSAAH 65 Ajay ya ajiye wayar hannunsa bayan ya ga abinda google ya bayyana masa a matsayin ribbon, kamar zai sake kiran Jay kawai ya fasa ya ja tsaki ya jingina da gadonsa kalmomin Jay na ci gaba da yi masa yawo a kai, sai kuma ya kalli kofar dakinsa don har sannan Khaleesat bata dena knocking continuously ba, kamar bazai tashi ba sai kuma ya tashi daga karshe ya nufi kofar, bude kofar yayi fuska daure yana kallonta without saying anything, ta ɗan koma baya taki barin su hada ido a hankali tana wasa da fingers dinta tace "Don Allah dama gida nake son ka kai ni pls...." Ya dakatar da ita yace "Sai na kai ki? Baki san hanyar gidan ba, ko ni na kawo ki?" Ta daga kai ta kallesa ta ma rasa abinda zata ce, ya wani murtuke fuska yace "Ni ba Jay bane da kike ma iskanci iri iri kina controlling din sa" Juyawa tayi a hankali ta bar bakin kofar yayi banging kofarsa ya kulle, ya koma ya dau wayarsa har yayi dialing number Jay sai kuma ya katse kiran ya ja tsaki, Khaleesat na komawa dakin da take ta dau handbag dinta da wayarta sannan ta fita daga dakin, tana tafiya a hankali ta sauka downstairs ta nufi kofar fita daga babban parlon sai taga kofar a kulle, duk kokarin da tayi na ganin ta bude kofar ta kasa budewa gashi bata ga makulli a jiki ba, ta fi minti biyu tsaye bakin kofar tana jin tana flow a hankali, ta juya ta kalli hanyar sama, komawa tayi tana tafiya kamar bata so ta nufi bangarensa, jingina tayi da bango kamar bazata kwankwasa kofar ba sai kuma dai tayi knocking din kamar tana tausayin kofar, Ajay da har ya kashe wutan dakinsa ya kalli kofar babu ko kiftawa, sai kuma ya gyara kwanciyarsa bai motsa daga inda yake kwance ba, Khaleesat ta fi minti biyar bakin kofar bata kuma fasa knocking din da take ba, cire Duvet din jikinsa yayi ya jefar gefe sannan ya sauka daga kan gadon fuska daure ya nufi kofar ya bude yana kallonta at the same time cutting her a serious warning yace "Ki ka sake knocking din min kofa zan maki walakanci wallahi, why are you such a nuisance? Pls get out before i loose my temper" Khaleesat dake kallonsa ta wani hade rai tace "To ta window kake son in fita daga gidan bayan kofar parlon a kulle yake??" Yace "Ki bi ta roof ma ba window ba" Yana fadin haka zai kulle kofarsa tayi saurin shiga cikin dakin kamar zata fashe da kuka ta nufi tsakar dakin ta tsaya tace "Kasan dalilina na cewa zan tafi gida ne? Kawai kayi ta ma mutum masifa baza ka tsaya kayi considering dinsa ba ka basa listening ears, kawai haka nan zan taso cikin daren nan in ce zan tafi gida? Ni ban ce sai kai ka kaini ba ka zo kawai ka bude min kofa inyi tafiyata...." Magana take amma gaba daya hankalin Ajay na kan dakinsa da ta shiga kai tsaye, he look shock irin he didn't see that coming, he ignored her ailment that he understood immediately, ya ɗan yi calming din kansa yana kallonta yace "Saboda kin ga ranan ya shigo dake nayi persuading kaina ban yi reacting ba sai kika yi zaton public room ne wannan? An gaya maki ko shi Jay din yana shigar min daki anyhow? Baki da hankali ne or are you out of ur mind? Come and get out before u push me to the wall, kuma kar ki kuskura ki taka min carpet dina da wannan kafafuwan naki, wannan filthy dakin da kika shiga kika kwanta duk ƙura da datti common sense dinki bai gaya maki ki share dakin ki goge ba sannan kiyi changing bedsheet, sannan zaki shigo min daƙi ki kakkabe min duƙ kuran da kika kwasa a jikinki ki cuceni, plss come and get out before i loose my temper...." A fusace ya kare maganar yana kara bude mata kofa da kyau ta yanda zata zo ta fita, Khaleesat ta wani taɓe baki tace "To ai sai kaje ka bude min kofar parlor" Tsawa yayi mata yace "Baza ki fice min daga daki ba?" Ta fashe da kuka ta nufi kofar tace "To kasan me yasa zan je gida ne, ko ba saboda urgent issue bane" Yace "Ke kika san urgent issue din, get out of my room" Ganin he is damn serious don gaba daya mood dinsa ya canza tun da ta shiga dakin yasa ta fita daga dakin tana kallonsa tace "Don Allah ka bude min kofar parlon before it's too late" Banging kofar dakinsa yayi ya kulle, Khaleesat ta dinga kallon kofar, after a minute sai gashi ya fito, ya saka takalmin da yake yawo da shi a gidan, ta bi sa da kallo sai kuma ta bi bayansa tana hararansa, downstairs ya sauka ya tafi ya bude mata kofar parlon, tana tafiya a hankali ta karasa bakin kofar sannan ta fita tana kallonsa, kulle kofar parlon yayi, Khaleesat taji wani sanyi don iya Hijab ne jikinta babu rigar sanyi, walking slowly ta fita daga compound din gidan gaba daya wani mugun sanyi ke shigarta, sai yanxu ta kara tabbatar da Ajay mugu ne kuma ba shi da conscience, ta ciro wayarta taga ko zata iya order din ride, tana ta tsaye a Neighborhood din bayan ta duba ride din, after almost 5 minutes taga hasken fitilar mota daga compound din gidan, dauke kai tayi har ya fito da motar, taga yayi parking inda take tsaye, ta wani kallesa, fuska daure yace "Do not waste my time Malama" Ta wani tura baki ta bude front seat, sai dai kuma tsoro take kar ta zauna ta ɓata masa motar ta shiga uku, haka dai ta shiga sai bata sake jikinta gaba daya a zaune ba, tana shiga ya ja motarsa, har suka isa apartment dinta bai ce mata komai ba, bayan yayi parking murya can ciki tace "Nagode" Daga haka ta sauka daga motar ba tare da ta kallesa ba ta nufi kofar apartment dinta ta bude da makulli ta shiga ciki, bata kulle kofar ba ta tsaya jikin window ta ɗan bude labule kadan tana lekawa taga ko ya tafi, haska inda ta zauna taga yana yi da wayarsa, ta zaro ido ta juyo hijab dinta da sauri sai taga bata yi stain ba, ta sake kallonsa taga ya gama haske haskensa ya kashe fitilar wayan, ta ma san kilan ya gane me yasa tace zata dawo gida, turo baki tayi saboda kunyan da taji, tana ta tsaye jikin window har bayan minti biyar bata ga yayi Reverse ba, ita kuma so take taga tafiyarsa sannan ta kulle kofarta da makulli don saboda zuwan da yayi daxu ya bar mata kofa a bude Aymaan ya fado mata gida kamar barawo, bude motar taga yayi after almost 10 mins ya fito, sai da taga ya nufo kofar apartment din sannan ta ruga sama da sauri ta shige dakinta... Ko da Khaleesat ta shiga bandaki taga hatta kayan jikinta ma bai yi stain ba, pad din da ta siyo tun daga Nigeria ta dauka a cikin akwatinta, bayan ta gama gyara jikinta ta fito ta canza kaya sannan ta saka rigar sanyinta ta kwanta, wajen karfe dayan dare Khaleesat ta farka daga baccin da ya dauketa a firgice duk da bata dade tana baccin ba ta mike zaune zuciyarta na bugawa, mafarki tayi wai Aymaan ya zo yana ta bubbuga mata kofa, dama kuma har tayi bacci hankalinta na kan kofar parlor ko ya tafi ya kulle mata kofar ko a bude ya bar mata oho, a hankali ta sauka daga kan gadon ta bude dakinta ta fita corridor tana leka downstairs, kwance ta gansa kan kujera idonsa a lumshe ya maida wutan parlon zuwa dim light, a hankali ta sauka downstairs din yanda bazata yi making sound ba, after some seconds ta koma sama ta dauko masa duvet, tana dawowa parlon ya bude ido, ta koma baya tana kame kame tace "Duvet ne, naga akwai sanyi sosai yau...." Ya nuna kansa yace "I should use ur duvet? Me? Ke da kika iya shiga daki duk ƙura da datti comfortably ki kwanta shi ne zaki kawo min duvet din ki i should use saboda nayi hauka, ai duk macen da zata iya zama comfortably cikin daki me datti da ƙura without cleaning it, kuma ta dinga yawo a gida babu takalmi a kafarta to babu kalan kazantar da bazata aikata ba, shi yasa taku ta zo daya da Jay, bird of the same feathers, ba gwara in kwanta sanyi ya kasheni ba da inyi amfani da abinda ya fito daga dakin ki, kujeran nan ma don sabbin furnitures ne yasa na kwanta" Khaleesat ta wani kallesa, sai kuma ta juya ta koma sama da duvet din, kuma sabo ne ko amfani da shi bata taɓa ba a ledansa ma ta ciro yanxu, can kasan ranta ta dinga ce ma kanta Allah ya kara mata, tsaki ta ja bayan ta shiga daki ta kulle kofarta da makulli tayi kwanciyarta. Washegari wajen karfe bakwai Khaleesat ta fito daga dakinta, bata gansa a parlon ba, hakan yasa ta sauka downstairs ta tafi kofar ta murda taji a kulle, ta leka garage taga babu motarsa, tabe baki tayi ta wuce kitchen don dama da yunwa ta kwana, sai wajen karfe goma ta gama duk abinda take ta bar gidan zuwa school, har suka gama lectures bata sake fuska ba ranan, tun Safiyyah na jan ta da magana har ta gaji ta kyaleta, bayan sun fito department Safiyyah na kallonta tace "Is there any problem Khaleesat? Naga gaba daya yau mood dinki babu kyau" A takaice Khaleesat tace "Nothing" Safiyyah tace "Ke dai ki gaya min gaskiya, kila ma haushina kike ji ban sani ba ma" Sai a sannan Khaleesat ta kalleta tace "Saboda me bazan ji haushin ki ba Sophie? Kawai kin ja ɗan iska mara kamun kai ya shigo rayuwata ina zaman zamana, you caused me all this wallahi" Safiyyah tayi shiru, sai kuma a hankali tace "Wai Aymaan? Wallahi ban san ɗan iska bane Khaleesat, kin ji na rantse, na zata yana da kamun kai ne yanda nake ganinsa sumi sumi a department" Khaleesat tace "To jiya wajen karfe shidda na yamma sai gashi a apartment dina unfortunately na bar kofa a bude kawai ya fado min cikin parlor kansa tsaye" Bude baki Safiyyah tayi tana kallon Khaleesat ko kiftawa babu with shock, a hankali tace "Apartment din ki kuma Khaleesat? Na shiga uku, sai aka yi yaya?" Khaleesat taki bata amsa don takaici, Safiyyah ta hade rai tace "To kuwa sai nayi masa hauka, uwarsa yaje nema maki a gida ko an gaya masa kowa shege ne kamar sa?" Kallonsa kawai Khaleesat take daga nesa har ya nufo inda suke zaune, Safiyyah kuwa ko lura da shi bata yi ba rai bace take cewa "To ke baki kira masa Cops ba? don Allah ki gaya min sai aka yi yaya da yaje apartment din naki? Yau ga mahaukaci kai" Juyawa Safiyyah tayi ganin shadow din mutum a gabansu, yana kallon Khaleesat da kyau yace "Kara ta kika kai gun wancen garan don ya min me? Me kike tunanin zai iya min? Muscles dinsa na banza har ni zai nemi ya daka? Who did he think he is? Me yake takama da shi? Sarautar tasu da bata taka kara ta karya ba ko me? Sannan naga kamar yana mance a America mu ke not Nigeria, ni zai nuna ma dabanci bai san course dinsa nayi a Nigeria ba?" Safiyyah ta mike tace "Look Aymaan, ita fa Khaleesat ba irin wa ennan shegun matan da kake tunani bane gaskiya, ka bar ganinta sakaka a Amurka, yarinya ce ita me mutunci da ta san ciwon kanta, kuma harkar duniya bata gabanta wallahi, wannan get together din ma ni na ja ta don dole taje ba wai ra'ayinta bane shi yasa throughout ta kebe gefe daya a wurin u saw that too, shi kuma wanda kake kira da gara fiance dinta ne, ba wai shisshigi yake yi ba, sannan sarautarsu kuwa ta taka kara ta karya don gidansu a nan Amurka ma ba ko wani shege bane a Nigeria ke iya mallakan irin wannan babban gidan a wata kasar, kai kuma naga hayan apartment kake a Amurkan, Sannan iyayen Khaleesat basu fara turata wata kasa karatu ba sai da suka tabbatar da mijinta a hannu, kuma shi ma a kasar yake, ka ga ai baza kace masa gara ba" Aymaan na mata wani kallo yace "Ke ki iya bakin ki kar ki ja ma kanki matsala a rayuwarki, Fiance din banza, a ina Fiance ya zama miji? ranan daurin aure ma an fasa balle common Engagement, shi da Engagement din yake takama dama?" Safiyyah tayi wani shewa tana rike kugu tace "Na ga kamar ba zaman lafiya kake so ba Malam, to wallahi idan baka fita harkar kawata ba a kasar nan a gaban idon ka zan kira maka 911 in lafta maka sharrin da babu me fitar da kai sai Allah, kamar yanda ka fada nan ba Nigeria bane tuni za ayi mana maganinka wallahi, kuma Unguwan da take tsaf za a bincika surveillance camera a ga sanda ka shiga apartment dinta ta yanda za a tabbatar ba sharri aka maka ba..." Aymaan ya gyara tsayuwa yana kallonta da kyau yace "Really?? dama ke mahaukaciya ce ban sani ba?" Safiyyah tace "Dawanau ce ni karewa, wallahi idan baka yi hankali da mu ba a kasar nan zaka ga jahilci tsantsa, ai ni da nake ganin ka sumi sumi a makaranta ban san gogaggen dan iska bane kai sae yanxu, to banda ɗan iska waye zai fada apartment din mutum kamar gidan ubansa? Ashe dama ciwon ƙwaƙwalwa gare ka ake yada jita jitar ciwon zuciya gare ka?" Har ya daga hannu zai wanka mata mari sai kuma ya rike fist dinsa ya cije hakora yana kallonta yana huci, Safiyyah tayi wani dariya tace "No slap me, try it plss, mare ni mana.... wallahi rabon ayi deporting dinka back to Nigeria a cikin jirgin ruwa ne ke tunzura ka, try slapping me ka ga ikon Allah" Yace "Daga ke har kawar taki zan yi maganin ku wallahi...." Daga haka ya juya kamar zai tashi sama ya bar wajen, Safiyyah tace "Ni wallahi da aka ce min babanka Deputy ne sai da kunya ya kamani ranan na rufe fuska, na zata ɗan vice president ne kai irin wannan jijji da kan da kake ashe common Deputy ne ma da ba a san da ku ba a Nigeria, kuma in ka fasa maganinmu baka cika namiji ba wallahi, dama ana ganinka an ga kwararren ɗan shaye shaye ɗan codeine, ban san wani tsautsayin yasa har mu ke gaisawa da kai ba banda nima dai gantalalliya ce bani da kamun kai" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* _Assalamu Alaikum yan mata da matan Oga ina me maku albishir da cewa Han-Ash skin beauty ta zo maku da kayan gyaran jiki iri iri wanda zai mayar da fatarki kamar Madara ta yanda duk inda kika shiga sai an kalleki, ki sai mayukan da zesa fatar ki tayi kyau, muna kuma maraba da siyan daya ko sari, i am assuring you that duk wani product dinmu is tested and trusted, ga kuma arha, for more information contact Han Ash via 0902 469 2720_ HALYSAAH 66 Khaleesat tsabar yanda ta zama shock kasa cewa komai tayi a inda take zaune kamar ruwa ya cinye ta, ta shiga uku ita kam ga kuma wani da yafi Abdul tashanci, Safiyyah na huci tace "Ta shi mu je, don dai ban san yanda ake yi bane a kasar nan, da Nigeria ne ai daga nan police station na nufa in je in kai report, to su nan ban san ko ana haka ba" Ita dai Khaleesat ta kasa tashi don duk jikinta yayi sanyi kamar an watsa mata kankara, Ganin Khaleesat taki tashi Safiyyah tace "Ki tashi mu tafi don Allah kar ya sake dawowa" Khaleesat ta kalleta tace "In tafi ina? Am not going anywhere Safiyyah, haka kawai in koma apartment dina ya bi ni can?" Safiyyah na huci tace "Kuma fa haka ne" Khaleesat ta dafe kanta da yayi mata nauyi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Safiyyah tace "Wannan fa kamar ya fi Abdul zama ɗan daba, ni wallahi ban san haka yake ba da ko hanyar da ya bi a makarantar nan ma bazan dinga bi ba, in ba dai in danna 911 yanxu su taho ba gaskiya" Khaleesat ta wani kalleta tace "Su taho su yi maki me? Kar kiyi dialing ki bari sai na bar nan tukunna" Safiyyah ta koma ta zauna tayi tagumi, Khaleesat ta bude handbag dinta duk jiki a sanyaye ta ciro wayarta, ta fi second talatin ta kasa dialing number Ajay don ta tsani masifarsa ita kam, but did she have a choice? Haka kawai ta koma Apartment dinta Aymaan ya bi ta ko kofar a kulle yake ya balle ya shigo mata ta shiga uku, ita sai yau ma ta kare masa kallo kana ganinsa kaga someone on drug shi yasa idonsa suka zama kamar me sexy eyes ashe tsabar shan kwaya ne, Safiyyah ta kalleta tace "Dole dai wancan mara mutuncin za ki kira, don ni wallahi bana son Ajayn nan gwara Housemate sau miliyan, ki ji fa ranan har da korata saboda kawai zai maki magana sai kace bai san yanda muke da ke ba, ya maida ni kamar wata bare ranan, abinda Housemate dinki bazai taɓa yi ba kenan yace in tashi wai zai maki magana, tun daga ranan na kullacesa a raina wallahi, ashe haka yake da baƙin hali ban sani ba, nace masa good afternoon wai ya amsa da evening tsabar rainin hankali, pls i don't like him" Khaleesat tace "To ina da wanda zan kira bayan shi ne?" Safiyyah tace "Yaushe Housemate din naki zai dawo ne? Gaskiya we are missing him yayi maza ya dawo" Khaleesat tace "Oho" Daga haka tayi dialing number Ajay, sai da ya katse ta sake kira sannan ya daga, taji yace "What again Madam?" Hurriedly yayi tambayar as if in a haste to cut the call, ta sauke idonta a hankali tace "Zuwa yayi ya same mu a department ni da Safiyyah" Ajay yayi shiru, sai kuma yace "Sai aka yi yaya?" A sanyaye Khaleesat ta gaya masa abubuwan da ya zo ya fada da kuma yanda suka yi da Safiyyah daga karshe, Ajay dake ta sauraronta yace "Kin ga wannan kawar taki me shegen rawan kai sai ta ja maki bala'in da baki yi tunani ba a rayuwarki, who sent her to exchange words with him? Duk ba ita ta kai ki inda kika hadu da gayen ba? And meye kike son in maki da kika kirani yanxu?" Khaleesat ta katse wayarta ta ajiye, Safiyyah dake ta kallonta tace "What is he saying?" Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba, sai ga wayarta ya fara ring ta duba taga shi ke kiranta, Safiyyah ta taɓe baki tace "Allah sarki Housemate gaskiya yana kokari da wannan Ajay din ashe haka yake? Wallahi yanda kika san Malamin islamiyya haka nake ganinsa ni dai yanxu, kullum a fusace yake, ki daga kar ya katse, ni yanxu na gaya ma Mustapha wannan magana ai zai gano na tafi Party bayan ce masa nayi baki da lafiya zan je apartment din ki daga schl ranan" Khaleesat tayi picking call din ta kai kunne taki cewa komai, yace "Kashe min waya kika yi?" Tace "To me zan yi idan ban kashe ba, kawai kayi ta ma mutum masifa kullum" Yace "Sai ki je kiyi sorting self din ki out" Daga haka ya katse wayarsa, Safiyyah tace "Tirrr, anya wannan zai iya zama da mace kuwa? Ina ga a world din da ya tashi iya maza ne kawai suka yi surrounding dinsa, amma sam bashi da sympathy wa mace, kawai tashi zaki yi mu tafi gidan Yaya Mustapha don nima ban baki goyon bayan zuwa apartment din ki ba, Aymaan drugs din da yake sha basa gaya masa gaskiya" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, gaba daya taji zaman America din ma ya fita kanta har ma da karatun, shikenan ita daga wannan sai wannan a rayuwarta, hawaye taji ya cika idonta, Safiyyah tace "Ke kuma matsalata dake kenan, komai sai kice kuka kamar wata er yaye, Meye abun kuka kuma? Ni fa ina da strong mind yanda bakya zato" Ita dai Khaleesat goge hawayen idonta kawai take don ta gaji kuma haka, Safiyyah ta tabe baki ta koma gefe, haka suka zauna for almost 10 minutes a wajen kowa da tunanin da yake a ransa, murya can kasa Safiyyah tace "Kin ga kuma gashi can zuwa, wannan mutumi dai bashi da alkibla" Khaleesat ta daga kai tana kallon inda Safiyyah ke kallo, lkci daya ta dauke kai fuskarta a daure, A hankali Safiyyah tace "Ni dai kinga tafiyata...." Daga haka ta dau handbag dinta kamar munafuka ta bar wajen kan Ajay ya karaso, har Ajay ya iso wajen Khaleesat bata sake kallon direction dinsa ba, Yana kallonta yace "Rashin kunyan ki har ya kai ki dinga katse ma mutane waya yanxu?" Ta wani kallesa amma taki cewa komai, sai kuma ta kauda kai, yace "Ba magana nake maki ba?" Bata fuska tayi tana shirin kukan da ya tokare mata a makogwaro yace "Sai dai kiyi ma kanki kuka ba ni ba, and in case u don't know.... work load dake kaina yafi karfin duk wani kananun issues din ki, Jay ne yake iya combining both ni kam bazan iya ba, i will be taking you home ki zauna can har sanda Jay zai dawo ku ci gaba daga inda ku ka tsaya, i don't have much time to be fighting with a tout because of you" Ita dai bata ce komai ba, ya hade rai yace "Baza ki tashi ba?" Mikewa tayi without looking at him, ya juya ya bar wajen ta fara bin bayansa tana hararansa, can apartment dinta ya fara kai ta, bayan yayi parking yace "Kar ki bata min lkci ki shiga ki dauko duk abinda zaki bukata for now, don't waste my time" Bude motar tayi ta sauka ta nufi apartment din, sai da ta ɓata kusan minti ashirin a cikin gidan bata fito ba, patient dinsa ya kare ya dau waya zai kirata kenan ya ga motar da ya tsaya dai dai apartment din, kallon motar ya dinga yi don ya gane motar waye, wanda ke cikin motar na ganin motarsa sai yayi gaba ya wuce apartment din yana driving slowly, Ajay ya dinga kallon motar da mamaki, wato uban fist din da yayi masa banda frnds dinsu sun shiga tsakani bai ishesa ba kenan, few a cikin abokan Aymaan are also his frnds shi yasa matter din ma bai yi escalating ba har suka shiga tsakaninsu suna ba Ajay hakuri, amma fa Aymaan ya sha kulli kafin abokan su yi intervening, haushin hakan yasa yaje ya samu su Khaleesat a department dinsu, sai kuma yanxu gashi ya sake biyota gida, Ajay ya gyada kai, ya ci sa'a ba a Nigeria suke ba, wayarsa ne ya fara ring ganin Jay ke kiransa ya daga, daga daya bangaren Jay yace "Yarima me yasa baza kayi respecting title din da kake holding ba pls, why are you like this? menene ya kai ka fada da Aymaan? A America ku ke fa ba Nigeria ba Bruh" Ajay dake sauraronsa yace "Ai ba mu yi fada ba, kilan dai nan gaba za mu yi, don sai na karya masa hannu in bai yi hankali ba, dama naga ba shi da Stamina bugu daya ya tafi kasa don haka karyasa ba wahala zai min ba..." Jay ya ja tsaki yace "Can you hear ur self plss? I will report you to Abba in dai baza ka dena wannan abun da kake yi ba, kai bini bini ka kai fist kamar wani ɗan dambe? who does that pls, haba wannan zubar da class dinka kake wallahi" Ajay yace "To wa ya jawo? Ba kai da wannan brat din bane ku ka ja har nake fada? Da baka bar ni da ita ba hakan zai faru ne?" Jay yace "A'a dama can hannunka kaikayi yake, stop using us to cover ur foolishness, sannan ni ban bar ka da ita ba because i know she is old enough to care for her self with no supervision kai ne dai ka maida care dinta hannunka voluntarily for reasons best known to you, Kuma ni ba gashi nayi ma Aymaan din magana ba kuma ya fahimce ni, amma kai komai sai ka sako hargagi ciki kamar jira kake ka fara dambe" Shiru Ajay yayi, kawai sai yayi ignoring wasu daga maganganun Jay yace "Ohk, kayi masa magana shi yasa naga motarsa yanxu a kofar apartment dinta ko?" Jay yayi shiru, sai kuma yace "Kai me ya kai ka apartment dinta?" Ajay ya katse wayarsa ya ajiye, sosai yaji Jay ya bata masa rai, and he was boiling from inside, ji yayi kamar ya ja motarsa yayi tafiyarsa ya bar ta da faith dinta a gidan tunda dama ba idea dinsa bane dawowarta America, har ya fara reverse amma kuma sai ya kasa tafiya, ya sake kallon direction din da Aymaan ya bi yaga babu motarsa alamar ya tafi, Jay ya dade bai ɓata masa rai kamar haka ba, kawai ya dau wayarsa ya shiga contact dinsa ya danna masa block sannan ya ajiye wayar, sai ga Khaleesat ta fito daga apartment dinta, ko kallonta Ajay bai yi ba har ta gama saka duk abubuwan da ta dauko a back seat don taga bai bude booth ba babu kuma alamar zai bude, bayan ta kulle seat din ta bude front seat ta shiga motar ta kullo kofar a hankali, ita ma bata kallesa ba kamar yanda shi ma bai ko kalleta ba ya fara reverse din motar. Har suka isa gidan ba abinda yace mata ita ma haka, yayi wucewarsa ciki ya bar ta da kayanta, haka nan ta dauka kayan bit by bit tana shiga da su gidan, har sannan yana tsaye parlor waiting for her to finish, sai da ta gama shigo da kayan babu yabo babu fallasa yace "Meet me in the kitchen" Daga haka ya nufi kitchen din ta bi bayansa, Utensils da aka kebe a kitchen din ya nuna mata wajen da suke a takaice yace "That is a no go area, duk ma me zaki taɓa a kitchen din nan banda su" Yana kai wannan ya fice daga kitchen din ta dinga kallon Utensils din ba ma sae an gaya mata ba ta gane iya shi ke amfani da su, can ta tabe baki ta juya ta fita, bayan ta kai duk abubuwan ta dakin da ta sauka jiya taji wayarta dake jaka na vibrate, ta dau jakan ta bude ta ciro wayar, sosai gabanta ya fadi ganin number Housemate dinta, duk da tayi deleting number amma tsaf yana kanta don special digits ne bbu wahalan haddacewa.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* https://chat.whatsapp.com/I7uDGV8V2DQDVS5RHRi0St wa.me/2347031524695 Kina neman inda zaki samu ingantattun kayan gwanjo wato thrifts ma yaran ki kwantar da hankalin ki yar uwa oumokasha thrifts store ta kawo muku kala kala kaya na fita kunya akan farashi mai sauki tun daka kan overalls jumpsuits bodysuit bibs jeans tops blouses da sauran kaya na kece raini from 0 to 15 years Location kaduna and abuja Nation wide delivery 🚚 wa.me/2347031524695 HALYSAAH 67 Khaleesat ta zauna gefen gadon dakin tana kallon screen din wayarta, zata yi picking call din ya katse, it took her almost 2 minutes before returning the call amma har ya katse bai daga ba, ta dinga kallon wayar waiting to see if he will call back amma har bayan minti goma bai kira ba, hakan ya sa ta ajiye wayar a hankali ta mike ta fara gyara dakin, ta sauka downstairs tana dube duben inda zata ga abun shara da goge goge na gidan, har ta fidda rai da samu sai gashi ta gani a under stair storage din gidan, bayan ta gama gyaran dakin da take ciki da Babban corridor din sama sai kuma ta sauko downstairs ta fara gyaran babban parlon hade da goge goge, it took her almost 2 hours kafin ta gama aikin gidan gaba daya, kitchen kuma bata ga abinda zata gyara ba cause it was very neat and tidy alamar yana gyarawa a ko da yaushe, ta maida Household cleaners din da tayi amfani da su a under stair storage din da suke sai gashi yana saukowa downstairs ya canza kayan jikinsa, yi yayi kamar ma bai san me tayi ma gidan ba ya dau makullin motarsa da ta ajiye saman Centre table ya nufi kofa ya fita daga parlon, tabe baki tayi ta tafi sama don ta gaji sosai ba kadan ba, sai da tayi gyaran gidan sannan ta kara tabbatar da girman gidan. Khaleesat na zaune a daki da laptop dinta a gabanta tana studying wani course dinsu da za su yi test dinsa ranan monday, it was a Saturday afternoon, ta juya ta kalli wayarta dake vibrate, sau uku kenan Safiyyah na kiranta taki picking don tasan me zata ce, can dai ta jawo wayar tayi picking ta kai kunne tayi shiru, daga daya side din Safiyyah tace "Haba mana Khaleesat don zaki koya min abu sai kiyi ta min walakanci gashi test za mu yi ranan Monday, is it fail that you want me to fail?" Khaleesat ta sauke wani ajiyar zuciya tace "To ya kike son inyi Sophie? i said u should be coming kin ki" A fusace Safiyyah tace "A'a wallahi bazan zo wannan gidan ba kinji har na rantse, haka kawai in zo ya koreni, shi ba wai kara garesa ba balle ince zai ji kunyan korata, gaskiya bazan zo ba don zan iya zaginsa idan ya koreni" Khaleesat tayi dariyar da bata yi niyya ba tace "Wai ban gane ya kore ki ba, why will he do so bayan yasan wajena ki ka zo" Safiyyah tace "In dai baza ki zo school din ba shikenan kawai i will look for another person to teach me, ni kinsan ba gane lectures nake a aji ba sai in an min bayani dalla dalla gani ga mutum" Khaleesat dai tayi shiru tana jin ta, Safiyyah tace "Sai anjima don Allah...." Khaleesat ta ɗan yi murmushi tace "To let me see if i will be able to come, kin ga karfe biyu da rabi yanxu fa, da tun jiya sai ki gaya min ai, kina school ne?" Safiyyah tace "Eh mana, tun 12 na shigo schl ai" Khaleesat tace "Ohk, i will be coming now" Katse wayar tayi, ta sauka daga kan gadon ta canza kayan jikinta ko rigar sanyi bata sa ba don sanyin ya ragu sosai yanxu, ta dau backpack dinta bayan ta saka laptop ciki ta kashe wutan dakin ta fito, downstairs take leke daga passage way din da take tsaye, ta ga Ajay zaune parlon da wasu turawa biyu alamar frnds dinsa ne ga wine a gabansu, she can't even remember the last time da suka hadu a cikin gidan da shi, it is more than a month now da take gidan amma zata iya kirga sau nawa suka yi crossing part da shi a gidan, yawanci yana bangarensa take fita school da safe, kuma daya daga ma'aikatan gidan ne ke dropping dinta sannan ta gaya masa sanda zai je ya daukota kamar dai yanda aka basa instruction yayi, in kuma aka dawo da ita gidan bayan ta gama lectures zata ga babu motar Ajay a compound alamar ya fita, tunda a daki take zama bata sanin sanda yake dawowa gidan, the next day kuma the same process will repeat it self, girki kuwa tunda tayi sau uku da shi taga duk bai ci ba don ko kusa da abinda ta dafa baya zuwa kawai sai ta dena sai dai tayi nata ita kadai, but tayi noticing anyi restocking foodstuffs irin na Africa a kitchen din probably because of her, don ita duk wani ciman turawa ba damunta yayi ba, may be yayi noticing hakan ne yasa ya siyo mata irin wanda take so, gyaran gida kuma tunda workers din are around iya dakin da take ciki kawai take gyarawa, tana saukowa downstairs ta gaida friends dinsa sannan ta kallesa shi ma ta gaishesa, bai amsa gaisuwan ba without looking at her yace "Ina za ki je?" Ta sauke idonta tace "Zan shiga school" Still not looking at her yace "Ki yi me a school on a Saturday?" Ta ɗan kallesa, sai kuma tace "Tutorial zan ma Safiyyah" Sai a nan ya juya ya kalleta yace "As per the lecturer you are in John Hopkins ko? to baza ki je ba" Tayi shiru tana kallonsa, ya hade rai yace "Ko baki ji me nace ba?" Bata fuska tayi tana kallonsa, ya ci gaba da maganar da yake da friends dinsa, tana jan veil din jikinta tace "To zata iya zuwa nan?" A takaice Ajay yace "Baza ta zo, leave this parlor Madam" Ta wani tura baki ta juya ta koma sama, tana komawa daki ta kira Safiyyah, a hankali tace "Sophie i met the door locked kuma no one is around...." Safiyyah ta katse ta tace "Har workers din gidan?" Khaleesat tace "Kawai ki nemi wanda zai maki Tutorial din Sophie, ranan Monday before the test zan sake yi maki" Safiyyah tace "Ai shikenan, dama ban saka ran za ki zo ba, in ma Ajayn ne ya hanaki shi ya sani don ko a jikina wallahi, dama tun ranan farko da muka je duba Housemate dinki da na fara ganinsa sam bai kwanta min a rai ba naji tsoronsa, wai don Allah yaushe Housemate din ki zai dawo ne abu almost 2 months yanxu, ko dai anyi awarding dinsa doctorate Degree dinsa ne shi ne ya tafi yayi wasu abubuwan a Nigeria? shi kuma wancan uztaz din ko anyi cancelling work dinsa ne yake sakewa daga farko?" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, magana Housemate din nata yake mata balle tasan sanda zai dawo? Kuma kullum da damuwan hakan take kwana take tashi a ranta, ta rasa gane me yasa communicating din da baya yi da ita ya tsaya mata sosai a rai har yake damunta, well... may be he have his reasons, she is not even judging him, but deep down she knows she misses him so much, she misses everything about him, wani lkcn in ta kasa hakuri takan dake zuciyarta tayi masa magana ta WhatsApp, zai kuma yi mata reply amma casually, in yayi mata haka kuma bata iya daurewa sai tayi kuka, last maganar da tayi da shi almost a week ago ta tambayesa yaushe zai dawo, kawai yace mata soon and that was how the conversation ended, after that basu sake magana ba har yau, dama kuma ita ke yi masa, Safiyyah tace "Ni dai sai anjima, ina ta maki magana zaki min shiru katina na tafiya" Daga haka ta katse wayarta, a hankali Khaleesat ta ajiye wayar hannunta a gefen gado. Few weeks later Khaleesat na zaune ranan friday ita kadai a haraban department dinsu, Voice call suka gama da Aunty Farida ta WhatsApp bayan ta turo mata wasu videos da ta kasa fahimta sai kawai ta kira Aunty Faridan don tana online, tunda suka gama wayar Khaleesat ta kasa kwakkwaran motsi a inda take zaune, she looks so confuse and shock at the same time, kamar ance ta daga kai ta ga Aymaan da wata yarinya suna tafiya, yarinyar na ta masa labari da turanci, bata yi kama da er Nigeria ba duk da kana ganinta kasan er Africa ce yarinyar, Khaleesat ta sauke idonta tana kallon wayar hannunta har suka wuce ta, sai ga Safiyyah ta fito daga Hall din karatu da Backpack dinta a hannu, tana isowa kusa da Khaleesat ta zauna tace "Ke baki ga Aymaan ya wuce ba yanxu?" Khaleesat dai tayi shiru don har sannan bata yi recovering daga shock din da take ciki ba, Safiyyah ta kyalkyale da dariya tace "Ni wallahi naji haushi da ya Musty ya neme sa wai har da basa hakuri akan abinda muka masa, me muka masa in ba cowardliness irin na Musty ba? Abinda ma shi ne ya nuna mana halin jakanta, tunda uwata ta haifeni ban taɓa ganin matsoraci kamar Ya Musty ba, ni da nake mace ma na fi sa dakakken zuciya, wai ka samu namiji kamar ka kana basa hakuri, wallahi ban so ace case din nan ya mutu da wuri ba na so ayi ta gwabzawa, na tsani in ga an shashantar da Case me zafi irin haka, bayan hakurin da Ya Musty ya basa naga kamar yana shakkar Ajay ma, kinsan na gaya maki frnd dina Sulaiman ya gaya min ashe narka masa duka Ajay ya so yayi aka maza aka shiga tsakaninsu, amma duk da haka ya sha kulli wajen Ajay, to duk har da hakan ya tsoratasa ya kama kansa da mu, amma nasan zai fake da cewa Ya Musty ne ya basa hakuri, kuma yaga Ajay ya daukeki daga apartment din ki ya maida ki gidansu, kinga ai dole ya tsorata da lamarin, Allah ya sa dai Housemate din ki ma bai ba Aymaan din hakuri ba don daga yanda ya sameni yayi min magana ta WhatsApp sanda abun ya faru har da bani lefi wai me yasa zan yi ma Aymaan rashin kunya wallahi babu tantama shi ma Housemate din naki ya basa hakuri, ni fa na tsani in ga maza suna baya baya da case din tashin hankali kamar wasu mata, shi yasa Ajay ya burgeni da ya nuna masa hauka, wo koma yaya ne dai can ta matse masa shege, ai kinga bai sake bi ta kanmu ba a school din nan, kaiii mun ga jalala ashe lafiyarsa qlau mutumin, sannan bai taɓa aure ba sai yawon iskanci..." Shiru Safiyyah tayi ganin hankalin Khaleesat gaba daya baya jikinta, Safiyyah tayi kasa da murya ta kamo hannunta tace "Me ya faru kawata? Is anything the matter? Naga lafiya na bar ki naje dauko Backpack dina, why the sudden change of mood? Ko Aymaan din yace maki wani abu ne?" Khaleesat ta kasa ce ma Safiyyah komai, sai ga hawaye cike idonta, Safiyyah ta dire jakar hannunta a kasa tace "Subhanallahi, don Allah me ya faru? Me Aymaan din yace maki mu kira Ajay yanxu" Khaleesat na goge idonta cike da karfin hali tace "I spoke with Aunty Farida now" Safiyyah ta zaro ido tace "Me ya faru?" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "Kawai ce min tayi Housemate dina yaje can gidanmu jiya" Safiyyah ta wani kalleta, can tace "Don Allah ji yanda kika sa gabana ya fadi na zata mutuwa aka yi a gidan naku, to don ya je gidanku sai ki fara kuka? Ko dai dama akwai abinda ke damunki kike son kiyi kukan amma sai yanxu kika samu sarari?" Khaleesat ta girgiza mata kai, wasu hawayen na taruwa idonta tace "Gida wai ya siya ma Abbana" Safiyyah ta bude baki da mamaki tana kallon Khaleesat, can ta dafe kirji tace "Gida fa Khaleesat?" Khaleesat ta kasa cewa komai wasu hawayen na sauka idonta, ta bude wayarta ta shiga chat dinsu da Aunty Farida ta tsaya dai dai wajen videos din ta mika ma Safiyyah wayar, Safiyyah was speechless for almost 2 minutes bayan ta gama kallon videos din gidan, wato gida ne har gida irin na zamani that is well furnished, a hankali Safiyyah tace "I am short of words too Khaleesat, wallahi ban san me zan ce ba, but just know that ur Housemate is one in a million Khaleesat...." Khaleesat ta fashe da kuka, Safiyyah ta rungumeta soothingly tace "It's something to be happy about ba kuka za ki yi ba, yanda ya saka iyayenki farin ciki Allah Ubangiji ya dawwamar da shi cikin farin ciki na har abada, Allah ya saka masa da mafificin alkhairi, ya biya masa duk bukatansa na alkhairi, yanxu kina komawa gida sai ki nutsu ki kirasa" Cikin kuka Khaleesat tace "Ko na kirasa baya picking" Safiyyah tayi shiru, can tace "May be he have his reasons Khaleesat, just compose a text for him sai ki tura masa ta WhatsApp, and i will also thank him via WhatsApp on ur behalf, duk wani abun farin cikin ki nawa ne nima...." Ita dai Khaleesat ta kasa cewa komai but she is soo emotional, ta kasa daina kukan da take, a haka driver ya zo daukanta, Safiyyah ta rakata har inda yake parking ta bude mata back seat tace "Don Allah kar ki je gida kina wannan kukan, wannan ai abun farin ciki ne ba na bakin ciki ba da zaki yi ta kuka har haka" Khaleesat ta gyada mata kai kawai tana share hawayenta, Safiyyah ta daga mata hannu tace "Anjima zan kira ki in sha Allah" Nan ma dai kawai kai Khaleesat ta gyada mata a haka drivern ya ja motar suka bar wajen. Bayan sun isa gida Khaleesat ta bude kofar parlor ta shiga da sallama can kasa, kanta a kasa ta gaida Ajay da ta gani zaune parlor da Salem, sannan ta wuce sama, sau daya Ajay ya bi ta da kallo sai kuma ya dauke kansa, after some minutes yana kallon Salem yace "I am going up to get some rest, will you still be around?" Salem yace "Ohk i will wait har ka sakko" Mikewa Ajay yayi ya dau wayarsa sannan ya saka House Slippers dinsa ya wuce sama, kofar dakin da take ciki ya tsaya yayi knocking, Khaleesat da ta kwanta gefen gado ta dora kanta saman pillow feeling so emotional ta mike zaune tana kallon kofar, yana bude kofar ta fara goge sauran hawayen idonta, ya shigo closing the door behind him yana kallonta yace "What happened?" Sauke idonta tayi bata ce komai ba, yace "Ba kya ji na ne?" Girgiza masa kai tayi a hankali tace "Ba komai" Yace "Bakomai zaki shigo ma mutane gida kina kuka?" Ita dai tayi shiru bata ce komai ba, yace "Sake kula ki yayi a school din ne?" Ta daga kai ta kallesa ta girgiza masa kai cikin sanyin murya tace "A'a, kawai kaina ne ke min ciwo" Daga sama har kasa ya kalleta sannan yace "Kukan ya baki magani" Daga haka ya juya ya fita daga dakin.... Wajen karfe biyar Khaleesat ta farka daga baccin da ya dauketa tun bayan da Ajay ya bar dakin, da yake ba sallah take ba, mikewa zaune tayi ta jawo handbag dinta a hankali ta bude ta ciro wayarta, number Housemate dinta da bata kara saving ba har sannan tayi dialing hoping he will pick her call today, amma har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa nan ma bai daga ba, to yanxu me ma zata ce masa ta WhatsApp, words failing dinta kawai za su yi in ma tace tayi masa magana ta can, bata ma san ta yaya zata fara ba, ɗaga kai tayi ta kalli kofar dakin jin ana knocking, sai da aka sake knocking din sannan ta sauka daga kan gadon tana tafiya a hankali ta tafi ta bude kofar, daya daga workers din gidan ne rike da tray din abinci, mamaki tayi don tun zuwanta gidan babu worker din da ya kawo mata abinci har daki, infact ita ce ma ke girka abinda take ci a gidan, ta dai amshi tray din cikin sanyin murya tace "Thank you" Sannan ta juya ta koma daki, bayan ta ajiye tray din ta bude plate din dake rufe a kai taga Jollof rice ne yana tiriri alamar yanxu aka gama girkin, ga wani aroma me dadi na tashi, ta bude wani plate din taga full chicken laps biyu anyi grilling dinsu, sai kuma bowl din veggies da dressing dinsu a gefe, with 2 bottles of water and a glass cup da can drink, still a kan tray din taga maganin ciwon kai, a hankali ta dau spoon ta goge sa da tissue din da aka yi wrapping dinsa sannan ta fara cin abincin, kuma sosai abincin yayi dadi, ya kuma yi yaji kamar a Nigeria aka yi, ta dai ci abinda zata ci ta ajiye sauran for dinner. Washegari still haka aka kawo mata breakfast har daki, bacci ma take tunda ba school zata je ba ta sauka kan gadon ta saka hijab sannan ta bude kofar, bayan ta amshi tray din ta kulle kofar dakin ta tafi ta ajiye breakfast din don sai ta fara wanka.... Wajen karfe biyar din yammacin ranan Ajay na parlor tare da Salem aka bude kofar parlon, tun da ta shigo Ajay ke kallonta da wa enda ke biye da ita a baya, wato jakadiyarta da aminiyarta Hajiya Usaina, sai er aminiyarta da bazata wuce 25 years ba, Salem ya mike tsaye yana welcoming dinta da ladabi, ta amsa masa sama sama without looking at him, sai da ta zauna parlon bayan jakadiyarta tayi saurin gyara mata throw pillow sannan Ajay ya gaisheta, ta amsa cike da isa tace "Daga Massachusetts Boston mu ke, mun je convocation din Afrah a Havard University, we will be passing the night here before leaving for Nigeria tomorrow" Ajay dai bai tanka ta ba, ya gaida aminiyarta warce convocation din er ta suka je a Havard din, Afrah dake ta kallonsa ta gaishesa, ya amsa without looking at her sannan ya mike ya nufi sama, shi dai Salem ya juya ya fita daga parlon, Ajay na haurawa sama direct dakin da Khaleesat take yayi knocking sannan ya bude kofar. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* Shin ke yayar amarya ce ko kanwar ta, ko kawarta ko ma Amaryar ce da kanta, to matso kusa, ina yannen da kannen Ango! Albishirinku!!! Muna sayar da Latest Designs na kayan amarya da duk wani abu da amarya ke sawa, kuma muna fitar da UNIQUE ANKO wanda be cika gari ba, ba nan muka tsaya ba, muna bada haya wato (renting) na kayan amare na kowane events, ina nan a sokoto, kuma ina tura kayana kowane gari. Domin shiga group dina a ga kaya iri -iri, a danna wannan link na kasa. https://chat.whatsapp.com/I5vo38MH2jH8pDvzVF0Q4w HALYSAAH 68 Khaleesat dake karatu da Laptop dinta ta juya tana kallonsa, a takaice yace "Don't look at me that way, ki dau duk wani abinda zaki bukata yanxu zaki koma dakin Jay don muna da baki a gidan...." Ko rufe baki bai yi ba aka bude kofar dakin, ta madubin dakin yake kallonta don tsayuwa tayi bakin kofa tana kallon Khaleesat with mouth agape, Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "Ina yini...." Aunty ta karaso cikin dakin da mamaki tana kallon Ajay tace "Junaid? Wacece wannan kuma?" Ba tare da Ajay ya juya ya kalli inda take ba a takaice yace "Kanwar Salem" da wani expression Aunty tace "Kanwar Salem? Me take yi a gidan nan? Kuma a cikin daki zaune a saman gado?" Sai a sannan Ajay ya juya, looking at her in the eyes yace "The apartment she was staying was sold out yesterday, and she is homeless, so she is here for today before moving to her new apartment tomorrow...." Aunty tace "Da iznin wa kayi hakan? Dama gidan ka ne nan din da zaka yanke hukunci kanka tsaye kamar me gidan? I can't remember his Highness saying this house is urs in anyway Junaid, baka da right, sannan iyayenta da suka turota karatu basu nema mata wani alternative ba sai kai sarkin Hausawan Nigeria dake Baltimore? Beside ban ga ta inda take kama da Salem ba, Salem da yake baki me ya hadasa da wannan farar yarinyar? karya kake yi daya daga matan banzan da kake iskancin ka da su ne a kasar nan, ka zata duk bamu san abinda kake yi ba ne?" Calmly Ajay yace "You can say whatever, kawai dai ni dai i also can't remember Abba saying we are to share this house with you and ur visitors, saboda ni da Jawwad Abba ya siya gida a garin nan ba don kowa ba, don haka ban ga dalilin da za ki dinga zuwa da wasu mutane can babu notice ba ki maida mana gida gidan saukan baki, kaf Massachusetts babu hotels da dole sai kin taho Maryland za ki samu masauki? Beside all this... u are not even in the rightful place to tell me what to do and what not don da sunana da na Jawwad Abba ya siya gidan nan, don haka babu ruwanki da duk wanda zan kawo gidan, since you can't do without intruding, ki zo kiyi intrusion dinki in peace kiyi tafiyarki without questioning me...." Aunty da ta bude baki tana kallonsa tace "Zagin nawa da ka saba zaka yi Junaid? Ni kake gaya ma bakaken magana? Rashin kunyan da ka saba yi min zaka yi a nan ma?" Ajay yace "Whatever, all i know is that u can't just be appearing in here without notice tare da wasu mutane can kina inconveniencing din mu kina sa mana ido" Wani murmushi kawai tayi ta kalli Khaleesat sannan ta juya ta fita daga dakin, gaba daya jikin Khaleesat yayi sanyi ta kasa motsi a inda take, after few seconds ta sauka daga kan gadon tana kallon Ajay da ya kafe ma dressing mirror ido yasan fitar da tayi Abba zata je ta kira, cikin sanyin murya Khaleesat tace "Why will u speak to her that way Ya Junaid?" Ya dakatar da ita fuska daure yace "Ba ruwanki Malama, kin san ta ne?" Khaleesat ta sauke idonta bata sake cewa komai ba, ya juya ya fice daga dakin yana birkita gashin kansa, ga wani zafi da yake ji, where is he even going to start explaining this to his dad for the second time, gashi Jay baya gidan just him and the lady in the house, wani bayani zai yi ma Abba da zai yarda da shi? ɓangarensa ya nufa ya zauna gefen gado ya dafe kansa da yaji yayi masa nauyi, in mahaifiyarsa ce ai sai dai su kashe su rufe tare da ita without her involving his dad in this issue, infact baza ma ta so wani yaji ba, he felt soo emotional, Aunty na komawa downstairs ta zauna kan kujera ta jawo jakarta ta ciro wayarta, Hajiya Usaina dake kallonta tace "Ya naga ranki a bace Fulani?" Aunty tayi wani murmushin takaici tace "Bari dai inyi waya da mai martaba tukunna Usaina" Tana fadin haka ta tafi dakin da take sauka ta tarar da jakadiyarta a ciki tana ta faman goge goge duk da dakin fess yake, zata fita Aunty ta mata alamar ta ci gaba da abinda take, sannan ta zauna kan kujera tayi dialing number mai martaba tana girgiza kafa at the same time tana fatan Allah ya sa ya samu damar daga kiran don zuwa yanxu dai tasan yana ɓangarensa shi kadai, ai ko babu jimawa ya daga kiran, bayan sun gaisa cikin ladabi da kwantar da murya tace "Allah ya taimake ka ya ja zamaninka, mun iso Maryland babu dadewa yanxu" Daga daya bangaren yace "To maa sha Allah fulani..." Ta kara yin kasa da murya tace "Amma Allah ya ja zamaninka ban ji dadin abinda na zo na tarar a gidan nan ba" Shiru Mai martaba yayi bayan yaji me tace, don tana fadin haka babu abinda ya fado masa sai abinda ya gani dakin Ajay kwanaki da ya sauka Baltimore, Jin Mai martaba yayi shiru Aunty tace "Ko kana tare da baki ne ranka shi dade babu sararin mu yi magana?" Calmly Abba yace "Ina sauraron ki" Aunty ta gyara zama tace "Mace na zo na tarar a dakin Yarima cikin wani yanayi mara dadin fade, hankalina yayi matukar tashi ranka shi dade, na dimauce ba kadan ba da abinda idona ya gane min, ban ji dadin hakan ba ko kadan wallahi, kuma da alama ba wannan bane karo na farko, ya saba yin hakan, Allah Ubangiji ya shirya mana su kawai" Mai martaba yayi shiru don sosai yaji abinda ta fada ya dake sa don har sai da ya jingina kansa da kujeran da yake zaune, tayi kasa da murya tace "Amma ba komai ranka shi dade kar hakan ya sa kaji babu dadi a ranka ko kuma ka damu, in sha Allahu idan na dawo sai mu san abun yi, mu san inda za mu billo ma lamarin don baza mu zuba ido a ci gaba a haka ba, kaga wannan big slap to our faces ne idan aka samu labarin abinda yake yi a kasar nan, hakan zai zubar mana da reputation din masarautarmu ne kawai, shi yasa kwanaki nace maka a samu yarinya me hankali da nutsuwa er manya a aura masa ko da kuwa ba er gidan sarauta bace, sai naga kamar hakan bai gamshe ka ba tunda baka ba maganar tawa muhimmanci ba na lura baka son yi masa dole ne, ni kuma abinda yasa na kawo wannan shawaran shi ne saboda shi Yarima ba kula yan matan yake ba a gida Nigeria" Cikin nutsuwa mai martaba yace "Bangaren nasa kika je?" Aunty ta ɗan fara kame kame tace "Ehh can na je ranka shi dade, gani nayi tunda muka shigo gidan ga dai motarsa amma shiru bamu gan sa ba, da yake kwanaki ai ya ɗan yi zazzabi saboda weather sai nayi tunanin to ko baya jin dadi ne, sai na karasa bangaren nasa, shi ne fa idona yayi mummunan gamon nan" Mai martaba yace "If possible try conversing with the lady u saw ki ji er wace jaha ce a Nigeria, ina son sanin background dinta, just Converse with her Fulani...." Aunty tayi shiru bayan taji me Mai martaba yace, can tace "Ranka shi dade ai ba er Nigeria bace matar, baturiya ce fa, kuma irin tsofaffin turawan nan, da kyar ma in bata haifesa ba" Mai martaba ya sauke ajiyar zuciya yace "Na fahimta" Aunty tace "Yanxu dai idan na dawo za mu tsara komai ur Highness, ka kwantar da hankalinka, in sha Allahu anyi na karshe, we will put a stop to this soon, kuma ko makusantan ka na fada don Allah kar ka gaya ma wannan magana, don ba magana bace da ya kamata ace ya fita" Mai martaba was quite, don tunanin da yake yi ma shi daban, daga karshe Aunty tayi masa sallama ya katse wayar, tana kallon jakadiyarta dake zaune kasa tayi murmushi tace "Mace na samu a dakin baƙi, amma ban san tun yaushe take zaune gidan ba ya dai ce min jiya ta zo gidan, sannan babu cin mutuncin da ya mance bai min ba" Jakadiya ta kara bajewa a kasa tace "Ja'iri, gaskiya ya kamata wannan karan ki dau mummunan mataki akan sa ranki shi dade kar ki dau lamarin da wasa, abubuwan da yake maki sun isa haka, duk baya ganin mutuncin ki kuma wannan abu na saka ni damuwa uwar gijiyata, yanxu dai kamata yayi ki kira daya daga ma'aikatan gidan ku kebe ki tambayesa ki ji tun yaushe ya ajiye yarinyar a gidan nan..." Aunty tayi wani murmushi tace "Kin kawo shawara kuwa...." Mikewa tayi ta fita daga dakin Jakadiya na jero mata kirari.... Bayan wani lokaci Ajay ya fito dakinsa ya tafi dakin da Khaleesat take, without looking at her yace "Ina jiran ki downstairs" Daga haka ya fita daga dakin, har zai sauka kasa ganin su Aunty a parlon ga uban kayan ciye ciyen da aka baje masu a tsakar parlon, sai kawai ya tsaya a corridor, a hankali Khaleesat ta mike tsaye ta dau Hijab dinta ta saka ta bude kofar dakin ta fito, yana jin alamar ta fito ba tare da ya juya ba yace "Mu je, kuma ban ce ki ce zaki gaida kowa Downstairs ba" Daga haka ya fara sauka kasa tana biye da shi a baya jiki a sanyaya, tun da suka sauko Aunty da kawarta da Afrah ke kallon Khaleesat, Ajay dai ko kallonsu bai yi ba ya nufi kofa Khaleesat na biye da shi ita ma bata yarda ta kalli direction din su ba, gun motarsa taga ya nufa ya bude ya shiga, ta karaso gun motar ganin bata shigo ba ya daure fuska yace "Baza ki shigo ba?" A hankali ta bude seat din ta shiga, yana kallonta yace "Haka kika fito baki dauko komai ba?" Tayi shiru, sai kuma tace "Ai baka ce min in dau komai ba" Tsaki ya ja ya bude motar ya fita ya koma cikin gidan, ita dai ta bi sa da kallo, dakin da take ya koma ya dau laptop dinta da charger sai wayarta shima da Chargern sa sannan ya fita daga dakin yayi locking kofar yanda ba wanda zai bude ya sauka downstairs, nan ma su Aunty suka bi sa da kallo, Afrah kamar idanuwanta za su bi sa har compound din.... Har Ajay ya isa apartment din Khaleesat bai ce mata komai ba, ita ma dai tayi shiru da tunani iri iri a ranta, kana ganinta kasan duk a sanyaye take, bayan sun sauka motar ya nufi entrance din shiga apartment din ya ciro makullin a aljihunsa ya bude ya shiga parlon, ta bi bayansa. Jay na zaune gaban mai martaba kansa a kasa yana jin duk abinda yake cewa, Cikin nutsuwa mai martaba ya ci gaba da cewa "I am so disappointed in you Ahmad, kana kallon abinda ɗan uwan ka ke yi amma ka kasa gaya min, i am really disappointed, even if you can't tell me directly there are other ways to approach me and i will understand you, to yanxu kana tunanin rufa masa asiri kake yi yana aikata sabo kenan?" Jay ya dago kansa a hankali, after few seconds murya can kasa yace "Abba ba abinda ku ke tunani bane, i promise you Junaid is doing nothing that is against the teaching of Islam, ba ma shi da lokacin da yake kula mata balle har yayi wani doguwar mu'amala da su, ka yarda da ni Abba bazan maka karya ba" Mai martaba dake kallonsa yace "Na je Maryland na ga mace a dakinsa, Auntynku ta je jiya and same thing happened, ta yaya zan yarda da maganar ka Ahmad? What sort of silly coincidence is that?" Jay yace "A gafarce ni Abba, amma nasan ba a dakinsa Aunty ta ga mace ba sai dai a dakin baki, shi Junaid wani irin mutum ne wanda idan yaga mutum stranded be it namiji ko mace bai ki ya ajiye ko ma waye a gidan ba har zuwa sanda mutumin zai yi sorting kansa out, you can confirm this from the workers of the house, wallahi halinsa kenan ba wai don ya hada komai da wa enda yake taimaka ba, Abba kasan bazan maka karya ba wai don in rufe laifin da kake tunanin Ajay ya aikata don in nayi hakan nima Allah bazai bar ni ba, Billah i am telling you nothing but the truth Junaid ba shi da hadi da koma wacece Aunty ta gani a gidan nan" Abba yayi shiru, after a while yace "Na ji, kuma na yarda, but i am afraid hukuncin da na tsara a kansa bazai masa dadi ba, but he still have to accept it cause hakan kadai ne zai sa in samu nutsuwa da kwanciyar hankali" Jay sai kallon Abba yake, a hankali yace "Wani hukunci kenan Abba?" Abba yace "Na yanke hukunci zan masa aure and he just have to accept ko ma wacece matar, you are not excluded also, duk da kai akwai maganar ka da Hadiyah....." Jay ya kwantar da murya yace "Don Allah kayi hakuri Abba, we have just few months remaining da muke saka ran za mu gama karatun nan da muke yi, bamu yi tunanin za mu kawo har warhaka bamu gama ba, plss Abba a saurare mu har zuwa sanda za mu gama, in just 2 to 3 months" Abba yace "Kwanaki ma haka ku ka min dadin bakin nan, kun maida ni kakan ku" Jay yace "Kayi hakuri Abba, mun san ka bamu dama sosai and this will be the last in sha Allah" Murmushi kawai Mai martaba yayi yana kallonsa, kowa yasan sa a mutum mai magana daya, amma ga yara sai juyasa suke yanda su ke so, after a while Abba yace "Yaushe zaka koma Amurkan?" Jay ya sunkuyar da kansa yace "Watan da za mu shiga in sha Allah" Abba yace "Allah ya kai mu" Khaleesat na zaune saman darduma wajen karfe shidda na yamma, tun da tayi sallan la'asar take zaune kan darduman take karatu a laptop dinta don in a month and few days time za su fara Spring semester exams din su, wayarta taji yayi vibrate alamar shigowar text, ta jawo wayar tana duba text din taga number Ajay, "Come out" iya abinda ya tura mata kenan, ta ajiye wayar ta mike ta dau Hijab dinta ta saka, tunda ta dawo apartment din nata kusan kullum zai zo wani lkcn ya gama zamansa a motarsa da yake parking a garage sai kuma yayi ordering ride ya bar motar tasa a garage din ya tafi, wani lkci kuma ya shigo parlon nata bazai dai dade ba zai fita, kuma ba wai magana yake yi mata ba, da ta lura bai son magana iyaka kawai ta gaishesa ta koma ta ci gaba da abinda take, wani lkcn ma sai ta dawo school zata ga alamar ya zo apartment din idan taji kamshinsa a parlor, duk ta lura for security purpose yake hakan, har ma da barin motarsa da yake yi a garage din apartment din, don ko da ya zo da safe ya dau motar ya tafi inda za shi to zai maida nan yayi parking da yamma sannan yayi ordering ride da zai kai sa gida, and she really appreciate all this that he is doing for her safety, don farko da ta dawo gidan kusan kullum sai tayi kuka gashi bata iya bacci da daddare don gani take kamar at anytime Aymaan zai iya zuwa gidan, gradually kuma ta hakura barin da ta ga Ajay na yawan zuwa gidan, amma fa duk wannan abubuwan ba shi ne yasa bata tunanin Housemate dinta ba, babu ranan da zai zo ya fadi bata yi tunaninsa ba, wani lkcn har da kukanta ta rasa dalilin hakan, zuwa yanxu kam ta ma hakura ta dena masa magana ta WhatsApp din tana ganin kamar takurasa take maganar da take masa duba da yanda yake amsa mata kamar baya so, tana bude kofar apartment din bayan ta sauka downstairs taga ledojin dake ajiye bakin kofar, sai kuma ta kalli garage ta gan sa zaune cikin motarsa, sai da ta fara shiga da ledojin parlor sannan ta fito ta nufi gun motarsa tana kallonsa ta gaishesa, ya bude motar ya sauka ya amsa without looking at her ya kulle motarsa, sai kuma taga ya nufi lyft din da ke jiran sa, tana tsaye tana kallo har ya shiga sannan ta juya ta koma apartment dinta ta kulle kofar da makulli, kayan shayi ta gani a ledojin da ya kawo mata, gwangwanin madara manya biyu, milo biyu, kwalayen sugar, Lipton, coffee powder, da kuma chocolate, har da bread manya uku da cookies iri iri, kilan ya shiga kitchen ne yaga babu madara shi ne ya siyo mata, kuma lokaci ne bata samu ba tana ta son zuwa taje tayi shopping din kayan shayin.... Bayan kwana biyu Khaleesat na isa school Safiyyah dake zaune lecture hall ta dinga mata wani kallo tace "Wai don Allah baza ki dena yafa manyan mayafan nan ba kina kunyata ni Khaleesat, kin fa gama wannan kadararren iddan ba wai baki gama ba, ko sau biyu za ki yi masa iddan ne?" Murmushi kawai Khaleesat tayi tana kallonta tace "Ni na ce maki na gama?" Safiyyah tace "Ai shi yasa na tambaya ko sau biyu za kiyi don ina nan ina taya ki lissafi wallahi kin gama, duk na kagu inga kin fara cin gayu kina zuba zawarcin ki son ranki, ai yanxu kuma ba da bane kin shiga wani level daban" Khaleesat tace "To bakya lissafi dai dai kuwa..." Safiyyah tace "Wallahi ina yi sai dai in kece bakya lissafin" Khaleesat bata tanka ta ba ta nemi waje ta zauna don yanxu wani sabon gayu Safiyyah ke ji a makarantar ita ga final year student, ko ta zo da mayafi sai ta saka a jaka tayi ta yawo da hula kawai kamar er Enugu, ko kuma tayi azababben English dressing ta daura karamin dankwali a kai, ita dai har ta gaji da yi mata magana ta zuba mata ido, a tare suka koma apartment din Khaleesat ranan don danwake Safiyyah tace zata masu, sai kusan yamma likis Safiyyah ta bar gidan shi ma Mustapha ne ya isheta da kira, Khaleesat na kitchen ta gama wanke duk Utensils din da Safiyyah taki wanke mata tana goge gogen kitchen din taji an bude kofar apartment din, dama tasan dole zai zo tun da taga ya mance charger dinsa a parlor alamar da taje school ya zo apartment din daxu, a hankali take wanke hannunta a pampon kitchen din trying to be sure of what she is perceiving, gently tayi patting hannunta jikin towel din kitchen din tana goge ruwan hannunta, sai kuma ta juya, sai da numfashinta ya tsaya for some seconds tsabar yanda gabanta ya fadi, yana jingine jikin bango kusa da kofar shiga kitchen din ya rungume hannu yana kallonta, ta sunkuyar da kanta, sai kuma ta nufi kofar kitchen din zata fita zuwa parlor, hannunta ya kamo yana kallonta with smile on his face, bata san sanda ta fashe da kuka ba zata kwace hannunta ya jawota kusa da shi murya can kasa yace "Halysaah" Hawaye kawai ke zuba idonta ta kasa kallonsa, slowly ya rungumota jikinsa murya can kasa yace "I am sorry" Bude kofar parlon aka yi, Jay yayi saurin saketa amma tuni Ajay ya shigo, sau daya ya kallesu sai kuma ya sauke idonsa ya tafi ya dau charger dinsa ya juya ya fita daga parlon.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* https://chat.whatsapp.com/I5vo38MH2jH8pDvzVF0Q4w HALYSAAH 69 Khaleesat ta bi Jay da kallo ganin ya nufi parlor, kana ganinsa zaka gane shi ma bai so abinda yayi ba don bai yarda ya sake hada ido da ita ba, kamar bai san sanda ma yayi hakan ba, ganin ya zauna a parlon ta sauke idonta daga kallonsa, sai kuma ta juya ta koma kitchen, Jay yayi dialing number AJ amma har ya katse bai yi picking ba, bai yi zaton zai shigo parlon ba don har yana ce masa kar ya bata masa lokaci, ya mike ya tafi window din parlon yana duba garage amma sai yaga ya tafi don babu motarsa a garage din, komawa yayi ya zauna ya cire face cap dinsa, Khaleesat na fitowa kitchen ya maida face cap din without raising his head, ita dai kanta a kasa ta karaso parlon tana rike da bottle water da glass cup ta duka gabansa ta ajiye masa, still not looking at him a hankali tace "Sannu da zuwa" Sai a sannan ya ɗan kalleta, ganin ba kallonsa take ba with calm in his voice yace "How are you Halysaah?" Cikin sanyin murya tace "Alhamdulillah, ya hanya?" Yace "Cool" Tana wasa da fingers dinta tace "Yaushe ka dawo?" Har sannan bai cire idonsa a kanta ba yace "Not less than an hour ago Housemate" A hankali tace "Ya su Mama da mutanen gida?" Yace "They are all good Halysaah, ya karatu? In few weeks time za ku fara Spring semester exams ko?" Ta gyada masa kai, shi dai kallonta kawai yake, can yace "How is Safiyyah?" Ta kwantar da kanta saman gwiwowinta har sannan tana jin kamshin turarensa na tashi a jikinta tace "She left not long ago" Sai kuma ta daga kai ta kallesa, sauke idonsa yayi daga kallonta, ita ma ta sunkuyar da kai tace "What should i make for you? Daxu danwake Sophie tayi mana and it's finished, should i make you pasta or rice?" Yace "No don't worry Housemate, Ajay made some food for me back home" Ta ɗan bude ido tana kallonsa tace "Can he cook?" Kawai yayi murmushi wanda iyakarsa lips bai bata amsa ba, sai kuma ya nuna mata trolley din da ya shigo da shi parlon yace "I got you some stuffs, hope you will love it" Shiru tayi tana kallon akwatin, yace "Check them" Ta sauke idonta sai kuma ta mike ta bude akwatin, tsadaddun Abaya ta fara cin karo da tana bude akwatin, ta daga kai ta kallesa suka hada ido ya sakar mata murmushi, sauke idonta tayi ta rufe akwatin kawai, cikin sanyin murya tace "Thank you soo much, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya kara budi" Yace "Ameen Halysaah" Still bata dago kanta ba a hankali tace "And i also want to appreciate you for what you did to my parent, Allah Ubangiji ya sa kafi haka, Allah ya biya maka duk bukatun ka na alkhairi...." Bai tanka ta ba yana kallon agogon wrist dinsa ganin bakwai saura yace "I will take my leave now Housemate, it's late already" Ita dai bata ce komai don sai taji babu dadi da yace zai tafi, ya mike yana kallonta yace "Kina da lectures gobe ne?" A hankali tace "Sai karfe daya na rana" Yace "Ohk, i will come before then in sha Allah, Aunty Farida ta bada sako a kawo maki, yana mota kuma Ajay ya tafi da motar" Ita sai a sannan ma ta tuna ashe Ajay ya shigo gidan fa, ta kallesa tace "Ohk, but how are you going back home tunda ya tafi da motar? Kayi order din Uber ne?" Jay yace "Ohh, na ma manta" Komawa yayi ya zauna yana danna wayarsa yace "Let me order the ride now" Ita dai tayi shiru tana kallonsa babu ko kiftawa, har ya gama order din ya daga kai suka hada ido, sunkuyar da kanta tayi tana jan yatsunta tace "Toh baza kayi sallah ba kafin ride din ya karaso?" Yace "Ohk bari in yi alwala" Mikewa yayi ya nufi bandakin dake parlon, ita ma ta tashi ta tafi sama dauko masa darduma, bayan Jay ya idar da sallah Khaleesat na kallonsa daga bayan kujeran da take tsaye tace "Or should i make you tea?" Yace "My ride is waiting Outside Housemate" Ta gyada masa kai kawai, tana biye da shi a baya har suka fita daga apartment din, ta rakasa har gun Lyft din dake jiransa, yana kallonta kafin ya shiga motar yace "Sai na zo gobe, take care of ur self" Ta gyada masa kai don har cikin ranta take jin da ma kar ya tafi, sai yanxu ta kara tabbatar da irin missing dinsa da tayi, memories dinsu tare na old apartment dinta ya dinga dawo mata a kai, and she misses every bit of those moment, she wish it's gonna happen again, a hankali ta juya bayan ya shiga Lyft din tana tafiya kamar mara lafiya ta koma apartment dinta ta kulle kofar. Jay na komawa gida ya bude kofa parlor ya tarar da Legend zaune bakin kofar alamar shi yake ta jira, tun da ya dawo gidan daxu bayan Ajay ya daukosa a airport Legend ke ta tsalle kansa yana haushi kamar zai rungumosa wanda hakan ke nuni da yayi missing dinsa ba kadan ba kuma ya bi sa har daki yana wagging tail dinsa yana kada kai alamar farin ciki ya nemi waje ya zauna a dakin, kafin su fita daxu kuwa sai da Jay ya kullesa a Cage dinsa don bin sa ya so yi yana ta haushi, Jay ya kalli Ajay dake zaune parlorn yana danna wayarsa ko dago kai bai yi ba, dukawa Jay yayi gaban Legend yana patting kansa ya bude steak din da ya siyo masa a hanya ya ajiye masa a pack din sannan karen ya kyalesa ya maida hankali kan Steak din, Jay ya mike ya karasa cikin parlon yana kallon Ajay yace "Didn't you see my call?" Ba tare da Ajay ya kallesa ba yace "I didn't" Jay bai sake ce masa komai ba ya nufi kitchen, bayan wasu yan mintoci ya fito yana kallon Ajay yace "Where is the food you said you made?" Still not looking at him Ajay yace "Nayi zaton can zaka kwana ae, i gave all the food to the workers" Kallonsa kawai Jay yake, can ya juya ya koma kitchen din to make a cup of tea for him self, ko kafin ya fito kitchen din Ajay ya bar parlon. Washegari wajen karfe sha daya Khaleesat ta sauko downstairs jin ana danna bell, bayan ta tambayi waye ta bude kofar parlon, gaishesa tayi tana kallonsa, ya amsa da murmushi, zata amshi ledan hannunsa yace "Don't worry Halysaah" Juyawa tayi ta koma cikin parlon, ya bi bayanta, bayan ya ajiye ledan yana kallonta yace "Sakon Aunty Farida da tace a kawo maki" Khaleesat ta karasa ta dau ledan ta kallesa tace "Thank you so much" Kitchen ta tafi da shi ta duba taga cin cin ne me yawa aka yi packaging sai alkaki da dublan, a wani ledan kuma ta ga kayan kamshi na dafa shayi, sai flour, kuka da kanwa, da dakakken yaji me yawa, tana gani ta gane saboda danwake aka aiko mata, ɗan murmushi tayi sai kuma ta dau take away a kitchen ta dibi cin cin din da su alkaki ta saka a wani ledan ta dawo parlor da shi, dukawa tayi gefensa da ledan, yana kallonta yace "What's that?" Tace "Cin cin ne da alkaki da Aunty Farida ta bada a kawo, i fetch some for you" Ya ɗan bude ido yace "No, ta bamu namu ni da Ajay, it's at home wannan naki ne" Ta wani kallesa tace "Ban yarda ba" Yace "I am serious, har da tea spice da grounded pepper duk ta bamu" Khaleesat tayi murmushi tace "To na yarda" Mikewa tayi ta maida cin cin din kitchen, sannan ta fito tace "I made you some food in kawo maka yanxu?" Yace "I had breakfast before leaving home Halysaah" Ɓata fuska tayi tana kallonsa, yayi murmushi ya sauke idonsa yace "Ohk... amma kadan zaki zubo min ba da yawa ba" Juyawa tayi ta koma kitchen din, ba a dau lokaci ba ta kawo masa shinkafa da stew din kaza da tayi, yana kallon abincin yace "Wannan ai yayi yawa" Tace "Eat and remain" Shi dai murmushi kawai yayi, ta koma kitchen ta dauko masa ruwa da glass cup ta ajiye masa, yace "Karfe nawa kika ce kina da lectures?" Tace "Karfe daya" Yace "Ohk to ki shirya idan na gama sai inyi dropping dinki nima zan shiga school din" Tace "Ohk, nagode" Sama ta wuce ta bar sa a parlon. Ko da Khaleesat ta sauko downstairs wajen karfe sha biyu da rabi ta gansa kwance kan 3 sitter idonsa a lumshe, murmushi tayi cause this is one of the part she misses so much about him, ta dafa bayan kujeran a hankali ta duka tana kallon innocent face dinsa, zagawa tayi tana tafiya a hankali ta tafi gun Vase din artificial flower dake parlon ta zari daya ta dawo gabansa ta duka dai dai fuskarsa ta kai flower din a hankali moving it back and forth his face, cikin bacci ya kai hannu fuskarsa da sauri ya kauda kai, hakan bai sa ta dena abinda take ba, yana kokarin mikewa zaune ya kusa cin karo da ita banda tayi saurin matsawa baya, ta dinga kyalkyala dariya tana kallonsa, murmushi yayi ya jinginar da kansa da kujeran yace "See this girl, wa yace maki ban ga sanda kika sauko ba, i just pretended i was sleeping" Tana dariya tace "Wallahi baka gan ni ba, you were sleeping" Shafa kansa yayi still smiling ya mike tsaye yace "I am waiting for you at the garage, amma ni dai nasan ba bacci nake ba i was just meditating..." Daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo tana murmushi, ta kalli wayarsa da ya bari kan kujera without noticing, sai da ta jira har ya fita daga parlon sannan ta duka kusa da kujeran ta dau wayar taga babu lock, miss calls ta gani guda hudu na wani number da aka yi saving with Hadiyah tare da text message dinta, call logs din duk yawanci miss calls dinta ne, amma kuma yana picking wasu call din nata, Khaleesat ta dinga kallon number, can ta shiga cikin message din da ta turo masa, "You should have at least pick, just wanted to know if you've arrived safely" shine content din message din, A hankali Khaleesat ke strolling text messages din taga inda Hadiyah ta turo masa "I love you so much Baby, and i want to spend forever with you" Da bai mayar mata reply ba sai ta sake tura masa uhmm, sai ya mata reply da "Love yah 2" Fita daga messages din Khaleesat tayi without going any further, tana kokarin clearing duk inda ta shiga don kar ya gani kawai taga kamar hoton da suka yi a park da shi among many other apps da ya bude a ranan, tayi tapping zata shiga hoton kawai ya nuna mata wajen is locked, ta fi minti biyu durkushe a wajen rike da wayar don gaba daya jikinta yayi sanyi ko motsin kirki ta kasa, can dai ta mike a hankali ta dau jakar laptop dinta ta nufi kofa walking slowly, kafin ta bude kofar ya riga ta budewa har sai da ya ci karo da ita, komawa baya yayi da sauri, ita kuma ta dafe kanta, Ya shigo parlon yana kallonta da damuwa yace "Hope u are not hurt? I am sorry i should have knock" Ta girgiza masa kai kawai ba tare da ta kallesa ba, yace "Are you sure you are okay Housemate?" Zame hannunta tayi daga fuskarta tana kallonsa, a hankali yace "Sorry Halysaah, i forgot my phone shi ne na dawo dauka..." Mika masa wayar tayi ya amsa yana kallonta, ita dai ta sauke idonta, bude mata kofar yayi ta fara fita sannan shima ya fita, ta mika masa makullin apartment din ya amsa ya kulle sannan suka nufi motarsa har a lkcn bai daina waigawa yana kallonta ba to be sure she is okay har suka iso garage, ita dai bata sake yarda ta kallesa ba, ya bude mata gaban motar yana kallonta, ɗan murmushin karfin hali tayi still not looking at him murya can kasa tace "Thank you" Sannan ta shiga motar, tana shiga ya daga mata veil dinta da ya fito waje ya daura kan cinyarta yana kallonta, sae a sannan ta daga manyan idanuwanta ta kallesa ya sakar mata murmushi, ita ma murmushin tayi har sai da dimple dinta ya lotsa ta sunkuyar da kai tana wasa da gefen veil dinta, ya kulle motar ya zaga ya shiga driver seat yayi igniting motar, bayan sun yi nisa ya ɗan kalleta murya can kasa yace "Are you sure you are okay Halysaah?" Khaleesat ta ɗan bude ido tace "Sure..." Don tabbatar masa da hakan tayi kokarin creating conversation tace "Ya Junaid fa?" Jay ya maida dubansa kan titin gabansa yace "Ba kuna magana da shi ta waya ba" A hankali Khaleesat tace "A'a, sai if there is something important" Without looking at her yace "Something important like?" Tace "May be idan ya kawo min abu apartment" Yace "Abu kamar me?" Khaleesat ta juya ta kallesa tace "Grocery shopping" Jay ya gyada mata kai yana ci gaba da driving dinsa, har suka isa school babu wanda ya sake cewa komai a cikinsu, ita kam Khaleesat ta tafi duniyar tunanin da take..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* https://chat.whatsapp.com/I5vo38MH2jH8pDvzVF0Q4w HALYSAAH 70 Bayan Jay yayi parking a school din ya juya yana kallonta, zata bude motar ta sauka yayi kasa da murya yace "Halysaah" Ta juya tana kallonsa, yace "What happened? Why the sudden change of mood?" Khaleesat ta ɗan bude ido, sai kuma tayi murmushin karfin hali ta girgiza kai tace "Ba komai fa" Yace "Are you sure?" Ta sauke idonta tace "Sure" Yace "Yaushe za ku gama lectures din?" Tace "Lecture daya kawai za mu yi" Yace "Zuwa 3pm kun gama kenan?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk, i will pick you then" A hankali tace "To Nagode" Murmushi kawai yayi mata yana kallon idonta, ta bude motar ta sauka ya bi ta da kallo, sai kuma ya dau wayarsa, Lkci daya ya gane ta shigar masa wayar cause yasan yana da miss calls din Hadeeyah da message a gaban screen, swiping yayi ya bude wayar yaga alamar ta shiga har cikin message din bayan call logs dinsa, jinginar da kansa yayi a hankali jikin kujeran motar with different thoughts running his mind. Har Khaleesat suka gama lectures bata ga Safiyyah ta shigo school ba ranan, tana zaune inda suka saba zama tana ta kokarin kiran Safiyyah tun daxu amma numberta baya shiga, lkci lkci take bin inda take zaune da kallo as if wanting to figure out something, at some point she became confuse and afraid at the same time don wasu memories that are not welcome in her heart ne suka hau dawo mata kai, Student sai harkan gabansu suke a vicinity din babu ma wanda yake kallon inda take zaune, tana kokarin tashi ta bar wajen kawai sai ga kiran Safiyyah ya shigo wayarta, Khaleesat ta koma ta zauna tayi picking call din ta kai wayar kunne, Safiyyah tace "Kin ga ban shigo school ba shine ko ki kirani matar nan?" Khaleesat tace "I have been trying ur line tun daxu baya shiga, hope you are fine? Why are you not in school today?" Safiyyah ta kyalkyale da dariya tace "Ke da ba sai dai in kira ki ince maki Surayya ta rasu yau ba" Khaleesat tace "Me ya faru?" Safiyyah tace "Ni dai wallahi har na fidda rai da ita in gaya maki kawata" Khaleesat ta hade rai tace "Don Allah ki gaya min me ya same ta?" Safiyyah tace "To wani azababben zazzaɓi ne ya damke ta har tana suma, sai ga Surayyan ki har da kamo hannuna yau tana neman agaji duk ta ruda ni, yanxu haka tana can an bata gado a asibiti, ni kuma ina gida saboda Aslam shi yasa ma ban shigo school yau ba, Aslam din da ko kusa da ni bata bari ya zo, kinga in ni mayya ce ai yau da babu abinda zai hanani cinye mata ɗa" Khaleesat tace "To Allah ya sauwake, Allah ya bata lafiya, wani asibitin ne?" Safiyyah tace "Oho ni dai ba an bar ni da baby sitting ba, Housemate dinki fa? Wallahi naji haushi da bazan samu zuwa in masa sannu da zuwa ba, ai sai ya zata ma walakanci ne ya dawo naki zuwa" Khaleesat tayi murmushin da bata yi niyya ba tace "Ni dai sai anjima, har mun gama lectures din" Safiyyah tace "Don Allah ni dai in ya je apartment din naki anjima ki kirani ki gaya min, ko goyo Aslam ne sai inyi in taho, kin ga ba dadi ace ban masa sannu da zuwa ba har zuwa yanxu" Khaleesat ta dake don bata son tayi dariya tace "Till we speak Sophie, sai anjima...." Safiyyah tace "Ke dalla ba cewa zan yi ina son sa ba, kowa yasan Housemate ai naki ne duk wanda yace zai maku shisshigi ma ai sai dai ya mutu, kilan ma har ya tambayi baba aurenki baba kuma ya basa bamu sani ba" Bude baki Khaleesat tayi a bit shock, don she never saw those words coming from Safiyyah, Safiyyah tayi dariya tace "Atoh, mu ba mu ki gobe a daura auren ba ma wallahi, Uztax Ajay sai ya bada sadakin yayansa, shi kuma Housemate kawai ya tare a nan apartment din naki Ajay da Salem su rakasa, in kayan mata ne sai in debo maki na Surayyah don a kitchen ma take jerasu don in gani, Ghana must go dinsu ake aiko mata daga gida, kin ga kawai sai in debo maki kina da gwangwanin madara da yoghurt abun ki, yanda dai zaki dawo babu banbanci da warce bata taɓa aure ba" Khaleesat bata san sanda ta katse wayarta ba ta kife a kafarta kamar warce taji wani mugun abu daga bakin Safiyyah, tafi minti goma zaune a yanda take kamar an dasa ta, taji wayar hannunta ya fara vibrate, a hankali ta juya wayar taga number Housemate, at first ta kasa daga call din nasa, sai da taga ya kusa katsewa sannan tayi picking ta kai kunne tayi shiru kamar munafuka, daga daya bangaren yace "Are you done Halysaah?" Ta gyada masa kai tace "Um" Yace "Ohk, i am waiting for you" A hankali tace "To" Sannan ta katse wayar ta mayar cikin jakarta, ta mike ta fara tafiya zuwa inda zata samesa. Har ta shiga motarsa bata yarda ta hada ido da shi ba, shi dai kallonta kawai yake, Bayan ta kulle motar a hankali tace "Ina yini" Calmly yace "Lafiya lau Halysaah, ya lectures din?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Frnd din ki ta tafi ne ita?" Khaleesat ta girgiza masa kai tace "Bata zo schl yau ba, matar brother dinta bata da lafiya" Yace "Allah ya bata lafiya" Daga haka ya fara driving zuwa gidanta, sai da suka kusa apartment din nata ya kalleta speaking slowly yace "Do you mind going out for dinner with me later Housemate?" Sai a sannan Khaleesat ta dan kallesa, suna hada ido ta sauke idonta a hankali tace "Alright" Yayi mata murmushi ya ci gaba da driving dinsa, Yana parking gaban apartment dinta ba tare da ta kallesa ba tace "Thank you so much" Yana kallonta yace "You are welcome Housemate..." Ta bude motar ta sauka sannan ta ɗan kallesa suka hada ido, murmushi tayi ta daga masa hannu sannan ta juya ta nufi apartment dinta, shi dai ya bi ta da kallo har ta shiga. Tun da Khaleesat ta ga karfe bakwai na yamma yayi ta zama tense, ta rasa dalilin da yanxu kuma take jin nauyin Housemate din nata sosai, duk da ba yau ta saba fita dinner da shi ba, amma yau gaba daya sai take jin wani nauyi na musamman, har lkcn kuma bata shirya ba tana dai zaune saman darduma after praying, karfe bakwai da minti goma kiransa ya shigo wayarta, ta jawo wayar a hankali tayi picking ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren yace "I am on my way now Halysaah" A hankali tace "Ohk, Allah ya kawo ka lafiya" Sai bayan da ta ajiye wayar ta mike ta fara duba kayan da zata sa, har ya iso apartment din nata after 15 minutes bata gama shiryawa ba, sai da ya jirata for another 10 minutes sannan ta fito, ta gansa tsaye jikin motarsa ya rungume hannu yana jiranta, sauke idonta tayi har ta karaso inda yake tsaye, yayi mata murmushi yana kallonta ya bude mata front seat, ita dai taki yarda su hada ido ta shiga motar, yana kallonta yace "Housemate" Sai a sannan ta daga idanuwanta ta kallesa, kamar me rada yace "You look cute" Rufe fuskarta tayi da veil dinta tana murmushi, ya kulle motar ya zaga ya shiga driver seat. The ride was silent, tunanin da take yi daban a ranta shi ma haka, bayan sun isa wajen cin abincin after offering her a seat ta fara zama sannan shi ma ya zauna opposite dinta, ya dau menu din eatry din yana mika mata yana kallonta, ta sauke idonta tace "I am okay with anything u order" Yace "Are you sure? Ke da baki son abincin turawa ni kuma nafi son sa" Murmushi tayi tace "Zan koya ci" A hankali yace "Really?" Ita dai bata ce komai ba kuma bata kallesa ba, yayi masu order din abincin irin wanda yasan she can cope with, bayan an kawo abincin ta dau lemonade dinta tana sipping a hankali, kamar ance ta daga kai taga kallonta yake, murmushi yayi ya dau nasa lemonade din yana sha yace "Naga kin yi kyau ne sosai" Khaleesat ta kasa kallonsa tace "Kai ma haka" Yace "Ni da baki kalla ba ta yaya kika san haka" Tayi murmushi ta daga idanuwanta tana kallonsa, kashe mata ido yayi slowly, ta boye fuskarta tana dariya a hankali, A haka suka fara cin abincin, amma ta kasa sakin jiki ta ci, shi kuma sai ya tsallake nasa abincin ya dau na gabanta, ta tallabi chin dinta tace "Ko in hada maka dukka ne?" Yace "Ke ma zaki iya daukan wanda kika ga yayi maki a nawa ai, it's called sharing..." Ta wani kallesa, sannan ta ci gaba da cin abincinta a hankali, har ta mance rabon da ta jita so happy and lively irin haka, gani tayi yayi exchanging abincinsa da nata, ta daga idanuwanta ta kallesa bata dai ce komai ba tayi murmushi, ya buda ido yace "Naji naki yafi dadi ne" Yana fara cin nata sai kuma taga ya mike ya dawo kusa da ita ya zauna da abincin yana kallonta yace "I think i can see the food more clearly from here..." Khaleesat dai kallonsa kawai take don gaba daya kamshin turarensa ya cika ta, ya bude pizza dake kan table din, kawai gani tayi ya dau slice daya ya kai mata baki yana kallonta babu ko kiftawa yace "Here...." She couldn't look at him in the eyes, at the same time she was a bit shock at his action, murya can kasa taji yace "Take Halysaah...." A hankali ta bude bakin ya bata pizzan, duk wani abu da yaga ta ki ci sai ya dauka ya kai mata baki, she was so shy, daga karshe ta girgiza masa kai cikin sanyin murya tace "I am full" Yana kallonta yace "Are you sure?" Ta gyada masa kai ta dau lemonade dinta tana sha, shi dai kallonta kawai yake, ta mika masa sauran lemonade din don shi ya shanye nasa, yayi murmushi ya amsa yayi sipping kadan ya ajiye sauran, after some seconds yace "I will like to discuss something with you Housemate, something that's bothering me, may be zaki bani shawara..." Khaleesat ta kallesa a hankali tace "Ohk...." Amma haka kawai taji gabanta yana faduwa, Calmly ya fara magana yace "You know i am an only child right?" Khaleesat tayi shiru tana kallonsa don bata san da haka ba, yayi murmushi yace "Yeah, my dad was late before i was even brought to the world" Sosai jikin Khaleesat yayi sanyi tana kallonsa, ya ci gaba yace "Junaid's Dad was my father's younger brother, and he inherited the throne after my father's demise who was then a king...." Khaleesat ta sauke idanuwanta cikin sanyin murya tace "Allah Ubangiji yayi masa rahama, ya gafarta masa" Jay yace "Ameen, i was partially raise together with Ajay, don Mamina couldn't let go of me gaba daya, so lokaci lokaci nake zuwa emirate din, wani lkcn inyi hutu a can, Ajay also lost his Mom when he was just 3 years old" Khaleesat ta dinga kallon Jay ta kasa cewa komai, Jay ya ɗan yi murmushi yace "Yeah, it's still not easy for him till date, but Alhamdulillah on his behalf" A hankali Khaleesat tace "Allah ya gafarta mata, Allah ya sa ta huta" Jay yace "Ameen, so now kinsan me yake faruwa Housemate?" Khaleesat ta girgiza masa kai, yace "I have this cousin sister Hadiyah...." Sosai gaban Khaleesat ya fadi don tsaf ta haddace sunan nan a zuciyarta, saura kadan tace masa ma bata son zancen amma ta dake zuciyarta tunda shawara yace yake son ta basa, ɗan farin cikin da take ciki na wnn moment din taji ya fara fading gradually, Jay ya ɗan yi shiru sai kuma ya daga kai ya kalleta directly in the eyes yace "A gida ake son hada mu aure da ita, Mamina, Mom dinta, my late father's senior sisters, infact all the family members, ya kai ya kawo har sun kai maganar gaban Mai martaba yanxu, kinsan mata idan suna son abu... At first Ajay aka so hadata da and he bluntly turn down the offer..." Khaleesat ta sauke idonta bata ce komai ba, A hankali yana kallonta yace "I think all this explanation isn't necessary Halysaah, kawai a takaice i want to refuse the offer too nan ba da jimawa ba for reasons known to me alone, but i don't know where to start from Halysaah, I don't know how everyone is going to take this, but deep down i don't think Mamina zata tilasta ni aka abinda bana so, she is always after my happiness and comfort, nasan bazata min dole ba...." Khaleesat was mute, don bata ma san me zata ce ba, amma jikinta kan yayi sanyi sosai ba kadan ba, ji tayi ya kamo hannunta murya can kasa yace "Kin yi shiru Housemate, say something pls" Kasa kallonsa tayi, idonta a kan hannunsa dake nata tana jin heartbeat dinta na karuwa, a hankali ta zame hannunta daga nasa tana murmushin karfin hali cikin sanyin murya tace "Amma baka tunanin hakan da zaka yi zai ja issues a family din naku?" Jay yace "I don't care, as far as Mami is in support of me i really don't care ko me za ace, idan naga ran Mami ya bace da decision dina shine kadai hankalina zai tashi, cause i love my mom so dearly...." Khaleesat still couldn't look at him in the eyes, after some seconds a hankali tace "Menene yayi triggering din canza decision da kake kokarin yi all of a sudden, bayan a farko ka riga kayi masu accepting zaka aureta?" Jay ya ɗan yi murmushi yana kallonta, kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "Look at me in the eyes Halysaah" Khaleesat felt like she is melting cause his intonation was something else, gaba daya ta kasa kallonsa, underneath his breathe yace "Look at me Halysaah" Da kyar tayi karfin halin daga manyan idanuwanta ta saka cikin nasa.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* Ur evidence 07087865788 https://chat.whatsapp.com/I5vo38MH2jH8pDvzVF0Q4w HALYSAAH 71 Tun kan Jay yace komai Khaleesat ta kasa ci gaba da kallonsa ta sunkuyar da kanta tana jin kamar ta nutse a wajen, bata taɓa jin tana kunyarsa ba kamar wannan lokacin, ta kasa gane wani irin kallo ne wannan yake mata da yake sa ta kara jin kunyarsa, shi ko bai fasa kallonta ba yana admiring kunyanta, she became so uncomfortable lokaci daya a wajen, taji ɗan composure din nata na neman guduwa ya bar ta, yayi kasa da murya yace "Halysaah..." Bata yarda ta sake kallonsa ba, speaking with calmness yace "Ban taɓa sanin akwai lokacin da zai zo inji wata daban nake so ba Hadiyah ba, i never saw that coming, and i can't help it...." Shiru Khaleesat tayi har sannan taki yarda su hada ido, a hankali yace "Kin yi shiru Housemate" Tayi murmushin karfin hali, sai kuma ta fara kame kame tace "To ai ni ban ma san me zan ce ba, the issue is too big for me to give out any advice, it's ur family matter, or better still kawai kayi addu'an abinda yafi zama alkhairi a gare ka, just pray about it, pray for the best...." Yace "Is that all u have to say, ke da ake neman shawara a wajen ki" Tayi shiru for the second time, sai kuma ta samu kanta da cewa "To idan zaka iya masu adalci sai ka hadasu duk biyun ai ba haramun bane" Bata san sanda furucin ya fito bakinta ba, sai kuma ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake babu ko kiftawa, sunkuyar da kanta tayi da sauri, a hankali yace "Haka kike ganin yafi?" A takaice tace "Nima ban sani ba" Yace "But you suggested it" Kin cewa komai tayi tana wasa da edge din veil dinta, shiru Jay yayi kamar wanda ya fada duniyar tunani, after a while Khaleesat ta daga kai ta kallesa, suna hada ido ta dauke nata idon, slowly yace "Ohk then, i will think about that, but..." Kafin ya karasa Khaleesat ta dau handbag dinta tace "I think hadari ne a garin, kar ruwa ya sauko" Yace "Yea akwai hadari, i can perceive it too" Mikewa tayi without looking at him, yace "To saurin me kike sai kace a kafa zaki koma gidan" Ta ɗan yi yake tace "Gobe fa akwai jarabawan da za mu yi kuma ko karatu ban yi ba" yace "Ai ke Genuis ce...." Khaleesat dai bata ce komai ba amma taki komawa ta zauna, a hankali yace "Kin kawo Suggestion kuma kina fushi da Suggestion din naki Housemate" Khaleesat ta zaro ido tana kallonsa, bata san sanda tace "Ban gane ba" Murmushi yayi ya mike yace "To mu je kar ruwa ya sauko" Sosai ta sha jinin jikinta da furucinsa ta kasa motsawa a inda take tsaye har ya wuce ta, after clearing the bills ya dawo kusa da ita yana kallonta yace "Let go Housemate, ko baki koshi bane let's place another other" Ta wani kallesa, dariya yayi yace "To mu je in ba dai wani abincin kike son ci ba" Kamar warce aka zare ma laka take biye da shi a baya tana tafiya a hankali har zuwa gun motarsa, ko da suka fito an fara yayyafi amma ba da yawa ba, ya bude mata front seat bayan ta shiga ya kulle motar ya zaga ya shiga mazaunin driver, yana fara driving wayarsa ya fara vibrate, Khaleesat ta kalli screen din wayar, Hadiyah ta gani, ta dauke idonta, ya kai hannu yayi silencing wayar gaba daya sannan ya kifar ta yanda ma bazai dinga ganin hasken wayar ba, ita dai bata sake kallon inda wayar yake ba, the ride back to her apartment was silent, ga yayyafin da ake sosai, ko wannensu da tunanin da yake a ransa, ita kam gaba daya farin cikin da take ciki as at 15 mins ago duk ya bace kamar bata yi sa ba, kawai taji zuciyarta ya tunkushe babu abinda yake mata dadi a rai, sai da suka kusa gida ya ɗan kalleta a hankali yace "Amma idan kun gama Exams za ki je Nigeria ko?" Khaleesat tayi shiru, ita har tana da choice din cewa zata je Nigeria ko bazata je ba, abinda ba ita zata ma kanta kudin jirgin ba, murya can kasa taji yace "Kin yi shiru Housemate..." Murmushi tayi ta buda masa hannu alamar ita ma bata sani ba, yace "Za ki je in sha Allah, ko 2 weeks sai kiyi kafin ayi resuming summer and final semester din ku...." A hankali tace "To Allah ya kai mu" Yace "Ameen" Ya kalli agogon wrist dinsa dake nuna takwas da rabi yace "Idan nayi dropping din ki zan je wajen abokina ne da ya shigo garin nan daxu, he will be leaving early tomorrow, ko mu je dake ku gaisa? He is looking forward to meet you" Khaleesat ta girgiza masa kai a hankali tace "Ruwa ake yi, kuma ina son zan yi karatu" Shiru yayi idonsa akan titi, can yace "Ohk then, may be some other time sai ku gaisa, he is my very good frnd, a Nigerian also" Khaleesat dai bata ce komai ba, duk ta kagu ta ganta a apartment dinta taje tayi sallah ta kwanta ko zata samu nutsuwan da ta rasa ga zuciyarta dake a tunkushe, dai dai garage din apartment din nata yayi parking yana kallonta yace "But cikin ruwan nan zaki fita Halysaah, kar ruwa ya taɓa ki kiyi mura" Khaleesat ta kirkiri murmushi tace "The rain is not heavy ai" Yace "Give me the key idan na bude sai ki sauko..." Bude jakarta tayi ta ciro makullin ta mika masa ya amsa yana kallonta, sai kuma ya sauke ido yace "Before then i have something little for you" Ita dai kallonsa kawai take har ya dauko wani karamin box a nan cikin motar ya bude yana mika mata, kallon zoben dake cikin box din yana ta kyalli kawai take, sai kuma ta kallesa taga kallonta yake, yayi murmushi yace "Haska da wayarki ki gani, i hope you will love it" A hankali Khaleesat ta ciro wayarta a handbag dinta ta ajiye handbag din gefe, sannan ta kunna fitila tana haska siririn diamond ring din dake wani kyalli, sauke idonta tayi ta ma rasa me zata ce, ya ajiye mata a cinya sannan ya bude motar ya fita cikin ruwan, da ido ta bi sa har ya isa kofar apartment din ya bude, jiki a sanyaye ta dau box din zoben ta kashe fitilar wayarta sannan ta bude motar ta sauka, zuwa sannan ruwan ya fara karfi, yana tsaye bakin kofar yana jiranta har ta karaso ya mika mata makullin apartment din yana kallonta yace "Good night Halysaah" Hawaye ya gani idonta, ta amshi makullin zata yi magana ya daura fingers dinsa a lips dinsa ya girgiza mata kai sannan ya juya ya koma gun motarsa ta bi sa da kallo tana son ce masa ko zai yi spending night din a apartment din nata because the rain is getting heavy, amma tuni ya bude motarsa ya shiga, a hankali ta dinga goge hawayenta, ta shiga parlon ta kulle kofar ta wuce sama, gefen gado ta zauna ta kife kanta da pillow wasu hawaye masu zafi na zuba idonta, bata san da ta fashe da kuka ba bayan ta tuno maganar da yayi mata na Hadiyah, tafi minti goma a haka taji an danna bell din gidan, mikewa zaune tayi ta kalli wayarta da ke hannunta, dawowa kuma yayi cikin ruwan nan, sai a sannan ta tuna ta bar Handbag dinta a motarsa, ko jakar ya kawo mata, ta kalli agogon wayarta dake hannunta, sai kuma ta mike ta bude kofar dakinta a hankali ta sauko downstairs, sake danna bell din aka yi making it the 3rd time, ta karasa har bakin kofar ta bude a hankali, kiris ya rage numfashinta bai dauke ba bayan tayi ido hudu da wanda ke tsaye bakin kofar, bata gama recovering daga matsanancin shock din da ta shiga ba kawai taga ya shigo parlon yana kallonta, wani kara tayi duk da babu me jinta saboda ruwan da ake, ya tura kofar speaking calmly yace "Listen to me Khaleesat" Bata sake yarda ta hada ido da shi ba tsabar rudewa sai ta nufi kitchen maimakon ta gudu sama, shi dai ya bi ta da kallo yana tsaye inda yake, sai da ta shiga kitchen din taga babu makulli jikin kofar, hannunta na rawa ta shiga call log dinta tana neman number Ajay tayi dialing, don tasan tsayawa kiran Housemate dinta ma will be a waste of time, he might not even see the call balle yayi picking, jikinta na rawa ta dinga addu'an Ajay ya daga kiran, rikicewa tayi ganin sa a kitchen din ya biyo ta, ya karasa har gabanta ya amshe wayar hannunta yana kallonta ya kashe wayar gaba daya ya ajiye saman cabinet din kitchen din, cikin sanyin murya yace "Listen to me Khaleesat, i promise you I am not here to hurt you" Kuka kawai Khaleesat take ta rakube jikin bango har lkcn jikinta na ɓari tana kallonsa, he look so lean kamar ba Abdul din da ta sani ba, sai dogon hancinsa da haske da ya kara, daxu tana zaune department dinsu a schl taji exactly kamshin turaren da yake using wanda hakan sai da ya sa ta tsorata ta rasa nutsuwarta, does it mean bibiyanta yake ta yi kenan all this while? How did he even know her apartment? Ta shiga uku ta lalace, Muryarsa taji a hankali yace "Kiyi hakuri na shigo maki apartment without permission Khaleesat, i know it's not right, bani da courage din tare ki a hanya don ban san yanda zaki yi reacting ba cikin mutane, i have no choice shi yasa har kika gan ni a nan this late, kiyi hakuri don Allah" Sai a sannan Khaleesat ta samu kwarin gwiwan hade rai ganin how calm and soft he was speaking to her, cike da karfin hali tace "Pls i don't want to report you to the cops, ka fita ka bar min apartment dina tun wuri" A mugun tsorace ta dake take masa maganar, instead sai taga ya sauke idonsa, a hankali yace "Zan fita, amma kafin nan ina son kiyi hakuri ba don ni ba kar ki sanar ma bodyguards dinki i badged into ur house, plss kar ki gaya masu Khaleesat.... Ni ba tashin hankali bane ya kawo ni i promise you.... nasan you are soft Khaleesat, ke mace ce me raunin zuciya sannan ke me yafiya ce, i am not using ur good characters to blackmail you Khaleesat, i am just saying the fact about you, ki dubi girman Allah da soyayyar da kike yi ma ma'aiki ki yafe min sannan ki tsaya ki saurareni ko na minti biyar ne...." She was so shock ganin ya duka a gabanta ya sauke idanuwansa daga kallonta cikin muryarsa da baya fitowa sosai yace "Ki duba alkhairina gareki ki saurareni ba don halina ba Khaleesat, i am begging you to pls give me a listening ear, na maki alkawarin ba dadewa zan yi ba zan fita...." Khaleesat ta dauke idanuwanta daga kallonsa tana jin hawaye na zuba idonta, alkhairansa da yace ne kawai ke ringing a kanta amma duk da haka ta dake zuciyarta, cikin rawan murya tace "Ni dai don Allah ka rufa min asiri ka fita in kulle apartment dina bani da lokacin sauraron ka ko na minti daya wallahi, i am begging you plss ka fita" Kamar zai mata kuka yace "Baza ki saurareni ba kenan Khaleesat?" Muryarta na rawa tace "In saurareka akan me? Bani da lokacin sauraranka, ka tashi ka fita before it's too late" Cikin sanyin murya yace "To zan fita, amma kiyi hakuri kar ki gaya masu i am here, i came with a pure intention not otherwise, plss do not tell them i am here" Duk don ta samu ya fitar mata a gida tace "Na ji, ka tashi ka tafi" Mikewa yayi ya juya ya nufi kofar kitchen din ta bi sa da kallo hawaye masu zafi na zuba idonta, sai kuma ta bi bayansa da sauri don tabbatar da fitan zai yi ko akasin haka, yana sa takalmansa dake bakin kofar parlon, Khaleesat ta karasa window da sauri ganin haske a labulen parlon, tana dubawa taga motar Ajay yayi parking a garage, ta juya da sauri ta kalli Abdul, zuciyarta na bugawa tace "My call went through, kuma gashi ya xo..." Abdul ya bude labulen dai dai sanda Ajay ya fito daga motar, kallonta Abdul yayi and she could see the panic in his eyes, ita kanta jikinta rawa yake don ko kadan bata son ayi wani tashin hankali a gabanta, muryarta na rawa tace "Ni ban san ta inda zaka fita ba, just go upstairs before he comes in...." sama ya nufa, within a blink of an eye ta dena hangosa, ta karasa tsakar parlor da sauri zuciyarta na bugawa ta zauna hawaye na zuba idonta, dai dai sanda Ajay ya bude kofar parlon, tsaye yayi bakin kofar yana kallonta, ita dai taki yarda su hada ido da shi wasu hawayen na zuba idonta, ya karasa cikin parlon still looking at her yace "Why did you call my line?" Kin cewa komai tayi tana goge sabbin hawayen dake sauko mata, ya hade rai yace "Kee, baki ji na ne? Me yasa kika kirani?" Muryarta na rawa tace "Nima ban sani ba" Tana fadin haka ta fashe da kuka sosai tana kallonsa, ya cire takalmansa going closer to her yace "Ban gane baki sani ba, What happened?" Tana shesshekan kuka ta bude masa hannu alamar ita fa bata sani ba, bin parlon ya dinga yi da kallo, nan taji gabanta ya fara faduwa sosai, cikin rawan murya tace "May be i was just hallucinating...." Sai kuma ta rakube jikin kujera ta kwantar da kanta tana wani sabon kukan, shi dai kallonta kawai yake, can ya zauna kan kujera that is near to her yace "What did you see?" A hankali tace "Abubuwa da yawa" Ya dinga kallonta kafin yace "Abubuwa kamar me?" Ta bude masa hannu alamar bata sani ba, yace "Ina wayarki? And why did you switch off the phone after calling me?" Ta fara kalle kallen parlon a hankali tace "Nima ban sani ba ai" Yace "Ina kika ajiye wayar da kika kirani?" Hanyar kitchen ta kalla tayi shiru, ya kalli kitchen din sannan ya mike ta bi sa da kallo zuciyarta na tsananta bugawa har ya shiga kitchen din, sai gashi ya fito yana rike da wayarta dake a kashe, tuni ta lumshe ido da sauri don kar ma su hada ido yayi mata wani tambayar, ya karasa har gabanta, ita dai idonta na lumshe tana sauke ajiyar zuciya a hankali, dukawa yayi gabanta ya kai hannu forehead dinta to feel if she is running temperature, amma yaji temperature dinta is normal, kawai with the way she is breathing zaka gane a tsorace take, ta bude ido a hankali tana kallonsa, sai kuma murya can kasa tace "Bacci nake ji" Yace "Why won't you hallucinate, wani kika ba ma contract din ya dinga maki Azkar din ki?" Ta sauke idonta bata ce komai ba, mikewa yayi ya koma kan kujera ya zauna yana ƙare ma parlon kallo, a hankali ta mike ta kwanta saman dogon kujera ta takure waje daya tana jiran taga ya tashi ya tafi, shi dai Ajay bai ma san wani tunani zai yi ba, ta kirasa yana jin kukanta a background and before you know it kuma yaji an kashe wayar gaba daya, he tried reaching her but to no avail, tunani ya fara yi ko tana da jinnu ne, ya sake juyawa ya kalleta, ita dai idonta a lumshe yake, a haka bacci ya dauketa bata sani ba. Khaleesat bata yi minti sha biyar tana bacci a kan kujeran ba ta farka a gigice bayan tayi mafarkin Ajay ya ga Abdul a gidan ya kamasa yayi ta duka, kawai daga karshe ya harbesa da bindiga, rikicewa tayi bayan ta fado daga kan kujeran ta dinga nanata "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" jikinta na rawa, Sai bayan da ta tabbatar mafarki ne ta daga kai har lkcn jikinta na rawa tana kallon Ajay da ya durkusa gabanta yana tofa mata addu'o'i, jinginar da kanta tayi jikin kujera tana jin hawaye na zuba idonta, after almost 10 minutes, speaking calmly yace "Ta shi ki tafi sama kiyi alwala ki kwanta" Make masa kafada tayi tana shesshekan kuka tace "A'a ni tsoro nake ji, zan kwanta a nan" Tana fadin haka ta mike ta sake kwanciya kan kujeran, shi dai kallonta yake, tun da bacci ya dauketa yake tsaye jikin window din parlon yana son tafiya amma bai tafi ba, kuma har lokacin ruwa ake, and before he know it 15 minutes into her sleep ta farka cikin firgici, Khaleesat ta dade bata ji irin wannan tsoron dake zuciyarta ba, yanxu idan ya ga Abdul a gidan nan me zata ce? Ko dai kawai ta gaya masa gaskiya, to amma idan ta gaya masa kuma ya kamasa da duka har ya aiwatar da abinda ta gani a mafarki ba, Da tunane tunanen nan wani baccin ya sake awon gaba da ita bata sani ba, cikin baccin taji an rufa mata duvet, ta bude ido da sauri sai kuma ta mike zaune tana kallon duvet din da ya rufa mata don parlon yayi sanyi sosai, tana zaro ido bata san sanda tace "A ina ka dauko?" Yace "Ban sani ba" Tsoronta kar yaje ya shiga dakin da Abdul yake, ta koma ta kwanta a hankali tayi lamo, Ajay ya tafi ya ci gaba da tsayuwarsa a jikin window din parlon yana duba wayarsa ganin Jay ke kiransa ya maida wayar aljihu. Karfe daya da rabi Khaleesat ta kara farkawa a bacci, ta cire duvet din jikinta tana kallon Ajay dake zaune kan one sitter ya jingina kansa da kujeran idonsa a lumshe, amma tana mikewa zaune ya bude ido, ta fara sosa kai taki barin su hada ido tace "Fitsari zan je in yi" Bai ce mata komai ba, ta mike tsaye tana tafiya a hankali ta wuce sama, waige waige ta dinga yi kamar munafuka a corridor din dakunan sannan ta bude one of the 3 rooms dake sama, taga Abdul baya ciki, ta dai san baya dakinta tunda har Ajay ya shiga dakin ya dauko mata duvet, dakin dake kallon nata ta bude a hankali, ta gansa kwance kan carpet at the far end of the room yana bacci, ta shiga uku ta lalace, how did she find her self in to this mess, duk don saboda tausayi, a hankali ta jawo kofar ta kulle har da makulli sannan ta cire makullin ta tafi dakinta da shi ta ajiye a handbag dinta, bayan kusan minti 7 Khaleesat ta sauko downstairs rike da darduma da Hijab don alwala tayi bayan ta tuna bata yi sallan isha'i ba, shi dai Ajay bin ta da kallo yake, ta shimfida darduman ta sa Hijab din sannan ta tada sallan, bayan ta idar tayi sallan Nafila, ta dade zaune kan darduma, lkci lkci take satan kallon Ajay don idonsa biyu har sannan, ganin ta fara jin bacci ta mike a hankali ta koma kan kujera ta kwanta ta rufa da duvet, a nan ne bacci ya dauketa wanda bata sake farkawa ba sai safe, don har gari ya fara wayewa, ta mike zaune da sauri don yaushe rabonta da makara haka, kalle kallen parlon ta dinga yi ganin Ajay baya parlon ta mike tsaye ta nufi window tana leka garage taga babu motarsa, ta fi minti biyu tsaye jikin window din sai kuma ta juya ta wuce sama bayan ta dau dardumanta da hijab, tana idar da sallah ta fito da makullin dakin da Abdul yake ta bude kofar dakin tana tsaye daga bakin kofa ta hade rai tana kallon cikin daki, yana zaune kan carpet, alamar tun bayan da yayi sallah yake zaune a haka, hade rai tayi tace "Ka zo ka fita don Allah" Mikewa yayi ya nufo kofar ta matsa ta basa hanya fuskarta daure, yana kallonta yace "Good morning Khaleesat" Ƙin amsawa tayi waiting for him to go downstairs, cikin sanyin murya yace "Nagode da rufa min asiri da kika yi" Yana fadin haka ya nufi downstairs, ita dai ta bi sa da kallo, sai kuma ta bi bayansa to be sure he is leaving, ko da ta sauka downstairs taga har ya bude kofar apartment din, tana tsaye tana kallonsa har ya fita ya kullo mata kofar, ta karasa ta saka ma kofar makulli, ta jingina da kofar letting out a sigh of relief..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 72 Wajen karfe tara Khaleesat ta sauko downstairs bayan tayi shirin tafiya makaranta, zaunawa tayi kan kujera ta jinginar da kanta jikin kujeran tana jin kanta na mata ciwo, banda suna da test da baza ma taje schl din ba don har a lkcn she was still stunned at what happen yesterday, gaba daya a dar dar take cikin gidan, ko appetite din yin breakfast bata da shi, ganin it's almost 10am ta ciro wayarta a jaka tayi ordering Uber da zai kai ta school din, bayan ya iso ta mike ta dau jakarta ta nufi kofa, tana isa school taga Safiyyah bata iso ba, kiranta ta fara yi a waya amma baya shiga, dab da za su fara test din sai ga Safiyyah, bayan sun fito Safiyyah ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Kawai daga na ɗan sake ma yaro fuska uwarsa bata da lafiya shine ya kai ni ya baro Khaleesat" Khaleesat ta kalleta amma bata ce komai ba, Safiyyah ta gyara zama tace "Gaba daya ya lalata min jakunkuna da jambakin uwarsa, duk ya goggoga, daga in shiga wanka in fito, ai ko ni dai na dokesa in ma uban ya kullace ni shi ya jiyo, jakunkuna na masu shegun tsada sai kace uwarsa ce ta siya min" Khaleesat dai ta ɗan yi murmushi kawai without saying anything, Safiyyah na kallonta da kyau tace "Me kuma ya faru na gan ki haka?" Khaleesat ta bude jakarta ta ciro zoben da Housemate ya bata ta mika mata, Safiyyah ta amshi box din ta bude, zaro ido tayi with awe tace "Oh my God, who got u this Khaleesat? diamond ne fa, don Allah wa ya baki, kamfanin Forevermark fa...." Ganin Khaleesat taki bata amsa Safiyyah ta hade rai tace "Don Allah ki min magana, where did u get this from?" A hankali Khaleesat tace "My Housemate gave me" Mikewa Safiyyah tayi baki bude tana zaro ido tace "Don't tell me he proposed to you?" Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba tace "Ko ba propose ba, he just gave me as a gift Sophie" Safiyyah tayi wani ƙara tace "Omg, wallahi proposing yayi maki amma saboda sense is far from you kinga ai baki gane ba, ya salam luxury brand ne fa Forevermark, to da ya baki me kika ce masa? Kuma ta yaya ya baki, kuna zaune ne ko kuna tsaye sanda ya baki?" Safiyyah ta koma ta zauna kusa da Khaleesat looking so excited tace "Don Allah how did u react da ya baki?" Khaleesat tace "Bai ma jira nayi masa godiya ba kawai ya wuce" Safiyyah tace "A apartment din ki ya baki?" Khaleesat tace "A'a, he took me out for dinner yesternight, bayan da muka dawo shi ne ya bani a mota" Safiyyah ta kyalkyale da wani shegen dariya tace "Yanxu fa sai kice har yanzu baki gane Housemate dinki is in love with you ba ko? Duk sai kice he is just being kind ko?" Khaleesat ta wani kalleta, Safiyyah na dariya tace "Ae ba abun mamaki bane kice baki gane yana sonki ba har yanxu, amma wallahi Housemate dinki na bala'i son ki kawata, don wannan care din is extra ordinary, ko kanwarsa da suka fito ciki daya bazai dinga yi mata irin wannan hidimar da yake maki ba, kai budurwar da saurayinta zai mata haka ma ba karamin musulmin sonta yake ba, yan mata nawa ne yanxu ko Naira biyar baya hadasu da samarinsu kuma a haka wai aurensu za ayi, ke dai wallahi you are very lucky om earth, Allah ya kashe ya baki kawai, ni kuma zan baki shawara kar kiyi misusing privilege din nan, cause it's a privilege to you wallahi, bai duba wai kin taɓa aure ba kawai shi tsakani da Allah yake son ki a zuciyarsa, come to think of who he is, daga gidan sarauta fa ya fito, in zaki ajiye kunya ki nuna masa kema kina sonsa to zai dai fi maki, you are not a kid Khaleesat, kinsan sonki Jawwad yake, so me tsanani kuwa" Khaleesat ta sauke idonta kamar bazata ce komai ba, sai kuma a hankali tace "Kinsan me Sophie?" Safiyyah na kallonta tana washe baki tace "Ina jin ki" After some seconds Khaleesat tace "Abdul came to my apartment yesterday night" Mikewa Safiyyah tayi ba tare da tasan ta yi hakan ba a tsorace, tana kallon Khaleesat with shock all over her face tace "Waye kuma Abdul? Did you have another frnd that is Abdul by name da ban sani ba?" Khaleesat ta daga idanuwanta ta kalleta, cikin sanyin murya tace "Abdul dai guda da kika sani" Safiyyah tace "Na shiga uku na lalace, Abdul tsohon mijin ki wai kike nufi?" Khaleesat ta kasa ce mata komai, Safiyyah ta koma ta zauna tana kallonta da wani expression tace "Ta yaya yasan apartment din ki Khaleesat? Kuma me yaje yi maki a apartment? Don Allah ki min bayani yanda zan gane, i am lost...." Khaleesat ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Wallahi ban san ta yaya yasan apartment dina ba Sophie, ni kaina i am still shock up till now, ko breakfast na kasa yi saboda tsoro, yanda kika san an jefo sa" Safiyyah ta maida jakarta gefe tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ji min shege ɗan iska, to wai uban me yaje maki a apartment din, tell me what happen da yaje, ke kuma da yaje kofa kika bude masa ya shigo?" Khaleesat tace "Bayan Housemate dina yayi dropping dina a gida ya tafi ana ruwa, after like 10 mins sai aka danna bell, to na mance jakana a motar Housemate i was thinking shi ne ya dawo ya kawo min jakar, da na sauka downstairs sai na bude kofa kawai, ashe Abdul ne" Safiyyah da tayi mitsi mitsi da ido tana sauraron Khaleesat tace "Go on, ina jin ki, sai aka yi yaya?" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "I was very shock and afraid bayan na bude kofan ya shigo, shi ne na shiga kitchen da gudu dama wayata na hannuna nayi dialing number Ya Junaid, sai gashi ya biyoni kitchen din ya karbe wayar" Buda baki Safiyyah tayi tana kallonta da firgici a fuskarta, cikin sanyin murya Khaleesat ta gaya mata duk abubuwan da Abdul yace mata a kitchen din bayan da ya sameta a ciki, da kuma yanda Ajay ya zo gidan duk bata boye mata komai ba.... Safiyyah na girgiza kai tace "Amma kin bani mamaki Khaleesat, yanxu shi Abdul har wani abun tausayi ne shi da zaki boyesa a apartment dinki? Abdul fa???" A hankali Khaleesat tace "Ce min fa yayi in tuna alkhairansa gare ni Sophie, kuma he look afraid also baya son Ajay ya gansa, shi ne yace in rufa masa asiri" A fusace Safiyyah tace "Wani shegen alkhairin yayi maki da zaki tuna? Harrassing dinki da ya dinga yi ko kuma gorin da yake lafta maki da walakanta ki da yake yi? Nan nan ranan kika bani labarin zaman ukuban da kika yi a gidansa kafin ya sake ki, da yanda ya bar ki da kwalin indomie ko albasa babu balle tarugu, marukan da ya dinga maki da zagin cin mutunci ne alkhairin da zaki tuna game da shi? Mutumin da ya ci mutuncinki ya sake ki bayan ya samu abinda yake so a wajenki har shi ne abun tausayi Khaleesat? Yanxu kina nufin kika boye Abdul har washegari a apartment din ki kika bar Ajay da gadin ku? Ikon Allah, Gaskiya baki taɓa bani tsoro irin yau ba Khaleesat, i fear who no fear you, me yake damun ki ne haka?" Khaleesat da duk jikinta yayi sanyi tana kallon Safiyyah tace "Safiyyah kar ki manta this is America, we are not in Nigeria, Ya Junaid na lura temper dinsa a kusa yake, yana da zuciya sosai, what if yaje ya masa wani illa wajen dukansa don nasan definitely bazai kyalesa ba idan ya gansa a gidan, kina tunanin idan yayi masa wani abu za a kyalesa ne a kasar nan? dole doka zai yi aiki a kansa, kuma duk saboda ni sai haka ya faru Sophie??" Safiyyah ta wani kalleta tace "Sannu me hangen nesa, da duk baki san da hakan ba kika doka masa kira? Why did you call him at the first place idan ba don ya zo ya fitar maki da Abdul ba?" Hawaye ya cika idon Khaleesat tace "Ai a sannan ban san da wani Intention ya zo min gida ba, kinga if he just came to harm me wannan daban ne, amma he meant no harm he was even afraid, banda haka ai bazai rokeni kar in gaya masu ya zo gidan ba" Safiyyah tayi wani murmushi tace "Maa sha Allah, kinga shawara daya kawai Abdul ya koma Nigeria ya bada sabon sadaki a kara daura maku aure kije can ku karata, tunda yanxu kam ya tuba kuma har kin yarda da tubansa kina mugun tausayinsa a rai, Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a masu yawa" Khaleesat ta hade rai tace "Come off it Safiyyah, ni nace maki i am ready to accept his repentance? Ko sake daura min aure aka yi da shi ba sai dai a kai gawata gidan ba, how will I forget what i went through so soon Safiyyah, wallahi kawai kalman alkhairi da ya furta ne da kuma irin sigar da naga ya zo min yasa na rufa masa asiri, ni ba butulu bace bazan ce Abdul bai min abubuwan Alkhairi ba a rayuwata, in ba don shi ba yaushe har ma zan zo kasar nan in hadu da su Housemate dina? I lacked nothing tun da Abdul ya kawo ni kasar nan karatu, don har nafi wasu da iyayen nasu ke daukar nauyinsu, kinga bazan ce Abdul bai min wani abun alkhairi ba, kuma bazan taɓa iya biyansa abinda yayi min ba, ki fahimce ni plss Sophie, ba wai nace ya kamata in sake kulasa bane, don wallahi ko ganinsa bana son yi don hakan na fama min ciwon dake zuciyata..." Safiyyah ta tabe baki tace "Tun da kin rufa masa asiri kin ga yau ma nasan yana can bakin apartment din naki yana jiran ki, hauka ake zan rufa ma Abdul asiri idan ni ne a shoe din ki? Abdul fa? Ai ko duk alkhairan duniya yayi min wallahi bazan rufa masa asiri ba sai dai Allah ya yafe min kawai, Monster in form of human ne fa Abdul, gaskiya kin ci amanar Junaid, kin cuce sa, kuma da ya kuskura yasan abinda kike boyewa a gidan nasan ko ciki daya ku ka fito da shi bazai sake barin wata alaƙa ta hada ku ba har abada, kuma bazai taɓa yafe maki ba, in kina tsoron kar Ajay ya masa illa me ya hanaki kiran 911?" Khaleesat dai tayi shiru tana bin inda suke zaune da ido, Kawai ganinsa suka yi a gabansu, ta rike numfashi tsabar yanda tayi shock tana kallonsa babu ko kiftawa, Safiyyah da ita ma ta gwalo ido tana kallonsa da mugun mamaki ta mike tana huci tace "Kai bawan Allah lafiya muna zaune zaka tsaya mana a kai, ko dai batan hanya kayi ne?" Sau daya ya kalli Safiyyah sannan ya mika ma Khaleesat wayoyin dake hannunsa guda biyu yana kallonta, daya na Jay daya na Ajay, Khaleesat ta wani hade rai tace "Abdul kaga bana son muyi creating scene a nan, kindly stay away from me, are you even okay? Meye zaka dinga bibiyata?" Safiyyah ta figi jakarta tana kokarin ciro wayarta tace "Idan ban kira maka 911 ba Allah ya tsine min albarka...." Tana ciro wayar ya fixge daga hannunta yana kallonta da kyau yace "Wajen ki na zo da zaki kira min 911 Malama?" Safiyyah ta kundumo wani zagi tana kallon Khaleesat tace "Kin dai ga crook din da kika ji tausayi har kika boye a apartment din ki kar Ajay ya gansa ya jibgesa ko, kin taɓa ganin inda shedan ya tuba dama? Shey u can see the useless monster you are pitying har da boyesa kar a dokesa?" Abdul na mata wani kallo yace "Hey watch your tongue, idan ba haka ba i will teach you a bitter lesson Billah, Ajay kika kirasa ko? To ya zo ya dokeni tunda ni statue ne, ina ga shi ko gidan dambe bai taɓa zuwa ba, ki je ki tambayi wanene ni a Lagos..." Khaleesat ta maida box din zobenta cikin jaka sannan ta mike ta amshe wayar Safiyyah dake hannunsa, ta dau jakar Safiyyah da nata ta fara janta su bar wajen, banda zagi babu abinda Safiyyah ke kunduma ma Abdul idonta rufe tana cewa "Munafuki kawai algungumi, wato saboda ka san tana da tausayi shi ne ka dawo sumui sumui da kai kamar na Allah zaka kara yaudaranta ka cuceta, har kana cewa ta rufa maka asiri, to kuwa sai na tona asirin nan naka wallahi, shegen duka za ayi maka da zai sumar da kai, in ka farfado ka siya ticket ko koma gida kayi jinya, tsabar baka samu daman ci gaba da musguna ma kawata ba har da rama sai da kayi kamar me ciwon Aids, to wallahi in baka fita harkar Khaleesat ba sai nayi maka abinda har ka koma ga Allah bazaka manta ba, mugu azzalumi kawai" Gaba daya attention din mutane ya dawo kansu a wajen, Abdul yayi wani murmushi yace "Sai kinyi regretting duk kalaman nan naki wallahi, sai na sa an lalata maki rayuwa i promise you this...." Khaleesat dai ta samu ta ja Safiyyah suka bar wajen gaba daya, banda rawa babu abinda jikinta yake yi don tsoro, Safiyyah ta warce hannunta tana kallonta a fusace tace "Kin dai ga ɗan iskan da kike tausayi ko? ashe da sabon salo kawai ya dawo don ya samu attention din ki, ke kuma ga sarkin masu tausayi, to kuwa rabon a karyasa yasa ya dawo Amurka don wallahi Ajay karyasa kawai zai yi" Khaleesat ta zauna ta rufe fuskarta da hannunta tana kuka a hankali, gaba daya ta gama tsorata, ta ma rasa wani irin tunani zata yi, zaman apartment din nata ita kadai ya fara bata tsoro kuma, can ta kalli Safiyyah dake ta bambami cikin rawan murya tace "Sophie ko dai in ma Ya Musty magana da kaina ki dawo apartment dina da zama tunda exams za mu fara? Wallahi bazan iya zama ni kadai ba kuma a gidan nan Sophie, i am afraid..." A fusace Safiyya tace "Ai baki zama afraid ba tunda har kika iya boye kasungumin ɗan daba a gidanki ya kwana, Abdul har abun yarda ne bayan duk mun san ɗan iska ne shi? Wani dadin baki zai maki har ki yarda da shi? Kin dai ga abinda yayi min ai yanxu, dama kuma me hali baya taɓa fasa halinsa" A hankali Khaleesat tace "To ko dai in yi ma Ajay bayanin abinda ya faru jiya kar ya zo ya gano yaji haushina? Wallahi i am so confuse Sophie" Safiyyah tace "To nima naji haushin ki balle Ajay da yayi gadin ke da Abdul ku ka sharbi baccin ku? ai wallahi kin cuce Ajay kuma sai Allah yayi masa sakayya" Khaleesat ta goge hawayen gefen idonta tace "To amma sai dai inje can gidan nasu in masa magana ko? Don kar yaje yayi misinterpreting dina ta waya idan na kirasa, i want to explain to him ta yanda zai gane" Safiyyah tace "Dama ai gwara ki samesa face to face kiyi masa bayani, sannan kar ki kuskura ki ce masa a gidan Abdul ya kwana don daga nan zai fatattake ki ya kora ki, ko ya hadaki da karensa ya kora ki, inda Ajay ke burgeni kenan wallahi, no nonsense Man kike ji, sam baya daukan wargi, tsayayyen namiji kenan, kawai ce masa zaki yi kin shiga kitchen zaki zuba abinci sai kika ga kamar Abdul a jikin window din kitchen dinki yana kallonki, shi ne duk kika rude kika kirasa jiya da daddare, daga baya kuma kika ga wajen wayam ba kowa, amma da ya zo sai baki gaya masa hakan ba tunda baki tabbatar ba kin zata hallucination kawai ki ke yi don dama kanki na ciwo jiyan, sai ki ce masa yau kina department muna zaune ni da ke kawai sai ga katon a gabanmu, ashe jiya shi din dai kika gani a jikin window, kinga ai maganata tayi making sense akan ki ce masa ai boyesa kika yi a daki jiya...." A hankali Khaleesat tace "To bari inyi order din Uber zuwa gidan" Safiyyah tace "Sannan idan kin je gidan ki fara masa godiyan gadin ki da yayi jiya ya hana kansa bacci, don nasan ba hankali gare ki ba kina iya zuwa ki fara maganar da ya kai ki kanki tsaye...." Khaleesat ta ciro wayarta za tayi order din Uber da zai kai ta gidansu Ajay, kafin tayi order din ta kalli Safiyyah tace "Ko zaki rakani mu je mu biyu?" Safiyyah ta rike haɓa tace "Wa?? Ni? Salon inje ya koro ni mutumin da ba kirki ne da shi ba, a'a wallahi bazan je ba, ko kadan bai taɓa burgeni ba dama ni, tun farko tamu bai zo daya da shi ba don na tsani mutum fitinanne, da dai Housemate ne sai in bi ki mu je, kuma banda ma yafi Housemate zafi me zai sa ma a sako sa cikin wannan case din, to tsorona muna iya sako Housemate yaje ya fara ba Abdul din hakuri kinga ai lamari ya lalace kenan, babu dai yanda muka iya Ajayn zaki je ki sama duk da mugun halinsa, ayi mutum ace bai son mutane kullum yayi ta daure fuska yana fushi shi kadai" Khaleesat na kallon Safiyyah cikin sanyin murya tace "Ko dai kawai in gaya ma Housemate in kyale Ya Junaid din?" Safiyyah ta wani hade rai tace "Wani Housemate, hakuri kike son ya tafi ya ba Abdul din kenan yanda zai ji dadin ci gaba da iskancinsa, ai karki kuskura ki gaya ma Housemate he won't help matters at all, gwara Ajay no nonsense, tsaf zai mana maganin Abdul, amma Housemate ai har durkusawa sai ya iya yi ya ba Abdul din hakuri yanda suka yi ma Aymaan shi da Ya Musty, Ajay ai shi ne namiji" Khaleesat dai bata ce mata komai ba tayi order din ride din, Safiyyah ta zaro ido tana kallon hannun Khaleesat tace "Ina zoben naki? Mun shiga uku ko dai Abdul din ya kwace?" Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba tace "Ga fa shi nan a jaka" Safiyya tace "Atoh, don ni yanda na gansa wujiga wujiga anya karayar arziki bai fada masu ba kuwa, kamar wanda yake yunwa duk ya rame sai idanuwa da hanci, da kyar idan ba talauci a tattare da shi" Khaleesat dai bata tanka Safiyyah ba, Safiyyah tace "To ki saka zoben mana, ko jere zaki yi da shi a gaban madubi?" Khaleesat ta bude ido sosai tace "Ina zan je da zan saka zobe Sophie?" Safiyyah tace "Ke dai kin ki wayewa a rayuwarki Khaleesat, ba don gayu ya siya maki ba dama?" Warce jakar tayi ta ciro box din zoben tace "Dalla ki saka" Khaleesat tayi murmushi ta amshi zoben ta saka tana kallonsa admiringly, cif ya zauna mata ta kalli Safiyyah dake ta murmushi ita ma kamar bakinta zai yage tace "It's sooo cute, gaskiya Housemate is so romantic, har na hango kun yi aure, wallahi kashe ki zai yi kawai da soyayya, in soyayya ne a bar ma Housemate kawai, in kuma kwato hakki ne a bar ma Ajay" Dariya sosai ta ba Khaleesat, kawai ta mike bayan ta maida wayarta da empty box din zoben cikin jaka, Safiyyah ta rakata har zuwa inda Lyft dinta ke jira, ta bude motar ta shiga, hannu ta daga ma Safiyyah dake ta murmushi tana kallon zoben yatsanta dake ta kyalli, a haka Lyft din ya bar wajen, tun da suka kama hanya Khaleesat ke ta waige waige to be sure babu motar dake bin su a baya, don ita kam yanxu duk a tsorace take, tunda har Abdul ya iya gano apartment dinta to babu kuma abinda bazai iya yi ba, har dai suka isa bata ga alamar ko wani mota dake biye da su a baya ba, ta sauka daga lyft din tana tafiya a hankali ta shiga compound din, it's almost 4pm na yamma, motar Ajay ta fara gani a parking space din gidan, sannan ta ga motar Jay ma alamar duk suna gidan, walking slowly ta karasa har entrance din parlon dai dai sanda aka bude kofar parlon, ta ɗan koma baya tana kallon Housemate dinta dake kallonta da mamaki, cikin dubara ta boye zoben finger dinta da veil dinta kar ya gani, tana kirkiran murmushi a hankali tace "Good evening" Yace "Evening Housemate, come in" Ta sauke kanta kasa ta bi bayansa har zuwa cikin parlon, ta zauna kan kujera shi ma ya zauna yana kallonta hoping all is well don sai yaji gaba daya hankalinsa ya tashi ganinta a gidansu, jin tayi shiru yana kallonta yace "Hope all is well Housemate?" Tana murmushi tace "Alhamdulillah, babu komai, Ya Junaid yana nan? I came to greet him" Jay yayi shiru yana kallonta, after some seconds yace "Yeah, he is upstairs" Ta sunkuyar da kanta a hankali tace "Ohk, i want to meet him" Jay ya gyada mata kai yace "He is at the parlor upstairs, ki samesa a can" A hankali tace "Sai na je sama?" Jay ya mike yace "He is there, ni zan fita yanxu...." Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, ya ɗan yi murmushi ya nufi kofar fita parlon ta bi sa da kallo har ya fita, bayan fitarsa da kusan minti goma Khaleesat ta mike, walking slowly ta tafi sama, tsaye tayi ɗan nesa da parlon dake sama tana kallon Ajay dake kallon kwallo a Tv, ga grapes a gefensa yana sha, ko lura da ita bai yi ba, he was so engrossed in the football match he was watching..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500* https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 73 Khaleesat ta sauke idonta daga kallonsa ganin for almost 2 minute bai lura da ita ba kallon ball kawai yake da duk attention dinsa, ta ɗan yi kasa da murya tayi masa sallama, juyawa yayi da sauri suna hada ido ya gyara zamansa don kishingide yake saman kujeran, nan da nan yayi keeping straight face ya ci gaba da shan grape dinsa idonsa a kan TV, tana tafiya a hankali ta karaso cikin parlon ta tsaya jikin kujera trying to gather up courage tace "Good evening..." Ya ɗan kalleta, sai kuma yace "Yes?" Ta ɗan langwabar da kai tana kara rungume handbag dinta tace "Ina son zan maka magana ne pls" a takaice yace "I am busy as you can see...." Ta kalli football din da yake kallo, a hankali tace "To shikenan, sai anjima" Tana fadin haka ta juya zata bar parlon yace "Ke.... awa daya zaki yi using kiyi min maganar ne, say what u want to say in few seconds i am listening" Tayi shiru tana kallonsa, after few seconds ta zagayo ta zauna kan 1 sitter tana kallonsa, har a sannan kusan duk hankalinsa na kan TV din kamar baya son missing kwallon da yake kallo, bayan kusan minti biyar ya juya ya kalleta, shi har ya mance tana wajen, yace "Kee fadi abinda ya kawo ki and stop staring at me that way" Tace "To ai naga kallo kake" Yace "Ido ke ji ko kunne? Ina ruwanki da kallon da nake yi?" Ɗan taɓe baki tayi, ita shi yasa bata ma son abu yana hadata da shi, komai sai yayi masifa, ta sauke idonta cikin sanyin murya tace "Dama Abdul ne ya biyoni school yau..." Lokaci daya ya juya ya kalleta, ta sunkuyar da kai, can yace "Waye Abdul?" Ta ɗan kallesa taga kallonta yake, tayi karfin halin cewa "My ex" Shiru ya sake yi, after some seconds yace "In zaki min bayani in details ki bude baki kiyi min and stop wasting my time" Ta ɗan saita kanta ta yanda zata fara koro masa duk abinda Safiyyah tace ta gaya masa, tayi inhaling numfashi sannan ta fara masa bayanin exactly yanda Safiyyah tace tayi, ya rage volume din TV, yana sauraronta attentively amma ba kallonta yake ba, har ta kai aya tana kallonsa, bai ce komai ba for almost a minute as if yana processing duk bayanin nata a kansa, still not looking at her yace "So now what did you want me to do?" Shiru Khaleesat tayi don bata san me zata ce ba, can taji yace "Saki nawa yayi maki?" Ta sauke idonta a hankali tace "Kawai ce min yayi ya sakeni, bayan da na dawo gida kuma aka aiko takarda daga gidansu da saki uku a jiki, amma ba rubutunsa bane" Ajay ya wani kalleta yace "Rubutun ki ne kenan?" Sunkuyar da kanta tayi, ya sauke idonsa kan zoben hannunta dake kyalli, ta ɗan saci kallonsa taga he is still looking at her, dauke kansa yayi bai sake cewa komai ba na ɗan lokaci, sai kuma taji yace "So what did you want me to do now da kika zo kika gaya min?" Khaleesat ta daga idanuwanta ta kallesa, lkci daya jikinta yayi sanyi, yace "Ko nan gidan kike son ince ki dawo?" Ta girgiza masa kai tace "A'a, i will cope in sha Allah, kawai na gaya maka ne" Sai kuma ta mike a hankali tace "Nagode, i am going back home" Ya watsa mata wani kallo yace "Are you okay? Ina maki magana zaki mike tsaye? Ni nace ki tashi?" Ta sunkuyar da kanta sai kuma ta koma ta zauna, nan da nan taji hawaye ya cika idonta, da ta sani kawai da Housemate dinta ta gaya ma duk da Safiyyah tace kar ta gaya masa, Ajay ya dau grape dinsa yana ci yace "Shi Guardian din naki me ya hanaki gaya masa sai ni? Baki fi kusa da shi ba a kaina zaki tsallakesa ki zo ki sameni? Am i ur Bodyguard?" Jin tayi shiru ya juya ya kalleta, hawaye ya gani a idonta, ta kai hannunta tana goge hawayen, bai sake cewa komai ba idonsa a kan grape din gabansa, after almost 30 seconds ya kalleta yace "Ya ma kike da suna, Yaushe zaku fara exams?" Bata dago kanta ba cikin sanyin murya tace "In less than a month time" Yace "Amma kinga silly frnd din nan taki wataran sai ta jefa kanta masifar da bazata iya fita ba, har ke sai ta jefa cikin matsala, shi tout din ta tsaya take exchanging words da saboda rashin kamun kai...." Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, Ajay bai sake cewa komai ba a parlon yana nazarin how to tackle the issue, shi ya dade bai ga ɗan iska kamar Abdul ba, amma zai yi maganinsa, shafa kansa yayi still thinking of where to start from, a yanxu dai baza su fara cewa ta zauna a gidan nasu ba don Mai martaba went on a trip to Toronto, kwanansa hudu kenan a can kuma basu san ko zai biyo ta Amurka ba, infact zai ma biyo don in dai ya taho overseas komin nisan inda yaje da Amurka dole sai ya zo Maryland in har suna kasar to check on them, so they won't take the risk of accommodating her in the house, assuming the semester isn't late da kawai sun mata applying for On-campus residence halls a cikin makarantar ta zauna, Ajay ya daga kai yana kallon Cousin brother dinsa Mukhtar that was coming towards the parlor, Mukhtar yayi kasa da murya yace "Tare mu ke da Mai martaba...." Ajay bai san sanda ya mike tsaye ba dai dai sanda yayi ido hudu da Abbansa dake biye da Mukhtar a baya, ƙamewa yayi a inda yake tsaye with surprise, what a bad coincidences this is, Mai martaba ya shigo parlon with a broad smile on his face yayi kamar ma bai ga Khaleesat ba, Ajay ya sauke kansa kamar wanda ruwa ya cinye a wajen, at first ya ma rasa abun cewa, can kuma yayi karfin halin cewa "Barka da zuwa ranka shi dade....." Khaleesat ta daga kai tana kallon Mai martaba sai kuma ta sunkuyar da kanta ta zamo kasan carpet ta gaishesa cikin sanyin murya, sai a sannan mai martaba ya kalleta still smiling ya amsa gaisuwarta, Mukhtar yayi offering masa kujera ganin bai zauna ba, Mai martaba yace "I am fine Mukhtar..." Sai kuma ya kalli Ajay da ya kasa kallonsa har sannan yace "Ina Jawwad?" A hankali Ajay yace "I think he went out just now..." Mai martaba yace "Ohk" Mikewa Khaleesat tayi da niyyar barin parlon, Mai martaba ya kalleta yace "No yi zamanki yarinya, ya sunanki?" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta koma ta zauna a hankali tace "Sunana Jiddah" Yayi nodding kai yace "Maa sha Allah, ke er Nijar ce?" Khaleesat ta ɗan yi murmushi tana wasa da gyalenta tace "A'a, er Nigeria ce" Mai martaba yace "That's good, Nigeria wani state?" Tace "Kano" Ajay dai yaki daga kansa yana jin zufa na karyo masa a forehead, can kawai ya juya ya bar parlon yana tafiya a hankali, Mai martaba ya zauna saman kujera still looking at Khaleesat yace "Karatu kike a kasar nan Jiddah?" Khaleesat tace "Eh karatu nake" Yace "That's good, wace makarantar?" A hankali Khaleesat tace "John Hopkins university..." Mai martaba na jinjina kai yace "Maa sha Allah, kano a wani unguwa iyayenki suke?" Khaleesat tace "Muna mariri ne" Shi dai Mukhtar na ta tsaye a parlon yana mamakin yanda Mai martaba ya tsaya ya bada lokaci yana conversing da Khaleesat bringing her down to his level, Ita kanta Khaleesat bata yi tunanin sarki bane shi duk zaton ta ko dai brother din babansu ne shi din, Mai martaba yace "Maa sha Allah Jiddah, Allah ya bada sa'an karatu" Tace "Ameen Abba Nagode" Mikewa tayi zata bar parlon ya kalli Mukhtar yace "A bata dala dubu biyar Mukhtar" Mukhtar ya ɗan risina kai da ladabi yace "To ranka shi dade" Khaleesat na kallon Mai martaba a hankali tace "Abba Nagode, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya kara girma" Daga mata hannu kawai yayi with smile, sannan ta mike ta bi bayan Mukhtar, tun basu fita parlon ba sai ga Jay ya shigo, kasa karasowa yayi bayan yayi ido hudu da Khaleesat ga Mai martaba zaune a parlon, can ya kalli Mukhtar da ya daga masa hannu alamar gaisuwa, ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, shi kam ya sunkuyar da kai walking slowly, a hankali tace "Sai anjima" Murmushin karfin hali kawai yayi mata without saying anything, ta bi bayan Mukhtar suka bar parlon, Jay ya karasa har cikin parlon ya zauna kasan carpet yana gaida Mai martaba da ladabi, Mai martaba ya amsa yace "Ina Ahmad din?" Jay ya mike ya bar parlon zai kira Ajay, ba a dau lokaci ba suka dawo tare, shi dai Ajay ya kasa hada ido da mahaifin nasa, ya zauna kan carpet gefen Jay, sae kuma yayi karfin halin cewa "Ya hanya ranka shi dade?" Cikin nutsuwa Mai martaba yace "Alhamdulillah...." Daga haka mai martaba bai sake cewa komai ba, Jay da Ajay ma duk suka yi shiru kamar masu jiran hukunci a gabansa, after a while Mai martaba ya kalli Ajay yace "Ita ce yarinyar da za aje gidansu kenan..." Ajay ya ɗaga kai yana kallon Abban nasa, can ya ɗan sosa kai yana murmushin karfin hali yace "Abba ai budurwar Jawwad ce, wajensa ta zo ba wajena ba" Mai martaba ya kalli Jay da bai dago kai ba, Can Abba yace "Budurwar Jawwad kuma na gan ku zaune tare a parlor" Ajay ya gyara zama yace "Ranka shi dade abinda na fada gaskiya ne, ba wajena ta zo ba wajensa ta zo" Mai martaba ya kalli Jay, cikin nutsuwa yace "Jawwad" Jay ya dago kai amma ya kasa hada ido da mai martaba, jin mai martaba yayi shiru yasan bayani yake jiran ji daga garesa, hakan yasa ya fara magana with calm yace "Gaskiya ya fada Abba, haka ne..." Mai martaba yayi shiru na kusan minti daya kafin yace "Ita Hadiyar fa?" Jay ya kasa cewa komai, Mai martaba sam bai yarda da abinda suka ce masa ba don gani yake kamar Jay is covering for Ajay, after some minutes cikin hikima Mai martaba yace "Ko hakan yasa kake ta jan maganar Hadiyah?" Jay ya gyada masa kai still not looking at him, Mai martaba ya numfasa speaking with calmness yace "So ta yaya zan yarda da ku yanxu? Don na fara kokonton ka yanxu Jawwad, a da dai baka min karya amma yanxu ka fara" Jay yayi karfin halin cewa "Allah ya taimake ka, believe me ba karya nayi maka ba" Mai martaba yace "Ai shi ne nake tambayarka ta yaya zan yarda da hakan? Yanxu nema maka auren yarinyar zan sa ayi idan na koma Nigeria so i can clear away my doubt?" Jay ya daga idanuwansa ya kallesa, a hankali yace "Da zan yi farin ciki da hakan ranka shi dade" Mai martaba yace "To batun Hadiyah fa?" Jay ya rasa abinda zai ce, after few seconds yace "I will be glad idan aka amince min na janye daga batun auren Hadiyah" Mai martaba ya ɗan yi murmushi yace "Ai bazan maka dole ba Jawwad, ya rage naka kayi ma iyayenka mata bayani su bar maganar Hadiyah tunda kana da yarinyar da kake so da aure, don waƙa a bakin me ita tafi dadi, in kuma kaga zaka hadasu su biyun it's fine, as far as zaka yi adalci... By so doing iyayenka mata baza su dau lamarin da zafi ba tunda duk sun saka ran auren ka da Hadiyah" A hankali Jay yace "But i am afraid za su yi shunning batun idan na kai masu ranka shi dade" Mai martaba yace "Not when i am alive Jawwad, duk abinda kake so shi zan maka in sha Allah" A hankali Jay yace "Allah ya kara girma ranka shi dade...." Mai martaba ya kalli Ajay yace "Kai kuma ina sauraron ka har yanzu" Mikewa Mai martaba yayi ya bar parlon, bayan tafiyarsa suna ta zaune kamar wa enda aka yi planting a wajen sai dai ko wannensu akwai abinda yake tunani a ransa, Ajay ya ɗan kalli Jay sai kuma yayi breaking silence din yace "Allah ya sanya alkhairi me mata biyu" Jay ya wani kallesa, Mikewa Ajay yayi zai bar wajen Jay ya sa masa kafa sai gashi timmm ya fada kan kujera, juyowa yayi ya hade rai yana kallon Jay da ya fara dariya, yaushe rabon su zauna waje daya a gidan, har magana ma sama sama suke yi... Jay ya dakata da dariyan da yake, sai kuma yayi kasa da murya yace "So what did you think about all this?" Ajay yace "About what?" Jay ya juya ya kallesa bai ce komai ba, Ajay yace "Getting married to ur Ward?" Jay dai kallonsa kawai yake, Ajay ya ɗan yi murmushi yace "All this while ka zata wataran zan so ta ne da kake creating attitude a gidan nan? Saboda me ma zan so ta? Dama shi son haka yake very cheap? Ai ba class dita bace yarinyar nan, i like nothing about her most especially her silly cry, duk abinda nake mata saboda kai nake mata, if not because you bazan taɓa saninta from anywhere ba, ba ma abinda zai sa nayi crossing path da ita, so chill bruh.... Just that har na fara hango maka challenges din da zaka yi facing a wannan familyn naka, considering the fact that ta taɓa aure, sannan she is a nobody, familynka kuwa basa son someone that is a nobody not to talk of bazawara, kaga you have to tighten up ur belt kayi facing all the up and downs that will approach you.... Wishing you the very best of luck" Yana kai wa nan ya mike ya nufi dakinsa, Jay dai ya bi sa da kallo, sai kuma Ajay ya tsaya sannan ya juya yace "In addition, tsohon mijinta na bibiyanta yanxu haka, that was why she was here earlier on" Daga haka Ajay yayi tafiyarsa Bedroom dinsa ya bar Jay da ya mike tsaye jin abinda Ajay yace. Ajay na shiga dakinsa ya tafi jikin window ya tsaya yana kallon Neighborhood dinsu, everywhere was so silent and calm as usual, sai kuma ya sauke idonsa ya juya ya tafi ya dau wayarsa ya koma jikin windon ya tsaya, number Khaleesat yayi dialing, yana fara ringing tayi picking, yace "Where are you?" Khaleesat dake cikin Lyft tace "Ina cikin mota" Yace "Za ki ina?" Kallon wayarta tayi jin shigowar kira taga Jay ne ke kiranta, ta maida wayar kunne a hankali tace "Gidansu Safiyyah zan je" Yace "Ohk, remain there idan kin je, do not go back to ur apartment...." Yana kai wa nan ya katse wayarsa, Khaleesat tayi picking call din Jay don bai katse ba har sannan yace "Kina ina Halysaah?" Tace "Ina hanya" Yace "Kar ki koma apartment din ki, wait for me somewhere, i will be on my way now" A hankali tace "Dama gidansu Safiyyah zan je" Yace "Ohk to ki je, zan same ki a can" Tace "To Nagode" Katse wayar tayi ta mayar cikin jakanta, wai yau ita ce zata kai kanta gidansu Safiyyah yau saboda rashin choice, to ya zata yi, ko zaginta Surayyah tayi ai sai dai kawai ta bata hakuri in dai zata barta ta zauna a gidan, a haka ta isa gidan, bayan ta sauka Lyft ta nufi kofar apartment din ta danna bell...... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* 07087865788 🗣️ HADJIBS DATA SERVICES Barkan ku da zuwa HADJIBS DATA SERVICES Wannan wuri ne da muke: 📌 Siyar da data (MTN, Airtel, Glo, 9mobile) 📌 Siyar da airtime cikin sauki (VTU) 📌 Biya kudin DSTV, GoTV, Startimes 📌 Biya wutar lantarki (NEPA/PHCN) 📌 Siyar da WAEC Scratch Cards 📌 Reseller Wallet System – zaka iya siyarwa da riba 📌 Dama ga masu so su fara sana'a a wayarsu Kawai zaku bude account dinku ku fara sana'ar ku cikin sauki. 🖱️ Shiga: https://hadjibsdata.com.ng 📲 App ɗin mu yana nan a Play Store da App Store. Idan kana da tambaya ko bukatar taimako, tuntubi admin kai tsaye, 07017133099. HALYSAAH 74 Safiyyah na bude kofa ta washe baki tana kallon Khaleesat tace "Wallahi na zata wasa kike da kika ce kina hanya, shigo ciki mana" Khaleesat ta ɗan yi murmushi ta shiga parlon, Safiyyah ta ja ta zuwa Bedroom dinta tace "Ni kadai ce a gidan, ko ina suka tafi oho, ni sai nake ga kamar fa ciki Surayyah tayi, in ko haka ne zan kama kaina in dena biyeta a gidan nan kar taje ta haifi kyakkyawa kamar ni..." Khaleesat ta cire veil din jikinta tace "Sallah zan yi" Safiyyah tace "Kin ci abinci a can kuwa?" Khaleesat tace "Abinci kuma?" Safiyyah tace "Ko da yake waye zai baki gida duk maza, bari inje in dafa maki noodles kafin ki idar da sallahn" Mikewa Khaleesat tayi ta shiga bandaki, Safiyyah kuma ta fita zuwa kitchen, bayan Khaleesat ta idar da sallah Safiyyah ta shigo dakin da indomie da kwai da ta dafa mata ta ajiye, Khaleesat ta kalleta tace "Thank you" Safiyyah tace "Naga duk kinyi wani sanyi, ko dai koran ki Ajayn yayi?" Khaleesat tayi er dariya tace "Saura kadan dai ya kore ni" Safiyyah ta kankance ido tace "Fitinanne, to sai aka yi yaya? Did u meet Housemate in the House?" Khaleesat tace "Eh na gansa" Sai kuma ta jawo handbag dinta ta bude ta ciro kudin da Mai martaba ya bata, Safiyya tace "Wa ya baki wannan kuma?" Khaleesat tace "I think their uncle, ya zo ya same mu a gidan ne, shi ne ya bani da zan tafi" Safiyyah ta ɗan bude ido tace "Ko dai babansu?" Khaleesat tace "Babansu kuma? babansu fa Sarki ne, a'a ba babansu bane" Safiyyah ta amshi kudin tana kirgawa tace "Atoh, dama sai dai ko uncle din nasu, amma ina sarki yaga lokacin tsayawa dake har ya baki kudi, da sarki ne ai kya gansa da guards dinsa kuma yaushe ma zai tsaya maki magana, dogarawansa ma baza su bari ba, amma fa ke Hajiya ce kinsan nawa kudin nan in an canza a Naira?" Khaleesat tayi murmushi ta fara cin indomie din gabanta, Safiyyah tace "Wallahi kudade ne masu yawa, har karamin gida sai ya iya siya maki a maririn ku, yanxu ya ku ka yi da Ajay din bayan kin gaya masa abinda ya faru?" Khaleesat tace "Ai bamu gama magana ba Uncle din nasu ya zo, but after i left the house ya kirani yace kar in koma apartment dina, Housemate dina ma ya kirani...." Safiyyah ta hade rai tace "Ba nace kar ki sako Housemate a ciki ba? Shi fa Abdul namiji fitananne ne kawai zai iya dealing da shi, shi kuma Housemate dinki ba mutum bane me son hayaniya" Khaleesat tace "Kilan Ajay din ne ya gaya masa...." Safiyyah ta mike jin ana danna bell tace "Kilan sun dawo daga gantalin da suka je" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba Safiyyah ta mike ta fita daga dakin, ba a dau lokaci ba ta dawo tace "Ban ga kowa a bakin kofar ba kuma, ko dai kunne na ne yaji kamar an danna bell?" Khaleesat ta ajiye fork din hannunta tace "Kuma kin bude kofar?" Safiyyah tace "Haba dai sai kace ni ce ke, ta peephole na duba mana" A hankali Khaleesat tace "Ban san me yasa gabana ke ta faduwa ba Sophie, Abdul can be cunning kar ace ya fa biyo ki yaga gidan nan baki sani ba" Safiyyah tayi wani dariya tace "Saboda yana shan codeine sai ya biyo ni gidanmu, ai yasan ni ba ke bace hauka tuburan zan masa wallahi, to ya biyo ni akan me?" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, taji abincin ma ya fita ranta, Safiyyah tace "In zaki ci abincinki ki ci, idan su Ya Musty sun dawo zan sa ya duba surveillance camera din bakin kofar mu ga wani shege ne ya danna bell" After a while Khaleesat ta tura abincin gabanta don ya isheta ga baccin da take ji, Safiyyah dai chatting kawai take da wayarta, Khaleesat ta dau kudin da Safiyyah ta ajiye mata ta cire dala dubu biyu a ciki ta ajiye mata kusa da ita, Safiyyah ta hade rai tace "Meye wannan?" Khaleesat bata kalleta ba tace "Na baki" Safiyyah tace "Inyi me da shi? A'a bana so wallahi, ki ajiye kudin ki kawai zai maki wani amfanin" Khaleesat bata tanka ta ba ta mike tayi kwanciyarta gefen gado ta lumshe ido, cikin dubara Safiyyah ta jawo handbag dinta ta mayar mata da kudin ciki sannan ta ajiye. Wajen karfe shidda da rabi Safiyyah ta tashi Khaleesat dake bacci ta dalilin wayarta dake vibrate, Safiyyah tace "Ana kiran ki a waya" Khaleesat ta mike zaune ta jawo wayar ta duba taga Housemate ne ke kiranta, daga kiran tayi ta kai kunne, daga daya bangaren yace "I am outside Halysaah" A hankali Khaleesat tace "To" Veil dinta ta dauka Safiyyah ta rakata zata bude mata kofa, Khaleesat ta riko hannunta da sauri tace "Ki fara duba waje kafin ki bude mana" Safiyyah tace "Ke dai matsoraciya ce wallahi, shi Abdul din ai ba ɗan iska bane da zai zo ido na ganin ido, baki ga kamar barawo ya shige maki gida ba ranan da daddare" Bude kofar tayi Khaleesat ta makale a bayanta gabanta na faduwa, bayan ta hango motar Jay ta ɗan sauke ajiyar zuciya, Safiyyah na washe hakora tace "Yau dai Allah yayi za mu gaisa da shi" Khaleesat ma murmushin tayi suka fita zuwa gun motarsa a tare, yana ganin Safiyyah ya sauko daga motar, ya rungume hannu yana kallonta yace "Good evening kawar Housemate" Safiyyah ta tuntsire da dariya tace "Welcome Yaya Housemate, sai yau Allah yayi za mu hadu tunda ka dawo" Yace "Amma ai ina ce ma kawarki ta gaisheki" Safiyyah tace "Wallahi bata taɓa gaya min ba" Jay ya ɗan kalli Khaleesat dake kallonsa, ta sauke idonta da sauri bayan sun hada ido, murmushi yayi yace "Gaskiya ban taɓa cewa ta gaishe ki ba, it's not her fault..." Safiyyah tayi dariya tace "Wai don ka kareta ko, ai nafi ka sanin wacece Housemate dinka" Jay na murmushi yace "Ya mutan gidan?" Safiyyah tace "Duk lafiya lau suke, yanxu take gaya min uncle dinku gave her much money a taya mu yi masa godiya plss, ranan kuma ta nuna min diamond ring da ka siya mata, Allah ya saka da alkhairi Yaya Housemate, Allah ya bar ku tare" Khaleesat ta bude baki tana kallon Safiyyah with shock, Jay dai yayi murmushi yace "Our father... not uncle Safiyyah" Daga Safiyyah har Khaleesat kallon Jay suka yi, Safiyyah ta bude ido sosai tace "Kana nufin Mai martaba da kansa? That's surprising, Allah ya kara masa girma....." Jay na murmushi yace "Ameen" Ita dai Khaleesat tayi shiru tana tunanin yanda yayi ta hira da ita a parlon kamar random person babu wanda zai yi tunanin sarki ne, Safiyyah tace "To ni zan koma ciki Housemate" Jay yace "Alright Safiyyah, thank you so much" Tana murmushi ta juya ta koma cikin gida, shi dai Jay kallon Khaleesat yake, sai kuma ya bude mata front seat, ba musu ta shiga motar ba tare da ta kallesa ba, ya zaga ya shiga driver seat yana kallonta yace "Kin ci abinci ne?" Kai ta gyada masa, jin bai sake cewa komai ba ta daga idanuwanta ta kallesa, zoben hannunta taga yana kallo baya ko kiftawa, tayi saurin boye hannun a bayanta kamar ta nutse don kunya, yayi murmushi yana kallonta a hankali yace "Wai yaushe kika fara jin kunyata Housemate? I am only admiring the ring, it look soo cute in your finger" Taki daga kai ta kallesa, ita kanta ta rasa gane wannan sabon kunyan nasa da take yi, ya jinginar da kansa da kujeran motar yana kallonta babu ko kiftawa, tunda taji yayi shiru tasan kallonta yake hakan yasa ko da wasa bata yarda ta dago kanta ba balle su hada ido, murya can kasa taji yace "Me yasa ni baki gaya min Ex dinki yaje wajenki a schl ba sai Ajay?" Shiru tayi jin tambayar da yayi mata, can ta dan kallesa, still speaking slowly yace "Why?" Tace "Ae ko an kira ka baka picking call dinka..." Yayi shiru yana kallonta kafin yace "Yaushe kika kira ban yi picking ba?" Ta langwabar da kai tace "Anytime i call, you don't pick" Jay ya sauke idonsa kasa, after some seconds yayi kasa da murya yace "I promise i won't do that again, i will prioritize ur call from henceforth yanda nake prioritizing na Mami da me martaba" Khaleesat ta daga kai suka hada ido, tayi saurin dauke idonta daga nasa, yace "Me yace maki da ya sameki a school din?" Khaleesat tace "Safiyyah ce ta kulasa suka yi exchanging words" calmly Jay yace "Do not worry Halysaah, i will bring an end to ur fright about ur Ex Husband very soon in sha Allah, i promise you this, zaki samu kwanciyar hankali fiye da yanda kike tsammani" Khaleesat ta kallesa, cikin sanyin murya tace "But i don't want you to confront him pls, he can be cunning" Jay ya ɗan yi murmushi yace "I am not confronting him Halysaah, kawai dai zan yi abinda zai yi cutting duk wani Intention din da yasa ya dawo yake bibiyan ki, i will put a total stop to that, kuma babu yanda ya iya haka nan zai hakura ko ba don Allah ba...." Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, After some seconds tace "Amma yanxu i will prefer inyi ma brother din Safiyyah magana to let me stay in their home har sanda zan gama exams, don bazan iya zama a apartment dina ni kadai ba kuma, i am very afraid" Jay yace "Kar kiyi inconveniencing dinsu Housemate, and I don't want you to be a burden to them considering the high cost of livelihood in this state.... ki zauna a apartment dinki kawai, i will be there also, i will be there to protect you...." Khaleesat tace "Zaka dinga zuwa kamar sanda muke former apartment dina?" Yayi murmushi yana kallon kwayar idanuwanta yace "Sure, anything for you Halysaah" Sosai taji hankalinta ya kwanta, cikin sanyin murya tace "To Nagode" Yace "Lokacin sallah ya kusa, can we go home now" Tace "Let me get my handbag" Gyada mata kai yayi, ta bude motar ta sauka, ya bi ta da kallo har ta shiga apartment din, after some minutes sai ga ta ta fito daga gidan da handbag dinta da waya, ta shiga motar ta rufe tana kallonsa taga kallonta yake.... Khaleesat na zaune dakinta wajen karfe takwas da rabi na dare suna WhatsApp call da Aunty Farida, gaba daya jikinta a sanyaye yake ga faduwar da gabanta yake ta yi jin abinda Aunty Farida ke gaya mata, labarin biyota da Abdul yayi har sabon Apartment dinta da kuma cikin makaranta take ba Aunty Farida, a nan ne Aunty Farida ke sanar mata ai yaje Mariri ma yafi a kirga few weeks ago kawai gaya mata ne bata yi ba don bata son daga mata hankali, Cikin sanyin murya Khaleesat tace "To Aunty ya aka yi yasan ina America ne?" Aunty Farida tace "In kin tambayeni in tambayi wa Khaleesat? Kilan ko bincike yayi a unguwan aka gaya masa, kinsan babu abinda yan unguwan nan baza su yi ba akan kudi, dama kuma ga tsegumi ya masu yawa, in kuma ba a unguwan ya bincika ba kilan shi ma yaga hotonki da wannan mutumin da ya dora ki a Instagram" Khaleesat kamar zata yi kuka tace "Toh me yake so kuma a guna Aunty da yake bibiyana ne?" Aunty Farida tace "Mutumin da yana zuwa cewa yayi ya maida auren ku, Allah ya so Nenne ta zo ranan sai abinda ta manta ne bata gaya masa ba ta kusa tara masa yan unguwa, kuma tace ai kin gama iddansa tun wani shekara in ma yau ya farka bacci tun sanda ya sake ki to yaje ya duba calendar yaga yau shekara nawa da yayi sakin, Nenne ta sille sa tas, ni ai shi yasa hankalina bai wani tashi ba, da dai baki idar da iddansa bane shine babban tashin hankalinmu gaba daya, amma da baki da hakkinsa ai kinga Allah ya kada hankalinsa sai bayan da kika gama ya waiwayo ki, yana sake zuwa inda kike ki kira masa hukuman kasar kawai su ja maki layi da shi...." Khaleesat dai ta kasa cewa komai, Aunty Farida tace "Dama in kika ga ya hakura da bibiyanki ai sai in wani auren kika yi tunda babu tsoron Allah a ransa, ban taɓa ganin mara kunya ma irin sa ba, babu kunya babu tsoron Allah fa ya zo ya marairaice ma Babanki wai ya maida ke, ya zo gidan nan yafi sau goma wallahi, to Allah na tuba ko da ace baki gama iddansa ba da ba sai dai mu makasa a kotu ba akan ki koma gidansa, shi ɗan iska, danginsa matsiyata marasu mutunci" Khaleesat taji hawaye ya cika idonta tace "Toh Aunty ni tsoro nake kar ya sake cewa zai daukeni kema kinsan halins 🗣️ HADJIBS DATA SERVICES Barkan ku da zuwa HADJIBS DATA SERVICES Wannan wuri ne da muke: 📌 Siyar da data (MTN, Airtel, Glo, 9mobile) 📌 Siyar da airtime cikin sauki (VTU) 📌 Biya kudin DSTV, GoTV, Startimes 📌 Biya wutar lantarki (NEPA/PHCN) 📌 Siyar da WAEC Scratch Cards 📌 Reseller Wallet System – zaka iya siyarwa da riba 📌 Dama ga masu so su fara sana'a a wayarsu Kawai zaku bude account dinku ku fara sana'ar ku cikin sauki. 🖱️ Shiga: https://hadjibsdata.com.ng 📲 App ɗin mu yana nan a Play Store da App Store. Idan kana da tambaya ko bukatar taimako, tuntubi admin kai tsaye, 07017133099. HALYSAAH 74 Safiyyah na bude kofa ta washe baki tana kallon Khaleesat tace "Wallahi na zata wasa kike da kika ce kina hanya, shigo ciki mana" Khaleesat ta ɗan yi murmushi ta shiga parlon, Safiyyah ta ja ta zuwa Bedroom dinta tace "Ni kadai ce a gidan, ko ina suka tafi oho, ni sai nake ga kamar fa ciki Surayyah tayi, in ko haka ne zan kama kaina in dena biyeta a gidan nan kar taje ta haifi kyakkyawa kamar ni..." Khaleesat ta cire veil din jikinta tace "Sallah zan yi" Safiyyah tace "Kin ci abinci a can kuwa?" Khaleesat tace "Abinci kuma?" Safiyyah tace "Ko da yake waye zai baki gida duk maza, bari inje in dafa maki noodles kafin ki idar da sallahn" Mikewa Khaleesat tayi ta shiga bandaki, Safiyyah kuma ta fita zuwa kitchen, bayan Khaleesat ta idar da sallah Safiyyah ta shigo dakin da indomie da kwai da ta dafa mata ta ajiye, Khaleesat ta kalleta tace "Thank you" Safiyyah tace "Naga duk kinyi wani sanyi, ko dai koran ki Ajayn yayi?" Khaleesat tayi er dariya tace "Saura kadan dai ya kore ni" Safiyyah ta kankance ido tace "Fitinanne, to sai aka yi yaya? Did u meet Housemate in the House?" Khaleesat tace "Eh na gansa" Sai kuma ta jawo handbag dinta ta bude ta ciro kudin da Mai martaba ya bata, Safiyya tace "Wa ya baki wannan kuma?" Khaleesat tace "I think their uncle, ya zo ya same mu a gidan ne, shi ne ya bani da zan tafi" Safiyyah ta ɗan bude ido tace "Ko dai babansu?" Khaleesat tace "Babansu kuma? babansu fa Sarki ne, a'a ba babansu bane" Safiyyah ta amshi kudin tana kirgawa tace "Atoh, dama sai dai ko uncle din nasu, amma ina sarki yaga lokacin tsayawa dake har ya baki kudi, da sarki ne ai kya gansa da guards dinsa kuma yaushe ma zai tsaya maki magana, dogarawansa ma baza su bari ba, amma fa ke Hajiya ce kinsan nawa kudin nan in an canza a Naira?" Khaleesat tayi murmushi ta fara cin indomie din gabanta, Safiyyah tace "Wallahi kudade ne masu yawa, har karamin gida sai ya iya siya maki a maririn ku, yanxu ya ku ka yi da Ajay din bayan kin gaya masa abinda ya faru?" Khaleesat tace "Ai bamu gama magana ba Uncle din nasu ya zo, but after i left the house ya kirani yace kar in koma apartment dina, Housemate dina ma ya kirani...." Safiyyah ta hade rai tace "Ba nace kar ki sako Housemate a ciki ba? Shi fa Abdul namiji fitananne ne kawai zai iya dealing da shi, shi kuma Housemate dinki ba mutum bane me son hayaniya" Khaleesat tace "Kilan Ajay din ne ya gaya masa...." Safiyyah ta mike jin ana danna bell tace "Kilan sun dawo daga gantalin da suka je" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba Safiyyah ta mike ta fita daga dakin, ba a dau lokaci ba ta dawo tace "Ban ga kowa a bakin kofar ba kuma, ko dai kunne na ne yaji kamar an danna bell?" Khaleesat ta ajiye fork din hannunta tace "Kuma kin bude kofar?" Safiyyah tace "Haba dai sai kace ni ce ke, ta peephole na duba mana" A hankali Khaleesat tace "Ban san me yasa gabana ke ta faduwa ba Sophie, Abdul can be cunning kar ace ya fa biyo ki yaga gidan nan baki sani ba" Safiyyah tayi wani dariya tace "Saboda yana shan codeine sai ya biyo ni gidanmu, ai yasan ni ba ke bace hauka tuburan zan masa wallahi, to ya biyo ni akan me?" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, taji abincin ma ya fita ranta, Safiyyah tace "In zaki ci abincinki ki ci, idan su Ya Musty sun dawo zan sa ya duba surveillance camera din bakin kofar mu ga wani shege ne ya danna bell" After a while Khaleesat ta tura abincin gabanta don ya isheta ga baccin da take ji, Safiyyah dai chatting kawai take da wayarta, Khaleesat ta dau kudin da Safiyyah ta ajiye mata ta cire dala dubu biyu a ciki ta ajiye mata kusa da ita, Safiyyah ta hade rai tace "Meye wannan?" Khaleesat bata kalleta ba tace "Na baki" Safiyyah tace "Inyi me da shi? A'a bana so wallahi, ki ajiye kudin ki kawai zai maki wani amfanin" Khaleesat bata tanka ta ba ta mike tayi kwanciyarta gefen gado ta lumshe ido, cikin dubara Safiyyah ta jawo handbag dinta ta mayar mata da kudin ciki sannan ta ajiye. Wajen karfe shidda da rabi Safiyyah ta tashi Khaleesat dake bacci ta dalilin wayarta dake vibrate, Safiyyah tace "Ana kiran ki a waya" Khaleesat ta mike zaune ta jawo wayar ta duba taga Housemate ne ke kiranta, daga kiran tayi ta kai kunne, daga daya bangaren yace "I am outside Halysaah" A hankali Khaleesat tace "To" Veil dinta ta dauka Safiyyah ta rakata zata bude mata kofa, Khaleesat ta riko hannunta da sauri tace "Ki fara duba waje kafin ki bude mana" Safiyyah tace "Ke dai matsoraciya ce wallahi, shi Abdul din ai ba ɗan iska bane da zai zo ido na ganin ido, baki ga kamar barawo ya shige maki gida ba ranan da daddare" Bude kofar tayi Khaleesat ta makale a bayanta gabanta na faduwa, bayan ta hango motar Jay ta ɗan sauke ajiyar zuciya, Safiyyah na washe hakora tace "Yau dai Allah yayi za mu gaisa da shi" Khaleesat ma murmushin tayi suka fita zuwa gun motarsa a tare, yana ganin Safiyyah ya sauko daga motar, ya rungume hannu yana kallonta yace "Good evening kawar Housemate" Safiyyah ta tuntsire da dariya tace "Welcome Yaya Housemate, sai yau Allah yayi za mu hadu tunda ka dawo" Yace "Amma ai ina ce ma kawarki ta gaisheki" Safiyyah tace "Wallahi bata taɓa gaya min ba" Jay ya ɗan kalli Khaleesat dake kallonsa, ta sauke idonta da sauri bayan sun hada ido, murmushi yayi yace "Gaskiya ban taɓa cewa ta gaishe ki ba, it's not her fault..." Safiyyah tayi dariya tace "Wai don ka kareta ko, ai nafi ka sanin wacece Housemate dinka" Jay na murmushi yace "Ya mutan gidan?" Safiyyah tace "Duk lafiya lau suke, yanxu take gaya min uncle dinku gave her much money a taya mu yi masa godiya plss, ranan kuma ta nuna min diamond ring da ka siya mata, Allah ya saka da alkhairi Yaya Housemate, Allah ya bar ku tare" Khaleesat ta bude baki tana kallon Safiyyah with shock, Jay dai yayi murmushi yace "Our father... not uncle Safiyyah" Daga Safiyyah har Khaleesat kallon Jay suka yi, Safiyyah ta bude ido sosai tace "Kana nufin Mai martaba da kansa? That's surprising, Allah ya kara masa girma....." Jay na murmushi yace "Ameen" Ita dai Khaleesat tayi shiru tana tunanin yanda yayi ta hira da ita a parlon kamar random person babu wanda zai yi tunanin sarki ne, Safiyyah tace "To ni zan koma ciki Housemate" Jay yace "Alright Safiyyah, thank you so much" Tana murmushi ta juya ta koma cikin gida, shi dai Jay kallon Khaleesat yake, sai kuma ya bude mata front seat, ba musu ta shiga motar ba tare da ta kallesa ba, ya zaga ya shiga driver seat yana kallonta yace "Kin ci abinci ne?" Kai ta gyada masa, jin bai sake cewa komai ba ta daga idanuwanta ta kallesa, zoben hannunta taga yana kallo baya ko kiftawa, tayi saurin boye hannun a bayanta kamar ta nutse don kunya, yayi murmushi yana kallonta a hankali yace "Wai yaushe kika fara jin kunyata Housemate? I am only admiring the ring, it look soo cute in your finger" Taki daga kai ta kallesa, ita kanta ta rasa gane wannan sabon kunyan nasa da take yi, ya jinginar da kansa da kujeran motar yana kallonta babu ko kiftawa, tunda taji yayi shiru tasan kallonta yake hakan yasa ko da wasa bata yarda ta dago kanta ba balle su hada ido, murya can kasa taji yace "Me yasa ni baki gaya min Ex dinki yaje wajenki a schl ba sai Ajay?" Shiru tayi jin tambayar da yayi mata, can ta dan kallesa, still speaking slowly yace "Why?" Tace "Ae ko an kira ka baka picking call dinka..." Yayi shiru yana kallonta kafin yace "Yaushe kika kira ban yi picking ba?" Ta langwabar da kai tace "Anytime i call, you don't pick" Jay ya sauke idonsa kasa, after some seconds yayi kasa da murya yace "I promise i won't do that again, i will prioritize ur call from henceforth yanda nake prioritizing na Mami da me martaba" Khaleesat ta daga kai suka hada ido, tayi saurin dauke idonta daga nasa, yace "Me yace maki da ya sameki a school din?" Khaleesat tace "Safiyyah ce ta kulasa suka yi exchanging words" calmly Jay yace "Do not worry Halysaah, i will bring an end to ur fright about ur Ex Husband very soon in sha Allah, i promise you this, zaki samu kwanciyar hankali fiye da yanda kike tsammani" Khaleesat ta kallesa, cikin sanyin murya tace "But i don't want you to confront him pls, he can be cunning" Jay ya ɗan yi murmushi yace "I am not confronting him Halysaah, kawai dai zan yi abinda zai yi cutting duk wani Intention din da yasa ya dawo yake bibiyan ki, i will put a total stop to that, kuma babu yanda ya iya haka nan zai hakura ko ba don Allah ba...." Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, After some seconds tace "Amma yanxu i will prefer inyi ma brother din Safiyyah magana to let me stay in their home har sanda zan gama exams, don bazan iya zama a apartment dina ni kadai ba kuma, i am very afraid" Jay yace "Kar kiyi inconveniencing dinsu Housemate, and I don't want you to be a burden to them considering the high cost of livelihood in this state.... ki zauna a apartment dinki kawai, i will be there also, i will be there to protect you...." Khaleesat tace "Zaka dinga zuwa kamar sanda muke former apartment dina?" Yayi murmushi yana kallon kwayar idanuwanta yace "Sure, anything for you Halysaah" Sosai taji hankalinta ya kwanta, cikin sanyin murya tace "To Nagode" Yace "Lokacin sallah ya kusa, can we go home now" Tace "Let me get my handbag" Gyada mata kai yayi, ta bude motar ta sauka, ya bi ta da kallo har ta shiga apartment din, after some minutes sai ga ta ta fito daga gidan da handbag dinta da waya, ta shiga motar ta rufe tana kallonsa taga kallonta yake.... Khaleesat na zaune dakinta wajen karfe takwas da rabi na dare suna WhatsApp call da Aunty Farida, gaba daya jikinta a sanyaye yake ga faduwar da gabanta yake ta yi jin abinda Aunty Farida ke gaya mata, labarin biyota da Abdul yayi har sabon Apartment dinta da kuma cikin makaranta take ba Aunty Farida, a nan ne Aunty Farida ke sanar mata ai yaje Mariri ma yafi a kirga few weeks ago kawai gaya mata ne bata yi ba don bata son daga mata hankali, Cikin sanyin murya Khaleesat tace "To Aunty ya aka yi yasan ina America ne?" Aunty Farida tace "In kin tambayeni in tambayi wa Khaleesat? Kilan ko bincike yayi a unguwan aka gaya masa, kinsan babu abinda yan unguwan nan baza su yi ba akan kudi, dama kuma ga tsegumi ya masu yawa, in kuma ba a unguwan ya bincika ba kilan shi ma yaga hotonki da wannan mutumin da ya dora ki a Instagram" Khaleesat kamar zata yi kuka tace "Toh me yake so kuma a guna Aunty da yake bibiyana ne?" Aunty Farida tace "Mutumin da yana zuwa cewa yayi ya maida auren ku, Allah ya so Nenne ta zo ranan sai abinda ta manta ne bata gaya masa ba ta kusa tara masa yan unguwa, kuma tace ai kin gama iddansa tun wani shekara in ma yau ya farka bacci tun sanda ya sake ki to yaje ya duba calendar yaga yau shekara nawa da yayi sakin, Nenne ta sille sa tas, ni ai shi yasa hankalina bai wani tashi ba, da dai baki idar da iddansa bane shine babban tashin hankalinmu gaba daya, amma da baki da hakkinsa ai kinga Allah ya kada hankalinsa sai bayan da kika gama ya waiwayo ki, yana sake zuwa inda kike ki kira masa hukuman kasar kawai su ja maki layi da shi...." Khaleesat dai ta kasa cewa komai, Aunty Farida tace "Dama in kika ga ya hakura da bibiyanki ai sai in wani auren kika yi tunda babu tsoron Allah a ransa, ban taɓa ganin mara kunya ma irin sa ba, babu kunya babu tsoron Allah fa ya zo ya marairaice ma Babanki wai ya maida ke, ya zo gidan nan yafi sau goma wallahi, to Allah na tuba ko da ace baki gama iddansa ba da ba sai dai mu makasa a kotu ba akan ki koma gidansa, shi ɗan iska, danginsa matsiyata marasu mutunci" Khaleesat taji hawaye ya cika idonta tace "Toh Aunty ni tsoro nake kar ya sake cewa zai daukeni kema kinsan halinsa fa" Aunty Farida tace "A American zai dauke ki saboda ba shi da seti?" Khaleesat dai tayi shiru gabanta na faduwa don har yanzu bata mance yanda aka dauketa aka kai masa ita ba, tunanin hakan yasa hawaye ya fara zuba idonta, Aunty Farida tace "Yanxu dai ki kwantar da hankalin ki tunda kin ce Jarabawa za ku fara, su Junaid ma baza su bari ya cutar dake ba in sha Allahu, kiyi ta addu'a kina neman tsari daga sharrinsa, in sha Allahu Allah zai kare ki" Khaleesat ta gyada mata kai cikin sanyin murya tace "To Aunty" a haka suka yi sallama da Aunty Farida tana goge hawayen da yaki tsaya mata, kiran Safiyyah ne ya shigo wayarta tayi picking ta kai kunne, Safiyyah tace "Khaleesat kin san wa yayi ring din bell daxu kuwa?" Sosai gaban Khaleesat ya fadi tun kan Safiyyah ta gaya mata, Safiyyah tayi wani dariya har da kyakyatawa tace "Wallahi shi ne in gaya maki, Abdul ne ba wani ba, gashi nan an duba Camera na gansa, to da na bude kofar uwar me zai min ne? Wato ban taɓa ganin ɗan iska mara aikin yi kamar sa ba, ki ji har yayi locating inda nake saboda rashin aikin yi, to me zai min da Allah bai min ba?" Cikin rawan murya Khaleesat tace "Kin dai ga abinda nake gudu ko, wallahi da baki kulasa ba Safiyyah, ba kowa ake musayar yawu da ba" Safiyyah tace "Wallahi ba abinda ya isa yayi min da izinin Allah, shi kuma yaya Musty idan ya gama bambamin fadan da yake yana cewa ina dauko masa magana a kasar nan sai ya daukeni mu tafi mu kai ma Cops report, sai an gano Abdul duk inda yake ya fadi abinda ya zo yi a apartment dinmu wallahi..." Tana kai wa nan ta katse wayarta, knocking din kofar dakin Khaleesat taji ana yi, ta juya ta kalli kofar har sannan zuciyarta na bugawa ta mike ta dau hijab dinta ta saka ta tafi ta bude kofar, sauke idonta tayi bayan sun hada ido, yana kallonta da damuwa ganin hawaye idonta yace "Are you crying Halysaah? Me ya faru?" Kamar jira take ta jingina da kofar dakin ta fashe masa da kuka dama ta kwana biyu bata yi ba, nan da nan ta rikitasa a wajen..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* *Ur evidence 07087865788* https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 75 Juyawa Jay yayi ya sauka downstairs don bai son yayi abinda zuciyarsa ke tunzura sa yayi a wannan moment din, yasan in ya ci gaba da tsayuwa yana sauraron kukanta a wajen the case will be totally different, sai da Khaleesat taga ya sauka kasa sannan ta dena kukan da take har lokacin tana jingine da kofar tana goge idonta a hankali, juyawa tayi ta koma dakinta ta dau laptop dinta ta zauna kan gado zata yi karatun wani course dinsu amma ta kasa karatun, sai kuma tayi tagumi tana kallon screen din laptop din babu ko kiftawa, after a while ta maida Laptop din gefe ta sauka daga kan gadon ta nufi kofa ta fita daga dakin, walking slowly ta fara sauka downstairs tana kallonsa, zaune yake kan kujera idonsa a wayar hannunsa, ya juya yana kallonta jin foot step dinta, har ta karaso karshen staircase din, ta sunkuyar da kai ganin kallon da yake mata, mikewa yayi ya nufeta yayi kasa da murya yace "Halysaah... " Ta daga idanuwanta ta kallesa amma bata ce komai ba, yace "Why are you crying?" Kamar bazata ce komai ba sai kuma ta jingina da bango ta rungume hannunta tace "Ba sai kace min inyi hakuri ba amma ka wani tafi...." Murmushi yayi yace "To ai ban san ta yanda zan fara cewa kiyi hakurin bane ta yanda zaki gane da gaske nake baki hakurin, shi yasa na tafi" Ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, can ta juya zata bar wajen, ya dakatar da ita yace "Halysaah" After some seconds ta juyo fuska a daure, ya ɗan yi murmushi yace "Mu je parlor in baki hakurin to" Ta wani turo baki ta kara rungume hannunta, yana murmushi ya juya ya koma parlon, sai kuma ta bi bayansa, ya jira har ta karaso ta zauna kan kujera, sannan ya zauna same kujeran leaving some space between them yana facing dinta yayi kasa da murya yace "Now tell me, why were you crying Halysaah?" Ta sauke idonta a hankali tace "I just can't understand why Abdul is still after me..." Jay yayi shiru yana kallonta babu ko kiftawa, can yayi kasa da muryarsa yace "But mun gama maganan nan just few hours ago ai Housemate, i told u i will put a stop to that soon, i promise you this, kina gama jarabawa idan mun koma Nigeria komai zai zo karshe in sha Allah" Muryarta na rawa tace "Why not now? Ai bazai daina bi na ba, and i want to concentrate fully on my exams...." Jay yayi shiru yana kallonta, ya sauke idonsa with calmness in his voice yace "Are you sure you will want that now?" Ta gyada masa kai looking so confuse tace "Ya fa je har gidanmu a can kano so many times, sannan daxu muna gidansu Safiyyah sai da yaje gidan fa ya danna bell and left immediately...." jay ya daga idanuwansa yana kallonta da mamaki yace "Really?" Ta marairaice masa tace "Aunty Farida ta gaya min yana ta zuwa gidanmu, pls kawai we should report him to authorities don ya fita hanyata, ni wallahi tsoronsa nake ji, he can be so cunning...." Jay was quiet for almost a minute, sai kuma ya daga kai suka hada ido don kallonsa take, ita ta fara dauke idonta, har zai kamo hannunta sai kuma bai yi hakan ba ya fara kokarin kara barin enough distance tsakanin, yayi kasa da murya yace "Do you want to get married Khaleesat?" Shiru Khaleesat tayi tana kallonsa babu ko kiftawa don tambayar tasa ya zo mata a bazata, shi dai kallonta kawai yake yana jiran amsarta, a hankali tace "Aure kuma?" Jay yace "Yeah" Tana son tambayarsa aure da wa amma ta kasa, nan da nan jikinta yayi sanyi don babu inda tunaninta ya tafi sai ko yana da wani da zai hadata aure da, speaking slowly yace "Aure ne kawai zai sa ya hakura ya dena bibiyanki Halysaah, in kuwa ba haka ba bazai hakura ba ko da an hadasa da hukuma he will only change his tactics..." Hawaye taji ya fara taruwa idonta, sai tayi da ta sanin sauko ta samesa a parlon, kilan da bai gaya mata wannan magana ba, ganin hawaye a idonta cikin sanyi yace "Baki shirya auren ba ko Housemate?" Ƙin ce masa komai Khaleesat tayi tana kokarin ganin bata fashe da kuka ba a wajen, ta rasa me yasa ta zama heartbroken all of a sudden da jin furucinsa, was it because that wasn't what she was expecting or wanting, she still can't tell, Jay ya sauke idonsa daga kallonta, after some seconds yace "To kiyi hakuri, i shouldn't have brought this suggestion up, may be you have other plans than marriage ko" Ita dai bata ce komai ba tana goge hawayen dake sintiri a fuskarta, ya jinginar da kansa da kujera bai sake cewa komai ba, tayi karfin halin cewa "Ai baka ce min da wanda zan yi auren ba" Ya girgiza mata kai still not looking at her yace "A'a, naga ba aure bane plan dinki na gaba, i am sorry i came up with the idea, kawai ina ganin kamar hakan kadai ne mafita... I am sorry" Tana girgiza masa kai still trying not to cry out loud tace "Ni bani da wani plan wallahi, kawai burina Abdul ya fita rayuwata ya kyaleni, duk wani abu da zai tabbatar da hakan i will welcome it wholeheartedly, as far as he will stay far away from me" Jay ya kalleta a hankali yace "To nace aure kin fara kuka ai Housemate" Ta girgiza masa kai tace "In hakan ne best solution i will welcome it, kawai dai ban san da wanda zaka hadani bane" Jay dai kallonta kawai yake amma ya kasa cewa komai, ita kuwa sai goge hawayenta take without looking at him, yayi kasa da murya yace "I don't know ko za kiyi turning down din wanda zan hada ku Halysaah, bazan so in maki dole ba, ko kuma nauyina yasa ki amince bayan ke ba hakan kika so ba a ranki" Khaleesat ta girgiza masa kai cikin karfin hali tace "I won't... as far as it's ur choice i will never turn it down, i trust ur choice, and i know it will be the best for me, nasan baza ka min zabin da bazai yi favouring dina ba, i know this..." Magana take amma Allah yasani karfin hali kawai take, she was very very heartbroken deep inside her and she can't even say why, Jay dai bai fasa kallonta ba yana tunanin what he is about to voice out and how she will react to it, jin shirun nasa yayi yawa ta daga idanuwanta da har sun fara ja suka hada ido, kamar me rada yace "Za ki iya aurena Halysaah?" His question almost took away her breathe cause it hit her unexpectedly, she was stunned into silence at the same time paralyzed with surprise, she couldn't stop staring at him with wide eyes, shi ma kallonta yake babu ko kiftawa kamar yanda take kallonsa, and she realize they've been staring at each other for almost 30 seconds, da sauri ta dauke gaze dinta daga idonsa zuciyarta na bugawa, cikin dubara ta fara kokarin mikewa zata bar masa parlon, yana gano abinda zata yi yayi saurin rike hijab dinta yana kallonta murya can kasa yace "Ba inda za ki je without giving me my answer Halysaah" Boye fuskarta tayi jikin kujera da sauri taki yarda su sake hada ido tana jin kamar ta nutse cikin kujeran, ta dade bata ji irin wannan kunyan da take ji a yanxu ba, yana kallonta yace "Halysaah" Taki dago kanta tana kara shigewa cikin kujeran tace "Uhm" Yayi kasa da murya yace "Look at me plss" kamar zata yi kuka tace "Uhm ni bazan iya ba" Gaba daya ta gama narkar da shi a wajen, ya duka gabanta yana kallonta as if he is whispering yace "Pls say something Halysaah, i want to hear you say something" Khaleesat dai taki yarda ta dago kai su hada ido da shi, she can't even explain what she is feeling at the moment, slowly yace "To tashi ki je ki kwanta, sweet dreams Dear, I love you so much...." Sake gigitata yayi da kalamansa, ta fara kokarin mikewa daga kan kujeran tana rufe fuskarta da Hijab din jikinta, saboda saurin da take ta bar wajen ta take dogon hijab din jikinta kiris ya rage ta fadi har zai rikota kawai ya hana kansa yin hakan, tayi regaining balance dinta within a twinkle of an eye har ta isa staircase ta wuce sama da sauri ta shiga dakinta ta kulle kofa ta jingina jikin kofar tana sauke ajiyar zuciya kamar warce tayi tseren gudu... Daren ranan Khaleesat bata yi baccin kirki ba, she can't even explain her emotions, da gari ya waye har karfe sha daya na safe ta kasa sauka downstairs gashi karfe takwas suke da class ranan, har ta gaji da kiran da Safiyyah ke ta doka mata tun daxu, da sauri ta juya jin ana knocking kofar dakinta, ta kasa tashi ta bude kofar, ita kanta bata san kunyanta ya kai haka ba sae yanxu, da kyar ta mike jin an sake knocking kofar, ta dau veil dinta ta yafa kamar sabuwar amarya ta karasa bakin kofar, nan ma sai da ta tsaya for almost 30 seconds kafin tayi karfin halin bude kofar kanta a sunkuye, yana tsaye bakin kofar calmly yace "Good morning Housemate" Still not looking at him cikin sanyin murya tace "Ina kwana" Yace "Lafiya lau, baki da lectures ne?" Kanta a kasa tace "Ina da" Shi dai kallonta kawai yake ganin wani sabon kunyansa da ta tsira kuma, ya ɗan yi murmushi ya mika mata karamin tray din hannunsa yace "Here.... Idan kin gama sai inyi dropping dinki a school din" Iya abinda yake mika mata kawai ta ɗan kalla sannan ta amsa, shi dai kallonta kawai yake ta juya ta koma cikin dakin sannan ta kulle kofar, Hot chocolate da cookies ta gani a saman tray din, ta zauna saman carpet din dakin da breakfast din a gabanta, bayan Khaleesat ta gama sai da ya kira wayarta sannan dai ta karasa shirinta ta dau handbag dinta da tray din breakfast dinta ta sauka downstairs, yana zaune parlon ta samesa, kanta a kasa ta wuce kitchen ya bi ta da kallo, bayan ta wanke utensils din ta fito daga kitchen din ta tsaya bayan kujera tana wasa da fingers dinta a hankali tace "Na gama" Mikewa yayi ya dau makullin motarsa yace "Ohk mu je" Kofa ta nufa yana biye da ita a baya zata bude kofar taji a bude yake ta fita sannan shi ma ya fita, ta tafi garage ta jirasa ya kulle apartment din, as usual shi ya bude mata door din motar bayan ta shiga ya kulle, sannan ya zaga ya shiga driver seat ya tada motar ya fara Reverse, sai da suka dau hanya yace "We saw our dad off to the airport in the morning, na san kilan bacci kike lokacin da na fita" A hankali Khaleesat tace "Ya koma Nigeria kenan?" Jay yace "Yeah in sha Allah" Khaleesat tace "Toh Allah ya kai su lafiya" Jay yace "Ameen" duk wannan maganar da take taki yarda ta kallesa balle har su hada ido, ya ɗan yi murmushi kamar bazai ce komai ba sai kuma yayi kasa da murya yace "Ko sai mun yi auren zan cire maki wannan kunyan naki?" Wani sabon kunyan ne ya kara lullebeta a motar, ta kauda kanta kamar zata yi kuka tace "Ni dai bana so" Yana murmushi ya gyada kai yace "Za ki yi bayani" Gaba daya Khaleesat ta zama so uncomfortable a motar, Allah Allah take su isa makaranta ta sauka, shi dai lokaci lokaci yake kallonta yana kara admiring din irin kunyarta, can dai yayi murmushi yana gyada kai, suna isa makarantar bayan yayi parking Khaleesat ta bude motar, a hankali yace "Halysaah" Bata fita ba amma kuma bata kallesa ba tana dai jiran jin abinda zai ce, taji yace "To kalleni mana" Ta girgiza masa kai still looking outside, yayi kasa da murya yace "Please" Ta marairaice tace "Bazan iya ba" Yace "Please" Shiru tayi tana jin kamar ya hadata da wani gagarumin aiki kallonsa da yace tayi, da gasken gaske kunyarsa take ji yanxu, a hankali tace "Don Allah nayi latti fa" Yace "To me yasa baza ki kalleni ba" Cikin sanyin murya tace "Zan kalle ka anjima" Yace "A'a ni yanxu nake so" Shiru tayi tana ɗan murmushi tana kallon wajen motar, shi dai kallonta kawai yake, sai da tayi gathering buhun courage sannan ta dake ta ɗan juya a hankali ta kallesa suka hada ido, she could see nothing but her love in his eyes, sai yanxu ta kara fahimtar irin kallon da yake mata tun bayan dawowarsa daga Nigeria, kallon so ne tsantsarta yake mata, ya kashe mata ido daya yana murmushi yace "I love you" Ta rufe fuskarta da mayafinta da sauri, sai kuma ta bude motar cikin hanzari ta sauka ta kulle without turning back ta bar wajen ya bi ta da kallo, Jay was sitted in the car for almost 15 mins ya kasa tafiya, nan kuma duk tunanin inda Khaleesat zata zauna har ta gama Exams dinta yake don shi dai yasan a yanxu dai bazai iya zama under the same apartment with her ba, he just can't, a sanda suka zauna gida daya he had no feeling toward her, ganinta yake just as his normal Housemate and nothing more, babu komai game da ita a ransa har ma sanda suka samu encounter din farko da Abdul a apartment din, he is just being kind and nice to her as a Housemate sannan kuma matsayinta na er uwarsa musulma from Nigeria, ko a sanda ya biya mata kudin jirgi taje duba Ummanta yayi hakan ne kawai saboda shi yasan girman mahaifiya don baya wasa da tasa, but outside of their apartment bayan abubuwa sun faru tsakaninta da Abdul ya maidata gidansu he gradually started developing feelings for her from nowhere, shi kansa bai san ta yaya ba amma yafi tunanin tausayinta da ya saka a rai ne ya ja hakan, he can't even say how everything happened all of a sudden and he fell deeply for her tun period din da suke Exams dinsu, yanxu kuma bazai ce zai kai ta gidansu ta zauna ba don baya fatan wani family member dinsa su sake ganinta a gidan, Ya jinginar da kansa jikin kujeran motarsa ya lumshe idanuwansa cause he is so confuse, yasan yanxu kam ba ɗa bane and he won't risk staying in the same apartment with just the both of them inside, yeah she need him to protect her from her Ex amma zuciyarsa bazai jure zama gida daya da ita ba don yasan lallai na ukun su Shaidan zai zama, and getting another apartment for her is not even an option, bude ido yayi jin wayarsa na vibrate yana dubawa yaga Ajay ne ke kiransa, picking call din yayi ya kai kunne kafin Ajay yace komai yace "Are you at home?" Ajay yace "Did you come across my debit card?" Jay yace "Tare muke amfani da card din... Are you home now cause i need to speak to you Ajay" Ajay dake sauraronsa yace "Bout what?" Jay ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "I will be home now, kar ka fita ka jira ni" Yana fadin haka ya katse wayar ya tada motarsa ya kama hanyar gidansu...... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa bello jidda* Ur evidence 07087865788 https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM HALYSAAH 76 Ajay na cin strawberry dake gefensa idonsa a kan movie din da ake yi a TV, Jay ya dinga kallonsa kafin ya fixge remote ya kashe Tvn, Ajay ya juya ya kallesa yace "Wai kunne ke ji ko ido? Ina fa sauraronka Jawwad" Jay yace "If you are not giving me ur attention i will leave this parlor, tun daxu ina magana hankalin ka na wani waje daban, what's all this pls" Ajay ya tabe baki, sai kuma ya juya yana kallonsa direct in the eyes yana ci gaba da cin Strawberry dinsa yace "Oya be fast pls" Mikewa Jay yayi zai bar parlon Ajay ya fixgosa yace "Kai matsala ta da kai kenan banzan zuciya, ba gashi ina sauraron ka ba" Jay yace "Kar ka rena min hankali mana Malam" Ajay dai ya ci gaba da cin fruit dinsa yace "Ka kashe Tv din ai, i am listening" Jay ya koma ya zauna, for peace to reign yasa Ajay ya maida hankali yana sauraron maganar da Jay ke yi masa, can ya ɗan yi murmushi ya jawo grapes dinsa zai fara sha yace "This is weird... All of a sudden sai ka ji bazaka iya zama gida daya da ita ba, why is that? Meye dalilin ka? Da ba apartment daya kake zaune da ita ba some months ago, ko ni ban san gida daya ku ke ba sai ranan da baka da lafiya, meye kuma ya canza ra'ayin ka all of a sudden...." Jay yace "To yanxu bazan zauna ba, period! in zaka kawo Suggestion din yanda za ayi ka kawo ina sauraron ka...." Ajay yace "Ai ni dalilin hakan nake son sani" Jay yace "Ni dai babu ruwan ka da dalilina kawai solution nake nema, just tell me yanda kake ganin ya kamata ayi.... Tunda kaga we are not going to make the mistake of accommodating her again in this House" Ajay yayi shiru, kamar bazai ce komai ba can dai yace "Kai din dai ya kamata ka zauna a apartment din tare da ita, that's the only solution for now tunda jarabawa za su fara, ko da za a samar mata sabon Apartment definitely sai ya bi ta can din ma kamar yanda ya gano wannan, da mun san haka kawai da a cikin makaranta aka biya mata accomodation to avoid all this, wannan wawiyar kawar tata mara hankali kuma will just worsen the situation idan aka ce taje can gidansu ta zauna, beside no one loves being inconvenience in this state...." Jay ya sauke ajiyar zuciya, after a while ya fixge remote din da Ajay ya dauka yana kokarin kunna TV alamar ya gama maganarsa, Ajay yace "Na fa baka solution din da ka zo nema, ka bar ni in ci gaba da abinda nake yi" Jay yace "I told you staying in the apartment with her isn't an option Ajay, kaga kenan har yanxu babu solution" Ajay yace "Wai saboda kana gudun ka ci gaba da rungumeta ne yasa ka kasa zama gida daya da ita? To ai wannan norms ne a wajen ku tunda iya runguma ce kawai..." Jay ya dinga masa wani kallo, Ajay yayi murmushi yana gyara zama yace "Ko kuma kawai ka kira gida a daura maku auren, ko ni sai in rakaka ka tare a can apartment din kawai" Jay yace "What is this u are saying?" Ajay yayi dariya yana shan grape dinsa bai ce masa komai ba, Jay dai kallonsa kawai yake, can Ajay ya daga kafada yace "Or better still idan kanwar Baabarta na da Passport kawai ka nema mata visa idan Allah yasa an bata sai ta zo ta zauna da ita har ta gama jarabawan....." Jay yayi shiru kamar me nazarin abinda Ajay yace, after some seconds yace "What if ba a bata visa din da wuri ba, sannan before Everything is process kasan zai ɗan dau lkci may be kafin nan ma sun fara jarabawan" Ajay yace "To ni iya shawaran da zan iya badawa kenan, ban san kuma yanda zaka yi ba, stop stressing me with ur problem plss" Jay yace "Why not stay in the apartment with her, har zuwa sanda kanwar Mom dinta zata zo" Ajay ya daga kai ya kallesa, can yace "Wa zai zauna a apartment din?" Calmly Jay yace "Kai....." Ajay ya ajiye fruit din hannunsa yace "Amma ka ma raina min hankali Jay, ni ne zan zauna da ita a apartment din ga ni Bodyguard ko? Can you even hear ur self? kawai sai in koma apartment dinta in zauna gadin ta saboda ni bani da aikin yi, in da gaske neman me gadinta kake ka sa Salem ya koma apartment din da zama mana tunda ya gama masters dinsa, after all she was sharing an apartment kafin ka santa a kasar nan, so yanxu ma zata iya sharing da Salem as her Housemate" Jay ya dinga kallonsa babu ko kiftawa, har ransa yaji zafin abinda Ajay yace wai ya hada Khaleesat da Salem a gida daya, duk da ba wai Salem na da wani mugun hali bane amma yaji haushin hakan sosai, har Salem din da bai masa komai ba sai da yaji ya fara jin haushinsa a zuciya, mikewa yayi ya fice daga parlon kamar zai tashi sama, Ajay ya taɓe baki ya ci gaba da shan fruit dinsa ya jawo remote ya kunna TV. Khaleesat na zaune tare da Safiyyah bayan sun gama lectures wajen karfe shidda saura na yamma, ita dai sai kallon Safiyyah dake bata labarin yanda Mustapha yace zai nemi Abdul duk inda yake ya basa hakuri don shi baya son fitina a kasar mutane, cikin bacin rai Safiyyah ke bata labarin tana cewa "Mustapha ɓata mana sunan family kawai zai yi a zata mu coward ne matsorata, abun duk ya dameni wallahi, har da cewa in na sake kula Abdul zai kira babana ya gaya masa, ni kuma tsoron old Man dina nake wallahi...." Ita dai Khaleesat kallonta kawai take ba don tana sauraron abinda take cewa ba, infact gaba daya ma bata san me take cewa ba, kawai memories din jiya da daddare ne ke dawo mata a kai, ko karatun ma yau bata san abinda aka yi ba sunan ta zo school ne kawai, kana ganinta kasan she is in a very happy mood today, Safiyyah tace "Wai yau naga sai fara'a kike kamar warce aka biya ma kujeran mecca, meye sirrin kawata, wallahi na zata idan na shigo school zan ga idanuwanki sun kumbura don kuka tunda aikin ki kenan, amma naga sai farin ciki kike kina nishadin ki, yau har da kula Coursemate dinmu a Hall kamar ba ke ba" Khaleesat tayi murmushi tana wasa da zoben hannunta tace "To saboda me zaki ga idona ya kumbura don kuka?" Safiyyah tace "Akan issue din Abdul mana, ai nasan halin ki sai ki iya kwana kina kuka" Khaleesat ta taɓe baki har sannan tana murmushi tace "That was then, I don't have time for that now Safiyyah, ni fa na ma dena tsoron nasa yanxu, kuma ba abinda ya isa yayi min...." Safiyyah ta kyalkyale da dariya tace "Nagode tawan, don Allah a wani kasuwan kika siyo liver din nan naki me shegen kyau?" Khaleesat bata san sanda tayi dariyan ba ita ma tace "Allah da gaske i am not afraid of him any longer Safiyyah" Safiyyah tace "Ko ke fa, yanzu tun asali da haka kike ai babu me taka ki kawata, amma naji dadin wanda ya siyar maki da liver din nan har kika samu kwarin gwiwa...." Shiru Safiyyah tayi ta daga kai tana kallon Abdul that is coming toward them, tuni Khaleesat ta hade rai bayan ta gansa ita ma, ta fara tattara reading materials dinta a jaka, ta dau jakar tana kallon Safiyyah tace "Mu je Sophie" A tare suka mike Safiyyah na taɓe baki, Khaleesat na fara tafiya Abdul ya riko veil dinta yana kallonta yace "Don Allah ki bani minti biyar mu yi magana Khaleesat" Ta juya ta kallesa fuskarta a murtuke tace "Let go of my veil Abdul" Yayi kasa da murya yace "Plss Khaleesat, i want to say one or two words, don Allah ki bani lokacin ki ba don ni ba" Fixge veil dinta tayi a fusace kafin ta bar wajen kawai taga ya shige gabanta yana mata magiya yace "Don Allah fa nace maki Khaleesat, ko minti biyu ne ki bani" Safiyyah dai ta koma gefe tana wani dariya kamar taga wawan zama, lallai Abdul ya zama abun dariya yanxu don tsakaninsa da Allah ya marairaice ma Khaleesat, Khaleesat ta juya tana jin zuciyarta na tafarfasa zata bi daya direction din taji ya riko hannunta this time around, bata san sanda ta juyo ta sauke masa mari a fuska ba, cikin fushi tace "Baka da hankali ne Abdul?" a hankali ya sake hannunta don bai ma san hannunta ya rike ba, yana kallonta calmly yace "I am sorry Khaleesat, I didn't mean to...." Tuni ta juya ta bar wajen kamar zata tashi sama, Safiyyah da ta saki baki hangangan ta bi Khaleesat da kallo, slapping Abdul was the least thing da tayi zaton Khaleesat zata iya yi a rayuwa, Safiyyah ta kalli Abdul da ya zauna inda Khaleesat ta tashi ya rike kansa, bin bayan Khaleesat tayi har sannan ta kasa rufe baki with shock, ita kuwa Khaleesat ta sha kunu Kamar bata yi komai ba tana ta tafiyarta, bayan sun yi nisa a hankali Safiyyah tace "Khaleesat?? Did you just slap him?" Without looking at Safiyyah tana ci gaba da tafiyarta tace "He asked for it, don me zai rike min hannu, ko bashi da hankali ne" Safiyyah da ta bude baki tace "Don Allah wa ya koya maki haka? Dama kin iya haka all this while kike maida kanki rubabbiya ake taka ki yanda aka ga dama? I still can't believe your action Khaleesat, Omg" Khaleesat ta tsaya ta ciro wayarta dake vibrate, number Housemate dinta ta gani dama kuma she was expecting his call don shi yace ta jira zai zo ya dauketa, tayi picking call din ta kai kunne, after some seconds tace "Eh mun gama tun daxu" Safiyyah dai kallonta kawai take da mamaki har ta gama wayan, sannan Khaleesat ta kalleta tace "He came to pick me, mu je sai yayi dropping din ki tunda hanya daya ne" Safiyyah ta rike haɓa tace "Ni fa na kasa yarda marin Abdul kika yi da gaske, don da bana wajen aka yi ko jikina kunnuwa ne bazan yarda ba, ko ni duk fitina ta bazan yi gigin marin Abdul ba wallahi" Khaleesat ta hade rai tace "Ni dai don Allah mu tafi, kawai yayi ta bibiyata a makaranta yana daga min hankali for what reason? babu komai fa tsakanina da shi yanxu don me bazai bari inyi rayuwata irin na kowa ba, i am fed up with this" Hawaye ne ya ciko idonta ta fara gogewa tana ci gaba da tafiya, Safiyyah dai tayi shiru tana bin ta, don yau kam Khaleesat ta goge mata hadda tasss, a haka suka karasa inda Housemate yayi parking motarsa, yana ganinsu ya sauko daga kujera me zaman banza, Safiyyah na washe baki ta gaishesa ya amsa da murmushi fuskarsa yace "Ya lectures din? Ko kuma ince revision, since exams is around the corner" Safiyyah tace "Alhamdulillah Yaya Jawwad" Juyawa yayi ya kalli Khaleesat, ganin mood dinta nan da nan fara'ar dake fuskarsa ya bace, ita kuwa Safiyyah sai gwale ido take bayan ta hango Ajay zaune driver seat, shi kuwa dama tun da ya hangosu da Khaleesat ya toshe kunnensa da ear pod yana kallon gabansa, Housemate na kallon Khaleesat ya bude mata back seat, cikin sanyin murya ta gaishesa sannan ta shiga motar, ya kalli Safiyyah yace "Tun da hanya daya ce ki shiga mu ajiye ki ko?" Safiyyah na kirkiran murmushi ta girgiza kai tace "A'a akwai wata Coursemate dinmu da nake jira akwai reading material dina a wajenta" Jay yace "Alright Safiyyah sai anjima" Daga haka ya bude front seat ya shiga, Safiyyah ta daga ma Khaleesat hannu sannan ta jefa ma Ajay harara duk da ko kallon inda take bai yi ba, ta juya tayi wucewarta, Allah ya rabata shiga mota daya da fitinannen nan, kila ma tana dosana kugunta a kujeran motar zai ce ta fita, in ya mata haka kuma tsaf zata masa rashin kunya ita kam, to ina dalili, gwara da ta kama kanta taki bin su.... Bayan sun bar school din Jay ya kasa daurewa ya juya yana kallon Khaleesat yace "What happened Housemate?" Khaleesat ta girgiza masa kai alamar ba komai, yace "No there is something, why are you Moody? Tell me pls, wa ya bata maki rai?" Kamar Khaleesat bazata ce komai ba, sai kuma ta sauke idonta tace "He still followed me again today" Ta madubin mota Ajay ya kalleta jin abinda tace, Housemate yace "Sai me ya faru kuma?" Khaleesat tace "Rike min hannu yayi wai in tsaya in sauraresa ni kuma na maresa nayi tafiyata" Ba Housemate dinta ba, Hatta Ajay sai da ya bude baki yana kallonta ta madubi, Jay was totally speechless yana kallonta, can ya juya ya kalli Ajay, Ajay yace "Kika maresa? Saboda baki da hankali zaki maresa? Ana kokarin protecting dinki by all means kina kara jawo ma mutane aiki? nasan wannan baƙar kawar taki ce zata zuga ki ta koma gefe tana kallo, dama kuma nace idan kika ci gaba da mu'amala da ita sai ta ja maki bala'in da yafi karfin ki don ban ga alamar tana da seti ba yarinyar nan, kina er mitsitsiyar ki zaki daga hannu ki mari gabjejen mutumi haka ko tsoron tsayinsa baki ji ba, da kika maresa sai ta fara hailing din ki ko..." Kuka Khaleesat ta fara yi a motar kamar jira take, Jay ya juya ya kalli Ajay yace "Look Ajay, no one is above mistake, we all make mistake, don haka ba gigitata zaka yi ba, she is frustrated shi yasa tayi hakan, so we shouldn't blame her...." Ajay ya wani kallesa sannan ya maida dubansa kan titi bai sake tofa nasa ba a cikin motar, Jay ya kalli Khaleesat dake kuka, cikin kwantar da murya yace "Ki kwantar da hankalin ki Housemate, babu abinda zai maki in sha Allah, i am giving you assurance, marinsa da kika yi kuma baki yi kuskure ba shi ya ja ma kansa" Ta gefen ido Ajay ya kallesa bai dai ce uffan ba, Ita dai Khaleesat kuka kawai take a hankali har suka isa apartment dinta, sauka tayi daga motar ta nufi kofar apartment din ta bar su cikin motar. Jay ya kalli Ajay yace "You are not suppose to scold her that way, she is already frustrated, cikin kwantar da murya ya kamata ayi mata gyara, beside ita yarinya ce fa har yanzu" Sai a sannan Ajay ya juya ya kallesa yace "A'a, sha'awar gado ce" Jay bai sake ce masa komai ba a motar, bayan kusan minti daya ya kallesa yace "Ka shiga ciki... let me get some food from the restaurant for her, kai nasan zaka yi sorting kanka out, there is everything available at the kitchen" Ajay yace "Wait pls, ni kaji nace maka na amince da tsarin ka ne da kake wannan bayanin?" Jay yayi shiru yana kallonsa, can yace "Pls ka daina maido da magana baya Ajay, i tot we are done with all this, nayi ma Aunty Farida magana daxu tace bata da passport, but getting a passport isn't an issue, Visa ne babban damuwan yanxu, kasan baza a samu da wuri haka ba" Ajay yace "Yanzu me kake nufi? Shikenan ni sai inyi inconveniencing din kaina in takura rayuwata just to please you? Bayan ka fi kowa sanin ba ko ina nake zama comfortably inyi rayuwa ba, You know how irritating everything can be to me, why not consider me?" Jay yace "I will make the apartment very Comfortable for you to stay, beside i will be coming around too, wata daya ne fa an gama exams din...." Ajay yace "To wai ba na baka shawaran kawai kayi ma mai martaba magana a daura maku aure ba? What are you still waiting for?" Jay yace "Me yasa kake mantawa da Mamina ne? I didn't birth my self, har yanxu fa Mami bata san komai kan wannan maganar ba, i need to speak to her about it face to face ta yanda zata fahimce ni... After their exams dama tare za mu koma Nigeria, so i can speak to Mami" Ajay ya ɗan yi murmushi ya shafa gashin kansa bai dai ce komai ba, Jay dake ta kallonsa yace "Meye ma'anar hakan?" Ajay ya daga hannu da sauri yace "Nothing..... Just wishing you luck" Jay bai sake cewa komai ba kuma bai fasa kallon Ajay ba, after some seconds yace "Ban taɓa nuna ina son abu Mami taki abun ba ko da bai mata ba, she is after nothing but my happiness, bata da kowa sai ni, farin cikina shi ne first priority dinta, kuma kai ma kasan da wannan, you can attest to that" a hankali Ajay ya jinginar da kansa jikin kujeran motar keeping silent..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* Ur evidence 07087865788 _We sell all kind of spices like grand masala, 7 mixed spice, all purpose spices, Mandy spices, biryani, pepper soup spice, ginger mix, Curry, suya spice and tsire mix all at affordable prices_ _Siyan daya ko sari, contact +234 803 298 6552 for more info_ HALYSAAH 77 https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM Wajen karfe sha daya na dare Khaleesat na zaune saman gadonta tana karatu a laptop din gabanta, ba sosai take gane karatun ba saboda yunwan da take ji, abincin da Housemate dinta ya siyo mata daxu ɗan kadan ta ci a ciki don bai mata dadi ba, tayi tagumi tana kallon slide din gabanta, kofar dake kallon nata taji kamar an bude, ta juya tana kallon nata kofar, after almost 5 mins ta sauka daga saman gadon ta dau hijab dinta har kasa ta saka sannan ta nufi kofa zata je kitchen ta hado shayi, dama tun daxu ta kasa fita ne don kar ta hadu da Housemate dinta a parlor, don yanxu wani kunyansa kawai take ji, a hankali ta bude kofar ta fito corridor tana tiptoeing, tana fara sauka downstairs ta tsaya da mamaki tana kallon Housemate dinta dake kwance 3 sitter idonsa a lumshe, duk da ba wuta me haske bane kunne a parlon amma tsaf take iya ganinsa, juyawa tayi ta kalli dakin dake kusa da nata with confusion, ko dai kunnenta ne yaji kamar an bude kofar dakin? Lokaci daya taji gabanta yayi mugun faduwa bayan Abdul ya fado mata a rai, kaddai Housemate dinta mance kofar yayi a bude yayi bacci, tana cikin wannan tunanin zuciyarta na bugawa aka bude kofar dakin dake kallon nata, wani kara ta kurma a mugun tsorace tun ma bata ga wa zai fito daga dakin ba, Jay ya mike da sauri yana kallonta, sai kuma ya nufeta da mamaki yace "What happened Housemate?" Tana hada ido da Ajay da ya fito daga dakin shi ma yana mata kallon mamaki ta durkusa wajen ta fara kuka tana jin har lkcn zuciyarta bai dawo dai dai ba, tuni Jay ya karasa inda ta durkusa yana kallonta yace "Me ya faru?" Tana kuka a hankali ta daga idanuwanta ta kallesa tace "Tsoro ya bani ai, ni na zata fa ya tafi daxu..." Ajay yaji kamar yayi ball da ita ta gangara downstairs tsabar yanda ta bashi haushi, don shi kansa sai da ihunta ya juya masa kai, Jay dai kallonta kawai yake ya kasa cewa komai ma, Ajay ya fara saukowa downstairs fuska daure yace "Tashi ki ban waje kar inyi ball dake a nan, silly gal" Turo baki tayi tana goge idonta ta basa hanya yayi tafiyarsa downstairs ya bar su a wajen, ta ɗan daga kai a hankali ta kalli Jay dake ta kallonta ya ma rasa me zai ce, boye fuskarta tayi da hijab din jikinta tana lekosa ta ɗan space din da ta bari a hankali tace "Kayi hakuri, ni wallahi ban san a gidan nan zai kwana ba shi ma, na zata ya tafi tun daxu" Murmushi yayi mata, calmly yace "It's fine Halysaah, you need something?" Ta gyada masa kai, a hankali tace "I want to take tea" Yace "Ohk, let me get you some, ki koma dakin ki" Tana murmushi cikin sanyin murya tace "Thank you" Daga haka ta juya ta koma sama zuwa dakinta, shi kuma ya sauka downstairs Ajay ya bi sa sa kallo har ya shiga kitchen, kwafa yayi ya dau remote ya kunna TV, after some minutes Jay ya gama hada mata tea ya debar mata cookies a plate sannan ya tafi sama, Ajay ya taɓe baki ganin yanda ya maida kansa Boy Boy dinta kawai, alhalin ko 5% din treatment din nan baya yi ma Hadiyah, Jay na kai mata shayin sama yayi knocking ta fito ta amsa amma ta kasa kallonsa, cikin sanyin murya tace "Nagode sosai" Kai kawai yayi mata nodding, slowly yace "Good night Halysaah" Ta juya ta koma cikin dakin ta kulle kofar. Washegari wajen karfe tara na safe Khaleesat ta sauko downstairs bayan tayi wanka ta shirya duk da bazata je school ba ranan, kallonsa ta dinga yi yana kwance saman kujera ya rufe fuskarsa da karamin towel ya kife wayarsa a kirji, karasawa tayi har inda yake kamar tana son gano wani abu, lokaci daya ya cire towel din fuskarsa suka yi ido hudu, komawa baya tayi with shock tana ɗan zare ido tace "Ohh, I tot it's my Housemate" Ya mike zaune yana kallonta babu yabo babu fallasa yace "Kin taɓa ganinsa da wannan kayan? Ko kuma ina wasa dake ne?" Ta ɗan langwabar da kai tace "To ai dai bazan san ba shi bane, since you are having the same height and complexion with him" Yace "I could slap you idan baki fita a gabana ba Malama" Ta wani taɓe baki ta nufi kitchen, irish ta diba ta fere wanda zata yi using, tana yanke yanken veggies da zata soya kwai da shi a ranta tana mamakin Why Ajay is in the house instead of her Housemate, kawai daga jiya zuwa yau ya mata masifa sau biyu, turo baki tayi ta ajiye wukan sai a sannan ta zaro ido ta dau irish dinta ta zuba a man gyada da ta dora don har ta manta da man gyadan, rufe baki tayi da hannunta jin fire alarm din kitchen din ya dau ruri, gaba daya ta mance da shi, don in dai zata yi soye soye wani lokacin lullubesa take da Shower cap dinta ta yanda bazai yi detecting komai ba balle ya fara tona mata asiri yana ruri, ta juya ta fito daga kitchen din tana kallon Ajay kamar munafuka tace "Don Allah ka zo ka min stopping din alarm din ya dena" Ajay yace "A'a ki dai kona masu gida ni ina ruwana, kin zata a Nigeria kike ba" Ta marairaice tace "Don Allah mana, kaga it's very loud fa" Ko kallon inda take bai sake yi ba, ta juya ta koma kitchen din tana kallon inda smoke alarm din yake, ita bata ma san ya ake kashewa yayi shiru ba, ta rage abun girkin zata sake komawa parlor ta masa magana ta kusa cin karo da shi zai shigo kitchen din, komawa gefe tayi tana kallonsa har yayi silencing smoke alarm din sannan ya fita daga kitchen din, Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta ci gaba da girkin da take yi, bayan ta gama ta fito daga kitchen din dama iya wanda zata ci da Housemate dinta kawai tayi, tana kallon Ajay tace "Housemate dina fa?" Bayansa ya nuna mata alamar gashi ya goya shi, juyawa tayi ta wuce sama ya bi ta da wani kallo, tana shiga dakinta ta dau wayarta ta zauna gefen gado tayi dialing number Housemate dinta, yana fara ringing ya daga, in his calm voice yace "Good morning Halysaah" Ta ɗan yi murmushi kamar yana ganinta ta fara wasa da gefen duvet dinta a hankali tace "Good morning" Yace "How was your night?" Tace "Alhamdulillah, naga baka nan" Yace "Yea i went to get something, i will come over later" Tace "I made some breakfast for you" Yace "Really" Tayi shiru bata ce komai ba don har ranta ta so ya ci breakfast din, yace "Ohk give me 30 mins zan dawo sai in ci" Tayi murmushi har sai da dimples dinta ya lotsa tace "Toh Allah ya kawo ka lafiya" Katse wayar tayi sannan ta mike ta fita daga dakin ta koma downstairs, bata ko kalli Ajay ba tayi wucewarta kitchen ta ajiye ma Housemate dinta nasa breakfast din ta dau nata ta fito, hada ido suka yi ta sauke idonta har zata wuce sai kuma ta ɗan kallesa tace "There is everything available in the kitchen, idan kana son kayi making breakfast for ur self" Ya juya ya kalleta yace "Kee, ki shiga hankalin ki, ni ba Jay bane" ita dai tayi tafiyarta sama bata ce masa komai ba. Da yammacin ranan Khaleesat na kitchen tana stew taji an danna bell, fitowa parlor tayi amma ta kasa karasawa gun kofar gabanta na faduwa, kaddai Abdul ne ya biyota, tunawa da tayi Ajay na gidan sai kuma taji hankalin ta ya kwanta, amma dai bata karasa gun kofar ba tana tsaye inda take, sama ta kalla ganin Ajay na saukowa downstairs, bai kalli inda take ba ya nufi kofar ya bude, Safiyyah ta koma gefe ganinsa ta fara kame kamen yafa mayafinta tace "Yaya Ajay ina wuni" A takaice yace "Lafiya" still kuma bai bata hanya ba, yana tsaye bakin kofar, Ta ɗan sosa kai tace "Kwana biyu nace ko laifi nayi maka da ban sani ba Yaya Ajay" Kamar bazai ce komai ba, sai kuma yace "Kin taɓa ɗaga hannu ke kin mari namiji da har kika zuga kawarki tayi hakan?" Safiyyah ta gwalo ido ta cire handbag dinta a kafada tace "Na rantse da Allah ba da sanina tayi haka ba, ta yaya zan zugata? yanxu ma wallahi zuwa nayi zan mata fadan abinda tayi bata kyauta ba, ita Khaleesat bata jin magana kwata kwata ne, ko ni bazan daga hannu in mari lukeke irin Abdul ba, i am trying my best in dinga sakata a hanya amma abun yaci tura, ka tambayeta wallahi ni bani nace ta maresa ba" Ajay yace "Daga ke har ita za ku san yanda za ku yi da shi duk ranan da ya cafke ku a kasar nan..." Yana kai wa nan ya juya ya bar bakin kofar, Safiyyah ta tura masa maki, sai kuma ta shiga parlon tana gwale ido, ganin Khaleesat a tsaye a parlon sai kuma ta washe baki, suka zauna a nan parlon Khaleesat na tambayarta daga inda take ganin uban gayun da ta ci, kasa kasa take bata labarin Birthday din karen wani coursemate dinsu da taje da yanda masu karnuka ke ta zuwa da nasu ita kuma bata da ko mage balle kare, can tace "Da na sani na su Housmate na ara na tafi da shi wallahi" Khaleesat don takaici ma ta kasa ce mata komai sai kallonta take, Safiyyah tace "Har hotuna fa sai da muka yi da karnuka gwanin ban sha'awa in gaya maki" Khaleesat ta taɓe baki ta mike ta tafi duba stew din da take yi, bayan ta fito ta ajiye ma Safiyyah drink din da ta dauko mata ko zaunawa bata yi ba Safiyyan tace "Me jarababben nan ke yi a gidan ki, ina Yaya Housemate din mu?" Khaleesat bata san sanda ta fashe da dariya ba don Ajay yana bakin stairs a tsaye, kamar Safiyyah ta sani ta juya da sauri tana ganinsa ta sinne kai kamar munafuka, dai dai nan Housemate ya shigo parlon, Yana shigowa Ajay ya nufi kofa ya fice alamar dai shi yake jira dama, Safiyyah ta gaida Housemate da fara'arta tana masa sannu da zuwa, ya amsa ya karaso ya zauna parlon yana kallonta yace "Social function kika je ne haka" Tayi dariya har da tafe hannu tace "Eh wallahi birthday din karen wani coursemate din mu na je" Jay yayi murmushi yace "To sannu da dawowa" Tace "Shi ne nace bari in biyo ta nan, kwana biyu ban san me nayi ma Cousin dinka ba sai yayi ta ɗaga min hanci idan ya gan ni...." Jay ya shafa kansa yace "Don't mind him, wani lokacin haka yake" Safiyyah ta taɓe baki tace "Gaskiya abun nasa ba kyau..." Jay ya ɗaga ido ya ɗan kalli Khaleesat dake tsaye parlon tana kallonsa kamar ranan ta fara ganinsa, suna hada ido ta tura masa baki ta juya tayi wucewarta kitchen ya bi ta da kallo, duk Safiyyah na kallonsu tana ɗan murmushi, sai kuma ta rataye jakarta a kafada still smiling tace "To ni zan koma gida Housemate, kafin yayana ya fara kirana" Jay ya maida dubansa kanta yace "Kin jima da zuwa ne?" Tace "Ai ko minti goma ban yi ba, Cousin dinka ne ya bata min mood dina don ban ji dadin abinda yayi min ba, kawai albarkacin ka ya ci yasa na danne zuciyata, har fa da ce min ni nake zuga Khaleesat a America, abun nan ya min ciwo wallahi" Housemate na murmushi yace "Kiyi hakuri, but kinsan me Safiyyah.... Don Allah ko da kun sake haduwa da shi a school kar ki ce zaki yi wani sa'insa da shi" Safiyyah tace "Wai Abdul?" Yace "Eh" Tace "Ai tun da yayana ya hanani ban sake ba wallahi, ko zagina yayi iyaka in kira masa 911 kar yaje ya min wani mugun abu, amma na dena kulasa" Yace "Good...." Mikewa yayi yace "Let me talk to your frnd in the kitchen" Tana ɗan murmushi tace "Ohk" Kitchen ya nufa bayan ya shiga ya kulle kofar ya jingina jiki ya rungume hannu yana kallon Khaleesat dake goge goge a kitchen din bayan ta gama stew din da take yi, ta kasa juyawa ta kallesa, a hankali yace "Weldone Halysaah" Ta ɗan yi murmushi kawai, yace "Let drop off your friend at home" Ta gyada masa kai alamar to, yana kallonta yace "Sai mu je park daga can ko?" Sai a sannan ta ɗan kallesa, sai kuma tayi murmushi ta juya masa, shi dai kallonta kawai yake, after some seconds a hankali yace "Get ready ina jiran ki" Daga haka ya bude kofar kitchen din ya fita, Tsaye ya tarar da Safiyyah tana jiran su fito ta kama gabanta don bata gane irin wannan kallon da taga suna ma juna ba, Jay yace "Ki jira ta shirya sai mu yi dropping dinki a gida" Komawa tayi ta zauna tana murmushi tace "Ai ko Nagode, bari in maza inyi cancelling ride dina" Yace "Idan ta shirya ku sameni a Garage" Safiyyah tace "Toh" Fita yayi daga parlon, Khaleesat na fitowa kitchen Safiyyah ta gaya mata abinda Housemate dinta yace, a tare suka tafi dakin Khaleesat, Safiyyah ta zauna gefen gado tace "I wish i have freedom like you in this country...." Khaleesat tayi murmushi tana duba kayan da zata sa tace "Yanxun ma ai abinda kika ga dama kike yi, gashi har da zuwa birthday din Dog" Safiyyah tace "A'a wallahi, kinsan da yanda na fito yau kuwa, ni da ma ayi sacking Mustapha a wajen aiki su tattara su koma Nigeria" Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba, tana fiddo kayan da zata canxa Safiyyah tace "Waow, dadina dake in kika so akwai fashion, kina sa wannan kaya ai har ku dawo gida Housemate bazai gaji da kallonki ba" Khaleesat tace "To bazan sa ba" Zata maida kayan Safiyyah ta tare press din dakin tayi bake bake a wajen tace "Ke dalla wasa fa nake maki" Da kyar Safiyyah ta lallabata ta saka kayan daga karshe, bayan nan still tayi forcing dinta ta ɗan yi mata light make up a fuska, Safiyyah ta koma gefe ta rike haɓa tana kallonta tana nazarin ace ita Allah ya ba kyan Khaleesat irin abubuwan da zata yi a duniya ai sai Allah, can ta sauke wani nauyayyen ajiyar zuciya tace "Kullum kika yi sallah ki dinga gode ma Allah Khaleesat, he created you differently, wallahi you are so beautiful...." Khaleesat ta wani kalleta, sai kuma ta tsaya gaban madubi tana duba abinda zata goge a fuskarta, just eye pencil da powder kadai Safiyyah ta shafa mata, sai lip gloss shi ma lightly, ta ma rasa abun gogewa a fuskar tata, cause there is nothing special, a hankali Safiyyah dake ta kallonta tace "Ji fa lips dinki wani ba sai ya rantse kin shafa jan baki ba kawata, wallahi ki dinga addu'a idan zaki fita don nasan mutane ne daddaya basa tanka ki a zuciya idan kika fita suka gan ki, duk da dai nan kasar kowa ma da hasken sa" Safiyyah ta zaro ido tace "Lahhh, mun bar Housemate dinki a garage tun daxu fa" Khaleesat ta marairaice mata tace "Ni wallahi kunya nake ji Sophie, i am not comfortable with the dress and the make up" Safiyyah tace "Naga jaraba, idan ku ka yi auren haka zaki dinga kunyar tasa?" Khaleesat ta bude baki tana kallon Safiyyah ta ma kasa cewa komai, Safiyyah ta fixgo hannunta bayan ta tayata daukan handbag dinta ta ja ta suka fita daga dakin, har suka fito daga apartment din Khaleesat taki sakin jiki, Safiyya ta karɓe makullin apartment din a hannunta tace "Tafi ki shiga mota zan kulle gidan" Khaleesat taki tafiya, haka kawai aje bata kulle kofar da kyau ba Abdul ya samu hanyar shiga gidan, Safiyyah ta gama kulle kofar ta juya tana kallon Khaleesat tace "Don Allah ki dena yin abu kamar yan unguwan ku mana, America fa ne nan" Khaleesat ta kai hannu handle din kofar ta murda taji sa a bude, wani kallo tayi ma Safiyyah ta kwace makullinta ta kulle kofar da kyau, Safiyyah tace "Oho na zata ya kullu, mu je" Tunda Khaleesat ta nufi garage Housemate ke kallonta babu ko kiftawa, Safiyyah da taya bera bari ta bude mata front seat tana murmushi, Khaleesat ta wani kalleta sannan ta shiga motar ba tare da ta bari sun hada ido da Jay ba, Safiyyah ta koma bayan motar ta shiga, he wants to compliment her amma yayi shiru saboda Safiyyah, ya fara driving yana kallonta lokaci lokaci, daga karshe ya kasa hakuri yace "You look beautiful Halysaah" Safiyyah dake bayan motar ta fara blushing kamar ita aka ce ma haka, tana ɗan murmushi tace "Nima na gaya mata wallahi, amma ta zata am just pulling her legs, nace mata kyanta na daban ne a cikin kyawawa, duk mijin da ya aureta ya more a rayuwa, ko bacin rai yake ya kalleta zai ji ransa yayi fari ƙal, kuma ace ta samu miji me kyau kamar yanda dae kake din nan, waiiiii Allah kadai yasan yanda kids din ku za su zama don kyau..." Khaleesat taji da ma kawai hakura tayi da fitar nan gaba daya tsabar kunya, shi kam Jay murmushi kawai yake idonsa akan titi yana driving, Safiyyah ta bude jakarta ta ciro wayarta ganin Mustapha ke kiranta ta danna wayar a silent a fusace ta mayar cikin jaka, Jay ya kalli Khaleesat yayi kasa da murya yace "Wani park din kike son mu je?" Karaf a kunne Safiyyah, tace "Park za ku je Yaya Housemate" Yace "Yeah Safiyyah" Safiyya tace "To aje da ni mana don Allah sai in zama photographer" Khaleesat ta dafe kanta, Jay na murmushi yace "To nawa za a biya ki for the Job?" Ta kyalkyale da dariya tace "Haba, ko er lemonade ne kawai a siya min" Yana dariya yace "To an gama, amma baza a kira ki a gida ba?" Tace "A'a ba wanda zai neme ni wallahi" Ko da suka isa park din Safiyyah taki yarda ta zauna kusa da su Khaleesat wai za su yi inconveniencing dinta tana son ta nutsu tayi enjoying ambience din wajen da kyau, Khaleesat tasan duk scope din barin ta daga ita sai Jay ne yasa Safiyyah tace haka, shi ko Jay yaji dadin hankalin da Safiyyah tayi a nan, hotuna tace zata fara masu kar yamma yayi sosai, dadi kamar zai kashe Safiyyah ganin azababben kyan da hoton da ta fara masu yayi, can ta karasa inda suke tsaye tace "Ba fa wanda zai tsaya a space din nan da ku ka bari a tsakaninku gwara ku cike sa kawai" Khaleesat ta wani kalleta, Shi dai Jay Murmushi kawai yayi, Safiyyah tace "Ka ɗan matsa kusa da ita kadan Yaya Housemate so that the space won't make the picture look somehow" Slowly ya matsa kusa da Khaleesat yana kallonta yana murmushi, Khaleesat ta ganta er karama a kusa da shi ga daddaden kamshin turarensa da ya cika ta, tuni Safiyyah ta koma baya da gudu ta ci gaba da daukan hoton da take tana washe baki, farin ciki kamar ya kasheta, haka ta dinga controlling dinsu wajen daukan hotunan, tace su koma can, tace su dawo nan, ta tabbatar tayi masu hotuna masu bala'in kyau, har dai daga karshe Jay yace mata ya isa ita ma ta shigo su yi hoton, zai ba wata er Africa dake wajen wayarsa ta masu hoton har Safiyyah amma Safiyyah taki shiga tace "A'a kar in bata maku hoto ina baƙa da ni" Dariya Housemate yayi haka dai ya lallabata ta shigo aka yi masu hoton su uku, Safiyyah na murmushi tace "Amma fa tunda nake daukan hoto ban taɓa daukan wanda ya dauku kamar hotunan nan da na maku ba wallahi" Jay na murmushi yace "Dollar nawa za a baki to?" Dariya tayi ta tattara lemonade dinta da tacos da ya siya mata tace "Wannan ma da aka siya min Allah ya amfana" Daga haka ta kara gaba ta bar masu wajen, Jay was amaze at how Safiyyah snapped the pictures so well, ya kasa daina kallon Khaleesat a hoton, the pictures where so beautiful, Khaleesat tun da ta kalli hoto daya ta kasa ci gaba da kallon sauran ta koma ta zauna kawai, after a while ta daga ido ta ɗan kalli Jay taga kallonta yake, da sauri ta maida kanta kasa, a hankali yace "Halysaah" Bata dago kanta ba still tace "Uhm" Yace "Me yasa baki sakin jiki da ni yanxu? You weren't like this before, ko don nace zan aure ki?" Sunkuyar da kanta tayi alamar kunya, yace "To meye amfanin zuwa nan tunda baza ki saki jikin ki ba, i want us to have a quality time together amma kiyi ta sunkuyar da kai...." Tana murmushi a hankali tace "To ai kunya nake ji" Yace "To kalleni zaki dena jin kunyan" Taki dagowa tayi shiru, yace "Halysaah" Tace "Ni bazan iya ba" Bai sake ce mata komai ba, ganin haka ta daga idanuwanta ta kallesa taga kallonta yake, murmushi yayi mata murya can kasa yace "You are specially made Halysaah" Rufe idonta tayi tana murmushi a hankali tace "Thank you" Yace "Kin dai ji me kawarki ta ce ko?" Khaleesat ta daga ido ta kallesa tace "Me ta ce?" Yayi kasa da murya yace "We will make beautiful Babies together...." Khaleesat ji tayi wani azababben kunya ya rufeta, yana murmushi yana kallonta yace "Ni ko guda daya kika bani me kama dake i will appreciate..." Kamar zata yi kuka tace "Ni dai mu tafi gida" Yace "A'a sai kin ban labari, kina ban labari ko daya ne sai mu tafi" Shiru tayi, sai kuma tana wasa da straw din drink din gabanta tace "Wani irin labari?" Yace "Ko ma wani iri ne, ko kuma ki bani labarin yanda ku ka hadu da Funny frnd dinki Safiyyah" Khaleesat tayi murmushi ta dago kai tace "Ohk...." Babu bata lokaci ta fara basa labarin farkon haduwarta da Safiyyah a school, shi dai kallonta kawai yake ko kiftawan kirki baya yi, everything about Khaleesat is just beautiful and breathtaking, tsakaninta da Allah take ta basa labarin Sophie ashe ko sanin abinda take cewa bai yi ba ya kafeta da ido with many imagination running his mind, daga bada labarin Safiyyah kawai ta saki jiki a wajen, dama kuma haka yake so... kamar yanda ya so hakan ne ya faru don they had a wonderful time together, labari sai wanda ta manta ne bata basa ba a kan experience dinta a America tun daga shekaran da ta zo har zuwa yanxu, wani yayi dariya, wani yaji tausayinta wani ya ga wautan ta, babu abinda ya kara burgesa da ita tana basa labarin sai turancin ta, she was so vocal, duk da timidness dinta she was very outspoken kamar ba a unguwan nan da gidansu yake ta tashi ba, he never knows she speak so well sai yau, yayi kasa da murya yace "You know what Halysaah?" Ta girgiza masa kai tana kallonsa, a hankali yace "I love you so much" Rufe fuskarta tayi da sauri tana murmushi... Sai wajen karfe bakwai suka bar park din, sai da suka fara dropping Safiyyah a gida before heading home, Jay na parking Khaleesat ta kalli motar Ajay dake parking Space, can ta kalli Jay tace "Is he waiting for you?" Jay yace "I don't think so, kinsan yana da aboki a Neighborhood din nan shi ma PhD yake, the frnd is at the far end of this street, External defense dinsu is around the corner...." Khaleesat tace "Ohk har da kai?" Jay yace "Yea in sha Allah, period din exam din ku ne Defense dinmu" A hankali tace "To Allah ya baku nasara" Yana murmushi yace "Ameen" Tace "To a ina zaka yi parking since he is occupying the space?" Yace "Zan je gida in dawo anjima" A hankali tace "To ni kadai a apartment din?" Yace "Ga motar Ajay kina gani, ai yana ciki kenan" Shiru tayi tana kallonsa, ya mata murmushi yace "Mu je in raka ki ciki to" A tare suka sauka daga motar ya rakata har cikin apartment din, yana kallonta calmly yace "Can i go now?" Jingina tayi da bango a kusa da shi ta langwabar da kanta kawai ta marairaice tana kallonsa, ya sauke idonsa daga kallonta trying to calm his self down, a hankali yace "I need to go Halysaah, ki kulle kofar" Daga haka ya juya ya fita daga parlon without looking at her, ta bi sa da kallo kafin ta kulle kofarta.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke HALYSAAH 78 Bayan Khaleesat tayi karatun da zata yi ta kashe laptop dinta ta ajiye sannan ta saka hijab ta fito daga dakin don tun da ta dawo bata ci abinci ba gashi har karfe goma ya wuce, downstairs take leke ko zata ga Housemate dinta, Ajay ta gani yana danna wayarsa, hannunsa rike da Can din soft drink, tana ta tsaye a corridor din don da ba don yunwan da take ji ba komawa dakinta kawai zata yi ta hakura da abincin, after a while ta fara saukowa staircase din trying not to make any sound, tun daga nesa take kallon screen din wayarsa ganin kamar hoton da suka yi da Jay daxu a park, tsaye tayi tana ta kallon wayarsa da mamaki, after some seconds taga ya fita daga hoton kasa gane inda ya samu hoton tayi, tasan dai Jay bazai tura masa pictures din ba, to kaddai a status Housemate dinta ya dora hoton, ta shiga uku, sosai taji gabanta ya fadi, lokaci daya Ajay ya juya bayan yayi sensing kamar mutum na tsaye bayansa, ta ɗan koma baya kamar munafuka tana kame kame tace "Kitchen zan je dama" Ajiye wayarsa yayi ya juya da kyau yana kallonta da mamaki, ta langwabe kai sai kuma ta nufi kitchen din da sauri tana ɗan waigen sa, ko da ta fito bata gansa a parlon ba, bayan ta koma daki ta ajiye shayin hannunta ta dau wayarta da sauri ta bude WhatsApp dinta, status din Housemate dinta ta bude taga hoton amma ya rufe fuskarta with the caption "Halysaah" da yayi ma hoton, to amma wanda ta gani a wayar Ajay fuskarta a bude yake, ta dinga kallon hoton duk da fuskarta a rufe yake, bata san sanda murmushi yayi escaping lips dinta ba don sun yi kyau sosai, har ta ajiye wayar sai kuma ta dauka tayi masa reply din picture din tace "What if gal frnd dinka ta gani" ajiye wayar tayi ta dau cup din shayin da ta ajiye tana juyawa a hankali, taji wayarta yayi vibrate alamar shigowar message, daukan wayar tayi taga ya mata reply yace "Ke ba Gal frnd dita bace? Ai ke zabina ce, ita kuma zabin iyayena" Hmm kawai ta mayar masa sannan ta kashe data dinta ta ajiye wayar, lokaci daya duk jikinta yayi sanyi tana maimata zabin iyayensa da yace a ranta, duk yunwan da take ji haka nan ta neme sa ta rasa shayin ma bata wani sha sosai ba, bayan ta gama shirin kwanciya ta dauro alwala ta fito sannan ta kashe wutan dakin ta kwanta, wayarta taji na vibrate ta jawo wayar a hankali tana dubawa taga Housemate dinta ne ke kiranta, sai da ya kusa katsewa tayi picking call din ta kai kunne tayi shiru, yace "Why did you go offline Halysaah?" Ta ɗan yi murmushin karfin hali tace "Na je nayi alwala ne zan kwanta" Yace "Ohk, kina da class gobe ne?" Ta ɗan yi shiru, duk da bata da shi tace "Eh ina da...." Jay yace "Yaushe?" Tace "Da safe" Yace "Ohk, na tsaya wani aiki ne a system dina shi yasa ban dawo ba, may be we will meet in school tomorrow in sha Allah" Tace "Allah ya kai mu" Yace "Ameen, Good night Halysaah, naga kamar kin fara jin bacci ko?" Cikin sanyin murya tace "Uhm, sai da safe" Yace "Allah ya kai mu lafiya" Daga haka ya katse wayar sa, Khaleesat ta ajiye wayar hannunta ta juya ta lumshe ido. Da safe Khaleesat na saukowa downstairs taga parlon soo tidy, kamshi sai tashi yake ta ko ina via diffuser da ta gani a parlon, makalewa tayi jikin staircase tana ta kallon parlon, ai kuma ta shiga uku da gori, after a while ta nufi kitchen, ta window din kitchen din take kallonsa don karamin garden ne a waje, entrance din garden din yana ta wajen Garage, tunda ta zo apartment din bai fi sau biyu ta shiga wajen ba, press up yake yi a wajen, juyawa tayi ta kalli Yoghurt da diff kind of berries da granola da nuts sai kiwi and apple dake ajiye kitchen din, nan ta gane parfait zai hada, har zata hada masa wata zuciyar tace ta kama kanta tayi abinda zata yi ta fita, noodles ta dauko zata dafa, tana cikin dafa noodles din ta daga kai taga ya fita daga garden din, bayan ta gama girkin ta fita daga kitchen din zuwa dakinta, after almost 20 mins ta sake saukowa downstairs ta shiga kitchen din, har sannan fruits din suna wajen, ta ɗau karamin bowl ta fara tsinkar different berries din wajen ta yanda bazai gane ta taɓa masa ba, tana wankesu a sink ta fara sha, da sauri ta juya tana kallon kofar kitchen din tayi ido hudu da shi, ita kanta bata san dalilin da yasa ta fara dariya ba, ta ciro berry din da ta kai baki tace "Wanke maka su zan yi fa, so that i can help you dice them" Tana fadin haka ta ajiye bowl din hannunta ta dau wuka zata fara fere Kiwi fruit dake wajen, taji yace "Zo ki fita ki ban waje" Ta ɗan kallesa tace "I want to help you wash them...." Tana ganin kallon da yayi mata, ta ajiye wukan ta wanke hannunta a sink sannan ta ajiye masa bowl din Berries din da ta diba a kofar sauran fruits din, kofa ta nufa ta bi gefensa ta fita daga kitchen din ya bi ta da kallo yace "Ke da baki iya gyaran gidan da kike ciki ce zaki wanke ma mutum abinda zai ci" Khaleesat ta juya ta kallesa dama tasan sai yayi maganar nan, tace "Tun da kai ka gyara ba shikenan ba, ai don ina zuwa school ne...." Yace "You are dirty dai Malama, do not use school to cover ur untidiness" Yana fadin haka ya karasa cikin kitchen din, ta tsaya bakin kofar tana kallonsa taga ko da Liquid wash zai wanke fruits din karewar tsafta, sai da ya fara tura bowl din Berries din da ta diba zuwa can far end of the kitchen yanda bazai dinga ganinsa a kusa da shi ba sannan ya fara wanke fruits din a sink, bayan gishiri har da Venegar yayi using wajen wanke fruits din, a ranta tace to ai wannan ba sabon abu bane kowa na yi, ita tsakaninta da Allah take jiran taga ya zuba liquid wash wajen wanke fruits din, amma taga bai yi hakan ba, tana ta tsaye jikin kofar kitchen din har ya gama hada lafiyayyen parfait dinsa, ta shiga kitchen din ta dau bowl din Berries dinta da ya gantalar gefe daya ta ajiye kusa da shi ta kallesa, ko kallonta bai yi ba, can ta ga ya jawo sauran Yoghurt da ya rage ya tsiyaya mata a bowl din ya ci gaba da abinda yake yi, dariya ya bata amma ta dake bata yi ba, tana ta kallon rich parfait dinsa da yaji fruits da Granola da Nuts, tana kallo ya dau zuma ya tsiyaya a kai, dai dai nan aka bude kofar parlor, ya ajiye zuman hannunsa ya karasa kofar kitchen din don ganin wanda ya shigo, da sauri Khaleesat ta kai hannu ta lakaci honey din da yoghurt, akan idonsa don har ya juyo ya dawo cikin kitchen din, komawa baya tayi da sauri, bai ko kalleta ba ya dau spoon yayi scoping dai dai inda ta saka hannu sannan ya ajiye spoon din a sink, ita dai bata san ya aka yi ba kawai ganin bowl din parfait din tayi ya kife a kasan kitchen, ya koma baya yana kallon parfait babu ko kiftawa, tun tana daurewa har ta kasa ta dafe base cabinet din kitchen din ta tuntsire da dariya kamar an aikota, Ajay dai kallon Parfait din kawai yake a kasan kitchen din, after some seconds ya shafa kansa trying not to laugh too, don dariyarta kadai ya isa ya saka mutum yayi dariya bai yi niyya ba, irin dariyar muguntar nan kawai take yi, ita kuwa ba abinda ya bata dariya ganin bai tsam mata ba gashi duk sun tuntsire a kasan kitchen, kuma shi ya kifar da kayansa da alama, kawai ya juya ya fice daga kitchen din ta bi sa da kallo tana kyalkyala wani sabon dariya, sai kuma ya sake dawowa yana kallonta yayi kasa da murya yace "Kin ga idan ina abu a kitchen kika sake shigo min i will fling you out of this window, ai ni ban san ke mayya bace" Yana fadin haka ya sake ficewa daga kitchen din, Khaleesat dai bata fasa dariyan da take ba, da ta kalli bowl din da ya ɗan tsiyaya mata zallan yoghurt sai ta kalli rich parfait dinsa dake kasan kitchen a kwance, sai ta kara kwashewa da dariya, ta dade abu bai bata dariya kamar haka ba, tayi dariyarta ma'ishi sannan ta fara gyara kitchen din, sai kuma ta fara jin tausayinsa don duk effort dinsa bai sha ko spoon daya ba, gwara ita ta ɗan lasa zuma da yoghurt, the incident was so funny to her, haka duk ta kwashe fruits din da granula dake kasa tayi disposing a shara, bayan ta gama goge kitchen din ya dawo fess ta fito parlor taga Housemate dinta zaune a parlon yana danna wayarsa, tana murmushi ta karasa cikin parlon ta zauna sannan ta gaishesa, ya daga kai ya kalleta ya amsa, bata sake cewa komai ba, shi ma haka, after a while yace "Ba kince zaki school da safe ba?" ta langwabar da kai tace "Kawai fasawa nayi" Juyawa tayi ta kalli Ajay dake saukowa downstairs fuskarsa babu yabo babu fallasa yana rike da makullin motarsa, ta bi sa da kallo trying not to start another laugh har ya fice daga parlon, sai kuma ta kalli Jay ta fara basa labarin abinda ya faru a kitchen, she couldn't hold her self anymore ta dinga kyalkyala dariya har da saukowa daga saman kujera, shi dai Jay kallonta kawai yake, sai kuma ta dena dariyar da take tace "Isn't it funny?" Jay yayi murmushi wanda iyakarsa lips yace "It is, sai yace maki me?" Tace "He was very shock too, nasan da ya san abinda zai faru kenan da ya debar min, Allah ne ya kamasa, ga shi yayi stressing kansa ya gyara gidan nan gaba daya yau" Tana dariya ta kare maganar, Jay yace "Gaskiya ne, amma baza ki je school ba me yasa kika ce min za ki je?" Shiru tayi, sai kuma tace "Kawai da gari ya waye na canza mind" Jay yace "Ohk" Wayarsa ne ya fara vibrate ya mike yace "Zan fita sai anjima" Khaleesat na kallonsa tace "Kayi breakfast ne?" Yace "Nayi" Tace "Ohk, byee" Juyawa yayi ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita.... Khaleesat na kitchen da yamma bayan ta dawo school taji an bude kofar apartment dinta, sosai taji gabanta ya fadi don dama tunda ta dawo taga ba kowa apartment din take a tsorace, sai da taji muryar Ajay a parlon sannan hankalinta ya kwanta, jingina tayi jikin cabinet din kitchen din tana kirga kwanakin da taga Jay last, after a while ta kashe wutan girkin don ta gama, ta dan leka parlon taga Ajay da wani abokinsa ne bayerabe yana gwada masa abu a Laptop dinsa da alama shima Phd yake yi, fitowa tayi daga kitchen din ta gaida abokin ya amsa yana kallonta, sai kuma ya kalli Ajay yace "Is she ur sister" a takaice Ajay yace "Yeah" Yana ci gaba da nuna masa abinda yake nuna masa, da broken English abokin yace bazai basa ita ya aura ba, Ajay ya daga kai ya kalli Khaleesat yace "Ke dalla malama wuce ki ba mutane waje" Khaleesat ta kallesa da mamaki don ita dai ba tsayuwa tayi a parlon ba, sama ma zata wuce, Femi na kallon Ajay yace "I am very serious Prince, i will marry her as far as una go give me, she's very beautiful, is she Halfcast?" Ajay yace "Meet Jay about that Femi" Femi ya gyara zama yace "Jay no get joy at all, he isn't as straight as you" Ajay yace "He will listen, since it's about you marrying his sister..." Femi yayi dariya sosai yace "I will definitely visit Bauchi soon be that" Ajay dai bai sake ce masa komai ba. A kwana a tashi lokacin Exams din su Khaleesat ya matso don satin da za su shiga za a fara jarabawan, tun ranan da ta mari Abdul har zuwa yau bata sake ganin ko giftawarsa a school din ba, ita dai har sannan hankalinta yaki kwanciya don gani take kawai jira yake ta koma Nigeria before doing anything to her, sosai tayi da ta sanin marin da tayi masa, she wish bata yi hakan ba, da kawai ignoring dinsa ta dinga yi since he is not harming her, da ta tuna sati biyu kawai za su yi suna jarabawan sannan ta koma Nigeria sai taji jikinta yayi sanyi sosai, During all this time haduwanta da Jay ya ragu sosai ba kadan, ko apartment din nata sai in zai kai mata abu yake zuwa kuma ba dadewa yake yi ba, but tayi masa uxuri tunda yace mata su ma a wannan period din ne External defense dinsu may be he is concentrating on that and also giving her space to concentrate on her own studies too, amma abinda ke bata mamaki kafin taga Ajay da laptop ko wani abu da zai nuna karatu yake sau daya to ta gansa da remote din TV da bowl din fruit yana ci yana kallon football ko wrestling sau goma, gashi kamar baya bacci, abokansa kuwa in suka xo baya shigowa da su apartment din.... Ranan Friday Khaleesat na school tare da Safiyyah suna studying course din da za su yi exams dinsa ranan Monday, hadari ne sosai a garin, Khaleesat tace "Mu je apartment dina sai mu ci gaba da karatun a can ko?" Safiyyah tace "Tabb, ni ce zan je apartment din ki wannan Uztaz din na nan? Ni har yanxu kin ki gaya min dalilin da yasa suka yi switching da Housemate din ki" Khaleesat na kallonta tace "To ta yaya nima zan sani, na tambaye Housemate dina yace kawai sbda he is busy because of his upcoming defense ne baya samun time sosai he is always in the Library" Safiyyah tayi dariya tace "Shi kadai zai yi defense din? Shi ma Ajay ba defense din zai yi ba ko ba lokaci daya za su yi bane? Ni har na gano dalilin da yasa yaki zama a apartment dinki wallahi" Khaleesat tace "Meye dalili?" Safiyyah tayi dariya tace "Gaskiya na kara respecting Housemate dinki, wallahi iya da addini da sanin ya kamata, kinga a baya ai babu komai tsakaninku shi yasa ku ke zaune kowa na harkar gabansa a tsohon Apartment din ki, iyaka kuyi mutunci, yanxu kuwa da ya fara son ki yana tsoron kada shaidan yayi using Opportunity din zaman ku gida daya ya cuce ku, kinga hakan bazai haifo ɗa me ido ba, gaskiya yaya Housemate iya da addini" Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba sai ma murmushi da tayi kawai, Safiyyah tace "Abinda ya guje ma kenan kawai ba wani abu ba, don shi zuciya ba shi da ƙashi, shi kuma Ajay masifarsa da fitinarsa kadai ma bazai sa ya shiga harkar ki ba a gidan, shi fitinarsa ma zai iya zuke mutum wallahi" Khaleesat na maida wayarta cikin jaka tace "Sai ka masa abinda baya so yake masifa ai, he just love being on his own kar a shiga harkarsa that's all, but he is kind, caring and down to earth, sai da muka zauna yanxu na gane haka" Safiyyah ta saki baki tana kallonta, can ta gyara zama tace "Ikon Allah, yau ke kike yabon Ajay da kanki, to me da me yayi maki da kika ga he is caring and kind zaman ku a apartment din naki" Khaleesat ta daga ido ta kalleta, can tace "Kilan baza ki yarda ba idan na fara gaya maki wallahi" Safiyyah tace "Ai ina jin ki, gaya min yanda aka yi kika gane hakan in ga ko zai yi convincing dina..." Wayar Khaleesat ya fara vibrate a jaka, ta bude jakar ta ciro wayar, Safiyyah ta leka screen din don ganin me kiranta, sae kuma ta riƙe haɓa tace "Ikon Allah" _Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa bello jidda Ur evidence_ 07087865788 *Hakika duk wacce ta Bari aka barta abaya ita taso domin mu mata da ado da kwalliya aka sanmu. Assalamualaikum, barkanmu dai Yan uwana ma masu albarka, ayau na zo maku da batun sababbin kayan da na kawo Mana masu matukar kyau da kuma inganci,oum eman collection 🤝😍, takawo maku jakunkuna da takalma,hadi da abayas da kuma sarkoki masu matukar kyau da kuma sauki,07018872587 Ena amare da uwayan gida masu capacity's toh duk wacce ta yarda da tacika mace da wacce takeso ta zamo ma abociyar kwalliya toh ta garzayo gunmu domin hadewarki cikin ado da kwalliya kedai nemeni a wannnan number domin kisami kayayyaki masu kyau da kuma quality akan kudi kalilan hajiyata 07018872587 ngd 🤝 ado da kwalliya shine takenmu* HALYSAAH 79 Khaleesat tayi picking call din ta kai kunne tayi shiru, after some seconds ta mayar da wayar cikin jaka ta kalli Safiyyah tace "Makulli zai amsa" Safiyyah tace "Toh shi ina na shi makullin? Haba, he is a kind of person that is way too organized da har za ace zai manta makulli a gida, ai irinsu are always cautious of everything, ta yaya zai mance abu me muhimmanci kamar makulli, shi dai yasan me yasa ya kira ki amma ba wai makulli ba" Khaleesat tace "To ni dai bai taɓa requesting makulli a wajena ba sai yau, probably he was carried away shi yasa ya manta, waye baya mantuwa" Safiyyah tace "To meye na wani karesa?" Khaleesat tace "A'a ba karesa nake ba, naga kamar you are trying to put meaning into everything" Safiyyah tace "Ko me yasa Housemate zai wani hada ku waje daya salon ku saba, ke dama gashi zuciyarki kamar ta yara mutum na maki kirki sau daya to har abada yana da kirki a wajen ki" Khaleesat bata san sanda ta fara dariya ba tace "Wa yace maki mun saba? An ce maki har yanxu baya masifarsa ne? Kawai dai bayan masifar tasa he will still be kind to you and give u a listening ear that's one thing about him, kin tuna abincin da na kawo school ranan har kika hanani kika cinye duka?" Safiyyah tace "Ehen sai aka yi yaya?" Khaleesat tace "To shi ya dafa" Safiyyah ta bude baki tace "Ban gane shi ya dafa ba, wannan abincin da nayi ta santin sa kina nufin girkinsa ne?" Khaleesat tayi dariya tace "Wallahi.... he can cook so well fiye da tunanin ki, amma iya jollof rice, sai rice and stew da Alfredo pasta kawai ya iya, i notice su ne favorite food dinsa, he can also make you different kind of salad and fruit salad, yana son su sosai...." Safiyyah ta hade rai, sai kuma ta taɓe baki tace "To shi ne ya burge ki kike haƙilon bani labari? Nasan Housemate ma babu abinda bai iya girkawa ba kawai chance ne baki basa yayi maki ba, beside he is always busy ina yaga lokacin wani girki" Dariya sosai Khaleesat tayi tace "See me see trouble, ni kin ji na ce maki Housemate bai iya ba? To in gaya maki bai ma iya din ba, sanda muke old apartment dina ba sai dai in dafa ya diba ba, shi ko wanke wanke bana tunanin ya iya balle shara da gyaran gida" Tana dariya ta kare maganar, Safiyyah ta wani kalleta tace "Abinda shi ba mace bane ta yaya zai iya wanke wanke ko kuma ya fara girke girke a kitchen kamar wani da ya taso cikin mata, girki da gyaran gida ai sai mata, ni tun da aka haifeni ban taɓa ganin Yarima da girki ba ma sai wannan karan, kawai dai wahalalle ne wannan Yariman...." Khaleesat ta kasa daina dariya tana kallon Safiyyah tace "OCD fa garesa, baya cin abincin wanda bai yarda da shi ba shi yasa yake kayansa da kansa, kika sani ko a can masarautar su akwai masu yi masa girki? Even here in America ai yana cin abincin Cook din gidansu...." Safiyyah tace "Ashe ma kawai kina zaune da wanda ke maki kallon gagarumar kazama ne tunda baya cin girkin ki, in ni ce ma bazan zauna gida daya da shi ba yana min kallon katuwar kazama, shi ne har kike bada labarinsa kina babbaka dariya bayan ya gama raina tsaftar ki, to meye abun dariya a nan, sannan kawai daga barin ki da shi a gida shi ne zaki je ki sake masa fuska har haka bayan kin san ɗan uwansa mutuwar son ki yake? Ai kamata yayi tsakanin ki da shi a gidan gaisuwa sama sama, don Housemate dinmu bazai ji dadin ganin kina washe ma Cousin brother dinsa hakora ba" Khaleesat ta hade rai tace "To ni yanxu ce maki nayi abu na hadani da shi a gidan ne wai?" Safiyyah ta daga hannu biyu sama tace "A'a kar ki canza baki Malama, bana son karya, yanzun nan kika gama yaba ma mutum kina cewa he is kind and caring amma kina neman lauye magana, in ba sake masa kika yi ba ta yaya kika san he is down to earth? Wato ke kawai kulasa kike yi kaca kaca a gidan ma kenan" Khaleesat tace "Ni dai wallahi ban ce maki haka ba kece dai baki fahimce ni ba, mutumin da ba magana ma sosai yake min a gidan ba" Safiyyah tace "Oho dai ni har kin bata min rai wallahi, sai kace wata kuturwa meye na dinga cin abincinsa da ya dafa da baza ki dafa naki ba" Khaleesat dai kallonta take, Safiyyah na gyara ɗankwalin kanta tace "Housemate ai bazai ji dadi ba fisabilillahi, ni ma kaina ban ji dadi ba balle shi da baza a rasa sa da kishi ba tunda duk mun san yana sonki" Ita dai Khaleesat bata ma san me zata ce ba, amma da gaske Ajay ko lkcn kulata ma baya da shi a gidan, iyaka yayi masifa in ta debar masa abinci kuma wani lkcn late take komawa gida shi yasa ma bata girkin in taga yayi sai ta debi nasa, kuma kaɗan yake dafawa kamar abincin rowa, can ta taɓe baki tace "Wai ke ance maki yana da time dina ne a gidan, shi fa kawai ya kalli football ko wrestling or boxing sai kuma ya buga PS5 dinsa" Safiyyah ta kalleta da sauri tace "Ke haba, da gaske? yaushe ya kawo PS5 din?" Khaleesat tace "Oho kawai gani nayi nima" Safiyyah tace "Ki ce wataran idan naje gidan baya nan za mu buga" Khaleesat tayi dariyar da bata yi niyya ba tace "Za ki buga dai, ni ba ruwana" Safiyyah tace "Kin tuna na saurayin former Housemate dinki Nancy, a sannan fa kema kika iya, Mutumin kirki haka ya bar mana ps4 dinsa a gidan da yaga muna so, kullum sai naje apartment dinki saboda shi lokacin muna level 2, mu yi ta buga game" Khaleesat tace "Hmm na tuna, ai yanxu ma idan naga yana yi sai in makale in ta kallo, kamar inje inyi" Safiyyah tayi kasa da murya tace "Wani rana da wani rana ne baya zaman gidan?" Khaleesat tace "Every Saturday saboda ina tsayawa school mu yi karatu baya zama gidan sai sanda zan dawo da yamma yake dawowa shi ma" Safiyya tace "Tunda dai ba mu muka kawo karatun nan duniya ba, gobe kawai in kin taho school sai mu koma apartment dinki tare da sauri mu buga PS5 din, abinda ma mun gama karatun course din da za muyi ran Monday in de ba haram za mu kara karantawa ba, kawai mu je mu shoshale a apartment din ki da Ps5" Khaleesat ta zaro ido jin wayarta na vibrate tace "Lahh, na manta ban kai masa key din ba" Safiyyah tace "Je ki kai masa ki dawo mu ci gaba da maganar mu, ai ni ban san yana da ps5 ba" Khaleesat ta mike ta bar wajen, duk da hadarin dake gari Safiyyah ke ce mata taje ta dawo su ci gaba da magana ko a jikinta idan ruwa ya musu duka. Khaleesat bata karasa inda Ajay yayi parking ba aka fara yayyafi, tana isa wajen ta bude front seat ta mika masa makullin apartment din, zata kulle motar yace "Kwana za ki yi a makarantar?" Tayi shiru bata ce komai ba, can tace "To zan je in ma kawata sallama" Yace "Ohk" Juyawa tayi ta koma inda ta baro Safiyyah, Safiyyah na ganinta tace "Kin ga an fara yayyafi, mu koma department mu ci gaba da maganar mu..." Khaleesat tace "Gida ma zan wuce" Safiyyah ta tabe baki tace "Motarsa za ki shiga kenan? Dama abinda yasa ya kira ki kenan ya ga hadari" Khaleesat tace "To ba waje daya za mu ba in ma saboda hakan ya kirani? Dama dawowa nayi in maki sallama sae gobe" Safiyyah tace "Ai shikenan" Khaleesat tace "Ko kuma tunda hanya daya ne mu je yayi dropping din ki kawai mana" Safiyyah tace "Wa?? Gwara inyi trekking inje gida, salon ya koreni, kema da kike iyayin cewa in shiga motar ba kyaleki zai yi ba.... Hadawa zai yi ya fatattake mu" Khaleesat bata sake ce mata komai ba suka nufi inda Ajay yayi parking, suna karasawa wajen Khaleesat tayi shiru ta tsaya ganin babu motarsa, can ta ɗan kalli Safiyyah ta gefen ido, Safiyyah dake ta waige waige tana neman motar Ajay tace "Ina motar tasa?" Khaleesat tace "Kawai mu tafi mu hau Uber" Da Safiyyah ta fara baɓɓaka dariya har da durkusawa kasa, tun Khaleesat na daurewa har ta kasa ita ma ta fara dariyan, da kyar Safiyyah ta dago tsabar dariya har da hawaye tace "Har kina min iyayin in shiga ayi dropping dina ke me sabon Housemate, yanxun nan kika gama kakkaresa sai gashi ya shuka maki rashin mutunci, an gaya maki Ajay zai canza halinsa ne" Khaleesat ta taɓe baki ta bude handbag dinta ta ciro waya zata yi ordering ride, har suka rabu da Safiyyah dariya take mata kamar zata shide, ita dai ko tanka ta bata sake yi ba.... Jay na zaune motarsa yana waya da Mami yaga Khaleesat ta sauka daga Uber din da ya ajiyeta, ya bi ta da kallo har ta shiga apartment dinta bata lura da shi ba, Muryar Mami yaji tana ta masa magana, ya ɗan sauke boyayyen ajiyar zuciya a hankali yace "Idan na dawo za mu yi magana Mami it's nothing to be worried about, in less than 3 weeks zan dawo Nigeria in sha Allah" Daga daya bangaren Mami tace "Jawwad kana tunanin da akwai wani abinda zaka tambayeni da zan ki maka ne? Plss tell me what you want, hankalina bazai kwanta har nan da sati uku ba, ko kuma in taho Maryland din ne?" Jay yace "A'a Mami ba sai kin zo, ba wani abu bane da zaki damu kanki, idan na dawo za mu yi magana" Mami dai tayi shiru, alamar bata gamsu ba. Khaleesat na shiga apartment dinta ta ji alamar Ajay yana kitchen, ta karasa kitchen din ta tsaya a bakin kofa tana kallonsa fuska daure tace "Ba sai kace min kar in dawo bazan same ka a wajen ba..." Ba tare da ya kalleta ba yana slicing fruits yace "Saboda ina tsoron ki" Tace "Amma ai da bazan koma wajen ba har ruwa ya doke ni...." Sai a sannan ya juya ya kalleta, lokaci daya taga ya ajiye wukan hannunsa da sauri yana kallon finger dinsa, dariya tayi tace "Dama wa yace maka haka ake slicing abu da wuka?" Ko kallonta bai yi ba har sannan yana kallon finger dinsa, Ita ma dai kallon hannun take don bata ga jini ba, can ta karasa kitchen din tace "Ai ba haka ake yanke hannu ba, idan da gaske ne jini za a fara gani yana zuba" Tana fadin haka ta bude tap ta wanke hannunta da liquid wash ta dau karamin towel ta goge hannun sannan ta karasa kusa da fruit din da yake slicing ta dau wukan tace "Let me just show you how to handle a knife in case of next time" Slicing fruit din ta fara, ya wani kalleta daga sama har kasa, can ta daga kai ta kallesa tace "Hope you are watching how i am using the knife?" Juyawa taga yayi ya nufi fridge ita dai ta ci gaba da yanka fruit din tana kallonsa, wasu fruits din ya debo alamar ya bar mata wa encan din, bata san lkcn da ta jefar da wukar hannunta a gigice ba jin wani sharp pain sai ga jini ya biyo baya, ya juya ya kalleta at first ta so ta daure, kawai taji ya fara dariya irin ta mugunta da yake ma Jay, sai a sannan ta fashe da kuka sosai, ta juya zata fita daga kitchen din ya tura kofa yace "Waye zaki zubar ma jini a parlor, jira ya gama tsiyayewa a nan kar ki bata ma mutane gida" Kuka kawai take zata fita ya tsaya bakin kofar yaki barin ta fita, sai kuma ya hade rai yace "Baza ki je ki wanke hannun ba" Ta koma jikin bango tana kuka a hankali tana kallon finger dinta da ta gaftare, Yace "Sorry... but that serves you right" Tap din kitchen din ya bude mata, bata ko kallesa ba ta tafi ta fara wanke hannun tana duba how deep the cut is, shima kallon finger din yake don wajen har yayi ja, ya tafi ya bude fridge ya dauko Venegar ya bude ya zuba mata a hannun, wani ihu ta kwala ya bude kofar kitchen din yace "Fita" Fita tayi daga kitchen din tayi ido hudu da Housemate dinta dake zaune parlon yana danna wayarsa, goge idonta tayi a hankali ta nufesa, ta zauna kasan carpet tana kallonsa cikin sanyin murya tace "Good evening" Sai a sannan ya kalleta yace "Evening Halysaah, how are you?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Ya preparation din exams?" Tace "Lafiya lau, yaushe ka zo?" Yace "Just now..." Finger dinta ta nuna masa a hankali tace "I just hurt my self" Yace "Sorry, Allah ya sauwake" Tayi shiru bata sake cewa komai ba, ya ci gaba da danna wayarsa, after some minutes Ajay ya fito daga kitchen din da bowl din fruit Salad da ya zuba ma orange drink da zuma, sau daya ya kalli Jay ya tafi ya zauna ya fara shan fruit salad dinsa ya kunna TV ya kamo tashar kwallo, ta gefen ido Khaleesat ta ɗan kalli Ajay, sai kuma ta kalli Jay that is just pressing his phone, abinda Safiyyah ta ce mata daxu ne ya dawo kanta, lokaci daya jikinta yayi sanyi, after almost 5 mins ta kalli Jay a hankali tace "Should i make the fruit salad for you too?" Jay ya kalleta yace "No i am full Halysaah" Ta sunkuyar da kanta, after a while tace "Ina son zan tafi sama in canza kaya, amma pls kar kace zaka tafi since it's raining, idan na gama zan sauko" Jay ya ɗan yi murmushi yace "Take your time Halysaah" Mikewa tayi ta wuce sama, shi dai Ajay kallon TV kawai yake yana shan fruit salad, sai da Khaleesat ta wuce sama sannan ya kalli Jay yace "Yau bazan kwana a gidan nan ba because i have somewhere important to go, so ur staying in this apartment for today means nothing...." Jay yace "Ka fasa tafiya Nigeria din ne, i tot u said few weeks after i return zaka je" Ajay yace "Me ake yi a Nigeria din? Duk sanda nayi niyyar tafiya ai ba sai ka tuna min ba..." Ko da Khaleesat ta sauko downstairs kusan karfe shidda taga Housemate dinta baya parlon, kallon Ajay tayi tace "Housemate dina fa?" Game dinsa kawai yake without looking at her balle ta saka ran amsa, shiru tayi tana kallonsa kafin ta nufi kitchen, fruits din da take yankawa daxu kafin ta yanke hannu ta duba bata gani ba a kitchen din, ta duba waste bin bata ga alamar fruit din ba, ta sake dawowa parlor tana kallonsa tace "To ina fruit din da nake slicing daxu?" Without looking at her yace "Na zubar" Tace "Amma ban gani a waste bin ba" Yace "Ke kika zuba a waste bin din da zaki gani?" Tace "Ko dai ka shanye ba" Bata jira cewarsa ba ta juya ta koma kitchen din, after some minutes ta fito da bowl din fruit bayan tayi yanda taga yayi da fruit Salad din sa daxu, ya bi ta da wani kallo har ta wuce sama, wayarta ta dauka ta kira Jay, har ya katse bai daga ba, bayan few minutes sai gashi ya biyo kiran, kamar zata yi kuka tace "Shi ne ka tafi bayan nace kar ka tafi" A hankali yace "To in na zauna me zaki bani?" Ta ɗan yi murmushi tace "Abu me dadi mana" Yace "Uhm... Abu me dadi kamar me? Kin san abubuwa masu dadi kala kala ne" Tace "To ai dawowa zaka yi sai in baka" Yace "Salon in zo ki fara sunkuye kai ki ki kallona balle ki ban abu me dadin" Dariya tayi tace "A'a bazan yi haka ba wallahi" Yace "Sure?" Tace "Yeah" Yace "Ohk, bari ayi magrib...." Ta marairaice tace "Nasan ba zuwa zaka yi ba, haka ka min ranan nan" Yana murmushi yace "Zan zo, amma a mota zaki sameni bazan shiga gidan ba" Tace "Toh sai ka zo" Yana katse wayar ta dau fruit salad dinta ta fara sha, sosai yayi mata dadi saboda orange juice din ciki... Wajen karfe takwas kiran Housemate dinta ya shigo wayarta, ta mike daga kan darduma da take zaune ta dau wayar tayi picking ta kai kunne, calmly yace "Ina jiran ki" Ta ɗan yi murmushi tace "To" Katse wayar tayi ta nufi kofa ta fita daga dakin ta sauka downstairs, Ajay dake waya ya bi ta da kallo ta shiga kitchen, gun da Ajay yake ajiye tsadaddun Chocolates dinsa ta bude tayi tsalle ta dauko daya, kiris ya rage ta fadi kasa, ta dai kulle wajen da sauri sannan tayi unwrapping chocolate din ta boye a Veil din jikinta, sannan ta fito daga kitchen din ta nufi kofar parlor zata bude kofa yace "Ke" Juyawa tayi ta kallesa sai kuma ta langwabar da kai tace "Housemate dina ne ke jirana a waje" Yace "Shi yasa kika yi wanka da turare kenan" Ita dai bata ce komai ba ta fita daga parlon ta nufi inda ta hango motar Jay tana tafiya a hankali, kallonta yake har ta iso gun motar ta bude front seat a hankali ta shiga ta zauna, ta ɗan kallesa tana murmushi taga kallonta yake babu ko kiftawa, sauke idonta tayi a hankali tace "Good evening" Yayi kasa da murya yace "Ina abu me dadin?" Murmushi kawai take, after some seconds tace "Close ur eyes" Lumshe idonsa yayi, ta dake ta kamo hannunsa ta saka masa chocolate din sannan ta sake hannun da sauri ta kauda kanta, bude ido yayi yana kallon Chocolate din, sai kuma yace "A'a ni ba Chocolate nake so ba..." Ta ɗan kallesa kamar zata yi kuka tace "Me tsada ne fa" Yace "I appreciate it amma ba shi nake so ba, ni abu me dadin da nake so daban" A hankali tace "To meye shi? Sai in siya maka" a hankali yace "Halysaah nake so" Dariya tayi tana kallonsa tace "To ai ni ba abu me dadi bace" Yayi kasa da murya yace "Wa yace maki?" Tace "Eh mana ga dai su Chocolates da Lollipops" Yana kallonta kasa kasa yace "Duk kin fi su, baza ma a hada ba...." Shiru Khaleesat tayi as if everything is beginning to dawn on her, bata sake yarda ta kallesa ba, shi kuwa kallonta kawai yake, kamar me rada yace "You are not saying anything again" Ta ɗan yi murmushi tana tunanin ta yanda zata yi diverting zancen, da sauri tace "Daxu Safiyyah ke tambayata kai, wai bata ganka ba kwana biyu" Yayi murmushi yace "Why are you diverting the conversation?" Dariya ya bata amma tayi murmushi kawai tace "To ai don kar ku hadu da ita kace ban gaya maka bane" A hankali yace "Kin san yanda nake jin ki a rai day by day kuwa Halysaah? Ina jin kamar idan na rasa ki abu zai iya samu na" Khaleesat ta daga idanuwanta ta kallesa amma ta kasa cewa komai, kamar yanda shi ma yayi shiru yana kallonta yana jin wani sabon sonta na mamayan zuciyarsa, Jinginar da kansa yayi jikin kujerar motar ya lumshe ido. Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/B8DsB9xMdou36YgiMRcSlr Ena kuke masoyan ado da kwalliya,Ena amaran da uwayen gida masu capacity's ,oum eman ta tanadar maku hadaddun jakunkuna, takalma, abaya, dakuma duk wani nau'ika na jewelry's, masu matukar kyau da kuma quality, wani abun armashin shine muna kawo maku Kaya na Yan gayu masu class zakisa kayn mu kije unguwa kidawo batare da kinci karo damai irin Shiba , mekike jira kedai kawai shiga group domin kisami naki a price kalilan🤝😁 HALYSAAH 80 Khaleesat tayi shiru tana kallon Jay da idonsa ke lumshe har na kusan minti uku, after another minute ya bude idonsa a hankali ya kalleta, tayi murmushi tace "Ai na zata bacci ka fara yi" A hankali yace "Eh mana, kuma har da mafarki nayi" Bata san sanda tayi dariya ba tace "Mafarki kuma?" Ya gyada mata kai yana kallonta calmly yace "Yea, i dreamt we got married and made 2 beautiful girls" Dauke kai tayi da sauri tana murmushi, shi ma yana murmushin yace "Yanxu dai ba babu abinda zaki bani kika sa na zo cikin ruwa ko?" Chocolate din hannunta ta mika masa without looking at him, yana murmushi ya amshi chocolate din yana kallo, can ya kalleta yace "Na Ajay kika dauko..." Dariya tayi tace "How did you know?" Ya gyara zama yace "How won't i know, ai nasan Chocolate din da yake ci" Khaleesat tace "Wayo nayi masa na tafi kitchen na dauko bai sani ba" Jay ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "I see, dama kin saba dauka kenan" Tayi er dariya tace "Bayan inda height dina bazai kai ba yake ajiye chocolate din a kitchen, bai san idan nayi tsalle ina iya daukowa ba...." Jay dai kallonta kawai yake babu ko kiftawa, can yace "Naga you are so comfortable together with him, gashi har kun saba ko?" Lkci daya abinda Safiyyah tace mata ya dawo kanta, ta kallesa ta girgiza masa kai da sauri tace "A'a ba haka bane...." Yace "You mean you are not comfortable with him a gidan?" A hankali ta gyada masa kai tana kallonsa, yace "Ohk, akwai wani frnd dina muna PhD under same course, tare suke apartment da cousin sister dinsa, but she just got her apartment recently nan kusa da school, although ba John Hopkins take ba ita, will you mind staying with her during ur exam period tunda apartment dinta kusa yake da school?" Khaleesat tayi shiru tana kallonsa kamar yanda yake kallonta yana jiran jin me zata ce, sauke idonta tayi, yace "If you are not okay with that kawai ki gaya min, kar ki ji komai" A hankali tace "I am not okay with it..." Yana kallonta yace "Why?" Ita dai bata yarda sun sake hada ido ba, she wasn't expecting him to ask her why she is not comfortable, ta ma rasa me zata ce masa, taji yace "I am listening Halysaah" A hankali tace "I.... i don't want to inconvenience her, kuma kullum Safiyyah zata dinga zuwa wajena muna karatu tare, and you know how loud Safiyyah can be, kaga kar mu takura ta" Jay dai kallonta kawai yake, kamar bazai ce komai ba sai kuma ya ɗan yi murmushi yace "Yarinyar bata da matsala ko kadan, amma don kar mu yi inconveniencing dinta we can give her half of the house rent since you won't be staying long, just for 2 weeks ne, kinga baza ki ga kinyi inconveniencing dinta ba ke da Safiyyah, amma in kin fi son Apartment din ki together with Ajay, it's fine" Da sauri Khaleesat ta kallesa tace "A'a shikenan, zan koma can din, ya ma fi hakan" Yace "Are you sure?" Ta gyada masa kai tana kallonsa, yace "Ohk, i will speak to Ayo about it this night sai yayi ma cousin din tasa magana, kafin ma ki koma can after speaking to the girl zan fara kai ki, ki ga apartment din gobe" A hankali tace "Allah ya kai mu" Ɗan murmushi tayi yace "Za ki koma ciki ki ci gaba da karatu?" Tace "Na ma yi karatun, kawai ina son inyi bacci da wuri ne" Yace "Are you going to school tomorrow?" Ta gyada masa kai tace "Za mu yi revision da wasu coursemate din mu" A hankali yace "Alright Halysaah" Tayi murmushi tana kallon chocolate din hannunsa tace "To bani in shanye tunda baza ka sha ba" Ya kai mata chocolate din baki yace "Bude bakin" Rufe fuskarta tayi tana murmushi sai kuma ta bude baki ya saka mata chocolate din yana kallonta, murya can kasa yace "I love you so much Halysaah" Ta ɗan juya tana murmushi, yace "Is that the reply?" Kasa kallonsa tayi, a hankali tace "Ni kunya nake ji" Ya ɗan yi murmushi yace "Za ki san kunya..." Ita dai taki juyowa tana murmushi, Yace "Good night Halysaah, Sleep like a baby..." Tana murmushi a hankali tace "Thank you so much" Shi dai kallonta kawai yake baya ko kiftawa, ta bude motar ta sauka, ya bi ta da kallo har ta isa kofar apartment din, tana murda kofar taji a kulle, knocking kofar tayi ta ɗan jira amma shiru, ta sake knocking nan ma taji shiru, sai da ta kwankwasa kofar kusan sau biyar ba a bude ba, ta juya ta kalli Housemate dinta don bai tafi kuma duk yana kallonta, ta kalli kofar ta daure fuska tace "Ni ka bude min kofa baka san akwai sanyi ba, wallahi nasan kana parlon" Shi dai Housemate kallonta kawai yake, har zai kirata su tafi can gidansu sai kuma kawai ya bude motar yana rike da makullin apartment din ya karasa ya bude mata kofar, Khaleesat da tasan akwai makulli wajensa da tunda tayi knocking sau daya bazata sake ba zata tafi ta amso key a wajensa, bayan Jay ya bude kofar ya kalleta yace "Good night" Tayi murmushi tace "Allah ya tashe mu lafiya" Juyawa yayi ya koma gun motarsa ta bude kofar ta shiga sannan ta rufe tana kallon Ajay dake zaune parlon yana shan parfait yana kallon American movie, ta hade rai tace "Shi ne kaki ka bude min kofa kana ji ina knocking?" Ko kallon inda take tsaye bai yi ba, hakan yasa ta tura baki tayi wucewarta sama kamar zata tashi, ya bi ta da wani kallo..... Washegari tun karfe bakwai da rabi Safiyyan ta dinga doka ma Khaleesat waya, Khaleesat dai bata biye ta ba, ta gama shiryawa wajen karfe goma ta sauko downstairs, as usual Ajay ya gyara ko ina na parlon, every where is just sparkling, ta shiga kitchen tana kallon lafiyayyen Salad din da ya hada, plate ta dauko ta fara diba da sauri sauri ta bar kitchen din kafin ya shigo, kawai taji muryarsa a bayanta yana tsaye bakin kofar kitchen din yace "Mayar min kar ki sha mari...." Juyawa tayi ta kallesa, sai kuma ta langwabar da kai a hankali tace "Kadan fa dama zan diba, i am going to school" Ganin kallon da yake mata ta juye salad din ta dungurar da plate din hannunta ta bi gefensa ta fice daga kitchen din ya bi ta da kallo yace "Ba abinda kika iya sai ki fesa turare ki dau handbag ki ce kin tafi school, what is the use of ur hands da baza kiyi naki salad din ba, common gyaran gida baki iya ba, sai dai kiyi wanka ki fesa turare" Khaleesat dai ko kallonsa bata yi ba ta tafi sama ta dauko handbag dinta da waya ta sauko downstairs ta fice daga gidan, a nan waje ta jira har Lyft dinta ya karaso sannan ta shiga zuwa makaranta. Safiyyah na zaune tana ta jiran Khaleesat a school din don tun karfe bakwai da rabi ta shigo, tana hangota ta fara washe baki Khaleesat ta zauna gefenta tace "Toh meye na shigowa school da sassafe" Safiyyah tace "Kin mance apartment din ki za mu koma tare ne, ko yana gida ne yau?" Khaleesat tace "Ya ma shirya zai fita shi ma" Safiyyah na murmushi ta makale handbag dinta a kafada tace "Yi mana order din ride mu koma gidan da sauri" A hankali Khaleesat tace "kinsan me Sophie?" Safiyyah ta wani kalleta tace "Me?? Ni fa in kika ga ban je na buga PS5 yau ba to Ajay ne ya koreni, bayan mun gama tsarinmu tun jiya yanxu kuma kina wani ce min nasan me, ba a abun arziki dake din nan dama" Khaleesat tace "A'a ba shi ba fa" Safiyyah ta gyara zama tace "Aiho, to menene?" Khaleesat bata boye ma Safiyyah duk yanda suka yi da Housemate dinta daren jiya ba, Safiyyah ta bude baki tana kallonta, can ta ajiye jakarta a gefe tace "A'a wannan karan Housemate ya zo da bidi'a, sai kika ce masa me ke kuma? To wai ma menene don kina zaune da ɗan uwansa na jini a gida daya da har zai dinga yi kamar kina zaune da wani bare? Wanda a class irin na Ajay ma ko kallo nasan baki ishesa a gidan ba in ba ke kika shiga harkarsa ba, me yasa Housemate yake haka? Gaskiya kice masa ke a'a kin fi son Apartment din ki, kuma da Ajay ne a shoe din Jay wallahi ko a jikinsa, insecurity ne kawai ke azabtar da Jay da bakin kishi, tun yaushe aka dena yayin kishi kowa ya waye yanxu, wallahi kice masa ke ba inda zaki je, da abinda zai saka ma Ajay kenan da ya yarda ya zauna yake ta masa gadin ki? Ke kuma maimakon kice masa kin fi gane apartment dinki akan ko ina shine kika masa shiru?" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "To na rasa me zan ce masa ne, kuma bana son in bata masa rai" Safiyyah tace "Ai ko sai dai ran nan nasa ya baci, ni da nake murna ga ps5 a gida sai yanda muka yi da shi, shi ne Housemate zai kirkiro wannan abu kawai don ya bata ma Ajay rai ya kwashe PS5 dinsa ya bar gidan? Shi fa Ajay mutum ne da ba ruwansa ba sa wa ba hanawa tuni na gano haka, A'a gaskiya Ajay na hakuri da Housemate dinki, balle ma me Ajay zai yi da budurwarsa sai kace a garin gaɓa gaɓa? Jay ya canza hali gaskiya, da kyar wannan ya bari ki gama karatun bai je an daura auren ba idan muka koma hutu bayan exams, irin yanda Abdul yayi haka shi ma zai yi sai dai ki dawo Amurka da aurensa a kanki..." Ita dai Khaleesat tayi shiru don bata ma san me zata ce ba, Safiyyah tace "Ki tashi mu tafi ko ki ban makulli ni inyi tafiyata, da Ajayn zai yarda ai har ni komawa gidan zanyi in ce ma Ya Musty a makaranta muke kwana saboda jarabawa" Khaleesat tace "Wai fa yau yace zai kai ni gidan in gani" Safiyyah ta hade rai tace "Ki ce masa baki da lokaci muna ta revision a school kuma ba da wuri za mu gama ba saboda course ne me uban yawa ga exam ranan Monday, haba ya fiye fitina wannan Housemate din naki wallahi, Ajay ya fi sa saukin kai shi sa tamu ta zo daya da shi tun asali" A haka Safiyyah ta ja Khaleesat suka koma apartment dinta, banda murmushi babu abinda Safiyyah take bayan ta sauka a Lyft taga babu motar Ajay a parking space... Khaleesat da Safiyyah sun sakankance suna ta game tun shigowarsu apartment din ko wacce rike da Wireless Controller a hannu, Safiyyah sai nishadi take abun nema ya samu bakinta har kunne, wayar Khaleesat ne ya fara vibrate a jaka, Safiyyah tayi pausing game din da suke, Khaleesat ta ciro wayar a jaka ta kalli Safiyyah tace "Shi ne yake kirana" Safiyyah tace "Housemate din?" Khaleesat ta gyada mata kai, Safiyyah ta hade rai tace "Ɗaga kice masa muna ta jin yunwa mun dawo apartment dinki muna girki yanxu" Khaleesat tace "Toh" Picking call din tayi ta kai kunne a hankali tayi masa sallama, Safiyyah ta mike ta tafi kitchen don yunwa ma take ji, hadadden Jollof rice ta gani da chicken lap har biyu, ta juyo masu jollof din da chicken laps biyu a plate ta saka cokali ta bude fridge ta debi soft drink biyu ta dawo parlon, bude baki Khaleesat tayi tana kallonta, sai kuma ta fara dariya tace "Wallahi ba ruwana na Ajay ne, ni ban yi girki ba, gwara ki maida masa abincinsa" Safiyyah ta zauna tace "Ke ya fa ci ya rage ne, raguwa ne wannan..." Khaleesat tana kallon abincin tace "A ina kika gani?" Safiyyah ta fara cin abincin tace "A gantale a kitchen mana, alamar ya koshi" lumshe ido Safiyyah tayi tace "Ke kin ji dadin abincin kuwa? Wallahi wannan matarsa ta huta, ko ince ya huta, duk ranan da matarsa ke jin iskanci taki masa girki ya girka kayansa, gaskiya wannan yarima ne me capacity, uwa uba ga tsafta" Khaleesat ta dau spoon ta debi abincin ta kai baki, sosai ya mata dadi ita ma, ko wa ya koya masa girki haka oho, Safiyyah na cika baki da shinkafa tace "Kin gaya ma Housemate din abinda nace maki?" Khaleesat ta gyada mata kai alamar ta gaya masa, tass suka cinye abincin suka ci gaba da game dinsu dama gashi duk ba sallah suke ba, Wajen karfe biyu da rabi aka bude kofar parlon, daga Safiyyah har Khaleesat suka juya da sauri, Tsaye Ajay yayi a bakin kofar parlon yana kallonsu, a hankali Safiyyah ta dora ma Khaleesat Game controller din hannunta a kan cinyarta, cikin dubara ta matsar da plate din abincin da suka ci kusa da Khaleesat. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah, ur evidence* 07087865788 HALYSAAH PAGE 81.... Khaleesat ta langwabar da kai tana kallon Ajay a hankali tace “Good evening” Ya kusa 30 seconds tsaye yana kallonsu ya ki cewa komai, Safiyyah ta jawo handbag dinta a hankali ta rataye a kafada tana kallon Khaleesat murya kasa kasa tace “Kar Ya Musty ya fara kirana ni zan tafi gida” A tare suka bi Ajay da kallo ganin ya rufe kofar parlon ya cire makullinsa ya nufi staircase ya wuce sama, Safiyyah ta maida handbag dinta ta ajiye gefe tana washe baki tace “Ba daxu daxun nan na gama ce shi da matsala ba, maki ba ta cinye sannan ta ajiye ta dau Controller din da ta ajiye kan kafar Khaleesat zata ci gaba da yame din tana cewa “Ai ba abinda zai ce mana wallahi, yana da saukin kai” Khaleesat tayi dariya tace “Kika san me yaje daukowa a sama, ni dai ba ruwana wallahi…” Tana fadin haka ta mike tsaye tana dariya, Safiyyah ta kara jawo handbag dinta da ta ajiye ta makala a hammata ta mike tsaye ita ma tace “Mu je ki bude min kofa ni dai kafin Ya Mustapha ya fara nemana” Khaleesat ta dafa kujera ta dinga dariya ba kakkautawa, Safiyyah ta hade rai tace “Meye haka don Allah, ina makullin gidan yake ni dai ki bude min in wuce” Ganin Khaleesat taki kulata sai dariya take babbakawa, Safiyyah ta fixgo handbag din Khaleesat ta bude ko zata ga makullin gidan a ciki amma bata gani ba, tace “Ni don Allah meye abun dariya, ki bude min kofa in tafi kar yayana ya fara nemana mana” Khaleesat tace “Ki tafi ina? Ai wallahi babu inda zaki je ki bar ni a gidan nan, ba ke kika ce mu zo muyi game ba” Safiyyah tace “Da nace mu zo daxi daxun nan na gama ce maki ba shi da matsala ba, wallahi dama nasan bazai ce mana komai ba don kowa yasan PS da shiga rai, ai ba kowa ne fitinanne ba” Plate din abincin da suka ci ta dauka la kankare sauran shinkafar jiki ta cinye sannan ta ajiye ta dau Controller din da ta ajiye kan kafar Khaleesat zata ci gaba da game din tana cewa “Ai ba abinda zai ce mana wallahi, yana da saukin kai” Khaleesat tayi dariya tace “Kika san me yaje daukowa a sama, ni dai ba ruwana wallahi…” Tana fadin haka ta mike tsaye tana dariya, Safiyyah ta kara jawo handbag dinta da ta ajiye ta makala a hammata ta mike tsaye ita ma tace “Mu je ki bude min kofa ni dai kafin Ya Mustapha ya fara nemana” Khaleesat ta dafa kujera ta dinga dariya ba kakkautawa, Safiyyah ta hade rai tace “Meye haka don Ailah, ina makullin gidan yake ni dai ki bude min in wuce” Ganin Khaleesat taki kulata sai dariya take babbakawa, Safiyyah ta fixgo handbag din Khaleesat ta bude ko zata ga makullin gidan a ciki amma bata gani ba, ana ciki toco “Mi don Alich hun dariva bi hudo mir bofo in tafikika ce mu zo muyi ga ba” Safiyyah tace “Da nace mu zo muyi game tunda kin san baya so ba sai kice min A’a ba, ta yaya ni zan san baya so a taba masa kayansa, kin ga kar raina ya baci ki bude min kofa in tafi gida, wannan wani irin iskanci ne ana magana kina dariya” Dariya kawai Khaleesat take yi kamar zata shide, ran Safiyyah yayi mugun baci ta kankance ido tana kallon Khaleesat, Ikci Ikci take kallon sama kar Ajay ya sauko ya riske su, a fusace tace “Wallahi ban san haka kike ba da bazan biyo ki ba, ina zaman zamana kika ce min akwai Ps5 a gidan nan, in baki gaya min ba ta yaya zan sani, nayi da na sanin biye ki wallahi” Shiru tayi ganin Ajay na saukowa downstairs, Khaleesat ta hadiye dariyar da take tana kallonsa, Safiyyah ta sha kunu bayan ta koma gefen Khaleesat ta tsaya kamar masu jiran hukunci, shi dai ko kallonsu bai yi ba ya nufi kofa ya bude ya fita, da sauri Khaleesat ta tafi tana lekasa ta windon parlor, motarsa taga ya shiga ya tafi, ta dinga kyalkyala dariya tana kallon buge ko zata ga makullin gidan a ciki amma bata gani ba, tace “Ni dori Allah meye abun dariya, ki bude min kofa in tafi kar yayana ya fara nemana mana” Khaleesat tace “Ki tafi Ina? Al wallahi babu inda zaki je ki bar ni a gidan nan, ba ke kika ce mu zo muyi game ba” Safiyyah tace “Da nace mu zo muyi game tunda kin san baya so ba sal kice min A’a ba, ta yaya nı zan san baya so a taba masa kayansa, kin ga kar raina ya baci ki bude min kofa in tafi gida, wannan wani irin iskanci ne ana magana kina dariya” Dariya kawai Khaleesat take yi kamar zata shide, ran Safiyyah yayi mugun baci ta kankance ido tana kallon Khaleesat, Ikci Ikci take kallon sama kar Ajay ya sauko ya riske su, a fusace tace “Wallahi ban san haka kike ba da bazan biyo ki ba, ina zaman zamana kika ce min akwal Ps5 a gidan nan, in baki gaya min ba ta yaya zan sani, nayi da na sanin biye ki wallahi” Shiru tayi ganin Ajay na saukowa downstairs, Khaleesat ta hadiye dariyar da take tana kallonsa, Safiyyah ta sha kunu bayan ta kankoma gefen Khaleesat ta tsava kamar masu iiran hukunci 100taga ya shiga ya tafi, ta dinga kyalkyala dariya tana kallon Safiyyah dake maka makale jikin windown ita ma tana lekansa, bata ma san sanda ta zo jikin windan ba, Safiyyah ta washe baki tace “Atoh ba nace maki bazai ce mana komai ba amma duk kika bi kika firgice, ai Ajay mutum ne, shi dai kar ka masa rashin kunya kawai” Bata jira cewar Khaleesat ba ta koma gun game din, Khaleesat tace “Ba gida kika ce zaki tafi ba Ya Mustapha na kiran ki” Safiyyah taki tanka ta tana gyara zama ta ci gaba da game dinta, Khaleesat ta dau plate din da suka ci abinci ta kai kitchen, bude baki tayi ganin ashe duka abincin Safiyyah ta juyo masu suka cinye, gashi ya dawo ya tarar suna masa game tasan kuma dole sai yayi mata magana ko ba yau ba, ga kuma an cinye masa abinci, jingina tayi jikin cabinet din kitchen din, ko dai kawai ta dafa masa wani abincin ai ba sani zai yi ba, fara harhada ingredients din da zata yi girkin tayi, sai ga Safiyyah ta shigo kitchen din tace “Don Allah ki zo mu ci gaba mana, tunda bai ce mana komai ba alamar va bamu permission kenan ai.daryjar da take tana kallonsa, Safiyyah ta sha kunu bayan ta koma gefen Khaleesat ta tsaya kamar masu jiran hukunci, shi dai ko kallonsu bai yi ba ya nufi kofa ya bude ya fita, da sauri Khaleesat ta tafi tana lekasa ta windon parlor, motarsa taga ya shiga ya tafi, ta dinga kyalkyala dariya tana kallon Safiyyah dake makale jikin windown ita ma tana lekansa, bata ma san sanda ta zo jikin windan ba, Safiyyah ta washe baki tace “Atoh ba nace maki bazai ce mana komai ba amma duk kika bi kika firgice, ai Ajay mutum ne, shi dai kar ka masa rashin kunya kawai” Bata jira cewar Khaleesat ba ta koma gun game din, Khaleesat tace “Ba gida kika ce zaki tafi ba Ya Mustapha na kiran ki” Safiyyah taki tanka ta tana gyara zama ta ci gaba da game dinta, Khaleesat ta dau plate din da suka ci abinci ta kai kitchen, bude baki tayi ganin ashe duka abincin Safiyyah ta juyo masu suka cinye, gashi ya dawo ya tarar suna masa game tasan kuma dole sai yayi mata magana ko ba yau ba, ga kuma an cinye masa chinni inaine tavi ilkin cabinet din bitahan din bin dai kaunkitchen din tace “Don Allah ki zo mu ci gaba mana, tunda bai ce mana komai ba alamar ya bamu permission kenan ai, ke dai kin fiye tsoro” Khaleesat tace “Sophie ashe duka kika juyo abincin, yanxu idan ya kara dawowa yaga babu wani abincin fa?” Safiyyah tace “Ba sai kice masa Housemate ne ya zo ya ci ba, ai bazai san mu muka ci ba” Khaleesat ta wani kalleta, can tace “Kawai sai in ma Housemate dina sharri, ni dai wani zan dafa masa kawai” Safiyyah tace “To ki dafa har mu don ban koshi ba dama, kuma yayi dadi irin nasa don Allah” Daga haka ta koma parlor ta saka game din ita kadai tana yi, har kusan karfe biyar na yamma Safiyyah na bakin PS a zaune tana ta yi, Khaleesat tuni ta gama girkin da take har da grilling masa chicken lap biyu yanda dai yayi sannan ta kira Safiyyah tana tambayarta yanda ta ga abincin a kitchen, Safiyyah ta jera masa yanda taga ya bar kayansa sannan suka koma suka ci gaba da game…. Wajon karfe shidda game din ya dauke ya shiga wani waje daban, sai yayi mata magana ko ba yau ba, ga kuma an cinye masa abinci, jingina tayi jikin cabinet din kitchen din, ko dai kawai ta cafa masa wani abincin ai ba sani zai yi ba, fara harhada ingredients din da zata yi girkin tayi, sai ga Safiyyah ta shigo kitchen din tace “Don Allah ki zo mu ci gaba mana, tunda bai ce mana komai ba alamar ya bamu permission kenan ai, ke dai kin fiye tsoro” Khaleesat tace “Sophie ashe duka kika juyo abincin, yanxu idan ya kara dawowa yaga babu wani abincin fa?” Safiyyah tace “Ba sai kice masa Housemate ne ya zo ya ci ba, al bazai san mu muka ci ba” Khaleesat ta wani kalleta, can tace “Kawai sai in ma Housemate dina sharri, ni dai wani zan dafa masa kawai” Safiyyah tace “To ki dafa har mu don ban koshi ba dama, kuma yayi dadi irin nasa don Allah” Daga haka ta koma parlor ta saka game din ita kadai tana yi, har kusan karfe biyar na yamma Safiyyah na bakin PS a zaune tana ta yi, Khaleesat tuni ta gama girkin da take har da grilling masa chicken lap biyu yanda dai yayi cannan ta kira Safivvah tana tamhavarta vanda to na ahincinn shidda game din ya dauke ya shiga wani waje daban, kokarin gyarawa Safiyya ta dinga yi amma yaki, Khaleesat tace “Dama sai da nace mu bar game din haka kika ki ji” Safiyyah taki tanka Khaleesat sai kokarin gyarawa take, garin gyara kawai ya dauke gaba daya, Khaleesat ta bude baki tana kallonta, Safiyyah ta ajiye controller din hannunta ta jawo handbag dinta ta makala a kafada tace “Kilan ma Ya Musty na ta kirana wayar na silent” Kokarin mikewa tsaye take Khaleesat ta rikota tace “Ban gane Ya Mustapha na ta kiran ki ba, waye zai gyara masa kina ganin abu ya dauke gaba daya?” Safiyyah tace “To ni bakanikin PS5 ce, ki kashe socket din kawai ki wuce sama ni kuma in tafi gida, ai mu ma bamu san me ya samu abun ba ya dauke, kilan ya dau zafi ne” Zaro ido Khaleesat tayi jin karan mota a garage, Safiyyah ma ta gwale ido tana kallonta, mikewa Khaleesat tayi ta tafi window da sauri tana leka garage, ganin motar Ajay ta dawo da sauri tace “Wallahi shi ne ya dawo, gashi kin Lalata masa ahu Safiwah ta zaro idu tace “Ran nane na da take har da grilling masa chicken lap biyu yanda dai yayi sannan ta kira Safiyyah tana tambayarta yanda ta ga abincin a kitchen, Safiyyah ta jera masa yanda taga ya bar kayansa sannan suka koma suka ci gaba da game…. Wajen karfe shidda game din ya dauke ya shiga wani waje daban, kokarin gyarawa Safiyya ta dinga yi amma yaki, Khaleesat tace “Dama sai da nace mu bar game din haka kika ki ji” Safiyyah taki tanka Khaleesat sai kokarin gyarawa take, garin gyara kawai ya dauke gaba daya, Khaleesat ta bude baki tana kallonta, Safiyyah ta ajiye controller din hannunta ta jawo handbag dinta ta makala a kafada tace “Kilan ma Ya Musty na ta kirana wayar na silent” Kokarin mikewa tsaye take Khaleesat ta rikota tace “Ban gane Ya Mustapha na ta kiran ki ba, waye zai gyara masa kina ganin abu ya dauke gaba daya?” Safiyyah tace “To ni bakanikin PS5 ce, ki kashe socket din kawai ki wuce sama ni kuma in tafi gida, ai mu ma bamu san me ya samu abun ba ya dauke, kilan ya dau zafine” Zaro ido Khaleesat tavi iin karan mota a garaneAjay ta dawo da sauri tace “Wallahi shi ne ya dawo, gashi kin lalata masa abu…” Safiyyah ta zara ido tace “Ban gane na lalata ba? Ni kadai nake game din? Me yasa bakya tsoron Allah Khaleesat” Cikin few seconds Khaleesat ta kashe komai ta mayar masa da controller dinsa inda yake ajiyewa, ta mayar da throw pillows dake kasan carpet zuwa kan kujera, tana juyawa taga Safiyyan har ta haura sama, ta bi bayanta da sauri suka shige dakinta, Khaleesat ta dinga kyalikyala dariya har da rike ciki, Safiyyah ta hade rai tace “To wai meye abun dariya? Ke abinda ya kamata ayi dariya ba shi kike ma dariya ba sai wanda ba na dariya ba, yanxu meye abun dariya don Allah a nan, ni ban ma san yamma tayi haka ba ai da tuntuni na tafi gidanmu….” Khaleesat dai bata fasa dariyar da take ba, suka ji ya bude kofar daya daga dakunan dake sama, Safiyyah na jin haka ta bude kofar dakin Khaleesat a hankali ta fice, kafin Khaleesat ta fito har Safiyyah ta bar apartment din gaba daya ta mike can karshen lavi tana vi tana hadawa da quin Khaleesat ta kasa bamu san me ya samu abun ba ya dauke, kilan ya dau zafi rie” Zaro ido Khaleesat tayi jin karan mota a garage, Salyyah ma ta gwale ido tana kallonta, mikewa Khaleesat tayi ta tafi window da sauri tana leka garage, ganin motar Ajay ta dawo da sauri tace “Wallahi shi ne ya dawo, gashi kin lalata masa abu…” Safiyyah ta zaro ido tace “Ban gane na lalata ba? Ni kadai nake game din? Me yasa bakya tsoron Allah Khaleesat” Cikin few seconds Khaleesat ta kashe komai ta mayar masa da controller dinsa inda yake ajiyewa, ta mayar da throw pillows dake kasan carpet zuwa kan kujera, tana juyawa taga Safiyyan har ta haura sama, ta bi bayanta da sauri suka shige dakinta, Khaleesat ta dinga kyalkyala dariya har da rike ciki, Safiyyah ta hade rai tace “To wai meye abun dariya? Ke abinda ya kamata ayi dariya ba shi kike ma dariya ba sai wanda ba na dariya ba, yarıxu meye abun dariya don Allah a nan, ni ban ma san yamma tayi haka ba ai da tuntuni na tafi tafi hoto foon dariune do tako Khaleesat dai cute li va bude unter downtabaidan…. fito har Safiyyah ta bar apartment din gaba daya ta mike cankarshen layi tana yi tana hadawa de gudu. Khaleesat ta kasa dena dariya ta dawo cikin apartment din ta kulle kofar ta wuce sama ta shige dakinta don kar ma ta hadu da shi. Karfe tara saura Khaleesat ta bude kofar dakinta a hankali ta fito corridor tana leka downstairs don yunwa take ji, zaune ta gansa a parlor yana online game, ta sauko downstairs ganin ya gyara game din da suka rikitar, plate din abincin da ya ci ta kalla, saura kadan tayi dariyar da bata yi niyya ba, ga dai shi ya ci abincin da ta girka yau, kitchen ta nufa tana kallonsa, shi dai ko kallonta bai yi ba game dinsa kawai yake, ta duba sauran abincin da ya rage a kitchen din sai kuma ta fito tana kallonsa tace “Zan iya daukan sauran abincin?” Ba tare da ya kalleta ba yace “Da can tambayata kike kafin ki dauka, so you can steal it as usual ai kin saba” Juyawa tayi ta koma kitchen din ta juyo sauran abincin sannan ta fito, zaunawa tayi a bakin stairs tana cin abincin tana kallon como din da uske ul house to come cin shincin to har plato Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/B8DsB9xMdou36YgiMRcSlr Ena kuke masoyan ado da kwalliya,Ena amaran da uwayen gida masu capacity's ,oum eman ta tanadar maku hadaddun jakunkuna, takalma, abaya, dakuma duk wani nau'ika na jewelry's, masu matukar kyau da kuma quality, wani abun armashin shine muna kawo maku Kaya na Yan gayu masu class zakisa kayn mu kije unguwa kidawo batare da kinci karo damai irin Shiba , mekike jira kedai kawai shiga group domin kisami naki a price kalilan🤝😁 HALYSAAH 81 Khaleesat ta langwabar da kai tana kallon Ajay a hankali tace "Good evening" Ya kusa 30 seconds tsaye yana kallonsu ya ki cewa komai, Safiyyah ta jawo handbag dinta a hankali ta rataye a kafada tana kallon Khaleesat murya kasa kasa tace "Kar Ya Musty ya fara kirana ni zan tafi gida" A tare suka bi Ajay da kallo ganin ya rufe kofar parlon ya cire makullinsa ya nufi staircase ya wuce sama, Safiyyah ta maida handbag dinta ta ajiye gefe tana washe baki tace "Ba daxu daxun nan na gama ce maki ba shi da matsala ba, wallahi dama nasan bazai ce mana komai ba don kowa yasan PS da shiga rai, ai ba kowa ne fitinanne ba" Plate din abincin da suka ci ta dauka ta kankare sauran shinkafar jiki ta cinye sannan ta ajiye ta dau Controller din da ta ajiye kan kafar Khaleesat zata ci gaba da game din tana cewa "Ai ba abinda zai ce mana wallahi, yana da saukin kai" Khaleesat tayi dariya tace "Kika san me yaje daukowa a sama, ni dai ba ruwana wallahi..." Tana fadin haka ta mike tsaye tana dariya, Safiyyah ta kara jawo handbag dinta da ta ajiye ta makala a hammata ta mike tsaye ita ma tace "Mu je ki bude min kofa ni dai kafin Ya Mustapha ya fara nemana" Khaleesat ta dafa kujera ta dinga dariya ba kakkautawa, Safiyyah ta hade rai tace "Meye haka don Allah, ina makullin gidan yake ni dai ki bude min in wuce" Ganin Khaleesat taki kulata sai dariya take baɓɓakawa, Safiyyah ta fixgo handbag din Khaleesat ta bude ko zata ga makullin gidan a ciki amma bata gani ba, tace "Ni don Allah meye abun dariya, ki bude min kofa in tafi kar yayana ya fara nemana mana" Khaleesat tace "Ki tafi ina? Ai wallahi babu inda zaki je ki bar ni a gidan nan, ba ke kika ce mu zo muyi game ba" Safiyyah tace "Da nace mu zo muyi game tunda kin san baya so ba sai kice min A'a ba, ta yaya ni zan san baya so a taɓa masa kayansa, kin ga kar raina ya baci ki bude min kofa in tafi gida, wannan wani irin iskanci ne ana magana kina dariya" Dariya kawai Khaleesat take yi kamar zata shide, ran Safiyyah yayi mugun baci ta kankance ido tana kallon Khaleesat, lkci lkci take kallon sama kar Ajay ya sauko ya riske su, a fusace tace "Wallahi ban san haka kike ba da bazan biyo ki ba, ina zaman zamana kika ce min akwai Ps5 a gidan nan, in baki gaya min ba ta yaya zan sani, nayi da na sanin biye ki wallahi" Shiru tayi ganin Ajay na saukowa downstairs, Khaleesat ta hadiye dariyar da take tana kallonsa, Safiyyah ta sha kunu bayan ta koma gefen Khaleesat ta tsaya kamar masu jiran hukunci, shi dai ko kallonsu bai yi ba ya nufi kofa ya bude ya fita, da sauri Khaleesat ta tafi tana lekasa ta windon parlor, motarsa taga ya shiga ya tafi, ta dinga kyalkyala dariya tana kallon Safiyyah dake makale jikin windown ita ma tana lekansa, bata ma san sanda ta zo jikin windan ba, Safiyyah ta washe baki tace "Atoh ba nace maki bazai ce mana komai ba amma duk kika bi kika firgice, ai Ajay mutum ne, shi dai kar ka masa rashin kunya kawai" Bata jira cewar Khaleesat ba ta koma gun game din, Khaleesat tace "Ba gida kika ce zaki tafi ba Ya Mustapha na kiran ki" Safiyyah taki tanka ta tana gyara zama ta ci gaba da game dinta, Khaleesat ta dau plate din da suka ci abinci ta kai kitchen, bude baki tayi ganin ashe duka abincin Safiyyah ta juyo masu suka cinye, gashi ya dawo ya tarar suna masa game tasan kuma dole sai yayi mata magana ko ba yau ba, ga kuma an cinye masa abinci, jingina tayi jikin cabinet din kitchen din, ko dai kawai ta dafa masa wani abincin ai ba sani zai yi ba, fara harhada ingredients din da zata yi girkin tayi, sai ga Safiyyah ta shigo kitchen din tace "Don Allah ki zo mu ci gaba mana, tunda bai ce mana komai ba alamar ya bamu permission kenan ai, ke dai kin fiye tsoro" Khaleesat tace "Sophie ashe duka kika juyo abincin, yanxu idan ya kara dawowa yaga babu wani abincin fa?" Safiyyah tace "Ba sai kice masa Housemate ne ya zo ya ci ba, ai bazai san mu muka ci ba" Khaleesat ta wani kalleta, can tace "Kawai sai in ma Housemate dina sharri, ni dai wani zan dafa masa kawai" Safiyyah tace "To ki dafa har mu don ban koshi ba dama, kuma yayi dadi irin nasa don Allah" Daga haka ta koma parlor ta saka game din ita kadai tana yi, har kusan karfe biyar na yamma Safiyyah na bakin PS a zaune tana ta yi, Khaleesat tuni ta gama girkin da take har da grilling masa chicken lap biyu yanda dai yayi sannan ta kira Safiyyah tana tambayarta yanda ta ga abincin a kitchen, Safiyyah ta jera masa yanda taga ya bar kayansa sannan suka koma suka ci gaba da game.... Wajen karfe shidda game din ya dauke ya shiga wani waje daban, kokarin gyarawa Safiyya ta dinga yi amma yaki, Khaleesat tace "Dama sai da nace mu bar game din haka kika ki ji" Safiyyah taki tanka Khaleesat sai kokarin gyarawa take, garin gyara kawai ya dauke gaba daya, Khaleesat ta bude baki tana kallonta, Safiyyah ta ajiye controller din hannunta ta jawo handbag dinta ta makala a kafada tace "Kilan ma Ya Musty na ta kirana wayar na silent" Kokarin mikewa tsaye take Khaleesat ta rikota tace "Ban gane Ya Mustapha na ta kiran ki ba, waye zai gyara masa kina ganin abu ya dauke gaba daya?" Safiyyah tace "To ni bakanikin PS5 ce, ki kashe socket din kawai ki wuce sama ni kuma in tafi gida, ai mu ma bamu san me ya samu abun ba ya dauke, kilan ya dau zafi ne" Zaro ido Khaleesat tayi jin ƙaran mota a garage, Safiyyah ma ta gwale ido tana kallonta, mikewa Khaleesat tayi ta tafi window da sauri tana leka garage, ganin motar Ajay ta dawo da sauri tace "Wallahi shi ne ya dawo, gashi kin lalata masa abu..." Safiyyah ta zaro ido tace "Ban gane na lalata ba? Ni kadai nake game din? Me yasa bakya tsoron Allah Khaleesat" Cikin few seconds Khaleesat ta kashe komai ta mayar masa da controller dinsa inda yake ajiyewa, ta mayar da throw pillows dake ƙasan carpet zuwa kan kujera, tana juyawa taga Safiyyan har ta haura sama, ta bi bayanta da sauri suka shige dakinta, Khaleesat ta dinga kyalkyala dariya har da rike ciki, Safiyyah ta hade rai tace "To wai meye abun dariya? Ke abinda ya kamata ayi dariya ba shi kike ma dariya ba sai wanda ba na dariya ba, yanxu meye abun dariya don Allah a nan, ni ban ma san yamma tayi haka ba ai da tuntuni na tafi gidanmu...." Khaleesat dai bata fasa dariyar da take ba, suka ji ya bude kofar daya daga dakunan dake sama, Safiyyah na jin haka ta bude kofar dakin Khaleesat a hankali ta fice, kafin Khaleesat ta fito har Safiyyah ta bar apartment din gaba daya ta mike can karshen layi tana yi tana hadawa da gudu, Khaleesat ta kasa dena dariya ta dawo cikin apartment din ta kulle kofar ta wuce sama ta shige dakinta don kar ma ta hadu da shi. Karfe tara saura Khaleesat ta bude kofar dakinta a hankali ta fito corridor tana leka downstairs don yunwa take ji, zaune ta gansa a parlor yana online game, ta sauko downstairs ganin ya gyara game din da suka rikitar, plate din abincin da ya ci ta kalla, saura kadan tayi dariyar da bata yi niyya ba, ga dai shi ya ci abincin da ta girka yau, kitchen ta nufa tana kallonsa, shi dai ko kallonta bai yi ba game dinsa kawai yake, ta duba sauran abincin da ya rage a kitchen din sai kuma ta fito tana kallonsa tace "Zan iya daukan sauran abincin?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Da can tambayata kike kafin ki dauka, so you can steal it as usual ai kin saba" Juyawa tayi ta koma kitchen din ta juyo sauran abincin sannan ta fito, zaunawa tayi a bakin stairs tana cin abincin tana kallon game din da yake yi, bayan ta gama cin abincin ta bar plate din a wajen ta koma cikin parlon ta zauna kan carpet ɗan nesa da shi kamar munafuka tana satan kallonsa, sai kuma ta jawo controller daya ta langwabe kai tace "Zan yi nima pls" Ya daga ido ya kalleta, sai kuma ya hade rai yace "Duk wanda kika yi yau bai isheki ba" Bata san sanda tayi dariya ba tace "Ba mu sake yi ba fa bayan da ka dawo daxu da rana" Yace "Karya kike, daga yau ku ka sake taɓa min PS ke da loud friend dinki Allah sai kun siyo sabo kun ajiye min, an gaya maku na public ne PS din, in game za ku yi ku je kuyi da na Jay, shima yana da shi ae" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba tana jiran ya gama fadan su yi game din tare, juyawa tayi ta kalli wayarsa dake vibrate, ya dau wayar ganin Mai martaba ke kiransa ya mike ya nufi kofa ya fita waje, kafin ya dawo har ta saita game din yanda za su yi su biyu tana jiransa, yana shigowa parlon ta kallesa tace "Sau daya zan yi kawai pls" Bude baki yayi yana kallonta ganin ta cire game din da yake yi, ta langwabe kai ita ma tana kallonsa, ya hade rai yace "Yaushe na fara wasa dake zaki canza min game?" Tace "Idan kayi defeating dina sai in tashi in bar maka, idan kuma nayi defeating dinka zan ta yi har sai sanda na fadi" Bata jira me zai kara cewa ba ta fara game din, after some seconds ya dau controller dinsa, ko minti daya ba ayi ba yayi defeating dinta, ya juya ya kalleta, dariya tayi tana girgiza kai tace "Wallahi ban yarda ba this is foul play, don Allah last chance...." Sau biyu suna haka duk yana defeating dinta, a na uku ya juya ya kalleta yace "Tashi ki bar parlon nan" Marairaice masa tayi tace "Ni wallahi mugunta kake yi, ai ba haka ake game din ba, just this last time plss..." Ya gyada kai yace "Last time kika ce ko" Ta wani kallesa, suka fara game din, tana ganin alamar zai yi defeating dinta ta mike da sauri ta nufesa zata amshe controller din hannunsa yaki bata, tace "Wallahi ban yarda ba, mugunta kake yi a game din" a haka ta samu ta kwace Dual sense controller din hannunsa tana dariya, Lokaci daya duk suka juya jin an bude kofar parlon, zamewa Khaleesat tayi ba tare da tasan tayi hakan ba ta zauna kan carpet ganin Housemate dinta, Ajay ya kwace Controller din hannunta ya ci gaba da game dinsa har sai da yayi defeating dinta, Jay ya karaso cikin parlon yana kallonsu ya zauna yace "PlayStation ku ke yi" Sai a sannan Khaleesat ta daga kai ta kallesa, haka kawai taji gabanta na faduwa, a hankali tace "Ina yini?" Jay ya ɗan yi murmushi yace "Lafiya lau, continue with ur game" Ta ɗan kalli Ajay tace "Foul Play yake yi ai..." Mikewa tayi ta nufi Jay ta mika masa controller din hannunta tace "Ka taya ni let defeat him" Jay ya kalli Ajay, sannan ya amshi Controller din, Ajay ya ɗan kallesa sai kuma ya canza zuwa game that is more complicated suka fara, Khaleesat sai addu'a take Allah sa Housemate dinta yayi defeating dinsa, ai ko bayan wani lokaci Housemate yayi defeating Ajay, wani shegen dariya ta kyalkyale da a parlon, dariyarta ne ma yasa Jay yayi dariyar da bai yi niyya ba, har ranta taji dadi kada Ajay da Jay yayi, Ajay ya ɗan yi murmushi suka ci gaba da game din, Jay ya sake defeating dinsa, sai da suka yi haka sau uku ana kada Ajay, Khaleesat abun nema ya samu dariya kamar ana mata cakulkuli, Ajay ya hade rai yana kallonta, gwalo tayi masa ta kwace Controller din hannun Jay ta ajiye tace "Kace baka yi kuma, dama tun daxu sai ojoro yake ta min kar ya fara maka haka kai ma" Bata yarda su ci gaba da game din ba don kar ma Ajay yayi defeating Jay yayi masu dariya, Jay dai kallonta kawai yake yi, mikewa Ajay yayi ya ajiye controller din hannunsa kan kujera ya wuce sama, Khaleesat ta kalli Housemate dinta tana dariya tace "Kilan haushi yaji ko? Daxu fa he didn't give me a breathing space sai kasheni kawai yake ta yi" Ganin Jay kallonta kawai yake bai ce komai ba ta sunkuyar da kanta tana murmushi, Calmly Jay yace "A sama kika bar wayarki kika sakko downstairs kuna game kenan" Khaleesat ta kallesa tace "Did you call me?" Kai ya gyada mata, tace "Wayar na sama, kasan me? Safiyyah ce ta zo daxu muna ta game din da ita shi ne ya dawo ya kama mu, yace kar mu sake taɓa masa, idan game za mu yi wai kai ma kana da shi, ni da ita muna son game din sosai fa... Sanda muna level 2 Former Housemate dita saurayinta ya kawo apartment dinmu, kullum sai mun yi" Jay yace "Baku yi karatu ba dai kenan yau?" Khaleesat ta ɗan kallesa, sai kuma tace "All works and no play...." Murmushi yayi yace "I see" Tana murmushin ita ma tace "Kayi dinner?" Yace "Wa zai bani?" Mikewa tayi tace "Ohk let me make you noodles" Yace "A'a kar ki ba kanki wahala" Tace "Ni dai sai nayi" Bata jira cewarsa ba ta wuce kitchen da sauri, ya bi ta da kallo, Ajay ne ya sauko downstairs ya dau dual controller da Khaleesat ta ajiye ya jefa ma Jay sannan ya dau nasa ya zauna, irin bai yarda din nan ba, dariya kawai Jay yayi suka fara game din. Har wajen karfe sha daya suna abu daya, Khaleesat har ta gaji da kallon game din ta kwantar da kanta saman kujera ta fara bacci, Jay ya tasheta ta tafi daki ta kwanta, tana murza ido ta mike ta bar parlon zuwa dakinta, wajen karfe daya da rabi ruwan sama da ake ya farkar da Khaleesat, mikewa zaune tayi bayan ɗan lokaci ta tashi ta fita daga dakin, leka downstairs tayi tana ganin mutum kwance a parlor ta san Housemate dinta ne don Ajay tunda ya dawo gidan bai fiye kwana a parlorn ba, sauka tayi ta kunna wutan parlon me haske to be sure is her Housemate, taga Housemate din nata ne ke bacci a parlon, ta kashe wutan sannan ta koma sama ta dauko masa duvet, tana rufa masa ya bude ido, ta ɗan masa murmushi a hankali tace "The weather is cold, I don't want you to catch cold" Bata jira me zai ce ba ta wuce sama da sauri, a corridor din dakunan taga Ajay a tsaye ashe ba bacci yake ba, ya bi ta da wani irin kallo yace "Munafuka" Ta wani kallesa, sai kuma ta tura baki ta shige dakinta ta kulle. The Spring semester exams was so smooth for Khaleesat, da yake bata da damuwar komai a ranta unlike last exam da tayi sa cikin tension da tashin hankalin Abdul, a satin farko na Exams din nasu kullum sai Safiyyah ta biyota gida don su yi playing Ps5 ko karatun kirki Safiyyah ta dena yi saboda game, Allah Allah take su yi exam su kamo hanyar apartment din Khaleesat ayi game, ita Khaleesat dama cikin dare take karatun ta sai ta biyeta su yi ta game, ranan alhamis suna dawowa gidan da rana suka ga an kwashe PS5 din, Safiyyah ta kalli Khaleesat cikin bacin rai tace "Dama me hali bazai taɓa canza halinsa ba, bai san lada yake samu ɗan nishadin da muke yi da game din ba, da ace na Housemate ne nasan bazai taɓa kwashewa ba sai dai yace mu rage buga game din saboda Exam" Ko minti daya Safiyyah bata kara a gidan ba ta kara gaba rai a bace, nan ko bata san Housemate bane ya kwashe PS5 din. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* 07087865788 HALYSAAH 82 Yau laraba Khaleesat suka zana exam dinsu na karshe for the semester, suna zaune da Safiyyah a haraban department dinsu Safiyyah tace "Yanxu ranan Friday din za ku tafi Nigeria ke da Housemate?" Khaleesat tace "Haka dai yace amma ban sani ba" Safiyyah tayi tagumi tace "Wallahi nayi da na sanin hadani da Yaya Musty da aka yi a kasar nan, daga ce masa zan kira Babana in ce zan taho hutu Nigeria ya fara surutu wai me zan je inyi bayan ba hutu me tsayi bane, ina ruwan Musty in ba gudun biya min kudin jirgi yake ba, gashi yanzu kema tafiya zaki yi ki barni ni kadai raina a garin nan, wallahi ko me zai faru bazan yi hutu a garin nan da er iskar matarsa da bata son kwanciyar hankalina ba" Khaleesat tayi murmushi tace "Na zata ai kun yi settling disputes dinku ke da ita" Safiyyah tace "Wa?? Don kinga na dena kawo maki korafinta? Gajiya nayi kawai in gaya maki, amma tana nan bata fasa abubuwanta ba ashe ba ciki gareta ba kwanaki da nace maki kamar tayi ciki..." Khaleesat tace "Toh Allah ya kyauta, kilan idan kika lallabasa zai bar ki ki tafi Nigeria din" Safiyyah tace "Shi fa ta aljihunsa yake, kudin jirgin da zai biya min ke daga masa hankali, alhalin ni babana nace zan kira ya turo min kudi bance ya biya min ba, Yanxu kenan Ajay kawai za ku bari a kasar nan?" Khaleesat tace "He is leaving today, don ma yayi rescheduling Flight ticket dinsa da tun Monday zai tafi ai" Safiyyah tace "Kin ji ko? Wato duk tafiya za ayi a bar ni ni kadai a garin nan kamar mara galihu, wallahi bazan yarda ba, wannan ai sai Depression ya kama ni kafin ku dawo" Dariya kawai Khaleesat tayi bata ce komai ba, truly hutun babu tsayi sosai kuma banda she is missing her mother da sai tace Housemate ya tafi kawai ya bar ta a kasar saboda Safiyyah, amma a yanxu kam ji take kamar ta jawo Friday don tayi missing Ummanta so much, kiran Jay ne ya shigo wayarta tayi picking call din ta kai kunne, bayan sun gama waya ta kalli Safiyyah da tayi shiru kana ganinta kasan hankalinta ya tashi za a bar ta ita kadai a Maryland, Khaleesat tace "Mu je Housemate dina yana jiran mu..." Safiyyah ta sauke wani ajiyar zuciya ta kara rafka tagumi tace "Ki je kawai ni zan zauna nan inyi tunanin rayuwata, In ba rashin gata ba menene wannan, in zauna a Maryland in ci uwar me? Wallahi bazan zauna ba bakin ciki ya kasheni, ko duka kudin account dina ne gwara in siyi ticket in gudu, sai dai Mustapha ya tashi rana daya yaga babu ni, yayi ta iko da ni sai kace wata matarsa daga dai ina zaman cin arziki a gidansa" Khaleesat tayi murmushi tace "Kilan ma wasa yake maki amma duk kika daga hankalin ki, ni dai ki tashi mu tafi..." Safiyyah tace "Kiyi tafiyarki kawai ni ina nan bazan je ko ina ba" Duk yanda Khaleesat ta so Safiyyah ta tashi su tafi Housemate yayi dropping dinta a gida Safiyyah taki bin ta, haka nan Khaleesat ta kyaleta ta dau Backpack dinta ta tafi inda Housemate yayi parking yana jiranta, bayan ta shiga motar ta kara gaishesa, ya amsa yace "How was the exam Halysaah?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Safiyyah bazata tafi gida bane ban gan ku tare ba?" Khaleesat ta ɗan yi murmushi tace "Eh wai bazata ba, she is angry saboda yayanta yaki barin ta tafi hutu Nigeria" Jay yana murmushi yace "Shi zai biya mata kudin ticket din ne?" Khaleesat tace "Nima ban sani ba" Jay yayi igniting motar yace "Indai zai bar ta sai in siya mata flight ticket din, probably bai sa kudin Flight dinta a Budget dinsa for this month ba, beside kilan yayi considering hutun bai da tsayi" A hankali Khaleesat tace "She is so sad about it" Jay ya dau wayarsa yace "Let me call her" Ita dai Khaleesat kallonsa kawai take har ya gama waya da Safiyyah, komai nasa burgeta yake, yana daga idonsa tayi saurin sauke nata idon, yayi kasa da murya yace "Me da me kike bukata da zaki tafi Nigeria da shi?" Khaleesat ta girgiza masa kai cikin sanyin murya tace "Ba komai, recently kayi min shopping ai" Yace "But zaki yi ma mutanen gida tsaraba" Tana murmushi tace "A'a ba abinda zan siya" Yace "To ni zan siya masu" Ta langwabe kai tana kallonsa tace "Don Allah kar kayi, expenses din yayi yawa pls" Bai sake tankata ba, tasan kuma sai yayi tunda yace zai yi, ya kalli agogon wrist dinsa don anjima zai yi dropping Ajay a airport, bayan kusan minti biyu ya kalleta calmly yace "How about coming back to Maryland as a bride?" Khaleesat ta daga idanuwanta ta kallesa don sai da gabanta ya fadi jin abinda yace, ya sakar mata murmushi a hankali yace "How about that?" Sunkuyar da kanta tayi don bata ma san me zata ce ba don kunya, yayi kasa da murya yace "Halysaah" Ɗan murmushi Khaleesat tayi ta kauda kai kawai, yace "Say something" a hankali tace "Ni ban san me zan ce ba" Yana murmushi yace "To a matsayin amarya zaki dawo in sha Allah" Khaleesat dai taki yarda ta juyo ta kallesa, shi ko bai fasa kafeta da ido yana ta kallonta ba, a haka Safiyyah ta iso gun motar, ta bude back seat ta shiga da sallama kamar mara lafiya, Jay ya amsa ya kalleta yayi murmushi yace "Cheer up Safiyyah, yayanki zai bar ki in sha Allah, duk yanda ku ka yi da shi sai ki min magana ta WhatsApp" Safiyyah tace "To Yaya Jawwad" Khaleesat sae kallon Safiyyah take tana murmushi ganin yanda ta nutsu irin tana cikin damuwa din nan, ta gefen ido Safiyyah ta harareta, Khaleesat tayi dariya tace "To ni me nayi maki?" Jay yayi driving motar suka bar wajen. Wajen karfe uku Khaleesat ta sauko downstairs tana kallon Housemate dinta dake parlor don wayarta ya kira, ya juya ya kalleta yace "Are you sleeping?" Ta girgiza masa kai, yace "Ohk get ready let go drop Ajay at the airport" a hankali tace "Toh" Sannan ta juya ta koma sama, bayan ɗan lokaci ta sauko cikin shiri, ganin baya parlon ta fita waje ta gansa yana jiranta a garage, kulle apartment din tayi ta karasa ta shiga motar bayan ya bude mata front seat.... Suna isa gidan nasu Jay yayi parking a waje ya bar ta a motar ya shiga cikin gidan, after a while suka fito tare da Ajay, bude front seat din tayi ta sauka ta koma back seat, Ajay ya bude booth ya saka hand luggage dinsa, sannan ya shiga gaban motar, Jay ma ya shiga driver seat, sai da Jay ya fara driving Khaleesat ta ɗan kalli Ajay don yi yayi kamar bai san tana cikin motar ba, tace "Ina yini" Yana fastening seat belt dinsa yace "Good" After some minutes ride Jay yayi parking a inda zai cire kudi, yana kallon Ajay yace "Let me get some cash" Ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, ya juya yana dubanta yace "I am coming" Ta gyada masa kai ya bude motar ya sauka, ta daga ido tana kallon Ajay ta madubin gaba suka hada ido, ta tallabi chin dinta tace "Are you going to kano or Bauchi?" Ear pod dinsa ya ciro ya toshe kunnensa, ta wani kallesa, after some seconds ta ɗan buga seat din da yake zaune tace "Ina tambayar ka ne" Ya juya ya kalleta yace "Baki da hankali ne?" Ta langwabe kai tace "To ai nasan kana ji na, i am just asking a harmless question" Yace "Mind your business" Daga haka ya juya, tabe baki tayi ta matsa zuwa can karshen motar ta zauna, Jay ya dawo bayan ya cire kudin ya shiga motar, har suka isa airport ba wanda yace komai cikin su, Ajay ya bude motar ya sauka ya zaga ya bude booth ya dau jakarsa ya dawo ya daga ma Jay hannu, Jay yace "Journey mercies bro" Ajay yace "Thanks" Ita dai Khaleesat ba abinda tace, Ajay ya ɗan kalleta sannan ya juya ya nufi cikin airport din, Jay ya kalli Khaleesat yace "Dawo gaba Madam" Murmushi tayi ta bude motar ta sauka ta koma front seat, yace "Me yasa baki masa Allah ya kiyaye ba" Khaleesat tace "Ohk, na ma manta" haka suka bar airport din, eatry ya tsaya ya siya masu abinci don baya son ta ba kanta wahalan girki, daga nan suka koma Apartment dinta, ko abincin Khaleesat bata ci ba ta tafi ta kwanta a dakinta don bacci take ji. Wajen karfe bakwai na dare Khaleesat ta bude kofar dakinta tana kallon Jay dake tsaye bakin kofar, yace "Are you still sleeping?" Ta ɗan yi murmushi tace "Na tashi" Yace "Knocking dina ya tashi ki dai, nasan ko sallah baki yi ba?" A hankali tace "Zan yi" Yace "Ohk kiyi sallah ki sakko downstairs ki dau abincin ki, idan ya so sai ki ci gaba da baccin ki" Tana murmushi ta gyada masa kai, Bayan ta idar da sallan magrib ta sauko downstairs, tun da suka dawo daxu da ta tafi sama ta kwanta sai yanxu ta sauko kasa, kallo daya yayi mata ya ci gaba da kallon TV da yake, taga yayi mata micro waving abincin nata ta dauka da bottle water tana kallonsa tace "Thank you" Without looking at her yace "Are you going upstairs with the food?" Ta gyada masa kai tace "Uhm" Yace "Alright, sai da safe kenan?" Ta ɗan kallesa, sai kuma ta gyada masa kai, shi ya ma fi so taje tayi ta baccin da ta sauko downstairs ta zauna inda yake, upstairs ta koma bayan ta ci abincin a dakinta ta dau wayarta ta duba ko Aunty Farida tayi mata message amma taga bata hau online ba, ta jira har lokacin Isha'i yayi, tayi sallah sannan tayi wanka tayi shirin bacci ta kwanta. Washegari da safe wajen karfe goma saura Khaleesat ta sauko downstairs, kallon Housemate dinta dake kwance idonsa lumshe a parlon tayi, har yayi wanka ya shirya, ta kalli makullin motarsa alamar ya ma fita ya dawo, taga ya bude ido a hankali yace "Good morning Halysaah" Ta zaro ido don ta zata bacci yake yi, sai kuma tayi murmushi tace "Good morning" Yace "I got us breakfast, ga naki saman Centre table" Tace "Kayi breakfast din?" Ya gyada mata kai, tace "Ohk" zagawa tayi zuwa inda ya ajiye mata breakfast din, Ya mike zaune yana shafa gashin kansa yace "I am going out, dama ina jira ki tashi ne, should i drop you at Safiyyah"s place? Cause i don't want you to be home alone" Khaleesat tace "Mun yi chatting da ita daxu tace zata zo nan da karfe goma, kilan tana hanya, she is coming to help me wash my hair" Kallon kanta yayi duk da akwai hula a saman kan sannan ta daura dankwali yace "Kin rage gashin ne?" Dariya Khaleesat tayi bayan ta tuno yanda yace ta rage gashin kanta da dadewa and he was serious about it, tace "Eh na rage" Yace "Da gaske? Ta gyada masa kai tana kallonsa, yace "To in gani" Sunkuyar da kanta tayi tana Murmushi taki ce masa komai, yace "Ko baza ki nuna min ba" Ta ɗan kallesa tace "To saboda me zan nuna maka?" Yace "So that i can confirm ko da gaske kike" Ita dai bata fasa murmushin da take ba, can ta ɗan yi baya da hulan kadan tace "Ka gani?" Yana kallon gashin gaban kanta that's so Curly and black, a hankali yace "Ban gani ba" Dariya tayi tace "To ai shikenan" Yace "Baza ki nuna min ba dai kenan" Shiru tayi tana kallonsa kamar yanda ya kafeta da ido, after some second ta cire hulan kanta duk gashin suka sauka har kusan gadon bayanta, mikewa Jay yayi yana kallon gashin with astonishment, it was very black, full and long, hannunsa ya kai kan gashin yana feeling texture dinsa, he couldn't believe this is her real hair, Khaleesat ta zaro ido ta koma baya da sauri ganin abinda yayi, kiris ya rage ta fada saman Centre table din bayanta yayi saurin rikota yana kallonta babu ko kiftawa ya kai forehead dinsa saman nata murya can kasa yace "You've got a very beautiful hair Halysaah, I love it..." Gaba daya Khaleesat ta daburce tana kokarin kwace kanta aka danna bell din gidan, that was when he realised and quickly let go of her, dukawa tayi da sauri zuciyarta na bugawa ta fara neman hulanta, shi kuma ya nufi kofar parlon ya bude, Safiyyah ce tsaye bakin kofar ta gaishesa tana washe baki ya amsa yana mayar mata da murmushin ya juya, makullin motarsa kawai ya dauka ya fita daga gidan, Safiyyah ta zauna kan kujera tana kallon Khaleesat da mamaki tace "Ya na ganki duk kamar a daburce, shi ma Housemate din naga yake kawai yayi min, kuma har ya fita" Khaleesat ta mike taki yarda su hada ido da Safiyyah tace "Ban gane a daburce ba, ba kince da Aslam zaki zo ba, me yasa baki zo da shi ba" Kitchen Khaleesat ta nufa Safiyyah ta bi ta da kallo har ta shiga ciki, Sai kuma ta bi parlon da kallo tace "Uhmm abi did i interrupt anything?" Bayan Khaleesat ta fito kitchen din da plate a hannunta da cup din shayi still taki yarda su hada ido da Safiyyah ta fara bude breakfast din da ya siyo mata, Safiyyah tace "Goben ne tafiyar taku?" Khaleesat tace "Ehh in sha Allah" Safiyyah tace "Ni ya Musty yace in bari next week dukanmu ma za mu tafi Nigeria din da gantalalliyar matarsa" Khaleesat ta fara cin fries din da ta zuba a plate ta kalli Safiyyah a karo na farko tace "Sakko mu ci, sai yanxu zan yi breakfast" Safiyyah tace "A'a ni nayi tun daxu" Khaleesat bata sake ce mata komai ba ta ci gaba da cin fries dinta, Safiyyah sai kallonta take a ranta kuwa cewa take yaushe Housemate ya lalace haka har yake neman gantalar mata da kawarta da ko hannunta bata yarda namiji ya taɓa, sam bata gane wannan birkicewar da kawarta tayi ba, kaddai kiss dinta yayi, dama taga kamar lip gloss a lips dinsa, what if har da romance, ta kalli Khaleesat tace "To kallo ku ke a parlon ne ku ka kashe Tvn da na zo?" Khaleesat ta wani kalleta, sai kuma tace "Ni fa wallahi yanxun nan na sakko downstairs tun da gari ya waye, baki ga breakfast dina akan Centre table ba sai yanxu na dauka, i am just coming down now" Safiyyah sai kallonta take ganin a duburce take duk bayanin nan, can ta kyabe baki ta sauka kusa da ita zata fara cin fries din ita ma, Kamshin turaren Housemate ne ya daki hancinta daga jikin Khaleesat, Safiyyah tayi tagumi tana kallonta amma bata dai ce komai ba, can ta dau fries din ta fara ci, a ranan Safiyyah bata yarda ta koma gida ba ta kira Ya Musty ta lafta masa karya wai Khaleesat na kwance bata da lafiya, har da ba Khaleesat wayar yayi mata sannu, ita kanta Khaleesat taji dadin kwanan da Safiyyah zata yi a gidan because she is still shocked at what happened in the morning..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence* 07087865788 *Hakika duk wacce ta Bari aka barta abaya ita taso domin mu mata da ado da kwalliya aka sanmu. Assalamualaikum, barkanmu dai Yan uwana ma masu albarka, ayau na zo maku da batun sababbin kayan da na kawo Mana masu matukar kyau da kuma inganci,oum eman collection 🤝😍, takawo maku jakunkuna da takalma,hadi da abayas da kuma sarkoki masu matukar kyau da kuma sauki,07018872587 Ena amare da uwayan gida masu capacity's toh duk wacce ta yarda da tacika mace da wacce takeso ta zamo ma abociyar kwalliya toh ta garzayo gunmu domin hadewarki cikin ado da kwalliya kedai nemeni a wannnan number domin kisami kayayyaki masu kyau da kuma quality akan kudi kalilan hajiyata 07018872587 ngd 🤝 ado da kwalliya shine takenmu* HALYSAAH 83 Safiyyah na zaune gefen gado a dakin Khaleesat tayi tagumi tana kallon Khaleesat da ta gama shiryawa ta dau Charger dinta ta saka a backpack dinta kar ta manta shi, a hankali Safiyyah tace "Shikenan yanxu dai tafiya za ku yi ku bar ni a kasar nan" Khaleesat tace "Toh ba kince Ya Musty yace next week za ku taho ba, nan da few days ne next week din fa" Safiyyah ta taɓe baki ta mike tace "Ai shikenan, kafin nan da next week din ai kadaici ya min illa Khaleesat, babu ke babu Housemate, ga Ajay ma ya tafi, i have nobody remaining in this country kenan ai" Khaleesat ta kashe komai na dakinta sannan ta dau karamin mayafinta suka fita, tun daxu Jay ke jiransu a waje patiently, bayan sun sauko downstairs Safiyyah tace "Ya kai luggages din mota ne gaba daya?" Khaleesat na kashe duk wani abu dake kunne na wuta a parlon tace "Tun daxu ya fita da su ai" Safiyyah ta wani kyabe baki tace "Sae wani rawan jiki kike za ki tafi Nigeria kamar irin nima ba zan zo ba din nan" Dariya Khaleesat tayi tace "Ban gane rawan jiki ba, don Allah mu fita tun daxu fa yake garage yana jiranmu" Safiyyah tace "Da Ajay ne da ya cika mu da bala'i yanxu mun gigice, ai Housemate akwai patient" A haka suka fito daga apartment din suka gansa zaune a mota yana danna wayarsa, yafi minti talatin da biyar a motar yana jiransu, ya bude motar ya sauko yana kallonsu har suka karaso inda yake sannan yace "Done with preparation?" Khaleesat ta gyada masa kai, yace "Ohk let me order a ride, dama ina son ku bata duk lokacin da za ku bata ne so that we won't keep the Uber driver waiting" Safiyyah tace "To mu shiga motar mu ɗan yi hirar bankwana kafin nima in zo Nigeria din Yaya Jay" Murmushi Jay yayi ya bude masu back seat, Safiyyah ta shige, ita dai Khaleesat na tsaye bata shiga ba, ya kalleta yace "Baza ki shiga ba?" Ba tare da ta kallesa ba tayi Murmushi ta girgiza masa kai, hakan yasa shi ma bai shiga motar ba ya gama order din ride din da wayarsa sannan ya jingina da motar yana kallon Safiyyah yace "So what is ur plan when back in Nigeria?" Safiyyah ta gyara zama tace "Ni dai da za a bar ni a gidanmu ina son in je masarautan ku ziyara, dama ban taɓa shiga ko wani Emirate ba a Nigeria" Jay yayi dariya yace "Really?" Tace "Wallahi, kuma gashi bamu da yan uwa kwata kwata a Bauchi, Khaleesat ce dai kanwar Babanta ke can amma ita ma bata taɓa zuwa ba tace min, sai dai ko in yi karya ince Gombe zan je biki, don akwai Cousin sister dita an kusa bikinta kawai dai bama shiri da ita ne kuma ban yi niyyar zuwa bikin ba, amma tunda naji ance Bauchi da Gombe neighbouring state ne kawai sai in fake da bikinta inje Masarautan ku in gaida Mai martaba in de baza a koreni ba" Tana washe baki ta kare maganar, Jay dai murmushi kawai yake, Khaleesat dama juya masu baya tayi don ta gaji da halin Safiyyah, Jay ya kalli Khaleesat yace "Kuna da yan uwa a Bauchi dama?" Khaleesat tace "A'a ni ban taɓa gaya mata haka ba, we have nobody in Bauchi..." Safiyyah tace "Kai haba, na zata kince Aunty Murja a Azare take" Babu yabo babu fallasa Khaleesat tace "Ni ban ce maki haka ba Sophie" Safiyyah tace "To ni muna da yan uwa a Gombe, ga er uwata nan ma zata yi aure a can" Jay yace "In dai zaki je bikin that won't be an issue in Sha Allah, I will bring you down to the Emirate" Tace "Har Mai martaba zan samu gani?" Yana Murmushi yace "In sha Allah zan kai ki har gabansa" Ya ɗan kalli Khaleesat da ta kagu Uber din ya zo ko Safiyyah zata hakura da surutun haka, yace "Ina makullin apartment din?" Khaleesat ta mika masa ya amsa yace "Let me check the electrical appliances ko akwai wanda ku ka manta baku kashe ba" Daga haka ya nufi cikin apartment din, Khaleesat ta leka motar tana kallon Safiyyah tace "Does it even make sense to you ki ce zaki je masarautan su ziyara?" Safiyyah tace "Ban gane ba? Wani mugun waje nace zan je? Ai ba wani abu bane a ciki kema in zaki ki shirya kawai mu je sai mu fake da bikin Karima, balle ni nasan denying kika yi kawai amma kin taɓa ce min Aunty Murjan ku a Bauchi take, haba ai kamar Excursion ne wannan za mu je ba wani abu ba, ke duk abun wayewa kun yi hannun riga da shi, har Yankari Game reserve ni dai zan je wallahi idan naje masarautar tasu, su ma kuma za su ji dadi idan naje, har Ajay zai yi mamaki yaji dadi kuma, Ni dai it's a privilege for me" Khaleesat bata sake ce mata komai ba ta koma can Edge din motar ta tsaya tana kara mamakinta ita dai duk wani harkar kareranci ta iya, Jay na fitowa sai ga Uber da yayi order ya iso. Har Airport Safiyyah ta masu rakiya, sai da Jay ya jira ta samu Lyft da zai maida ta gida sannan ya bata 1000 dollar, da farko kin amsa tayi yace "Common Safiyyah, na taɓa baki kudi ne? I won't be happy idan baki amsa wannan ba" Tana ɗan murmushi ta amsa kudin sannan ta masa godiya tace "Allah ya kai ku lafiya nima in sha Allahu ina nan zuwa ranan litinin ko bai bar ni ba zan gudu da izinin Allah" Jay yayi dariya yace "A'a gwara dai ki jira ya bar ki Safiyyah kar ki gudu" Safiyyah ta juya ta kalli Khaleesat dake kallonta don har ta fara missing kawartata, rungumeta Safiyyah tayi tace "Safe trip kawata, Allah ya kiyaye hanya" Murmushi kawai Khaleesat tayi cikin sanyin murya tace "Ameen, Thank you so much Sophie" Safiyyah tayi kasa da murya tace "Kuma saura ki kunyata ni ki ki sakin jiki da shi idan kun shiga jirgin, ko abinci aka baku ki tabbatar kun ci tare haka masoya suke yi idan za su yi tafiya tare, don nasan dai kusa da kusa ya siya maku ticket din, kin dai gane me nake nufi" Khaleesat ta turata ta bar wajen tana murmushi, a haka suka shiga cikin airport din Safiyyah kuma ta koma gida. Just handbag kawai Khaleesat ke rike da shi da za su shiga jirgi don hatta backpack dinta Jay sai da ya amsa ya rike mata, bai bari ta dau komai ba, jiran 30 mins kawai suka yi Departure lounge before boarding, su ne kuma farkon boarding din jirgin kasantuwar ticket dinsu Business Class ticket ne, kamar yanda Safiyyah tayi guessing seat dinsu kusa da kusa ne, ita dai Khaleesat tun incident din jiya da safe har yanxu ta kasa sakin jikinta wani irin kunyarsa take ji, ko kallonsa bata iya yi ko yana mata magana, bayan duk an gama boarding jirgin ta bude handbag dinta ta ciro wayarta zata ajiye ma Aunty Farida message tace za su taso, don tace mata ta gaya mata idan za su taso din, bayan ta tura message din ta daga kai ta ɗan kalli Jay taga kallonta yake kamar ya samu TV, murmushi tayi ta sunkuyar da kanta, yayi kasa da murya yace "You need help with the seat belt?" Ta girgiza masa kai ba tare da ta kallesa ba tayi fastening seat belt dinta don tashi jirgin zai yi.... Suna ɗagawa sararin samaniya Khaleesat ta ɓige da bacci don dama surutu da zantukan Safiyyah bai bari tayi bacci da wuri daren jiya ba, sai da suka kai karfe uku da rabi na asuba Safiyyah na labari yaki ci yaƙi cinyewa, suna idar da sallahn asuba kuma wai yunwa take ji su je kitchen suyi girki, haka ta hanata ɗan baccin safen da take yi ma, da rana kuma Jay ya fita da su shopping din tsaraban da Khaleesat zata kai gida, yayi ma har Safiyyah ma shopping din, kudi sosai ya kashe masu a wajen, daga nan kuma suka tafi gidan abinci me tsada suka yi lunch, sai kusan yamma suka dawo gida, suna dawowa kuma sai shirin tafiya Airport, Jay na ganin Khaleesat ta fara bacci ya mike ya karasa kusa da ita ya kwantar mata da seat dinta gently ta yanda zata zama comfortable tayi baccinta, ta bude ido a hankali tana kallonsa, murmushi ya sakar mata yana kallonta, ta mayar da idonta ta lumshe ya koma seat dinsa after making sure she is comfortable, haka ya dinga watching dinta tana bacci kamar an basa gadinta, ko da Khaleesat ta farka after few hours taga ya rufa mata blanket din da Airline din suka yi providing ma business class passengers, ta kara gyara kwanciya ta ci gaba da baccinta, after some Hours ya tasheta daga baccin ta ci abinci, ta marairaice masa tace "I am not hungry" Daga haka ta koma ta kwanta shi dai kallonta kawai yake.... Karfe shidda da yan mintuna na asuba suka sauka airport din Abuja, a cikin Airport din suka jira next flight dinsu to Kano which is 7 am flight, tun basu karaso Nigeria ba suna ƙasar da suka yi Transit ya sa a siya masu ticket din kan su karaso, Khaleesat dake ta kallonta ta jira har ya gama wayar da yake wanda da alama da Maminsa yake magana, yana daga kai ya kalleta a hankali tace "Gidan da Ya Junaid ya taɓa sa aka kaini a nan Abuja is she his late mother's sister?" Jay yace "Ammi?" Khaleesat ta gyada masa kai, Jay yace "No, she is his mother's Childhood frnd, since after his mother's demise she was always there for him, har hutu Mai martaba yana bari yaje yayi wajenta when he was little, a Bauchi take da mai gidanta before suka yi relocating to Abuja years back, so she is just like a mother figure to him, yana kuma bata value sosai" Sosai jikin Khaleesat yayi sanyi, ta tuna irin yanda Ammi ta ja ta a jiki kamar ta taɓa saninta lokacin da ta sauka gidan, ta kalli Jay a hankali tace "She is very kind" Jay yayi murmushi yace "Sure she is, Ajay doesn't joke with her matter, ko abu zai yi idan ta hanasa ya hanu, in kuma tace ga yanda zai yi to hakan zai yi, although yana son Grandma dinmu ma amma kuma ita baya jin maganar ta" Khaleesat tace "To kana da number din Inteesar din Ammin?" Jay yace "A'a bani da numberta, sai dai Ajay" Khaleesat tace "Pls ka amso min wajensa, da ace Flight dinmu zuwa Kano ba na yanzu bane da naje gidan in gaisheta" Jay yayi murmushi yace "Da nasan za ki je ai da nace ayi mana booking ticket din yamma, da sai in kai ki gidan ku gaisa" Khaleesat ta langwabar da kai tana kallonsa, yace "Ko ayi cancelling ticket din kawai?" Ta zaro ido, sai kuma tayi murmushi ta girgiza masa kai tace "A'a, ba haka nake nufi ba" Yace "To ya kike son ayi ur Royal Majesty?" Er dariya tayi tace "In ka amsar min number wajensa sai in kira Inteesar daga nan sai ta ba Ammi wayar mu gaisa" Jay yace "Ohk zan ce ya turo min number idan muka isa Kano in sha Allah" Khaleesat tace "Yana Kanon ne ko yana Bauchi?" Jay yace "Yana Bauchi, bai tsaya Kano ba" Khaleesat ta langwabe kai tace "Da ma ya auri Inteesar kawai because of her Mother, since she sees him as a son, and he takes her as a Mom, kuma Inteesar din ba ruwanta i like her so much, she will be of a good wife to him, she is so gentle, and she is beautiful" Jay yayi dariya yace "Ko?" Khaleesat tace "Allah..." Jay yace "Toh ko za ki basa shawara?" Khaleesat ta wara ido tace "Kai dai da yake brother dinka ka basa shawaran, zai samu peace of mind sosai idan ya auri Inteesar" Jay na murmushi yayi kasa da murya yace "Kamar yanda zan samu peace of mind idan na auri Halysaah?" Rufe fuskarta tayi da sauri tana murmushi, shikenan kuma yayi cutting conversation din don bata sake yarda ta ci gaba da hirar ba, he wish she will continue don yana jin dadin conversing da ita barin idan ta saki jiki, har wani natsuwa yake ji a ransa, don dai ta ci gaba da magana yace "Yanxu dai baza ki bi kawar ki ku zo masarautar mu ba?" Khaleesat tayi dariyar da bata yi niyya ba tace "Are you taking Sophie serious?" Jay yace "To ai ita da gaske take, she was so serious saying it" Khaleesat tace "Uhm, nasan ma baza a bari taje bikin da take cewa a Gombe ba balle har taje Bauchi, her father is very strict" Jay yace "Amma gaya min gaskiya, kuna da yan uwa a Bauchi kamar yanda tace?" Khaleesat ta ɗaga manyan idanuwanta ta kallesa, murmushi tayi ta girgiza masa kai alamar a'a, yace "Ban yarda ba, tunda har Safiyyah ta fada haka ne, so why are you hiding it?" Khaleesat tayi shiru, after some seconds tace "Stepsister din Dad dina ce a can amma a kauye suke, Nenne ce ta rike ta don tun tana karama Baabarta ta rasu" Jay yace "Ina kenan a Bauchi?" Khaleesat tace "Nima ban sani ba wallahi" Yace "Baki taɓa zuwa ba kenan?" Khaleesat tace "Ban taɓa zuwa ba, amma Aunty Farida da su Ummanmu suna zuwa idan ya kama, step mothers dina ma duk suna zuwa" Jay yace "Amma ita ta Bauchin bata zuwa Kano?" Khaleesat tayi shiru, sai kuma a hankali tace "Tana da yarinya with Cerebral palsy, and she is almost 14 years, saboda yarinyar yasa bata zuwa ko ina tunda bazata iya tafiya da ita ba saboda condition dinta, kuma ba me kular mata da ita kamar yanda ita zata yi" Jay yace "Allah Sarki, Allah ya basu ikon cin jarabawa" Khaleesat tace "Ameen" Bayan few more minutes suka yi boarding jirgin da zai yi take off zuwa garin Kano wanda shi ne jirgin farko da zai tashi zuwa Kano a ranan, duk da farin cikin da Khaleesat take zata je gida taga Ummanta da Aunty Farida da Siblings dinta har ma da Babanta, amma deep down her she is so afraid don bata kuma san me zata tarar wannan karan ba ko kuma me zai faru zuwanta kano, da ta tuna tashin hankalin da ta tarar zuwanta na karshe tare da Ajay sai taji faduwan gabanta na tsananta, bayan jirgin ya tashi Jay dake lura da ita don kusa suka zauna yace "Halysaah" Juyawa tayi ta kallesa, yayi kasa da murya yace "What happen?" Tayi murmushin karfin hali ta girgiza masa kai, yace "No Halysaah, tell me why you became tensed all of a sudden..." Sauke idonta tayi jikinta yayi sanyi, ganin yana jiran amsarta ta kallesa a hankali tace "Kawai naji gabana yana faduwa ne, I don't know what I will meet home this time around" Calmly Jay yace "Babu abinda zaki tarar sai alkhairi in Sha Allah, stay positive dear" Sosai taji hankalinta ya kwanta with just his words, tayi murmushi tace "Toh Nagode" hannunsa ya saka a nata shi ma yana murmushin yana kallonta, ta zame hannunta da sauri, ta wani kallesa, kashe mata ido yayi yace "Ashe idan kina bacci sleeping beauty kike komawa..." Zaro ido tayi jin abinda yace, yana murmushi ya ciro wayarsa ya shiga videos din da yayi mata ƙashi ƙashi tana bacci, buda baki tayi with shock tana kallon video din da yake playing, kamar zata yi kuka tace "Innalillahi, ni dai wallahi ka goge" Murya can kasa yace "Anki" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah, ur evidence via 07087865788* HALYSAAH PAGE 84.…Sun sauka garin Kano karfe takwas bai karasa ba na safiyar, motar da zai dauke su har ya iso airport din yana jira, bayan drivern ya saka luggages din a booth Jay ya bude ma Khaleesat back seat ta shiga tana dan murmushi cikin sanyin murya tace “Thank you” murmushin yayi mata shi ma ya bude front seat ya shiga, Khaleesat tried her best to stay positive kamar yanda Jay yace mata all through the ride home, but she is excited and still tensed at the same time, suna isa layinsu driver yayi parking dai dai inda Jay yayi instructing dinsa, Khaleesat ta sauke boyayyen ajiyar zuciya, Jay ya juya ya kalleta tayi murmushi a hankali tace “Thank you soo much Housemate” Har ta mance rabon ta kirasa da hakan a gabansa, shi dai kallonta kawai yake can yace “I don’t understand why you are thanking me for” Langwabe kai tayi tana murmushi tana kallonsa yace “Za ki sani” Tuni Drivern ya sauka daga motar ya zaga zuwa booth, Jay ya sauka shi ma ya nuna masa luggages din ta, Khaleesat na sauka daga motar yaran makotansu na kyallara ido suka ga ita ce suka taho da gudu suka baibaiyeta suna Oyoyo, Jay dai ya juya yana kallon ikon Allah, yaran ta hada da boxes dinta su shiga mata da shi gida, duk suka fara rige rigen dauka, ta juya ta kalli Jay tana murmushi tace “Zaka shiga ciki ne?” Ya rungume hannunsa yace “A’a, amma da yamma zan zo in sha Allah” A hankali tace “Allah ya kai mu” Yana murmushi yace “Ameen Halysaah” Ita ma murmushin tayi tace “Amma zaka dan kwana biyu a Kano before going to Bauchi?” Yace “A’a, gobe zan tafi in sha Allah, Mai martaba is worried about how of recent we are traveling separately with Ajay which is unlike us, kinsan for many month now bama tafiya tare kuma ba haka muka saba ba, duk tafiya tare muke yi da shi, so his highness is worried may be we had issues that we are hiding away from him, muna Turkey ya kirani nace masa gobe zan shiga Bauchin in sha Allah….” Khaleesat dai tayi shiru tana kallonsa, can ta sauke idonta tace “Toh Allah ya kai mu goben” Yace “Ameen” Dubu hamsin rudin Nigeria ya dauko a gaban motar da alama Drivern ya sa ya taho masa da shi, ya mika mata yace “In case you will need anything Halysaah” Khaleesat ta zaro ido tace “A’a ni babu abinda zan bukata wallahi” Juyawa tayi zata bar wajen yace “Halysaah” Ta juyo amma bata ce komai ba, yace “Bana son kina min haka, ba ni na baki ba?” Ta marairaice tace “Wallahi ni babu abinda zan yi da kudi, beside i have money in my account, don Allah kayi hakuri ka bar shi Nagode” Ya hade rai yace “I didn’t ask weda you have money or not, ni na baki ki amsa bana son musu” Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, lokaci daya jikinta yayi sanyi sosai, ganin kallon da yake mata ta dan risina ta amshi kudin a sanyaye tace “To Nagode, thank you soo much, Allah ya saka da alkhani… Bai jira ya gama sauraronta ba yace “Ki gaida rain su Umma, sai na shigo anjima in sha Allah” Ta gyada masa kai tana kallonsa, ya zaga ya bude front seat ya shiga, Jiki a sanyaye ta juya zata shiga gida taga Mama Shatu da Mama Zubaida suna lekosu ta bakin kofa da ‘ya yansu kariana gaba daya, sai a sannan ta lura da sabon kofar da aka saka a entrance din shiga cikin gidan nasu, lokaci daya su Mama Zubaida duk suka bar bakin kofar, ta kalli yaran da suka shigar mata da akwatunanta don auk suna tsattsaye a kofar gidan suna kallonta tace “Nan da minti talatin duk ku shigo ku amshi tsaraban ku kun ji” Murna suka fara yi gaba daya suna tsalle, ita dai tayi murmushi ta karasa ta shiga cikin gidan, step Siblings dinta duk suka yo kanta suka rungumeta suka dinga mata Oyoyo cike da farin ciki dama iyayen ne suka hana su fita kofar gida su je wajenta, Khaleesat tace “Ba ku je islamiyya bane?” Dan Mama Shatu me suna Sulaiman yace “Ba a biya mana kudin wata ba Aunty” Khaleesat tace “Nawa ne kudin watan?” Yace “Dubu uku ne” Khaleesat ta kalli Aunty Farida da ta fito daya cikin dakin Umma ta tafi cike da farin ciki ta rungumeta, Aunty Farida dai sai murmushi take ta dago kanta tana kallonta ganin yanda ta yi kumari sai wani glowing skin dinta yake, Aunty Farida tace “Sannu, ya hanya Khaleesah, Junaid din na kofar gida ne?” Khaleesat ta bude ido tace “Ya Jawwad fa nace maki ba ya Junaid ba, ai ya ma tafi yace sai da yamma zai dawo, Aunty su Islam sun tafi islamiyya ne? Ummata fa?” Aunty Farida tace “Su Islam na islamiyya, Umma tana daki” Khaleesat na murmushi tace “Toh ina zuwa in ba su Sulaiman kudin wata” Daga haka la koma gun Step Siblings dinta dake tsaye sun yi cirko cirko a tsakar gidan suna kallonta, Dubu hamsin din hainunta ta cire dubu uku ta mika ma Sulaiman don shi ne babba cikinsu, sauran kananun yaran maza da mata ma haka ta dinga bin su tana kirga dubu uku uku tana mika masu, nan take sai da ta rabar masu da dubu talatin da shidda, suka diriga cewa saura Munzali, Khaleesat tace “in ya dawo ya sameni sai in basa” Murna yaran suka dinga yi a tsakar gidan, ta juya ta kalli inda kishiyoyin Ummanta ke zaune daga bakin kofar su ko wacce ta tabe baki gashi sai naso suke, ga wani uban tagumi da Mama Zubaida ta zabga, karasawa tayi har inda suke ta gaida su with respect, a dakile duk suka amsa mata kamar dole, babu ya hanya babu komai sai ido da suke bin ta da shi, Khaleesat ta juya ťa tafi dakin Ummanta don Allah Allah take ta ganta, tana shiga cikin dakin ta rungume Umma cike da farin ciki tace “Ummana na dawo” Umma na murmushi tace “To sannu da zuwa Khaleesah, ya hanya?” Khaleesat tace “Alhamdlih, Babana fa?” Umma tace “Ya fita kasuwa, Ahmad din ya tafi ne?” Khaleesat na murmusii tace “Eh ya tafi, yace sai da yamma zai zo” Umma tace “To Allah ya kai mu” Umma dai kalionta kawai take ganin yanda tayi kyau sosai, Khaleesat ta mike ta jawo akwatin ta zata bude wanda tulin Chocolates din da Jay ya siya mata suke ciki, ta ciro daddaya zata ba yaran makotan da suka shigo mata da kayan daki, ta hada ma ko wani yaro da dubu daya, don duk baza su wuce su goma ba, Aunty Farida ta kasa daina kallon Khaleesat don taji dadin yanda ta ganta sosai ba kadan ba, Aunty Farida tace “Ki garra rabe raben tsaraban ki je ga ruwa can zan juye maki kiyi wanka sai ki karya” Khaleesat dai sai kirga Chocolates din take don har da na Step Siblings dinta take son ta cire. Karfe sha biyu da yan mintuna Nenne ta shigo gidan fuskarta babu yabo babu fallasa, har ta cire gyalenta zata rataye saman igiya ganin tsakar gidan cike da hayaki don su Mama Shatu na ta girkin siyarwan su ta fasa ta nufi dakin Umma da gyalen a hannu, ko amsa gaisuwan su Mama Shatu bata yi, tun da Umma taji muryar Nenne ta fara ma Khaleesat mita tace “Sai da nace ki je ki gaisheta kafin ta samu labari kin dawo, yanxu sai abinda ta manta ne bazata fada mana ba” Khaleesat dai na kwance saman gadon Umma tana danna wayarta, tun da tayi breakfast take son tayi bacci amma yan unguwan sai shigowa dakin Umma suke wai yi mata sannu da zuwa, alhalin da yawansu gulma ce ke shigo da su ba komai ba, ga Sha’awa da taki tafiya tun da ta shigo dakin kusan awa daya da rabi kenan, har da wasu makotansu biyu duk sun zauna sun ki tafiya ko me suke jira oho, Nenne na tsaye daga bakin kofa don labulen dakin a dage yake tace “To Zahra’u sai me don Khaleesah ta dawo anki zuwa a gaya min ko kuma a turata ta gaisheni har sai da almajirina ya shigo ya gaya min, naga dai ba don ni ba ai ko iyapot bazata sake zuwa ba balle har ta koma wata Amurka, kuma ba wani ya haifar min uban nata ba dai da za a dinga nuna min an fi ni iko da ita” Khaleesat dai tayi murmushi ta sauko daga kan gadon ta zauna kasa tace “Sannu da zuwa Nenne” Nenne ta kauda kai ta tsirtar da yawu ta kalli su sha’awa tace “Su kuma wa ennan fa? Baku ganin dakin babu sareri gashi duk ya dume bayin Allah sai shakan raumfashin juna ake, ke sha’awa zanin daddawan naki kika shigo dakin mutane da shi kika zauna? Haba ki dinga ji tsoron Allah mana sha’awa” Mikewa sauran makotan biyu suka yi suna kallon Khaleesat suka ce “Allah ya huce gajiya Khaleesah” Daga haka suka nufi kofa suna gaida Nenne suka fita, Nenne ta tsirtar da wani yawun tace “Tabdijam….” Sha’awa ta mike tace “Nenne shigowa ta kenan babu dadewa na zo yi ma khaleesah sannu da zuwa, ashe ma tun da safe ta iso, ina can na gama curin daddawa ban san ta dawo ba” Nenne ta bata hanya da sauri don kar ta goga mata jikinta, a haka Sha’awa ta fita daga dakin, Nenne ta kalli Umma tace “LallaiZahra’u kina da aiki, ke ba kazama ba ki bar mata kazamai su shigo maki daki su cıka da warin jiki har da me daddawa? duk dakin ki ya dume ba dadin shaka? yanxu da kin yi bakon kunya ina zaki ajiyesa, ga daki ba daki ba kamar zuciyar talaka, halan ina parida ta tafi don dai nasan da tana nan da tuni ta fatattake yan iska ta koresu, to dai duk komai ya zo karshe, Alhamdulillahi tun da Khaleesalı ta dawo lafiya zuwa nan da yan kwanaki kadan sai mu tattara mu bar tsinannen unguwan nan mu koma inda bawon Ailahn can dan albarka Ahmad ya siya mana, dama dai ni ce nace lallai sai an jira ta dawo tunda ta dalilinta aka yi mana wannan abun arziki baza mu yi mata butulci mu tare a gida babu ita ba, shi ne nace lallai ita zata jagorance mu zuwa sabon gidan a bude mu shiga cikin farin ciki, saukan al-qurani dama na saka anyi yafi a kirga a gidan, shikenan Allah ya rabamu da masu warin unguwan nan kuma haka” haka Nenne ta ajiye kwanon hannunta tace “Ga shi nan kwadon zogala na maki da naji ance kin dawo, to Ahmad din fa?” Khaleesat tace “Sal anjima zai shigo” Nenne tace “Ai ko bari in maza in tafi in dora masa tuwon shinkate da miyar agushi, in bada dubu biyu a siyo min nama me kyau in zuba a miyar” Daga haka ta juya da sauri tana yafa gyalenta ta rufi kofar fita daga gidan, Umma dai murmushi kawai tayi, Khaleesat ta kalleta tace “Dama Nenne ce tace baza a koma gidan ba Umma?” Umma tace “Gashi nan ta gaya maki kuwa, babanki ma bai yi na’am da gidan ba har yanxu” Mikewa Khaleesat tayi bata ce komai ba, ta dauko kwanon da Nenne ta ajiye mata ta bude, ai ko taji dadin ganin zogalen don hadadden hadi Nenne tayi masa. Wajen karfe hudu da rabi Jay ya zo gidansu Khaleesat, bayan sun gaisa da Umma da Aunty Farida Khaleesat ta dauko masa bottle water din da ta siyo masa ta ajiye masa, Aunty Farida dai sai godiya take masa ya ma kasa kallonta yana dan murmushi kawai, Khaleesat ta zauna gefen Uinmanta tana kallonsa babu ko kiftawa, tsadadden Gezna ne fari jikinsa, kayan sun masa kyau ba kadar: ba, anya ta taba ganinsa da manyan kaya kuwa, ya fito sak Hausa Fulani yau, Aunty Farida tace “Za ku karasa canı gidan Nenne da shi ai ko?” Khaleesat ta gyada mata kai sannan ta mike, Hijab dinta ne har kasa jikinta dama, ta dau nikab ta dora, ta fita tsakar gida tana jiransa, after almost 5 minutes ya fito daga dakin, step mothers dinta dake tsakar gida duk suka kafesa da ido kamar yanda suka yi san da ya shigo, Khaleesat dai ko kallonsu bata yi ba ta nufi kofar fita gidan ya bi bayanta, sai da suka fita kofar gida ya kalleta yace “What is this u are covering ur face with Halysaah?” Dariya tayi tace “Nikab ne baka sani ba?” Kallonta kawal yake suna tafiya, can yace “Tell me why you are covering ur face?” Tana murmushi tace “Saboga kallona za ayi ta yi a unguwan, kuma na saba sakawa in zan fita dama” Murmushi kawai yayi bai ce komai ba, a hankali tace “Ko in cire?” Ya kalleta yace “A’a, gwara haka, kinga za a rage kallon ki” A haka suka isa gidan Nenne. Nenne ta rasa inda zata sa Jay tsabar tarba, ta kinkimo masa gaba daya coolern tuwon da tukunyar miyan ta dire a gabansa, lemon kwalba kuwa dama guda biyar ta sa aka siyo masa da ruwan gora biyu, shi dai sai murmushi yake gashi ba yunwa yake ji ba, Khaleesat ma sai murmushi take, can ta cire nikab dinta ta ajiye, Nenne tace “In ma kunyata kake ji bari in shiga makota ka ci tuwonka ka koshi, don kai kadai nayi tuwon nan wallahi in ma baka ci da yawa ba wallahi bazan ji dadi ba, wanda ka rage ma a leda zan juye maka ka tafi da shi, ni ko gurin Zahra’u sai in je anjima ta tsam min tuwon daren ta…” Daga haka Nenne ta yafa gyalenta ta fita daga gidan, Khaleesat sai kallonsa take tana murmushi, ya cire hulan kansa ya ajiye gefe don har ya fara zufa ganin abincin da aka dire masa, yana kallon tuwon yace “Ya za ayi da tuwon nan Housemate, Ni fa na ci abinci kafin in fito wallahi” Khaleesat tayi dariya tace “Haka nan zaka tuttura ka ci, kasan tun yaushe take maka girkin nan kuwa?” Plate ta jawo ta saka tuwo daya, ya zaro ido yace “I can’t finish even quarter of this Halysaah, a koshe fa nake” Dariya kawai take bata tankasa ba ta bude tukunyar miyan dake ta kamshi ta zuba miyar a wani bowl daban, ta saka nama yanka hudu, ta maida tukunyar miyar gefe tace “Oya gashi” Ya kalleta yace “Where am I going to start from? Billah i am full, ki ci don Allah…” Khaleesat ta wanke haniunta ta dau cokali ta dibi tuwon da miya tana kallonsa tana…. Sun sauka garin Kano karfe takwas bai karasa ba na safiyar, motar da zai dauke su har ya iso airport din yana jira, bayan drivern ya saka luggages din a booth Jay ya bude ma Khaleesat back seat ta shiga tana ɗan murmushi cikin sanyin murya tace "Thank you" murmushin yayi mata shi ma ya bude front seat ya shiga, Khaleesat tried her best to stay positive kamar yanda Jay yace mata all through the ride home, but she is excited and still tensed at the same time, suna isa layinsu driver yayi parking dai dai inda Jay yayi instructing dinsa, Khaleesat ta sauke boyayyen ajiyar zuciya, Jay ya juya ya kalleta tayi murmushi a hankali tace "Thank you soo much Housemate" Har ta mance rabon ta kirasa da hakan a gabansa, shi dai kallonta kawai yake can yace "I don't understand why you are thanking me for" Langwabe kai tayi tana murmushi tana kallonsa yace "Za ki sani" Tuni Drivern ya sauka daga motar ya zaga zuwa booth, Jay ya sauka shi ma ya nuna masa luggages din ta, Khaleesat na sauka daga motar yaran makotansu na kyallara ido suka ga ita ce suka taho da gudu suka baibaiyeta suna Oyoyo, Jay dai ya juya yana kallon ikon Allah, yaran ta hada da boxes dinta su shiga mata da shi gida, duk suka fara rige rigen dauka, ta juya ta kalli Jay tana murmushi tace "Zaka shiga ciki ne?" Ya rungume hannunsa yace "A'a, amma da yamma zan zo in sha Allah" A hankali tace "Allah ya kai mu" Yana murmushi yace "Ameen Halysaah" Ita ma murmushin tayi tace "Amma zaka ɗan kwana biyu a Kano before going to Bauchi?" Yace "A'a, gobe zan tafi in sha Allah, Mai martaba is worried about how of recent we are traveling separately with Ajay which is unlike us, kinsan for many month now bama tafiya tare kuma ba haka muka saɓa ba, duk tafiya tare muke yi da shi, so his highness is worried may be we had issues that we are hiding away from him, muna Turkey ya kirani nace masa gobe zan shiga Bauchin in sha Allah...." Khaleesat dai tayi shiru tana kallonsa, can ta sauke idonta tace "Toh Allah ya kai mu goben" Yace "Ameen" Dubu hamsin kudin Nigeria ya dauko a gaban motar da alama Drivern ya sa ya taho masa da shi, ya mika mata yace "In case you will need anything Halysaah" Khaleesat ta zaro ido tace "A'a ni babu abinda zan bukata wallahi" Juyawa tayi zata bar wajen yace "Halysaah" Ta juyo amma bata ce komai ba, yace "Bana son kina min haka, ba ni na baki ba?" Ta marairaice tace "Wallahi ni babu abinda zan yi da kudi, beside i have money in my account, don Allah kayi hakuri ka bar shi Nagode" Ya hade rai yace "I didn't ask weda you have money or not, ni na baki ki amsa bana son musu" Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, lokaci daya jikinta yayi sanyi sosai, ganin kallon da yake mata ta ɗan risina ta amshi kudin a sanyaye tace "To Nagode, thank you soo much, Allah ya saka da alkhairi..." Bai jira ya gama sauraronta ba yace "Ki gaida min su Umma, sai na shigo anjima in sha Allah" Ta gyada masa kai tana kallonsa, ya zaga ya bude front seat ya shiga, Jiki a sanyaye ta juya zata shiga gida taga Mama Shatu da Mama Zubaida suna lekosu ta bakin kofa da 'ya yansu kanana gaba daya, sai a sannan ta lura da sabon kofar da aka saka a entrance din shiga cikin gidan nasu, lokaci daya su Mama Zubaida duk suka bar bakin kofar, ta kalli yaran da suka shigar mata da akwatunanta don duk suna tsattsaye a kofar gidan suna kallonta tace "Nan da minti talatin duk ku shigo ku amshi tsaraban ku kun ji" Murna suka fara yi gaba daya suna tsalle, ita dai tayi murmushi ta karasa ta shiga cikin gidan, step Siblings dinta duk suka yo kanta suka rungumeta suka dinga mata Oyoyo cike da farin ciki dama iyayen ne suka hana su fita kofar gida su je wajenta, Khaleesat tace "Ba ku je islamiyya bane?" Ɗan Mama Shatu me suna Sulaiman yace "Ba a biya mana kudin wata ba Aunty" Khaleesat tace "Nawa ne kudin watan?" Yace "Dubu uku ne" Khaleesat ta kalli Aunty Farida da ta fito daga cikin dakin Umma ta tafi cike da farin ciki ta rungumeta, Aunty Farida dai sai murmushi take ta dago kanta tana kallonta ganin yanda ta yi kumari sai wani glowing skin dinta yake, Aunty Farida tace "Sannu, ya hanya Khaleesah, Junaid din na kofar gida ne?" Khaleesat ta bude ido tace "Ya Jawwad fa nace maki ba ya Junaid ba, ai ya ma tafi yace sai da yamma zai dawo, Aunty su Islam sun tafi islamiyya ne? Ummata fa?" Aunty Farida tace "Su Islam na islamiyya, Umma tana daki" Khaleesat na murmushi tace "Toh ina zuwa in ba su Sulaiman kudin wata" Daga haka ta koma gun Step Siblings dinta dake tsaye sun yi cirko cirko a tsakar gidan suna kallonta, Dubu hamsin din hannunta ta cire dubu uku ta mika ma Sulaiman don shi ne babba cikinsu, sauran kananun yaran maza da mata ma haka ta dinga bin su tana kirga dubu uku uku tana mika masu, nan take sai da ta rabar masu da dubu talatin da shidda, suka dinga cewa saura Munzali, Khaleesat tace "In ya dawo ya sameni sai in basa" Murna yaran suka dinga yi a tsakar gidan, ta juya ta kalli inda kishiyoyin Ummanta ke zaune daga bakin kofar su ko wacce ta taɓe baki gashi sai naso suke, ga wani uban tagumi da Mama Zubaida ta zabga, karasawa tayi har inda suke ta gaida su with respect, a dakile duk suka amsa mata kamar dole, babu ya hanya babu komai sai ido da suke bin ta da shi, Khaleesat ta juya ta tafi dakin Ummanta don Allah Allah take ta ganta, tana shiga cikin dakin ta rungume Umma cike da farin ciki tace "Ummana na dawo" Umma na murmushi tace "To sannu da zuwa Khaleesah, ya hanya?" Khaleesat tace "Alhamdllh, Babana fa?" Umma tace "Ya fita kasuwa, Ahmad din ya tafi ne?" Khaleesat na murmushi tace "Eh ya tafi, yace sai da yamma zai zo" Umma tace "To Allah ya kai mu" Umma dai kallonta kawai take ganin yanda tayi kyau sosai, Khaleesat ta mike ta jawo akwatin ta zata bude wanda tulin Chocolates din da Jay ya siya mata suke ciki, ta ciro daddaya zata ba yaran makotan da suka shigo mata da kayan daki, ta hada ma ko wani yaro da dubu daya, don duk baza su wuce su goma ba, Aunty Farida ta kasa daina kallon Khaleesat don taji dadin yanda ta ganta sosai ba kadan ba, Aunty Farida tace "Ki gama rabe raben tsaraban ki je ga ruwa can zan juye maki kiyi wanka sai ki karya" Khaleesat dai sai kirga Chocolates din take don har da na Step Siblings dinta take son ta cire. Karfe sha biyu da yan mintuna Nenne ta shigo gidan fuskarta babu yabo babu fallasa, har ta cire gyalenta zata rataye saman igiya ganin tsakar gidan cike da hayaki don su Mama Shatu na ta girkin siyarwan su ta fasa ta nufi dakin Umma da gyalen a hannu, ko amsa gaisuwan su Mama Shatu bata yi, tun da Umma taji muryar Nenne ta fara ma Khaleesat mita tace "Sai da nace ki je ki gaisheta kafin ta samu labari kin dawo, yanxu sai abinda ta manta ne bazata fada mana ba" Khaleesat dai na kwance saman gadon Umma tana danna wayarta, tun da tayi breakfast take son tayi bacci amma yan unguwan sai shigowa dakin Umma suke wai yi mata sannu da zuwa, alhalin da yawansu gulma ce ke shigo da su ba komai ba, ga Sha'awa da taki tafiya tun da ta shigo dakin kusan awa daya da rabi kenan, har da wasu makotansu biyu duk sun zauna sun ki tafiya ko me suke jira oho, Nenne na tsaye daga bakin kofa don labulen dakin a ɗage yake tace "To Zahra'u sai me don Khaleesah ta dawo anki zuwa a gaya min ko kuma a turata ta gaisheni har sai da almajirina ya shigo ya gaya min, naga dai ba don ni ba ai ko iyapot bazata sake zuwa ba balle har ta koma wata Amurka, kuma ba wani ya haifar min uban nata ba dai da za a dinga nuna min an fi ni iko da ita" Khaleesat dai tayi murmushi ta sauko daga kan gadon ta zauna kasa tace "Sannu da zuwa Nenne" Nenne ta kauda kai ta tsirtar da yawu ta kalli su sha'awa tace "Su kuma wa ennan fa? Baku ganin dakin babu sarari gashi duk ya dume bayin Allah sai shaƙan numfashin juna ake, ke sha'awa zanin daddawan naki kika shigo dakin mutane da shi kika zauna? Haba ki dinga ji tsoron Allah mana sha'awa" Mikewa sauran makotan biyu suka yi suna kallon Khaleesat suka ce "Allah ya huce gajiya Khaleesah" Daga haka suka nufi kofa suna gaida Nenne suka fita, Nenne ta tsirtar da wani yawun tace "Tabɗijam...." Sha'awa ta mike tace "Nenne shigowa ta kenan babu dadewa na zo yi ma Khaleesah sannu da zuwa, ashe ma tun da safe ta iso, ina can na gama curin daddawa ban san ta dawo ba" Nenne ta bata hanya da sauri don kar ta goga mata jikinta, a haka Sha'awa ta fita daga dakin, Nenne ta kalli Umma tace "Lallai Zahra'u kina da aiki, ke ba kazama ba ki bar mata kazamai su shigo maki daki su cika da warin jiki har da me daddawa? duk dakin ki ya dume ba dadin shaƙa? yanxu da kin yi bakon kunya ina zaki ajiyesa, ga daki ba daki ba kamar zuciyar talaka, halan ina parida ta tafi don dai nasan da tana nan da tuni ta fatattake yan iska ta koresu, to dai duk komai ya zo karshe, Alhamdulillahi tun da Khaleesah ta dawo lafiya zuwa nan da yan kwanaki kadan sai mu tattara mu bar tsinannen unguwan nan mu koma inda bawon Allahn can ɗan albarka Ahmad ya siya mana, dama dai ni ce nace lallai sai an jira ta dawo tunda ta dalilinta aka yi mana wannan abun arziki baza mu yi mata butulci mu tare a gida babu ita ba, shi ne nace lallai ita zata jagorance mu zuwa sabon gidan a bude mu shiga cikin farin ciki, saukan al-qurani dama na saka anyi yafi a kirga a gidan, shikenan Allah ya rabamu da masu warin unguwan nan kuma haka" Nenne ta ajiye kwanon hannunta tace "Ga shi nan kwadon zogala na maki da naji ance kin dawo, to Ahmad din fa?" Khaleesat tace "Sai anjima zai shigo" Nenne tace "Ai ko bari in maza in tafi in ɗora masa tuwon shinkafa da miyar agushi, in bada dubu biyu a siyo min nama me kyau in zuba a miyar" Daga haka ta juya da sauri tana yafa gyalenta ta nufi kofar fita daga gidan, Umma dai murmushi kawai tayi, Khaleesat ta kalleta tace "Dama Nenne ce tace baza a koma gidan ba Umma?" Umma tace "Gashi nan ta gaya maki kuwa, babanki ma bai yi na'am da gidan ba har yanxu" Mikewa Khaleesat tayi bata ce komai ba, ta dauko kwanon da Nenne ta ajiye mata ta bude, ai ko taji dadin ganin zogalen don hadadden hadi Nenne tayi masa. Wajen karfe hudu da rabi Jay ya zo gidansu Khaleesat, bayan sun gaisa da Umma da Aunty Farida Khaleesat ta dauko masa bottle water din da ta siyo masa ta ajiye masa, Aunty Farida dai sai godiya take masa ya ma kasa kallonta yana ɗan murmushi kawai, Khaleesat ta zauna gefen Ummanta tana kallonsa babu ko kiftawa, tsadadden Gezna ne fari jikinsa, kayan sun masa kyau ba kadan ba, anya ta taɓa ganinsa da manyan kaya kuwa, ya fito sak Hausa Fulani yau, Aunty Farida tace "Za ku karasa can gidan Nenne da shi ai ko?" Khaleesat ta gyada mata kai sannan ta mike, Hijab dinta ne har kasa jikinta dama, ta dau nikab ta ɗora, ta fita tsakar gida tana jiransa, after almost 5 minutes ya fito daga dakin, step mothers dinta dake tsakar gida duk suka kafesa da ido kamar yanda suka yi san da ya shigo, Khaleesat dai ko kallonsu bata yi ba ta nufi kofar fita gidan ya bi bayanta, sai da suka fita kofar gida ya kalleta yace "What is this u are covering ur face with Halysaah?" Dariya tayi tace "Nikab ne baka sani ba?" Kallonta kawai yake suna tafiya, can yace "Tell me why you are covering ur face?" Tana murmushi tace "Saboda kallona za ayi ta yi a unguwan, kuma na saba sakawa in zan fita dama" Murmushi kawai yayi bai ce komai ba, a hankali tace "Ko in cire?" Ya kalleta yace "A'a, gwara haka, kinga za a rage kallon ki" A haka suka isa gidan Nenne, Nenne ta rasa inda zata sa Jay tsabar tarba, ta kinkimo masa gaba daya coolern tuwon da tukunyar miyan ta dire a gabansa, lemon kwalba kuwa dama guda biyar ta sa aka siyo masa da ruwan gora biyu, shi dai sai murmushi yake gashi ba yunwa yake ji ba, Khaleesat ma sai murmushi take, can ta cire nikab dinta ta ajiye, Nenne tace "In ma kunyata kake ji bari in shiga makota ka ci tuwonka ka koshi, don kai kadai nayi tuwon nan wallahi in ma baka ci da yawa ba wallahi bazan ji dadi ba, wanda ka rage ma a leda zan juye maka ka tafi da shi, ni ko gurin Zahra'u sai in je anjima ta tsam min tuwon daren ta..." Daga haka Nenne ta yafa gyalenta ta fita daga gidan, Khaleesat sai kallonsa take tana murmushi, ya cire hulan kansa ya ajiye gefe don har ya fara zufa ganin abincin da aka dire masa, yana kallon tuwon yace "Ya za ayi da tuwon nan Housemate, Ni fa na ci abinci kafin in fito wallahi" Khaleesat tayi dariya tace "Haka nan zaka tuttura ka ci, kasan tun yaushe take maka girkin nan kuwa?" Plate ta jawo ta saka tuwo daya, ya zaro ido yace "I can't finish even quarter of this Halysaah, a koshe fa nake" Dariya kawai take bata tankasa ba ta bude tukunyar miyan dake ta kamshi ta zuba miyar a wani bowl daban, ta saka nama yanka hudu, ta maida tukunyar miyar gefe tace "Oya gashi" Ya kalleta yace "Where am I going to start from? Billah I am full, ki ci don Allah..." Khaleesat ta wanke hannunta ta dau cokali ta dibi tuwon da miya tana kallonsa tana murmushi, yayi kasa da murya yana kallonta shi ma yace "Ko feeding dina zaki yi?" Murmushi tayi ta sunkuyar da kai don hakan take son tayi amma kunya ya hanata yi, yace "In dai zaki yi feeding dina zan ci wallahi" Dakewa tayi ta kai masa tuwon baki ya amsa yana murmushi, nan da nan yaji ya samu appetite din cin tuwon.... Bayan kusan minti talatin sai ga Nenne ta shigo gidan, cikin dubara Khaleesat ta ɗan matsa daga kusa da Jay, Nenne ta bude Cooler din tana kirga tuwon ciki tace "Kana nufin guda daya kacal ka ci tuwon?" Jay yayi dariyar da bai yi niyya ba yace "Ai na koshi ne kaka" Bata san tare ma suka ci guda dayan da Khaleesat ba, Nenne tace "Ban ji dadi ba gaskiya, duk tunanina zaka tashi da malmala biyu, ai don kai nayi tuwon wallahi" Khaleesat na murmushi tace "Ba ya cin abinci da yawa fa Nenne" Nenne tace "To wa ya sako da ke, Allah ya sa ma bake kika sa guda dayan a gaba kika ci ba" Jay ya shafa kai yace "A'a Kaka, ni na ci" Nenne ta nemi waje ta zauna tace "To sai a juye maka sauran a leda ka tafi da shi kawai" Shi dai murmushi kawai yake, Nenne tace "Ya labarin innar ka, da fatan tana lafiya, da yan uwa da abokan arziki" Yace "Alhamdulillah Kaka" Nenne tace "To madallah, Allah Ubangiji ya maka albarka, ka ce min a can Bauchi kuke da zama ko?" Jay yace "Eh can muke" Nenne tace "To kuwa in sha Allahu za ku gan ni a Bauchi kwanan nan don zan je duba wata 'ya ta, tana da yarinya me laluran shafar aljanu, gashi er ta zama budurwa abun dai ba dadi, in de na shiga Bauchi zan neme ka, dama in zan je Parida ke min rakiya tunda da wayewarta, a wace unguwan ku ke a Bauchi?" Jay na murmushi ya kira mata sunan wata unguwa daban, don har sannan dai Nenne bata san ɗan wani family bane, Nenne tace "Ai ko cikin kwanan nan zan shigo garin naku, rabona da zuwa yau kusan shekara biyu kenan" Jay yace "Allah ya kai mu lokacin Kaka" Nenne tace "Ameen" After some seconds ya daga kai ya kalleta yace "To yanxu Kaka tunda ta dawo yaushe za ku koma can Tudun Yolan?" Nenne tayi kasa da murya tace "Ai in sha Allahu nan da kwana uku za mu bar unguwan nan da daddare, don mutan unguwan ba yan arziki bane, bana son ma su san inda muka koma, kaga da daddare ai yafi sirri, zuwa gobe zan kira yan uwa da dangi duk a basu adireshin sabon unguwan mu hade a can ba sai sun taho nan yi mana rakiya ba tunda bama son yan unguwan su san inda za mu koma, shi dai Malam Ali har yanxu dar dar yake banda ni da nake tausan sa gaskiya da bazai bar unguwan nan ba, don yana gudun abinda zai je ya dawo, nace masa da xuciya daya kayi mana alkhairin nan ya cire komai a ransa, ba komai tattare da kai sai alkhairi don kai ɗan halaq ne" Jay yayi shiru don bai ma san me zai ce ba, ko da ya kawo ma mahaifin Khaleesat takardun gidan ƙin amsa yayi ya nuna masa he is much okay with where he is leaving with his family, yasan kawai yana gudun abinda zai je ya dawo ne, shi kuma da zuciya daya ya siya masu gidan ba don yana son anything in return ba, Nenne ta marairaice tace "Mu dai wannan abun arziki da ka mana ɗan nan Allah ya iya maka duniya da lahira, Allah ya raba ka da sharrin masu sharri, yayi maka albarka ya bude maka hanyoyin samu, Allah kuma ya ji ƙan mahaifinka ya sabunta masa rahama" A hankali Jay yace "Ameen" Nenne tace "Iya abinda za mu iya ce maka kenan ɗan nan, kuma babban dalilin da yasa ko yan unguwan nan bana son su san inda za mu koma shine kusan duk bayan kwana biyu sai ɗan iskan yaron nan Awdul ya zo unguwan nan, haka zai samu ubanta yayi ta masa magiya wai mu zai kara yaudara, har nan ya zo min na koresa da tabarya shi ne bai sake zuwa min ba sai dai yaje can gidan Malam Ali da ya raina, kuma ni ban ga alamar nadama a tare da shi ba, sam ba alkhairi ya dawo da shi ba, kaga tunda bamu san me ke baƙar zuciyarsa ba tunda har yarinyar nan ta dawo kasar nan gwara tun wuri mu lallaba mu tashi cikin sirri babu wanda zai san inda muka koma, Shikenan mun rabu da shi lafiya, don wallahi ban yarda da yaron ba, sam babu Allah a ransa, da kyar in ba wani shirin yake ta yi ba, kaga kuwa ai dole mu ba er nan kariya kar ya sake cutar mana da ita" Jay yayi shiru ya kasa cewa komai yana kallon Nenne, sosai hankalin Khaleesat ya tashi jin abinda Nenne ke cewa kan Abdul, ta juya ta kalli Jay a sanyaye, ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace "In sha Allahu komai ya zo karshe Kaka" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* Ur evidence 07087865788 HALYSAAH PAGE 85 Karfe tara da kusan rabi na dare Khaleesat ta shigo dakin Ummanta da sallama tana rike da ledan tsire wanda babanta ne ya siya mata, tun bayan isha'i take wajen baban nata tare da Nenne sai yanxu ta dawo daki, Jay sai da ya jira har Malam Ali ya dawo suka gaisa sannan ya bar unguwan daxu, zaunawa Khaleesat tayi kusa da Aunty Farida tana bude ledan naman tace "Su Islam har sun yi bacci" Umma dake kallonta tace "Nennen "Ne inen ta tafi ne?" Khaleesat ta girgiza kai tace "A'a tana can bata tafi ba" Aunty Farida tace "Baza ki ci tuwon naki ba?" Khaleesat ta langwabe kai tace "Nama zan ci" tuwon masara da miyar kuka Umma tayi, tana ganin tuwon daxu kawai tasan bazata ci ba, Aunty Farida tace "Ina kawarki Hajiya Safiyyah" Murmushi Khaleesat tayi tace "Tana can Maryland" Aunty Farida tace "Haba? Ita bata dawo hutun ba kenan?" Khaleesat tace "Yayanta yace sai next week za su taho gaba daya" Aunty Farida tace "Allah sarki, Allah ya kawo su lafiya, na zata tare ku ka dawo ai... Wai saura wata nawa yanxu ku kare karatun gaba daya?" Khaleesat tace "Bai wuce wata hudu ba, final semester kawai ya rage mana" Aunty Farida tace "Toh Allah Ubangiji ya baku sa'a, ya sa ku gama lafiya, ai kun kusa" Khaleesat tace "Ameen Aunty" Aunty Farida tace "To amma me yasa baku dawo har Junaid ba ya riga ku tahowa shi" Umma ta rike haba tana kallon Aunty Farida tace "Ikon Allah, kika san uzurinsa?" Ita dai Khaleesat murmushi kawal tayi bata ce komal ba ta matsar da takardan naman gabanta kusa da Aunty Farida bayan ta debar ma Umma nata.... Bayan Khaleesat taje tayi alwala ta dawo dakin Umma tayi shirin kwanciya, ta kwanta ta dau wayarta zata bude WhatsApp don rabonta da hawa tun da asuba da suka sauka Abuja kuma tasan Safiyyah dole zata yi mata magana, tana shiga WhatsApp din ta ga status din Ajay, sosai tayi mamaki don bata yi zaton yayi saving numberta ba, ta bude status din, daily reminder quote taga ya dora, ta tura masa Sticker sai taga yana ma online, WhatsApp call tayl ma Safiyyah bayan sun gama magana still bal mata reply ba, dama bata sa ran zai yi ba ta kashe data dinta ta kwanta. Washegari Khaleesat na idar da azkar din da take ta kira Jay, don yace mata karfe shidda zai wuce Bauchi kuma driving zai yi, bayan sun gaisa tace "Are you still leaving early?" Yace "In sha Allah Halysaah, har na gama shiryawa ma" Tace "Toh Allah ya tsare hanya, Allah ya kai ka lafiya, don't forget to pray please...." Yace "I won't dear" Tace "Amma kayi breakfast?" Yace "Yea, I took tea, idan na fita gida zan kira ki in sha Allah, ko za ki koma bacci ne?" Ta girgiza kai tace "A'a" Yace "Ohk then, I will call you" Daga haka ya katse wayar. Karfe goma sha daya Nenne ta shigo gidan ta nemi kujera er tsugunno ta zauna tana kwalo ma Umma kira, Khaleesat dake wanke wanke a tsakar gidan ta gaida Nenne, Nenne ta amsa tace "Ahamad din ya tafi Bauchin kuwa, yace min da sassafe zai bi hanya yau" Khaleesat tace "Har ya isa tun karfe goma" Nenne tace "Maa sha Allahu haka ake so, in kun yi waya ki ce ina gaishesa don Allah, ni ba waya gareni ba balle in kirasa, amma kar ki ce masa haka, kawai kice ina gaishesa ina masa bangajiya" Khaleesat na dauraye kwanon hannunta tace "Toh" Sai da Umma ta fito sannan Nenne ta amsa gaisuwan su Mama Zubaida a dakile ba tare da ta kalli inda suke ba, Umma ta zauna kan tabarman dake shimfide ta gaida Nenne, Nenne ta amsa tace "Ina parida" Bata rufe baki ba sai ga Aunty Farida ta fito dakin Umma, ita ma ta gaida Nenne ta amsa sannan tayi kasa da murya tana kallon Umma tace "Zaura'u, ina ga fa lallai lallai yau za mu bi dare mu bar unguwan nan, don daxu almajirina ke ce min yaga Awdul ya shigo unguwan nan da safe" Khaleesat ta daga kai da sauri tana kallon Nenne gabanta na faduwa, Nenne tace "Don haka baza mu biye All ba, In yaga duk mun tattara mun tafi ya biyo mu da dan akwatinsa, don ba irin maganar da ban masa jiya da daddare ba kan ya hakura ya amshi gidan nan da bawan Allahn nan ya siya masa hannu bibbiyu don da zuciya daya ya siya masa, amma tsoro ya hana Ali sakat, yace shi tsoro yake gaskiya...." Umma dai tayi shiru don bata san me zata ce ba, ita kanta hankalinta ba a kwance yake ba tunda Khaleesat ta dawo jiya don bata san wani mugun abun ke ran Abdul ba, tana ta tsoron kar ya samu labarin ta dawo ma, Nenne tace "Sabili da haka cikin dubara a kira makota duk a basu sadakar abubuwan da baza mu koma sabon gidan da shi ba, irinsu rubabbun tukwanen ku da katifa da tarkacen kwanukan ku, don babu abinda yaron bai zuba mana a gidan ba har kujeru da kayan gado, sannan na aika aje kasuwa a kira min Ali yayi maza ya dawo babu lafiya, so nake ya dawo mu ji yanda zai yi da matansa don baza su bi mu gidan nan ba gaskiya, in ma kauye zai maida su ya dinga zuwa can duk sati yana duba su to" Daga Mama Zubaida har Mama Shatu suka juya suna kallon Nenne, Nenne tace "Don ban ga inda za a kunna icce ko kuma a dafa abincin talla a wannan tanfatsetsen gidan da yaron nan ya siya mana ba, ko ina tas ne malale a kasa, komai sabo dal" Umma dake ta kallon Nenne tace "Ki dai yi hakuri Nenne don da mu da su Shatu duk daya muke a wajen Malam, dakuna shidda ne a gidan banda gini daban me daki daya da parlor da bandaki da kitchen, duk zai ishe mu Nenne" Nenne tace "Ke in baki da hankali ni ina da shi Zahra'u, banda karamin tunani irin naki kinga gidan yayi kalan Shatu da Zubaida? Kinga alamar kazanta zata samu muhalli a wannan tanfatsetsen gidan kamar a kasar waje?Na kirga dakuna biyar a gidan da katon parlor sal wawakeken kitchen, sannan har da bangaren me gida duk a cikin gidan, shima naga parlor ne sai daki da bandaki, to wannan na Ali ne, ke kuma ki dau daki daya, Farida daki daya, Khaleesah daki daya, yan biyunki ma a basu daki daya, daki daya da ya rage ya zama na saukan baki, ginin dake waje dama nace nawa ne ni zan zauna ciki kada wanda ya saka ma ginin ido, to a ina kika ga dakunan da za a zuba su Zubaida da 'ya yansu rakacaa idan ba dai baki de nankali ba? Ai babu guri a gidan, kai ko da wurin ma ni sam bazan amince in zauna da su Shatu ba sai dai ni in hakura da tarewa a gidan inyi zamana a Mariri har wa'adin da Allah ya dibar min a duniya ya cika in koma garesa, in kuma ance lallal lallai sai sun bi mu ta sai dai Malam Ali ya siyar da wnn gidan da nawa ya tafi unguwan yaku bayi ya siya masu gida me dakuna uku ya ajiye su da 'ya yan su, amma wannan gida kam ta silan Khaleesah aka siyesa ba wani shege ba, yau in tace níma bazan shiga ba ya zauna balle wasu yan iska Zubaida da Shatu, da ma suna ganin mutuncin mijinsu ne balle ni, balle ke karan kada miya da suka rena, yau watanni kusan hudu kenan babu abinda Ali ya rage su da shi a gidan nan, tun da Allah ya saka ma hatsin da ya fara siyarwa a kasuwa albarka bai ragi iyalinsa da komai ba komai korrai yi masu yake, amma sun ki dena abincin siyarwa don su yi ta ja masa zagi a gari, kudin makarantan yara idan ya basu sai su bi su kwace su bar yaran suyi ta yawo kamar almajirai a unguwa suna talla, to ina amfanin matan nan? Shi dai wannan yaro da ya basa jari Allah yayi masa albarka..." Nenne te kalli Khaleesat tace "Ya sunan abokin Ahamad din nan mara fara'a?" Khaleesat ta daga ido ta kalli Nenne, Umma dai tayi shiru don bata san me zata ce ba kuma, Aunty Farida ma dai is speechless, Nenne ta mike tsaye tace "Duk ki fito da tarkacen ki Zahra'u a bada su sadaka, in sha Allahu baza mu kwana a gidan nan ba, gwara mu koma gida me get yanda sai an kwankwasa ma za mu bude, shi kuma Ali ya dawo yasan yanda zai yi da matan nan nasa, bari inje in fara harhada nawa kayan, ina nan dawowa nan ba da dagowa ba, ni dama ba shirgi ne da ni ba, ai 'ya mace abar alfahari ce in dai ka tsaya kayi mata tarbiyya yanda ya dace, da Khaleesat bata da tarblyya uban wa zai kalleta balle har ayi mana wannan abun arzikin ta dalilinta, wannan kadai ya ishi yan baya izini, in za su tsaya su tarbiyyantar da 'ya yansu su zama na kwarai to su za su ci riba ba wani ba" Nenne na kai wa nan ta kalli Aunty Farida tace "Dauko gyalenki mu tafi ki tayani parida, in akwal abinda zan bayar kawai aiken ki zanyi kiyi sallama gida ki kira matar gidan ku taho tare, cikin sirri nake son ayi komai" Daga haka ta fice daga gidan, Aunty Farida ta mike ta dauko Hijab dinta ta bi bayanta ta fita, Bayan yan mintuna Mama Zubaida ta mike ta tafi ta bude kofar gidan tana leka waje taga Nenne da Aunty Farida har sun sha kwanan gidanta, dawowa tayi tsakar idanta, gidan tana ma Umma matsiyacin kallo tace ""Aikin banza, aikin hofi, kurı zauna kun tsara kayan ku shine kike son ki mayar da mu yan iska ke ga er slyasa, bayan duk kin san da tsarin, kin ga wannan sabon gidan In anyi duniya don manzon Allah sai ya zame maku bala'l da fitinar da yafi karfin ku, sai kun gwammace ba a baku ba, kuma waye bai san me Khaleesah tayi aka bata gidan ba? Mu duk bamu yi mamaki ba don mun san ba yanxu ta fara karuwanci ba, kuma muna nan dake sai ta jajibo maku abun kunyan da har ku mutu bazai goge ba daga ke har Nennen, bakin cikin abun kunyan ne kuma zai kar ki har lahira" Umma ta mike tana murmushi tace "Ni dai kullum ina maku tuni da ku koma islamiyya ko za ku samu saukin jahilcin nan, in sha Allahu kuma ni da zuri'ata babu abinda za mu gani sai alkhairi, Allah ya baku lafiyan cutar hassadan dake neman nakasa maku zuciya..." Mikewa Shatu tayi, Umma bata sake bi ta kansu ba ta shige dakinta, Khaleesat dai murmushi kawai take ta mike ta wuce daki ita ma, hayaniya Mama Zubaida da Mama Shatu suka dinga yi a gidan suna batanci da fadin mugaven kalamai har sal da makota suka shigo bada hakuri, ita dai Umma tuni ta sake labulen dakinta tayi kamar bata san da ita suke ba. Bayan la'asar Nenne ta dawo gidan da Aunty Farida, sai ga sha'awa da wasu makotansu Umma su uku sun shigo gidan su ma, duk Nenne ce tasa Aunty Farida ta shiga gidajen su ta kirasu, Nenne na tsaye har Umma ta gama fiddo duk kayan da zata bada, Nenne ta dau zannuwan gado biyu ta wurga ma Sha'awa da wata tukunyar Umma, haka ta dinga rarraba kayan tsakanin makotan da tasa aka kira mata suna girmamata awa enda ke ganin mtuncinta suna girmamata a unguwan, bayan sun kare ta mike tace "Toh gasu nan saboda Allah, shirgi ne suka mata yawa take bayarwa..." Su Mama Zubaida dai na tsaye bakin kofar dakin su fuskokinsu a murtuke suna kallon ikon Allah, Nenne ta sallami makotan duk suka fita gidan suna godiya kaca kaca, sal kuma ta kalli Umma tace "Kin gama hade kayayyakin naku na sa wa dake da yaran ki? Har fa mun je mun samo motar da zata kwashe mu anjima, karfe sha daya da rabi na dare muka yi da me motar" Umma tace "To Allah ya kai mu" Malam Ali ne ya shigo gidan da sallama, Nenne tace "Yauwa Ali, mu dai anjima za mu bar gidan nan kamar yanda na gaya maka jiya, yanxu ya za kayi da shirga shirgan matan nan naka? Kauye zaka tura su zuwa sanda zaka samar masu gidan haya ne ko ya zaka yi da su? Don babu wanda zai saura gidan nan balle Awdul ya samu kishin kishin din inda muka koma" Malam Ali dake kallon Nenne yace "Kauye kuma Baaba, kin fa ce min dakuna bakwal ne a can gidan" Mama Zubaida ta gyada kai tana girgiza kafa alamar atoh dai, Nenne ta saki baki tana kallonsa, can tace "Sai aka yi yaya da nace maka dakuna bakwal ne Ali?" Malam Ali yace "Kawai ayi hakuri duk a koma can din tunda kince a bar unguwan, don ni gaskiya yanxu bani da isasshen kudin kama haya Baaba" Umma ta kalli Malam Ali tace "To kuwa sai kasan yanda zaka yi da su Malam, don wallahi babu warce zata bi mu gidan nan, in ko kace sai sun bi mu sai dai duk a fasa shiga" Nenne tayi wani dariyar keta har da kyakyatawa sannan ta ja kujera ta zauna tana kallon Umma da mugun mamaki kamar ranan ta fara ganinta, Aunty Farida kanta kallon Umma take da mamaki, Balle Malam All da yayi shiruu shi ma yana kaitonta ya kasa cewa komal, Nenne ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Allah ya mak albarka Zahra'u, in ya ga dama ya basu kudi ko wacce ta kama hanyar kauye, duk sanda Aliah ya hore masa sal ya nema masu hayan a birni" Malam Ali yace "Toh Shikenan, sai ayi hakan kawai" Mama Shatu ta fashe da kuka tace "Amma ka cucemu ka ci amanar mu Malam, wallahi sai Allah ya mana sakayya" Mama Zubaida ma ta fashe da kuka tace "Kuma kar ka manta hukuncin wanda baya adalci cikin iyalansa, wato ka fifita Zahra'u da 'ya yanta a kan mu kenan kake nufi, alhalin duk matsayinmu daya a wajenka tunda mu ma matan ka ne, kaji tsoron Allah Malam" Nenne tace "Ji bakaken jahilai, Alin ne ya siya gidan ko kurra shi ya zuba kayan cikin gidan da ya maku rashin adalci? Gida al na Khaleesah ne da uwarta kuma yanda suka ce haka za ayi, ko Ali bashi da ta cewa tunda babu biyar dinsa a gidan, balle ni uwarsa, don ma ku ji in gaya maku" Malam Ali dai ya nufi kofa ya fita daga compound din, Aunty Farida tayi murmushi ta koma ta zauna, har sannan Umma bata gaya mata abinda su Mama Shatu suka mata ba shi yasa ma tayi mamaki da action din Umma.... A daren ranan Malam Ali ya ba su Mama Zubaida da Mama Shatu kudin motan zuwa kauye da tulin 'ya yansu, gidan mahaifinsa na can kauyen har yanxu sai dai ginin kasa ne me dakuna hudu kuma babu kowa cikin gidan, sun ci kuka har sun gode Allah, karfe sha daya na dare motar da Nenne da Aunty Farida suka tafi suka yo haya can cikin gari ya iso kofar gidan, aka kwashe su gaba daya sai sabon gida, babban bakin cikin su Mama Zubaida basu san Inda su Khaleesah za su koma ba balle su yada a Mariri kowa ma yasan inda suka koma. Jay na zaune parlon Maminsa yayi nisa tunanin da yake, a karo na farko a rayuwarsa kenan da yaji sa kamar ba a parlon Maminsa ba don gaba daya he is not comfortable ya kasa sakewa, tunani iri iri ne ke yawo a zuciyarsa, tun jiya da ya iso Bauchi kawai gashi nan ne gashi nan dai, lokaci lokaci yake kallon Ajay dake zaune gefensa comfortably yana danna wayarsa, Ajay har ya mance rabon da ya shigo bangaren Mamin Jay a masarautan, duk da bata fiye zama ba sai tayi wata biyu ma bata gidan, Mami ta fito parlon daga Bedroom dinta don tana waya Jay ya shigo dakin sai kuma ya koma parlor shiru shiru kuma bata ga ya sake shigowa dakin ba bayan ta gama waya, dama yace mata da maganar da za su yi daxu saboda hakan ne ma bata fita ba don akwai inda zata, sai bayan da ta fito ne taga ashe shi da Ajay ne, Ajay ya ajiye wayarsa va gaisheta ba tare da ya kalleta ba, kallo daya tayi masa ta amsa sannan ta zauna tana kallon Jay tace "Ina ta jiran ka tun daxu Jawwad, yanxu in tafi inda zan je kenan sai na dawo kawai?" Jay ya daga kai ya kalleta yace "Ai yanxu za mu yi maganar da nace Mami" Marni ta kalli Ajay, sai kuma ta kallesa tace "Yanxu? Ka dai bari da daddare don fita zan yi yanxu gaskiya" Ta fadi hakan ne don bata ga dalilin da zai ce zai mata magana duk da bata san ko na menene ba kuma ya shigo mata da Ajay, tana bakin cikin yanda sam Jay bashi da sirrin kansa kamar tare aka haifosu duniya da Ajay, Ajayn da babu wanda ke sanin komai game da tasa rayuwar, bata jira cewar Jay ba ta mike ta wuce dakinta zata dauko mayafi, kafin ta fito har Ajay ya bar parlon, Jay ya bi sa da kallo, har cikin ransa baya jin dadin yanda Mami ta dauki Ajay, he felt really heartbroken, mikewa yayi kawai ya bi bayansa.... *Pls masu taya ni posting pages din Arewa da suke mayarwa typing ta nan WhatsApp kafin inyi posting su yi hakuri su daina saboda ina yin advert a pages din, be patient idan nayi update sai ku watsa duk inda ku ke son watsawa amma don Allah ku dena posting before I do because of people's advert that I have on ground, although naga pages daya kuke posting din amma dai kuyi hakuri ku dena, thanks...* https://chat.whatsapp.com/DtKRIBCkfHoGuMzWcuq87V?mode=ac_t HALYSAAH 86 Khaleesat bata yi zaton gidan da Jay ya siya ma iyayenta yafi yanda ta tsammacesa a hoto ba, she was totally speechless don gida ne lafiyayye kuma a unguwa me kyau sosai, babu abinda ba a zuba a cikin gidan ba, ga wuta da ruwa 24/7 don Solar ne a gidan, maimakon tayi farin ciki sai ta zamto so emotional tana kara jin Jay a ranta, tasan a yanxu dai bata da enough words da zata yi amfani da su wajen fara yi masa godiya tayi expressing how grateful she is, balle ko zata yi hakan ma bazai saurareta ba, Nenne kam baki yaki rufuwa don farin ciki tasa masa albarka tare da iyayensa yafi cikin Kwando, Chalet din da ta mayar nata tsabar murna bata kwana ciki ba, a main building din gidan ta kwana a parlor kan lallausan bargo da sabon Pillow ga AC da ta sa aka kure mata, ai ko da asuba ta tashi hanci duk sun toshe, sai ta ɓige da cewa yawace yawacen da suka yi jiya cikin gari da Farida ne ƙuran garin Kano ya saka mata mura, gari na wayewa Nenne aka dinga goge goge da share share a parlon duk da babu ko digon datti, Aunty Farida da Khaleesat kuma na kitchen suna girka breakfast don sun taho da few food stuffs dinsu na can gidan, Umma ta fito parlor zata amshi wayar Aunty Farida ta kira Malam Ali don nata babu kati, Nenne ta matse tsumman hannunta da take goge tsadaddun kujerun parlorn da shi tace "Kinga dai Ali da ya dawo nan ya kwana cikin ni'imar Ubangiji gwara ya kwana a takure cikin zafi da sauron Mariri, ko da yake ban ga laifin sa ba kinga dole zai yi ma su Zubaida rakiya zuwa tasha kuma zai ɗan hada masu hatsin da za su tafi da shi tunda su ma suna da hakki gwara ya sallamesu cikin mutumci su tafi" Ita dai Umma bata ce komai ba, Nenne tayi kwafa tana ci gaba da goge gogenta tace "Dama ai ance mahakurci mawadaci, yanxu da kika yi hakuri Zahra'u baki ga ribar hakuri ba? Ni nasan Allah bazai bar ki haka ba don hakurin ki abun dubawa ne, gashi yau dai kin ga riban hakurin ki, ni dai kullum addu'ata shine Allah Ubangiji ya albarkaci 'ya yan da kika haifa ya tsare maki gabansu da bayansu, gashi wai tun Khaleesah bata fara aiki ba mun fara cin moriyarta saboda kyawawan halayyan uwarta da irin tarbiyyar da aka mata, cikin ruwan sanyi kuma Allah ya rabaki da matsiyatan kishiyoyin ki lafiya duk tuggun da suka maki ya kare kansu, ke kika ci riba" Umma dai ta ɗan yi murmushi bata ce komai ba, amma da Nenne tasan action dinta na ƙin amincewa a taho da su Mama Zubaida jiya har baccin kirki sai da ya hanata da bata ce haka ba, gaba daya rasa sukuni tayi tana jin bata kyauta ma kanta ba tunda ita ma bata san Allah zai bada gidan nan ba, sannan ba dubaranta ko wayonta bane yasa Allah yayi mata hakan, yanxun ma wayar Aunty Farida da zata amsa Malam Ali take son kira tayi masa magana ko zai samu ya lallaba Nenne tayi hakuri su dawo gidan kawai, gudun tsine mata da Nenne zata yi yasa bata gaya mata abinda ke ranta ba kawai ta nufi kitchen ta tambayi Aunty Farida inda wayarta yake, bayan Aunty Farida ta gaya mata ta juya ta bar kitchen din, Aunty Farida na kallon Khaleesat dake juya miyan kan wuta don shinkafa da miya suke dafawa for breakfast, tace "Ina jin ki Khaleesah" Khaleesat dai bata kalleta ba tana ci gaba da juya miyan a hankali tace "Haka muka yi da shi Aunty, ni dai ban ce masa komai ba har yanxu" Aunty Farida dake ta kallonta cikin sanyin murya tace "Amma kina ganin iyayensa za su amince masa cikin sauki duba da status dinki ga kuma irin gidan da ya fito Khaleesat? Bana son ki saka ranki da yawa cause anything can happen, kin ga dai ai baza a boye ma iyayensa status dinki ba a yanxu, in ma aka boye magana irin wannan baya buya Khaleesah" Khaleesat ta kasa kallon Aunty Farida amma sosai taji jikinta yayi sanyi, taji ƙafafuwanta sun kasa ci gaba da ɗaukan ta, all this while ita bata taɓa kawo wannan tunanin a rai ba ko don tasan babu abinda ya shiga tsakaninta da Abdul ne yasa hakan, to amma bayan ita da Abdul din wa ya san ba abinda ya shiga tsakanin su? Aunty Farida ta jingina jikin cabinet ita ma dai duk jikinta a sanyaye, she wish everything will be easy as it seems now, amma gidan sarauta abun su sai su, babu abinda ya kara kashe mata jiki sai zancen Hadiyah da kuma alakarsa da Hadiyar da Khaleesat ta gaya mata, amma don ta kwantar mata da hankali ta sauke ajiyar zuciya tace "Ki ci gaba da addu'a Khaleesat, Nima zan taya ki, Umma ma zan yi mata magana duk za mu taya ki da addu'a, Allah Ubangiji ya kawo komai da sauki, kuma Allah ya tabbatar da alkhairi" Har sannan Khaleesat bata ce komai ba, Aunty Farida ta nufi kofa ta fita daga kitchen din, sai a sannan Khaleesat taji hawaye masu zafi sun zubo idonta, ta juya tana kallon windown kitchen din babu ko kiftawa, da Aunty Farida bata ankarar da ita ba da bazata taɓa hango kalubalen dake tattare da aurenta da Jay yace zai yi ba, she never saw all this coming, kasa controlling kanta tayi ta duka a hankali kitchen din hawaye na zubo mata, sai yanxu ta kara tabbatar da masifaffen son da take ma Jay a ranta, she can't imagine loosing him, hade kanta tayi da gwiwa hawaye masu zafi na zubo mata tana shesshekan kuka.... Aunty Farida na shiga dakin Umma ta sameta tana waya da Malam Ali, hakan yasa ta juya ta bar dakin, sosai wannan maganar da Khaleesat tayi mata ya tsaya mata a rai, she don't want her to go through another heartbreak, kuma ta lura tayi zurfi a son nasa ita ma with the way she reacted, tana shigowa parlor Nenne tace "Zuwa nan da anjima kadan fa za mu fara ganin yan uwa sun zo mana Allah ya sanya alkhairi Parida, er shinkafar nan zata isa a girka a ɗan tarfa ma kowa a kwano kuwa?" Aunty Farida tace "Idan mun karya za mu fita kasuwa da Khaleesat, da kudi a hannuna sai a siyo duk abubuwan da ya kamata...." Nenne tace "Allah Ubangiji dai ya baki miji nagari kema kiyi auren ki Parida, bauta kam kin bauta ma yayarki, abun ki bai rufe maki ido ba sam, kin rike zumunci gaskiya" Ita dai Aunty Farida kawai tayi murmushi bata ce komai ba, Nenne tace "Dama mun taho da tabarmin mu, su za a shimfida a tsakar gida babu shegen da zai shigo mana nan a lalata mana sabon waje, kowa yayi Allah ya sanya alkhairinsa daga tsakar gida ya kama gabansa" Wajen karfe goma da rabi Aunty Farida da Khaleesat suka bar gidan za su je kasuwa siyayya, Khaleesat har ta mance rabon ta shiga damuwa irin wannan da take ciki yanxu, sau biyu ta kira Jay daxu taga bai dauka ba shine damuwar nata ya linku akan wanda take ciki tun bayan maganganun Aunty Farida daxu a kitchen, Aunty Farida na kula da yanda tayi sanyi gaba daya bata da kuzari tun daxu, bayan sun shiga adaidaita Sahu da zai kai su kasuwan Aunty Farida tayi kasa da murya tace "Damuwa kike son sa ma kanki Khaleesat?" Khaleesat tayi murmushin karfin hali tace "A'a Aunty" Da sauri ta kauda zancen tace "Safiyyah ce ma daxu ta min voice tana kuka wai kilan shirgata yayanta yayi, gashi ta saka ran dawowa, ni dama a raina nasan ba lallai ya barta ta dawo ba" Tana dariyar karfin hali ta kare maganar, Aunty Farida tace "Ai ko bai kyauta mata ba, Allah sarki baiwar Allah" Har suka isa kasuwan Khaleesat was trying to act alright, amma Aunty Farida tasan deceiving kanta kawai take, Aunty Farida bata zo kasuwa da Khaleesat with the expectation of her buying anything ba don bata san tana da kudi ba ma, ita dama Aunty Farida da dubu ɗari biyu ta shigo kasuwan domin ta ɗan tsintsintar masu abubuwan da za su bukata na gida, har da su Bucket da sabulu da omo da su tsintsiya da mop, duk dai wani abun amfanin gidan, sauran kudin kuma tayi maneji ta ɗan hada masu kayan abinci da cefane ko babu yawa, amma nan take Khaleesat tayi withdrawing 1M a kasuwan, don kudi ne sosai a account dinta wanda Jay ke tura mata a kai a kai na Uber da kuma wasu abubuwa idan tana bukata barin sanda ya dade a Nigeria bai dawo ba, sanda yake Nigeria kuma Ajay ma ya amshi account dinta during that period ya tura mata kudi multiple times for her transportation to school and in case she needs to get anything for herself, duk da abubuwa da yawa shi yake siya mata a lokacin, kuma in ya tashi tura mata kudin shi ma ba kudi kadan yake saka mata ba, sannan ga 5000 dollars da Mai martaba ya bata, dama Safiyyah taki amsan wanda ta bata a ciki, Jay kuma ya amshi kudin yayi mata transfer dinsa gaba daya a account dinta, ganin uban kudin da Khaleesat ta cire Aunty Farida ta fara fada tace "Baki da hankali ne? Ke da ba gama karatun kika yi ba zaki ciro wannan kudi haka" Khaleesat tayi murmushin karfin hali tace "Aunty in babu ai bazan cire ba, akwai kudi a account din ne" Sai wajen karfe daya suka koma gida da siyayya maƙil, a compound suka tarar da yan zuwa sanya alkhairi Nenne ta shimfida masu tabarma ta hada kowa da pure water, tana zaune kan kujerar plastic ta ɗora kafa daya kan daya, ita ma Umma na zaune tsakar gidan don ta rasa yanda zata yi da Nenne, ko kadan bata ji dadin barin jama'a da tayi a tsakar gida ba taki bari su shiga cikin gidan. Nenne tayi kicin kicin da fuska don bata so su Aunty Farida sun shigo da kayan da suka siyo kan idon mutanen dake tsakar gidan ba, a haka dai su Islam da Noor suka dinga diban kayan da za su iya dauka suna kai wa cikin gidan, Khaleesat ta dau iya wanda zata iya dauka sannan ta wuce ciki ta tafi daki tayi wanka ta dauro alwala tayi sallah sannan ta kwanta, sosai hankalinta ke a tashe ganin Jay bai biyo kiranta ba har lkcn, Umma ta shigo daki tana kallonta tace "Khaleesah ke da ke karatu har yanzu menene na kashe kudi har haka?" Khaleesat ta kalli Umma tace "Na fa ce ma Aunty Farida akwai kudi a account din ne Umma" Umma tace "Toh Allah yayi albarka, ki tashi ki zubo abinci ki ci" Khaleesat tace "Anjima zan ci Umma" Umma tace "Allah ya kai mu" Daga haka ta fita daga dakin, Khaleesat ta koma a sanyaye ta kwanta, gaba daya ta rasa me ke mata dadi a ranta, hawaye taji ya cika idonta ta rufe fuskarta da Pillow ta fara shesshekan kuka a hankali.... Nenne ta fita ta zagaye unguwan tana neman almajirai da za su kama buhunhunan shinkafar da su Aunty Farida suka siyo a shiga da shi kitchen, da kyar ta samo almajiran biyu ta dawo tana mitan su Mariri yaushe za a nemi almajirai a rasa, daya daga mutanen dake zaune tsakar gida tace "Ai da kin mana magana mu kama mu shiga da shi ciki Nenne" Nenne tayi banza da ita tana tafe almajiran na biye da ita a baya har aka shiga da buhunhunan kitchen, naira hamsin ta basu suka tsaya suna kallon ta, tace "Lafiya ku ke kallona haka?" Wata er cousin din Malam Ali tayi dariya tace "Ya masu kadan Nenne, ke baki ga unguwan ta masu kudi bace, ai hansin ta masu kadan" Nenne ta juya ta kalli almajiran baki bude, kafin tace komai Umma ta mika masu dari biyu su hada da Naira hamsin din, suka amsa suka fita daga gidan, Nenne ta kalli Umma tace "Kin ji almajirai kamar barayi, mu Mariri yaushe almajirai za su yi haka? Kudin ne ya maki yawa kika basu dari biyu, ai niyyar ce masu su shiga su fito da buhunhunan shinkafar nake da shi" Nenne bata rufe baki ba aka rafka sallama bakin gate, duk aka juya ana kallon gate din gidan sai ga Sha'awa da yan Mariri su hudu sun shigo cikin compound din kafafuwansu butu butu da ƙura, Nenne da ta girgiza sosai ganinsu tace "Su waye nake gani haka, daga ina?" Sha'awa na washe baki tace "Su mu ne Nenne, Sha'awa ce da su Maman Sagir da Maman Balki da Maman Shehu, sai sabuwa" Nenne da zufa ya keto mata ta ja kujera ta zauna da kyar tace "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'una, wa ya nuna maku gidan?" Ita kanta Umma was so shock amma hakan bai hanata dinga ce masu sannu da zuwa ba da murmushinta duk da gaba daya hankalinsu na kan Nenne da ta tsare su da tambayoyi cikin kidimewa, Sha'awa tace "Almajirin ki ne wai an taɓa zuwa da shi yayi share share da goge goge sanda aka siya gidan, ai ko ranan yayi ma Salisun Tabawa kwatancen gidan ashe Salisu sun taɓa zuwa aikin pilamba a wani gida a Tudun Yola, shi ne muka sa yayi mana kwatance, tun karfe sha dayan safe muke neman gidan sai da muka zaga kaf Tudun Yola muna cewa sabon gidan da aka tare jiya da daddare muke nema, da kyar wallahi aka gano gidan da taimakon wasu yara, ga uban kudin mota duk bamu san haka unguwan ke da nisa ba, ko sallan azahar bamu yi ba ga la'asar ta gabato" Nenne ta rike kai tace "Hu....huhu, ashe dama ƊanLami munafiki ne ɗan iska ban sani ba nake alaka da shi jama'a? Wa iyazubillahi" Ita dai Umma ta shimfida masu wani tabarma tana welcoming dinsu da fara'a kafin Nenne tayi recovering daga shock din da ta shiga ta fatattake su daga gidan don tsaf next action dinta kenan. Wajen karfe takwas na dare Jay ya shigo parlon Maminsa ta dalilin kiransa da tayi har sau biyu a waya, tun da ya shigo parlon take kallonsa har ya zauna, tace "Ina ka shiga ne tun daxu Jawwad?" Ya ajiye wayarsa ba tare da ya kalleta ba yace "Ina gidan ai" Mami tace "Duk na bi na damu kace zaka min magana me muhimmanci saboda kai ban je inda zan je ba yau amma don rashin sanin ciwon kai da ka tashi shigowa bangaren nan sai ka shigo min da Junaid, to da a gaban Junaid din kayi niyyar min magana saboda baka da sirrin kanka Jawwad? Ko har ka fesa masa ne shi" Ya daga kai ya kalleta, can yace "Ni ban san me Junaid yayi maki da yayi deserving wannan ill treatment din ba Mami, Billah bana jin dadin wannan abun da kike masa, beside ni na shigo da shi kinsan baya taɓa saka kansa a abinda bai shafesa ba ai, he is even sick but still followed me and you treated him that way, I wasn't happy at all Mami, Ni Ajay na daukesa ne kamar brother dina da kika haifa bayan ni, kuma shi ma haka ya daukeni, then why all this Mami?" Mami ta katse sa tace "Toh ubana, dama ai ka saba zuba ma idonka toka ka gaya min son ran ka akan Junaid, I have no issue with Junaid coming to my part, my issue in here is u bringing him to my part when you know we have an important issue to discuss, kai abubuwa nawa ka sani a kansa? Ina ce kawai sai dai kaga yayi abun sa, Duk ya maida kai wani wanda bai san ciwon kansa ba yayi ta controlling dinka yanda ya ga dama, ya maida kai wawa, baka da kwakkwaran say din kanka sai abinda yace maka kayi, haba Jawwad, yaushe zaka yi hankali ne wai?" Jay bai sake ce mata komai ba a parlon yana kallon direction daban, tace "Me ya samesa da yake rashin lafiya? Shi kullum yana dawowa gidan nan sai yace rashin lafiya, meye ma'anar hakan?" Still Jay bai ce mata komai ba, Mami tace "To Allah ya basa lafiya, amma ya kamata ka gaya masa yaje kakarsa ta basa maganin baki, daga ya tsallaka kafa ya shigo gidan nan sai yace rashin lafiya, in kuma da wata manufar da yasa yake hakan it's left to him" Jay was still silent, da ace akan wani abu daban ne ya bata rai haka da yanxu ta fara lallabasa tana kokarin ganin ya sake fuskarsa don babban damuwarta Jay ya ɓata rai, amma akan Ajay duk fushin da zai yi yayi zai sakko da kansa ba lallabasan da take yi, abun na bakanta mata rai yanda ya maida kansa kamar wawa wajen Ajay yana juyasa yanda ya ga dama, in Ajay yace kar yayi abu to fa abun nan komin kyansa bazai yi ba, in ko yace yayi to zai yi, ko kuma in tace yayi abu sai yace Ajay ya basa shawaran kar yayi saboda abu kaza, to ina dalili ita da ɗan ta, in kuma tace yayi sai yace ai Ajay yace kar yayi ya kuma zayyano mata reasons dinsa, Mami tace "To ka ci abinci kuwa? Ga abinci na ajiye maka tun daxu shiru shiru baka shigo ba" Jay yace "Na ci" Mami har ranta ta tsani abinda zai ɓata ma ɗan nata rai ko ya yake, ta kwantar da murya tace "To ina jin ka Son, maganar meye za mu yi, speak to me dear" Mikewa yayi ya dau wayarsa yace "I don't want to talk about it now Mami" Yana fadin haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo, wato yayi fushi ta taɓo kanin ubansa Ajay, Mami tace "Toh ga dai abincin idan kana bukata, ko kuma ka tafi maku da shi ku ci da Ajayn a can ɓangaren nasa" Tuni har ya fice daga parlon, Mami ta kyabe baki don ta san zai ma huce, anjima zata dau abincin ta kai masu can shi da Ajayn su karata. Jay na komawa bangaren Ajay ya tarar da Mai martaba zaune a parlon, zaunawa yayi gefen Ajay da ya ajiye PS Controller din hannunsa bayan mahaifin nasa ya shigo, Mai martaba na kallon Jay yace "Ashe jikin nasa ma yayi sauki" Jay ya sauke kansa yace "He is much better now ranka shi dade" Mai martaba ya jinjina kai yace "To maa sha Allah, ina jin Hajiya ma gobe zata shigo in sha Allah" Jay yace "Allah ya kawo ta lafiya" Mai martaba yace "Ya ku ka yi akan maganar yarinyar nan da Fulani?" Jay ya sauke kansa cikin ladabi yace "Anjima nake son zan mata magana ranka shi dade" Mai martaba yace "Alright then, sai ka gaya min duk yanda ku ka yi" Jay yace "In sha Allah ranka shi dade" Mai martaba ya kalli Ajay da kansa ke kasa, ya mike yace "Allah ya tashe mu lafiya" Duk suka amsa masa da "Ameen" Ya nufi kofa, Ajay ya dau fruit da yake sha kafin Abban nasa ya shigo ya ci gaba da sha, Jay ya duba wayarsa dake vibrate yaga Khaleesat ce ke kiransa, kallon screen din ya dinga yi don yana ta son zai kirata tun daxu but he was together with Ajay tun safe don in bashi da lafiya ya dinga yi ma mutane surutu kenan, kuma baya son Jay na nisa da shi, katse kiran nata yayi ya mike ya tafi kan kujera ya zauna sannan ya kira ta, tana picking yayi kasa da murya yanda ita kadai zata ji sa yace "Halysaah, I am sorry I didn't call all through, ya kike ya gida?" Khaleesat dake sauraronsa tana jiran jin excuse dinsa tace "Lafiya lau" From her intonation he knows she is not happy, ya sake yin kasa da murya yace "I am so sorry Halysaah, Ajay ne ba shi da lafiya but he is better now, shi yasa kika ji ni shiru all through, hope you will forgive me?" Khaleesat tayi shiru jin abinda yace, can a hankali tace "To Allah ya basa lafiya, tun yaushe ne bashi da lafiya?" Jay yace "Da safe, amma yaji sauki ma" Tace "Ku na tare ne?" Shiru ya ɗan yi, sai kuma ya ɗan kalli Ajay yace "Nop" Tace "Toh Allah ya basa lafiya" Yace "Ameen, so ya su Umma and everyone back home, kaka tace gobe za ku koma Tudun Yolan ko?" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "Ai mun ma koma jiya" Ya ɗan bude ido yace "Haba dai?" Ta gyada masa kai tace "Uhm" Mikewa yayi ya fita daga parlorn Ajay ya bi sa da ido, bayan Jay ya kulle kofar parlorn yana tafiya down the long hallway yace "So now tell me the truth gidan yayi maki Halysaah?" Kasa ce masa komai tayi, yace "Are you there Halysaah?" A sanyaye tace "Ban san me zan ce maka bane, i don't even know where to start thanking you from...." katse ta yayi yace "Come off it pls Halysaah...." Hawaye taji ya taru idonta, yayi kasa da murya yace "I miss you soo much Halysaah" Tayi murmushi don bai san ta fi sa missing din da yake cewa ba, sun kusa minti ashirin suna waya daga karshe yace "Zan kira ki zuwa karfe goma da rabi in sha Allah Halysaah" Tace "Toh Allah ya kai mu" Yace "Ameen Dear" Bangaren Ajay ya koma suka ci gaba da game din da suke, wajen karfe goma saura Mami ta shigo parlorn Ajay tare da daya daga worker din palace din dake biye da ita da abinci, bayan worker din ta ajiye abincin ta gaida Ajay da Jay cikin ladabi sannan ta juya ta fita, a kujeran da Mai martaba ya zauna Mami ta zauna, Ajay ya gaisheta bayan ya ajiye Controller din hannunsa, Mami na kallonsa tace "Kai baza kaje kakarka ta nema maka maganin baki ba, ko baka gaji da ciwace ciwacen da kake a gidan nan ba, kowa ya bude baki yace Junaid, ko da yake maganinka kenan gwara kayi ta yin abin da za a dinga saka ka a bakin duniya, in zaka sauke wannan shegen girman kan naka ka bi mutane a yanda suke so ka zauna lafiya da su then you will be doing justice to ur self, in kuma kace baza ka bi su ba to ya rage naka" Shi dai Ajay bai kalli inda take ba, Jay kuwa sai kallon Mami yake cikin bacin rai, ta mike ta nufi kofa ta fita daga parlon, Ajay ya dau strawberry dinsa ya ƙishingiɗa ya ci gaba da sha... Karfe goma da minti sha biyar Jay ya bar bangaren Ajay bayan ya tuna yace ma Khaleesat zai kirata karfe goma da rabi sannan yana son discussing issue dinta da Mami a daren yau, yana barin parlon ko minti biyar ba ayi ba wayar Ajay ya fara ringing, ya kalli screen din wayar har kiran ya katse bai yi picking ba, ita din ce ke kiransa, sake kira tayi sai da ya kusa katsewa sannan ya dau wayar ya daga ya sa handsfree ya ajiye yana jiran jin me zata ce, daga daya bangaren tace "Good evening" Babu yabo babu fallasa yace "Wacece wannan?" Khaleesat ta hade rai kamar yana ganinta, can ta tura baki tace "To ai dai Housemate dina ne yace min baka da lafiya that is why I called to check on you" Ajay yace "I see... Sai dai in shi ne bashi da lafiya, ni kin ji alamar bani da lafiya?" Khaleesat ta ɗan taɓe baki tace "Toh ai shikenan, bye...." Zata katse wayar, Calmly taji yace "Kar ki kashe min waya Malama" *Halysaah is 500 via 3276052019 Fcmb Hauwa bello Jiddah* Ur evidence via 0708786578 https://chat.whatsapp.com/DtKRIBCkfHoGuMzWcuq87V?mode=ac_t HALYSAAH 87 Khaleesat tayi shiru jin abinda yace, can ta tallabi chin dinta tana jiran jin maganar da zai yi da yace kar ta kashe masa waya, ganin shima shirun yayi babu kuma alamar zai ce komai ta langwabe kai tace "Karar min da katin za ka yi?" Taji bai tanka ta ba, after some seconds ta turo baki tace "Sai da safe" A nan taji yace "Ke..." Dariya ya bata, amma ta hade rai tace "Ban gane ba, kawai kira fa nayi ince maka ya jiki nothing more" Kallon screen din wayarta tayi jin shigowar sako taga katin dubu ashirin ya tura mata, zaro ido tayi ta bude baki tana kallon amount din, bata san sanda tayi dariya ba tace "Ni nace maka bani da kati da zaka turo min har na 20k?" Taji bai tanka ta ba, tace "Hummm" A hankali tace "Tohm Nagode Allah ya saka da alkhairi, thank you soo much" He was still not saying anything, ta langwabe kai tace "Zan iya kashewa yanxu?" Sai a sannan taji yace "Ai sai katin nan ya kare" Bata san sanda tayi dariya ba sosai tace "Wanda ka turo min yanxu ko kuma katin da nake da shi kake nufi" Yace "I don't know for you" Tace "To ai ko nawa ma zai iya yin 3 hours bai kare ba, wanda ka turo min kuma ban san awanni nawa zai yi ba" Jin bai ce komai ba ta ajiye wayar ta sauka daga saman gadon ta tafi gun boxes dinta ta bude zata saka kayanta cikin wardrobe, sai kuma ta koma ta dauko wayar taga he is still on the line, ta langwabe kai a hankali tace "Ni fa aiki zan yi wallahi, should I cut the call?" Taji yace "Ke" Taɓe baki tayi ta ajiye wayar ta koma ta ci gaba da abinda take yi, ta dau lokaci me tsayi tana ta gyara kayanta bata sake komawa ta duba wayar ba, aka bude kofar dakin Aunty Farida ta shigo rai bace zata fara mata mitar abinda Nenne tayi yanxu a parlor, Khaleesat tayi saurin yi mata alamar tayi shiru tana nuna mata wayarta dake kan gado, Aunty Farida ta juya ta kalli wayar, Khaleesat ta karasa saman gadon ta dauko wayar tana kallon screen din taga bai fa katse ba har lokacin, mamaki hakan ya bata, da gaske katin yake don karar wa kenan, ta kai wayar kunne tace "Hello, ga Aunty Farida nan za ku gaisa" Taji yace "Ohk" mika ma Aunty Farida wayar tayi ta koma ta ci gaba da abinda take yi, sun kusa 10 mins suna magana da Aunty Farida har abun ya bata mamaki ashe yana bude baki yayi magana me tsawo haka dai, daga karshe suka yi sallama da Aunty Farida ta mika ma Khaleesat wayar ta fita daga dakin, Khaleesat ta kai wayar kunne tace "Sai da safe" Yace "Ai ban ƙona katina ba Malama" Ta hade rai tace "Toh sai cajina ya kare bayan ba wani magana muke yi ba" Yace "Na hanaki magana?" Kallon screen din wayar tayi taga minti nawa aka dauka all this while, zaro ido tayi ganin miss calls din Jay a saman screen din wayar, da sauri tace "Kaga Housemate dina yana ta kira ban sani ba kuma" Yace "Ni na hanaki sani?" Zata yi magana taji ya katse wayar, ajiyar zuciya ta sauke ta zauna gefen gado tayi dialing number Housemate, har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa nan ma bai dauka ba, ajiye wayar tayi hoping zai yi returning call dinta amma har bayan minti goma taga bai kira ba, ta kalli agogo dake nuna karfe sha daya dai dai, sake kiransa tayi bai daga ba, Khaleesat ta dauko kayan baccinta ta saka don tayi wanka tun wajen karfe takwas da rabi, Hijab ta daura a kai ta fita zata je tayi ma Umma sai da safe, ba a dau lokaci ba ta dawo daki ta kwanta tana duba wayarta hoping Jay ya kira amma taga akasin haka, sosai taji ta damu, to ko dai yayi bacci ne, gashi sanda ya kira ji zai yi she is on another call, sai yayi tunanin tana ganin kiran nasa bata ɗaga ba, sosai jikinta yayi sanyi ta rasa yanda zata yi, Aunty Farida ce ta shigo dakin tace "Har kin kwanta ne Khaleesah" Khaleesat ta daga kai ta kalleta, Aunty Farida ta zauna gefen gadon tana kallonta tace "Yana kiran ki ne dama Junaid" Khaleesat tace "A'a ni na kirasa bashi da lafiya nayi masa ya jiki, Housemate dina ya gaya min he is sick" Da damuwa Aunty Farida tace "Ayyah, to Allah ya basa lafiya, ai ban sani ba da na tambayesa ya jikin" Khaleesat dai bata ce komai ba, Nan Aunty Farida ta hau bata labarin abinda Nenne tayi daxu, ita dai Khaleesat kallonta kawai take don abinda ya tsaya mata a rai daban, har daga karshe aunty farida tayi mata sai da safe ta fita wajen karfe sha biyu da minti ɗaya, Khaleesat ta jawo wayarta a sanyaye ta kunna data ta bude WhatsApp, dai dai sanda Jay yayi updating Status with Ajay's picture, wishing him a Happy Birthday, tayi masa reply tace "Baka ga kirana ba?" After some minutes ya maido mata sako yace "Just woke up now" Kasa rubuta masa komai tayi jin abinda yace, after some minutes tace "Toh shikenan" Ya maido mata da reply din "Good night" Bata sake ce masa komai ba ta kashe data tayi kwanciyarta zuciyarta babu dadi. Da asuba bayan Jay ya dawo masallaci ya nufi part din Ajay don ko masallacin ma bai je ba, kwance ya samesa har ya koma bacci bayan yayi sallan sa a daki, Jay ya kalli drugs din da ke ajiye kan beside drawer da ruwan gora, ya karasa kusa da shi ya kai hannu forehead dinsa to feel his temperature, yaji his temperature is normal, although sau uku yana shigowa part din nasa cikin dare to check up on him, a zuwansa na karshe ne ma yaga Mai martaba a dakin shi ma, bude ido Ajay yayi bayan Jay ya kai hannunsa goshinsa yana kallonsa, Jay yace "Good morning Bruh, wishing you more fruitful years ahead" Ajay har ya mance yau ne ranan zagayowar haihuwarsa, juyawa yayi, yayi kwanciyar rub da ciki ya mayar da idonsa ya lumshe without replying him don bacci yake ji saboda maganin da ya sha, Jay ya juya ya fita daga dakin, Bangaren Maminsa ya tafi yayi sallama yana tsaye kofar dakinta ta amsa sannan ya shiga, har lokacin tana zaune saman darduma rike da counter, ya zauna yana kallonta ya gaisheta, da murmushi fuskarta tace "How was ur night Dear?" Jay yace "Alhamdulillah" Mami tace "Jiya na shiga part dinka wajen karfe sha daya naga kayi bacci" Jay bai ce mata komai ba, don idonsa biyu ba bacci yake ba sanda ta shigo, shi bai ma yi bacci ba sai kusan karfe daya da rabi jiya don gaba daya baccin kaurace masa yayi, Mami tace "Hadiyah ma wai nan da sati biyu zata dawo ko?" Jay yace "Ohk..." Don shi bai ma sani ba, after some seconds a hankali yace "Pls Mami Ina son maki magana ne amma don Allah ki fahimce ni, zan shiga damuwa idan kika yi misinterpreting dina cause kece mutum na farko da nake saka ran zata fara fahimta ta bayan Mai martaba, I need you to consider my points plss Mami" Yana kai wa nan ya daga kai ya kalleta yaga kallonsa take with full attention don har taji hankalinta ya tashi ganin damuwar da ya bayyana karara a fuskarsa cikin kankanin lokaci, shiru yayi bai sake cewa komai ba ya sauke idonsa, Mami ta kwantar da murya tace "Kana da wani a duniyar nan da zaka gaya ma damuwar ka da ya wuce ni ne Jawwad? Why is it taking you so long to voice out what the issue is? Kusan wata biyu kenan kana min nuku nuku ka ki gaya min menene matsalar, ko ka taɓa min wata magana ne kaga ban baka goyon baya ba ko da kuwa bana son abun nan son? I don't think there is anything I can't do for you, ka kwantar da hankalinka ka min bayanin menene ke faruwa" a hankali Jay yace "Ohk, dama Mami gaskiya ni yanxu ina da warce nake so zan aura, na duba abubuwa da yawa naga i and Hadiyah are not compatible, dama ita din zabin ku ce ba zabina ba, a wancan lokacin saboda inyi biyayya yasa na amince ban yi ma kowa gardama ba, yanxu kuwa i have my choice Mami kuma ina sonta sosai, ki yi hakuri Mami ban san yanda zaki dau wannan zancen ba, amma goyon bayan ki shine kwanciyar hankalina...." Shiru ya ɗan yi na few seconds har sannan kansa na duke yana kallon kasa, a hankali ya ci gaba yace "Amma kuma i have no issue marrying them both saboda gudun abinda zai je ya dawo considering our relationship with Hadiyah is in this family, in dai za a amince min ni na yarda zan hada su duka.... Zan kuma yi adalci tsakanin su in sha Allah" Mami dai kallonsa kawai take yi babu ko kiftawan kirki, bayan kusan minti ɗaya ya daga kai a hankali ya kalleta jin she is still silent, ta ɗan yi murmushi ta ajiye counter din hannunta tace "Wannan ne maganar dama Jawwad" Sosai yaji gabansa ya fadi, ya dai yi shiru bai ce komai ba yana kallonta yana jiran jin abu na gaba da zai fito daga bakinta, ajiyar zuciya yaji ta sauke me nauyi, after few seconds cikin nutsuwa ta fara magana tace "Toh a yanxu dai i am speechless Jawwad, cause this is something I never saw coming, gaba daya kaina ya kulle, amma ita yarinyar a Amurkan ku ka hadu ko a ina ka santa?" A hankali Jay yace "Can na santa, she is schooling there also" Mami ta gyada kai tace "Ohk that's good, brief me a little about her, amma bana son karya Jawwad kuma kasan haka" Jay ya daga idanuwansa ya kalleta, murya can kasa yace "Mai martaba yasan da maganarta Mami, kuma har ya hadu da ita a can wani zuwa da yayi Maryland, shi ne ma ya bani shawaran hadasu su biyu for peace to reign, sannan yace In fara magana dake akan maganar tukuna" Mami tace "Ohk, er wace gari ce yarinyar?" Jay yace "Kano" Mami ta jinjina kai sannan tace "So shima Junaid ya goyi bayan ka kenan dai akan hakan?" Jay yace "Eh, yasan komai" Mami tace "Ba damuwa, er wace unguwa ce a Kanon?" A hankali Jay yace "Tudun Yola" Mami ta gyada kai tace "Shikenan, ni yanxu kwanciya zan yi Jawwad, idan na tashi anjima ma ci gaba da maganar" Jay yace "To Mami" kansa a kasa ya mike ya fita daga dakin Mami ta bi sa da kallo har ya kullo mata kofa, tana ta zaune saman darduman har bayan fitarsa da kusan minti goma sannan ta mike ta fita daga part din nata, bangaren Junaid ta nufa ta bude kofar parlorn ganin baya cikin parlor ta karasa har Bedroom dinsa, yana kwance yana danna wayarsa don tun da Jay ya shigo daxu ya tashesa bayan ya fita sai ga Mai martaba da Aunty, bayan su ma sun fita Ammi ma ta kirasa shi ne bai sake komawa baccin ba, duk idan ranan zagayowar haihuwarsa ta zo yakan je Abuja wajen Ammi ne amma wannan karan baya jin yana da strength din zuwa Abujan, ya daga kai yana kallon Mami da ta shigo dakin ko sallama babu, ya mike zaune ya ajiye wayar hannunsa tun kan ya gaisheta tana dukan tafin hannunta da yatsu biyu tace "Wato yanda kayi bakin jini cikin family ka zama kamar mujiya shi ne bari ka goga ma Jawwad shi ma a ki jininsa ko? duk wata salon mugunta da rashin mutunci ka san shi Junaid, to bari kaji in gaya maka... yanda ka ba Jawwad muguwar shawaran yayi fatali da auren Hadiyah yace shi wata daban zai aura ba ita ba haka tun muna mu biyu da kai zaka koma ka zaunar da shi ka sake basa shawaran ya bar wannan zancen, don ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba kai ne algungumin da ka zugasa Jawwad ba haka yake ba, wannan ba halinsa bane, sam bashi da tsaurin idon da zai zauna yace min shi baya son zabina yaga wata daban yana so, wallahi muddin ina numfashi a duniya babu wata yarinyar da Jawwad zai aura da ta wuce Hadiyah kuma daga ita babu ƙari, ban haifar ma ko wace 'ya mace miji ba bayan Hadiyah, don in dai ita yake aure babu me rabani da shi ko ya nisanta ni da shi bayan iya shi kadai Allah ya bani, tarayyar ka da Jawwad kwata kwata babu alkhairi a cikinsa sai sharri, babu yanda zan yi ne amma na tsani ganin ku a tare har cikin raina don bakin jininka kake shafa masa ta hanyar dora sa a keken beran da kake yi, babu alkhairi a tarayyar ku sai sharri wallahi, don haka tun wuri muna mu biyu da kai ka koma ku warware wannan kullin da ku ka yi da shi don koma er uban wacece bazai aureta ba billahil azeem, sarai nasan wannan zugin ka ne ba na kowa ba tunda ka tsani ganin yana zaune lafiya da kowa, ci gabansa ma ai ba wani so kake ba, kuma muguntar ka da sharrin ka tsaff zai kare maka, Balle ni ko me zaka yi ma baya bani mamaki don kusan gado kayi....." Ajay ya sauka daga saman gadon ya shiga bandakinsa ya kulle kofar don in dai ya zauna ya ci gaba da sauraron maganganun karshen nan da take shirin yi tsaff zai mayar mata, Mami tace "To ai ba sabon abu bane, fitsara ai ba yau ka fara ba, kai da baka san darajan iyayenka ba ma balle na wasu, meye kuma baza kayi ba, in sha Allahu sai Allah ya kawo karshen alakarka da Jawwad don babu alkhairi cikinta sai sharri da hassada" Tana kai wa nan ta fice daga dakin rai bace ta tafi bangaren Aunty.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah ur evidence via 07087865788* HALYSAAH 88 Mami ce zaune parlon Aunty cikin bacin rai ta kare maganar da take yi da cewa "Don haka nake rokon ki alfarman duk yanda za kiyi convincing Mai martaba ya rushe zancen ya nuna masa bai isa ya maida mu yara ba to kiyi, Mai martaba ya nuna masa ba wani yace lallai sai ya yi accepting auren Hadiyah da farko ba, kawai ni so nake a sace masa gwiwa a nuna maganar bazai taɓa yiwuwa ba, kinsan dai yana jin maganar mai martaba..." Aunty ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Ba idan ina kokarin nuna maki illar alakar Jawwad da Junaid baki daukata serious ba, babu yanda banyi akan kiyi kokarin datse alakarsu ba amma kika ki daukar maganata da muhimmanci don baki son ɓata ma Jawwad rai, ai ba shi ya haife ki ba yau in kika ce baki son yana mu'amala da Junaid kika yi masa jan ido dolensa yaji maganar ki, yanxu dai ga irinta nan, kuma kamar yanda kika fada babu me zugasa sai Junaid, ai bai son ci gabansa tun ba yau nake kokarin fahimtar dake haka, yanxu baki ga Walid ko ga maciji basa yi da shi ba" Mami ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Ban sake tabbatar da Junaid ɗan iska bane sai yau Fulani, nayi da na sanin katse alakarsu da Jawwad da ban yi ba ta karfi da yaji" Aunty ta gyara zama tace "Bana mancewa shekarun baya har ce maki nayi ko addu'a ne ayi don farrakasu amma kika ki daukar hakan da muhimmanci" Mami tace "A'a ni duk wata sabgar shirka babu ni a cikinsa...." Aunty ta katse ta da sauri tace "Kai haba, meye kuma shirka ana zaune qlau Fulani, in aka ce addu'a ai bai wuce a ja carbi ba a roki Allah, ko kuma ka saka malaman zaure su saka ka cikin addu'ar su da bakunansu masu albarka, kai ma kuma kana yi ma kanka, amma nima ai kinsan babu ni a harkar saɓon Allah kwata kwata" Mami dai ko kallonta bata yi ba, shaff Aunty ta mance ta kawo ma Mami irin wannan maganar tsabar ƙin Junaid da take da kuma burin duk wani abu da zai tarwatsa sa, balle ko shirin kirki basa yi da Mami kamar yanda suke yi shekaru masu yawa da suka wuce a baya, Mami tace "To yanxu dai ke menene shawaran ki akan wannan mummunan lamarin Fulani? Kina ganin kuwa Mai martaba zai saurarari uzurin da zaki kai masa har ma ya dauka? Don Jawwad din fa har ce min yayi Mai martaba yasan da maganar tun ma a Amurka, kinga kuwa shi ma ya goyi bayansa kenan ai" Aunty tace "Ai ina ga mu ajiye batun yi ma Mai martaba magana tukunna, yanxu kamata yayi ma musan asalin ita yarinyar da yace maki yake so, Er wani gari ce ita, sannan waye ubanta a kasar nan, yaushe ma har ya hadu da ita ya fara son ta, informations dinta kawai ya kamata ace mun fara samu before anything else, ni ban so kin ma samu ɗan iskan Junaid din kin masa wata magana ba don kar ya koma ya gaya ma Jawwad, tunda kince baki nuna ma shi Jawwad din komai ba" Mami tace "Ae kuma kin san sa da shegen zurfin ciki da miskilanci, ba lallai ya ce ma Jawwad komai ba, kai bazai ma gaya masa ba" Aunty tace "Wannan gaskiya ne, a dai halinsa bazai gaya masa ba kam, yanxu kawai kara nuna ma Jawwad din zaki yi babu komai kawai yayi ta addu'a akan lamarin daga nan cikin siyasa ki bugi cikinsa mu san wacece yarinyar waye kuma ubanta a Nigeria" Mami tace "Ya ce min er Kano ce Tudun Yola" Aunty tace "Tudun Yola? To ai can cousin sister na Bara'atu take da zama, nan gidan mijinta yake" Mami tace "Kin ga ya zo mana gidan sauki kenan" Aunty tace "Ai kuwa dai ya zo mana gidan sauki, abinda yayi saura yanxu ki lallabasa cikin dubara a san a ina suke a cikin Tudun Yola" Mami tace "Kinsan sa da kaifin tunani fa Fulani, yana jin tambayoyin sun fara yawa zai ɗago wani abu" Aunty tace "In yasan wata ai bai san wata ba, number yarinyar kawai zaki nema a wayar sa bakin ki alekum" Mami ta sauke ajiyar zuciya tace "Shikenan, bari in je koma ya ake ciki dai zaki ji ni" Daga haka Mami ta mike ta nufi hanyar fita babban parlon, Aunty tayi murmushi tana girgiza kafa a hankali, ai ko tana ga yanxu ne dai dai lokacin ma da ya kamata ta farraka Jay da Ajay don da ta dau alwashin duk wani tsabgar Mami bazata sake shiga ba, duk da Jawwad din ma ba wai sonsa take ba, amma gwara dai shi sau dubu akan Junaid, farrakasu da zata yi shi ne zai sa rayuwar Junaid ya kara daidaicewa yanda take fata a kullum. Wajen karfe tara Jay ya bude kofar dakin Ajay, yana tsaye bakin kofar yake kallonsa ganin yana kulle tsadadden traveling box dinsa, Jay yace "What is the meaning of that?" Without looking at him Ajay yace "I am leaving for Abuja" Da mamaki Jay yace "Abuja? But you are not well Ajay" Ajay yace "I am" Jay yayi shiru still looking at him, after some seconds yace "Amma baka gaya ma Mai martaba ba tukun" Ajay yace "Na gaya masa" Jay yace "To ka bari zuwa gobe sai mu tafi tare mana" Ajay yace "Yau zan tafi" Jay yace "Amma bai fi kayi kwana biyu ba ai" Ajay yace "I can't say" duk da kwana biyun ma Mai martaba yace yayi ya dawo tunda baya jin dadi, Juyawa Jay yayi ya bar bakin kofar ya tafi can ɓangaren Maminsa, Mami ta ajiye wayar da take bayan ya shigo tace "Kayi breakfast Jawwad?" Ya zauna saman kujera yace "Nayi" Mami ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "Ya jikin ɗan uwan naka, ka shiga wajen nasa kuwa?" Jay yace "Daga can nake" Mami ta dinga kallonsa ta ji ko zai ce komai cause he look moody, har ta fara zargin ko Ajay ya gaya masa maganganun da taje ta masa daxu ne, Jay yayi breaking silence din yace "Abuja ma zai wuce yau" Mami tace "Wajen Amina?" Jay yace "Eh" Mami ta taɓe baki tace "Gwara ai yaje ya huta a can din" Jay ya kalleta yace "Duka kwanansa nawa a nan da zai je Abuja ya huta? Nan da Abuja ina ne asalin inda ya kamata ace ya samu hutu? The occupants of this palace ain't being fair to him, they are just making the palace miserable for him to leave in, gida da mutum yake saka ran dawowa ya samu rest of mind and peace but in Ajay's case it is totally different, he is always sad and restless in his father's palace, walwalarsa iya America ne ko kuma wani state a nan Nigeria aside Bauchi, sau da yawa in ya dawo Nigeria sai Mai martaba ya dinga takurasa ya zo garin nan, till when za a bar shi ya zauna peacefully a gidan nan ya samu kwanciyar hankali? Shi ba shiga harkar kowa yake ba he is always on his own baya shiga sabgar da bata shafesa ba, sai ya ga dama zai tanka abu, step Siblings dinsa gaba daya an dora su kan hanyar maida sa bare a masarautan nan, what is his offense pls? Menene yayi triggering attitude din da ake ganin yake showcasing a gidan nan?" Mami dake ta kallonsa ta kwantar da murya tace "Ya ce maka an masa wani abu ne yanxu?" Jay ya mike yace "Sai yace Mami? Nafi kowa saninsa idan da abinda yake damunsa ko kuma yana cikin bakin ciki, Kullum ya dawo gidan nan ba shi da walwala, ba shi da farin ciki, nan din kamar ba comfort zone dinsa ba, banda Mai martaba dake son ganinsa a kusa ni na tabbatar Ajay bazai dinga shigowa garin nan ba balle ya zauna gidan nan" Mami ta taɓe baki tace "In zaka bar wahal da kanka ka bari Jawwad, yanda kaga halin sa din nan haka mahaifiyarsa take ba wai, ci kanka sai ta ga dama zata ce ma mutum a sanda take raye, bata fiye son shiga harkar abinda bai shafeta ba ita ma, she is always on her own, miskila ce ta ajin karshe, in ba saninta mutum yayi ba sai yayi zaton tana da damuwa ne amma tsabar miskilanci da nukurci ne, don haka ka bar Ajay gado yayi ba taka haye ba, Mai martaba kansa ai yana da miskilancin da izza, shi abun ne yayi masa yawa wai shege da hauka, in zaka yi harkar rayuwarka ka bar damun kanka akan Junaid da zai fi maka alkhairi, sannan ni da kake kawo ma korafi zama nake a gidan nan? Ba sai inyi wata ba a gan ni ba, na hanaka shiga sabgar da bata shafe ka ba amma baka ji Jawwad" Jay dai kallon Mami kawai yake, Mami tace "Allah dai ya kyauta kawai, shi ma in zai zauna ya saki ransa ya zauna lafiya da kowa ya bi su a yanda suke so da zai fi masa" Jay yace "Zan shirya za mu tafi Abujan tare yau...." Mami ta hade rai tace "Kanwar uwarka ko ta ubanka ce a Abujan Jawwad, ka kawo min magana mai muhimmanci ina jiran ka ka shigo mu iddasa magana kuma kace min zaka bi sa ku je Abuja?" Jay yayi shiru jin abinda Mami tace, after some seconds ya zauna a hankali yace "Yeah haka ne Mami, amma ai za mu iya gama maganar yau sai mu tafi, bai wuce yayi kwana biyu ba kawai" Mami tace "Kai ka sani, tun da ga Boss dinka zai tafi Abuja ai dole hankalinka ya tashi kace zaka masa rakiya" Shi dai Jay bai sake cewa komai ba, bayan wani ɗan lokaci Mami ta kwantar da murya tace "Amma Jawwad baka ganin maganar can da ka kawo min daxu da safe zai kawo tangarda a zumunci tunda kasan wacece Hadiyah a gidan nan?" Jay yace "Ai Mami ni ban yi deciding kwata kwata bazan aureta ba, na dai ce idan hakan zai zo da matsala ni na amince zan iya hadasu su biyu" Mami tace "Haka ne, a nan ma kayi tunani me kyau, kuma ana ta jiran ku dawo ne a tsaida rana fa, don a yanda aka tsara wannan lahadin ake son tsaida ranan in sha Allah, sai gashi ka dawo da wata magana kuma" Jay yayi shiru jin abinda Mami tace, a hankali yace "Mami in dai kun amince min don Allah a haɗa duk biyun a saka gaba daya" Mami ta ɗan yi murmushi, sai kuma tace "Ai kuma dole a ɗaga saka ranan Jawwad, don kaga wannan maganar da ka kawo dole sai an yi calling family meeting kowa yasan abinda ake ciki, yanxu ya sunan ita yarinyar?" Jay ya kalli Mami, sai kuma yace "Sunanta Jiddah" Mami tace "Ikon Allah, ba ka yi ma ɗan uwanka ƙara ba kenan dai, haka kake kiran nata?" Jay ya ɗan yi murmushi yace "A'a, Halysaah ake kiranta" Mami tace "Maa sha Allah, Allah Ubangiji yayi zabi mafi alkhairi" Yace "Ameen" Mami tace "To ba damuwa, zan fara samun Mai martaba da maganar sai mu ga yaya za ayi kafin ma a kira meeting din" Jay yace "To Mami" Mikewa yayi don hankalinsa na can wajen Ajay duk da bai san Flight din karfe nawa zai bi ba, in ma na yanxu ne yasan dai bazai tafi bai kirasa ba, Mami tace "Fita zaka yi ne" Jay yace "A'a ba da nisa zan je ba" Mami tace "Toh kira min Maman Hadiyah ta wayar ka naji an min warning ina waya kafin ka shigo" Jay na kallonta yace "Maganar zaki mata Mami?" Mami tace "Haba, sai kace wata yarinya, maganar mu daban, in ma maganar ne ai yayanta ne zai mata" Jay ya ciro wayarsa ya mika ma Mami, ta amsa tace "In ji dai babu password, naga ka miko min haka" Yace "Babu" Tace "Ohk" Juyawa yayi ya fita daga parlon, Mami ta shiga call logs dinsa, Miss call ta gani da number da yayi saving with Halysaah with love emoji a gefe, ko picking call din ma bai yi ba kuma tun karfe takwas ta kirasa, wayarta ta jawo ta kwashe number gaba daya ta adanasa a wayarta, sannan ta fita daga call log din, gallery dinsa ta shiga nan ta ci karo da recent pictures da suka yi da Halysaah a amurka wanda Safiyyah tayi masu, kallon hoton ta dinga yi babu ko kiftawa with shock, tayi zooming din Halysaah sosai tana kare mata kallo, ajiye wayar tayi tsabar yanda ta girgiza taji zuciyarta na bugawa, ita Jawwad zai jajibo ma wannan yarinya me kama da buzuwa ko halfcast, mutanen da aka san su da mugun mallake miji, sannan ko me miji ya mallaka to a kansu yake karewa su kadai ke mora don raba mijin suke da danginsa kaf, sosai hankalin Mami ya tashi ba kadan ba, ta dinga kallon duk hotunan, da irin kallon tsantsan kauna da Jay yake ma Halysaah a duk hotunan kamar zai cinyeta, Mami ta ajiye wayar ta dafe kanta da yayi mata nauyi ta dinga nanata Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un, rabon da ta shiga irin wannan tashin hankalin da kidimewa har ta manta, wayarta ta jawo ta shiga WhatsApp dinsa tayi ma kanta sending hotunan guda biyu sannan tayi deleting yanda shi bazai gani ba ko yasan abinda tayi, daga nan ta fita daga WhatsApp din ta goge duk wata alamar da zai nuna wajajen da ta shiga a wayar nasa gaba daya, ta fi minti biyar a kidime sannan tayi dialing number Maman Hadiyah ta wayar sa don kar yaga bata kira ba, minti uku kawai suka yi suna magana da Maman Hadiyah sannan ta ajiye wayar tasa ta dau nata ta fita ta nufi bangaren Aunty cikin tashin hankali. Aunty dake zaune kan kujera ta dinga kallon hoton da Mami ta fiddo mata a wayarta, can ta kalli Mami baki bude tace "To ai na taɓa ganin yarinyar nan a Amurka da muka je kwanaki Fulani" Cikin tashin hankali Mami tace "Da gaske?" Aunty tace "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un, wallahi a gidan nasu na Amurka take zaune sanda naje, don dakin da suke saukan baƙi a sama duk kayanta ne da akwatunan ta a ciki, har sai da na kira Mai martaba na kai masa kara" Mami tace "To ai a sanda ku ka je Jawwad na nan Nigeria Fulani" Aunty tace "Kwarai kuwa, daga ita sai Junaid da ma'aikata na tarar a gidan, Junaid ya min rashin kunya ya gaggaya min bakakken maganganu a kanta, daga karshe ya kuma dauketa ya bar gidan, Wato tunda watsattsiya ce kuma ba son ci gaban Jawwad din yake ba shine zai zugasa ya aureta, Shi idan ba mugu azzalumi ba me yasa bai ce zai aureta ba, don mugunta sai ya tusa ma Jawwad saboda shi ne dai dai er bariki, yo er bariki mana, in ba er bariki ba me take yi a cikin wannan gidan cikin maza har biyu sannan ga masu aiki? Wallahi a yanda Jawwad ke tsoron Junaid idan ya hanasa auren yarinyar nan tsaf zai hanu, duk mun fa san Junaid ke controlling dinsa kinga kuwa tabbas da goyon bayan Junaid dari bisa dari akan maganar yarinyar" Mami ta dafe kanta da yayi mata nauyi don gaba daya ta ma kasa cewa komai, cikin tashin hankali tace "Ba fa er Nigeria bace Fulani, bamu ma san ko er wace kasa bace suka dawo Nigeria da zama" Aunty tace "Ni tafi min kama da Buzuwa, kuma akwai su da mallake miji kuwa da rabasa da danginsa, Wallahi in zaki fito ma Jawwad a mutum ki yi masa fata fata ki ajiye wannan kulafucin nasa da kike yi a rai to zai fi maki, don wannan kamata yayi ki ci masa mutunci sosai ba kadan ba ki nuna masa bacin ranki" Mami tace "Bazan masa haka ba Fulani, amma nasan me zan yi..." Aunty tace "To ga shawara, kuma shi kadai ne mafita a yanxu dai...." Mami ta daga kai tana kallonta tana jiran jin me zata ce..... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello* Ur evidence via 07087865788 https://chat.whatsapp.com/HVViEW83j9p1CPuLj0GcaA?mode=ac_t HALYSAAH 89 Karfe goma da rabi still that morning Jay ya koma bangaren Mami, zaune ya sameta parlor tayi nisa tunanin da take, ta daga kai tana kallonsa, yace "Lafiya kuwa Mami?" Murmushi tayi tace "Ba komai Jawwad, kawai nazari nake ko in tafi Gomben da nace zan je yau ne ko kuma dai in bari gobe" Yace "Ai da sauran lokaci yau din Mami, karfe sha daya ma bai yi ba, in zaki je kawai kiyi tafiyarki yau din" Mami tace "To bari in shirya, shiru shiru baka dawo ka amshi wayar ka ba" Jay ya dau wayar sa dake gefen Mami, sannan ya zauna yana kallonta yace "Mami kiyi hakuri plss zan bi Ajay za mu tafi Abuja, amma kwana biyu kawai za mu yi mu dawo in sha Allah" Mami tayi shiru tana kallonsa, can tace "Yanxu za ku tafi Abujan kenan?" Jay yace "Eh, amma driving za mu yi zuwa Kano sai mu kwana a can, gobe mu bi flight zuwa Abujan" Mami tace "To ai shikenan, Allah Ubangiji ya kai ku lafiya, ya tsare hanya" Yace "Ameen" Mikewa yayi yace "Let me go and get ready" Tace "Ohk" Daga haka ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita daga parlon ya kullo mata kofa, ta rungume hannunta tace "Tabdi jam" Da yamma Jay ya gama shirin da yake ya fito daga daki yana kallon Ajay dake kwance kan 3 seater yace "Mu je..." Ajay ya daga kai ya kallesa yace "Mu je ina?" Jay ya hade rai yace "Plss ka dena rena min hankali mana" Ajay yace "Dole ne sai naje? Kayi tafiyarka mana" Jay yace "In ka zauna kai kadai a gidan me zaka yi?" Ajay yace "Me nake yi yanxu?" Jay ya ja tsaki yace "Don Allah ka tashi mu je yamma na yi, in ma bazaka shiga gidan ba kayi zamanka a mota mana" Ajay yace "Wai dole ne sai naje gidan da ko shawara ba ayi da ni ba wajen siya? Saboda kana ganin zan hanaka siya ko me? But at least I should have know as a brother, ni bazan taɓa yin abu without ur knowledge Ba no matter what it is" Jay ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Ohk My bad... Yanxu dai ko bazaka shiga ba ka tashi mu je, i don't want you to start running temperature again, kana ganin an bar ka kai ɗaya kake fara running temperature...." Ajay ya wani kallesa, sai kuma yace "Do I look sick to you now? Ai na ji sauki" Jay ya kamo hannunsa zai dagosa daga saman kujeran with one hand, Ajay yayi wata dariya yace "That is a lie, Kai ka isa" Karfe biyar saura suka isa Tudun Yola, Jay yayi parking dai dai gate din gidan, Ajay dai kallon unguwan kawai yake don manyan gidaje ne kawai a unguwan, Jay ya kallesa yace "This is the House" Ajay ya kalli gate din gidan sannan yace "Allah ya sanya alkhairi" Jay yace "Ameen" After some seconds yace "Yanxu dai bazaka shiga ba?" Ajay yace "Ina jiran ka a nan" Jay yace "Ohk then, Amma kasan kuwa nayi ma Mami maganar Housemate?" Ajay ya kallesa yace "Ohk... ai baka gaya min ba" Jay yace "Yea, i don't want to stress you with talk duba da baka jin dadi" Ajay yace "Na fa ce maka ni naji sauki, You can see for ur self" Jay ya sauke ajiyar zuciya yace "Mami was so calm about it, and she wish me nothing but what's best for me, ta amince lokaci daya without prolonging the issue, dama kuma nasan bazata taɓa ƙin abinda na nuna ina so ba I told you that, tunda Mami da Mai martaba sun amince min, i don't care what others will think or say about this..." Ajay dai kallonsa kawai yake bai ce komai ba, can ya ɗan yi murmushi yace "I am happy to hear that, Allah ya sanya alkhairi" Jay na kallonsa yace "Ameen...." After some seconds yace "Or is there anything you want to tell me but you are not telling me?" Ajay yace "Kamar me kenan? Why did you say so?" Jay yace "Naga kamar har yanxu kai baka yi na'am da batun nan dari bisa dari ba, You are just being neutral about it" Ajay yayi dariya yace "I don't get you Bruh, idan akwai wani abu ance maka bazan gaya maka bane?" Jay bai sake cewa komai ba ya bude motar ya sauka yace "Bazan dade ba in sha Allah" Ajay yace "Kana wuce minti goma i promise you I am leaving" Jay yace "Ai ba motar ka bace Malam" Bai jira cewarsa ba ya nufi cikin gidan, Ajay ya jinginar da kansa jikin kujeran motar maganganun Mami suna kara dawo masa a kai kamar a lokacin take gaya masa su, rufe ido yayi trying to erase the thought of his mind. Duk da ɓacin ran da Nenne ke ciki mara misaltuwa tana ganin Jay ta watsake lokaci daya ta dinga masa sannu da zuwa cikin fara'a, ta dauko masa rabin ledan pure water ta dire masa a gabansa baki har kunne tace "Ai ni bata ce min kana hanya ba da na bada kudi an amso maka lemon kwalba da ruwan gora nayi maka tuwo da miyar taushe, sai dai kawai matsalar unguwan nan masu kantin barayi ne, komai nasu tsada kamar yan fashi" Shi dai Jay murmushi kawai yake, Umma ta fito suka gaisa da Jay cikin fara'a sannan ta bar parlon, Nenne tace "Amma kuma kace mata zaka zo shi ne ta kama hanya ta tafi Hotoro da kanwar uwar, wai sun je wajen wata wai ita Gaje" Jay na murmushi ya girgiza mata kai yace "A'a ba mu yi waya da ita ba yau, bata san zan zo ba" Nenne tace "To bari in je in sa uwar ta kira mana ita" Jay yace "Zan kirata da kaina Kaka" Nenne tace "To hakan ma ba laifi, sai dai ka zo ina cikin wani bakin ciki wanda rabon da in shiga irinsa har na manta wallahi" Jay yace "Subhanallahi, me ya faru Kaka?" Nenne ta gyara zama rai bace tace "Rimi rimi muka kamo hanya tsakar dare muka dawo gidan nan don bama son kowa yasan inda muka koma saboda tsaro da gudun surutun mutane, amma maganar da nake maka yanxu ɗaiɗai kun 'yan Mariri ne basu zo ganin gidan ba wai sun zo mana Allah ya sanya alkhairi, gaba daya labari ya baza Mariri an san gidan da muka dawo, to duk ba wannan ba, kasan ba mu dawo da matan Malam Ali gidan nan ba, kai dai kaga irinsu kaga yanda suke rayuwa, yanxu fisabililahi ina wajen da za a ajiye su a gidan nan? shi ne uwar Khaleesat ta munafurce ni ta zaga suna ta kulle kullen yanda kishiyoyin nata za su dawo gidan nan mu gwamutsu...." Jay ya ɗan yi murmushi yace "Kiyi hakuri Kaka, baza a biye ta halinsu ba ai" Nenne tace "Ba halinsu nake gudu ba ɗan nan, wallahi rubar da gidan za su yi ya koma dena ba kowa sha'awa, in don ta mugun halinsu ne ni ina ruwana, babban damuwata kar a dena sha'awar gidan nan gaba, sai kaga yanda ake turuwan zuwa ganin gidan nan wallahi, har da yan unguwan, to aka dawo da su Zubaida ai zance ya lalace kuma" Jay na murmushi yace "Ki dai yi hakuri Kaka, gida in ana gyaransa babu abinda zai yi in sha Allah" Nenne tayi shiru bakin ciki kamar ya kar ta, nan Jay ya dinga lallabata yana bata baki akan ta bar su su dawo kawai ko don Baban Khaleesat, bayan kusan minti goma ta sauke wani bala'e'en ajiyar zuciya tace "Shikenan ɗan nan, ai ka wuce ka ban shawara in ki dauka, kuma babban banza ne baya daukan shawara, zan samu Zahra'un ta kira min Malam Alin mu yi magana ta waya" yana murmushi yace "Maa sha Allah Kaka" Tayi shiru a ranta tana cewa "Zubaida me 'ya ya rakacaaa dama sai dai ta zauna tsakar gida, kawai ita ta hakura ta bar masu wannan ginin da take cewa nata ne su karata can, parlor daya da kitchen daya da daki da banɗaki ya ishi ita da 'ya yanta rayuwa, ita kuma Shatu a samu dakin kusa da kitchen a hadata da shi ita ma ta karata da kananun yaranta, su kuma yan matan gidan a basu daki daya su karata su ma, Aunty Farida sai tayi hakuri su zauna tare da Khaleesah kawai tunda haka Allah ya kaddaro masu, ta sauke wani ajiyar zuciya a fili tace "Toh ya iyayen naka?" Jay yace "Duk suna lafiya Alhamdulillah" Ta mike tace "Bari in duba ko da sauran shinkafar in zubo maka, dama Khaleesah ce ta dafa" Bata jira cewarsa ba ta wuce kitchen da sauri. Tunda Khaleesat da Aunty Farida suka sauka daga cikin adaidaita sahu take kallon motar da aka yi parking kofar gidan with the front seat slightly open kuma an kwantar da seat din motar, lokaci daya kawai tasan Ajay ne a motar for some reasons, ta kalli Aunty Farida tace "Kamar Ya Junaid" Aunty Farida tace "Haba" Khaleesat ta karasa har front seat din ta leka cikin motar tana kallonsa, taga idonsa a lumshe, a hankali ta kai hannu zata dau wayar sa dake ajiye lokaci daya ya bude ido, Mikewa zaune yayi da sauri yana komawa baya ta kyalkyale da dariya ta daga nikab din fuskarta don da alama Nikab din ne ya firgitasa cause he was sleeping, sosai ya bata dariya ba kadan ba ganin da gaske ya ji tsoro, shi ko ya hade rai yana kallonta, tace "To guduwa zaka yi da?" Aunty Farida ta karaso gun motar, ya gyara zama suka gaisa tace "To me yasa baka shigo ciki ba Junaid" Ya ɗan shafa kansa yace "Ina ɗan waya ne, amma Jawwad yana ciki" Khaleesat ta ɗan bude ido jin abinda yace, sau uku tana kiran Housemate din nata yau yaki picking call dinta, wanda hakan yasa tun daxu bata da wani walwala sai yanxu ne ma tayi dariya tunda gari ya waye, Aunty Farida tace "To mu shiga tun da ka gama wayar" Ya sauke idonsa bai ce komai ba, Aunty Farida ta nufi cikin gidan, Khaleesat na tsaye har ya sauko daga cikin motar, ya kara hade rai yace "Wai ke mayya ce ne, Kiyi tafiyarki mana" Ta ɗan yi murmushi kawai tace "Ai ko mayyar ce i will finish you first before anybody" Tana fadin haka ta nufi gate kafin ma ya bata amsa, kulle motar yayi ya ɗan tsaya for some seconds before walking toward the gate too. Khaleesat na shiga parlor Jay dake zaune ya daga kai ya kalleta, suna hada ido ta hade rai ta dauke idonta ta karaso cikin parlon ta zauna kasan carpet, Nenne na kallonta tace "Kun samu Gajen ta ku?" Khaleesat tace "Eh" Nenne ta kalli Jay tace "To bari in shiga wajen Zahra'u in yi yanda kace ayi, ai tunda kace inyi hakuri an gama magana kawai" Ya ɗan yi murmushi yace "To Nagode Kaka" Mikewa tayi ta bar parlon, Sai a sannan Khaleesat ta gaishesa ba tare da ta kallesa ba tana wasa da Hijab din jikinta, shi dai kallonta kawai yake babu ko kiftawa, can ya ɗan yi murmushi don yasan fushin me take, sai kuma yayi kasa da murya yace "Should I take my leave?" Sai a sannan ta daga idanuwanta ta kallesa, kamar zata yi kuka tace "Mene yasa baka son yi ma mutum uzuri?" Kamar bazai ce komai ba, sai kuma yace "Uzurin me za a maki Halysaah?" Tace "Da ka kirani jiya ban daga ba ai wayar baya wajena ne Aunty Farida ce tayi waya da shi" Yana kallonta yace "Why didn't u explain to me on Whatsapp yesterday? Instead you only asked weda I didn't see ur call and that's all" Shiru tayi bata ce komai ba, yayi murmushi yayi kasa da murya yace "You know one thing about you Halysaah?" Ta daga idanuwanta tana kallon sa, still smiling yace "Idan kika yi wani action that needs explanation, ignoring explanation din kike kiyi acting as though nothing happened, I called you 4 times yesterday and ur line was busy, da kika min magana ta WhatsApp sai ki bada uxurin ki amma sai kika yi ignoring din hakan" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "To kayi hakuri" Shi dai murmushi kawai yake yana kallonta yace "In ban yi hakuri ba ai bazan zo yau ba Halysaah" Ta langwabe kai tana kallonsa, yace "Kun ga Ajay a waje ne?" Ta ɗan bude ido sai kuma ta mike tace "Ina zuwa" Da ido ya bi ta har ta fita daga parlon, a compound din gidan taga Ajay zaune ta tafi har inda yake, ita har ta manta ma da shi, tana kallonsa tace "Baza ka shigo ba ne" juyawa yayi, yayi backing dinta yana kallon different direction yaki tanka ta, dariya ma ya bata, ta taɓe baki ta juya ta koma cikin gidan kawai, ta zauna tana kallon Jay tace "He is sitting outside, kilan bazai shigo ba" Jay yace "Ohk, i think I will take my leave now, dama Abuja za mu tafi gobe so we decided to spend the night in Kano Today" a hankali Khaleesat tace "Ohk, to ko inyi girki sai anjima ka zo ka amsa? May be after magrib" Jay yace "A'a kar ki ba kanki wahala Halysaah, we will get food at a restaurant" Khaleesat ta kalli wayarta dake vibrate alamar shigowar kira sai kuma tayi silencing call din don bata da number dake kiran nata, Jay yace "Wa yake kiran ki" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* ur evidence 07087865788 HALYSAAH 90 Khaleesat ta kallesa ta langwabar da kai tace "I don't have the number, ban san waye ba...." Jay yace "Let me see it" Daukar wayar tayi ta mika masa ya amsa yana kallon screen din, after some seconds ya mayar mata da wayar ta karba tace "Kilan 'yan can unguwan mu Mariri ne, daxu ma wata ta kirani za su zo nan wai Aunty Sha'awa ta bata number na" Jay yace "Ohk, but ya kamata a samu Gate Man for security" Khaleesat tayi murmushi kamar zata ce masa ai Nenne ce ke ajiye kujera ta zauna baƙin gate din tun sassafe amma kawai ta fasa, Jay ya shafa kansa yace "I will take my leave now Halysaah, ki ce ma su Kaka na tafi...." Khaleesat tace "Za ku yi celebrating birthday din Ya Junaid ne? Ko ba ya celebrating?" Jay ya ɗan kalleta yace "Ai ban san ko yace maki yana Celebrating ba" Khaleesat tayi dariya tace "A'a ni ban ma yi wishing dinsa Happy Birthday din ba ai, ko nayi bazai kulani ba ma nasani, kai yaushe ne naka Birthday din?" calmly yace "Rana daya da na Halysaah" Tayi murmushi tace "Uhmm... ai shikenan tunda baza ka gaya min ba" Shi ma murmushin yayi yace "Lokaci na wucewa bari in tafi" Tayi kasa da murya tace "Kasan me?" Yana kallonta yace "A'a sai kin fada" Tace "Promise me you will listen to me" Shiru yayi yana kallonta, can yace "To me zai hana Halysaah?" Tace "A'a ni dai kayi alkawarin zaka zauna kaji duk abinda zan ce har karshe" Cikin few seconds ya fara nazarin meye zata fada masa haka amma ya kasa ganowa, Yana kallonta with much interest yace "Ina jin ki Halysaah, meye kike tunanin zaki gaya min da bazan tsaya in saurare ki ba?" Sauke idonta tayi a hankali tace "I just want to solemnly appreciate you for everything you've done to me and my parent so far, I know words will never be enough to express all my gratitude... Words will definitely fail me but I believe you are a God sent angel to I and my family and I appreciate the very day I met you in my life...." Tun da ta fara yake wani kallonta, cikin sanyin murya tace "And I also want to appreciate Ya Junaid too, duk da nasan he won't give me a listening ear, Amma Nagode da duk abubuwan da yayi min shi ma, Allah ya saka masa da alkhairi..." Mikewa Jay yayi, Khaleesat ta kallesa ta hade rai tace "You promise to listen till the end fa" Ya ɗan yi murmushi yace "You are wasting my time Halysaah, ta shi ki rakani, keep ur words for another day" Ta ɓata fuska ta mike tana kallonsa, A hankali yace "To yi hakuri, za mu ci gaba ta waya" Ita dai tayi shiru bata ce komai, ya fara tafiya yace "Ko in tafi baza ki rakani ba" Tana tafiya a hankali ta bi bayansa, suna isowa gate ta zaro ido tace "Nayi mantuwa, i am coming plss" Daga haka ta juya da sauri ta koma cikin gidan, shi dai ya fita daga gate din ya karasa gun motarsu ya samu Ajay zaune yana jiransa a gaban motar, front seat din ya bude Ajay ya hade rai yace "Thanks for wasting my time" Jay ya ciro wayarsa a aljihu jin ana kiransa, yana dubawa yaga Mami ce, daxu ma ta kirasa bai samu ya daga ba, komawa bayan motar yayi ya jingina jiki yayi picking call dinta ya kai wayar kunne, Khaleesat ta fito daga gate din gidan ta nufi gun motar ganin Ajay kadai zaune a front seat ta fara dube duben inda zata ga Jay, can ta hangosa tsaye yana waya, kallon Ajay tayi taga far end of the street yake kallo kamar ma bai san tana tsaye wajen ba, abinda ke hannunta ta ajiye masa a gefensa tace "I got you this for ur Birthday, Allah ya karo shekaru masu albarka" Ya kalli package din da ta ajiye masa, sai ga Nenne ta fito daga cikin gida da sauri tana gyara yafin gyalenta, karasowa gun motar tayi cikin hanzari tana cewa "Na fito parlor naga wayam ba kowa, nace kaddai tafiya kayi yarinyar nan bata sanar mana ba, ga Parida can ta ɗora maka koren shinkafar nan da ake yi da hanta da karas, don Allah ka tsaya ka ci abinci tukun ko kuma a juye maka a Cooler ka tafi da shi" Tana ganin Ajay ta saki baki tana kallonsa, sauke kansa yayi ya sauko daga motar ya gaisheta kansa a kasa, a hankali tace "Lafiya lau ɗan nan, ashe dama tare ku ke, me ya hanaka shigowa, ko da yake naga baka da sakewa kai kamar sa, kowa da irin halittarsa dama, Malam Ali ma haka yake bai sakewa in bai saba da mutane ba" Shi dai sai murmushi yake wanda iyakarsa lips, sai ga Jay ya zagayo don saboda muryar Nenne ne ma yasa yayi ma Mami sallama har ta fara tambayarsa muryar wace tsohuwa ce take ji haka, Nenne tace "Wallahi bata ce mana zaka tafi ba Ahamad, ga kuma girki can ana maku kai da ɗan uwanka" Khaleesat ta hade rai tana kallon Nenne, can ta daga ma Jay hannu shi dai ya bi ta da ido har ta wuce cikin gidan, duk tunaninsa da ta ce masa tana zuwa kiran Nennen taje yi, sai da Nenne ta ɓata masu kusan minti goma tsaye a wajen tana zuba sannan daga karshe suka samu suka bar unguwan tana daga masu hannu... Lokaci Lokaci Ajay ke kallon abinda Khaleesat ta ajiye masa har suka isa gida, Jay ko kula da package din bai yi ba, sai bayan da yayi parking ya kashe motar yayi ido hudu da package din ya dauka yana kallo yace "Where did you get this Ajay?" Ajay dai kallonsa yake, kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "Oho yanda ka gansa nima haka na gansa a wajen" Jay ya wani kallesa ganin raina masa hankali zai yi, bude package din that is wrapped neatly and beautifully ya fara yi, har sai da ya bude gaba daya, Ajay dai sai kallon Box din hannun Jay yake, Jay ya bude box din ya ci karo da designer perfumes biyu wanda kudinsu zai yi 200k each ko ya kusa, making almost 400k kenan, ya kalli Ajay da shima kallon turarurrukan yake, Jay ya ciro wrist watch shi ma me shegen tsada dake cikin box din, iya abinda ke cikin package din kenan sai Birthday card from a friend, ya kalli Ajay yace "Tell me how you got this? Ko dai Paul ne ya ajiye a motar daxu kafin mu fita?" Ajay ya bude hannu alamar shi ma bai sani ba, Paul worker din gidansu ne na nan kano, shi ke kula da gidan ko akwai mutane ko babu, sosai suke jin dadin mu'amala da Paul, shi ma kuma haka yake ji da su saboda kyautatawar da suke masa, ya kuma rike amana sosai ba kadan ba, Jay let out a grin yana jujjuya Birthday card din hannunsa yace "But you are his boss not his friend...." Sai kuma yayi murmushi yace "This is soo thoughtful of Paul, few months back ba ka basa kudi masu yawa ba, yana da hankali sosai ai" Gently Jay ya bude turarurrukan duk ya fesa daya bayan daya to perceive the scent, ya lumshe ido don kamshin sun tafi da shi, yace "This is waow" Lokaci daya kamshi ya cika motar gaba daya, Shi dai Ajay bai ce komai ba ya bude motar ya sauka, Jay ya maida duk gifts din cikin box sannan ya fito daga motar yana rike da su ya kulle motar, suka nufi cikin gidan.... Karfe tara saura Ajay ya dau laptop dinsa da waya zai wuce daki yana kallon Jay da Cousin Bro dinsu Mukhtar yace "Good night" Sannan ya wuce dakinsa, kulle dakin yayi da makulli ya ajiye laptop dinsa ya zauna gefen gado yayi dialing number Khaleesat, Khaleesat na zaune tare da Nenne a dakin da Nenne ta zabar ma kanta a gidan, Islam ta shigo da wayar Khaleesat a hannunta ta mika mata tace "Aunty ana kiran ki" Amsan wayar tayi tana duba me kiranta ganin Ajay ne ta mike don dama ta gaji da zancen da Nenne ke mata, fita tayi daga dakin tayi picking call din ta kai kunne tace "Good evening" Yace "Ke... Ni na aikeki ki siya min Birthday present? Who sent you message? A ina kika samu wannan kudin da kika siyo turaren nan?" Khaleesat dake ta sauraronsa ta kyabe baki tace "For once kayi acting like how every other person will do, kawai godiya zaka min for getting u a present and Birthday card, shikenan...." Yace "To bana so, zan kuma bada a maida maki kayanki" Ɗan murmushi tayi tace "Ka maido min da kudin dai...." Katse wayar taji yayi, ta taɓe baki, dama tasan he will never change kuma ko kadan bata ji haushin abinda yayi mata ba, in ma bai yi bane zata yi mamaki, although she sees him as the senior brother she never had, shi yasa bata jin haushinsa ko kadan, ko barin wajen da take tsaye bata yi ba sai ga Alert din 1M ya shigo wayarta, dakinta ta tafi ta zauna ta dinga dariya kamar taɓaɓɓa, wato har da riba ya kara mata a kai, kamar ta kirasa tace saura Birthday Card din yaushe za a maido mata kawai dai ta kyalesa ta bar wayar a daki ta fita parlor, yaran Mama Shatu ne zaune kasan tiles din parlon suna kallo tunda Nenne ta hanasu zama kan Carpet wai kar yayi datti, Nenne ta fito dakinta tace "Ace har karfe tara Ali yaki shigowa gidan nan, yana can zaune kofar gida kan benchi wani ba sai yace Mai gadi bane" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba don tun dawowarsu gidan har yanxu fa Babanta dari dari yake, yaki sakin jiki da gidan, in yana unguwan to a kofar gida zaka samesa zaune kan Benchi da ya sa kafinta ya buga masa, Nenne tace "Wannan ai salon ya ja mana kallon raini ne a unguwan nan, sai ya nuna ma kowa talakawa ne mu kyauta aka bamu gidan nan sannan hankalinsa zai kwanta, kwata kwata yaki sakin jiki yayi kamar shi ne Mai gidan da ya gina gidan" Khaleesat ta koma daki ta dau mayafinta ta fita compound, ita kanta she is feeling somehow yanda Babanta yaki zama comfortable a gidan, da alama babu yanda ya iya da mahaifiyarsa ne yasa ma yake gidan nan, one thing about her father is bai yarda mutum yayi maka gagarumin kyauta babu wani dalili me karfi ba, shi yasa har yau bai sake yayi na'am da gidan ba, don yace bai san dalilin siyan gidan ba, kamar kullum yana zaune kan Benchi da karamar wayarsa da yake kunna Radio yana saurare ga carbi a hannunsa yana ja, ya juya jin an bude gate, Khaleesat ta karasa ta zauna daga gefensa tana kallonsa tace "Baba bbu sauro a nan kuwa?" Malam Ali yace "Ai shi yasa na saka Safata Jiddah, sauro kam ai ba a rasa su a ko ina" Khaleesat ta ɗan yi murmushi tace "Amma Baba me yasa baka son ka dinga shiga ciki sai dai kawai ka shiga idan dare yayi sosai, da sassafe kuma ka fita kasuwa" Malam Ali yayi murmushi yace "To ai zaman gida na mata ne Jiddah, ni yaushe zan ta zama a cikin gida tare da mata" Sauke idonta tayi cikin sanyin murya tace "Baba ka kwantar da hankalinka plss, tsakaninsa da Allah ya bamu gidan nan ba don wata manufa ba, trust me pls" Malam Ali yayi wani murmushin ya jinjina kai yace "Ke yarinya ce har yanxu Jiddah, haka kawai babu wani dalilinsa bazai siya mana wannan gida me tsada da komai na more rayuwa a ciki ba, babu yanda na iya da Baabata ne amma wannan gida ba gidan da za mu saki jiki a cikinsa bane mu zauna don komai zai iya faruwa in ma yanxu in ma nan gaba, shi yasa ma nayi amfani da wannan dama wajen fara gyaran gidanmu da muka baro a Mariri tunda babu kowa ciki, yanxu haka har an fara plaster a kasa, kuma duk za a canza zinc din gidan da Ceiling, sannan a kara girman window din dakunan, a fitar da inda ruwa zai dinga fita ya dena taruwa cikin gidan, duk abokaina na can ni bance masu gida aka siya min ba, na dai ce an bani gida in zauna har zuwa sanda zan gama gyara nawa gidan na Mariri" Khaleesat ta kasa cewa komai, amma duk jikinta yayi sanyi sosai, tasan bata da wani kalman da zata sake using wajen convincing Babanta, don his belief will be his belief, ita dai tasan daga ɓangaren Housemate dinta baza a taɓa samun matsala akan gidan nan ba balle tuni ya basu takardun gidan da komai, wasu motoci uku ne suka shigo layin a jere, Malam Ali da Khaleesat suka juya suna kallon motocin da suka dallaro masu hasken fitila, amma lokaci daya duk aka kashe fitilun motar masu haske wanda da alama saboda su aka yi hakan, haka kawai Khaleesat taji gabanta na faduwa barin da taga motocin all halted at the same time a kusa kusa da su, Malam Ali dai ya gyara zama har sannan yana kallon motocin shi ma, after almost 2 minute da tsayuwar motocin, motar dake gaba wani ya bude ya sauko daga front seat da alama dai Security ne, ya bude back seat wanda ke bayan motar ma ya sauko, Malam Ali dai sai kallonsa yake don kara tabbatar da shi din yake gani ko ba shi ba, can ya kalli Khaleesat yace "Tashi ki shiga ciki Jiddah" Gaba daya hankalin Khaleesat ya gama tashi ta girgiza kai tace "A'a baba I will remain here" Guard din mutumin na biye da shi a baya ya nufo Malam Ali da murmushi fuskarsa ya kai masa hannu yace "Assalamu alaikum Alhaji Aliyu" Malam Ali ya mike ya kai masa hannu yana mamakin me kuma ya hadasa da Deputyn garin nan, Khaleesat dai bata ma ganesa ba amma ta mance rabon da ta shiga tashin hankali irin na wannan moment din, me zai kawo su wajen Babanta da daddaren nan da motoci har uku, Deputy ya kalleta yace "Sannu yarinya" Dakewa tayi ta gaishesa ya amsa da fara'a sannan ya maida dubansa kan Malam Ali yace "Idan babu damuwa Alhaji Ali mun zo maka ne akan wani batu me muhimmanci, Allah yasa zaka bamu lokacinka ka saurare mu, in kuma lokacin da za mu dawo zaka saka mana to duk babu damuwa" Malam Ali yace "To ni dai Allah ya sa lafiya ranka shi dade" Deputy yace "Babu komai sai Alkhairi ka kwantar da hankalin ka, ni da abokina ne da sauran manyan mutane muka zo har inda kake muka same ka akan wannan batu da ke tafe da mu, amma sai dai muna baka hakuri mun maka zuwan bazata, and this could be sort of inconvenient....." Malam Ali ya dake don zuwa yanxu kam ya gama ƙaguwan yaji me kuma ya hadasa da manyan mutane kamar yanda Deputy yace, sannan me ya kawo Deputy da kansa inda yake, a ina ma ya san sa?? Duk da yasan Deputy mutumin kirki ne kuma kowa ya shaida amma fa hankalinsa yaki kwanciya, yana gyada kai cikin karfin hali yace "A'a ba komai ranka shi dade, bari a shimfida tabarma sai mu zauna a nan tsakar gida, hakan yayi ko?" Deputy yace "To babu laifi Alhaji Ali" Malam Ali ya kalli Khaleesat yace "Shiga ciki ki shimfida mana tabarma a compound Jiddah" Mikewa Khaleesat tayi jiki a sanyaye ta shiga cikin gidan don yin abinda Babanta yace tayi.... *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* 07087865788 HALYSAAH PAGE 91 https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM?mode=ac_t Bayan Khaleesat ta shimfida tabarmin da Babanta yasa ta shimfida ta koma parlor ta nufi kujera zata zauna har a lokacin hankalinta ya kasa kwanciya duk da irin approach din deputy toward her dad but she was so tense and confused, gashi ita bata ma san ko su waye ba, Nenne na kallonta har ta zauna kan kujera sannan tace "Yanxu baki lallabasa kun shigo gidan tare ba kika bar sa zaune bakin gate? Haka rayuwa zata ci gaba yana zaman kofar gida kamar Mai gadi kenan?" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, she was trying all possible best to keep calm at this moment, Nenne ta kyabe baki ta dau remote ta danna inda Islam ta nuna mata ana dannawa idan za a canza tashan kallo, tana canza tashar duk yaran dake zazzaune parlon suka juyo suna kallonta, ta tsuke fuska, Mikewa Khaleesat tayi ta bar parlon ta tafi dakin Ummanta ta sameta zaune tare da Aunty Farida sai Mama Shatu dake zaune daga kusa da kofar dakin a zuwan ta shigo hira da Umma, tunda Khaleesat ta shigo Umma ke kallonta, ganin Mama Shatu kawai Khaleesat ta juya ta tafi dakinta, Aunty Farida ma ta bi ta da kallo, bayan kusan minti biyar sai ga Umma ta shiga dakin nata tana kallonta tace "Lafiya Khaleesat?" Khaleesat ta sauke idonta har Umma ta karaso ta zauna gefen gado tana kallonta, sai ga Aunty Farida ma ta shigo dakin tana tambayarta me ya faru? Da kyar Khaleesat tace "Baba ne yayi baƙi a motoci ban san daga ina suke ba" Umma ta kasa daina kallonta ita ma a ɗan tsorace tace "A motoci kuma? Ke wa ya gaya maki?" Khaleesat tace "Muna zaune tare a waje sai ga su a motocin" Hankali tashe Umma tace "Yanxu yana ina Malam din?" Khaleesat tace "Ya ce in shimfida masu tabarma a tsakar gida, har ma sun gaisa da baƙin" Juyawa Aunty Farida tayi ta fita daga dakin, ta tafi can compound ita ma dai hankalinta a tashe, ai ko ta hangosu zazzaune saman tabarma su hudu sai Malam Ali na biyar da ya sinne kai ko me suke gaya masa oho, ta juya ta koma cikin gida. Karfe goma saura na daren Khaleesat ta shigo parlon Babanta tare da Aunty Farida, Umma ma na zaune parlon sai Nenne, Nenne ta gyara zama tace "To yanxu Ali ko don wannan girmama ka da yan unguwan nan suka yi suka shigo har gidan nan suka zazzauna a tabarma suna gabatar maka da kansu ya kamata ka rufa mana asiri kar ka sake zama bakin gate kamar Mai gadi, baka ji dadin da naji ba wallahi ganinka a tsakankanin manyan mutane a tsakar gida" Malam Ali dai kallonta kawai yake, can yace "Yanxu Baaba wa yace maki yan unguwan nan ne?" Nenne ta saki baki tace "Ba yan unguwan nan bane? To yan unguwan dake gaba da namu ne ko wanda ke bayan namu?" Malam Ali yace "Ni baƙin da suka zo gidan nan bama su da alaka da unguwan nan gaba dayan ta" Nenne ta zaro ido tana kallonsa tace "Kai haba dai? To a ina ka samo su Ali? Su waye?" Malam Ali ya sauke ajiyar zuciya yace "Dalilin tara ku a nan da nayi kenan Baaba, duk za ku ji waye su da kuma me ya kawo su gidan nan" Nenne ta gwalo ido tace "Wani laifin kuma ka sake yi Ali? Mun shiga uku mun lalace, abun arziki bai amshe mu ba, ko kwace gidan suka yi?" Malam Ali ya kara sauke wata ajiyar zuciyar cikin nutsuwa ya fara koro masu bayanin su waye mutanen da suka zo da kuma dalilin zuwan nasu gidan, tunda ya fara magana Khaleesat ke kallonsa babu ko kiftawa zuciyarta na bugawa, haka ma Umma da Aunty Farida that look speechless, Sai da Nenne ta jira ya kai har karshe sannan tayi mitsi mitsi da ido tace "Amma ka ban mamaki kuma ka ban tsoro da baka masu koran kare ba Ali, anya kuwa ba a canza min kai a daki na je wankan jegon ka a banɗaki ba kuwa tunda gidan yawa ne kuma mu uku muka haihu ba wani tazara tsakaninmu??? Ali yanxu kana nufin baka kore su ba ka zauna ka sauraresu har karshe?" Malam Ali yace "In kore su kuma Baaba? Na fa gaya maki su wa da su wa suka zo, ta yaya zan koresu fisabililahi?" Nenne ta mike a fusace tace "To ina ruwana da koma su waye, kai ko shugaban kasa ne in ya gaya maka abinda bai gamshe ka ba ai zaka kama kanka balle ma ba shi bane, yanxu a takaice kana nufin ce masu kayi toh shikenan?" Malam Ali yace "A'a, ni ban ce masu haka ba Baaba...." Nenne tace "Amma daga Awdul din har iyayensa Allah Ubangiji ya tsine masu albarka daga su har wanda ya basu shawaran turo maka manyan mutane su baka hakuri, kai kuma da yake gantalalle ne kai baka san ciwon er ka ba maimakon kace masu ai an sa mata rana biki saura sati daya yanxu haka shine ka zauna da wata safarka a kafa kamar ɗan bigilantee a tsakankaninsu kana sauraronsa, to wallahi idan ban kai karar su kotu ba Allah ya tsine min, ko Awdul ne kaɗai namiji da ya rage a duniya idan na kara basa auren jikata a kirani tsohuwar banza tsohuwar hofi, haba fisabililahi, sannan shi yaron nan da ya siya mana gidan nan kanin ubanmu ne shi ko na uwarmu da zai siya mana katon gida haka idan har ba sonta da aure yake ba, sai ya fito ya gaya mana yana sonta mu wani irin ƙwaƙwalwa gare mu da baza mu gane ba? ai ni ba yarinya bace nasan abinda nake, wallahi sonta yake so kuma na aure, haka kawai ka biye barayin gwamnati su saka ka a tsakiya don su tsorata ka ka sake daukar er ka ka bada a karo na biyu? Ko dai baka da lafiya ne Ali?" Malam Ali dake ta kallonta cikin nutsuwa yace "Yanxu fa Baaba baki saurareni na kai karshen bayani na ba...." A fusace tace "To ina jin ka maza maza tafi karshe" Malam Ali yace "Ni nace masu bazan ma Jiddah dole ba, duk abinda take so shi zan mata kuma shi nake so, in ma shi Abdul din tace take son komawa ni bazan hanata ba sai dai in bi ta da fatan alkhairi, in kuwa tace bata so to hakan ya zauna don bazan mata auren dole a karo na biyu ba" Nenne tace "To maza tun basu yi nisa sun isa gida ba ka bi su kace ai babu wannan zancen ko makamancin sa, yarinya tace bata sonsa ta tsanesa, in kuma wannan karan da karfin mulki za su yi amfani da shi wajen auren nata kamar yanda suka yi da kudi watannin baya to sai su yi mu gani, maza su gaya ma ɗan su ya cire shegun idonsa akan Khaleesah bata sonsa kuma tafi karfinsa nesa ba kusa ba wallahi" Hawaye ne kawai ke zuba idon Khaleesat tana shessheka tana jin wani zafi a ranta, ta jinginar da kanta jikin Aunty Farida cause she is beginning to loose her control, Sosai Aunty Farida ke jin dadin maganganun Nenne don ita ma banda tafarfasa babu abinda zuciyarta yake a inda take zaune, Umma kuwa dafe kanta da yayi mata nauyi sosai tayi, Nenne tace "Ka ji me nace maka ko baka ji ba Ali?? Tun gari bai waye ba ka san yanda zaka yi ka sanar masu babu wannan maganar da suka zo da shi don har an saka ma Khaleesah rana da wanda take so kuma ranan jama'ar nan daurin aure" Malam Ali yace "Shikenan Baaba, su a yanda suka zo ma suna tunanin bayan sun gabatar da bukatarsu nauyin su da ganin girmansu zai sa in amince lokaci guda babu ja in ja, amma wallahi ban yi haka ba, nuna masu nayi ni bani da ta cewa sai abinda 'ya ta tace shine magana don bazan kara mata dole ba, yanxu zuwa gobe suna saurarata su ji ya ake ciki, don haka bazan boye masu komai ba in sha Allah, zance su yi hakuri nayi mata miji" A fusace Nenne ta nufi kofa tana cewa "In Alhaji Musa bai yi hankali ba zan taka har gidan nasa in ci masa mutunci wallahi, tun da saboda shegen ɗan sa aka halitto Khaleesah ba sai ya zo ya sake daura auren ba mu gani, wato ya zo maka da manyan mutanen garin nan yanda zaka yi masu biyayya ga ka ɗan banza ko? To mu zuba da su" Tana kai wa nan ta fice daga parlon, Umma ma ta mike ta bi bayanta don bakin ciki ma bazai bari tace komai ba, shi dai Malam Ali kallon Khaleesat kawai yake, a hankali yace "Kiyi hakuri Jiddah, babu me maki dole in sha Allah, ki kwantar da hankalinki" Ita dai Khaleesat hawaye kawai take ta kasa cewa komai, Aunty Farida tace "Amma Malam tun farko bai kamata ma ka zauna ka ci gaba da sauraransu ba bayan kaji dalilin zuwan su, kamar yanda Nenne tace da kawai sai kace masu ai an saka mata rana kawai" Malam Ali yace "To tunanin nan bai zo min ba wallahi, amma ba komai in sha Allahu zan kira na kusa da Deputy din gobe in gaya masa yanda ake ciki don ya bani numbersa suna sauraran kirana gobe" Aunty Farida tace "Allah ya kyauta" Mikewa tayi ta dago Khaleesat suka fita daga parlon. Daren ranan nan Khaleesat kasa baccin kirki tayi, she was so disturb, ta rasa menene zai sa Abdul ya hakura da ita ya cire ransa a kanta cikin ruwan sanyi babu tashin hankali, dama kullum a ranta tana jin ba fa hakura yayi ba, he is definitely coming back amma bata san ta wannan salon zai sake dawowa ba, ko kadan bata yi mamakin gano sabon gidan nasu da suka yi ba ba don ko dubu biyu suka ba wani a Mariri tsaf zai kawo su tunda kusan kowa yasan inda suka dawo yanxu, sai kusan karfe hudu da rabi ta tashi daga saman darduman da take zaune bayan ta idar da sallolin da tayi sannan ta kwanta.... Da asuba bayan ta idar da Sallah tayi azkar ta tafi dakin Umma ta gaisheta, Umma dake zaune kan darduma har lokacin ta dinga kallonta don tana ganin idanuwanta ta gane bata yi bacci ba daren jiya kuma tayi kuka, Khaleesat ta zauna kusa da ita ta gaisheta cikin sanyin murya, Umma ta jawo ta jikinta a hankali tace "Bana son ki tada hankalin ki Khaleesah, in sha Allahu babu wani abu da zai sake hadaki da Abdul ina nan ina maki addu'a kema ki dage da addu'a kinji?" Hawaye ya cika idon Khaleesat ta gyada ma Umma kai kawai... Aunty Farida na zaune dakin Nenne tana kallonta tana ta koro mata jawabi, Nenne ta kare jawabinta da cewa "Don haka kema ki hada kayanki kala uku ko hudu zuwa nan da gobe mu kama hanya kawai, sam ban ga ta zama ba wallahi Parida, dole ko nawa ne in bada a min addu'a a dauke hankalin tsinannen yaron nan akan jikata ya rabu da ita na har abada, zuwa anjima kuma ki kira min Murja in sanar mata gamu nan zuwa Bauchi gobe, dama ina ta cewa zan je kwanan nan to ga babban dalili zai kai ni yanxu, ke ina ga ma har da Khaleesar za mu tafi don gwara mu je da ita aga warce za ayi ma addu'a ido da ido, in akwai wani taimako da za a bata tayi amfani da shi sai a bata in tsareta tayi, banda Ali ɗan banza ne da wani idon yake son mu kalli yaron nan dake ta mata hidima saboda soyayya, ai sonta yake Ahamad din, to kanin ubanmu ne shi zai mallaka mana kantamemen gidan nan haka babu dalili? Don haka maza mu shirya gobe mu tafi Bauchi mu samo mafita, farkon zuwan Ali furson ai can naje kishiyar Murjan ta rakani gun babanta ya bani taimako, babban bawan Allah ne mutumin a kauyen, kuma gun iyaye da kakanni ya gaji wannan baiwa tasa, in muka ce za mu biye Zahra'u da Ali to fa Khaleesah na cikin gararin rayuwa, miji wawa mata wawiya ga su matsoratan banza, don haka gwara mu rufa ma kan mu asiri Farida kar a mana dariya, naga ke da wayewar ki kuma kina da wayo, sannan hankalina bai kwanta ma ace mu tafi ba Khaleesah ba kar shegen yaron ya sake lallabowa ya dauketa tunda ba addini ne da shi ba, gwara mu je da ita kawai ayi abinda za ayi" Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya tace "To Allah ya kai mu goben Nenne" Nenne tace "Allah ya maki albarka, ku hada kayanku a akwati daya ke da Khaleesar, Ni kuma zan zuba ko a bacco bag ne mu kama hanya" Alhaji Musa ne zaune parlon sa wajen karfe sha dayan safe yana waya, Momy dake zaune ta hakikance kan kujera sai kallonsa take har ya idar da wayar ya ajiye, rai bace tace "Yanxu suna nufin su ce uban yaki amincewa kenan Alhaji??" Alhaji Musa ya sauke ajiyar zuciya yace "Gashi kuwa kina jin yanda muka yi a waya da Deputy, ban taɓa tunanin zai yi turning down din maganar nan ba duba da irin mutanen da suka je har gida suka samesa, idan Abdallah zai yi hakuri ya saka ma ransa salama ina ga zai fi alkhairi, this was the only option I tot will work" Momy tayi mitsi mitsi da ido tace "Amma wannan mutumi anyi tsinannen talaka, ko duba girman mutanen da suka je har gabansa suka zauna bai yi ba, banda Abdul ya nace har yana neman yi ma kansa illa ya ja min asara don Allah yaushe za mu zubar da girman mu da mutuncin mu haka a gaban talaka fakiri?" Alhaji Musa ya sauke ajiyar zuciya yace "Yanxu ke a matsayin ki na uwarsa babu hanyar da zaki bi ki masa magana ya saka ma ransa salama ya mance wannan yarinya ya hakura?" Cike da damuwa Momy tace "Wallahi Alhaji nayi, ba irin yanda ban bi da shi ba a matsayina na uwarsa amma abun yaci tura, ko baccin kirki Alhaji bana iya yi saboda halin nan da Abdul ya jefa kansa kan wannan er talakawan, ace mutum bazai ci abinci ba kullum gashi nan gashi nan dai ne kamar wanda ya fara samun matsala a kwakwalwa to ina lafiya a nan Alhaji? Kar wani abu ya samesa fa mu shiga uku shi Kenan garemu a duniya, shi yasa na kawo maka shawaran ka hada kan manyan abokanka ka nemi alfarman su je maka su samu matsiyacin uban yarinyar amma daga karshe dubi abinda yayi ma masu, nasan su kansu za su ga sun zubda mutuncinsu gaban mutumin da bai wuce drebansu ba" Alhaji Musa dai girgiza kafa kawai yake don shi kansa halin da Abdul ke kokarin jefa kansa ciki ba karamin damunsa yake ba, ya kira Malam Ali yayi sau uku tun ma lamarin Abdul din bai yi worst haka ba amma bai daga kiransa ba bai kuma biyo sa ba, har yayi zuciya ya goge numbersa, da ya ga dai Abdul bazai taɓa hakura ba yasa ya hada kan manyan abokansa ya turasu kamar yanda Momy ta basa shawara amma duk da haka babu wani fruitful result, mikewa Momy tayi ta fita daga dakin ranta a dagule ta tafi dakin Meemah, cike da damuwa tana kallonta tace "Meemah yanxu menene shawaranki akan wannan hali da ɗan uwanki ke kokarin jefa kansa? Yanxu haka fa tun jiya da safe yaki bude daki, ba ci ba sha, ban san wani hali yake ciki ba, tsorona kada wani abu ya samesa fa in shiga uku Meemah shikenan gare ni a duniyar nan" Sai kuma ta zauna gefen gado ta dafe kai ta fashe da kuka sosai, Meemah ta sauke ajiyar zuciya, ita fa ko kadan halin da Abdul ya jefa kansa ba wani damunta yayi ba in dai akan er talakawan can ce, ace duk class da girman kai irin nasa amma kan er matsiyata ya nemi maida kansa kamar mahaukaci zautattace, Cikin rawan murya Momy tace "Wallahi kwanaki da naga abun nasa yaki ci yaki cinyewa har kudi na bada a min aikin da zai maido hankalin yarinyar kansa amma a banza Meemah, in ba dai zuwa zan yi in tone abinda nace maki an bani na binne a garden ba in ƙone su" Meemah ta wani kalleta, can tace "Kema dai wallahi Momy, ki tone me kuma? Don Allah ki rabu da Abdul zai dawo dai dai nasani, lallai ne sai mutum ya samu abinda ya kwallafa rai dama in ba don yaga kuna biyesa ke da Daddy ba, ai abun nasa har da iskanci, ita kadai ce mace a duniya bayan ga mata wa enda ma suka fita komai" Wani tsawa Momy tayi mata tace "Tun ba yau ba nasan baki da imani baki da tausayi Meemah, kuma mugun nufinki akan Abdul sai dai ya kare maki wallahi, in dai dawowar yarinyar garesa ne zai dawo masa da farin cikinsa to ina maraba da hakan wallahi, da nasan wannan abun ne zai biyo baya yaushe har zan raba su ta karfi da yaji?? Ai da sai dai in ta gana mata azaba a gidan nan, amma ina neman rasa yarona akan mace kice kar in damu, to wallahi zan je in tono layun in Kona, sannan in har sato ta ne kadai mafita ni da kaina zan basa shawaran yayi hakan, dama wancan karan ma ai sato ta din yayi daga Lagos, ko ba a daura auren ba ya tafi duk inda zai tafi da ita kawai, yanxu ai jin ƙan ta take budurwa shi yasa zata yi ta iskanci tana rawan kai, kawai na cuci ɗa na a banza a hofi saboda dalilina mara tushe" Tana kai wa nan ta fice daga dakin, Meemah ta wani kyabe baki tana ci gaba da danna wayarta, da wuka Momy ta tafi garden din kamar dai zata yanko vegetables, tayi bake bake ta tona ramin da ta binne layun ta ciro tana kare masu kallo, sannan ta tafi kitchen zata ƙonasa saman gas... Tun da Khaleesat ta sanar ma Jay mutanen da mahaifin Abdul ya aiko wajen Babanta hankalinsa bai sake kwanciya ba kamar yanda nata hankalin ke a tashe tun daren jiya, gaba daya yaji zaman Abujan ma kamar a ƙaya yake, at first bata ma gaya masa ba sai da suna waya da yaji mood dinta da yanda take responding sai ya tambayeta abinda ke damunta shine har ta gaya masa, bayan la'asar Ajay ya shigo daki rike da Glass cup na Smoothie da Ammi tayi masu, ya ajiye ma Jay nasa yana kallonsa yace "Anything?" Jay ya kallesa kamar bazai ce komai ba, after a while kawai ya gaya masa abinda Khaleesat ta sanar masa, Ajay yayi shiru na kusan minti daya after listening to Jay, can ya kallesa yace "I think kawai ka samu Mai martaba da maganar, since Mami ta nuna maka she is fine with ur choice, gobe da safe sai mu koma Bauchi ka gaya masa ta amince.... But i will advise you duk yanda ku ka yi da Mai martaba kar ka gaya ma Mami, don nasan shi idan ya tashi zartar da ko wani hukunci sai ya gama zartarwa yake sanar da kowa" Jay dake kallonsa yace "Amma me yasa kace kar in gaya ma Mami yanda muka yi da Mai martaba?" Ajay yace "Just an advice, Ina ga kamar in baka gaya mata ba process din zai fi tafiya smoothly kuma da sauri, baza a tsaya wasu sirfa ba or anything of such, You know our mothers and exaggerating of things" Jay dai yayi shiru bai ce komai ba, Ajay ya ɗan yi murmushi yace "Dama nasan gayen nan bazai hakura ba, and he can do anything silly, I don't even think she is safe in kano...." *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* ur evidence via 07087865788 *TAKAICIN UBA…….* Na Nazeefah Sabo Nashe. 08033748387. 8…. Masu buƙata daga farko su yi following channel ɗinmu. https://whatsapp.com/channel/0029Va5fqs7E50UpMpXolU1T Driving yake yana sauraron Karatun Alkur’ani daga k’ira’ar sudais. Shi ka’dai ne abinda yake saurare ya rage masa zugi da ra’da’din rashin Hibbarsa. Ko da ya yi parking a makeken wajen shak’atawar kasa shiga ya yi ya shiga cusa hannayensa cikin tarin sumar gashin kansa da ya gadota daga gurin Ummeeynsa. Ya dinga cukuikuye gashin yana jin kansa na sara masa kafin ya mayar da seat ‘din kujerar ta sa ya koma ya kwanta tunanin rayuwarsu da Hibba na sake bujiro masa…. K’arar da wayarsa ta yi ne ya farkar da shi daga wancan tunanin, ba sai ya kalli screen ‘din wayar ba ring tone ‘din ya sanar da shi wacece ‘Ummeey’ ya fa’da yana sakin murmushin gefen kumatu kafin ya jawo wayar ya kanga a kunnensa. Cikin muryar shagwab’a kamar yarda ya saba mata magana ya ce “Hayateey!” Ummeey daga ‘daya gefen ta saki murmushi tana jin da’din sunan da yake kiranta da shi. “Amin ya gida hope dai kana lafiya, muma kwanan mu uku a Nigeria.” Ya ‘dan yi dum da waya a kunne kafin ya ce “Nigeria kuma how comes? Ya aka yi Abeey ya barku kuka je?” Dariya ta yi sosai kafin ta ce “Da kansa ya sauko ya ce mu je. Yauwa ba wannan yasa na kira ka ba, Amin bu’de kunne da kyau ka ji lokaci ya yi da ya kamata ka yi aure.” Wani irin dum ya ji k’irjinsa ya buga, Ummeey zata sake janyo masa wani jidalin kenan shi tun yaushe ya cire maganar aure a rayuwarsa, ya Riga ya gama da wannan babin an gama samun mata na gari tun bayan da Hibba ta rasu. “Ba ka ji ni ba ne?” Ummeey ‘din ta fa’da with a serious tone. Sakin ajiyar zuciya ya yi kafin ya ce “Na ji Ummeey, amma ina neman alfarma, not now please, wallahi ban shirya aure ba, ko kuma na ce na gama buk’atarsa a rayuwata tunda dai Hibba ta haifa min mai yi min addu’a.” Cikin b’acin rai Ummeey ta ce “Ko da nice nake so?” Muryarsa a cunkushe ya ce “Don Allah Ummeey a bar maganar, please!” “Ka yi k’arya kuwa in bar maganar aure, haka kawai da ranka da lafiyarka in dai ba mu’amala kake da matan banza ba ai ya kamata ace zuwa yanzu ka ajiye iyali, don haka magana ‘Daya da zan maka na samar maka mata y’ar aminiyata ta yarinta da nake yawan baku labarinta wato TALATU, don haka umarni na baka ba shawara ba..” kafin ya ce komai ta katse wayar don ta san idan ba haka ta yi masa ba, Ba zai ‘d’au zancen serious ba. Gaba ‘daya ji ya yi zuciyarsa ta karye, ya tabbatar tunda ta fa’da ‘din sai ta cika alk’awarinta. Ya runtse idonsa yana tunanin menene mafita? Wannan karan kam ya zama dole ya bijirewa umarninta, shi kam da zata bar shi haka ma tsaf zai iya rayuwarsa har ya koma ga lillahi babu aure. Wajen shak’atarwa da bai shiga ba kenan, ya da’de a zaune a motar kafin ya ja motar da sauri ya fice daga garden ‘din. ____________ Tun Asuba da ta mik’e bata farka ba, ta shiga gyaran gidan da abincin da ta san Amma ta fiso, gurasar larabawa da alkubus sai kunu da k’osai. May be idan Amman ta ga wannan hidimar da ta mata ta sassautawa zuciyarta daga fushin da ta tsiri yi da ita tun jiya da bak’uwarta da ta kira bak’ar bak’uwa ta zo gidan. Sai da ta jera kayan akan dinning table da taimakon mai aiki. Sannan ta kunna sunnah t.v tashar da ta san Amman ta fi muradin kallo a koda yaushe. Tsaf ta fito cikin shigar alfarma. Ta dinga bin falon gidan da kallo ganin yarda aka canja masa tsari. Ga dadda’dan k’amshi da aka baje falon da shi, na abinci da na k’amsashshen turaren wuta mai sanyaya ruhi na mutanen chad. Murmushi ne ya so sub’uce mata sanin cewa Ayra ce duk ta shirya hakan sarai ta san neman sulhu take tun jiyan tana lura da ita fushin da take da ita yana damun zuciyarta, sai dai ba zata bari ta fuskanta ba. Ta zauna tana sake addu’ar fatan alheri ga Ayran kamar yarda ta kwana tana yi a cikin sujuda, ji take kamar warwarar matsalar Ayran ce ta zo. Ita kanta ta ji tana son Ayran ta yi wannan auren ko da sonta ko ba son ranta. Tana jin takun tafiyar Ayran, ta kawar da waccan fuskar tata mai yalwar fara’a ta saka wacce ta aro tun yammacin jiya, mai wuyar kallo a wajen Ayran mai fa’dar mata da gaba da sakata ‘dimuwa. Zuciyar Ayra ta buga sosai ganin har a lokacin waccan caku’da’ddiyar fuskar tana nan tare da ita. Ta yi k’asa da kanta tana jin yarda zuciyarta take bugu a hankali take furta ‘Wannan bak’uwa ta cuceni na shiga uku, ban tab’a ganin fuskar mahaifiyata a haka ba kamar yau.’ Jiki a sanyaye ta isa gefen Amman kamar yarda ta saba ta rab’a jikinta da nata a hankali ta bata sumbata a kumatu “Ammaty Ina kwana?” “Lafiya” ta fa’da tana sake ‘d’aure fuskarta sosai, Ayran gabanta ya fa’di sosai ganin ba sassauci da da ne sai ta janyota itama ta ha’da goshinta da nata kafin ta ce “Lafiya lau Auta ta, kin tashi lafiya.” Ta dinga wasa da hannunta kafin murya a raunane ta ce “Amma I cooked your favourite dish.” Ta ‘dau tsawon lokaci kafin ta yi jarumta ta kawar da tausayin Ayran daga ranta ta ce “Ana sa’im.” Ayran ta dinga kallonta wani iri kafin ta ce “Sa’im kuma Amma? Yau fa laraba idan ban manta ba.” Zuciya a dake ta ce “Na sani. Kuma ki k’yaleni haka bana son magana.” Tuni idanun Ayra ya fara tsiyayar da hawaye ta dinga bin ta da kallo kafin ta fashe da kuka ta fa’da kanta. Amman bata hanata ba amma fa bata saka hannu ta rarrasheta kamar yarda ta saba ba. Duk da zuciyarta tana bugu haka ta mayar da idanunta kan T.V a zahirance kallon take amma a ba’dinance kukan Ayra ne yake tsaya mata a zuciya. Ta da’de tana kukan kafin Amman ta saki ajiyar zuciya ta ‘dago kanta. Idanunta cikin nata ta ce “Saurareni Ayra, idan kina son ganin walwalata ya zama dole wannan karan ki yi ya’ki da zuciyarka ki amincewa auren nan, idan ba haka ba kin bar ganin walwala ta. A kullu yau min ina gaya miki ba duka maza ba ne halinsu ‘daya akwai wa’danda halinsu ya Sha banban da na mahaifinki yanzu yayyenki ba duk sun yi auren ba, duk da ta ki k’addarar ta fi ta su girma, kada ki manta ni kaina idan na tuna lamarinki abin yana min ciwo wani lokacin kwana nake ban yi barci ba saboda tsananin b’acin rai kuma ma ba wannan ba, ki tuna wani abu ‘daya mana yau ace na mutu na barki ina za ki kama? D’an uwana ‘daya tak da nake da shi kina ganin dai shekaru ashirin ba mu ji labarinsa ba, aurenki fa shine abinda ya fi cancanta..” Hawaye take idanunta ba k’akkautawa ita Kanta Amman danne zuciyarta take bata bayyana nata kukan ba, amma wanda take yi a zuciyarta ya fi na Ayran yawa ya fi shi kuma ciwo. Ayran da sauri ta mik’e ta shige wani k’aramin falo da yake k’asa. Kuka take sosai tana tunanin ina ma zata iya da ta amincewa aurennan tunda yanzu ta lura burin Amma gaba ‘daya ya tattara ga son aurar da ita, sai dai ina har a lokaci zuciyarta bata karkata da neman rushewar wancan adawar da takewa aure ba, ba zata iya ba ba zata iya ha’da makwanci da namiji ba…. Ba zata iya bawa namiji lokacinta ba balle ta masa girki ko ta nuna masa wata kulawa Menene Mafita? Shine kawai abinda take tunani ta runtse idanunta kawai tana hango wata mafita da take tunanin ita ce zata tserar da ita daga wannan auren ba tare da kowa ya zargeta ko ya k’alubalanceta ba…. Ta dinga sakin ajiyar zuciya tana jin cunkoson b’acin ran da zuciyarta ta yi tana warwarewa hankalinta ya kwanta ta mik’e tana ka’de jikinta…. ________________ Magriba sakaliya ya shiga gidan nasa. Alh.Sulaiman turaki ya yi parking a bakin harabar gidansa. Kana ganinsa ka ga usulin fulani kuma ingarman namiji mai tsayi da fa’di fari tas da shi, farin nasa har wani ratsawa yake yellow. Ba walwala a fuskarsa ko ka’dan don bai kasance daga cikin mutane masu walwala ba. Ya dinga amsawa masu gadinsa sannu da zuwan da suke masa fuska a ha’de. Ta k’ofar baya ya shiga gidan nasa, k’ofar da direct zata sada shi da stair case ‘din da zai hau zuwa part ‘dinsa. Ta ga shigowar tasa ta ji kuma takunsa don haka ta mik’e tsam ta sake bulbulawa kanta turare sannan ta bi bayansa, ta cikin sashen da take da zai sadata itama da stair case ‘din nasa. Ta yi kyau sosai cikin shadda light brown da ta sha ‘dinkin y’an senegal, jelar gashinta sai reto take a gadon bayanta. Farin ciki fal fuskarta da zata yi arba da shi a yau bayan shafewar wasu watanni tunda ya dawo wajen amaryarsa bai sake waiwayarsu ba don haka ta shirya taran sa tana son kuma ta nuna masa tana nan a Hameedarta mai tsananin kishi wanda dama dalilin hakan ya sa ya barta a can k’asarsu ya kuma hanata zuwa Nigeria. Sai yanzu da ya tabbatar girma yazo mata hankali ya samu ya san da wuya ta zo ta aiwatar da haukan kishi zata ji kunyar hakan. Tsawon shekaru sha biyar da aurensa da amaryarsa tun a lokacin ta so dawowa mahaifarta cikin dangin babanta amma S.Turaki ya kafe sam bai amince da hakan ba kuma ko hutu bai amince ta zo ta yi ba. Yanzun ma an kai ruwa rana kafin ya amince da zuwan nata, kuma zuciyarsa tana d’ar-d’ar sai dai ko a waya bai nuna mata ba, dalilin yayan Babanta ne ya sanar da shi ya kamata ta zo ta ga dangi yaranta kuma su san dangin kakansu tunda Amin da y’ar uwarsa ne kawai suka tab’a zuwa. A can ya ha’du da ita wajen business ‘d’insa soyayya mai k’arfin gaske ta shiga tsakaninsu, duk da ra’ayinsu ya sha banban shi mai kafaffiyar zuciya ne yayin da ita kuma ta kasance mai sassauk’an hali. Ko a wajen tarbiyyar yara sai da suka sha artabu don sosai ya nuna mata ya fi son yaransa su tashi da harshen hausa a bakinsu ba harshen su na labanawa ba, don dole ta amince take musu magana da duka harsunan biyu shi yasa suka iya hausa kamar me? Tunda itama bahaushiyar ce mahaifinta haifaffen cikin garin kano ne kuma asalin bahaushe, mahaifiyarta ce kawai ta kasance daga jinsin larabawan labanon. Tun lokaci da ta rigime da son zuwa Nigeria shi kuma ya tattara ya mata yaji tsawon wata bakwai sai da ya ga abin nata ba na k’are bane sannan ya ce su tattara su taho ya gama musu gini. A hankali ta tura k’ofar idanunsu suka gamayya da juna. Fuskarsa ta ‘dan saki ka’dan yayin da tata ta washe da fara’a gaba ‘daya ta dinga jifansa da k’awataccen murmushi. Hannu kawai ya mik’a ya janyota kusa da shi ba tare da ya yi magana ba. Ta shige jikinsa sosai tana k’ok’arin kawar da kishin da yake k’asan ranta. Sosai ta shiga nuna masa yarda ta yi kewarsa tana gaya masa yayinda shi kuma ya shiga sarrafata ba bakin magana a tunaninsa hakan ne kawai Zai nuna mata ya yi kewarta ba ‘dan ka’dan ba….. Zazzafan coffee ‘din ta shiga jujjuya masa tana k’ok’arin mik’a masa murya a sauk’ak’e ta ce “Na samarwa Turaki mata…” gaba ‘daya cup ‘din ya sub’uce a hannunsa yana dubanta ya ce “Ba dani ba, na gama yiwa Turaki aure yana zubar min da mutunci ta hanyar sakin yaran mutane..” HALYSAAH PAGE 92 Nenne ta jawo handbag din Khaleesat bayan ta ajiye maficin da take yi ma Khaleesat din fiffita da shi ta bude jakar ta ciro wayar sannan ta fara tashinta tana cewa "Ga wayarki na ta ruri ki duba ko kira ne, kila ma Ahamad din ne" Khaleesat ta juya ma Nenne baya taki bude idonta kuma taki cewa komai don wani azababben ciwo kanta ke mata, Aunty Murja ce ta shigo dakin tace "Nenne ai da kin bar ta tayi baccin tunda bata jin dadi, kuma har da gajiyan hanya ma" Nenne tace "Ƙudajen nan naki ai ba bari za su yi tayi baccin cikin dadin rai ba, na tambayeki ko kiwon su kike kince A'a, banda ma ina korasu da mafici ai dakin bazai zaunu ba, ke dai kina da tsaftarki da sai ince kazanta ce ta kawo maki su, ina Parida ta zo ta duba ko kiran waya ne, tun daxu wayar ke ruri" Aunty Farida ce ta shigo dakin Nenne tayi maza ta mika mata wayar tace "Gashi yana ruri duba ko kira ne" Aunty Farida ta amshi wayar taga Jay ke kira, Aunty Farida tace "Jawwad ke kiranta" Nenne tace "Waye Jawwal, ko Ahamad din?" Aunty Farida tace "Eh shi ne" Da sauri Nenne tace "To ɗaga mana Parida, tun daxu fa yake ta kira, ki daga ki ce masa bata jin dadi tun da muka sauka Bauchi, yanxu haka a kwance take, kar ya ga an masa walakanci, maza ki ɗaga don Allah" Aunty Farida tayi murmushi ganin seriousness din Nenne, fita tayi daga dakin ta daga kiran, bayan kusan minti biyu ta dawo dakin tana kallon Aunty Murja tace "Wai gashi ki masa kwatancen nan din Aunty Murja" Aunty Murja ta amshi wayar, Nenne dai sai murmushi take har Aunty Murja ta gama yi masa kwatancen ta mika ma Aunty Farida wayar, bayan Aunty Farida ta katse wayar Nenne tace "To kun ga ai gwara haka, ai shi ma ɗan Bauchi ne, yaro me kirki ga hankali da nutsuwa" Aunty Murja ta mike tace "Allah sarki, Allah Ubangiji ya saka masa da alkhairi, to yanxu Nenne a dora tuwo ko kuma shinkafar za a sake maku naga yamma ya gabato" Nenne ta kalli Aunty Farida tace "Gwara ki hura iccen Parida tayi mana girkin ke kuma ki ji da yaranki kawai..." Nenne bata rufe baki ba sai ga yarinyar Aunty Murja me Cerebral palsy tana rarrafowa zata shigo dakin, Nenne tayi wani ihu tana yarfa mata mafici da sauri tana cewa "Tafi, tafi ki je can kofar gida, fitaa...." Aunty Farida ta ɓata rai tana kallon Nenne tace "Haba Nenne meye haka?" Nenne ta wani kalleta tace "Haɓa Nenne? Aljanu fa suka maida mata halittar ta haka tana dalalar da yawu, in bance ta fita ba me zance? Me zata shigo tayi cikinmu idan ba neman magana ba, ai laifin Murjan ne da take barin ta a sake, nace ta dinga daureta ko jikin bishiyar tsakar gidan nan nasu ne taki ji, ai ba a bari su shigo cikin mutane babu kyau haka, sa'ar su Islam ne fa amma ku dubeta kamar er shekara shidda in ba aljanu ba wa za su yi haka, su suka shafeta a ranan da aka haifeta" Ita dai Aunty Murja tayi shiru bata ce komai ba tana ɗan murmushi, Aunty Farida ta mike ta ɗaga yarinyar suka bar wajen, duk da ciwon kai da ya saka Khaleesat a gaba ga wani tashi da zuciyarta yake tun bayan da Nenne ta tilastata ta sha fura da Nonon da aka kawo masu daxu amma haka nan ta daure ta mike zaune tana ma Nenne wani kallo tace "To wai Nenne ita ba mutum bace kamar kowa? Wa ye yace maki aljanu ne suka shafeta? Tunda ba karatu kika yi ba ai baza ki san meye matsalar ta ba, ita da gidansu kuma ki dinga korarta bayan wajen Mamarta take son zuwa" Nenne tace "Ni bazan biye ki ba kiji da ciwon kan da ya saka ki gaba, mu zamaninmu yaushe za a bar irin wannan yarinya ta shigo cikin mutane, ai boye irinsu ake, ko a kai su wajen mai magani a bar su can, nono uwar zata bata da zata wani rarrafo ta biyo ta" Aunty Murja dake ta murmushi har sannan ta mike tace "Bari in hura abun girkin Nenne" Daga haka ta fita daga dakin, Khaleesat tace "Wallahi ki dena haka Nenne babu kyau, ita ma mutum ce kamar kowa kawai lalura Allah ya jarabceta da shi tun daga wajen haihuwa, yanxu duk an dena kalan wannan tunanin naku na mutanen da, kai ya waye, yara masu lalura haka jan su ake a jiki suna bukatar kulawa da soyayya ba tsangwama ba, Aunty Murjan ma ai bazata ji dadi yanda kike ma yarinyar ba" A fusace Nenne tace "Zamaninmu daban naku daban, mu dai mun san 'yan ruwa ake haifowa haka ko kuma wa enda aljanu suka shafa tun a cikin uwarsu" Komawa Khaleesat tayi ta kwanta don bata da strength din ci gaba da magana ga tashi da zuciyarta ke yi.... Karfe biyar da minti arba'in Khaleesat ta mike zaune da kyar ta dalilin tashinta da Nenne ke yi babu kakkautawa gashi ta samu bacci ya dauketa, Nenne na mika mata wayar da sauri tace "Maza daga kiran, kilan shi ne ya iso" Khaleesat ta amshi wayar taga Housemate dinta ke kiranta, komawa tayi ta kwanta tayi picking call din yace "Halysaah" Da kyar tace "Uhm" Yace "Are you still sleeping?" A hankali tace "Na tashi" Yace "How are you feeling now?" Tace "Uhm" Yace "Ina Aunt dinki da tayi mana kwatance daxu?" Khaleesat ta mika ma Nenne wayar tace "Aunty Murja zai yi magana da" Da sauri Nenne ta mike ta fita daga dakin da wayar tana cewa "To bara a kai mata, suna can sun daura mana sanwa da Parida" Bayan minti goma yaron Kishiyar Aunty Murja ya dawo tare da su Jay bayan yaje ya taro su, daurewa Khaleesat tayi ta mike ta dau Hijab dinta ta saka don Nenne takura ta tayi wai gasu can kofar gida ta tashi taje, tana fita waje taga Ride me suna ride da suka zo da shi, tana tafiya a hankali ta karasa har kusa da motar, Jay ya sauke glass din motar yana zaune front seat yana kallonta, ta kallesa shi da Ajay sannan ta jingina jikin motar don har ta gaji ɗan tafiyar nan da tayi, ya bude motar ya sauka yana kallonta yace "Halysaah" Ta ɗaga idanuwanta ta kallesa, yace "Me yasa kike damun kanki haka?" Ɗan murmushi tayi tace "Nace maka kaina ke min ciwo, kuma na gaji" Yace "Amma ai da wuri ku ka iso Bauchi" Ita dai ta sauke idonta tayi shiru bata ce komai ba, yace "Kin ci abinci?" Gyada masa kai tayi duk da bata iya ta ci komai ba sai fura kadan daxu, yace "Ohk bari mu duba pharmacy so I can get you some drugs, ki koma ciki, idan mun dawo zan kira ki...." Ta gyada masa kai ta fara tafiya a hankali ta shiga gidansu Aunty Murja, Jay ya koma cikin motar yana kallon Ajay yace "She is not feeling fine, mu ɗan duba ko za mu samu pharmacy a nan in siya mata magani" Ajay dai bai ce masa komai ba ya tada motar ya fara reverse. Bayan minti arba'in suka dawo Jay ya sake kiranta ta fito, Shopping yayi mata na abubuwan da zata bukata irin pack din bottle water, drinks, costly cookies,, Sae gwangwanin powdered milk da Milo with sugar, da carton din Indomie, bread ma manya uku ya siya da Butter, a gefe kuma ga kwai, duk dai wani abu da zai sa ta zama comfortable a gidan duk da bai san kwanaki nawa zasu yi ba, sannan ya siya ne not for only her to use, ya kuma siya masu abinci a restaurant pack biyar da gasassun kaji, Ita dai Khaleesat na jingine jikin motar ta ma rasa abinda zata ce har yara suka gama shiga gidan da kayayyakin, ya mika mata ledan drugs din yace "You check the prescription idan kin ci abinci sai ki sha" Cikin sanyin murya tace "Thank you so much, Allah ya saka da alkhairi" Ya wani kalleta, ita ma dai kallonsa kawai take ɗan tsayuwar nan da tayi har ta gaji, yayi kasa da murya yace "Pls Halysaah in sha Allah komai zai wuce ki dena saka ma kanki damuwa, i am assuring you babu abinda ya isa ya maki don ya gama samun nasara kuma a kanki, ki kwantar da hankalin ki and trust my words" Ɗan murmushi kawai tayi bata ce komai ba, yace "Go get some rest, ki ce da Kaka in sha Allah za mu dawo gobe yanxu Magrib ya gabato shi yasa baza mu shiga mu gaisheta ba, from our place to here is almost 45 minutes ride" Khaleesat ta ɗan bude ido cikin sanyin murya tace "Da nisa ashe" Ya ɗan yi murmushi yace "May be mu zo around 11 in the morning gobe" Tace "To Allah ya kai mu" Yace "Ameen, in kin ji zaki Iya magana anjima ki kirani, bana son in kira kina bacci kaka ta tashe ki" Tana murmushi ta gyada masa kai sannan ta ɗaga masa hannu alamar Bye bye ta juya ta wuce cikin gidan, Jay ya shiga mota yana kallon Ajay yace "Common ya jiki baza ka iya yi mata ba alhalin idan ita ce sai ta maka ya jiki ko baza ka amsa ba" Ajay ya kallesa yace "Dama bata da lafiya ne?" Banza Jay yayi masa don shi ne ma ya hado mata maganin a Pharmacy shi kuma ya shiga yayi shopping wanda duk da Atm card din Ajay din suka yi duk siyayyar don shi ya mance nasa a gida amma yake masa tambayar rainin wayo yanxu..... Washegari karfe takwas da rabi Jay ya kira wayar Khaleesat, Nenne dake ta tambayar wanene bayan Aunty Farida ta sanar mata Jay ne tace "Ɗaga ki bani shi" Aunty Farida tace "Ki ce masa me, bari dai in daga tunda bacci take" A fusace Nenne tace "Ki bani nace, ke komai sai kin nuna iyawa" Aunty Farida ta kyabe baki tayi picking call din ta mika mata, Nenne ta doka sallama tace "Ina kwana Ahamad" Jay na jin muryarta ya gaisheta cikin ladabi, ta amsa tace "Wallahi in gaya maka jiya dai ba mu yi baccin kirki ba, jikin nata ba dadi, dama tana dadewa ita bata yi ciwo ba amma in ta tashi yi ba kyau, da ta sha magungunan kamar zazzabin ya sauka sai kuma ya dawo da karfinsa, dama jiya muna mota zuwa garin nan sau biyu tayi amai, to daren jiya ma tayi sau biyu, gashi taki cin komai har shayi an ƙada mata ta kasa sha" Jay dake ta sauraronta duk sai yaji a hankalinsa ya tashi, a hankali yace "Toh ina ga za a hada mata da allurai Kaka..." Nenne tace "Atoh, ni na rasa kan ciwon nata..." Yace "Yanxu za mu taho in sha Allah" Nenne tace "Toh Allah ya kawo ka lafiya Ahamad" Bayan Nenne taji shiru alamar ya katse wayar ta ajiye tana kallon Aunty Murja tace "Lafiyan Allah take da, daga sanda iyayen tsinannen yaron can Awdul suka turo barayin gwamnati da daddare wajen Ali shikenan ta birkice, ba komai ne ya ja mata wannan ciwo ba sai damuwa, ta saka ma ranta damuwar abun sosai ba kadan ba, ba dole ta damu ba tunda ita tasan ukuban da ta sha gidan Awdul don bai da kunya ya kuma dawowa yace ga zance ga magana, in sha Allahu karshensa ne ya zo, in ma yana da mugun nufi ne a kanta to ga dai ta a Bauchi bazai kuma taɓa sanin inda take ba" Aunty Murja ta sauke ajiyar zuciya tace "Abun kam babu dadi, Kuma Allah ya fi sa, babu abinda ya isa ya mata wanda Allah bai yi mata ba" Nenne tace "Maza ku tashi ku tsaftace tsakar gidan can, banda ke ma ai sai dai gidan nan ya ruɓe don na lura kishiyarki akwai aukin kazanta, yarinyar can taki kuma ki kulleta a daki ki saka kwado kar ta kunyata mu idan bakinmu sun iso...." Aunty Murja dai tayi murmushi ta tashi ta fita. Da fara'a Nenne ke welcoming din Jay da Ajay tana nuna masu shimfidar da ta masu na tabarma, shi dai Ajay kansa na kasa har ya zauna saman tabarman, Jay ma ya zauna sannan suka gaisheta, mafici take mika masu tace "Kamar za ayi ruwa daxu kuma sai garin ya washe" Jay yace "Inda muka fito anyi ruwan" Nenne tace "Kaji ikon Allah, nan kuwa sai iska, to ya gidan da iyayen ku?" Jay yace "Alhamdulillah, ya me jiki?" Nenne tana cire bargon jikin Khaleesat tace "Ga ta nan, daga wanka daxu lamari ya sake lalacewa" A fusace Khaleesat ta fixgo bargon daga hannunta ta kara rufe jikinta, shi dai Jay kallonta kawai yake haka ma Ajay, Nenne tace "Haka fa take idan bata da lafiya tayi ta nukurci kamar mu muka dora mata, tunda kina jin su ai daurewa zaki yi ki tashi ki gaishe su" Jay yayi murmushi yace "Kyaleta kawai Kaka" Nenne tace "To ai shikenan..." Mikewa tayi tace "Ina zuwa" Daga haka ta fita daga dakin, Jay yace "Halysaah" Ta ɗan juya ta kallesa amma bata ce komai ba, yace "Are you running temperature?" Shiru tayi, ya tashi ya tafi kusa da ita ya durkusa yana kallonta, shi dai Ajay ya ciro wayarsa yana dubawa, Jay ya kai hannu forehead dinta yaji jikinta da zafi, yace "Bari a maki allura you will feel better in sha Allah" A hankali tace "Ai ban gama shan maganin ba" Yace "Duka za a hada" Juya masa baya tayi tace "A'a ni bana son wani allura bayan ga drugs" Ajay ya wani kalleta, Jay yace "Amma alluran zai taimaka maki ai" Bata sake tanka sa ba sae ma daure fuska da tayi, ya mike ya koma ya zauna, sai ga Nenne da kofin shayi biyu ta ajiye masu Aunty Murja na biye da ita da katon bread da soyayyen kwai lafta lafta a plate, Ajay ya kalli Jay, tana ajiyewa tace "Gashi nan yanxun nan aka soya maku, shayin ma sai tiriri yake kun ga..." Ajay yace "Ni na tashi da azumi yau alhamis, sai dai Jawwad" Jay ya juya ya kallesa, Nenne tace "Ai kuwa yau alhamis nima ina yi saboda ba a garina nake ba shi yasa ban yi ba" Matsar da farantin kwan tayi gaban Jay da katon bredin da kopin shayi duk ta maida gabansa, Khaleesat bata san sanda dariya ya kusa taho mata ba duk da yanda take fama da kanta ganin how shock Jay was looking at Nenne, shi kansa Ajay kawai dakewa yayi, yayi keeping serious face a gefen Jay kar yayi dariya, Nenne tace "In kuma baka ci ba Allah ya sani bazan ji dadi ba, kuma jikina zai yi sanyi" Daga haka ta nemi waje ta zauna tana jiran ya fara shan shayin, Jay ya ciro handkerchief dinsa yana goge fuskarsa, Aunty Murja ta nemi waje ta zauna ta kara gaisawa da su da fara'a sannan tace "Wani unguwa ku ke a Bauchi?" Nenne tace "Nima dai na tambaya ranan amma bai gaya min..." Jay ya ɗan kalli Ajay, shi dai Ajay babu abinda yace, Jay ya sauke idonsa ya sanar masu daga inda suka fito a garin Bauchi, Nenne ta saki baki tana kallonsu can tace "Kun hada wata dangantaka da sarki ne?" Jay yace "Mahaifinmu ne" Wani salati Nenne ta saki saboda shock tana kallonsu tace "Sarkin ne mahaifinku?" Jay bai sake cewa komai ba, Nenne ta kira full sunan Mai martaba tace "Kuna nufin shi ya haife ku??" Aunty Murja tace "Haka fa kika ji suka ce Nenne, ni dama ina ta kallon wannan na kusa da shi naga yana kama da yaran gidan sosai, tunda zaki ga ana nuno mana su ta waya yanxu, su dai wa ennan ban taɓa ganinsu a waya ba" Tsabar yanda Nenne ta girgiza ta kasa cewa komai sai kallonsu Jay take kamar ranan ta fara ganinsu, can ta ambato sunan Baban Jay me rasuwa sai kuma ta fashe da kuka tace "A sannan ina garin nan Allah yayi masa rasuwa, duk muka gigice, garin nan ya dawo shiru kamar ba kowa tsabar tashin hankali, Sarki adali me jin tausayin al'uma, mun yi babban rashi wallahi, kaninsa dake kan kujeran yanxu ne ban wani san sa ba, amma yanxu ace zan samu hanya wallahi zan je har fadarsa mu gaisa in saka masa albarka in masa addu'a" Jay na murmushi yace "Sai mu kai ki Kaka, ai yana nan" Nenne tace "Da kuwa nayi farin ciki wallahi, sai Parida ta rakani mu je, ita wannan rubabbiyar me ciwo ta zauna a gida ba sai mun je da ita ba, ita kuma Murja tana da yarinya me shafar aljanu bata zuwa ko nan da can saboda yarinyar...." Ko rufe baki Nenne bata yi ba sai ga yarinyar Aunty Murja na kokarin shigowa dakin, Nenne tayi wani ihuu ta dau mafici ta fara korar ta daga inda take zaune tana cewa "Fitaa, tafi kofar gida, Murja ba nace ki saka kwado a dakin ba wannan wani irin fitina ne saboda yarinyar nan nake fargaban zuwa gidan nan wallahi" Ajay ya mike yana kallon yarinyar yace "Ta fita kuma Kaka?" Nenne tace "Ta fita mana ɗan nan, er ruwa ce fa" Jay was totally speechless yana kallon Nenne, Aunty Murja ta mike zata dau yarinyar ta bar wajen Ajay yace "A'a ki kyaleta" Sai ya karasa ya shigo da ita dakin ya zaunar da ita kusa da shi, ga shi Fes uwar ta shiryata har da su packing gashinta me uban yawa, Nenne dai sai zazzare ido take tana kallonsu don ita abun kunya ta dauka ai, Ajay ya kalli Aunty Murja yace "Ya sunanta" Aunty Murja tayi murmushi, Nenne tayi karaf tace "Sunansu daya da Khaleesah, ita ma Hauwa ce, dama kuma sunan uwar Murjan Khaleesah ta ci, kunsan uwarta kishiya ta ce kuma mun yi zaman mutunci, Murja na da shekara biyar uwar ta mutu rikonta ya dawo hannuna har na aurar da ita, Ali na ji da Murja kamar ni na haifeta, yanda na sha wahala Ali yayi karatu ita ma haka don sai da tayi poly kafin tayi aure, da iliminta haka da ku ke ganinta har turanci tana ji, bayan na mata aure haihuwar farko ɗan ya rasu bayan shekara hudu Allah ya bata wannan yarinya er ruwa" Calmly Jay yace "Kaka ba haka bane, ki dena kiranta da er ruwa, ita din mutum ce kamar kowa, a ƙasashen da aka ci gaba masu irin wannan lalura kulawa ta musamman ake basu, babu tsangwama babu kyara sai soyayya da ake nuna masu ana jan su jiki, wannan lalura tasu a likitance ita ake kira da Cerebral Palsy ba wai yan ruwa ba kamar yanda yawancin Hausawa ke kiransu wasu ma su ce ai aljani ne ya taɓa su, to duk ba haka bane, kusan lalura ce ta ƙwaƙwalwa wanda jariri ke samu tun yana cikin mahaifiyarsa ko kuma bayan an haifesa, kyara da tsangwamar masu irin wannan lalura da ake yi yana jefa iyayensu cikin damuwa, duk da yanxu kai ya waye hakan ya ragu ba kamar da ba, don haka Kaka don Allah wannan yarinya soyayya take bukata da kulawa ba tsangwama ba, haka Allah ya so ya ganta, mutanen dake kewaye da ita sai su ja ta jiki su nuna mata so da kulawa" Nenne ta sauke ajiyar zuciya tace "Ai shikenan, mu ce mana ake yan ruwa ne zamanin mu, amma tun da ba haka bane ko ta shigo na dena korarta sai dai Allah ya kiyaye mu kar ta mana barna mu shiga uku" Ajay yayi murmushi kawai ya kalli Aunty Murja da kanta ke kasa yace "In sha Allah za a duba mata Wheelchair that will improve her mobility, da abubuwa da suka kamata" Mami ce zaune tare da Mai martaba a parlonsa, bayan sun gaisa tace "Dama Allah ya taimake ka akan maganar Jawwad nace bari in sameka, bayan sun dawo ya kawo min maganar wata yarinya da yake so da aure, duk da nasan kun yi magana da shi kafin yayi da ni, to nayi masa fatan alkhairi, shi ne yanxu na same ka inji what is ur take on the matter" Mai martaba yace "Ai mun gama wannan maganar, har nayi ma wakilai na maganan tafiya wajen iyayen yarinyar, akan haka ake yanxu" Mami tayi shiru tana kallonsu, can ta gyara zama tace "Amma Ranka shi dade ban tari hanzarin ka ba, daga magana sai tura wakilai na zata ai sai anyi bincike me zurfi kafin tura wakilai" Mai martaba kallonta kawai yake don dama ta saba fada masa duk maganar da ya zo bakinta, can ya sauke ajiyar zuciya bayan kusan minti daya yace "Kina ganin zan tura zuwa gun iyayen yarinyar babu bincike Fulani?" Mami tace "To naga abun yayi gaggawa ne ranka ya dade...." Mai martaba yace "To haka muka shirya Fulani" Tace "To yanxu har an tsaida ranan zuwa Kanon kenan?" Mai martaba yace "Kwarai kuwa... Nayi wasu baƙi zan je in same su yanxu Fulani" Yana kai wa nan ya mike ta bi sa da kallo har ya fita daga parlon. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* Ur evidence via 07087865788 HALYSAAH PAGE 93 Jay na zaune parlon Maminsa ta dalilin kiransa da tayi, ko minti talatin basu yi da dawowa gidan tare da Ajay ba don yau ma sun je duba Khaleesat, Mami ta kallesa tace "Ina kuma yake jan ka kuke tafiya duk kwana biyun nan daga safe zuwa dare" Jay ya daga kai ya kalleta, sai kuma yace "Yake ja na kuma sai kace wani yaro Mami?" Mami tace "To ai hakan kake a wajensa, ba kai ne Drivern sa duk inda za shi a garin nan ba" Jay bai sake ce mata komai ba don tunda suka fara zuwa unguwan da Halysaah suka sauka Ajay ne ke driving din, Mami tace "Daxu Me martaba ke gaya min yanda ku ka yi da shi, dama da ban je na samesa ba kawai sai dai inji magana a sama, kai menene dalilinka na ƙin gaya min yanda ku ka yi da shi? Kun je kun yanke shawara har za a zartar amma ni ba a fita hakkina an sanar min ba and you are okay with that" Jay dai yayi shiru don he was only following Ajay's advice, Mami tace "To ai shikenan, Allah Ubangiji yayi mana me kyau" Jay yace "Ameen" Mami tace "To a tudun yolan wace unguwa suke?" Jay ya daga kai ya kalleta yayi shiru, tace "Ko ba Tudun yola ka ce ba?" Yace "Eh can suke, amma ban rike address din gidan ba ai, any problem Mami?" Mami tace "A'a wai in ji, amma tunda baka sani ba ai shikenan" Wayarsa ne ya fara ringing yana dubawa yaga Mai martaba ke kiransa, ya daga kai ya kalleta yace "Mai martaba na kirana" Mami tace "Ohk" Mikewa yayi ya fita daga parlon, after a while ta tashi zata fita sai ga Aunty ta shigo, dama kuma wajen nata zata je don gaba daya akanta tayi relying all this while tunda tace ta bar mata komai, Mami ta koma ta zauna tace "Kuma gun ki zan tafi yanxu" Zaunawa Aunty tayi tana murmushi tace "Toh albishirin ki, yanxu haka na samo Address din gidansu yarinyar a wajen Mai martaba, ashe daga Kano zai wakilta aje gidan nasu, iyaka mutane biyu ne za su tafi daga nan" Mami tace "Da gaske kin samo Address din?" Aunty tace "Kwarai kuwa, ce masa nayi mijin er uwata dake Tudun yola yace min a basa address din gidansu yarinyar in dai Tudun Yola suke kilan bazai rasa sanin Ubanta ba tunda duk sun san kansu a unguwan, tun da safe muka yi hakan da shi shine ya kira Jawwad din ta waya a gabana ya tambayesa Address din, nan take kuwa ya gaya masa, sannan Mai martaba ya sake nanata min address din, ina komawa parlona na rubuce address din a waya don kar in mance, to na fita ne, sai yanxu na dawo shi yasa ban shigo na sanar maki ba" Mami tayi shiru tana kallon Aunty, can tace "Amma kinsan yanxun nan Yaron nan ya fita a parlon nan ina tambayarsa Address din yace bai sani ba???" Aunty ta taɓe baki tace "Ai ko ya gaya ma Mai martaba daxu da safe" Mami tayi wani murmushi tace "Ki bar ni da shi, in yasan wata ai bai san wata ba" Aunty tace "Ba nace ki fito masa a mutum ba kin ki kina gudun bacin ransa, tun yaushe za ki ce masa bai isa ba kuma hakan ya zauna" Jay na zaune gaban Mai martaba a parlonsa, Mai martaba was quiet for a minute kafin yace "Jawwad..." Jay ya daga kai ya kallesa don sai da gabansa ya fadi cause Mai martaba da serious tone ya kirasa, a nutse Mai martaba yace "Me yasa baka gaya min yarinyar da kake nema ta taɓa aure ba?" Jay ya dinga kallonsa babu ko kiftawa zuciyarsa na bugawa, Calmly Mai martaba yace "Ko ba haka bane?" Sauke kansa ƙasa yayi ya kasa cewa komai at first, shi gaba daya mance Khaleesat ta taɓa wani aure yake yi, lokaci daya yaji jikinsa yayi sanyi sosai, ya dafe kansa da yayi masa nauyi a take, Cikin kwantar da murya Mai martaba yace "Ba hakan zai sa in hanaka aurenta don ta taɓa aure Jawwad, my concern is why did you hide this important thing away from me? Idan da ban sa an min bincike kafin in tura zuwa ga mahaifin yarinyar ba da sai in wakilai na sun je mahaifinta zai sanar masu matsayin yarinyar kenan? Or probably kun ma riga kun hada plan ace budurwa ce duk ban sani ba... kuma duk hakan zai iya yiwuwa tunda har ka iya boye min, Kai ba aure ka taɓa ba Jawwad, this is ur first marriage idan Allah ya tabbatar, ka kuma san yanda al'adar gidan nan yake, tun asali da ka sanar min cewar ta taɓa aure ai sai an fara auren ka da Hadiyah idan ya so ko bayan wasu watanni ne sai ka auri ita wannan din, nobody will question you Jawwad, an sanar min abubuwa da yawa a binciken nan da na sa aka min wanda ina ga babu amfanin in zauna ina zayyano su a nan, har ma unguwan da suka baro kafin su dawo tudun yola na sani, just that I was taken aback knowing so many things.... kawai dai nasan ni bazan hanaka aurenta ba tunda kace kana sonta Ahmad, although bayan binciken nan da aka min akwai abubuwa da yawa wanda na kasa fahimta har yanxu, ban san ko da wani abu da ku ke boye min kai da Junaid ba, ko kuma akwai wani abu da ku ka juya kai da shi akan lamarin nan, anyway... ba hakan zai sa a fasa zuwa gun mahaifinta gobe asabar kamar yanda na tsara ba, sai dai za a fara zuwa gun dangin uban Hadiyah tukunna, so dalilin kiran ka kenan Ahmad, Allah ya maka albarka...." Jay dai ya kasa ɗago kansa don gaba daya jikinsa yayi sanyi qlau, kenan an sanar ma Mai martaba karatun da take a Amurka ma Saurayi ne ke sponsoring dinta tun bai aureta ba, bayan nan ya gano shi da Junaid suka ci gaba da dawainiya da ita a Amurka kenan bayan mutuwar aurenta? Yanxu har labarin prison din da aka kai babanta da dalili duk yaji, ta yaya ma har aka gano tsohon unguwan da suka baro?? Babu abinda ya kara sanyaya masa jiki sai batun gidan da ya siya masu don ya ma san har shi za a gaya ma Mai martaba kawai bazai dai ce masa komai bane, tun da gashi yace yaji abubuwa da yawa, Mai martaba ya katse masa tunaninsa yace "Ko da wata maganar da zaka yi ne Ahmad?" Da kyar ya ɗago kai, cikin sanyin murya yace "Kayi hakuri Abba, nayi kuskure boye maka duk abubuwan nan da nayi tun farko, a gafarce ni Abba" Mai martaba ya ɗan yi murmushi yace "It's fine Ahmad, i only called to correct you, in sha Allah bikin ma baza a saka lokaci me tsayi ba, kawai asalin mahaifin yarinyar ne ake contemplating har yanxu, ance Kano kuma aka dawo aka ce Bauchi... How true is that? Although ba mu ji daga mahaifin nata ba har yanxu ai, mahaifiyarta kuma aka ce buzuwa ce er Nijar ko?" Da kyar Jay yace "Haka ne, Mahaifinta a Kano aka haifesa amma asalin babansa ɗan Bauchi ne, zama ya maida shi Kano, daxu kakarta ke sanar mana don tana garin nan, har ma tace tana son a kawota ta gaishe ka" Mai martaba ya ɗan yi murmushi yace "A nan garin kakarta take kenan?" Jay yace "A'a zuwa tayi, dama kuma tana zuwa" Mai martaba yace "Shikenan, babu matsala sai ka kawo ta din, zaka iya tafiya..." Jay yayi masa sallama ba tare da ya yarda sun hada ido ba ya mike ya bar parlon, bangaren Ajay ya nufa, ya samesa zaune parlor yana dube dube a laptop, Bayan ya zauna Ajay ya kallesa, Jay ya jinginar da kansa jikin kujera a hankali yace "Kasan Mai martaba ya sa anyi bincike a Kano? And he found out everything, when I say everything I mean Everything Ajay" Ajay ya ɗan bude ido ya ajiye laptop dinsa yace "Really?" Jay ya sauke ajiyar zuciya yace "Dama ai zancen duniya baya buya, but banyi expecting za a gano komai easily haka ba, yau na kara jin tsoron mutum, mutum abun tsoro ne Ajay, nasan har gidan da na siya Abba ya sani yanxu, he was angry but calm at the same time, I wish I told him all this before he find out himself..." Ajay was quiet for some time don shi ma ya girgiza, can yace "To yanxu me yace maka at the end?" A hankali Jay yace "He said it's fine, I told him about her Grandma da tace zata zo, gobe kenan...." Ajay yace "Ba nace ka kyale wannan tsohuwar ba, sai ta zo ta karasa fada masa abinda ba a fada ba a Kanon hankalin ka zai kwanta, she talks too much shi yasa nace kayi ignoring kawota da tace kayi gidan nan, but you still went ahead and told Abba" Jay ya sauke wani ajiyar zuciyan yace "Bazata yi abinda kake tunani ba, i will bring her tomorrow in sha Allah, don Abba na contemplating asalin Baban Halysaah, an ce masa Kano aka dawo kuma aka ce Bauchi" Sosai Nenne ta nutsu tayi zaman ladabi da biyayya tun da aka shigo da ita babban parlon Mai martaba, don a iya saninta ba kowa ne ke da access din parlon sarki ba, ita a ganinta ba karamin karramata da mutunta ta aka yi ba haka, dama ta baza tsadadden turaren Khaleesat da suka barota a gida, sai zuba uban kamshi take abun ta ga sabon gyale da atamfa a jikinta kai baza ka bata shekarunta ba, zuwa sannan sun kusa minti goma kenan a parlon a zaune, Ajay ne yayi leading dinsu zuwa parlon sannan ya fita, Nenne ta saci kallon Aunty Farida da tayi picking call din da ya shigo wayarta ta hade rai tace "Ke Parida ba nace ki ajiye wayar nan ba, ba fa parlon gidanmu bane nan, ba fa kowa ake ma iso zuwa wannan parlon ba sai wanda ya isa, wannan wani irin kunyata ni kike son yi bayan na yarda dake na jajibo ki, Haba parida..." Ko rufe baki Nenne bata yi ba sai ga Mai martaba ya shigo parlon walking like the king he is, Nenne ta sinne kai irin babban mutum ya shigo, Sau daya Aunty Farida ta daga kai bayan ta gansa ta ajiye wayar hannunta, ya karaso har cikin parlon ya zauna a spot din da ya saba zama yana kallonsu, tuni dama Nenne ta fara jero masa gaisuwa tun bai kai ga zama ba, shi ma ya gaisheta cikin girmamawa, Aunty Farida ma ta ɗaga karamin Nikab din da ta dora kan Abayan jikinta ta gaishesa kanta a kasa, ya kalleta ya amsa sannan ya kalli Nenne yace "Kun zo lafiya Baaba" Nenne tace "Wallahi lafiya lau ranka shi dade, na ce ni dai yau a kawo ni in gaishe ka in sa maka albarka don kai din mutumin kirki ne kowa ya shaida, Allah Ubangiji yayi maka albarka ya kare gaban ka da bayan ka, ya rufa maka asiri duniya da lahira, Allah ya albarkaci zuri'ar ka, ya ja da ranka, ya kara maka lafiya da kwanciyar hankali, Allah ya taya ka riko..." Ya gyada kai with calmness yace "Ameen Baaba, Ameen, dama albarkan irin ku abun so ne gare mu, muna godiya kwarai, Allah ya kara girma, madallah" Nenne tace "Ni dai nayi farin ciki da ganin ka, nace duk yanda za ayi yau dai a kawo ni wajen sarki mu gaisa, shi ne na saka Parida kanwar surkata ta rakoni muka taho tare" Mai martaba yace "Madallah, ai ba a jima ba aka kirani ake sanar min wakilan da na tura sun isa can gidan Alhaji Aliyu, kuma anyi komai lafiya har an tsaida lokaci ban san ko sun sanar maki daga Kanon ba" Nenne da ta bude ido sosai tana sauraron abinda Sarki ke cewa tayi kasa da murya tace "Wallahi ba a sanar min ba, kilan Aliyun zai ce a jira in dawo kafin a sanar min, amma nayi farin ciki da wannan abun arziki haka, ai hada zuri'a da kai Mai martaba abun alfahari ne abun farin ciki ne, nayi murna sosai, Allah Ubangiji ya sanya alkhairi..." Maganar da Umma ta kira Aunty Farida zata yi mata kenan kafin shigowar Mai martaba da Nenne ke tayi mata bala'i, Aunty Farida ta dade bata ji farin ciki irin na wannan lokaci ba, she is finding it hard to believe it, yanxu har an aika neman auren Khaleesah kenan amma ko da wasa daga Jay har Ajay babu wanda yace masu komai all this while, kuma kullum sai sun je can gidan Aunty Murja, Nenne ta nuna masa Aunty Farida tace "Kanwar uwar yarinyar kenan uwar su daya uban su daya, ita kanta bata sani ba banda yanxu da muke ji tare..." Sarki ya jinjina kai yana kallon Aunty Farida yace "To Madallah, ke ya sunan ki..." Nenne ta gyara zama tace "Parida, sunanta Parida Isuhu, tun tana er shekara goma Aliyu ya daukota daga gaban iyayenta a Nijar ya kawota gaban yayarta wato uwar wannan jikar tawa da aka je neman aurenta yau, to Ali ne yayi mata auren fari aka zo zaman babu dadi kuma gashi abokinsa ne mutumin saboda ya yarda da shi ya basa ita ga manema kaca kaca ya hanasu, to daga karshe dai da kansa ya amso mata takardarta ya raba auren ganin tana cutuwa gashi ita ba me baki bane sai dai kuka, to tun sannan har yau tana gaban Ali, duk wanda ya zo neman aurenta sai taki basa hadin kai yau shekara bakwai kenan, duk bayan wasu shekaru za su shirya su je gaida iyayensu ita da yayarta a Nijar, iyayen nasu buzaye ne mutanen kirki wallahi, aure me hada mutanen arziki ga shi ya hada zumunci tsakanin Nijar da Najeriya" Mai martaba yace "Wannan gaskiya ne Baaba" Nenne tace "To tun da har mun samu ganin ka har mun gaisa, to ina ga mu za mu zo mu koma Ranka shi dade kar mu shiga lokacin ka" Mai martaba yace "A'a, ku bari a karasa da ku bangaren fulani ku samu ku ci wani abun kafin ku tafi Baaba, bazai yiwu ku tafi baku sha ko ruwa ba a masarautar nan..." Nenne zata yi declining offer din nasa sai ga kanwar Aunty ta shigo parlon da sallama tana rike da bowl din fresh fruits, tare da Auntyn suke amma ita tana can baya tana tafe tana waya don wani lkcn in har Aunty zata kawo ma Mai martaba abun ci ko sha kanwarta ke rike mata har zuwa parlonsa in ta ajiye sai ta fita, Sarki na kallon Zuwaira yace "Ki shiga da baƙin nan cikin gida Zuwaira, ayi masu duk abinda ya kamata" Zuwaira ta kalli Nenne sai kuma ta kalli Aunty Farida dake kallon direction daban hakan yasa bata ga fuskarta da kyau ba kawai dai tasan fara ce kamar za a latsa ta jini ya fito, kallon Mai martaba tayi da ladabi tace "To ranka shi dade" Ta kalli Nenne ta gaisheta a takaice sannan tace "Mu je" Nenne ta mike bayan ta amsa gaisuwanta, Aunty Farida ta sauke Nikab dinta sannan ta tashi ita ma, hada ido suka yi da Mai martaba, tayi masa sallama ta bi bayan Nenne dake biye da Zuwaira, sun fita daga parlon kenan sai ga Aunty cikin shiga ta alfarma ta sha gwala-gwalai tana taƙu dai dai, daga sama har kasa take kallon Nenne da Aunty Farida dake sanye da Nikab, Aunty ta kalli Zuwaira tana yatsine fuska tace "Su waye wannan kuma Zuwaira?" Zuwaira ta taɓe baki tace "Oho, Mai martaba ne yace in shiga da su cikin gida, a parlonsa na same su" Nenne ta kwantar da murya tace "Ina wuni Pulani, baƙi ne daga Gombe...." Ko amsa gaisuwan Nenne Aunty bata yi ba ta shiga parlon Mai martaba, Zuwaira tana kallonsu a walakance tace "Mu je don Allah ina da abinda zan yi ni kam...." Bata jira cewarsu ba ta ci gaba da tafiyarta, Nenne ta kalli Aunty Farida, sai da taga Zuwaira tayi nisa sannan tayi kasa da murya tace "Parida kira mana Ahamad kice mun gana da Sarki ya fito ya maida mu gida" Ko Nenne bata ce haka ba dama Aunty Farida bata yi niyyar bin Zuwaira ba, haka nan suka canza hanyar da zai sada su da Compound Aunty Farida na kokarin kiran Ajay ta wayarta... Aunty na shiga parlon Mai martaba tana kallonsa tace "Ranka shi dade, wasu baƙi ne wannan aka kawo su har cikin parlon ka? Kuma ni ban taɓa ganinsu ba alamar babu abinda aka hada da su, ita dayar Nikab ma ta saka balle in ga fuskarta, su waye ne su da za su shigo har wannan parlon bayan ga can inda ake sauke baƙi?" Calmly Mai martaba yace "Ina ce kin gaisa da su ai?" Aunty ta ɗan hade rai tace "Eh, wai daga Gombe suke in ji tsohuwar" Mai martaba yace "To haka ne" Mikewa yayi yace "An sanar min ina da baƙi a fada yanxu, zan je in same su Fulani" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* 07087865788 Bear with me pls, I am not well HALYSAAH 94 Calmly Ajay ke driving bayan sun baro masarautar, yana ta sauraron Nenne da tun fitowar su take fadin irin kirkin Mai martaba tana sa masa albarka, shi dai ba abinda yace don kawai gani yake ba a tare su da kyau ba, yasan dai Abbansa zai sake masu kamar yanda ya saba yi ma kowa amma mutanen cikin masarautar will never do so, ita dai Aunty Farida hankalinta na kan wayarta, Sai duk yaji bai ji dadi ba don ya fahimci ko ruwa basu sha ba balle har a basu wani abinci, ko da gangan Aunty zata iya hanasu barin ace ta samu labarin shi ya kawo su gidan, Nenne tace "Toh wai Ina Ahamad din, ko a masarautar ma fa bamu gansa ba" Sai a sannan Ajay yace "Ya je ajiye Baabarsa unguwa" Nenne tace "Allah sarki, iya sarki kawai mu ka samu muka gaisa da, kai ma kaga ko Baabar ka bamu gani ba" Ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Ni Mahaifiyata ta rasu" Nenne tace "Allahu Akbar, Allah sarki, Allah ya ji ƙan ta, ya gafarta mata, to ko dai kishiyar baabar taka muka gani za mu fito parlon Mai martaba, wata tana nan ita ba fara ba, sannan tana ɗan da narkeken jiki ba can can ba, tana da matsakaicin tsayi" Ajay yace "Eh..." Nenne tace "Amma dai bata da kirki kwata kwata, saura kadan ta walakanta mu in gaya maka" Ajay ya kalli Nenne ta madubi yace "Ta maku magana ne?" Nenne tace "Ina fa, ina gaisheta ko amsawa bata yi ba ta sha gwala-gwalai, ni na zata ma uwarka ce shi yasa na ja bakina nayi shiru ban gaya maka ba" Ajay yayi shiru, kuma bai yi mamaki ba kwata kwata, after a while yace "Ku yi hakuri, yawanci bata son baƙi dama" Nenne tace "To er sarkin wani gari ce take wannan uban girman kan haka da rashin son talakawa?" Ajay ya ɗan yi murmushi bai dai ce komai ba, sun yi tafiyar kusan minti talatin kiran Mai martaba ya shigo wayarsa, dagawa yayi ya kai kunne tare da sallama, after some seconds yace "Eh muna hanya ne yanxu zan maida su, na zata kun yi sallama ranka shi dade...." After few more seconds ya ajiye wayar ya kalli Nenne yace "Dama baku yi sallama da Sarki ba?" Nenne tace "Cewa yayi a shiga damu a bamu abun sha, da naga ba arziki yasa muka ki bin yarinyar tana nan wata kitiɓir kitiɓir da ita, dama Parida da nasani ba zuwa zata yi ba don bata son rainin wayo" Ajay yace "Ohk, yanxu yake gaya min ai baku yi sallama ba" Nenne tace "Tun da mun gansa ai an wuce wajen kawai, wataran za a sake haduwa in sha Allah" Suna kusa gidan Aunty Murja after 40 Mins ride Ajay ya ajiye wayarsa da yake driving yana dannawa, bayan sun shigo unguwan ya kalli Aunty Farida yace "Mai martaba ya bada sako a baku, na tura a account din Jiddah" Aunty Farida ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "To mun gode Allah ya saka da alkhairi" Nenne tace "Wallahi mu ba don ya bamu komai muka je gaishesa ba, banda shi din babba ne ai da nace kawai a maida masa, amma dai babu laifi, don Allah kayi masa godiya in ka koma gida tunda bamu da wata hanyar yi masa godiya" Ajay yace "In sha Allah" Suna shan kwanan gidansu Aunty Murja, Nenne ta fara hango Khaleesat karkashin bishiyar mangwaro dake gaba da gidan Aunty Murja da dogon sanda a hannunta ita da yaran gidansu Aunty Murja tana tsalle tana plucking Mangwaro, tsohon zanin Aunty Murja ta daura sai er karamar Hijab da slippers a kafarta, Nenne taji kunya ya lullubeta ta rike haɓa tace "Kwance fa muka baro ta sheme sheme daxu ba lafiya, yanxu meye wannan take yi cikin 'ya yan cikinta fisabilillahi?" Khaleesat bata hangosu da wuri ba don da suna shan kwana taga motar zata gudu ta shige gida tun basu karaso ba, sai kawai yara taji suna Nenne Oyoyo bayan sun ga motar, ta juya suka hada ido da Ajay dake kallonta a gaban motar, sai yanxu ya kara tabbatar da ashe yarinya ce er karama sae rashin kunya idan ta samu waje, Tuni Nenne ta sauka daga motar tana kara yi ma Ajay godiya, Khaleesat ta bi bayan Nenne da sauri zata shige cikin gida, Nenne ta hade rai tace "Baki da kai ne, baza ki je ki gaishesa ba tunda kin riga kin kunyata mu, meye hadin ki da bishiyar mangwaro kamar mayya, yanxu da tare muke da Ahamad din shi ma haka zae ganki kamar almajira" Khaleesat ta wani turo baki tace "To haka zan je, ai ba sai na gaishesa ba" Nenne tace "Ina ruwan sa dake idan kin je a hakan? Wannan ai ba sa'an yin ki bane, kina ganin mutum kamili ga nutsuwa wanda magana ma sai ya ga dama, ai ke Ahamad din shi ne dai dai ke shi zai dau ko wani kalar shirmenki da wauta tunda shi faram faram yake, yanxu banda shirme godai godai dake ki shige cikin yara kina tsalle zaki tsinko Mangwaro da kodadden zanin Murja" Khaleesat tace "Wallahi bazan je ba, ai ba wajena ya zo ba" Nenne tace "Ni zaki kunyata? Mutumi ya gan ki kice baza kije ki gaishesa ba dubi yanda yayi ta sintirin zuwa unguwan nan da Ahamad suna zuwa duba ki, sannan ya zo yau ya dauke mu ya kai mu har gaban ubansa yau, ni dai ki rufan asiri ki je ki gaishesa, ai babu dadi haka Khaleesah, dama bai ganki bane wannan daban" Khaleesat ta kalli Aunty Farida dake tsaye jikin motar suna magana da Ajay, can ta fara tafiya zuwa wajen, tana isowa Aunty Farida ta wani kalleta sai kuma tayi ma Ajay sallama ta bi bayan Nenne zuwa cikin gida, Khaleesat ta jingina jikin motar tana kallon wani direction daban, dama tun shekaranjiya take jin haushinsa baya ce mata ya jiki duk ciwon da take ta yi, sai dai kawai ya zo yayi ta kallonta, tada motarsa yayi ita dai bata matsa jiki ba kuma bata kallesa ba, taji yace "Baza ki bar nan ba??" Sai a sannan ta juya ta kallesa, yana kallonta da kyau yace "In kika samu waje ba karamar kazama bace ke, i am telling you this for free...." Ita kanta bata san me yasa ta fara dariya ba kamar warce ake yi ma cakulkuli, reverse ya fara yi ta zaro ido ta koma baya tana kallonsa tace "Buge ni kake son yi?" ko kallonta bai yi ba a haka ya juya ya bar unguwan, kallon kanta tayi daga sama har kasa, sai kuma ta taɓe baki tayi wucewarta cikin gida yara na biye da ita da Mango din da suka tsinko... Da daddare Ajay na zaune parlon Abbansa yana saurarensa kansa a kasa, Mai martaba yace "To amma ku menene dalilin ku na boye min gaskiyar lamarin gaba daya? Ko kai ka basa shawaran kar ya gaya min gaskiya? Sannan duk saboda yana son ya aureta ne duk yayi mata wannan hidima?" Ajay yayi kasa da murya yace "Ko daya Abba, need din fadin gaskiyar ne bai yi arising ba sai yanxu ranka shi dade, taimako kuma kai muka yi kwaikwayo don da haka muka san ka, nasan Jawwad duk abinda yayi mata ba yayi mata bane saboda yana sonta da aure at first, he did all what he did for God sake ba don ya aureta ba, tausayinta ne yayi leading har yaji zai aureta, kuma idan ba auren tayi ba tsohon mijinta will keep on hunting her" Mai martaba yace "Kuma duk zuwa biyun da nayi Amurka tare nake ganin ka da yarinyar a maimakon Jawwad din ae" Ajay ya kallesa, sai kuma ya sauke kansa yace "I helped him with some responsibilities too" Mai martaba yace "Then why were you trying to cover that up? Kace komai shi yayi" Ajay yace "I am not hiding it sir, we were all protecting her from her Ex differently, shi yasa har kake zuwa kake samunta a gidan..." Mai martaba yace "Duk yanda zaka kare kanka you are very good at that Junaid, shi kuma Jawwad always take the Consequences no matter how deep it is for you" Ajay yayi shiru trying to understand what his dad meant, after some seconds Mai martaba yace "Shikenan.... Kai ya batun naka maganar auren?" Ajay yayi shiru bai ce komai ba don shi kansa ya gaji da tsara new excuse kullum, Mai martaba ya ɗan yi murmushi yace "Karyar taka ta kare kenan?" Ajay dai bai ce komai ba. Ranan laraba Nenne ta gama hada kayanta a er jakar da Aunty Farida ta ara mata don a buhu ta so saka kayan nata tun daga Kano, Nenne na kallon Aunty Farida tace "Kar fa su zo su yi ta jiranmu Parida kiyi da jiki" Ita dai Khaleesat na zaune ta jingina da bango a dakin Aunty Murja idonta yayi jajir saboda kuka, Nenne tace "Ke da naga har kin saba da yaran unguwar, baki bishiyar mangwaro baki bishiyar Amburela ke da yara kuna tsinkar 'ya yan itatuwa, to me zai dameki don ance ki zauna kiyi sati biyu ayi maki magani ayi maki gyara yanda ya kamata, kin zata gidan sarauta gidan banza ne da za mu bari ki shiga kamar gantalalliya kai tsaye, miliyan biyu sarki ya bada a bamu da Parida amma haka nan na kashe kusan dubu ɗari biyu akan ki ina nema maki taimako saboda Allah, sannan ga gyaran jiki da za ayi maki tunda ba wani lokaci me tsayi aka saka na auren ba, Ina laifina a nan daga abun arziki?? So kike mu kwashe ki mu koma Kano Awdul din ya ji dadin sungume ki mu shiga uku, babu abincin da yaron nan Ahamad bai ajiye maki ba a gidan nan na jin dadin rayuwa, gashi shi da ɗan uwansa suna zuwa ganin ki, har wata panka me tsada ya siya maki saboda zafi da daddare yarinyar nan ke kadai kike saita pankan dai dai inda kike kwanciya mu kuma zafi ya kashe mu, to me kike so da ya wuce haka? Ai gwara tun yanxu ki fara sabawa da zaman Bauchi tunda nan aure zai kawo ki, Kano da zan koma cikin gaggawa duk domin ki ne inje asan shirye shiryen da za ayi na biki tunda ga damin kudi har dubu dari takwas a lalita ta, ki fa ji tsoron Allah Khaleesah" Aunty Farida dai ko kallon Khaleesat bata yi ba don dama a ranta tace bazata sake lallabata ba tunda kamar tunzurata ake kara yi in ana lallabata, ita ai duk tunaninta tun bayan da Abdul ya koya mata rayuwa ta ajiye wani shagwaba da iskanci a gefe ta canza hali, ashe ba haka bane waje ne bata samu ba kukan banzan na nan har yanxu, a haka su Jay suka iso za su kai Nenne da Aunty Farida park, Ba Ajay kadai ba hatta Jay sai da yayi shock da Khaleesat a kofar gidan don tara masu jama'ar anguwan tayi da kuka da ruri a kofar shiga gidansu Aunty Murja ita baza a tafi a bar ta ba, Aunty Murja na aikin lallashinta, Nenne ta dinga kauda kai tana daura gyale a kai tana rufe fuska tsabar kunya, Aunty Farida dama tuni ta shiga mota don bata da lokacinta, Jay dai ya kasa cewa komai don bai san lamarinta ya kai haka ba, can ya kalli Aunty Farida yace "Aunty ko dai kawai ta dauko kayanta ku tafi" Aunty Farida tace "Ai babu inda zata je sai tayi kwanakin da aka ce tayi a gidan nan tunda gidan kanwar Babanta ce" kiris ya rage Ajay bai yi dariya ba a front seat yana kallon Khaleesat, bakin ciki kamar ya kashe Nenne don Khaleesah ta gama kunyatasu gaban surkai, Jay ya bude driver seat ya sauka ya nufeta, tana ganinsa ta bar wajen da sauri alamar bata ma son jin abinda zai ce mata kuma bata fasa rusa kukan da take ba, Nenne ta kalli Ajay cikin sanyin murya tace "Kaga mu yarinyar nan zata kunyata ta tona mana asiri a unguwan mutane ko? Gudun wancan yaron Awdul ya sa fa nace ta zauna nan ko na sati biyu ne shi ne take mana wannan tijara haka kamar mun ajiyeta wajen yankan kai" Ajay dai yayi murmushi kawai ya bude motar ya sauka ya koma driver seat ya zauna, da su Nenne basa wajen tsaf babu abinda zai hanasa korata da dorinar gaban motar, ya danna ma Jay horn alamar ya shigo su wuce, Nenne tace "Madallah, gwara ya kyaleta da halinta ya shigo mu wuce don ba sauraronsa zata yi ba" Da kyar Aunty Murja ta shiga cikin gida da Khaleesat, Jay ya dawo ya bude front seat ya shiga, Nenne tace "Mu bamu san har yanxu bata dena wannan shagwabar ba wallahi, ko kanninta basa mana wannan iskancin mu dai" Duk bayan sati hudu zuwa shidda ake shirya meeting a fadan dake bangaren sarki, wanda kusan kowa na family din ke halartan wannan meeting din barin wa enda ke gari har ma wasu da ba gari suke ba kuma suna da sararin zuwa, tun daga jikoki, 'ya ya, kanni, yayyi, cousins da dai sauransu, akwai kuma meeting da ake yi bayan wata uku amma ba na kowa da kowa ba, duk meeting din da za ayi Mami bata taɓa halartan ko daya, don ko tana gari bata zaman meeting din, rabonta da zama ayi meeting da ita zai fi shekara goma, sai dai daga baya a gaya mata me aka yi wajen meeting din, duk aka yi mamakin ganinta a wajen ranan, shi kansa Jay was surprise seeing her at the meeting, sai da ta jira aka gama meeting lafiya sannan daga karshe tace tana da magana, Sarki na kallonta ya bata daman magana, Aunty ta gyara zama don duk tare suka shirya komai, Kai tsaye Mami ta fara magana tace "Ranka shi dade, duk da ni dai nasan bani da matsayin da za a sanar min abinda aka zartar kan Jawwad, amma dai na samu labarin har an kai kudin aurensa Kano, to ni duk wannan ba matsalata bace don yawanci duk abinda ya shafesa dama sai an zartar nake sani, to babban abun tambaya a nan shi ne haka aka je neman auren babu bincike kenan ranka shi dade?" Wata cousin sister din Mai martaba wanda duk ta girme ma matan dake zaune gun meeting din cikin fushi tace "Ki kula Fulani da sarki fa kike magana, ya kamata ki tausasa kalamanki ki kuma san abinda ke fitowa bakin ki" Mami ta wani kalleta daga sama har kasa, shi dai Mai martaba kallon Mami kawai yake, Ajay ya kalli Jay dake kallon Maminsa shi ma with shock, Mami ta ci gaba da maganarta babu yabo babu fallasa tace "To idan kuwa haka aka je neman auren yarinyar nan babu bincike ya kamata a koma ayi bincike kasan wacece kake kokarin hada ɗan ɗan uwanka aure da, ni da ya zame min dole tunda ɗa na ne shi nayi iya binciken da zan yi ban ga ta inda aure zai kullu tsakanin Jawwad da yarinyar nan ba, don kuwa shi din ba sa'an aurenta bane ta ko ina...." Bayan kusan minti daya Mai martaba yace "Fulani, no one is in the rightful place to question my decision in this palace, duk abinda na zartar hakan zai kasance in sha Allah, babu me canza hakan har ke da kike mahaifiyar Ahmad...." Mami tace "Kana nufin ka zartar da hukuncin Jawwad ya auri bazawara mara cikakken asali sannan er kananan mutane?" Tsawa Hajiya Shafa'atu da ta fara yi ma Mami magana tun farko a parlon ta sake yi mata tace "Kina cikin hayyacin ki kuwa Fulani? Shi Mai martaban kike furta ma wa ennan kalaman? Menene wannan ya same ki?" Rai bace Mami tace "In dai akan Jawwad ne baza a taɓa samuna cikin hayyacina ba, yau in uban Jawwad na da rai zai yarje ma Jawwad auren bazawara mara asali? Bazawara fa? Anya an duba ma uban Jawwad da ƙasa ta rufe ma ido kuwa? Yau don babu shi a duniya sai ayi ma ɗan sa haka?" Kowa dake zaune a fadan was speechless and shock at Mami's action banda Aunty, Mami ta ci gaba kanta tsaye babu ko shakka tace "In lamarin gaskiya ne a aura ma Junaid da ko macen auren bashi da ita har yanxu mana, sai Jawwad da kowa yasan da maganarsa da Hadiyah?" Mai martaba ya ɗan yi murmushi, abubuwa da yawa suka sa yake raga ma Mami kuma zai ci gaba da raga mata saboda abubuwan nan, bazai taɓa daukan mataki akan ta ba, with calmness yace "Ai Junaid bai kawo min ita yace yana so ba Fulani, don haka shi Jawwad din da ya ganta yace yana so shi din dai zai aureta ko ki amince ko kar ki amince, idan kuma da inda aka haramta auren bazawara a addininmu Enlighten us" Yana kai wa nan ya mike, Hajiya Shafa'atu ta fara basa hakuri cikin girmamawa tana jero masa kirari, Jay couldn't believe all what his Mami was saying, he was just shock and weak, Mai martaba na barin fadan Ajay ya mike shi ma zai fita, cikin fushi Aunty da Mami suka hada baki wajen cewa "Munafiki, me mugun nufi, duk kai ka hada wannan tuggun...." Shi dai ko kallon inda suke bai yi ba har ya fita, Mami ta ci gaba tana huci tace "Sai dai in bayan raina ne za a aura ma Jawwad bazawara wallahi, ai in an san wata ba a san wata ba" Tana kai wa nan ita da Aunty suka fice daga fadan, kuma duk wannan abun da Mami tayi bata yarda ko da wasa ta hada ido da Jay ba ko kuma ta kalli inda yake, yi ma tayi kamar bata san yana padan ba. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* 07087865788 HALYSAAH 95 Ajay ya bude kofar dakin Jay a hankali yana kallonsa, zaune ya samesa kan kujera yana danna wayarsa, karasawa cikin dakin yayi ya zauna still looking at him, shi dai Jay bai kallesa ba he was just pressing his phone, wani lokacin har mamakin karfin hali irin nasa Ajay yake yi ga dakiya da basar da duk wani situation that is a threat to him in anyway, bayan kusan minti daya Ajay yace "I think this shouldn't be something to be worried about Bruh, I guess you weren't expecting less duba da cewar baka sanar masu wacece yarinyar da kake son aure ba, sannan baka gaya masu matsayinta ba so their reaction is nothing to be surprised or worry about, even our dad was a bit disappointed at first after finding out truth, so sauran ma duk za su yi give up su hakura daga karshe, just that you have to turn deaf ear since the king is fully in support of you" Shi dai Jay bai ce komai ba kuma bai ɗago kansa ba, mikewa Ajay yayi yace "Abba yace kaje yana jiran ka..." Daga haka ya juya zai fita daga dakin sai kuma ya karasa gaban mirror dake dakin ya dau turarensa biyu da Jay ya ajiye wajen, ta madubi yaga Jay na kallonsa, Ajay ya bude turarurrukan yana perceiving kamshinsu yace "Why will you hijack my birthday gift..." Shi dai Jay bai ce masa komai ba, Ajay ya dau wanda kamshinsa yayi masa ya bar masa dayan sannan ya fita daga dakin. Jay na zaune gaban Mai martaba idonsa a kasa yana sauraronsa, Mai martaba yace "Don haka ka kwantar da hankalin ka Ahmad, babu me hanaka auren yarinyar nan as far as I am concern don baza a maida ni karamin mutum ba, Fulani kuma ka kyaleni da ita ni nasan yanda zan yi da ita, kaje ka ci gaba da shirye shiryen ka tunda kaga ba lokaci me tsawo aka tsayar ba don nasan ire iren issue din nan dole zai yi arising daga ɓangaren iyayenka mata dama, daxu mun yi magana da Shafa'atu akan kayan da ake hadawa na aure, so ita zata hada na ita wancan yarinyar, su kuma nan su hada na Hadiyah ina ga zai fi" A hankali Jay yace "Nagode Abba, Allah ya kara girma" Mai martaba yace "Za ka iya tafiya Ahmad" Mikewa yayi Mai martaba ya bi sa da kallo har ya fita. Jay na fita parlon Mai martaba babu dadewa sai ga Aunty ta shigo parlon, ta ajiye masa fruit din da ta kawo masa ta zauna tayi masa sannu da hutawa sai kuma tayi shiru, bayan wani ɗan lokaci cikin kwantar da murya tace "Ranka shi dade dama wata er shawara ko ince suggestion nake son badawa idan ka bani dama" Sarki na kallonta calmly yace "Ina jin ki Fulani" Ta gyara zama cikin nutsuwa ta fara magana tace "Ranka shi dade akan zaman Meeting din daxu ne da aka karesa babu dadi a zukatan mu gaba daya, sam ban ji dadin irin maganganun da Fulani Asiya tayi maka akan ɗan ta ba a gaban kowa da kowa, kuma ba yau ta saba maka irin wannan ba, amma na yau yayi min ciwo matuka, tun safe har yanzu bani da sukuni, ni kuma bana son biyeta mu yi batattciya a gidan nan, shi ne ni a nawa tunanin nake ganin for peace to reign da an hakura da batun auren ita bazawaran nan tunda har Asiya ta nuna bata so, yanxu zancen da nake maka maganar nan duk ya zagaye masarautar nan kan kace me kuma har cikin gari sai maganar nan ta fita, kaga nan jama'a za su dinga ganin don ba ɗan cikin ka bane shi yasa ka amince da bukatarsa na auren Bazawara, don guje ma wannan zargi ina ga zai fi kyau a ajiye batun auren yarinyar kawai mu yi facing na Hadiyah ranka shi dade, ba wannan karon bane na farko da mutane ke ganin kamar kana nuna bambanci tsakanin Jawwad da Junaid, ita dama Asiya kullum tunaninta a haka yake tana ganin baka yi ma ɗan ta adalci don kawai ƙasa ya rufe ma ubansa ido, to ina amfanin wannan ranka shi dade ana ɓata maka suna a gari? Tun asali bai kamata ka biye Jawwad da maganar nan ba duba da irin zaman da uwarsa ke yi da mu da wasu abubuwa marasa amfani da ta dauka ta saka a ranta taki a zauna lafiya, don haka ni a nawa karamin tunanin ya kamata kayi watsi da maganar bazawaran nan don a samu zaman lafiya a gidan nan ka kuma guje ma kanka zargin da jama'a za su fara yi maka, tunda ga ɗan cikin ka Junaid har yanxu ko buduwar auren ma bai da ita kuma baka ce lallai sai yayi ba, yanxu fa kamar ace Walid ya kawo maka bazawara mara asali yace zai aura ne, zaka fara sauraronsa? Amma fa ni a karamin tunanina nake magana ranka shi dade tunda ban fi ka hangen nesa ba, kuma ina fatan ban ɓata maka rai ba Ur Highness" Mai Martaba dake ta sauraronta ya ɗan yi murmushi yace "Kina zaune da ni shekara da shekaru kin taɓa ganin maganganun mutane ya girgiza ni ko ya hanani abinda nayi niyya Fulani?" Aunty tayi shiru, yace "Don haka in this case i don't think there is anything that will move me, as far as Ahmad is okay with marrying the lady, I am also okay with that, kawai dai Hadiyah ce zata zama matarsa ta farko kafin ita yarinyar wanda na riga na sanar da hakan tun farko, Walid kuma da kika ce in yau ya kawo min bazawa yace yana so zan basa shawara ya hada da budurwa duk a aura masa, hakan ma gata ne ai" Aunty ta sauke wani ajiyar zuciya ganin babu nasara a plan din nan ma, shiru tayi bata sake cewa komai ba. Har washegari Jay bai yarda ya hadu da Maminsa ba cause deep down he was really disappointed, tun jiya har yau bai dawo dai dai daga shock din da ya shiga ba, it was something he never saw coming, ko da ya dawo masallaci ko zuwa gaisheta kamar yanda ya saba bai yi ba ya koma bangarensa ya kulle, bai san ita ma ana idar da asuba ta bar masarautan ba da traveling luggage dinta.... Wajen karfe shidda na yamma Malam Ali na tsakar gida bakin pampo yana alwala, Nenne na zaune kan farin kujeran roba tana kara jaddada masa abubuwan da za ayi ma Khaleesat na fita kunya tunda ba karamin gida za a kai ta ba, Tace "Wallahi Ali sai kaga setin kayan gadon aka ce mana miliyan uku babu ragin ko biyar, setin kujeru kuma Miliyan biyu cif cif, in ba 'ya yan sarakunan ba ma ni bana jin akwai er da za ayi ma wannan setin kayan dakin, ko iya su muka kai mata babu me renamu wallahi, akan dai ace mu cakalkala kudi mu siya mata tarkacen banza masu arha da baza a ga darajarsu ba, don haka ni dai ga dubu dari biyar ina da shi a ajiye, Parida zata kawo Miliyan daya tace, ita Zahra'u dama babu ita a lissafi in ba dogon hancinta zata kai kasuwa ta siyar ba, don haka nake baka shawara wannan gidan nan naka na Mariri da nawa ka siyar kawai mu fita kunya, ko miliyan hudu aka samu aka siyar da gidajen kaga ai sai mu fitar da er mu kunyar gidan sarauta Ali, wallahi hankalina a tashe yake ga lokaci da aka sa ba mai tsawo ba, kan kace me zaka ga kamar gobe ne" Malam Ali dake ta sauraronta ya idar da alwalan da yake sannan yace "Allah ya rufa asiri ya nuna yanda za ayi amma siyar da gida kam bai taso ba Nenne, shikenan fa gare mu...." A fusace Nenne tace "Baza ka raba kanka da kalman nan na shikenan gare ka ba, shi kuma wannan da muke ciki na gwamnati ne?" Malam Ali dai bai ce mata komai ba, don su ne suke ma gidan nan kallon gidan zamansu amma banda shi, har cikin ransa ya riga ya sa cewar gida ne aka basa ya zauna na ɗan wani lokaci ya tashi, Tsayuwar mota suka ji a kusa da gate, Nenne ta kalli gate din, can tace "Kaddai tsinannun iyayen Awdul din ne suka sake biyo ka..." Mikewa tayi ta nufi gate din fuskarta babu rahama, wasu manyan mata ta gani har su hudu cikin shiga ta alfarma, suna kallonta suka ce sannu, Nenne ta koma gefe tace "Yauwa sannun ku, ko batan hanya ku ka yi ne" Daya daga matan tace "Ba nan ne gidan su Halysaah ba?" Nenne tace "Eh nan ne, Khaleesat ba, Malaman makarantar su ne halan?" Matar tace "To mu dai shiga daga ciki ko?" Nenne ta juya ta koma ciki da sauri tana cewa "Bisimillan ku, sannun ku da zuwa, ai Khaleesar ma ta ɗan yi tafiya bata nan, amma ku shigo ciki" Suna biye da ita har zuwa parlon gidan, shi dai Malam Ali bai ce masu komai ba kamar yanda babu wanda ya ce masa komai balle su gaishesa, Nenne na shiga parlor ta kora yaran Mama Shatu dake zaune suna kallo, duk suka fita daga parlon, ko wacce a cikin matan ta samu kujera ta zauna a parlon, Nenne na murmushi tace "Halan kun samu labarin an sa mata rana ne, bari in kira maku uwarta tana ciki" Da sauri Nenne ta tafi dakin Umma ta sanar mata Khaleesat tayi baki kamar Malaman makarantar su a Amurka don ko wacce shiga tayi ta alfarma ga gwala-gwalai, a tare Umma da Aunty Farida suka fito parlor, haka kawai Umma taji gabanta ya fadi, ta dai karaso parlon ta zauna ta gaishesu duk suka amsa, Aunty Farida ma ta gaishesu tana kallonsu, ledan pure wata guda Nenne ta kinkimo ta kawo masu tsakar parlon ta ajiye tana cewa "Wallahi yaran duk sun shanye wanda ke prij me sanyi" Matar dake tanka Nenne tun daxu tace "Mun san duk baku san mu ba, baku kuma san daga inda muke ba" Nenne ta daga kai ta kalleta, sai kuma tace "Ba Malaman makarantar su Khaleesah bane a Amurka?" Matar tace "Ko daya, ni sunana Hajiya Fatima, kuma ni din kanwata ce ga Mai martaba Sarkin Bauchi..." Ƙabbara Nenne ta saki ta mike tsaye tana tafe hannu tace "Lale lale, lale marhaba, sannun ku da zuwa, ashe manyan baƙi muka yi bamu sani ba, wallahi ba a sanar mana kuna hanya ba" Hajiya Fatima tace "Yana da kyau dai ki fara sauraronmu ki ji me ke tafe da mu tsohuwa" Nenne ta zauna kan Carpet tana kara masu sannu da zuwa baki har kunne, Hajiya Fatima ta nuna warce ke zaune gefenta tace "Fulani Asiya kenan, matar yayanmu Marigayi sarki Ahmadu Yusuf, mahaifiya ga Ahmad Jawwad...." Nenne tayi shiru tana kallon Mami da idanuwanta kamar za su fito, haka ma Umma da Aunty Farida da duk jikinsu yayi sanyi tun Hajiya Fatima bata fara introduction ba, suna ganinsu sun san babu alkhairi a tattare da zuwan su dama, Hajiya Fatima ta ci gaba da magana cike da isa da gadara tana nuna warce ke zaune 2 seater tace "Wancan Hajiya A'isha kenan kanwar Fulani Asiya, ta kusa da ita kuma Hajiya Nafisah kanwar matan Mai martaba Sarkin yanxu...." Nenne tayi karfin halin cewa "To Allah Ubangiji dai yasa lafiya, don ni ban gane kan wannan zuwan naku ba kuma" Hajiya Fatima tace "Gaskiya ba lafiya ya kawo mu ba tsohuwa, duk da zuwa muka yi cikin lumana ba tare da wani tashin hankali ba" Nenne ta ɗaga kai ta kalleta baki bude, cikin nutsuwa Mami ta fara magana tace "Ni ce Mahaifiyar Jawwad, kuma Jawwad shi kadai Allah ya bani a duniya, a burikan da nake da shi kan Jawwad a duniya babu auren bazawara ciki, ko kuma auren wata kabila can baya ga cikakkiyar Hausa Fulani, tun daga neman auren da aka zo aka yi na ɗa na har saka rana bani da masaniya akan ko daya, sannan duk wani bautatawa da kashe uban dukiya da Jawwad ya dinga yi akan er ku da ma ku kanku babu wanda ban sani ba, amma duk ba wannan ne damuwata ba, kuma bazan ce zan amshi duk wani abu na alkhairi da yayi maku ba, kamar yanda nace maku mun zo cikin aminci ne babu tashin tashina, don haka tun da girma da arziki ku cire ran auren er ku da ɗa na Jawwad idan ba haka ba wallahi duk wani mummunan matakin da na dauka a kanku ku kuka siya, er ku ba sa'ar auren Jawwad bace don shi din ɗan gidan sarauta ne, ɗan sarki jikan sarki babu abinda zai yi da er ku bazawara, kai ko da ba bazawara bace wallahi babu abinda zai yi da wata kabila warce ba ma na kasar nan ba, ina sake jaddada maku tun da girma da arziki ku janye batun auren er ku da ɗa na...." Cousin sister din Aunty me suna Aunty Nafisa tace "Iya tatsarsa da ku ka dinga yi ma ya isa haka, don hidimar da yayi maku in muka ce yafi na miliyan dari biyu tsaf bamu yi karya ba, da ace tsiya ya kawo mu hatta gidan nan wallahi sai mun kwace amma mun zo maku cikin lumana don mu din ba kananun mutane bane kuma mun fi karfin dukiyar da Jawwad ya kashe maku, kawai abinda za ku yi a zauna lafiya shi ne ku janye batun auren nan cikin ruwan sanyi tun kan tijara ya biyo baya" Har sannan Nenne ta kasa rufe bakin da ta hangame zaune kan Carpet with shock, Aunty Farida tayi wani murmushi tana kallonsu daya bayan daya tace "Mu janye batun aure sai kace mu muka je neman auren Jawwad din? Ina ce wa enda suka zo neman aure su za su dawo su janye sannan su amshi kudin da suka kawo, kuma ni a iya sanina ba mata bane suka zo neman auren Khaleesat, mazan nan dai da suka zo neman auren su nake tunanin za su sake dawowa su ce sun janye a maido masu da kudin ɗan su, ko kuma mafi sauki in kin isa da ɗan ki ai tun daga gida zaki masa umarnin ya janye ba sai kin zo mana nan ba, a yanxu mu dai bamu da sauran magana da ku sai dai iyayenmu maza su saurari wakilan Mai martaba, duk da dai ban san ko gidan sarautar taku har dankwali da dankwali na zama batun neman aure ba" A tare Hajiya Fatima da Hajiya Nafisah suka mike suka daka mata wani tsawa suna nunata da ɗan yatsa, Hajiya Nafisah tace "Ke karamar er iska mu kike gaya ma magana? Kin san su waye mu? Who the hell do u think you are?" Aunty Farida ta ja wani dogon tsaki ta juya ta bar parlon alamar bata da lokacin ci gaba da basu amsa, Cikin azama Aunty Nafisa ta bi ta a fusace, Mami tayi saurin dakatar da ita tace "Dawo Nafisah, dawo, kyaleta kawai" Umma dake hawaye ta dinga basu hakuri a rikice tana cewa "In sha Allahu duk bazai kai ga haka ba, in dai ta bangaren mu ne babu batun wannan auren da izinin Allah, mu mun janye ba wannan batun in sha Allah, don Allah ku yi hakuri" Mikewa Mami tayi tana kallon Umma cikin nutsuwa tace "Da ya fi maku, don in baku janye cikin lumana ba za ku janye saboda tashin hankali, bana hada ɗa na da kowa, kuma ba don ko wace irin mace na haifo ma ɗa na a duniya ba, in ma wani abu ku ka yi ma Jawwad irin naku na yan kabilar ku to tun wuri ku warwaresa tunda kun tatsi arziki son ranku daga jikinsa har da siya maku gida, to duk nafi karfin abinda yayi maku bazan kuma ce zan amshe ba, kawai dai ina me maku gargadi da babban murya ku raba kanku da ɗa na, ku nisanta er ku daga ɗa na" Mami na kai wa nan ta nufi kofa, sauran matan suka bi bayanta suna yatsine yatsine, rabon Nenne da shiga irin wannan shock din tun da Motar yan sanda suka zo tafiya da Malam Ali farkon case dinsa da Baban Abdul, Umma ta zauna kan kujera ta dafe kanta ta dinga kuka, Mama Shatu dake makale bakin kofar dakinta sai zazzare ido take taki karasowa cikin parlon, Sai a sannan Nenne ta samu bakin sakin salati ta rushe da matsanancin kuka kamar warce aka aiko ma da mutuwa, Duk wannan abun da aka yi Malam Ali dake zaune Balcony yana ji, har su Mami suka fito basu ce masa komai ba suka nufi gate. Sai bayan Magrib Aunty Farida ta samu Ajay a waya, he was shock an speechless bayan ta sanar masa abinda ya faru don sai da ya mike tsaye daga zaunen da yake, gaba daya ya ma rasa me zai ce, after some seconds ya dake yace "Zan kira ki Aunty" Yana katse wayar ya fita zuwa bangaren Mai martaba, Sarki ya fi minti biyar bai ce komai ba bayan Ajay ya sanar masa abinda Aunty Farida ta gaya masa, kana ganinsa kasan ransa ya baci sosai, after another 2 minutes ya numfasa cikin nutsuwa yace "Dau waya ka saka min Number Mahaifin yarinyar" A hankali Ajay yace "Bani da numbersa ranka shi dade" Mai martaba yace "Sa min Number Faridan" Mikewa Ajay yayi ya dau wayar Mai martaba ya saka masa number Aunty Farida sannan ya mika masa, Mai martaba ya amshi wayar yace "Wannan karan zan yi maganin Aseeyah, i have tolerated her for so long for the sake of my late brother, amma zan nuna mata na fi ta iko da Ahmad, kuma juma'an nan mai zuwa in sha Allahu za a daura auren nan" Murya can kasa Ajay ya fara basa hakuri don har ya mance rabon yaga bacin ran Abbansa haka, Mai martaba ya mike yana rike da wayarsa ya shiga dakinsa, ashe duk wannan abun Aunty na tsaye bakin kofa tun da taga Ajay ya taho parlon Abban nasa ta biyosa ta tsaya bakin kofar duk tana sauraron su, mikewa Ajay yayi zai fita yaga Aunty tsaye bakin kofar tana masa wani matsiyacin kallo, sauke idonsa yayi ya canza wata hanyar don kofa biyu ne a parlon. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* 07087865788 HALYSAAH 96 Aunty farina na zaune tsakar gida da umma da malam Ali,umma dai tayi tagumi ko bakin magana bata dashi idanuwanta duk sun kumbura saboda kuka,Aunty farida sai jira take malam Ali yace masu ga yanda sukayi da maimartaba a waya amma yaki cewa komi,Nenne ta fito daga cikin gida tana rike da wayar aunty farida Don har ita sai da maimartaba yayi magana da ita,Nenne tace," inba adalin sarki ba waye zaiyi haka sai kunga yanda ya ajiye izza da girman kai irin ta sarakuna yana ban hakuri,har saida kunya ta kamani wallahi,yana bani hakuri ina basa hakuri,to ni ai inba shegiya bace ai dole In hakura,Amma zance na gaskiya na tsorata da lamarin uwar Ahamad,taban tsoro sosai banga alamar akwai abun arziki a tattare da itaba,naji kuma ina tsoron auren nan,ace khaleesat tayi auren farko bataji dadi ba nabiyu ma yazo mata a haka? Kunga ai bazamu bari ayi na biyu ba yarinya da karancin shekarunta tayi ta walagigi gidan aure har sai wani cutar yaje ya sameta,gaskiya nidai nasha jinin jikina gaskiya da auren nan gara kawai duk a hakura dan babu alamar alkhairi a cikinsa,tunda har uwar sa ta nuna bata sonta bazata taba sontaba har abada kuwa, sannan fa duk a yau mukejin ashe ba ita daya ma ashe zai aura ba,harda yar uwarsa budurwa itama jinin sarauta kuma duk a rana daya za a daura auren,Ina khaleesah ina kishi da jinin sarauta inba dai hallaka akeson jefa yarinyar ba ga uwar miji tun baayi auren ba ta nuna bata sonta gaskiya jikina ya mutu,akan abun duniya bazamu sake salwantar da rayuwar er mu ba" Cikin sanyin murya umma tace" Damani auren ya fice man arai gaba daya Nenne,Hakura zatayi Allah ya fiddo mata da wani mijin kawai Don babu Alkhairi a wannan auren dama aikowa tayi akazo da sauki akan ta tako da kanta tazo gidannan tayi abinda tayi gwara a hakura kawai.....Nenne ta katseta da sauri tace"Ai bazamu bari wannan ya fito daga bangaren mu ba Zahara'u duba da yanda sarki duk yabimu yayi mana magana ta waya, in bama shi dinba wane sarkin ne zaiyi haka? Ai iyaka saidai yasa na kusa dashi su kiramu su bamu hakuri a gantale Amma badai yayi waya damu muji muryarsa ba,Ki duba lokacin daya dauka yana waya da farida,Sannan yayi waya da malam Ali ma,nima kuma yayi magana dani duk yana kokarin sanyaya mana zuciya akan tijarar da er iskar mata tazo har gida ta mana,kinga ko Don wannan bazamu yarda ace daga wujen mu mukace mun fasa bada yarinya ba,nasan kuma wannan matar er bariki ba hakura zatayi ba gwara ace ita ta ruguza zancen Auren da kanta da dai ace mu muka ruguza,Sam Ahamad baiyi dacen uwa ba gashi yaro mai hankali da nutsuwa ga kirki amma uwa er duniya,mu bazamuce komai ba Albarkacin mai martaba saidai in su suka ce sun janye batun auren shikenan yazo ma kowa gidan sauki ,Aunty farida ta sauke ajiyar zuciya tace"hakane Nenne" Nenne tace Atoh,kai meye shawararka malam Ali?Ana magana sai kayi shiru kamar wani bare a cikin mu,sai a sannan malam Ali ya daka kai a karo na farko yace" Shawara ta shine zuwa gobe ko jibi mu tattara mu koma mariri tunda har an kusan gama gyaran da akeyi gidana baaba,idan mun koma to koma me zai biyo baya me sauki ne..... A mugun fusace Nenne tace "Toka tattara ka koma mana Ali wani ya rike ka ne? Mudai muna nan babu inda zamuje tunda bamu bude baki mun roki yaron nan ya siya mana gida ba,kuma takardun gida na hannun mu balle ace zaa kwace gidan,ko kuma mu siyar da gidan mu tashi mu koma wani wajen mu siya ba shikenan ba,Amma wallahi babu shegen daya isa ya rabamu da gidannan,ko shi Ahamad din bazai fara tunkarar mu da zancen gida ba tunda saboda Allah yayi kuma jinin marigayi sarki Ahmadu na yawo a jikinsa,mahaifinsa kuwa kowa ya shaida mutumin arziki ne "Nenne na kaiwa nan ta Mike rai bace tana kallon Aunty farida tace" Taso mu shiga ciki muyi shawara parida " Ali da matarsa in kace zaka zauna cikinsu kayi maganar Arziki ranka ne kawai zai baci a banza,ban taba ganin sumbudaddu matsorata irin su ba "washegari har gida maimartaba ya tura akaje ba malam Ali hakuri akan abinda mami taje tayi,Shidai malam Ali Allah ya sani he is not longer comfortable with his daughter getting married to the royal family, Sam hankalinsa bai kwanta da auren ba amma nauyin me martaba yasa ya kasa nuna hakan,gashi wanda sukazo basa hakurin sunce ranar jumaar nan zaa daura auren,shi kansa me martaba ya sanar masa da hakan a maganar da sukayi jiya,gaba daya ya rasa ta inda zai bullo ma lamarin gashi yasan nenne bazata taba tsayawa ta fahimcesa ba balle suyi abinda ya kamata dan ceto rayuwar Khaleesat,baya fatan abinda ya samu ersa a baya ya sake samun ta yanzu,bayan wakilan me martaba sun bar gidan wajen karfe takwas da rabi na dare ya dau wayarsa ya zauna tsakar gida yayi dialing number khaleesat,yana fara ringing khaleesat dake shafe shafe bayan tayi wanka ta daga Kiran,bayan ta gaishesa ya amsa yace "yaushe zaki dawo jiddah"?a hankali khaleesat tace Nenne tace kada su bari in dawo yanxu amma ni ina son ranar Friday indawo ,malam Ali ya danyi shiru sai kuma yace"kina jina jiddah?tace inaji baba,yace farida sun fada maki abinda ke faruwa kuwa?Sosai khaleesat taji gabanta ya fadi ,ta ajiye kwalbar turaren hannunta tayi shiru ta kasa cewa komai,Har saida babanta yace "hello ta kifta ido cike da karfin hali tace "inaji baba,baa gaya min komi ba meke faruwa baba,?Cikin nutsuwa malam Ali ya fara sanar mata duk abinda mahaifiyar Jay tazo har gida tayi,babu abinda yayi mata excluding,daga karshe ya sauke ajiyar zuciya yace you know why I decided to call and inform you about this jiddah?Saboda nasan Nenne zatace kar a sanar maki,Ni kuma abinda yasa nike gaya maki ina son kiyi deciding duk abinda kikaga ya dace da rayuwar ki tunda ba wani zai maki zaman auren dashi ba jiddah,quite alright I knew Ahmad is a good man but come to think of the life you may find your self in with his mother as your in-law,Ni ina jin nauyin sarki ina matukar jin nauyin Ince bazan bada auren kiba beside har gida ya aiko aka ban hakuri akan abinda ya faru bayan Kiran da yayi min ta waya ,bazan iya ja in ja da me martaba ba jiddah amma ina jiye maki wannan auren,hankalina bai nutsu da auren ba bana son abinda ya faru dake a baya ya sake maimaita kansa saboda muna jin nauyin kwatar maki yancinki for the second time kamar wancan lokacin,sarki ba mutumin da zaa tsaya ayi ja in ja dashi bane Don girma da martabarshi ya wuce ayi masa haka koda kuwa bai turo wakilansa ba iya ta waya kawai mukayi magana,balle bayan munyi magana ta waya still ya sake aikowa har gida a bamu hakuri .....tunda ya fara magana khaleesat ke kallon kofar dakin aunty murja babu ko kiftawa dan mutuwar zaune rayi kawai a inda take,sosai maganganun babanta sukayi mugun girgizata taji wani sanyi na shigarta wannan shine dalilin da yasa taketa Kiran housemate baya picking call dinta tun jiya kenan,har take tunanin ko wani laifin tayi masa bata sani ba,daga karshe taji muryar babanta yace hope kin fahimceni jiddah?da kyar ta nemo muryarta dako fitowa sosai bayayi tace "Toh bana,yace kiyi abinda kikaga ya dace for your betterment dear,I want nothing but the best for you,nobody is in the rightful position to decide for you for the second time daughter "kai ta gyada mashi cike da karfin hali har ya katse wayar,sannan taji wasu hawaye masu zafi sun zubo idonta,whatsapp dinta ta bude ta shiga DM din Jay cikin minti daya ta gama rubuta masa abinda zata rubuta hannunta na rawa tayi sending,sannan ta kashe data ta kwanta hawaye masu zafi wasu na bin wasu a kuncinta, ji tayi kamar komi na duniyar sun tsaya mata cak tsabar confussion ,ko minti biyu baayi ba saiga kiranshi ya shigo wayarta,silencing Kiran tayi bata daga ba sau uku yana kiranta bata picking ba daga karshe tayi switch off din wayar gaba daya tana sheshshekar kuka tana jin zuciyarta na mata zafi,karfe goma da rabi na dare aunty murja ta gama shimfide yaranta da sukayi bacci tun dazu,ta tafi ta dauro Alwala ta dawo dakinta ta kashe fitila zata kwanta saiga wani Almajiri yana sallama bakin kofar dakinta tace waye? Yace wai Ana sallama da halysah a waje,aunty murja tace khaleesat da daddaren nan? Wai inji wa? Almajirin yace a mota yake,Duk khaleesat najin aunty murja da Almajirin amma ko motsi batayi ba,Aunty murja ta dau hijab tasa ta fita Don ganin wanda ke Kiran khaleesat a wannan lokacin bayan minti uku sai gata ta dawo dakin tana tashin khaleesat ,tace khaleesat tashi Ahmad na jiranki a waje,meyasa bakice masa yazo da wuri ba yanzu ai dare yayi khaleesat taki juyowa tace, na Riga nayi bacci ace nayi bacci,Anty murja tace haka nan zaki daure ki fita amma karki dade ,kar babansu ya dawo ya tarar dake a waje kije yace sako ya kawo maki,khaleesat taki tashi aunty murja tafi minti biyar tana fama da ita amma fir taki tashi,har saida kishiyar Aunty murja ta leko dakin tasa baki Don tana jinsu,khaleesat ta tashi zaune da kyar ta sunkuyar da kanta Don bata son suga idonta da yayi ja saboda kuka,banda tanajin nauyin kishiyar Aunty murja da babu abinda zai sa ta tashi harta fita kofar gida,hijab dinta ta saka har kasa akan kayan baccin jikinta Aunty murja na mika mata torchlight taki amsa ta fita daga dakin kanta a kasa ta isa kofar gidan ta tsaya daga jikin motar tana jinsa ya bude motar ya sauka sannan ya zagayo inda take tsaye yana kallonta ita dai wani wajen daban take kallo sai kuma ya bude mata back seat pleadingly yace pls ki shiga Halysah ita dai taki ce masa komi kuma taki kallonsa lallabata ya shigayi yana hadata da Allah ta shiga motar yafi minti biyar yana Abu daya ita dai taki cewa komai hawaye na sauka a idonta ganin anata wucewa Ana kallonsu yasa kawai ta shiga motar ya kulle sannan ya zagaya ya shiga ta dayan side din motar ya ajiye wayarsa ya matsa kusa da ita yana kallonta cike da damuwa yace why will you send me such txt halysah?da wanne kikeson inji pls? Meyasa zaki man irin wannan message din? Ta sauke idonta tana jin wasu hawayen na zubo mata kasa daurewa tayi kawai ta fashe da kuka sosai nan da nan ya kara rikice mata yace stop this pls halysah why are you doing this to me? Kuka kawai take taki ce masa komai taji ya jawota kusa dashi yace halysah kiyi min Alkawari ko ban aureki in this short period of time ba bazaki taba auren wani da namiji ba kiyi min wannan Alkawarin pls halysah ni kuma nayi maki Alkawarin zan aureki no matter the circumstances surrounding our marriage,koba yanzu ba ni nasan zan aureki insha Allah halysah nasan akwai sanda mamina da kanta zata amince man in aureki and this is not going to take long yanzu ma ban cire rai ba am hoping we will get married cikin satinnan insha Allah dan Allah kada ki bari a rabamu halysah I don't know what will become of me idan na rasaki kuka kawai khaleesat takeyi ta kasa cewa komi tana jin zafi a ranta kamar zai mata kukan shima yace say something pls halysaah kice wani Abu dan Allah,bata ankara ba kawai sai gani tayi ya rungumota jikinsa cikin zafin name, nan da nan ta hadiye kukan da take ta fara turasa tana son kwace kanta daga jikinsa amma yaki sakinta bata kara gigicewa ba saida taji yana lalubanta through hijab din jikinta at the same time attempting to kiss her jikinta ya dau rawa tana kauda kanta tana turasa tace pls housemate ka bari stop it pls,sosai khaleesat ta tsorata ganin da gaske yake jikinta na rawa tace walahi zan maka ihu kiris ya rage yayi kissing dinta wayar sa ya fara vibrate slowly ya saketa daga rikon da yayi mata Trying to control his breathing ya juya yana kallon wayarsa yaga Ajay ke kiransa ita kanta tasan ba karamin ceton ta me Kiran yayi ba a wannan lokacin Don badan Kiran ba babu abinda zai hana Jay kissing dinta deeply ko ina na jikinta rawa yake ta matsa ta koka karshen seat din motar tana zare ido takai hannu ta bude motar yana ganin haka yayi saurin miko hannun sa zai rikota kar ta fita amma tuni ta fice daga motar ko waigawa batayi bata hada harda gudu ta shige cikin gidansu aunty murja jikinta na rawa kife wayar Jay yayi bayan Kiran Ajay ya sake shigowa ,yafi minti goma zaune bayan motar har sai da yadan samu nutsuwa sannan ya sauka ya koma driver seat ya tada motar.washe gari Jay na dawowa masallaci ya tarar da mami zaune a bedroom dinsa sau daya ya kalleta ya sauke idonsa ya karasa cikin dakin ya gaisheta ba tare daya kalleta ba ta amsa tace ka zauna ina da magana dakai jawwad,zaunawa yayi baice komai ba. jawwad,zaunawa yayi baice komai ba mami tace jwwad ban taba tunanin akwai ranar da zaizoba Ince maka bana son Abu ka kafe kace sai kayi abunnan ba saboda me martaba na goya maka baya wanda hakan da zaiyi a banza tunda nidai nasan ba son tsakani da Allah yake makaba ,da yana sonka son gaskiya bazai ware nasa dan ya gwadama duniya shine asalin jininsa sannan magajinsa ba,banyi tunanin akwai ranar da zaka nuna ban isa dakaai ba bayan duk sadaukarwar danayi a kanka domin in ganka cikin farin ciki da walwala na toshe maka duk wata kafar da zaisa kayi maraicin mahaifinka na jajirce na zamar maka uwa na zamar maka uba sakayyar da zakayi man kenan After all this ahmad?Jay ya daka kai a karo na farko ya kalleta cike da karfin hali yace ,mami sorry to say amma ban gane me kike nupi ba,ni nasan baki nuna man bakison aure na da yarinyar ba kin nuna man kin amince kin kuma yi min fatan Alkhairi kin min addua har yanzu akan hakan nike, All I know mahaifiyata ta amince min da maganar auren Dana kawo mata har ta min fatan Alkhairi,ban kuma san reason dinki na nuna ma me martaba da sauran mutane baki amince ba bayan ni kin nuna man you are okay with that har mun gama magana ,so ni har yanzu akan amincewarki nike mami maybe kina da dalilin ki na nuna musu baki amince ba shiyasa hakan bai dameni ba dan nasan komi da dalili kike yinsa,amma dani dake munsan kin amince da batun auren so yanzu kuma ban fahimci maganar da kike minba in har kinzo bangarena ne domin ki canza maganar da kikayina farko akan amincewarki then I will be highly disappointed and heartbroken don ban sanki da magana biyu ba.infact I don't even know how I will take it Don harna fara jin zuciyata na man ciwo yanzu even though I don't want believe abinda ya kawoki kenan ki canza maganar da kikayi a farko saboda na yadda dake mami na yadda da duk maganar data fito daga gareki baki taba man magana kin canza maganar ba ko bayan shekara nawa ne duk abinda kika nuna man kin amince to har abada kin amince da abun nan and nothing can ever change that,shiru mami tayi tana kallonsa ganin yanda ya daureta da jijiyar jikinta after some seconds ta sauke wani boyayyar ajiyan zuciya tayi kasa da murya tace "kasan me nikeso dakai jawwad? Ya daga kai ya kalleta taga har idanuwansa sun canja launi cikin kwantar da murya tace kayi hakuri jawwad tace kasan duniyar nan babu wanda ya tsani yaga bacin ranka ko kuma ya ganka cikin damuwa sama dani,yanzu ma bazan yarda injefa ka cikin damuwa ba amma ina son I baka shawara kuma nima I will be highly disappointed idan idan baka dau shawarar nan da zan baka ba na kuma yi Alkawarin shawarar nan bame cutar dakai bane to ya tauyeka ya hanaka abinda kakeso in anyway,Amma fa dole kadau shawarar nan tawa,Jay dai kallonta kawai yake babu ko kiftawa yana jin zuciyarsa na bugawa...... Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah 07087865788 Bear with me. HALYSAAH 97 Mami ta kwantar da murya tace "Tun da ka nace kai sai ka auri bazawara, naji zaka aureta Jawwad amma ga sharadi na, duk da a farko nace shawara amma yanxu zan maida shi sharadi a maimakon shawara, yanda tayi aurenta na farko to haka kai ma zaka yi auren ka na fari kafin ka aureta, abun nufi shi ne ko zaka aureta sai bayan akalla wata hudu zuwa biyar da auren ka da Hadiyah, idan yaso sai kaje kayi ta auren nata ni bazan hanaka ba tunda kace kaji ka gani" Jay ya dinga kallon Mami babu ko kiftawa, Mami tace "Ko baka fahimci abinda nake nufi bane?" Shiru yayi bai ce komai ba har sannan yana kallonta, Mami ta gyara zama tace "Ina ga kamar baka fahimci zance na ba, Jawwad cewa nayi in har zaka auri bazawara to sai bayan wata hudu zuwa biyar da auren ka na fari, wato auren ka da Hadiyah, in wata biyar ya cika sai kaje can ka auro bazawarar ka, amma fa bazan taɓa sonta ba bari in gaya maka zance na gaskiya, kuma don bana sonta ba shi ke nufin zan musguna mata ba a matsayin surkata, kawai dai a raina nasan bana son ta kuma bazan taɓa son ta ba, amma tunda kai kana sonta sai ka je ka aureta ka zauna daga kai sai ita cause u will never expect ur family to like her also don Hadiyah ce ta mu, ba lallai ma sai na dinga haduwa da ita ba ko kuma ta zo inda nake duk na yafe wannan, ko ince duk mun yafe wannan a family" Jay ya sauke idonsa cikin sanyin murya yace "But Mami wata biyar sun yi yawa, plss reconsider this Mami, don Allah ki duba, lokacin yayi tsayi...." Da mamaki Mami ke kallonsa, can tace "Ikon Allah, wato wata biyar sun maka yawa? Wannan wani irin tsinannen asiri yarinyar nan da iyayenta suka yi maka ne Jawwad? Shi wata biyar din ne yayi maka yawa saboda a kage kake ka auri guzumar ko?" Jay ya ɗan hade rai yace "Ni babu asirin da aka min, ni na ganta nace ina so ba ita ta gan ni tace tana so ba, beside she is just 20 years, kema kuma nasan zaki so ta idan na aureta kika ga qualities dinta, daga ita har iyayenta babu me matsala ko kananan magana, ita Hadiyar da kike ganin baza a samu matsala ba ina me tabbatar maki da ita za a samu matsalar, kin fi kowa sanin wacece Mahaifiyarta and how she behaves, ki bar ganin tana maki biyayya tana bin ki sau da kafa, ita kanta yarinyar idan na fara lissafo maki flaws dinta you will be greatly shock, yarinyar da take sangartacciya...." A fusace Mami ta dakatar da shi tace "Rufe min baki, saboda buzaye sun baka ka ci ka sha shi ne har kake da bakin kushe Hadiyah da uwarta yau? Ita Kanwar mahaifin taka ce kake kushe akan wata yarinya yau? To ai da ka hada har ni ka kushe akan buzuwa sai in san da gaske kake, wallahi idan baka bi ni a sannu ba Ahmad ko magana ya sake haɗaka da yarinyar nan zan iya yi maka Allah ya isa, akan me za a nemi rabani da kai bayan kai kadai Allah ya bani, meye laifina don nace bazaka auri bazawara daga wata kabilar ba? Yau da ina da wasu 'ya yan da ba sai dai in kyaleka in zuba maka ido ba kayi duk abinda kaga dama tun da baka jin maganata, in ma baka min biyayya ba ai yan uwanka za su min, to amma kai kadai Allah ya bani shi yasa kake bani wahala yanda ka so" Jay ya sauke kansa bai ce komai ba, he wish zai iya hakura da Halysaah ko don saboda Maminsa, amma xuciyarsa bazata iya daukar rabuwa da ita ba, shi kansa bai san wani irin so ne wannan yake mata ba, bai taɓa zaton har zai so Halysaah ba duba da yanda suka dade a apartment daya tare amma ko sau daya bai taɓa jin komai a ransa game da ita ba, kallon just his sister in Islam yake mata during all that period, bai san me yasa so yayi masa haka farat daya ba, he can't even tell when he deeply fell in love with her, ya dai san ba a tsohon apartment dinsu bane, Mami dai sai studying dinsa take tana kallonsa, har cikin ranta da gaske ta tsani ganinsa cikin damuwa ko wani iri ne, saboda shi taki aure tun rasuwan Babansa don definitely in tayi aure dole zata bar rikonsa gaba daya ya koma wajen kanin Mahaifinsa ne kuma tana ganin irin rayuwar da Junaid ke yi a gidan a lokacin saboda rashin uwa, so tari ma ita ke jawo Junaid din jiki in kuma ta tuna wasu abubuwa sai ta dake zuciyarta ta kyalesa ya karata can hannun matar ubansa, sannan tana tsoron tayi aure ta tafi gidan mijin tare da Jawwad a dinga yi masa kallon agola bayan da gatansa kaca kaca, duk wannan yasa ta sadaukar da komai nata akan farin cikin tilon ɗan ta, yanda zai rayu gabanta bai yi kewar mahaifinsa ba balle uwarsa sannan ba a hantaresa ko an kyare sa ba, Mami ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya tace "Kamar yanda nace maka Jawwad tun da ka nace sai ka auri yarinyar nan ni bazan hanaka ba, amma sai bayan auren ka da wata biyar, wannan shi ne sharadi na kawai" Girgiza mata kai Jay yayi a hankali yace "Lokacin da kika diba yayi yawa Mami, kiyi hakuri ki rage" Da mamaki Mami ke kallonsa, murya can kasa yace "Ina laifin ki ce sati biyu zuwa uku" Tsabar mamaki Mami ta ma rasa abinda zata ce masa, after some minutes ta mike ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita. Wajen karfe goma Mami ta tafi bangaren Aunty ta sameta zaune da ɗan ta Walid, suna ganinta suka yi shiru kamar ba magana suke kasa kasa ba, Aunty tace "Kin tashi lafiya Fulani?" Mami ta karasa cikin parlon tace "Barkan mu da Safiya" Gaishe da Mami Walid yayi sannan ya mike ya fita daga parlon, Mami ta bi sa da kallo sannan ta zauna tana kallon Aunty tace "Ashe Walid na gari" Aunty tace "Eh jiya ya dawo...." Mami tace "Ikon Allah, daga UK din yake ko dama yana Nigeria tuntuni..." Tuni Aunty ta kawar da zancen ba tare da ta ba Mami amsa ba tace "Yanxu ya ake ciki ne Fulani, kin samu Jawwad din kuwa kin fito masa a mutum dinki? Jibi ne juma'an nan fa, kinsan halin Mai martaba a sanda yaga mun tubure bama son abu to a sannan yake daukar abun nan da muhimmanci" Mami ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Ana idar da Sallah daxu na tafi bangaren Jawwad din Fulani, kinsan tun da nayi wannan magana a wajen meeting ban kara saka sa a idona ba sai yau da naje har bangarensa na jira ya dawo daga masallaci, in takaice maki dai daure ni da jijiyoyina kawai Jawwad yayi daxu da asuba, wai ai shi bai san zancen da nayi na cewa bana son auren ba tunda shi ba haka nace masa ba kuma shi yana nan a kan abinda na fada masa da farko, wallahi Fulani kasa aiwatar da abinda ya kai ni dakinsa nayi, bana son duk wani abu da zai damesa ko ya ɗaga masa hankali...." Aunty ta saki baki tana kallonta da mamaki, can ta gyada kai tace "Tabdi, ai kuwa nan gaba sai kin gwammace dama kin bata masa ran kin masa kaca kaca an wuce wajen da dai abinda zaki fuskanta nan gaba, don wallahi wallahi kinji rantsuwar musulmi fulani zai kai ya kawo ke da Jawwad sai gani sai hange daga nesa, ke kinsan su waye buzaye kuwa? Naga kamar kina ɗaukar wannan issue din sakwa sakwa fa, wallahi in zaki cire kulafucin yaron nan a ranki Kiyi abinda ya kamata to ki cire, su fa Buzayen nan ko Nijar din ma an san ba can ne asalinsu ba, nomads ne fa da suka yada zango a Nijar sai kuma suka ki tafiya suka yi kaka gida a can, wallahi in har kika yi kuskuren zuba ma Jawwad ido ya auri yarinyar nan a sunan kina tausayinsa sai kin yi da kin sanin da baki taɓa yin irinsa ba a rayuwarki, zaki san su kika haifa ma ɗa, yanxun ma ai kin fara ganin haka tunda gashi gida me tsada ya cire miliyoyin kudi babu sanin ki ya siya masu, Jawwad ya taɓa yin abu da makudan kudi bai sanar maki ba? Ai tun daga wannan action din nasa ya kamata ki gagara bacci da daddare kuma" Mami ta dafe kai tace "Na rasa ta inda zan billo ma lamarin nan Fulani, yanxu fa saboda gudun bacin ransa har ce masa nayi ya bari ya auri Hadiyah zuwa nan da wata biyar sannan sai ya auri ita buzuwar, wai fa nan duk dubara ce nake masa, nasan yana auren Hadiyah suka tare zai manta da wata bazawara can, kuma tunda sun gama Phd din nasu ko Amurkan ma bazan bari ya koma ba ta yanda bazai ganta ko by mistake ba tunda a Bauchi zai zauna da Hadiyah ai, to amma kinsan me yaron nan yace min? Wallahi ba kunya ya kalli idona yace min shi wata biyar sun masa yawa in rage in mayar sati biyu ko uku, a sannan na kara shan jinin jikina da yaron nan Fulani" Aunty tayi wani dariya tace "Kin ji ko? Ai sun shanyesa sai abinda kika gani, to ki bar sa a lokacin da yace din tunda tsoronsa kike" Mami tace "Ban gane tsoronsa nake ba" Aunty tace "To haka ne mana Fulani, ka haifi yaro amma kana tsoron tunkarar sa da magana, da nayi niyyar kawai in zuba maki ido tunda ke in an kawo maki shawarar da zai amfane ki sai ki yi fatali da shi ki gwale mutum, to bari zan fito maki a mutum yanxu Fulani in dai ba ta karkashin kasa kika bi ma Jawwad ba to kina gaff da shiga uku wallahi, kin ji kina gani mace zata rabaki da tilon ɗan ki, yanxun ma me ya rage? Jawwad da na sani mai kawaici da gudun bacin ranki har ya tsaya yana ja in ja dake yace shi lallai sai yayi abinda bakya so, tun farkon lamarin nan nake nuna maki hanya kina kaucewa, ga abu har yayi nisa yanda bama zato, ta yanda suka bi suka juya hankalinsa mu ma ta nan din dai za mu bi mu dawo da hankalin nasa, ai ba wajen boka nace zan kai ki ba Fulani balle kiyi ta tsoron kauce hanya don nasan abinda kike tsoro kenan, da ilimina nima fa kin sani, to don me zan yi abinda zan kauce hanya, in dai zaki ji ta nawa ki yi shiru ki bar sa a sati ukun da yace idan ya so sai a daura auren nasa da Hadiyah wannan Juma'an tunda haka Mai martaba ya tsara, ana daura auren mu kuma muna abinda ya kamata a gefe, wallahi wallahi sai kinyi mamakin yanda Jawwad zai mance da wata buzuwar bazawara can, wai ke baki yi mamakin yanda Walid ya nutsu ba ya dena abubuwan nan da yake har da su ɗaga kwalba? Bazan boye maki ba taimako ake ta nema masa shi yasa kika ga Walid a haka yanxu, don haka shi ma Jawwad taimakon za mu nema masa don wannan halaka yake son fadawa Fulani" Mami dai tayi shiru ta rasa abinda zata ce, amma da alama maganar Aunty ya fara tasiri a zuciyarta, Aunty tace "Don haka in ma ke kina dar a zuciyarki har yanxu to kawai ki bar min wuka da nama, kawai magana ce ta kudi kuma in sha Allahu sai kin gode min wallahi, sati daya yayi yawa zaki ga aiki da cikawa" Mami ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Ni fa na zata maganganun da na gaya ma Mai martaba zai yi zuciya ya aura ma ɗan sa bazawarar sai naga ba haka ba kuma, wallahi da ni muguwa ce tsaf zan san yanda zanyi in juya auren ya koma kan Junaid shi ya auri bazawaran dama ai kince tare kika ganta da Junaid din a Amurka" Aunty ta ɗan bude ido jin abinda Mami tace, da sauri tace "A'a ba sai an kai ga haka ba Fulani, kin ga wannan ai babban magana zai zama a masarautar nan da ma garin Bauchi baki daya, mu dai bakinmu alekum mu yi abinda ya kamata hankalin Jawwad ya dawo jikinsa ya mance da wata bazawara" Mami tace "To shikenan Fulani, Nagode kwarai da gaske" Aunty tace "Haba ai yi ma kai ne, banda ma yan zugi sun shiga tsakaninmu a masarautar nan ai ke din mutuniyata ce a shekarun baya, yanxu dai ki nuna ma Jawwad kin ji kin amince sati ukun da yace sai yaje yayi ma ubansa Mai martaba magana a ɗaga auren" Mami tace "Zan sanar masa in sha Allah, bari in je ko breakfast ban yi ba" Daga haka Mami ta mike ta nufi kofa ta fita, Aunty ta kyabe baki murya can kasa tace "In bari a juya aure kan Junaid? Ashe ina ma son sa da alkhairi in har na bari aka yi haka, ai sai dai in sa a aura masa warce zata zamo ajalinsa in ma na bari yayi auren kenan...." Shiru Mai martaba yayi yana kallon Jawwad bayan ya gama sauraronsa, after a while ya sauke ajiyar zuciya yace "Fulani ce tayi maka wannan tsarin ko?" Jay ya sauke idonsa yayi shiru don bayan sun gama magana da Mami few hours ago sai da ta jaddada masa kar ma yace ma Mai martaba yayi magana da ita, Mai martaba yace "Nasan duk tsarinta ne wannan, so kana nufin yanxu in sake turawa a sanar masu na canza maganar da nayi shekaranjiya kenan?" A hankali Jay yace "Ai ba sai an tura ba ranka shi dade, ta waya ma idan aka sanar masu ina ga ya wadatar" Mai martaba dai yayi shiru yana kallonsa, bayan wasu mintoci yace "Baza a ɗaga daurin auren nan ba Jawwad, ranan Juma'ah kamar yanda na tsara za a daura auren, nothing is going to change that" Jay ya daga kai yana kallonsa a sanyaye bai iya yace komai ba.... Ko da ya koma bangaren Mami ya sanar mata yanda suka yi da Mai martaba kuka ta sakar masa tace "Ni kuma in dai ba nan da sati hudun da muka shirya da kai ba wallahi Ahmad kayi aure ne ba da yawu na ba, ba kuma da amincewata ba, kuma bazan taɓa saka maka albarka a wannan aure ba" Sosai jikin Jay yayi sanyi yace "Don Allah Mami ki yi hakuri, ni nasan yanda zan yi convincing Mai martaba zuwa lokacin da kika ce kina son ayi auren" Cikin kuka Mami tace "Da dai yafi maka, duk da bana son auren nan haka na kai zuciya nesa na amince amma nace ga yanda nake son ayi min a matsayina na mahaifiyarka nan ma sai a tauye ni a nuna ban isa ba?" A hankali Jay yace "Kiyi hakuri, yanda kike so in sha Allah haka za ayi" Ba karamin Courage Jay yayi gathering ba ya sake komawa gun Mai martaba bayan Magrib, ya risina kai cikin ladabi yace "Ka gafarce ni ranka shi dade, i don't mean to disobey or disagree with you in any way, amma kayi hakuri ranka shi dade ka ɗaga wannan aure zuwa nan da wata daya kafin nan nayi shirye shiryen da zan yi a tsanake" Mai martaba ya ɗan yi murmushi ya jinjina kai bai dai ce masa komai ba, shigowar Aunty Parlon yasa Mai martaba yace "Zaka iya tafiya Ahmad, I've heard you" Jawwad ya mike yayi ma Aunty barka da yamma sannan ya fita daga parlon. Wajen karfe tara Ajay ya shiga Bedroom din Jay yana kallonsa yace "Don me zaka samu Mai martaba kace a ɗaga auren?" Jay yace "I have no Choice Ajay, haka Mami tace take so" Ajay yace "Must you listen to everything?" Calmly Jay yace "C'mon Ajay, she is my mother, ta yaya zan yi aure babu blessings dinta? Yanxu ba cewa tayi bata son auren kwata kwata ba kamar yanda tace few days ago, kawai so take sai na fara auren Hadiyah da 4 weeks sannan in auri Halysaah, idan ina son ganin dai dai ai abinda tace take so shi zan yi" Ajay ya girgiza kai yace "Ina me tabbatar maka wannan wani plan ne nasu suka hada ita da Aunty cause ita ke zugata...." Jay yace "What ever, ni dai nasan wata dayan da tace bazai cika ba ta canza min magana, shi yasa ban damu ba" Ajay ya sauke ajiyar zuciya yace "Abba isn't happy with this, he wasn't expecting this from you, considering the fact that he supported you from the onset..." Jay yace "I have no choice kamar yanda nace maka Ajay, Mami ce ta sa inyi haka and I did that for peace to reign" Ajay ya ɗan yi murmushi yace "At the end ina ga fa sai dai tayi hakuri ta saka albarkan nan da tace bazata saka ba daga baya cause I am assuring you come Friday sai Abba yayi abinda ya tsara, saboda wani reason mara ma'ana bazai canza maganarsa ba a maida shi karamin mutum, come Friday you will be groom to 2 bride...." Jay na kallonsa da damuwa yace "Haka Abba yace maka?" Ajay ya ɗaga kafada bai ce komai ba ya juya ya fita daga dakin, Jay ya rasa ma me zai yi ko kadan bai son bacin ran Maminsa gashi har da kuka tayi saboda shi, nazarin maganganun da zai sake samun Mai martaba da shi ya fara yi, ya fi minti ashirin pondering on what to say to the king for the third time, daga karshe ya mike ya fita with the hope that wannan karan Sarki zai janye batun auren zuwa nan da wata daya. Karfe goma saura Jay ya tafi bangaren Ajay, a parlor ya samesa yana kallon kwallo, Jay ya sauke ajiyar zuciya ya zauna yana kallonsa yace "Daga wajen Mai martaba nake" Ajay ya ɗan kallesa, sai kuma yace "Ya ku ka yi da shi?" Jay yace "I am just hoping he consider all what I said" *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* 07087865788 HALYSAAH 98 Washegari da safe Jay ya tafi bangaren Maminsa don gaisheta, bayan ta amsa gaisuwarsa tana kallonsa tace "Ya ku ka yi da Sarki?" Jay ya sauke idonsa yace "Mami sau uku ina yi masa magana...." Mami tace "Ba sau nawa kayi masa magana nake tambayarka ba Jawwad, cewa nayi ya ya ku ka yi da shi daga karshe?" A hankali Jay yace "Kinsan bazai yi magana me tsayi ba Mami, he was quiet at the end kuma yace min ya ji, i am just hoping he is convinced kuma zai yi considering duk abun da na gaya masa, don haka ko da zaki ga wani abu daban Mami ki sani i tried my best in maki yanda kike so, duk yanda nake jin nauyin Mai martaba i confronted him thrice just to please you Mami" Sallaman Aunty yasa Jay yayi shiru ya daga kai yana kallonta, Aunty ta karaso cikin parlon tace "Fatan mun wayi gari lafiya Fulani" Mami tace "Lafiya lau Alhamdulillah, ya kwanan su Zuwaira?" Aunty ta nemi kujera ta zauna tace "Alhamdulillah" Jay ya sauke idonsa ya gaida Aunty ta amsa sannan ya mike yana kallon Mami yace "Zan ɗan fita Mami, sai na dawo" Aunty tace "Zaka ɗan fita ko dai za ku fita, Boss din naka na can naga ai ya shirya yana jiran ka kaje ka ja maku mota" Ko kallonta Jay bai yi ba har ya fita daga parlon, Aunty ta taɓe baki tana kallon Mami tace "Tare fa za su fita da Junaid don naga Junaid din ya fito yana rike da makullin mota" Mami dai bata ce komai ba don abinda ya dameta daban a ranta, ba kadan maganar auren nan ya tsaya mata a rai ba, Aunty ta gyara zama tace "To yanxu yaya ake ciki? Mai martaban ya yarda a ɗaga daurin auren ko kuwa?" Mami ta girgiza kai tace "Ina tantama Fulani, don sau uku Jawwad din ke samunsa da maganar amma yaki ce masa komai, kin ga kuwa bai amince ba kenan" Aunty tace "Sai kace ba Sarki ba, ai ni nasan ko don ya nuna mana iyakar mu fa sai yayi abin nan da yaga ba ma so, ga abu ya zo a kurarren lokaci balle a bi ta kasa a lalata, amma dai kin san abinda zai faru?" Mami na kallonta tace "A'a sai kin fada" Aunty ta mike ta koma gefenta ta zauna tana kallonta.... Ko kallon Jay Ajay bai yarda yayi ba ya nufi motarsa, Jay ya bi sa da kallo yace "Ni zaka walakanta?" Sai a sannan Ajay ya juya ya kallesa yace "Since when did I become ur driver Jay, if you are not too fine to drive ga drebobi sai wanda ka zaba a gidan nan, why do I have to drive you, on a serious note bazan je unguwan nan me nisa ba da daddaren nan, gwara ma ace hanyar Kano na kama in san tafiya me nisa dama zan yi kawai, haba ai unguwan yayi nisa sosai ga hanyar babu kyau ga dare yayi, throughout the day time me yasa baka ce in raka ka ba sai da daddaren nan, beside i told you i am meeting a friend yana jirana, you met me already prepared to go out balle kace kirkiro fitan nayi" Jay dai kallonsa kawai yake, Ajay yace "Zaka je wajen budurwar ka sai kace sai an raka ka, idan nace bazan je ba kuma ya zama issue, kaje for once kai kadai mana, haba you are stressing me wallahi" Kallonsa kawai Jay yake yaki tanka sa, Jin Jay yaki cewa komai kuma bai fasa kallonsa ba yace "To in har zan je sai ka min full tank, sannan akwai shopping da zan yi online the bill is on you, agreed?" Jay ya wani kallesa, haka nan babu yanda Ajay ya iya suka bar gidan a cikin motarsa yana mita, Jay dai ko kallonsa bai yi ba, karfe tara saura mintuna Ajay yayi parking dai dai kofar gidansu Aunty Murja, Jay ya ciro wayarsa after some seconds ya kai kunne duk da ba kira yake ba don yasan ko ya kirata ba lallai ta ɗaga ba, he tried calling her once yesterday bata yi picking ba kuma bata biyo sa ba, can ya kalli Ajay yace "Can you pls call Halysaah's line, I can't reach her" Ajay ya juya ya kallesa, sai kuma yace "You can't reach her? To ni ne zan iya reaching dinta kenan, ina ce same network muke using, in baka sameta ba ai nima haka, better still ka aika yaro cikin gidan ya kirata mana" Jay ya dau wayar Ajay dake ajiye, shi dai Ajay kallonsa kawai yake, number Khaleesat yayi dailing sai ga suna ya fito anyi saving as Jay's girl, Jay ya daga kai ya kallesa, dariya Ajay yayi, shi kansa bai ma san me ya basa dariya ba, May be the way he saved the contact, can dai ya fixge wayar yayi sending kiran, Jay yace "Sunanta ne baka sani ba?" Ajay yace "Oho, Haseenah kake ce mata ko Haseelah" kiran na shiga bayan ɗan lokaci Khaleesat ta ɗaga amma tayi shiru, Ajay yace "Ke kika saka min katin zaki yi shiru Malama?" A hankali tace "Good evening" Yace "Ana jiran ki a waje" Tace "Wa?" Yace "Kar ki bata ma mutane lokaci Malama" Daga haka ya katse wayarsa ya daga kai ya kalli Jay dake kallonsa, bayan kusan minti shidda sai ga Khaleesat ta fito tana sanye da hijab har kasa, kallon motar kawai take kamar bazata karasa ba can dai tana tafiya a hankali ta nufi gun motar, Ajay ya kunna fitilar cikin motar, shi dai Jay kallonta kawai yake suna hada ido ta sunkuyar da kai, kamar munafuka ta zaga ta wajen driver seat inda Ajay ke zaune, shi kansa kallon mamaki ya bi ta da shi har ta iso side dinsa ta tsaya tana kallonsa tace "Ga ni" Ajay ya juya ya kalli Jay da ya ɗan yi murmushi kawai don ko kadan bai ji haushin hakan da tayi ba, Ajay ya sake kallonta yace "Me zan maki?" Duk da abinda take ji a ranta sai da ya bata dariya amma bata yi ba ta wani kallesa kafin ta saci kallon Jay taga kallonta yake, sunkuyar da kanta tayi, Ajay ya hade rai yace "Malama you are obstructing the air from reaching me, matsa daga nan" Ta wani kallesa tace "To ai kai ne ka kirani" Ajay ya juya ya kalli Jay da yaki cewa komai, can ya bude motar, ta matsa gefe har ya sauko, tsayawa tayi gabansa ganin barin wajen zai yi kamar zata yi kuka tace "Toh ba kai ne ka kirani ba, why did you call me?" Da mamaki Ajay yace "Wai ina wasa dake ne, kinga na saba kiran ki dama?" Juyawa yayi ya bi ta gaban motar ya wuce ta bi sa da kallo, can ta saci kallon Jay suka hada ido, sauke idonta tayi lokaci daya jikinta yayi sanyi, ɗan murmushi yayi ya bude motar ya sauko sannan ya zagayo inda take tsaye, ta ɗan koma baya a hankali tace "Ina yini" Yace "But you know what happened few days ago wasn't intentional right?" Gyada masa kai tayi, cikin sanyin murya yace "To kiyi hakuri Halysaah, it's the work of the devil" Ita dai tayi shiru bata ce komai ba, yace "Kin hakura?" Ta gyada masa kai, yace "Ta yaya zan gane hakan?" Ɗan murmushi tayi ta jingina da motar bata ce komai ba, yayi kasa da murya yace "Kin riga kin ba Ajay insight cewar we had issues ai" Ta ɗan kallesa tace "Ai bazai sani ba...." Yace "Wa yace maki, ur reaction says it all..." Ta girgiza masa kai tace "Zai yi tunanin i am just pulling his leg saboda shi ne ya kira wayana" Jay yace "To shikenan Halysaah, just came to check on you, hope there is no problem" Ta gyada masa kai kawai, a hankali yace "Ki ci gaba da mana addu'a kin ji Housemate? We need it most at this point" Tace "In sha Allah, but...." Yace "But what?" A hankali ta jingina jikin motar cikin sanyin murya tace "No matter what ka zamo me yi ma Mahaifiyarka biyayya, may be aurenmu babu alkhairi ne shi yasa bata so...." Hawaye ne ya cika idonta ta kasa ci gaba, Jay dake ta kallonta da mamaki yace "Saboda me zaki ce aurenmu babu alkhairi Halysaah? Me yasa zaki ce haka? Kuma wa yace maki Mami bata son auremmu, ita kawai cewa tayi ga particular time din da take son ayi auren, Ajay ne ya gaya maki abinda ke faruwa har kika aiko min text din nan few days ago?" Cike da karfin hali Khaleesat tace "Da yaushe muke magana da shi har zai gaya min abinda ke faruwa, Kasan ai baza a boye min abinda Mom dinka taje tayi a gidanmu ba" Jay ya dinga kallonta babu ko kiftawa zuciyarsa na bugawa jin abinda tace, da kyar ya bude baki yace "Gidanku kuma Halysaah? Kina nufin Mamina taje gidan ku??" Khaleesat dai ta dinga kallonsa don reaction dinsa ya nuna kwata kwata bai san Mami taje gidansu ba, hawayen dake makale idonta ya gangaro ta sauke kanta, jingina yayi da motar ya ma rasa abinda zai ce zuciyarsa na bugawa da karfi, Khaleesat ta goge hawayenta cikin sanyin murya tace "Ai ya ma wuce don har Mai martaba ya aika an ba su Babana hakuri, and he spoke to them on phone" Jay was more than shock ya dinga kallonta babu ko kiftawa don duk bai san da haka ba babu wanda ya gaya masa har Mai martaba, a hankali yace "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un" Khaleesat ta goge idonta cikin sanyin murya tace "I think it's better mu jira har sanda zata so aurenmu, but for now mu hakura kawai, haka Abdul ya aureni Mom dinsa bata so na, yan uwansa basa so na, yanxu kuma...." kasa ci gaba tayi ta fashe da kuka sosai bayan ta tuna abinda Mom din Abdul tayi mata, don yana daga cikin mamakin da har yau ya kasa barin ranta, Lokaci daya Jay ya rikice mata ya fara bata hakuri, zuwa yanxu ta fahimci halin da yake shiga idan yaga tana kuka hakan yasa ta dake ta hadiye kukan nata tana goge idonta, damuwa ƙarara fuskarsa yace "Kina tunanin zan iya hakura dake no matter what Halysaah? Kinsan irin son da nake maki kuwa? What do you think will become of me idan na yarda aka raba mu?" Ita dai Khaleesat ta kasa ce masa komai hawaye na zuba idonta tana gogewa, Yayi kokarin calming kansa cike da karfin hali "Kiyi hakuri Halysaah amma no matter what ni bazan rabu dake ba, in sha Allah komai zai yi dai dai da izinin Allah, zan kira Aunty Farida in basu hakuri, I knew nothing about this babu wanda ya sanar min Billah" Khaleesat ta ɗan yi murmushi tace "Ya wuce fa, abinda nace maka har gida Mai martaba ya aika a basu hakuri, ai kaga ya wuce kenan" Jay was speechless, bai taɓa tunanin abun Maminsa ya kai har haka ba, to menene yasa shi zata dinga masa pretending, wannan abun da take yi ne yake kara weighing dinsa down, shi abinda zata nuna masa daban abinda zata je tayi kuma daban, this is so heartbreaking to him, Ajay ne ya zagayo wajen yace "Pls I can't endure the mosquitoes in this area anymore, in baku gama ba ka samu nearest hotel kawai kayi lodging ni gida zan tafi" Khaleesat ta daga kai ta kallesa, ya hade rai yace "Matsa min in shiga mota" Ta ɗan taɓe baki ta matsa, ya bude driver seat ya shiga, Khaleesat na kallon Jay a hankali tace "Shikenan sai da safe" Da damuwa yace "Ba mu gama magana ba Halysaah" Tace "Sai mu yi ta WhatsApp, ban gaya maka ba gobe da safe zamu tafi Kano da Aunty Murja da yarinyar kishiyarta sai Maman kishiyarta" Jay ya dinga kallonta, can yace "Amma shi ne baki gaya min ba all this while, gobe fa Friday" Ta ɗan yi murmushi tace "Na sani" Shiru yayi for almost 30 seconds kafin a hankali yace "In sha Allah zan zo da wuri sai in kai ku Kanon" Khaleesat ta ɗan bude ido tace "Tasha fa za mu je mu hau mota" Jay yace "Na ce zan kai ku, ku shirya da wuri..." A hankali tace "Toh Allah ya kai mu" Yace "Ameen" Hannu ta ɗaga masa alamar Bye bye sannan ta bar wajen, Jay dai ya kasa ce mata komai ya bi ta da kallo har ta shiga cikin gida, jiki a sanyaye ya zaga ya shiga front seat yana kallon Ajay with disappointment written all over his face yace "Nasan kasan cewar Mami taje gidansu Halysaah a Kano Amma ka boye min baka gaya min ba Junaid" Ajay ya ɗan kallesa yace "To meye amfanin gaya maka, me zaka yi? She is ur mother babu yanda ka iya, Mai martaba did the needful, so babu amfanin gaya maka ayi ta jan magana....." Jay ya dinga kallonsa kawai, Ajay ya daga kafada yayi igniting motarsa ya fara reverse, har suka isa gida babu wanda yace komai cikinsu, har sannan jikin Jay a sanyaye yake ya rasa dalilin da yasa yaji ya fara loosing hope kuma yanxu, yaji ya shiga damuwa fiye da wanda yake ciki a baya, bai taɓa expecting haka daga Maminsa ba, Ajay na parking Jay ya bude motar slowly ya sauka, Ajay ya bi sa da kallo har yayi nisa sannan ya sauke ajiyar zuciya ya kashe motarsa ya sauka shi ma, har ransa yake jin tausayinsa kuma shi dai yasan duk rashin kirkin Mami bata kai haka ba kawai Aunty ce ke instigating dinta tana exaggerating mata lamarin shi yasa take ta wannan abubuwan da take yi. Ajay ya kalli agogon wrist dinsa ganin there is still time ya nufi bangaren Abbansa don ya kirasa daxu suna unguwan su Aunty Murja, zai bude kofar parlorn aka riga sa budewa sai ga Mami ta fito daga parlon fuskarta a daure ko kallon Ajay bata yi ba tayi wucewarta, Ajay ya bi ta da kallo sannan ya shiga babban parlon, Zaune ya tarar da Mai martaba a parlon, Aunty dake zaune parlon ita ma tayi kasa da kai cikin kwantar da murya tana cewa "Allah ya huci zuciyarka ranka shi dade idan maganganunta sun maka zafi, Allah ya baka hakuri Me martaba, a gaskiya Fulani bata kyautawa sam, ban san me take son a mata ba, amma babu komai ita kanta tasan albarkacin wa take ci, kuma zata ci gaba da cin albarkacin nasa, Allah ya sanyaya ranka Mai martaba, Allah ya huci zuciyar ka, Allah ya baka hakuri" Ajay ya dinga yi ma Aunty wani kallo, sannan ya zauna kasan lallausan Carpet din parlon yayi kasa da kai yana gaida Mai martaba, Mai martaba ya ɗaga kai ya kallesa yace "Ka dawo Yarima" Ajay bai dago kansa ba yace "Mun dawo Ur highness" Sarki yace "To maa sha Allah, na ma ga takardun da na kira nake tambayarka daxu" Ajay yace "To in ba damuwa zan iya tafiya ur highness?" Duk da akwai maganganun da Sarki ke son yi da shi amma ganin Aunty a parlon kawai yace "Sure, Allah ya tashe mu lafiya" Mikewa Ajay yayi ya ɗan kalli Aunty yayi mata sai da safe sannan ya juya ya nufi kofa ya fita, direct bangaren Jay ya nufa yaji ya kulle kofar shiga part din nasa, hakan yasa ya juya ya koma bangarensa.... Ana idar da sallan asuba bayan Jay ya dawo masallaci ya tafi part din Ajay, bai samesa a bangaren nasa ba, ya zauna nan parlor ya jira har ya dawo, Jay ya ɗaga kai a hankali ya kallesa yace "Yau Halysaah da Aunt dinta za su koma Kano, na ce mata zan je da safe in kai su Kanon, but i don't think I am okay Ajay, bazan iya driving din ba..." Ajay ya katse sa ya zauna yana kallonsa yace "What's wrong with you?" Jay yace "I just need rest, zan kwanta ko zan ɗan yi bacci, shi ne nake son tunda bazan iya kai su Kanon ba ka taimaka kayi dropping dinsu motor Park su hau public transport, ban san nawa bane kudin motan but you can sort that out" Ajay dai kallonsa kawai yake, can yace "To me yasa baza a tura masu kudin motar ba kawai, har sai an je uwa duniyar unguwan nan nasu an dauke su an kai su Motor park" Jay ya mike yace "You just have to help pls, they are leaving very early this morning" Daga haka ya nufi kofa Ajay ya bi sa da kallo har ya fita, kawai yayi shiru ya kyalesa ne ganin da gasken he is not looking okay. Duk tunanin Khaleesat idan ta fito zata ga Ajay da Jay duk da Ajay ne ya kira wayarta, amma sai ta ga Ajay kadai, gaishesa tayi yace "I have where I am going, do not keep me waiting...." Juyawa tayi ta koma cikin gidan, sai da suka ɓata kusan 15 mins sannan suka fito, ya bude motar ya sauka yana gaida dattijuwar cikinsu sannan ya gaida Aunty Murja ya bude masu booth suka saka akwatinsu, ya bude masu back seat ya koma cikin motar ya zauna, sai da Khaleesat ta jira Inna da Aunty Murja suka shiga motar Zainab ma ta shiga sannan ta koma front seat ta shiga tana rike da handbag dinta, yan gidan gaba daya suka fito har da makota ana masu Allah ya kiyaye hanya har Ajay ya bar unguwan, at first tasha yayi niyyar dropping dinsu amma sai ya kasa hakan, still dai yana driving yana estimating lokacin da zai kai su Kano ga daurin aure yau, what if Mai martaba yayi realizing baya garin idan yana bukatarsa, daga karshe yayi deciding in ya samu available flight kawai sai ya bi ya dawo tunda bayan an sauko juma'a ne daurin auren and this is just few minutes to 7am, yana daukar hanya da raɓar AC ya bugi su Aunty Murja duk suka ɓige da bacci a bayan motar, tafiyar kusan 2 hours suka yi Khaleesat ta juya tana kallonsa a hankali tace "Don Allah zaka iya tsayawa, it seems I want to throw up" Ya daure fuska ya kalleta, tana ganin haka ta fara yunkurin amai tana rufe bakinta, gangarawa yayi gefen hanya yayi parking ta bude motar ta sauka, su Aunty Murja dai sai bacci suke basu san me ke faruwa ba, bayan kusan minti uku ya dau bottle water ya bude motar ya sauka ya nufeta, Mikewa tayi tana kallonsa a hankali tace "Ai ban yi ba" Yace "Kika sake tsayar da ni zan sauke ki inyi tafiyata Malama, you can't come and be stressing me here" Amsan ruwan hannunsa tayi ta bude ta wanke fuskarta, sannan ta mika masa sauran, daga sama har kasa ya kalleta ya juya ya koma cikin mota ta bi bayansa..... Har kofar gida Ajay yayi dropping dinsu bayan sun sauke kayansu an shiga da su ciki su Aunty Murja suka masa godiya suka shiga cikin gidan, Khaleesat ta zaga ta driver seat tana kallonsa tace "Mun gode Allah ya saka da alkhairi, amma baza kayi breakfast ba?" Sai bayan da ta fada hakan ne ta tuna waye shi, ta langwabar da kai tace "Shikenan, are you going back to Bauchi?" Tada motarsa yayi yace "Kina da sako ne..." Murmushi tayi ta girgiza masa kai, sannan tace "Allah ya kiyaye hanya, Allah ya kai ka lafiya" Daga haka ta juya ta nufi gate zata shiga gida, sai da ta shiga gidan sannan yayi reverse ya bar unguwan. Karfe uku saura Khaleesat na zaune parlor bayan Aunty Farida ta gama yi mata gyaran gashi, tun da suka shigo gidan da safe ta samu labarin har yanxu da batun daurin aurenta yau hankalinta ya kasa kwanciya duk tunaninta till further notice duba da abubuwan da suka faru a kwanakin nan, ba ita ba har su Nenne da Ummanta da Aunty Farida kawai sun zuba ma sarautar Allah ido ne gani suke auren fa ba mai yiwuwa bane kawai dai baza a ja da Mai martaba ba, Umma kuwa ko baccin kirki bata yi ba daren jiya haka ta kwana sallah tana rokon Allah Ubangiji ya kawo sanadin fasuwar wannan aure don kwata kwata bata son auren kuma, bata fatan er ta ta koma gidan jiya, gwara ta dauwama a gabanta har Allah ya fito mata da miji wanda ba shi kadai ba hatta yan uwansa da iyayensa za su so ta kamar yanda yake son ta, har zuwa yanxu da Umma ke zaune bata fasa wannan addu'a a ranta ba don tana cikin tashin hankali da rashin nutsuwa a zuciyarta, Ahmad mutumin kirki ne wanda ko wace uwa zata yi ma er ta fatan samu amma tun da uwarsa ta zo har gida ta nuna masu bata son auren Khaleesat da ɗanta tayi masu rashin mutunci Umma taji aurensa da Khaleesat ya fice mata a rai, amma kuma ga Mai martaba a tsakani shi yasa suka rasa say din kansu akan lamarin duk suka zuba ma sarautar Allah ido, Nenne ce ta shigo parlon a gigice da almajirinta da wasu matasa yan Mariri duk sun sha fararen yadi tana kallon su Aunty Farida da Mama Shatu sai Aunty Murja dake parlor tace "Kun ji fa wai an daura auren da Ahamad din, yanxu almajirina ya shigo yake ce min daga wajen daurin auren su ke yanxu haka, mutane ba masaka tsinke a wajen har da sarakuna da manyan mutanen kasar nan, sai jiniya ake ta ko ina...." Sosai Umma taji gabanta ya fadi tana kallon Nenne babu ko kiftawa, Khaleesat sai da taji kamar amai zai taho mata tsabar yanda maganar Nenne ya kidimar da ita ya rikitata, har sai da ta kasa daurewa ta mike da sauri ta nufi bandakin dake parlon tana yunkurin amai, Nenne ta kalli wani matashi me suna Sagir don duk yafi sauran nutsuwa cikin samarin tace "Kai Sagir sai kaji ance an daura auren wa da wa?" Sagir yace "Ni iya na Khaleesat kawai na rike don daurin auren biyu aka yi Nenne" Nenne ta sharce zufar da ya keto mata tace "To ya aka ce na Khaleesah din?" Sagir yace "An daura aurenta da Ahmad Yusuf...." Mikewa Umma tayi ta bar parlon ta wuce daki hawaye na zuba idonta, Aunty Farida da duk jikinta yayi sanyi ita ma ta mike da kyar ta bi bayan Umma, Mama Shatu tace "To mu ai wannan abun farin ciki ne a gare mu, tun da aka daura auren dama Allah ya ƙaddara mijinta ne babu yanda uwarsa zata yi sai dai ta bi su da fatan alkhairi" Nenne tace "Atoh dai, ni dai wallahi nayi farin ciki matuka nayi murna, yanxu tashi za ku yi ku baza turaren wuta a gidan nan da kyar in jiga jigan masarautan baza su yo nan a gaida uwar yarinya da kakarta ba, maza tashi murja kar mu ji kunya" Amai sosai Khaleesat tayi a bandakin, nan da nan taji kamar zazzaɓi zai rufeta ta fito ta wuce dakinta da kyar, sai a sannan hawaye masu zafi suka fara sauka idonta, she is just confuse, ta rasa wani irin tunani zata yi, bata taɓa tunanin za a daura aurenta kwana kusa ba with the way things were going, ko dai almajiran basu ji da kyau bane ba ita ake nufi ba, tayi karfin halin jawo wayarta tana kallon screen din, da kyar tayi dialing number Jay, amma kamar daxu da ta kirasa bai shiga ba yanxun ma bai shiga ba, hakan yasa tayi dialing number Ajay, har ya katse bai daga ba, ta ɗan jira ko zai biyota kamar yanda ya saba, amma har bayan minti biyar bai biyo ba, sake kira tayi still har ya gama ringing bai ɗaga ba, bata taɓa kiransa a take bai yi picking ba ko ya biyo kiran, ajiye wayar tayi ta kwanta gefen gado hawaye masu zafi na zubowa idonta, a haka Aunty Farida ta shigo ta sameta tana kallonta cikin sanyin murya tace "Kun yi waya da Jawwad din ne?" Khaleesat ta girgiza kai hawaye na sauka idonta tace "Wayarsa a kashe" Aunty Farida ta zauna kusa da ita amma ta rasa ma me zata ce, su kansu fargaban auren nan suke balle ita, can Aunty Farida tace "To ki kira Junaid sai ya hadaki da Ahmad din" Khaleesat ta mike zaune tace "Na kirasa bai daga ba" Tana fadin haka ta sake dialing numbersa sai taji a kashe, ta daga kai ta kalli Aunty Farida, Aunty Farida ma tayi dialing number tasa a nata wayar, ita ma taji switch off. *Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* Ur evidence via 07087865788 Halysaah Page 99 By Khaleesat Haydar Sai kusan Magrib Malam Ali ya dawo gida tare da wasu abokansa daga Mariri, bayan anyi magariba Nenne ta sa Aunty Farida ta kai masu abinci compound, Aunty Farida na komawa cikin gidan ta tafi dakin Umma, tana kallon coolern abincin dake dakin da damuwa tace “Wai har yanzu baki ci abincin ba dama Umma? Don Allah me yasa zaki sa ma kanki damuwa haka ne Umma?” Muryar Nenne suka ji tace “Don Allah ki rabu da ita Parida, ta dade bata sa ma ranta damuwa ba, wannan ai sai in iya cewa bakin ciki take ma er cikinta, tun da muka ga har aka daura auren nan to fa dama Allah ya kaddara sai an daura ba wani tsimi balle dubara, to meye bazata bi yarinya da fatan alkhairi ba da kyakkyawan addu’a, tunda dai mijinta da sarki suna son ta ba shikenan ba uwarsa taje can ta karata da mugun halinta, in taga ta haifo mata jikoki masu shiga rai sai a ga ta sakko ta so ta ko don jikokin, nima farko nan ba haka nayi ta fargaban Zahra’u zata raba ni da da na ba da na samu labarin buzuwa ce, har ya aurota ni dai bana sonta don ina tsoron asirin kabilar su haka kawai wataran ta janye min yaro ita da iyayenta, amma tana haifo Khaleesah na saduda saboda yanda yarinyar ta shiga raina da yan unguwa, to ita ma uwargabanta har abinci naga ta ci daxu, sai kece sarauniyar damuwa da kuncin yan Najeriya, to wallahi ki cire auren jikata a ranki, kada Allah ya dubi zuciyarki abinda kike tsoro ya je ya faru mu shiga uku, ai fata na gari lamiri” Nenne na kai wa nan ta fice daga dakin, Dakin Khaleesat Aunty Farida ta shiga ta sameta zaune saman darduma ta idar da sallah, Aunty Farida ta zauna gefen gado tace “kin same su a wayar?” Khaleesat ta girgiza mata kai kawai, Aunty Farida tace “Waya kuma a kashe tun safe, ai Junaid shi naga da wuya a ki samun sa….” Ita dai Khaleesat bata ce komai ba. Karfe takwas da rabi Malam Ali na zaune parlonsa sai su Umma da Aunty Farida da Nenne wanda duk shi yayi kiransu, Nenne na gyara zama tace “Wallahi har ka fara dawowa Alin ka na da, ga hasken ka sai dawowa yake” Malam Ali dai bai ce mata komai ba, babu bata lokaci ya fara sanar masu dalilin da yasa yayi kiransu gaba daya, tun da ya fara magana Nenne ta bude baki tana kallonsa, Umma da Aunty Farida ma sai kallonsa suke kamar ranan suka fara ganinsa, Nenne ta tsuke dankwalinta da kyau, cikin rashin fahimta tana zaro ido tace “Ban gane ba Ali, ba a daura auren ba kenan kake nufi ko me?” Malam Ali ya kwantar da murya yace “Shi ne nake kai ku ai Baaba, ban gama bayanina ba” Nenne ta zauna da kyau cikin kaguwa tace “Gama Ali, Innalillahi wa Inna ilaihi raji’una, muna jin ka Ali, ga jama’a duk mun gayyato mun ce gobe biki ya za mu yi da su ni Dije, amma Allah ya tsine ma wannan yaro Sagir da yace mana an daura aure” Malam Ali ya ci gaba da bayaninsa Nenne bata kara interrupting dinsa ba tana gwale ido har ya kai karshe, Umma ta juya ta kalli Aunty Farida da tsabar mamaki ita ma baki ta bude kamar Nenne tana kallon Malam Ali, Nenne fa bata fasa zare ido ba tana kallon Malam Ali duk da ya gama bayaninsa, can ta kwance dankwalin da ta tsuke tace “Kana nufin kace da wannan dan uwan nasa mara walwala wanda shi ne ainahin dan Sarkin aka daura auren?” Malam Ali yace “Haka maganar take, shi ma ai sunansa kenan Ahmad….” Nenne ta saki wani salati tana tafe hannu sai kuma ta dafe kanta, can tace “Ikon Allah yafi gaban haka Ali, dama shi bama shi da uwa a gidan ta mutu balle mu ji fargaban zata zo ta walakanta mu, yanxu dai kana nufin Yarima ne mijin Khaleesah, shi ainahin dan sarkin?” Umma ta rasa me yasa taji wani nutsuwa ya zo mata bayan bayanin mai gidanta, Aunty Farida tsabar yanda lamarin ya girgizata ta ma kasa cewa komai don ganin abun ta dinga yi kamar al’mara, Junaid kuma, Nenne ta sauke ajiyar zuciya tace “Lallai sarki ya cika mutum, wato da uwar Ahamad ta nuna masa ba shi ya haifi Ahamad din ba sai ya nuna mata me yayi zafi shima ai ya haifa, ikon Allah, to amma yanxu wannan kwamacalar ta ina za a fara Ali, shi dai wannan kamilin yaro da ko magana sai ya ga dama yake yi ma mutane bai ce fa yana son Khaleesah ba ita ma haka, to ta ina za a fara wannan lamari, sannan shi Ahamad wani hali ake son ya shiga yanda yake bala’in son yarinyar nan ace kuma yaga dan uwansa da ita a matsayin matar aure, anya Sarki bai bar baya da kura ba kuwa, kamar fa yan biyu zaka ga yaran daya me fara’a da faram faram da mutane, daya kuma dunkum, to a gaskiya uwar Ahamad er iskar mace ce mara tsoron Allah, hatsaniya kawai take son jawo masu a masarautar ta raba kan yaran nan biyu, anya Sarki yayi shawara kuwa kan ya zartar da wannan hukunci, ni dai jikata ma nake jiye ma kar ace ta raba kan yan uwa” Kuka Nenne ta fashe da shi tace “Amma Wallahi matar nan ta cuci dan ta, yaro mai biyayya zata yi ma irin wannan cutarwa ta hanasa abinda ransa ke so don son ranta, to ni dai shawarar da zan bayar a nan duk mu bar wannan bayanin a cikin ranmu, kada wannan yarinya Khaleesah ta daga mana hankali mu kanmu muji bama son auren gwara ayi mata shiru kawai tukunna….” Aunty Farida ta kalli Nenne tace “Avi mata shiru kuma Nenne? Ai wannan ba maqanar da za avi shiru bane qwara tasan abinda ke faruwadaga mana hankali da bakin dake gidan nan? to wallahi duk wanda yace ma zai gaya mata ya tada mata hankali Allah ya isa tsakanina da shi, gwara a bar mu muyi shagalinmu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, ga yan unguwan nan duk an gayyacesu gobe za mu yi taron biki me aji, yan Mariri ma duk za su zo, to a gaya mata ga abinda ake ciki ta watsar mana da taron tunda ba hankali gareta ba ku ke nufi ko me?” Duk aka yi shiru ana kallon Nenne, Nenne tace “Ai abinda yayi shi wannan miskilin shi yayi Ahamad din ma, kuma duk ta saba da su, naga ma ta fi tsokanar shi miskilin shi ne baya ma shiga sabgar ta, Ahamad din ne kawai abun tausayi don shi aka cuta, har raina kuma ban ji dadin wannan cutarwan da uwarsa tayi masa ba, don za mu fi jin dadinsa a matsayin surki tunda shi faram faram yake akan wannan miskilin” Nenne na kai wa nan ta mike ta bar masu parlon tana kara nanata Allah ya isa in aka gaya ma Khaleesat an canza mata miji ta tarwatsa masu taro, Umma ta kalli Malam Ali tace “Sai aki sanar mata abinda ke faruwa kenan Malam? Ai yana da kyau ta san matsayarta tun wuri, wannan ba abun da za a boye mata bane gaskiya, ai ba karamin magana bace wannan” Malam Ali ya sauke ajiyar zuciya yace “To kin dai ji abinda Baaba tace, amma ni kam wannan sauyin bai dameni ba Zahra’u, don dukkaninsu mutanen kirki ne masu girmama dan Adam duk yanda yake, kuma wannan privilege ne babba Sarki yayi mana, ya mutunta mu matuka, na kuma ji dadin irin yanda ya daukeni da kuma yanda ya kirani da kansa yayi min bayanin sauyin da za a samu kafin ma ranan daurin auren, ya kuma bukaci sai da amincewata ma za ayi hakan, naji dadin wannan abu matuka, Ahamad din ne kawai abun dubawa duk da bamu san ko da yardar sa Sarki yayi hakan ba tunda shi mahaifiyarsa bata so, bana tunanin Sarki zai yi haka ba tare da sanin shi Ahmad din ba, zai iya yiwuwa shi ne ma ya bar ma Junaid din auren Khaleesah” Umma ta sauke ajiyar zuciya tace “Ni kuma kawai sai naji hankalina yafi kwanciya da daurin auren da Junaid Malam, duk da ba wai bana son Ahmad bane don yaron kirki ne shi ma amma mahaifiyarsa ce abar tsoro, nayi mugun girgiza da abinda ta zo gidan nan ta mana, tun da garin Allah ya wave vau nake fargaban kar ta sake zuwa mana in taii an daura auren” Aunty Farida dai banda hamdala babu abinda take yi hanasa yin magana me tsayi da ita, sai dai deep down tana tausayin Jawwad sosai cause bai yi deserving haka ba, ya kuma yi masu abinda baza su taba mancewa ba a sanda suke cikin bala’in Abdul da iyayensa….Ajay ya dago kansa da kyar bayan duk ya gama sauraron kalaman Mai martaba, wanda tun safe sai yanxu ya samu suka zauna da mahaifin nasa, duk da Ac’s dake parlon banda zufa babu abinda yake yi, he have never been this confuse all his life, sai goge zufan goshinsa yake da karamin towel din hannunsa, after some seconds yayi karfin halin kallon Mai martaba, murya can kasa yace “Abba i am sorry, i am so sorry, ka gafarce ni, kasan bana taba questioning dinka akan duk decision din da ka yanke kaina, ko bai min ba haka nake accepting with no complain, but why me plss? Why me Abba?? Kasan Jawwad fa….” Sai kuma ya kasa ci gaba don gaba daya he is confuse, Calmly Mai Martaba yace “You because… You are My son, ba kuma wanda ya isa yayi setting min boundary da kai ko ya nuna min ban isa ba, na kuma san baka ja da duk abinda na yanke a kanka, shi yasa ban yi shawara da kai ba, Jawwad ya nuna min kallon kanin Mahaifinsa yake min ba Mahaifinsa ba, banda haka bazai fifita maganar mahaifiyarsa sama da nawa ba ya nemi ya maida ni karamin mutum a idon mahaifin yarinya bayan rashin mutuncin da uwarsa taje har gidansu yarinyar tayi, daga karshe sai Aseeyah tayi amfani da zuwan da yayi wajena sau uku ban basa listening ears ba ta nuna dan ta yace bai son auren yanzu amma saboda ni bana nufinsa da alkhairi shi yasa nace sai anyi auren…” Murmushi Mai martaba yayi kalaman Mami na sake dawo masa, wanda tsakaninsa da ita ne wannan ba sai ya tsaya yana furta ma Junaid ba, Ajay ya girgiza masa kai cikin karfin hali yace “Junaid ba, Ajay ya girgiza masa kai cikin karfin hali yace “Amma Abba considering our bond with Jawwad, why not Waleed? I think Waleed would have been better not me” Mai martaba Vace “Saboda totally speechless, ya dafe kansa dake masa wani irin ciwo tun dazu, har a sannan kuma ganin abun yake kamar a mafarki ya kasa aminta, babu kalan tunanin da bai zo ransa ba a wannan moment din, Mai martaba yace “In kai ma ban isa da kai bane let me know Ahmad” Ajay ya daga kai ya kallesa da sauri yana girgiza kai yace “Allah ya huci zuciyar ka ranka shi dade, Who am I to question ur act? Allah ya baka hakuri, bani da ja da duk hukuncin da ka zartar” Mai martaba yace “Zaka iya tafiya, ina bukatar zan huta, inda wani shirye shiryen da kake ganin za ayi ka sanar min” Ajay ya kasa cewa komai ya mike yana kallon Abbansa, lokaci daya idanuwansa suka kada sosai, ya juya yana jan kafa ya nufi kofa ya fita daga parlon with Jay in his mind. Mami na kallon Aunty da mugun mamaki kamar me counting words dinta tace “Junaid? Kina nufin da Junaid aka daura auren? Junaid dai Fulani?” Aunty da bakin ciki ke kwance fuskarta karara tace “Zan maki karya ne Fulani, bakina da na Mai martaba ya sanar min haka wallahi don da naji jita jitar ban yarda ba da farko, kan Junaid ya mayar da auren bazawarar, shi kuma Jawwad aka daura aurensa da Hadiyah” Mami ta mike tsaye tana kallon Aunty babu ko kiftawa tace “Shi Mai martaban yayi ma Jawwad haka? Ita buduwar tasa ya aura ma dan sa don ya kuntata mana ni da shi?” Sai kuma ta fashe da kuka ta koma ta zauna, Aunty ina ma ta samu abun cewa tsabar bakin ciki da takaici, just like that ace Junaid yayi aure bayan planning dinta a kansa, aure fa, cikin kuka Mami tace “Ban yi mamakin hakan da yayi ba, yayi hakan ne don ya nuna mana iyakar mu ni da da na a gidan nan, in da kara ya kamata ya aura ma dan sa budurwar Jawwad? Wannan wani irin damuwa yake son jefa min da na ciki? Jawwad yayi deserving haka daga sarki?? Duk yanda aka yi ya samu wannan labarin shi ma don ni tun daxu nake kiransa ban samu wavarsa ba kuma baya gidan nan” Wani kukan hakin ciki ne ya sake kwace mata, daga can ta fara magana cikin bakin ciki ya kashe min da kenan shi yasa ya yanke wannan danyen hukunci? Ko tsakaninsu da bond dinsu bai duba ba yayi wannan aika aikan? Ta yaya yake son Jawwad ya rayu yana ganin warce yake so a matsayin matar Junaid? Innalillahi wa Inna ilaihi raji’un, Lallai sarki ya nuna mana iyakar mu a gidan nan, kuma sai yayi da ya sanin wannan abun da yayi” Aunty ta mike ta fita zuwa bangaren Sarki, a Bedroom dinsa ta samesa ta zauna tana kallonsa cikin nutsuwa tace “Amma ranka shi dade ko dai ka sha’afa da tsarin masarautar nan ne da har ka dau bazawara ka aura ma Yarima da bai taba aure ba? Kasan irin maganganun da ake ta yi a masarautar nan yanxu haka kuwa, kuma kan kace me zance sai karade gari, tsarin dake nan tun iyaye da kakanni saboda kayi pleasing wasu can ka take wannan tsarin Mai muhimmanci ranka shi dade?” Mai martaba yace “Na soke tsarin nan daga yau a masarautar nan Fulani, shi yasa nayi using dan cikina as example wajen soke tsarin, kuma ban soke wannan tsari ba sai da na zauna da amintattu na, so ko Walid ya kawo min bazawara yau yace yana so zan aura masa, sarki na gaba zai iya maida tsarin idan ya so….” Aunty was speechless, ta dinga kallon sarki babu ko kiftawa tana jin wani mugun tsanar Khaleesah a ranta, wannan fa shi ne anyi ba ayi ba, da ta sani ai bazata taba biye Mami a fasa auren da Jawwad ba, yanxu gashi aure ya koma kan wanda bata fatan ace yau gashi da mace a matsayin matarsa a nan duniya, shikenan ana nufin shirin da take ta yi ya wargaje kenan saboda biye Mami da tayi, Mai martaba yace “Kina da sauran magana ne Fulani?” Ta sauke ajiyar zuciya tace “Duk abinda ka tsara ai ya zauna ranka shi dade, no one is in the position to question you, Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi” Yace “Ameen” Bayan kusan minti biyar ta mike ta fice daga dakin cikin tsananin bacin rai ta koma bangaren Mami… Halysaah Page 99 By Khaleesat Haydar Related Articles Matar Damisa Book 2 Complete txt Matar Damisa Book 1 Chapter 32 Complete Novel 6, December 2023 Abban Sojoji Chapter 63 Book 2 Complete Novel 22, April 2023 Kurkukun Kaddara Takun Farko Chapter 72 By Hafsat Bature 2, March 2024 Asanadin Makwabtaka Book 2 Complete Novel Txt Asanadin Makwabtaka Book 2 Page 38 Complete Novel 28, January 2025 My Uncle Page 4 Complete Hausa Novel 2, July 2025 Kanwar Maza Complete Novel Document Txt Kanwar Maza Page 55 Complete Novel By Ayshercool 30, December 2024 Follow us Facebook Twitter WhatsApp Google news You might like Masallacin Ka’aba da kuma wasu Gine-gine 10 mafiya darajar kudi a duniya 22, April 2023 Mijin Hanifah Hausa Novel Document 22, April 2023 Matar Taj Book 2 Complete Romantic Hausa Novel Document 30, April 2024 Tubali Book 2 Page 7 Complete Novel 22, April 2023 Wasu Hanyoyin Da Zaki Tsaftace Gabanki 11, May 2023 So Da Buri Page 52 Complete Novel 7, June 2025 Halysaah Page 19 By Khaleesat Haydar 23, May 2025 NIHAAD Chapter 25 By Khaleesat Haiydar Complete Novel 1, December 2023 Ku kalli Kaɗan daga cikin shirin kwana casa’in zango na 6 22, April 2023 Wace Ce Ita (Who Was She) Chapter 73 Complete Hausa Novel 26, April 2023 Maganin Ciwon Sanyi Sadidan Na Mata 28, April 2023 Kurkukun Kaddara Takun Farko Chapter 39 By Hafsat Bature 24, January 2024 Yadda za ki kula da jikinki lokacin sanyi 22, April 2023 DODON JATAU By RAZ Complete Document 22, April 2023 Ga Mata Masu Bukatar Kiba Ga Hanyar Da Zaku Bi Cikin Sauki 22, April 2023 Hadin Karin Ni’ima Don Ma’aurata 6, December 2023 Duk wani musulmi kuma wanda yake jin hausa ya kamata ya mallaki wannan 22, April 2023 Halysaah Page 67 By Khaleesat Haydar 22, July 2025 Asanadin Makwabtaka Book 2 Complete Novel Txt Asanadin Makwabtaka Book 2 Page 68 Complete Novel 15, February 2025 Raina Kama Book 1,2&3 From www.aihausanovels.com 22, April 2023 Hattara: Kada Ka/Ki Karanta Idan Baka/Ki Da Aure – Yadda Zaki Gamsar Da Mijinki 22, April 2023 Direban Gidanmu By SaNaz Deeyah Complete Document 22, April 2023 Pi Network Is False But Not Fraud – 3 Reasons From Crypto Currency Experts 22, April 2023 Abban Sojoji Takun Karshe Book 3 Chapter 122 Complete Novel 29, October 2023 Maganin Hips Cikin Sauki Ga Mata 22, April 2023 Daudar Gora Page 6 Hausa Novel By Bilyn Abdull 22, April 2023 YARIMA SUHAIL Complete Hausa Novel Document By Aihausanovels 22, April 2023 Yadda zaku cike sabon tallafin karatu zuwa kasashen waje daga ma’aikatar ilimi ta kasar Nigeriya. 22, April 2023 Sadiya Haruna Ta Kammala Hukuncin Wata Shida A Makarantar Islamiyya 22, April 2023 Nancy Isime: Portraying female entertainers as promiscuous damages young girls 22, April 2023 Load More Advertisement Categories Uncategorized1,259 Hausa novels769 Novel Document105 Sirrin Rike Miji100 Labarai62 Zafafa 202351 Kannywood39 Zamantakewar Aure26 Kimiya da Fasaha18 Mallama Juwariyya17 Job15 Health13 Education13 Daga Malamai6 Fassarar Mafarki4 Kalaman Soyayya4 Waka1 Litattafan Yaki1 Search for: Search … Abban Sojoji Complete Asanadin Makwabtaka Complete Billyn Abdul Hafsat Bature (Boss Lady) Hausa Novel Hausa Novels Hot Romantic Hausa Novel Kannywood Kanwar Maza Complete Novel Khaleesat Haiydar Ma'aurata Maganin sanyi Matar Damisa Complete Novel Sirrin rike miji Tusar gaba warin gaba warin kashi Zafafa 2023 Install AihausaNovels App Trending update 1 hour ago Mijin Marigayiya Page 22 Hausa Novel 1 hour ago Mijin Marigayiya Page 21 Hausa Novel 2 hours ago Mijin Marigayiya Page 20 Hausa Novel 2 hours ago Mijin Marigayiya Page 19 Hausa Novel 23 hours ago Mijin Marigayiya Page 18 Hausa Novel About Us | Terms and Conditions | Privacy Policy ©️ 2025, Aihausanovels | All Rights Reserved. Designed by JobTech Facebook Twitter WhatsApp Telegram Back to top button HALYSAAH PAGE 100 Washegari da safe yaran Mama Zubaida kanana suka shigo parlor da gudu suna sanar ma Nenne manyan motoci har hudu suna kofar gida wai a bude masu gate za su shigo, Nenne ta kalli su Aunty Murja da wata hamshakiyar makociyarsu na nan Tudun Yola dake zaune parlon, makociyar tasu me suna Hajiya Zaliha tace “To a bude masu gate din mana” Nenne dai sai zazzare ido take, can tace “Ina Parida?” Aunty Murja tace “Tana kitchen kamar” Da sauri Nenne ta mike ta nufi kitchen din ta samu Aunty Farida da Mama Shatu sun gama dama kunu a babban bokiti dan ko break fast ba ayi ba, Mama Zubaida da Sha’awa da wata makociyarsu na can Mariri kuma na backyard din kitchen din suna ta suyan kosai, Nenne na gwala ido ta tsaya kusa da Aunty Farida tayi kasa da murya tace “Ke Parida kin ji wai su Munzali suka shigo yanzu suke cewa ga can manyan motaci a waje suna jiran a bude masu get din gidan nan su shigo, su shigo su mana me? anya la fiya kuwa Parida? Ko aika su aka yi su kwashe mu?” Aunty Farida tayi shiru tana kallon Nenne da mamaki ita ma jin abinda take gaya mata, can tace “Bari inje in ga su waye tukunna Fita tayi daga kitchen din Nenne ta bi bayanta da sauri, sai da Aunty Farida ta dauko gyale sannan ta fita waje, nan ta tarar da Labibah ta shigo daga kafar gidan ita ma taje ganin matocin, Labibah tace “Wai kaya za su shigo da Nenne da duk ta gama tsurewa tace “Kayan me kuma? Labibah ta zauna Balcony tace “Oho” Aunty Farida dai ta nufi gate din gidan ta bude ta fita, gaisawa tayi da mutumin dake tsaye shi kadai jikin motar farko, don motoci ne hudu a jere kofar gidan kuma duk manyan motoci, mutumin na kallonta with calmness yace “Sunana Mukhtar, daga masarautan Bauchi muke, kaya ne za a sauke, ban san ko ba a sanar maku da zuwan mu ba Aunty Farida tace “Ачча, sannun ku da zuwa, bari a bude gidan Daga haka ta juya ta koma ciki, su Labibah ta sa su bude gate din bayan Nenne ta dubo makulli don duk makullan na wajenta dama, daya bayan daya duk motocin suka shiga compound din suka yi parking don akwai enough space, ita dai Aunty Farida na tsaye Nenne ma ta yafo tsadadden mayafinta ta fito ta tsaya tana kallon ikon Allah, Aunty Murja ma Nenne ta dauko mata hijab din Aunty Farida gogagge har kasa ta bata ta saka ita da wata er uwarsu, Hajiya Zaliha ma ta fito duk suna tsaye compound din gidan, Hajiya Shafa’atu ce ta sauko cikin shiga ta alfarma tare da wata da zata girme mata a shekaru, da fara’a fuskarta ta fara gaida su Nenne, Aunty Farida ta karasa har inda take ta gaisheta, Hajiya Shafa’atu ta amsa tayi mata side hug tace “Sai dai mun yi maku shigowar safe kuma babu notice, fatan mun same ku lafiya?” Aunty Farida tace “Alhamdulillah, Sannun ku da zuwa Har gaban Nenne Hajiya Shafa’atu taje ta kara gaisheta da ladabi, sannan ta kara gaida Hajiya Zaliha da ita ma ta sha gwala-gwalai, ita dai Hajiya Sumayya da suke tare da Hajiya Shafa’atu dama daga inda take tsaye tayi gaisuwanta bata karasa ba tana danna waya, tuni mazan dake ko wani mota suka sauko daga matocin suka fara sauke akwatunan cikin motocin, Nenne tace “To Bisimillan ku mu shiga ciki, Sannun ku da zuwa A haka duk suka karasa parlor suka zauna, a nan Hajiya Sha fa’atu ta gabatar masu da kanta da Hajiya Sumayya a matsayin kannen Mai martaba, Nenne ta kara masu maraba cikin mutuntawa, tuni su Mama Zubaida suka sauke kaskan kosai suka dawo parlor da Mama Shatu da Sha’awa don ganin me ke faruwa, Aunty Farida ta ma rasa me zata kawo ma su Hajiya Sha fa’atu, kawai dai ta tafi ta dauko masu ruwa da lemo bayan ta ajiye tana kallon Hajiya Shafa’atu tace “A hado maku breakfast ne ranki shi dade?” Hajiya Shafa’atu tace “A’a wallahi mun yı breakfast, ruwan ma ya isa, mu da ba a ma san muna hanya ba, ai ba komai ruwan ya wadatar maa sha Allah Aunty Farida ta tafi dakin Umma tayi mata magana ta fito su gaisa, Sai da mazan nan suka shigo da tsadaddun akwati daddaya har ashirin da hudu parlon su Mama Zubaida da Mama Shatu na kirgawa a zuci, Hajiya Zaliha sai cewa take “Maa sha Allah” few bozes aka bude ana duba uban kayan ciki sama sama, Hajiya Zaliha ta ja Aunty Farida zuwa kitchen tana kallonta tace “Farida ko dai snacks din da nayi nace za a rarraba ma jama’a kawai a dauko a ba ma bakin nan don bai kamata a bar su haka ba duk da ba a san da zuwan su ba, amma gwara a fito kunya ka yaya kika ce Aunty Farida tace “lo Aunty hakan ma yayı, ni dama duk jikina yayi sanyi wallahi ban san me za a basu ba Hajiya Zaliha tace “Bari in kira Mai aikina kawai su kawo snack din dama har anyi packaging a foil an rufe, sai a biyo da shi ta kitchen kawai, akwai ruwan goran da yawa ne a gidan nan?” Aunty Farida tace “Pure water ne, na goran bai wuce pack biyu ba” Hajiya Zaliha tace “Toh bari in yi waya su kawo min, sannan kun san fa ana bada tukuici, shi kuma ya za ayi?” Aunty Farida tace “Toh, kamar ya kike ga za a bada Aunty?” Hajiya Zaliha tace “Wannan kaya haka Maa sha Allah kyau ace ko Miliyan daya ne a basu, amma kar a takura kai, ko dubu dari biyar ce sai a basu in zai ywu Aunty Farida tace “lah akwar cash dama na ciro sai ayi hatan Hajiya Zalsha tace “To ki koma parlon bari ingi waya yanzu Aunty Farida tace “Tah” Juyawa tayi ta koma Parlon don har taji sanyi wannan solution da new neighbor din tasu ta kawo, mata me kirki, Hajıya Zaliha tayi wayar da zata yi, tana ta tsaye kitchen har sai da mai aikinta da yan matan ta biyu suka taha da snacks din, meat pie, cup cake, samosa, Doughnuts, Spring rolls, duk haka aka yi packaging dinsu separately kuma ba laiți suna da Clan yawa, nan suka dire su a kitchen din, Mai aikin ta koma dauko pack din ruwa da lemo da tace su taho da, ko da Aunty Farida ta dawa kitchen din kasa cewa komai tayi don ita bata zata Small chaps din sun kai haka ba da Neighbor din tasu tay, gadiya ta fara yi mata, Hajiya Zaliha tace “Naga jiya an saya kaji, in da inda za a dibar masu shi ma a diba masu A Cooler me dan girma Aunty Farida ta dibar masu kajin ta cika shi dam, sannan suka fita da snack din parlor da Hajiya Zaliha don har suna shirin tafiya ne za su koma Bauchi wai a ranan, sosai Hajiya Shafa’atu ta nuna jin dadin snacks din da carton din ruwa da Lemo me dan dama da aka ajiye masu banda Hajiya Sumayya da ko uffan bata cewa a parlon, a haka aka kai masu packaged snack din da drinks da coolern nama zuwa mota, Nenne na kallon Hajiya Shafa’atu cikin nutsuwa tace “To Hajiya, da yake bamu san ya tsarin gidan naku yake ba, shi ne nace yanzu can Bauchin za aje yi mata Jere ko kuwa ya abun yake Hajiya Shafa’atu tace “A’a kaka, in ma jere ne idan ya bude gidansa na nan Kana sai a baku makulli a kai kayan nata can, ai yana da gidansa a nan, barin kayan a nan Kano zai fi sauki akan ace sai anje kai su Bauchi, balle yanzu dole masarauta za a kai ta, kun ga ai babu abinda za a bukata a can, in dai ba gidansa na Bauchin ba” Nenne tace “To Madallah, hakan ma ba laifi Hajiya” a haka su Hajiya Zaliha da Aunty Farida da Nenne da ma sauran mutanen parlon suka masu rakiya har zuwa gun motocin su ana masu Allah ya kiyaye hanya, bayan sun bar gidan Nenne ta kalli Hajiya Zaliha tace Lallai kin fidda mu kunya Zaliha, da sai dai a kulla masu koko da kosai a leda, sai da nace ma Parida ayi su cin cin da alkaki da dublan tace ta bada ayi a duniya yau za a kawo wai yanzu haka ake yi an dena ba kai wahala, to har yanzu ban ga idon cin cin ba balle Alkaki, da ya za mu yi da kunya yau ni Dije, lallai kin rufa mana asiri wallahi, Allah Ubangiji ya maki albarka ya raya maki zuria, mu ina muka san haka ake yi banda ke Hajiya Zaliha dai murmushi kawai tayi tace “Haba dai, babu komai Nenne” nan suka fara duba kayan lefen Khaleesat a tsanake a parlon, Hajiya Zaliha taga duk kayan babu na banza, kaya ne masu suna kaya ga uban yawa, har da tsadaddun Alkyabba biyar da lapaya babu adadi, Nenne har da hawaye ta ma rasa abinda zata ce don farin ciki da murna, da ta tuna irin yanda Abdul ya auri Khaleesat a gantale ko akwati daya basu gani ba a sunan lefe sai ta rushe da kuka, su Mama Shatu suka hau bata hakuri, ita dai Aunty Farida duk jikinta yayi sanyi sosai ko don saboda yanda aka daura aure babu nutsuwa ita kam bata yi expecting za a kawo wani lefe ba, tafi tunanin may be a bar mata a dakinta a can masarautar, a karamin kit Hajiya Zaliha taga dala dubu biyar, tana kallon su Aunty Farida tace “Wannan duk yanda aka yi kudin dinki ne suka saka” Nenne tace “Amma naga ba irin kudinmu bane ai ko kuskure aka yi” Hajiya Zaliha tayi dariya tace “In kika ji nawa ne wannan idan aka canza ai sai kin kama baki Nenne” Nenne ta saci kallon su Mama Zubaida sai kuma tace “Toh yi shiru Zaliha, Allah Ubangiji ya nuna na yan baya haka, kema Allah ya kawo ma yan matan ki mazaje na gari” Hajiya Zaliha na murmushi tace “Ameen Nenne” Nenne ta gyara zama tace “Kin san daga inda kayan nan suka fito?” Hajiya Zaliha tace “A’a” a hankali Nenne tace “Masarautar garin Bauchi” Da mamaki Hajiya Zaliha tace “Kai haba Nenne?” Nenne tace “Kwarai kuwa, dan sarki ne mijin nata” Hajiya Zaliha tace “Ikon Allah” Mamaki ba kadan ba Hajiya Zaliha tayi, daga baya kuma taga meye ma abun mamaki a dai yanda Khaleesat take wanda ya fi dan sarki ma zai iya fitowa yace yana sonta don haka ba abun mamaki bane, ita kanta tana admiring komai na Khaleesat, tun da Hajiya Zaliha ta ji gidan da za a kai Khaleesat ta kebance da Aunty Farida tace “Farida ina ga gaskiya baza a fara taba masu duk abinda suka saka a lefe ba, probably idan aka kai ta Bauchin in suna da wani event da za ayi a can sai tayi using na lefen, in ma da event din definitely an ajiye mata kayan da zata yi using, amma dai daga nan gwara a canza kudin nan da suka sako a shiga kasuwa a siyo mata duk abinda zata yi amfani da shi na kece raini in za a kai ta, hakan ma kamar an kara kankaro mata mutunci ne, hatta Alkyabba baza a taba na lefen ba tunda ga kudi gwara a siya kawai, amma dai ban san yanda ku kuka tsara ba gaskiya, ina magana ne bayan na duba gidan da za a kai ta Kinsan irin wannan babban gida ba dai kananun zance ba, gwara su ga bata taba komai a kayansu ba hakan zai fi armashi” Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya tace “Wannan gaskiya ne Aunty, sai a je kasuwan kawai, nima nayi wannan tunanin wallahi, duk da akwai lapaya uku da na siyo mata da takalma da jaka, sannan akwal kayan dinkin ta da aka kawo jiya, amma gwara a karo mata wasu masu tsadan” Hajiya Zaliha tace “Amma sai kin yi shawara da Nenne da mahaifiyarta, wannan abu dai abu ne sau daya in a life time, so gwara ayi mata abinda ya kamata duba da inda za a kai ta ma” Aunty Farida tace “Toh ba damuwa bari in masu magana Aunty Ajay ya kira Jay for the countless time but he still can’t reach him, shi damuwarsa kawai yasan inda yake so they can talk, he needs to speak to him badly, shi dai yasan bai san ta yaya ba but probably they might arrive at a solution together idan suka hadu duk da bai ma san wani irin solution din ba at this point, gaba daya kansa a kulle yake tun jiya yake nazarin yanda zai billo ma al’amarin amma ya kasa arriving at any solution, duk tunanin da yayi sae yaga ba mafita bane cause he might end up disappointing his father, ko baccin kirki bai samu yayi daren jiya ba, har yanxu kuma kamar mafarki yake ganin al’amarin, ya kasa gane ta yaya Mai martaba ya iya switching comfortably without even considering the consequences after, a iya rayuwarsa bai taba zama confuse and lost kamar haka ba, bai ma san ko Jay zai yarda he knows nothing about the sudden switch ba, he don’t even know if he will believe him, ba a good 5 minutes Jay bai fado masa a rai ba and he is just restless, in his wildest dream he never saw this coming, bude kofar parlonsa aka yi ya daga kai da sauri, Mami ta shigo parlon kana ganinta kasan tana cikin tashin hankali matuka, tun da ya kalleta sau daya ya dauke kai, ta karasa har tsakiyar parlon cikin rawan murya tace “Amma ka bani mamaki Junaid, wallahi ka ban mamaki, ban yi tunanin zaka yi ma Jawwad haka ba, baka duba irin son da yake maka ba da irin goya maka bayan da yake yi in every situation ko da kai ne baka da gaskiya, baya taba sauraron wanda zai karanto masa laifin ka har ni kuma, a kan ka Jawwad sai ya rufe ido ya gaya min babu dadi, duk abinda zan ma Jawwad bazai daga ido ya kalleni ba amma inyi kuskuren fadan wani aibu a kanka ranan sae abinda ya manta ne bazai gaya min ba cikin fushi, ya dauke ka tamkar wanda ku ka fito ciki daya, ya dauki son duniya ya daura maka and he is always ready to protect you at anytime amma wai kai zaka ci amanarsa ka auri warce kasan yake bala’in so kawai don nace ba yanxu zai aureta ba sai nan da warni Lokaci…. Kuka ta fashe da shi sosai tace “Daga kai har Sarki kun nuna mana iyakarmu da ni da Jawwad a gidan nan, wallahi da da zuciya daya kake zaune da Jawwad ko sarki ne yace zai aura maka yarinyar nan baza ka amince ba duk yanda zai yi da kai kuwa, instead fighting zaka yi har sai kaga Jawwad ya samu, amma saboda baka tare da Jawwad da zuciya daya you are just using him shi ne zaka yi masa irin wannan sakayya ka auri budurwarsa, don Allah ka gaya min meye ribar ka Junaid?” Ajay dal different direction yake kallo amma duk yana sauraronta, Infact mamaki ma ya sa yayi stiff kawai a inda yake zaune jin kalaman Mami, cikin kuka Mami tace “Magana nake maka kake kallon wani waje daban, ka gaya min me da na yayi maka da kake son ganin downfalt dinsa haka? Is it a crime don ya nuna yana yin ka, kuma yana goyon bayan ka?” Ajay ya kalleta kamar bazai ce komai ba, can dai yace “I new nothing about this marriage, ban san komai a kai ba, ke kika ce ma Mai martaba ya maida auren kaina which he did, ni ban san komai a kai ba, bai kuma yi shawara da ni ba” A fusace Mami tace “Baka san komai a kai ba amma auren ke kanka har yanxu kuma ga ka zaune comfortable as if nothing? In baka san komai a kai ba al birkice ma Sarki zaka yi kace baka son auren baza ka iya cin amanar dan uwan ka ba, idan yaga ka daga hankalin ka ai zai nemi mafita, kuma ta nan ne zai san yayi babban kuskure abinda yayi, da nace ya maida auren kanka idan har ya dau Jawwad matsayin da sai yayi hakan? Wallahi duk abinda ya samu da na bazan taba yafe maku kai da Sarki ba, i will never forgive you two kuma sai na fito na sanar ma duniya duk abinda ake ciki babu abinda zan boye dama an dade ana ruwa kasa na shanyewa a gidan nan, an dade ana nuna mana iyakarmu ni da Jawwad, an kuma ci amanar Marigayi Yusufa, an ci amanar sa, da shi ne bazai taba yin haka ba, an ci amanar dan sa, in har wani abu ya samu Jawwad zan fito in sanar ma duniya komai wallahi” Cikin kuka sosal ta kare maganar, shi dai Ajay kallonta kawai yake don bai ma san me zal reba, Lace Dania sat da na ce ma jawwad shi ke son katsakani da Allah amma ba kai ba, kawai kana, using dinsa ne, shi kansa za gane hakari yanxu, tunda gashi ka ci amanarsa, in har ka cika dan halak samun Sarki zaka yi duk yanda zai yi yayi a warware auren nan da ya daura da kai, amma sain ka cika dan halak” Tana kai wa nan ta fice daga parlon Ajay ya bi ta da kailo, bai taba ganin mutum that is so perfect in manipulation kamar wannan matar ba, cikin few minutes ta juya lamarin ta dawo ita ce victim din, jinginar da kansa da yayi masa nauyi yayi ya lumshe idonsa, he wish zai iya da ya sake samun Mai martaba amma bazai so ya bata masa rai ba, don bata masa rai da aka yi tun farko shi ya ja har yayi wannan abun da yayi…. Tun da Nenne ta samu labarin Yau Lahadi za a kai Khaleesat Bauchi ta fara lissafin wa enda za su je kai amarya yanda baza ail kunya ba tunda ba garitalallen gida za a kal ta ba, Sha’awa har da kukanta da Nenne tace banda ita a yan kal amarya, Nerine ta gama lissato duk wa enda za su Bauchi ciki har da Baaba Gaje, Aunty Farida, Aunty Murja, Hajiya Zaliha da babban er ta, Uwar kishiyar Aunty, Murja, sai wata a manri wanda mijinta ke da kudi Hajiye Salaha, da kvar Menne ta lissafo Mama Shatu a cikinsu wal shima ann kar Maram All va kullacet………su raka yayarsu gidan auren ta, sai kuma Lamisah, sal da Aunty Farida tayi da gaske da Nenne sanrian Nenne ta yarda ta sa kawar umma wato: Mama Savame a yan kal amarya, daga karshe Nenne ta sa wata Cousin sister ginta ita ma dattijuwa kamar Baaba Gaje, duk sal da Nenne ta jaddada masu gidan Sarauta za aje kai Khaleesat su ruta mata asiri kar su bar abun fade a can, Aunty Farida tayi mamakin da Nenne bata ce zata je ba, bayan Nenne ta gama zayyano duk yan kal amarya sal kuma tace “In kuma a jirgi za aje kai amaryan to lallai sal an gaftare wasu mutane a wannan lissafin da aka yi kar ayi mana kallon yan iska” Throughout Jiya da shekaranjiya Khaleesat bata shiga darnuwar da take ciki ba yau da taji za a kai ta Bauchi, dama zuwa yanxu daga Jay din har Ajay babu wanda take kira a waya tunda bata samun su, duk wani……gayu tun daga jiya zuwa yau, ko dakin da take mutum ya shiga ba abinda zai ji yana tashi sal azababben kamshin jikinta, ga wani glowing da take, gashin kanta ma ya sha gyara na musamman dama gashi bakikirin, duk wanda ya kalleta sai ya sake kalionta, haka yarinyar Hajiya Zaliha ta zauna dakin tana ta kallonta kamar ta samu TV, komal na Khaleesat burgeta yake, turarurruka ba na wasa ba Hajiya Zaliha ta kai Aunty Farida suka siya ma Khaleesat har da turarumukan wuta tunda ga kudi enough, Banda Hajiya Zalihar abubuwa da yawa Khaleesat da… Halysaah Page 100 By Khaleesat Haydar ********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 09017242889 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ **************************