*A TRUE LIFE STORY* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL'AMARI* Page 1⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Copied By VISIT www.aihausanovels.com.ng For More Novel. AIHAUSANOVELS is website consists of hausa novels note, the reason of launching this site is to Entetaint, Motivate and Educate our readers. We provided hausa novels of many type, Such Adventure, love, romance, fiction, non-fiction, mystry, fantasy, action e.t.c from hausa Authors We provided a new and old novels both softcopy and hardcopy from our Author with thier permission. AIHAUSANOVELS shafin yanar gizo ne wanda yake ɗauke da littattafan hausa, dalilin bude wannan shafin shine domin Kayatar masu karatu da kuma ilimantar da su. *Gargad'i! Gargad'i! Gargad'i! dan Allah kar a juya mi wannan labarin tako wacce siga har sai an nemi izinina dan Allah ko harafin (A) kar a canza min bana so* *Ina mik'a sak'on Barka da sallah na ga d'aukacin al'ummar musulmai baki d'aya Allahu rabbi ya amshi ibad'un da muka aikata Allah ya maimaita mana shekaru masu yawa da al'bakar wad'anda ke k'asa mai tsarki Allah ya dawo daku cikin lafiya* *Alhamdulillah lillahi ala kulli halin na godewa Allah da ya bani rai da lafiya da nitsuba da konciyar hankali har na samu damar fara rubuta wannan littafi cikin k'oshin lafiya ya Allah ka bani iko da damar gama shi lafiya kamar yadda na fara lafiya Ameeen ya rabbil izzati* Suna iso kan layin uguwar tasu Usman ya dafa kafad'un abokin shi Nura dake jan motar tasu cikin dan fidda ido yace. "Kai Nuru tsaya a nan ba sai ka shiga cikin gidaba zan sauk'a a nan!." Kai Nuru ya juyo tare da k'are mishi kallon sai kuma yayi murmushi ganin yadda Usman sarkin surutu ya wani zaro ido cikin murmushin yace. "Kai Usman ni wallahi Hamma Umar mamaki yake bani ji yadda yake wani tsareka a gida kamar mace! ji yadda kake wani zaro ido dan kasan yanzu yana harabar gidan yana duba marasa lafiyan dake zuwa gunshi." Shi dai Usman balle marfin motar yayi ya fita yana hararan Nuru tare da cewa. "Ban za kawai lailamajanun duk ka zama majanuni akan mace sai dare yayi kazo kace in raka ka kakuwa sani sarai Hamma Farouq zai nemeni dan zai bani magani na." Shi dai Nuru dariya yayi tare da jan motarsa ya tafi. Shi kuwa Usman cikin sand'a da d'an d'aga k'afa da lek'e-lek'e ya shiga cikin gidan, gaba d'aya hankalin shi na can gefen wasu yan bukkoki da akayi da ginin zamani sai samansu kuwa da akayiwa rufi da ciyawa suka fita kamar bukkokin rigar Fulani sai fulawowi masu kyau da suka zagaye harabar gidan da haske tako ina cikin bukkokin da sukafi kama dana shak'atawa wani farin matashi ne mai cikar haiba da tsurawa wanda yafi kama da laraba Dr Umar Faruoq kenan shine yake zaune kan kujerun dake zagaye a bukkokin sai mutane kusan 8 dake zaune daga dukkan alamu sunzo ya duba lafiyar sune gaba d'aya hankalin shi na kansu. Shiko Usman ganin haka yasa cikin sauri da d'an d'aga k'afa ya zille yayi cikin gidan, kai tsaye Parlour Nenne ya nufa cikin yana yinsa na fara'a yayi sallama, tare da shiga cikin Parlour yana ta haki da d'an zare ido. Nenne ce ta fito daga cikin bedroom cikin sakin fuska tace. "Usman daga ina haka kaketa zare ido?." Dariya ya d'an yi tare da zamewa ya zauna gefen Ummul dake ta binshi da ido sai ya Adam da ya Sadik dake zaune a gafe duk sun zubawa Usman ido cikin murmushi Ummul tace. "Mugun ne ya koroka ko ya Usman?." Kai ya d'an juya cikin sauk'e ajiyan zuciya yace. "Tab Nenne Hamma Umar yazo ya nemeni ko.?" Cikin sauri da salon tsokana ya Adam yace. "Ehh yazo k'afa 3 yana neman ka." Ido ya kuma d'an zarowa yace. "Toh ni fa ba wani wuri naje ba! kawai na d'an raka abokina Nuru zance gun budurwar sane, kuma yanzu nasan Hamma Umar zaice yawo natafi ban sha maganina ba." Dariya Nenne tayi cikin kula tace. "A a baizo bafa Usman." Shima dariya yayi cikin sauk'e ajiyan zuciya yace. "Ummul me kika dafa mana me? Dan wallahi yunwa nikeji." Ya Sadik ne yace. "A a saidai ta tashi ta dafa maka ko indomi ne dan miyar ganye tayi kai kuma kasan an hanaka ci." Fuska ya d'an tsuke cikin badda zancen yace. "Ummul kawomin zanci na yau kawai bazai min komai ba." Nenne ce ta kalleshi cikin kula tace. "A a fa Usman ka kiyaye dokokin Doctors ko dan samun lafiyar ka." Baki ya kuma turawa yace. "Wallani ni nagaji da wannan dokokin ace duk wani abu green bazan ciba, dan Allah Nenne yau kawai kinji ko?." Ita kam Nenne gaba d'aya take jin tausan Usman a ranta sabida ciwon dake tare dashi gashi yaro matashi . Shi kuwa Usman cikin dariya ya kalli Ya Adam yace. "Ya Adam kasan me Nuru yakeyi in munje gun babynshi?." Murmushi ya Adam yayi tare da cewa. "Inako zan sani sai ka fad'a min dai." Ummul ce tayi carab tace. "Ya Usman me yake yi?." Hannu yasa ya kamo na Ummul d'in cikin yanayin shi na abin dariya yace. "Jeki kawo min abinci zan baku labari." "Toh" tace tare da haura saman d'an steps d'in da zai sadata da kitchen d'in sauri-sauri tasa mishi abincin a pilet sannan ta dawo parlour stol tajawo gaban shi ta ajiye mishi abincin cikin son jin zancen tace. "Toh ga abin cin bamu labarin." Murmushi yayi cikin raha ya mik'e tsaye tare da cewa. "Nenne kina jiko kullum Nuru zaizo yace na rakashi zance amman sam in munje ba abinda yake sai shirme." Ido ya Adam ya tsura mai cikin gimtse dariyar shi yace. "Kamar yayafa?." Dariya ya kuma tare da cewa. "kuna jiko Nenne kullum in munje muna zuwa k'ofar gidan su budurwar tashi sai Nuru ya kalle ni cikin in inarsan nan yace min k.. k.. kai Bosho k.. katsaya a cikin motar nan karka fito, ni kuma sai nayi dariya nace toh , in an aika ta fito sai yace ta zauna kan motar , ita kuma sai ta wani d'ale saman motar ta zauna tana kallon shi." Ajiyan zuciya tayi tare da cewa. "Hmmmm Nenne kin san me Ruk'ayyan take ce masa?." Su ya Adam kam da ya Sadik tuni sun fara dariya itama Ummul sai dariya take . Ita ma Nenne murmushi take yi tare da girgiza kai alamar a,a. Shi kuwa Usman cikin nuna musu abin a zahiri ya jawo hannun Ummul ya ajiyeta kan hannun kujera shi kuma ya matso gaban ta gab da ita ya d'an sa k'afarsa d'aya a gaba d'aya kuma ya maidata baya sannan ya rink'a d'an sunkuyawa yana d'an d'agowa kamar maiyin wazifa sai kuma ya kalli ya Sadik yace. "Ya Sadik Kunga haka ko?, wallahi haka Nuru yake tsayuwa a gaban ta kamar mai jin bacci yayi ta layi ita kuma sai tayi ta wani mishi murmushi kamar sokuwa." Sai ya kuma kalli Nenne yace. "Nenne kin san me take ce mata kuwa.?" Cikin dariya tace. "Me yake ce mata?." Dariya yayi tare da koikoyar muryar Ruk'ayya budurwar Nurun yace. "sai tace ,Nuru ina sonka." Sai kuma yayi dariya yace. "Nenne ba tace masa Nuru ina sonka ba?." Cikin dariya Ummul tace. "Ehh". Shima dariya ya kumayi tare da cewa. " shi kuma soko sai ya kalleta murya can k'asa yace. "Allah ya d'aiyiba." Sai kuma suka rink'a dariya cikin dariya Usman yace. "Kijifa Nenne wai Allah d'aiyiba sai kace wad'anda akayiwa haihuwa Allah ko Nuru yana bani dariya shi yasa nake son rakashi zance, kumafa kullum haka suke hirar tasu ,tace Nuru ina sonka shiko gogan yace, Allah d'aiyiba." Gaba d'aya dariya suke shiko Usman yaja pilet d'in abincin ya fara ci kamar bashi ya basu dariyar ba. Autan gidan ne Aliyu ya kalleshi cikin sanyi yace. "Ya Usman ba doctor ya hanaka cin duk wani abu green ba kuma kake cin miyar ganye kasan fa Hamma Umar zaiyi fad'a." Harara ya cillawa Aliyu tare da cewa. "Toh sai dai in kaine zaka gaya mishi naci miyar dan nasan ka ka iya gulma." Haka yaci gaba da cin abincin suna ta dariya da hira da raha. Yana cikin cin abincin ya d'ago kanshi da sauri jin k'amshin turaren Hamma Umar na ratso hancin sa, da sauri ya ture pilet d'in kasan kujara sai kuma yayi zuru-zuru da ido yana sauraron ta ina Dr Umar d'in zai shigo. Shi kuwa Doctor Umar dama sarai yasan Usman baya cikin gidan kuma ya ganshi lokacin da ya shigo cikin gidan haka yasa yana gama sallaman marasa lafiyan kai tsaye part d'in su ya nufa wonka yake sonyi amman bazai iya zama har yayi wonka baije ya bawa Usman maganin shi ba hakan yasa ya d'auko magungunan tare da goran FARO a hannushi ya nufi cikin gidan. Sallama yayi tare da tsayuwa a bak'in k'ofar yana jin suna ta hira da dariya bai shiga ba har sai da ya kuma sallama Nenne ta amsa mishi tare da bashi izinin shiga. Shi kuwa Usman tuni ya tonk'oshi kai yayi kalan tausayi . Ummul kuwa mik'ewa tayi ta koma gefen Nenne dan jin muryar Hamma Umar d'in dan ta sanshi sarai yanzu zai samo laifin da zai turama . Ya Adam da Ya Sadik kuwa Usman suka tsurawa ido. Shi kuwa Dr Umar kan shi a sunkuye ya shiga cikin parlon cikin girmamawa ya gaida Nenne amsawa tayi fuska a sake tare da cewa. "Umar bak'in naka duk sun tafi kenan?." Murya can k'asa yace. "Ehh" dan shi baida rakad'i irin na Usman kuma baya da yawan surutu bashi kuma da shiga sabgar wani baya kuma wasa da yara kasan cewarshi shine babba a family nasu baki d'aya gashi da iya horon marasa jin magana. Usman ya kafe da ido cikin tsuke fuska da yanayin tuhuma. Shi kuwa Usman a hankali ya tashi ya matso gaban yayan nashi cikin ladabi da tsantsar k'aunar juna yace. "Afwan Hamma Umar bazan sake ba." Ido Hamma Umar ya kawar sannan yasa hannushi ya rok'k'oshi kan Usman tare da kamo kunnen shi ya d'an matse cikin yanayin hukun tawa. Hannu Usman ya rink'a d'an yarfawa yana d'an k'ara tare da cewa. "Hamma na natuba kayi hakuri bazan kuma zuwa yawo ba." Sake mishi kunnen yayi sannan ya ajiyeshi kan kujera yana kallon fuskar sa, Magungunan ya b'abb'allo sannan ya mik'a mishi, hannu Usman yasa ya karb'a tare da afasu a bak'in sa yana mai yamutsa fuska, shi kuwa Dr Umar goran ruwan FARON ya b'alle cikin kula yasawa Usman bak'in goran a bak'in shi, shiko Usman ido ya rumtse sannan ya had'iye magungunan nashi. Murya can k'asa Umar yace. "Kaci abinci?." cikin sauri Usman yace. "Eh Hamma naci." Kai ya gyad'a sannan ya tattara magungunan tare da rufe goran ruwan ya juya ya kalli Nenne da ta zuba musu ido cikin tausayin su da mamakin irin kauna da kulawan da Umar yake bawa k'aninshi Usman. A hankali Doctor Umar yace. "Nenne sai da safe." cikin kula Nenne tace "Allah ya bamu al'heri Faruoq, Allah ya biya ka hidiman da kakeyi da d'an uwanka, Allah ya bashi lafiya." "Amin ya rabbil izzati." Yace tare da ficewa . Kai tsaye Bedroom d'in su ya wuce wonka yayi tsab sai k'amshi yake zubawa yana fitowa yasa wonddon shi 3 qtr sai rigarshi Mara hannu turare ya d'an fesa sannan ya jawo woyarshi da laptop d'in shi, Usman ya kira, Shi kuwa Usman tuni ya biyo bayan Hamman nashi ganin ya shi ga wonka ne ya dawo parlour ya zauna yana kallo, ganin kiran Hamma Umar d'in nashi yasa ya mik'e da sauri ya nufi cikin bedroom d'in, yana shiga gefen shi ya zauna cikin son juna suka kalli juna, a hankali Dr Umar Faruoq yace. "Na had'ama ruwan zafi kaje kayi wonka." "Toh" yace tare da mik'ewa ya dawo gaban Hamma Umar d'in ya tsuguna yana mai kallon shi da yana yin shi yake jira. Shi kuwa Dr Umar laptop d'in nashi ya d'an ture gefe sannan yasa hannu ya b'abb'ale boturan jikin rigar Usman d'in, yana gama bud'e mishi boturan Usman d'in ya mik'e ya cire rigarsa, sai kuma ya matso gaban Hamma Umar d'in ya tsaya , kai Hamma Umar ya girgiza tare da b'allewa Usman d'in beld'in dake k'ugunshi sannan ya d'an sunkuyo ya fara kuncewa Usman d'in igiyoyin takalman shi. Shi kuwa Usman sai kallon hannun d'an uwan nashi yake yi. Yana gama kunce mishi ya kalleshi a hankali fuska a d'an tsuke yace. "Wai kai Usman yaushe zaka koyi kula da kanka ne? , ace kana namiji baka iya d'aure igiyan takalmin ka da kuncewa ba bel d'in jikin kama baka iya. mannashi ba hatta botur bazaka iya sawa da cirewa ba komai sai nayi maka randa bana kusa da kai kuma toh ya za kayi?." Dariya yayi tare da shigewa toilet yana cewa. "Hamma Umar ai ko Aure kayi tare zamu tare a gidan bazan bari kayi nesa da niba." Shi dai Hamma Umar kai kawai ya jinjina tare da bin d'an uwanshi da kallo. Bayan ya fito wonkan ne, Umar ya had'a mishi tea sannan ya bashi ya sha, yana gamawa ya konta gefen Hamma Umar d'in nashi dake ta lallatsa laptop d'in shi. A haka har zuwa d'an wani lokacin sanna Hamma Umar ya rufe laptop d'in tare da jawo blanket ya rufe Usman d'in cikin kula yace. "B'iyaye na Usman kayi Addu'a kayi bacci kasan gobe ma akwai zuwa office ko?." Fuska ya d'an tab'e tare da d'ago hannushi zai fara Addu'ar yace. "aikin bankin ko aikin jaraba ni wallahi na gaji da aikin ma fa Hamma." Ido ya d'an tsura mishi tare da tsuke fuska yace. "Bacci fa nace muyi ba surutu ba , dan na lura kai kafi son zaman banza." Addu'a sukayi sannan suka konta baccin su. 2:00 Am Doctor Umar ya tashi yayi ta nafilfili tare da karatu k'ura'ani yana mai nemawa d'an uwanshi lafiya a gun mai bada lafiyar. Haka yayi ta karatu sai da aka kira assalatu sannan ya tashi Usman suka tafi masallaci.. Bayan sun dawo masalla cin ne Doctor Umar ya d'an koma bacci bayan ya fitarwa Usman kayan aikin shi tare da had'a mishi ruwan wonka, yana konciya lokacin d'aya bacci ya saceshi , shi kuwa Usman bai tasheshi ba dan sanin yau sai azahar zai tafi hospital d'in su. wonka yaje yayi sannan yazo ya kimtsa ya saka kayan shi, shiru yayi tare da kallon Hamma nashi sai kuma ya matso gaban Dr Umar Faruoq d'in cikin kallon fuskarsa yasa yatsunsa biyu ya matse hanc......... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBATACCEN AL'AMARI* Page 2⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Ya d'an matse saman hancin shi kad'an tare da tsura mashi ido, cikin bacci Hamma Umar Faruoq ya d'an bud'e ido jin an rik'e mishi hanci yasan ba maiyi mishi haka sai B'iyayen shi, idon ya tsurawa Usman yana kallon fuskarsa da hannushi dake rik'e da net d'inshi, a hankali ya mirgino bakin gadon yayi rufda ciki tare da zuro hannayen shi k'asa, shi kuwa Usman k'afarshi ya turo kusa da hannayen Hamma Umar d'in. A hankali Dr Umar Faruoq yasa hannu ya d'aurewa Usman igiyoyin takal man nashi sannan ya d'an d'ago hannushi ya manna mishi bel d'in shi, shi kuwa Usman duk abinda Hamman nashi ke mishi binshi da ido yake yana jin k'aunar B'iyayen nashi har cikin ranshi, yana gama manna mai bel d'in ya mik'e tsaye tare da kamo net d'in wuyan Usman d'in ya gyara mai zaman shi sannan ya kalleshi cikin muryar bacci yace. "zo kasha tea." Kai ya gyad'a cikin sauri yabi bayan shi a parlour suka tsaya shi Dr Umar Faruoq ya had'awa Usman d'in tea tare da mik'a mishi cup d'in, karb'a yayi yana d'an kurb'a yace. "Hamma zan shiga cikin gida." Kai ya gyad'a mishi ba tare da yayi magana ba, shi kuwa Usman murmushi yayi ya fita ya nufu cikin gidan, Usman d'in na fita shi kuwa ya mik'a a hankali yayi mik'a tare da yin salati cikin takun bacci ya nufi cikin d'akin da nufin ya koma baccin har ya konta idonshi ya haggo mishi magungunan Usman dake kan mirror daga duk kan alamu Usman baisha maganin ba hakan yasa Faruoq d'in mik'ewa da sauri ya d'auki magungunan tare da fitowa parlour goran Faro ya d'auka ya fito ya nufi cikin gidan. Shi kuwa Usman a part d'in kakarsu Hajjajo ya samesu suna zaune a parlorn ta suna ta hira, cikin yana yinsa na sakin fuska ya shiga hannun shi rik'e da cup d'in tea yana sha yana d'an lumshe ido, yana shiga Hajjajo ta kalleshi cikin k'aunar jikan nata fuska dauke da murmushi tace. "Usumanu ka fito ne." har yakai cup d'in bakin shi ya cire tare da yi mata kallon kinafa bata min suna fuska ya d'an tsuke yace. "Allah ko Hajjajo kina b'ata min suna wai Usumanu kice min Usman na kawai inbaza ki iyaba kibar kirana." Murmushi tayi tare da cewa. "Zo ka zauna kaci abinci." "Toh" yace sannan ya matso kusa da Ya Adam hannu ya mik'a mishi suka gaisa sannan ya gaida ya Sadiq, sannan ya juya zai k'arisa gaban Inna yazo dai-dai gaban Ummul khairi dake zaune kan hannun kujera sai ya tsaya ganin yadda ta karya wuya ta tsura mishi ido tana murmushi gaban ta ya matso dai-dai lokacin Nenne da Aliyu kuma suka shigo parlour, ita kuwa Ummul kai ta k'ara d'agowa cikin koikoiyar muryar Ruk'ayya budurwar Nuru tace. "Ya Usman ina son ka." Murmushi yayi tare da k'ara matso ta ya tura k'afa d'aya gaba d'aya kuma ya maida shi baya ya d'an rink'a sonkuyowa kanta sannan ya koikoiyi muryar abokinshi Nuru yace. "Allah d'aiyiba ." Gaba d'aya su Nenne da ya Adam da ya Sadiq kam sai dariya suke Aliyu harda rik'e ciki Hajjajo kuwa sai binsu tayi da ido tana murmushi dan tasan shek'iyan cin Usman yawa ne dashi. Shi kuwa Usman ko a jikin sa sai tea d'in shi yaci gaba da sha, Itama Ummul sai murmushi takeyi ta zauna gefen shi tana sa mishi abinci. dai-dai lokacin Dr Umar Faruoq kuma yayi sallama duk da yana jin yadda suke ta dariya, yana shiga ya gaida Nenne ya Adam da Sadiq kuwa suka gaida shi, gefen Hajjajo yaje ya zauna tare da tonk'oshe k'afafun shi kanshi a sunkuye yace. "Hajjajo an tashi lfy." Juyowa tayi tana fuskan tarshi tare da zubawa kekkyawar fuskar sa ido, shi kuwa bai bita kan ta amsa mishi gaisuwar ba ya sunkuyar da kai yana b'allo magungunan Usman d'in. Ido Hajjajo ta lumshe cikin k'aunar jikan nata da takeji tamkar ranta donko ya kasan ce shine jikanta na forko da ta fara mallaka uwa uba ga tsananin kamar da ya keyi da mahaifin shi gashi takwaran mijin tane hakan yasa take masa wani irin so mai tarin yawa gashi da halaiyar girma Doctor Umar Ibrahim Umar shuwa kenan. Cikin kula tace. "Umaru sanda kafi mata yanga Umaru kafi k'arfin kab'i mace sai dai ta bik'a Ummaru sanda mai k'amshin al'miski sanda babuga mai taimakon na gida da woje , Ummaru tsiyar ka rigima da mishkilanci ko maganar ka tsada gareta." Kanshi a k'asa ya d'an lumshe ido har ga Allah shi wannan halin nashi halittar sa ce haka Allah yayishi bai san ya zaiyi ya canza kanshi ba haka yake, a ranshi yace. "Ya zanyi da Rubutaccen al'amari haka Allah ya halicceni bazan iya canza kaina ba". Ita kuwa Ummul tuni ta tsuke fuska dan sam bata jin Hamma Umar Faruoq d'in nasu kamar jinin ta haka kuma ya samo asali ne da yanayin halin Faruoq baida shiga harkar da ba tasaba bayi da yawan magana baya kuma son raini da hayaniya yana da girmama na sama dashi har ranshi kuma yake jin son y'an uwanshi a ranshi yana kuma kula da yanayin tarbiyar k'annen shi a matsayin shi na babban yaya, suma kuma suna son d'an uwansu sai Ummul ce da sam bata ko son su had'a inuwa d'aya da shi. Tsuke fuska Ummul ta kuma yi jin yadda Hajjajo ke wani bashi kula ta musamman shiko ya wani shareta. Su Adam da Sadiq da Aliyu da Usman sai murmushi sukeyi. Shi kuwa yana gama b'allo maganin ya mik'awa Usman tare da bud'e mishi ruwan ya bashi yasha sannan ya had'a maganin wuri d'aya tare da mik'ewa ya fita a hankali yana zuwa bakin kofar woyarshi ta fara tsuwa cikin wani sautin wak'ar India kaal hoh nan hoh sautin ne da ya kasan ce ko ba,a ga Umar Faruoq a wurin ba matukar akaji sautin toh tabbas yana kusa da wurin sauti mai cike da sanyi da tausayi. A hankali ya fito a barandar Hajjajo ya koma gefen baya kad'an tare da zauna wa kan kujerun dake jere a wurin. Woyarshi ya zaro a hankali yayi picking ya fara magana a hankali. Su kuwa a parlour Usman ne ya mik'e tare da cewa. "Nenne bari in tafi gwadago." Murmushi ya Sadiq yayi tare da cewa. "Tab ai kai kam aikin wuya kam baka cikin kai da zuciyar ka take rabi ai sai dai kaje back kana shan rab'a." Hannun shi yasa ya d'an dafe k'irjin shi cikin lumshe ido yace. "Da kenan ya Sadiq yanzu nayi lafiya zuciya ta kamar taka take ko buhu zan iya d'agawa." Adam ne ya d'an kalleshi yace. "Sai dai buhun kam amman damuwa da firgicin da zuk'atan mu zasu iya jurewa taka zuciyar bazata iya d'auka ba." Murmushi sukayi baki d'aya ita kuwa Ummul maya finta ta gyara cikin fara'a tace. "Yauwa ya Usman dama zanje gidan Anty Sadiya dan tunda akayi sallah ban jeba." Hannu ya mik'a mata tare da cewa. "Zomu tafi yar k'anwata zan kaiki." Aliyu ne ya kalli Nenne da sauri yace. "Nenne kina ji wai zata tafi gidan Anty Sadiya kuma batayi girkin ranaba." Da sauri Nenne tace. "Ehh haka nefa Autana kaga har na manta, kai kam Usman tafi kawai abinka kar ka makara, Ita Ummul sai tayi girkin rana." Lokacin d'aya idanun Ummul suka ciko da k'ollah tib hannu ta rink'a yarfawa a hankali tana d'an buga k'afafun ta tare da yin kan Aliyu tana cewa. "Ma gulmacin yaro dan munafurci Aliyu duk k'asa min ido a rayuwa ta shi yasa wallahi na gomma ce ina school ba mai takura wa rayuwa ta." Sai ta kuma juyowa gun Nenne cikin muryar lallashi tace. "Ayyah Nenne na kiyi hak'uri ki barni naje wallahi zan dawo da wuri inyi aikin dare." Kai Nenne ta girgiza alamun bazata jeba. Sai hawaye car-car a fuskarta. Shi kuwa Aliyu dariya ya fara yi cikin jin dad'in ya d'ana mata tarko. Kanshi tayi a fusace tana. "Munafuki wallahi sai na dokeka." Cikin dariya ya zille ya fara gudu ita kuma tana binshi a baya ta kasa kamashi. Shiko Aliyu gudu yake tare da cewa. "Yoh ai laifin ba nawa bane tunda bani nace duk randa kika dawo Hutu ko weekend kece zakina yin girki ba, Hamma Umar Faruoq ne ya fad'a, kuma kice ni zaki daka, kije ki ce mishi bazakiyi girkin ba mana, ni me nawa a ciki?." Kuka ta farayi tana binshi tana cewa. "Ai shima mugun tace kawai ya hanani hutawa a rayuwa ta, ga masu aikin Amman don mugunta yace ni zanke yin girki mugu kawai mai bak'in hali." Dariya Aliyu ya kuma yi harda yi mata gwalo yace. "Shifa Hamma Umar yana tausayawa mijin da zaki aurane shi yasa yace ke zakina aikin , don karkije baki iya girkiba, a ga laifin iyayenmu." Binshi tayi da sauri shi kuma ya nufi woje da gudu yayi gefen da ya hoggo Hamma Umar d'in nasu yana gudu yana juyowa yana kallon ko ta kusa kamoshi. Shi kuwa Dr Umar Faruoq tun da ya katse kiran woyan da yake yin, yake jiyo hayani yarsu shi Aliyu a hankali yake tsokanar ita kuwa Ummul sai mita da kuka take yana jin tana ta cewa Aliyu munafuki, Kalmar da baya k'aunar yaji an suffanta mutun da ita. Ita kuwa sam bata lura da Hamma Umar d'in a wurin ba. Shi kuwa Aliyu ya zo dai-dai gaban Hamma Umar d'in ya sule yayi wani irin mugun fad'uwa a k'asan tayis, gum ya buge bak'in shi a take sai ga jini, cikin wahala ya saki kuka mai k'arfi, wanda yasa su Nenne fitowa a guje. Shi kuwa Hamma Umar da sauri ya mik'e ya d'ago Aliyu ranshi a b'ace ya kalli yadda bak'in yaron keta zubda jini, ita kuma tsayuwa tayi jikinta nata rawa ganin yadda jini yake zuba a bak'in k'anin nata ga wani irin mugun kallo da Hamma Umar ke watsa mata. Ganin su Nenne sun fito tayi maza tayi bayan ya Usman dan shi kad'ai ne mai kareta su ya Adam ma kullum fad'a suke mata da biyewa Aliyu da takeyi tayi ta jibagarsa. Ita kam Nenne da sauri ta k'arisa gaban Dr Umar Faruoq da ya tallab'e hab'ar Aliyu cikin fad'a tace. "Ummul zaki kashe min yaro a banza ga yadda kika fasa mishi baki akan zuwa uguwa." Ita dai Ummul sai hawaye hannun Usman ta rik'e da k'arfi ganin Dr Umar Faruoq ya kirata da hannunshi cikin rawan murya tace. "Ya Usman dan Allah ka bashi hak'uri wallahi bazan sake ba Allah ban san zai fad'iba." A hankali Usman yace. "Hamma tace kayi hak'uri." Fuska ya tsuke murya a fad'ace yace. "Zo nan." K'ara k'ak'k'ame hannun Usman tayi tana zubda k'olloh, shi kuwa Usman hannushi yasa a hankali ya b'amb'areta a jikin shi cikin rad'a yace. "In baki jeba zai k'ara hatsala kije ki k'arb'i hukun cinki." Cikin zubda k'olloh tayi gaban shi a hankali take taku har zuwa gaban shi tana zuwa ta durk'usa a gaban shi. A hatsele yasa k'afa ya tureta tare da cewa, " taso." Da sauri ta mik'e ta tsaya a gaban shi. Mari ya watsa mata cikin fad'a ya nunata da yatsa yace. "Kika kuskura kika k'ara cewa wani munafuki wallahi sai na fasa miki baki, ke kullum bakya jin magana, kiyi ta munafurta mutane kuma kece mai halin muna fukan, kalli yadda kike kuka tun ba'a tab'aki ba, ko shi da kika fasawa bak'in baiyi wannan kukan ba, kuma kiji daga baki na ba inda zaki je sai shegen son yawo." Sai ya kuma watsa mata mari tare da cewa. "Ki wuce kiyi cikin gida ki fara akin ki tun wuri." Baki na rawa tace. "Toh" Ta fice ta tafi tana kuka Usman ne yabi bayan ta da sauri yana lallashin ta har saida ta d'an huce ya kalleta cikin kulawa yace. "Allah ya d'aiyiba." Murmushi tayi tare da cewa. "Ya Usman Ina sonka." fuskarta ya shafa tare da koikoiyan muryar Nuru yace. "Allah ya d'aiyiba Dariya sukayi baki d'aya sannan ya fice ya tafi. Hajjajo kuma da Nenne da su ya Adam parlour Nenne suka bita, Nenne da su ya Adam fad'a suke mata, ita kuwa hajjajo lallashinta take yi. Shi kuwa Dr Umar Faruoq yana rik'e da hannun Aliyu har suka shiga parlour su, kan kujera ya kontar da Aliyu dressing na wurin yayi mishi tare da bashi maganin ya sha, sannan ya kunna mishi A,C da TV. a hankali Aliyu ya rink'a sauk'e ajiyan zuciya tare da lumshe ido, lokacin d'aya yayi bacci, shi kuwa Dr Umar Faruoq wonka yayi tare da kimtsawa ciki shigarsu irin ta manyan doctors sai k'amshi yake zubawa ya fito ya nufi katafaren chemist d'inshi mai suna Baba aura chemist dayake kusa dasu, yana zuwa dai-dai bakin wurin yayi wani irin....... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL'AMARI* Page 3⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Wannan shafi d'ugguruggum dinshi naki ne ke kad'ai Mamyn Najmah ina al'fahari dake ina sonki har cikin raina Allah ya bar zumunci ngd da k'aunar ki gareni 😘😍🤝* *A*jiyan zuciya tare da lumshe ido, ganin mutane da suke cike a harabar bakin chemist d'in mata da maza manya da yara, cikin ranshi yake fad'in, "Allah ya bashi ikion dubasu baki d'aya". Fitowa yayi cikin nutsuwa ya nufi wurin da ya kasance wurin zaman shi a ko wacce rana matuk'ar dai ya shigo potiskum toh shi baya samun hutun weekend d'in. Yana isa yaranshi da ke aiki chemist d'in suka yi mishi barka da safiya, sannan ya zauna ya fara duba marasa lafiyan d'aya bayan d'aya yana mai basu kulawa yadda ya kamata duk da ba sakin fuska yake yiba amman a fili za'a gane fuskarsa mai ciki da tausayi ne da jink'an marasa lafiyan, dan bashi da surutu maganar sa a k'aiyade take . Haka ya yayi ta dubasu har zuwa azahar daga nanne ya tashi tare da sa yaran nashi suka rufe chemists d'in sannan sukayi alwala suka nufi masallaci dan yin sallan a jam'i. Bayan an idar da sallah su suka koma bakin aikin su shi kuma kai tsaye gida ya nufa dan gaba d'aya ya gaji ga yunwa ga baccin da yake ji. Ita kuwa Ummul bayan ta shiga kitchen ta fara aiki kenan , woyarta ta fara suwa tun kafin ta d'aga tasan waye ne dan sautin kiran kawai ke shaida mata Mustapha ne ke kiran ta haka yasa cikin shauk'i da k'aunar juna suka fara magana a woyar, gas d'in ta kashe sannan ta fita cikin takunta mai cike da nitsuwa, kai tsaye ta nufi part d'in kakarsu Hajjajo bedroom ta wuce tana zuwa ta d'ale kan gadon ta mai rumfa cikin sanyin muryar da ko kana gefen ta a kan gadon bazaka ji abin da take fad'i ba, Ido ta lumshe cikin sauk'e ajiyar zuciya tace. "Habeebi" "Na'am." Yace mata tare da cewa. "Ummul kina sani d'imuwa soyayyarki tana cazamin kai da jinin jikina k'ok'olwata na cushe in banji muryar ki na awa 3 ba Ummul ki daure ki soni ko rabin yadda nake sonki." Ido ta kuma lumshe wa cikin hura mishi iska a kunne murya can k'asa tace. "Ya Habeebi ka kontar da hankalin ka Ummul taka ce jiki da jini da duk wani motsina kana cikin raina ko bacci nake fuskar ka itace k'awan yata." Mustapha kam k'ara sakewa yayi kan kujerar da yake konce gaba d'aya tsikar jikin shi yana mik'ewa lokaci d'aya kalaman ta suka sakar mai wani kasala da shauk'i k'aunar ta yakeji na ratsashi har cikin k'ahon zuciyarshi, yayin da ita kuwa Ummul take jin duk duniya ba yanayin da take so da jin dad'in shi kamar kasan cewa a haka suna musayan zantukan so masu sanyi, ji take matuk'ar babu Mustapha a rayuwarta toh gani take kamar ba nunfashi tare da ita. Haka sukaci gaba da soyewa kamar su shiga jikin juna, ita kuwa Ummul gaba d'aya ta manta da wani batun girkin da aka sata, haka yasa tayi ta woyarta sune basu katse hirar ba sai 12:23 pm tana katse kiran kuma bacci ya kwashe ta, bata farka ba sai yanzu da taji muryar Hamma Umar a parlour HaJajjo. Ita kuwa Nenne dama ta shiga mak'o tansu duba mara lafiya so batasan me Ummul tayi ba. *Asalin dengar takan su, Zuriya d'aya ce duk su jikokin Alhaji Umaru shuwa'arab ne* Alhaji Umaru Shuwa'arab asalin sa shi da matarsa Rabi'atu Hajjajo kenan su Shuwa'arab ne asalin ma zauna garin patiskum cikin unguwar tudun wada yamma da fce, kowa yasan shuwa'arab kyewawane kuma masu jin larabci ne, Alhaji Umaru da Hajjajo suna da yaran su 3 duk mazane babban d'ansu Alhaji Ibrahim Umar shuwa sai k'anneshi biyu tagwaye ne Hassan da Husaini sun tashi cikin gata da tsantsanr k'aunar juna, Alhaji Ibrahim shine babba kuma ya kasan ce mutun mai tausayi da k'aunar k'annenshi yana musu so mai tsanani, iyayensu kuwa sun basu tarbiya mai inganci tare da ilimin addini da na zamani sun tashi cikin tsabtacecciyar rayuwa, da kulawar iyayen su bayan sun girma ne Alhaji Ibrahim yayi aure ya auri matarsa Amina ba fullatanar potiskum d'in, mace mai mutunci da kara da sanin ya ka mata, bayan anyi auren bada jimawa ba Allah yayiwa Alhaji Umaru Shuwa rasuwa, daga nan ragamar gidan ya zama a hannun Alhaji Ibrahim yake ya rik'e k'anneshi da amana ya basu dukkan abinda uba zai bawa ya ranshi sunci gaba da karatu su . Yana zaune da matarsa da mahaifiyar shi a gidan shi da k'annenshi baki d'aya, Ranar da Alhaji Umaru Shuwa ya cika shekara d'aya da rasuwa a ranar Amina matar Alhaji Ibrahim ta haifi d'anta fari tas kekyawa dashi mai kama da babanshi, ran suna yaro yaci sunan kakanshi Umar Faruoq kenan. Yaro ya tashi cikin gata da kulawan mahaifiyar shi da kakarshi da k'annen mahaifinshi Hassan da Husaini, yaro mai farin jini da kwarjini. bayan shekara 4 Alhaji Ibrahim, yayiwa k'annenshi Aure rana d'aya, suka tare a gida jen da ya gina musu a gefen nashi. Bayan watannni 5 da auren Khadija matar Hassan ta fara laulayin cikinta na fari a lokacin kuma Amina matar Alhaji Ibrahim itama tana da cikin d'anta na biyu, matar Hussani kuma bata da ciki tukun , Bayan wani lokacin Amina matar Alhaji Ibrahim ta haifi d'anta na biyu mai suna Usman a lokacin Umar Faruoq kuwa ya cika shekara 5 da y'an watanni, Khadija matar Hassan kuma ta haifi d'anta na fari mai suna Adam wanda tsaka ninshi da Usman kwana 12 ne Usman d'in ya girmi Adam da kwana 12 haka yaran suka tashi cikin shak'u da juna ko mai tare akeyi musu, Umar Faruoq ya tashi da k'aunar k'annenshi. Usman da Adam suna da shekara d'aya a duniya Allah yayiwa Alhaji Ibrahim maifin Umar da Usman rasuwa. Rashuwa da ta shiga jikin Hassan da Hussain da Hajjajo sunyi kukan rashin d'an uwansu wanda shine madadin mahaifinsu a garesu. Amina matar Alhaji Ibrahim mahaifiyar su Umar wacce yaran ke karanta da Ammi tayi kukan rashin mijinta da rabuwa da yaranta dan tana gama ta kaba ta koma gidan iyayen ta, Alhaji Hassan wanda suke kira da Abba ya karb'i Umar da Usman ya dank'asu a hannun matarsa Khadija wacce yaran ke kira da Nenne sannan kakarsu Hajjajo itama tana gidan suka taru suka raini yaran cikin kulawa da tsantsar gata ta yadda su Umar basu san zafin maraici ba. Nenne kuma bayan ta haifi Adam ta kuma haihuwa yaran 4 Sadiq sai Sadiya sai Rabi'atu wacce take takwarar Hajjajo ce amman suna kiranta da Ummul khairi sai kuma d'an autanta Aliyu. Yaran sun tashi cikin k'aunar juna baka gane cewa Nenne ba ita ta haifi su Umar ba, Sai dai kowa da halinsa dan shi Umar mishkili ne baya wasa da yara kuma kasan cewarsa shine babba a family d'in su yasa k'annenshi suna girmamashi shi kanshi Umar yana jin haushin yadda yake halinshi, yayinda hakan ya jamishi kiyeyyah a uzuciyar Ummul ita kuma gani take yana takura rayuwarta a, zahiri Umar yana jin zafin yadda wasu lokutan ake gaza gane cewa wannan halin fa ba yin kanshi bane Allah ne ya halicce shi a hakan. Sun tashi cikin gata da kulawa inda Umar a yanzu haka shi babban doctor ne yana d'aya daga cikin yerdeddun governor damaturu shine doctor dake duba lafiyar governor nasu kuma shine babban doctor dake aiki a general hospital damaturu, Usman kuwa shi accounter ne sai . Sai Adam Airforce ne yanzu haka a Kaduna yake sai in yazo ziyara. Sai Sadiq shi kuma yana aiki a ministry of justice. sai Halimatu Sadiya ita kuma nurse ce tana aiki anan cikin garin potiskum. Sai Ummul khairi ita kuma bayan ta gama primary school d'in ta aka jona mata secondary school GGC damaturu inda ta koma cikin damaturu da zama a cikin makaran ta, yayin da shi kuwa Alhaji Hassan Abban Ummul kenan shi yana aikine a offishin gwamna a damaturu hakan yasa Abba yana da gida a can inda yake zama yana aikin shi sai alhamis ya taho week end cikin garin patiskum d'in, hakan yasa idan anyi hutu Ummul takan zauna a gidan shi dake gidan jen maikata na ministry of works and housing dake gashua road damaturu dan jira ya gama aikin sa sai su tafi tare su koma cikin potiskum tare. A hakan ne wata rana Ummul ta fita ita da k'awayen ta suna d'an zagawa cikin uguwar, anan ta had'u da Mustapha saurayin da suke soyayya a yanzu haka, shima yazo gun abokan shine a unguwar, dan shi Mustapha gidan su na commissioners quarters dake Maiduguri road damaturu, haka sukayi ta soyeyya in sunyi hutu yana zuwa har gidan su Ummul d'in dake potiskum, Haka yasa ya saba da ita ya saba da y'an uwanta suna yiwa juna so mai tsabta. Shi kuwa Umar sosai ya zuba ido kan lamuran Ummul, gashi in Abba baya nan kusan shine uba a gidan, so yana tsanani sa mata ido dan kare tarbiyar ta ita kuwa hakan yasa ta k'ara tsanarsa da jin tsoronshi, dan baya mata da sauk'i. Usman kuwa mutun ne mai fara'a da sakin fuska yana watsa da kawo dan shi ko da Abba wasa yake mishi kamar kakanshi, haka yasa Usman ya kasance wani jigo na gidan in ya fita ko na awa d'aya ne sai anyita ceki yarshi, shi da Umar kuwa suna yiwa juna wani irin so mai tsanani Umar yana k'aunar Usman fiye da komai a rayuwarshi suna yawan kaiwa Amminsu ziyara a gidan kakannin su. Usman tun yana k'arami ya tashi da ciwon zuciya mai tsanani inda Abba da Daddy Hussain in Abban kenan sukayi ta jin yarshi, a haka abin tashi hankali da fari an gane cewa zuciyar Usman tana da d'an hujin dake sashi ciwon zuciya so anyi ta bashi kula, amman kuma Usman na girma abin na k'aruwa haka yasa zuciyarshi ta zama ta tsage , dole aka fitar dashi Egypt so acan akayi mishi aikin tare da kulawar d'an uwanshi Umar Faruoq aikin da akayiwa Usman a cikin zuciyar shi aiki ne da yasa an bar wasu na'urori a cikin k'irjinshi d'an zuciyar tashi tayi raunin da bazata iya harba jininshi ba sai da wannan na'uran haka kuwa aka k'inda ya mishi dokokin aka hanashi cin duk wani abu green dan abubuwa green suna sa jinin d'an adam kauri shi kuwa zuciyarshi nada raunin harba tsinkekken jinima bare mai kauri sai na'urar ke iya harba jinin , haka duk bayan shekara 5 yake zuwa a canza na'urar, ko kusa da kai Usman ya zauna zakaji yedde na'urarnan take aikin a jikin shi tana, *cak-cak* yana harba amman sai ka matso kusa dashi sosai zakaji sautin a hankali. Wannan larura da Usman yake da ita yasa gaba d'aya zuriyarsu suke tausayawa mishi duk wata kulawa suna bashi, yayinda Umar Faruoq kuwa a duniya baida wata matsala sai damuwar ciwon B'iyayen shi, shi yasa duk wata kulawa ta duniya wacce uwa da una zasu bawa d'an su ya had'eta yana bawa k'aninshi Usman. Ummul kuwa da Usman suna rayuwa tamkar abokai, Anty Halima kuwa tana gidan mijin ta amman duk wata kulawa tana yiwa Ya Usman d'in nasu. Ya Adam da Usman kuwa su tamkar tagwaye suke tunda dama kwana 12 Usman yake bawa Adam. Ya Sadiq kuwa mutumin Hamma Umar ne. Auta Aliyu kuwa abokin fad'an Ummul ce shima yanzu ya kusa gama secondary school d'in shi ita kuwa Ummul sune suka gama this year so yanzu tana gida ana sama mata admission a FCE (T) potiskum zatayi NCE d'in ta akan maths and computer. toh fa a d'an wannan zaman da takeyi a gidanne take k'ara fuskantar takura fad'a da Umar ke mata hakan yasa ta k'ara tsanarshi. Haka Ita kuwa Ummul take da wani irin ciwon mara a duk lokacin da zatayi al'adarta kasan cewar a makaran ta tafara ciwon cikin sai ba'a santa dashi sosai ba tana dai fad'a tana ciwon ciki amman Nenne bata san ciwon mai tsanani bane..... *Tak'aitaccen labarisu kenan* Mun dawo kan labarin yanzu. Nenne na dawowa ta lek'a kitchen tana kiran Ummul tana fad'in. "Ummul kin gama ne?." Ido ta d'an zaro ganin ba abin da tayi a kitchen d'in cikin sauri ta fito parlour kan dinning table d'in ma ba komai agogo ta kalla da sauri ta fita ganin har 2:00 pm tayi. Parlour Hajjajo ta nufa tana kiran Ummul d'in. tana shiga Parlour ta kalli Umar Faruoq d'in cikin b'acin rai da fushi tace........ By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL'AMARI* Page 4⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Fatan alkhairi a gareku masoya na da wannan littafi nawa ina godiya da k'aunarku gareni 🙈🙈 kuyi hak'uri nasan wasu zasuce ba zasu fara karatu yanzuba sai nayi nisa sabida basa son farawa suzo suna jira toh dan Allah kuyi hak'uri duk wacce tasan sai anyi nisa zata fara toh ta Tarawa kanta kar sai nakai 20 ko 30 azo ayita bina P/C a nace ana so ni banzan iya hanaku ba sabida ina son mai sona kuma bana iya fiffik'e ido nayi banza da d'an Adam sabida d'an Adam abin karramawa ne Amman wallahi ina takuruwa gashi inada eyes problem kuyi hak'uri Ku tarawa kanku ngd Allah bar zumunci da k'auna GARKUWAR Fulani tana al'fahari da masoyan ta* Rai a b'ace cikin yana yin kai k'ararta tace "Umar kaga Ummul tafiya tayi bata yi aikin komai ba ko, yanzu-yanzun nan kira min Halima kace maza ta turota gida." Kallon Nenne yayi yace. "Tafiya tayi gidan Haliman ne? kuma batayi aikin ba?." Cikin takaici Nenne tace. "Ehh tafiya tayi mana tunda bata gidan nan tun dazu nake kiranta ban jita ba, gacan kitchen d'in kuma ba abinda ta tsinana." Hajjajo ce tayi tsaki dan ko ita bata san Ummul na cikin d'akin nata ba, cikin mita irin ta tsofaffi tace. "Wannan yarin ya akwai lalaci da k'in aiki, fisabillahi yanzu a haka za aurar da ita a kaiwa wani yayi ta famar yi mata bauta." Wani dogon tsaki Hamma Umar d'in ya ja, sosai yakejin zafin rashin jin maganar ta. Ita kuwa Ummul tuni ta fara had'a zufa dan tun dazu take son fita jin Hamma Umar d'in a parlour Hajjajo ya hanata fita, gashi yanzu kuma tanaji Nenne ta kawo kararta gun shi dama ya lafiyar kura a dawa bare an tab'oshi, hannu ta yarfa cikin sanyi da rawan murya tace. "Nenne nifa gani nan ba inda naje fa, kuma wallahi zanyi girkin." A hatsale Nenne tace. "Toh me kikeyi a cikin d'akin da kika kasa fitowa?, me kike aika tawa? wato ke har kullum indai batun aiki ne sai kin b'ata min rai ko?." Taku ta farayi a hankali tana fitowa parlour murya a hankali tace. "Ayyah Nenne kiyi hak'uri wallahi zanyi aikin yanzu zan gama." Hajjajo kam salati ta rink'a yi tana tafa hannu cikin mamaki tace. "Ke takwarata yanzu yaushe kika shigo ban ganki ba? kuma uwar me kikeyi a d'akin?." Baki ta d'an tura cikin kallon kakar tasu tace. "Wani abu nake yi." Harara Nenne ta watsa mata cikin jin haushi tace. "Bar min aikina zanje nayi abina, ki zauna nan ki gayawa Hamman ku dalilin ki na k'in yin aikin." Tana kaiwa nan ta fice part d'inta ta koma kai tsaye kitchen ta wuce ta fara aikin ta cikin sauri da tsanaki. Shi kuwa Hamma Umar tunda Ummul ta fito bai kalli inda take ba har Nenne ta fice , yana komce kan 3 str sai y'ar k'aramar k'orya da ke gaban shi mai cike da kindirmo mai kyau fari tas, konce yake rigin gine sai laptop d'in shi dake kan ruwan cikin sa ya hard'e k'afafun shi. Ita kuwa Ummul cikin tsarguwa ta tsuguna gefen shi kad'an tayi k'asa da kanta tana d'an satan kallon shi, Hajjajo kuwa mik'ewa tayi ta kalli Hamma Umar d'in cikin kula tace. "In dama maka da furane? ko insa maka dakkere ne?." Baiyi magana ba sai lumshe ido yayi, ita kuwa ganin haka ta shige d'aya d'akin ta fara dama mishi da fura. Shiru parlour su duka biyu ba wanda yayi magana har zuwa wani lokacin ganin haka Ummul ta gyara durk'usuwan da tayi don guiwowin ta sun fara tsami, fuska ta marairaice ta lokk'oshe kanta a kafad'ar ta tai rau-rau da ido murya can k'asa tace. " Hamma kayi hak'uri wallahi bazan sake ba". Shiru bai kula taba, itama shirun tayi dan ta sani da ta k'ara magana toh ta k'ara laifine dan zaice ta cika mishi kunne da hayani yarta." Haka yasa kawai sai ta rink'a jujjuya guiwowinta dan sun tara jini, gashi ta fara jin ciwon marar da yake mata duk wata, haka yasa ta fara zubda k'ollah tana d'an gogewa da tafin hannun ta, murya na rawa tace. "Hamma kayi hak'uri." Sai yanzu ya bud'e idanun shi a hatsale yace. "Uban me ya hana ki yin aikin?, wacce tsiyar kike aika tawa a cikin d'akin tun da safe?." Baki na rawa ta d'an matsa baya a hankali tace. "Hamma har na fara aikin fa, sai Mustapha ya kirani shine na zo nan d'in." Daga koncen yasa bayan hannushi ya yarfa mata mari da bayan hannun nashi, sannan ya tashi zaune ido ya kafa mata tare da cewa. "Amsa kiran Mustapha yafi aikin da zaki yiwa mahaifiyar ki ko?." Kai ta rink'a juyawa cikin toshe bak'in ta dan karta saki kuka, tana juya kai tace. "Kayi hak'uri Hamma bazan k'ara ba." Tashi yayi ya mik'e fuska a murtuk'e ya watsa mata harara tare da cewa. "Mik'e kije kiyi aikin kar in b'ab'b'allaki fitinenniya kawai mara jin magana." Da sauri ta fice tana zubda k'ollah tare da k'uk'k'ini k'asa-k'asa kai tsaye kitchen d'in ta shiga. tana zuwa tace. "Ayyah Nenne kiyi hak'uri' ki kawo aikin zan k'arasa." Rai a d'an had'e tace. "Je kici gaba da baccin ki, nayi aiki na, in bakiyi na gidan kuba ai zakiyi na gidan miji inda ko godiya baza'ayi miki ba." Haka Nenne tayi ta mata fad'a har suka gama aikin, itako tana bata hak'uri, Shi kuwa Hamma Umar nonon ya karb'a sannan ya koma part d'insu. Nenne kuwa suna gama aikin rana taje tayi wonka ta kimtsa d'akin Abba dan yau zai shigo potiskum d'in, haka yasa ta barwa Ummul sauran aiyu kan girkin dere da kuma abincin Usman da ban. Su ya Adam kuwa da ya Sadiq da Aliyu duk suna tare a parlour Nenne suna kan dinning table suna cin abinci. Aikin take yi cikin k'arfin halin dan ciwon da mararta keyi ya fara yawa sai ta shiga kitchen d'in ta d'an yi aikin in matar ta murd'a sai ta dawo parlour ta konta kan kujera tayi ta murk'ususu sai tayi jigib da zufa dan azaba. Shi kuwa Aliyu duk abin da take yi hankalin shi na kanta, dan yana matukar son yar uwarshi haka yasa yana lura da yadda take zuwa ta kontan . 8:00 pm Abba ya iso gida cikin family d'in shi su ya Adam da ya sadik duk suka nufi part d'in Hajjajo suna zuwa suka tsame shi shida Hussain in shi wato Daddy suna ta hira da dariya Hajjajo na zaune a tsakiyar su Hamma Umar kuma yana gaban su Abban kanshi a sunkuye yana zaune tsakiyar k'annen mahaifin shi, Abba ne ya kalleshi cikin kula yace. "Farouq ya ina k'annen naka? ban gansu ba." Ya d'ago kanshi zaiyi magana kenan su Adam suka shigo cikin girmamawa suka gaidasu sannan suka zauna sukaci gaba da hira, kallon Hamma Umar Abba ya kumayi tare da cewa. "Usman da ummul fa ina suke?." Aliyu ne yayi carab yace. "Abba Anty Ummul bata da lafiya tun d'azu kuka takeyi, ya Usman kuma yanzu ya dawo bai shigo ba tukun." Daddy ne ya kalli Hamma Umar d'in cikin yana yin tabbaya yace. "Farouq meke damun Ummul d'in.?" Kai ya sunkuyar a hankali yace. "Daddy ni ban san bata da lafiya bama sai yanzu." Nenne ya kuma kalla a hankali yace. "Nenne meke damun ta.?" Fuska ta d'an tab'e cikin kula tace. "Hmmm Umar kafa san Ummul da raki tun bayan sallan magariba take kuka wai cikin da mararta ke ciwo ko tashi tak'i tayi wai bazata iya ba." Cikin mamaki Abba yace kai Khadija mamana bata da lafiya kice raki , duk rakin Ummul indai taji na dawo toh zata zo tamin sannu da zuwa , tunda kikaga har ta k'asa tashi toh gaskiya tana jin jiki." Hajjajo tace. "Gaskiya kam gwara a dubata." Daddy ne ya kalli Hamma Umar din cikin bada umurni yace. "A gaskiya bata da lafiyan ne, Farouq kaje ka dubata." "Toh" yace tare da mik'ewa ya fita a ranshi yana cewa. "Mara lafiya ke zuwa gun doctor ita kuma uwar sakalci da raki doctor ne zaije ya sameta dan tsabar samun sake." A tsakar gida ya had'u da Usman murmushi Usman d'in yayi tare da sosa k'eya yace. "Hamma tun d'azu fa na dawo, yanzu sai naci abinci zanzo insha maganin." Kafeshi yayi da ido cikin k'aunar k'anin nashi da tausaya mishi, hannu yasa ya d'an bugi k'eyarsa tare da matse kunnenshi yana. "Usman baka jin magana , baka kula da lafiyar ka, baka jin tsoron da nake ji akan ciwon nan naka." Shi kuwa Usman d'an kara ya saki tare da cewa. "Wayyo Abba na Daddy kuzo Hamma na zai tsinke min kunne." Abba ne yayi dariya jin muryar Usman yace. "Da ka iso wuri ko ido bai ganka ba kunne zai shaida zuwan ka Usmanu shehu sarkin barkwanci shi kowa kakan sa ne." Daddy ne yayi murmushi tare da cewa. "Usman kenan shi shiya d'auki halin Baban mu komu y'ay'anshi bamuyi irin yanayin shi ba kamar yadda Usman yayi. , shiko Farouq koman shi. na Yaya Ibrahim ne har tausayin shi da kulawan shi a kan k'annenshi." Usman kuwa dariya ya rink'a yi yana juyawa Hamma Umar na binshi da ido yana kallon yadda k'anin nashi ke harkokin sa tamkar baisan ciwon da ke jikin shiba. A haka ya wuce ya nufi parlour Nenne, shi kuma Usman ya tafi gunsu Abba yana zuwa. Ya gaida su sannan ya kalli Aliyu cikin murmushi yace. "Kai Auta ina Ummul ban ganta ba?." Hajjajo ce ta kalleshi tare da cewa. "Bata da lafiya mai baka duk abinci da kake so kaci d'in, yau anan zakaci abinci." Cikin zillewa zancen yace. "Ni duk abinda doctors suka hanani bana cin karki wani had'ani da su Abba, kuma ko Nenne ma shaida ce bana cin komai matuk'ar dai green ne, dan haka karma kiyiwa Ummul lak'el kice ita ke bani komai naci, kowa yasan ina bin doka." Aliyu ne yayi carab yace. "A a kam ya Usman wallahi ko jiya kaci miyar ganye." Kai ya sunkuyar yana murmushi ganin yadda Abba da Daddy suka tsareshi da ido cikin tsoro Daddy yace. "Usman meyasa baka kiyaye lafiyar ka Usman ka rufa mana asiri kake bin dokokin doctors ko zamu samu ka rabu da ciwon nan." Murmushi yayi cikin k'arfin guiwa ya kalli Abba da gaba d'aya ya karaya jikin shi yayi sanyi hannun Abban dana Daddy ya d'an rik'e a hankalin yace. "Cuta ba itace mutuwa ba , lafiya kuma bata hana mutuwa nasan abinda kuke tsoro, ba haushe yace, nisan kwana maganin annoba, karku damu yanzu nayi lafiya jin zuciya ta nake kamar ta k'arfe." Murmushi su duka sukayi tare da sauk'e ajiyan zuciya sannan sukaci gaba da hirar. Shi kuwa Hamma Umar a hankali yayi sallama, a bak'in k'ofar ya tsaya jin ba'a amsa sallama ba sai sheshek'an kukanta da yake ji, haka yasa ya kutsa kanshi cikin d'akin kan gado ya hoggota konce sai murk'ususu takeyi hanna yenta rik'e da mararta kuka takeyi sosai cikin wahala gaba d'aya ta birki ce, A hankali ya matso bak'in gadon murya can k'asa yace. "Ke me haka? shin baki iya Addu'a bane sai kuka? ki nitsu ki gaya min meke damun ki?." Ido ta k'ara rumtsewa cikin wahala ta d'an mirgino tayi rigingine tare da cewa. "Wayyo Allah na! cikana! marana!." Fuska a tsuke ya sunkuye kanta kanshi ya kawar tare da rumtse ido a hankali ya tura hannun shi cikin rigar ta kan mararta yasa yatsunshi ya matse tare da danne matar tata. Mik'a tayi tare da sakin wani irin kuka cike da azaba a gigice ta yunk'uro cikin rawan jiki ta sa hannu ta dam k'o.... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL'AMARI* Page 5⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Wannan shafi naki ne k'awata ta gari Ngd da k'aunar ki gareni Hauwa Halliru (Mmn khairat) Allah bar zumunci da k'aunar Ngd Ngd Ngd 🤝😘😍* Hannun shi cikin wahala da gala baita ta ture hannun taci gaba da murk'ususu tana yarfa hannu da juya kai, duk da sanyin a/c dake ratsa d'akin ita zuface keta tsatstsafo mata duk ta inda hudan gashin jikin ta yake, tsayuwa yayi tare da tsuke fuska kai ya jinjina ya fice abin shi, Parlour Hajjajo ya nufa, sallama yayi tare da shiga gefen Abba ya zauna kanshi a sunkuye yace. "Abba tak'i ta tsaya in dubata sai kuka take yi." Nenne ta kalli Abba tare da cewa "Toh ai kunji ko mara lafiya da gardama, yoh ba sai abarta da ciwon taba, ai bai dameta bane da ita zata nemi maganin". Daddy ne ya mik'e tare da Hajjajo Ya Usman da Ya Adam na biye da su a baya har sunje bak'in k'afar Daddy ya juyo ya kalli Dr Umar Farouq d'in cikin murmushi dan yasan Umar ya hatsala ne, murmushi yayi kumayi sannan yace. " Farouq zo muje ka dubata ko." Kai ya kuma sunkuyar wa cikin yana yinshi na girmamawa ya mik'e yabi bayan su, Nenne ma da Abba da Aliyu biyosu sukayi. Suna zuwa Parlour Nenne Daddy ya zauna tare da d'an d'aga murya yace. "Ummul kizo nan, taso kizo ko mamana, kizo Hamman ku ya dubaki." Jin muryar Daddy ne yasa ta k'ara sakin kuka dan tasan Daddy yana matuk'ar k'aunar ta da lallab'ata, Jin ta fashe da kukan ne Hamma Umar ya zauna kan carpet a gefen Daddy a hankali yayi tsaki, Usman kuwa da Hajjajo cikin bedroom d'in suka wuce suna zuwa, Hajjajo ta zauna gefen ta cikin sauri ganin yadda take kuka da juyi gaba d'aya fuskarta tayi jazazir sai zuba da ya mik'a jikinta kab sai numfashi take a wahalce, da sauri ta rik'o ta cikin kid'ima take kiranta. "Subahannalhai Ummul me yake damun ki haka? yaushe ya fara miki wannan ciwon ?." Kanta ta kuma kifewa kam pillow cikin cije lips d'in ta ta junk'ura ta zauna gaba d'aya jikinta rawa yakeyi hannu ta rink'a damk'e wa baki na rawa tace. "Marata zata b'alle jiri nakeji cikina k'uguna yana sarawa." A kid'ime Hajjajo ta kamota tsayar da ita tayi tare da talla beta cikin tattaro k'arfinta tace. "wannan wanne irin ciwone kamar maiyin nak'uda." A haka suka nufi parlour Usman kuwa na biye dasu a baya gaba d'aya tausayin ta ya cika shi ya kasa komai sai. sannu yake ce mata. Kan 3 str Hajjajo ta kontar da ita . Nenne kuwa gaba d'aya jikin ta sai ya kama rawa ganin yadda yartata ta birkice. gaba d'aya sai sannu suke ce mata, abu kamar nak'uda duk ta galabai ta, Abba ne ya kalli Hamma Umar d'in tare da cewa. "Farouq me haka kuma? meke damun ta.?" Juyawa yayi gaban ta ya d'an taso ya tirk'usa kan giiwarsa sannan ya kalleta cikin tsura mata ido yace. "Ki nitsu ki gaya min ina ke miki ciwo." Kai ta jinjina a wahalce. Shi kuwa kai ya d'an sunkuyar sannan yace. "Meke damun ki?." "Cikina da marata." "Yaushe ya fara miki ciwon?." "Tunda yamma." Kallon ta ya d'an yi sannan yace. "Cikin da matar kad'ai ne ke ciwon?." Dafe k'ugunta tayi murya na rawa tace. "Harda k'uguna yana sarawa kamar zai b'alle." Harararta yayi k'asa-k'asa tare da tsuke fuska yace. "Karki cika min kunne da kuka in zaki magana kimin yadda zan gane kin sani sarai bana son hayaniya." Usman ne ya d'an matso tare dasa d'an kwalinta ya goge mata zufan ya kuma d'an kalli Hamman nashi a hankali yace. "Hamma meke damun ta?." Ya fad'a shima kamar zaiyi kuka Shi kuwa fuska ya kuma tsukewa yace. "Dama kina irin wannan ciwon ne?." Kai ta gyad'a alamar ehh. Juyawa ya d'an yi kanta sannan yace. "Bak'in ki bazai iya magana bane? ko kuma kin zama kurma?." "Ehh dama yana min." Ta fad'a a hankali. "Sau nawa ya tab'a yi miki hakan?." Ido ta rumtse cikin jin kunya tace. "Ko wanne wata sai yamin haka." Baki ya tab'e dan gano matsalar ta, Hajjajo ma da Nenne sun gano abin da ke sata hakan shiyasa sukayi shiru suna kallon ta. Shi kuwa Hamma Umar kamar cikin mugunta yace. "Allurai 3 za ayi miki." Jin allurai har 3 yasa ta zaro ido woje cikin rawan murya tace. "Ni dai a barni da ciwona zuwa gobe zai bari, dan Allah Hamma kar kamin allura." Daddy kuwa da Abba Umar suka ni da ido cikin yana yin tabbaya suka tsareshi da tabbayarki me yake sata ciwon . Shi kuwa Hamma Umar mutun ne mai tsananin kunya hakan yasa gaba d'aya sai ya resa ya zaiyi musu baya min ciwon nata. Sai ya kalli Ummul d'in cikin lumshe ido yace. "Ke me yake saki ciwon? kinaji ana tabbaya kinyi shiru, ko kina jiran ni zan amsa miki ne?." Kai ta sunkuyar cikin tsananin kunya da wahala sai hawaye car-car a fuskarta. Shi kuwa Hamma Umar ganin su Abba sun maida hankalin su kanta, yasa yayi maza ya zille ya fita. Part d'in su ya nufa yana zuwa ya had'a alluran da zai mata sannan ya ajiye cikin firij woyarshi ya zaro tare da kiran Nenne tana d'agawa yace. "Nenne Ummul d'in tazo zan mata allurar, tazo da sauri dan akwai masu jirana a woje zan fita gunsu." toh Nenne tace. sannan tasa Ummul d'in ta mik'e ta fita badon ta soba. Shi kuwa zama yayi ya d'an jirata, ganin shiru bata shigoba ya mik'e ya shiga toilet wonka yayi sannan ya fito daure da towel a k'ugunshi, parlour ya fito da nufin ya d'aukam woyarshi ya sake kiran Nenne. Ita kuwa Ummul a daddafe ta shigo parlour tana shiga yana shigowa shima. Ganin ta a tsaye ya sashi juyawa da sauri ya koma cikin bedroom d'in, tsaki yaja sannan ya kimtsa tare da fesa turare a jikin shi. Parlour ya dawo yana watsa mata harara, ita kuwa Ummul batama ganshi ba lokacin da ya fito d'in haka yasa bayan san abinda yakewa harara da tsakin ba. Bayan ta ya zagaya rigar ta ya d'an nad'e sannan ya d'an yi k'asa da zanin ta, ba tare da ya ture farin ondawunyan ta da pan d'in tabaya dire bakin alluran a kansu, dan shi haka yake matukar zai yiwa mutun allura mace ko namiji ba tab'a yarfa ya kalli fatar jikin mutun dai-dai yayi alluran a kan gajeron wonddon mutun inko mave ce kan siket d da pan d'in yake d'aura allurar. Tana jin yana murza bak'in alluran sai kuma ya tsaya cikin fad'a yace. "Ke ki sake jikin ki uwar tsoro allurace ba mashi ba kike wani Kane jikin ki, kuma d'aga yau karki sake shigo min d'aki tunda baki iya sallama ba, ki bari sai randa kika koti sallama." Ita dai kai kawai take gyad'awa da rumtse tafin hannun ta. K'ara ta d'an saki tare dasa hannun ta ta baya ta kamo k'ugunshi ta rik'e da k'arfi ido ta rumtse jin yadda ya zirnik'a mata allurar, k'ara damk'e shi tayi dan yadda taji zafin yadda ruwan allurar ke shiga jikin ta. Shiko Hamma Umar da sauri ya zare allurar sannan ya janye hannun ta dake kan k'ugunshi kan mazaunanta ya dire mata hannayen nata sannan ya tura ta murya a fad'ace yace. "B'acemin da gani, sokuwa kawai ba abinda kika iya sai koke-koke banza kawai duk kin cika min kunne." Ita kam Ummul tuni ta koma gefen ta jingina da jikin kujera dan jiri take ji ga wani irin suka da taji k'ugunta nayi lokaci d'aya kuma taji d'umin jini na bin k'afafun ta. Ido Hamma Umar ya zaro mata tare da buga mata tsawa fuska a yatsine yace. "Fice min a d'aki kina tsaya har saidakika zubar min da k'azan tarki , ubanwa zai goge miki wannan abin." Ya fad'a yana nuna jinin dake bin k'afafun ta a take kuma rumtse ido yana yamutsa fuska cikin fad'a yayi kanta. Dai-dai lokacin Usman kuma ya shigo. Da sauri yaje gaban ta cikin kula ya kamo hannun ta kai ya lok'osa a kafad'an shi cikin sanyi yace. "Hamma kayi hak'uri ni zan gyara wurin." tsaki yaja sannan ya fice yana cewa. "Wallahi ka gyara wurin kafin na dawo ita kuma ta bar nan." Yana fita Usman ya kalleta a hankali yace . "Kije cikin gida." A kunyace ta fice ta nufi parlour Nenne . Shi kuwa Usman gyara wurin yayi tsab sannan ya feffesa turare. Yana gama wa Hamma Umar d'in ya shigo rik'e da magungunan shi, kan kujera ya zauna sannan ya bashi maganin, d'aga nan kuma suka yita hirarsu tare da Ya Adam da Sadik da suka shigo. Ita kuwa Ummul kai tsaye toilet ta shige wonka tayi ta kimtsa jikin ta sannan tazo ta konta kusa da Nenne ta, a hankali Nenne tace. "Ummul yanzu duk wata haka like gama da wannan ciwon cikin?." "Ehh " tace mata tare da lumshe ido dan kunya takeji. A khana a tashi haka rayuwa tayi ta juyawa shak'uwa tsakanin Usman da Ummul kullum k'aruwa yake yi zuroyarsu cike da farin ciki. Nasu da wata matsala Sai matsalar ciwon Usman da Ummul, wasa-wasa ko wanne wota Ummul sai ta galabai ta abin yaci tsura tasha magunguna da allurai har tagaji a banza. Abba kuwa ya matsala Nenne da tabbayarshin dama haka ko wacce mace take fuskantar wannan matsalar ne yayin yin al'adarta. Nenne takan ce mishi . "Insha Allah in tayi aure zai bari." A haka suka bar maganar. Sai yau kuwa tunda gari ya waye Ummul ta tashi da. ciwon ciki da matar ga sarawar da k'ugunta keyi. Kasan cewa Hamma Umar baya gida yana cikin Damaturu yasa Abba ya d'auketa shida Nenne suka kaita jama'a clinic kasan cewa doctor abokin Hamma Umar ne. Gwajin forko da doctor yayi ya gane matsalar ta, cikin girmamawa doctor yayiwa Abba baya nin ciwon nata ya kuma k'ara da cewa. "Abba dama akan samu wasu matan da irin wannan larurar, maganar gaskiya duk magungunan da za'a bata ko allurai duk aikin banza ne mafita d'ayace wacce zata rabata da ciwon nan da izinin Allah muddin akayi mata aure ta mu'amalantu da zaman takewar aure toh insha Allah zata rabu da ciwon nan." Cikin kad'uwa Abba yace toh, "Doctor menene mafita?." Ajiyan zuciya ya sauk'e tare da cewa . "Mafitar dai itace ayi mata aure kawai." Da wannan shawarar Abba ya koma gida tare da Nenne Ita kuwa Ummul bata san abinda ke wakana ba. Sai fama da takeyi da ciwon ta. Bayan kwana biyu Abba ya kira Hussain shi suka zauna a d'akin Hajjajo suka tattauna kan maganar Ummul su yasu suka gama maganarsu ba and a yasan abinda suka zantar. Yau jumma'a tun safe Ummul keta gyare-gyare da girkr-girke dan yau Habeebin ta Mustapha yana kan hanyarshi ta zuwa, 4:15 pm Mustapha ya iso, yana isowa Abba da Hamma Umar suka shigowa, da sauri Mustapha yayi parking ya fito ya nufi su Abba yana zuwa kusa dasu,yayi sauri ya.... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 6⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Ya tsugana gaban Abba cikin girmamawa irin ta tsurkai ya yace. "Barka da dawo Abba." "Barka dai Mustapha ya hanya?." "Alhamudulallah Abba." "Masha Allah , taso ka isa daga ciki ko." Mik'ewa yayi cikin kunya tare da d'an murmushi a fuskar sa, gaban Hama Umar ya matso cikin sakin fuska ya mik'a mishi hannu. Shima Hamma Umar d'in d'an gajeren murmushi yayi tare da mik'o hannunshi suka gaisa. Abbanne ya kalli Hamma Umar d'in tare da cewa. "Farouq isar dashi parlour ciki." "Toh" yace sannan yayi gaba Mustapha na biye dashi a baya. Shi kuwa Abba part d'in shi ya nufa. Suna zuwa Umar ya kalli Mustapha a fakaice yace. "Ka isa ni zanyi cikin gida." "Toh nagode Hamma Umar Allah bar girma." "Amin" yace a tak'aice sannan ya fita , cikin gida ya wuce parlour Hajjajo ya nufa, yana zuwa yayi sallama jin shiru ba wanda ya amsa yasashi shigowa a hankali, parlour ba kowa, kan 2. str ya zauna tare da dan jingina jikin kujarar ido ya lumshe yana mai fidda numfashi a hankali, Hajjajo ce ta fito parlour hannun ta rik'e da carbi ido ta d'an zare tare da cewa. "Kai Umaru yashe ka shigo?." "Yanzu." ya bata amsa a gajarce, gefen shi taje ta zauna ta d'an kalleshi tare da tab'e baki tace. "Hmmm yau kuma halin ya motsone?." bai kulata ba sai zamewa yayi ya konta kan kujeran, ganin haka itama ta koma gefe ta zauna tana murmushi tana mamakin hali irin na Umar mutun ba'a gane inda ya dosa. A parlour Nenne kuwa Usman ne zaune yana kallon yadda Ummul ke zuba shek'i tayi kolliya mai kyau tayi shigarsu na shuwa'arab ta tubke gashinta tayi ras da ita riga da siket ne a jikin ta sunyi d'as gwanin shawa sai laffaya da ta yane jikin ta dashi har zuwa sama tayi irin yanawar da y'an mata sukeyi, ga wani irin k'amsi da take zubawa na turarukan humrarsu na shuwa, fuska ya d'an tab'e ya kalleta a d'an gyatsine yace. "Wai gasar kyau zaki je kike ta wannan kolliyar akan wannan Mustapha naki." Murmushi tayi tare da d'an juya ido ta d'an tsuke bakinta lips d'inta tad'an had'e tayi taku d'aya zuwa biyu tace. "Kai Ya Usman kaima da kanka kasan Mustapha da banne dole kuma komai nashi da banne." Fuska ya kuma tsukewa ya kalli Anty Halima dake ta nad'a mata laffayar yace. "Waike Halima me naki na zak'ewa kina shiryata kamar wata amarya." Murmushi tayi sannan ta kalli Usman cikin fara'a tace. "Ya Usman ai mace 'yar gyara ce." Ya Adam ne ya kalli Ummul d'in da Halima cikin harara yace. "Aiki ya same ku ai, ni wallahi sam Mustapha nan ba wani burgeni yake yiba kuma wallahi zan zuga su Abba a hanashi ma zuwa kawai ." Lokaci d'aya fuskar Ummul ta canza gaba d'aya annurin ta ya gimtse. Aliyu ne ya kalleta cikin tsokana yace. "Ummul in an hanaki shi zaki mutu ko? dan wallahi na lura jinshi kike kamar sarki." Harara ta cillawa Aliyu fuska a tsuke tace. "Mustapha yafi sarki a gareni shi shugaba zai zame min kuma shi tamkar jinina ne, shine bugun zuciya ta duk randa na ratsashi na rasa farin cikina." Ido Usman ya zuba mata yana mamakin yadda take son Mustapha, Halima ko murmushi kawai tayi , Ya Sadik ne ya kalleta a tsokone yace. "Kuma wallahi inaji a jikina bazaki auri Mustapha ba." Juyawa tayi tana fita tare da cewa. "Ashe ko duk wanda aka hanani Mustapha a dalilinshi toh tabbas yayi ban kwana da farin ciki a rayuwar sa zai fuskanci k'iyeyyar iya k'iyayya zai samu bak'in ciki mai isarsa." Tana kaiwa nan ta fice, Usman ne ya bita da sauri gaban ta ya tsaya cikin yin murmushi yace. "Koda ko d'an uwanki ne?." "Sosai ma ya Usman ko d'an uwa nane." K'irjinshi ya dafe cikin lumshe ido yace. "Koda ko nine ya Usman d'in ki?." Dariya tayi cikin lumshe ido tace. "Kai ai kai d'an uwa nane mai tayani son abin da nake so kai nasan bazaka zama silar bak'in cikina ba." Tana fad'in haka ta wuce ta tafi, shi ko Usman d'akin Hajjajo ya shiga yana murmushi gafen Hamma Umar d'in shi yaje ya zauna cikin sauk'e ajiyan zuciya yace. "Hamma yau kuma k'irjina yana min nauyi." Da sauri Hamma Umar ya mik'e tare da bud'e ido yana kallon Usman cikin tuhuma yace. "Me kaci? kashe maganin ka ?." Ido ya lumshe sannan yace . "Allah ko Hamma na ba abin da naci, maganin nedai ban shaba." Hannu yasa ya d'an bugi k'eyarsa cikin mik'ewa tsaye ya fice . Jim kad'an ya shigo hannushi rik'e da magungunan shi, bashi yayi yasha sannan ya kalleshi a hankali yace. "Jeka shirya kazo muje jama'a clinic na d'an dubaka sai mu biya, baba aura chemist na d'auko ma magungunan ka d'an sun kusa k'arewa." "Toh" yace sannan suka fito suka nufi part d'insu Usman ne ya fara wonka sannan yana fita Umar ya fitomai da kayan da zai saka, shima ya shiga yayi wonkan yana fitowa ya shirya tsab, shiga irin d'aya sukayi shigar shuwa'arab shigar da tafi kama da ta larabawa, sun fito ras tamkar tagwaye komai nasu irin d'aya hatta tafiyar su farar fatarsu sajen fuskarsu kamace ta sak da sak suke sun fito ras tamkar taurari sai shek'i da k'amshi suke zubawa, Suna fitowa Motar Umar suka shiga shi yake jan motar kai tsaye al'ameen restaurant suka nufa, suna zuwa suka shiga can ciki, lokaci d'aya aka had'a musu abinci dan sun saba zuwa wurin su maikatan har sunsan iya abincin da Usman ke iyaci so dama suna zuwa za'a kawo musu komai yadda ya kamata, kamar yaro Umar ya tasa Usman a gaba saida yaci yayi tik sannan ya biya komai suka fito, daga nan kuma clinic d'in suka wuce anan ya k'ara duba lafiyar d'an uwan nashi suna fitowa nan, kai tasaye katafaren chemist d'inshi suka wuce, ya had'a komai na maganin Usman d'in sannan, suna fita Umar ya sake jansu sai dicency super market , suna zuwa Umar ya had'e musu duk wani abin buk'atan su sannan aka loda musu a mota suka fito suka nufi gida. Ummul kuwa da Mustapha hirarsu sukayi sosai gaba d'aya sun susucewa juna hak'ik'a Mustapha yana son Ummul so na hak'ik'a haka itama take mishi so da iya gaskiyarta hirarsu suke basuma san maggariba tayiba saida suka ji kiran sallah, Mustaphanne ya kalleta cikin tarin so ido ya lumshe tare da sauk'e ajiyan zuciya murya can k'asa yace. "Ummul idanuna basa gajiya da ganin kekyawar fuskar ki! kunnuwana basa k'osawa da jin sautin ki mai zak'i ! hancina bayi da wani b'uri daya wuce shak'ar k'amshin ki, Ummul ina sonki son da bana yiwa kaina." Tafin hannun ta tasa ta rufe fuskar ta cikin jin dad'i da kunya tace. "Habeebi dani da murya ta da fuskarta da k'amshi na duk naka ne." Ido ya tsura mata tare da tasowa yazo gaban ta durk'usawa yayi a guiwowin shi a k'asa ido ya lumshe sannan ya bud'e su a hankali yace. "Ina jin tsoro Ummul inajin tsoron karna rasaki Ummul har yanzu baki zama tawaba gashi ban san yaushe Allah zai mallaka min keba ina sonki inason mu kasance ma'aurata Ummul kimin al'k'awarin duk rinsi kina tare dani ki min tattalin kanki kada idon wani namiji ya dira a kanki." Kallon shi tayi cikin murmushi tace. "Ako da yaushe ina shaida maka kai Habeebi da'iman ne a gareni zuciya ta ba inda wani zai samu ma tsuguni." Ajiyan zuciya ya sauk'e sannan ya mik'e yana kallon ta, itama mik'ewa tayi ta d'an matsa gefen shi, cikin sanyi tace. "Sai yaushe zaka kuma zuwa?." "Ko gobe in kina so zanzo, ina damaturu ina potiskum garin masoyi baya nida." "Gobe kam ai baka huta bama tukun." "Hutu kuma Ummul aini bani da wani hutu har sai na ganki cikin gida na." Murmushi tayi sannan tace, " toh muje kayi sallan maggariba sai ka tafi kar dare ya maka." "Kin gaji da ganina ne?." "Inko zangaji da kallon fuskar ka toh zan gaji da kallon tawa fuskar kenan." Murmushi yayi ya mik'a mata hannu wai suyi musabaha, kai ta sunkuyar a hankali tace. "Da saura." kai ya juya sannan ya had'e hannu a k'irjin yayi muryar tausayin yace. "Haka ne toh da wacce Kalmar za'a sallameni?." Juyawa tayi ta fara fita yana biye da ita a baya sunzo dai-dai inda zatayi cikin gida shiko zaiyi woje tace. "Laisa Lee misluka abadan ya habeebi. gareni bakada damka masoyina, ina sonka so mai tsananin Habeebi zanyi maka tattalin kaina dan cika zuciyar ka da farin ciki." Mustapha kam tamkar ya had'iye ta yakeji da tsabar k'aunar da da hali zai nuna mata sonta a fili amman ba dama, sai murmushi yayi tare da cewa. "Anti sururi, kece cikon farin cikina." Ya matsota zaiyi magana kenan yaga Hamma Umar dake zaune can gefen yana al'wala, haka yasa ya sallama ta, tayi cikin gida shiko yaje kusa da Hamma Umar d'in shima al'awalan yayi sannan suka tafi masallaci, ana idar da sallan suka nufi gida a bak'in gate Mustapha ya tsayai da Aliyu ya fito da manyan lododi guda biyu ya bawa Aliyun yace, ya kaiwa Ummul . Shi kuwa ya kama hanyar komawa damaturu A parlour suka baje tarkacen daya kawo mata kayan k'amshi ne sai atampopi guda 2 da les 2 sai shadda 2 sai yadukan laffaya masu kyau da taushi guda 3 , Anty Halima sai kallon Ummul take tana . "Iyeeh manyan masoya." Nenne kuma cewa tayi. "Maza Ummul had'e kayayya kin nan ki adana ko turaren bazaki fesaba." Fuska a marairaice tace. "Ayyah Nenne am kullum Mustapha ya kawo min abu sai ki hanani amfani dashi ban san me yasa ba ko kema bakya sonshi ne Nenne?." Murmushi Nenne tayi sannan tace. "Me yasa ina son Mustapha ai yaron kirki ne kawai dai wannan Al',adarmu ce budurwa bata amfani da kayan saurayi sai in sunyi aure, mu a gunmu in kiyi amfani da kayan saurayi kamar kasawa ce, toh kinga ke kuma ba abinda muka regeki dashi." Murmushi tayi ta tattara kayan, sannan suka ci gaba da hira, Abba da Umar da Usman dasu ya Adam kuma saida sukayi sallan ishah sannan suka dawo, suna shigowa su Usman sukayi parlour Nenne Hamma Umar kuma Abba ya kirashi suka tafi parlour Hajjajo, suna shiga suka samu Daddy ma yazo gun Hajjajon. Su Usman ko suna shiga, cikin halin girma Usman ya kalli Halima fuska a tsare yace. "Ke Sadiya har yanzu baki tafi ba?." Cikin girmamawa tace. "Ya Usman yanzu zan tafi." Mik'ewa yayi tare da cewa. "Muje in maida ki kinzo kin wuni bai kamata ki kai dare ba." Maza Ummul ta mik'e tare da cewa. "Yauwa ya Usman muje in rakaku." Kai ya gyad'a yace. "Oga Mustapha ya barki ne?." "Mustapha kuma ji ya Usman fa dama Mustapha ne ke hanani zuwa unguwa?." Juyawa yayi ya fita Sadiya na biye dashi a baya ita kuma Ummul tana gefen shi, kallon ta ya d'an yi sannan yace. "Keda ki kace Mustapha ya fimu matsayi." Murmushi tayi tare da rufe idon ta, shi kuma Sadiya ya kalla cikin murmushi yace. "Shiga baya kinsan Ummal da son zaman gaban mota kamar ba fullatana." Dariya sukayi sannan suka tafi. A parlour Hajjajo kuwa bayan su Abba sun d'anyi hira Abba yayi gyaran murya cikin kula ya kalli Daddy sannan ya kalli mahaifiyar su Hajjajo sai ya kuma kalli Hamma Umar cikin wani irin yanayi yace. "Farouq ina maganar aure da mukayi da kai?." Kai ya sunkuyar yayi shiru, ido Daddy ya tsura mishi tare da cewa. "Farouq shi fa aure dolene a gareka tunda Allah bai hanaka yadda zakayi ba, shin a zatonka munajin dad'in zaman ka hakan ne, Farouq ka sani duk girman mutun da darajarsa da matsayinsa matukar baiyi aure ba toh bai cika mutun ba." har lau dai baiyi magana ba sai sunkuyar da kai ya k'ara yi, a hankali Daddy yace. "Farouq me kake jira ne? da har yanzu baka fara maganar aure ba." Kanshi a sunkuye murya can k'asa a hankali yace. "Daddy ina jiran...... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 7⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *"Abba* ina jiran Usman ne." ido Abba da Daddy suka zuba mishi Hajjajo ko kai ta jinjina cikin mamaki tace. "Usman kana jiran Usman kuma? toh ka jirashi a kan me? me zakayi mishi da kake jiran shi?." shiru bai amsa mata ba bai kuma kalleta ba sai zaman shi da ya d'an gyara, juyowa gaban shi Abba yayi cikin son fahimtar sa yace. "Farouq! Usman kake jira? meyasa kake jiran shi d'in? ko so kake kuyi aure rana d'aya?." kanshi ya d'an d'ago cikin tok'k'oshi wuyanshi kan kafad'arsa cikin sanyi ya kalli Abba da Daddy murya a raunane yace. "Abba ina jiran Usman ne ! Abba inaso inga Usman ya samu mai kula dashi kafin nayi nesa dashi ! Abba in nayi aure yanzu wazai kula da Usman kaga baya son shan maganin shi kuma baya son bin dokokin doctors kuma kaga inba ana samishi idoba komai ya samu zaici, gashi ko yau saida yace min k'irjin shi na mishi nauyi." Sai kuma yayi shiru dan muryarsa da ta fara rawa, dan har cikin ranshi yake jin tausayin d'an uwanshi da yana da damar karb'awa Usman ciwon daya karb'a mishi. Abban ma shiru yayi tausayin 'yay'an d'an uwan nashi na ratsashi yana son Usman da Umar a ranshi fiye da yaran shi. Daddy ne ya d'an gyara zama cikin kallon Hajjajo da ta fara zubda k'ollah cikin k'arfin haki yace. "Farouq aure rahama ne meyasa kake ganin aure zai nesan taka da d'an uwanka Allah shike kula da Usman ba wayon mu ko dabararmu ba." Kai ya sunkuyar a hankali yace. "Daddy inajin tsoron barin Usman shi kad'ai dan baya son shan magani gashi dole dai in nayi aure zan koma cikin Damaturu da zama, Abba gashi bansan matar da zan auraba, gashi matan yanzu basa son dangin miji sai k'alilan ake samun masu son dangin mijin su, tayiwu nayi aure matar ta nuna bata son Usman yana rab'ata ko taga na fifita Usman a kanta har azo ta fara tunanin shiga tsaka nina da d'an uwana." Gaba d'aya parlour shiru sukayi cikin nazartan kalaman Hamma Umar tabbas matan yanzu k'alilan ke son dangin miji, kuma kamar yadda ya fad'a Usman tamkar yaro yake a gaban Umar, a hankali Abba yace. "Toh kai Farouq yanzu haka zakayi ta zama kenan?, ko dai auren ne baka so Farouq?." Kai ya jinjina cikin sanyin murya da tausayawa kanshi a hankali yace. "A,a Abba bawai auren ne bana soba! Abba ni bansan matar da zan aura bane , Abba ban san ya zanyi in samo matar da zata tayini kula da Usman ba." Sai ya kuma juyawa ya kalli Daddy da Hajjajo da take ta zubda k'ollah a hankali yace. "Ni da zan samu sai Usman yayi aure ya samu matar da zata kula dashi, in yaso daga nan sai na nemi auren, amman yanzu ina tsoron nayi aure nabar Usman gashi ni bansan ya zan fara neman auren bama bare na nemi wacce zata tayani kula da Usman." Gaba d'ayan su shiru suka yi kowa da tunanin dake ranshi. Cikin sanyi Abba yace. "Umar ba dai so kake ka auri matar da zata taya ka kula da Usman ba.?" Kai ya jinjina tare da murza yatsun hannun shi. Shiko Abba sai juyawa yayi ya fiskan ci d'an uwanshi Daddy kenan, Hajjajo kuwa shiru tayi cikin zurfin tunani... Su Ya Usman kuwa suna zuwa k'ofar gidan Anty Halima suka had'u da mijin ta zaije d'auko ta, ganin ya Usman ya dawo da ita suka gaisa, da mijin k'anwar tashi sannan suka juya shida Ummul suka nufi gida. Suna juyawa Ummul ta kalleshi cikin murmushi tace. "Yauwa ya Usman ya batun koyamin tuk'in ne? tun da muka fita sau 2 bamu kuma fitaba." Juyawa yayi ya d'an kalleta a fakaice yace. "Ke da kike da Mustapha ai shi zai koya miki." Baki ta d'an tura tare da cewa. "Wai ya Usman kaima ka tsani Mustapha ne kam? wai me yasa bakwa son bawan Allah nanne kam?." Baki ya d'an tab'e yace. "A,a Hajia ni bance ba, bance miki bana sonshi ba." "Toh ka koya min kaji ko Ya Usman na, Habeebi Katir katir." dariya yayi tare da cewa. "Allah ko Ummul kin rainani watoma Mustapha shine Habeebi da'iman ni kuwa Habeebi katir-katir na zama.?" murmushi tayi tare da cewa. "Ina sonka ya Usman dinnan." Murmushi yayi yace. "Allah d'aiyi ba." sai kuma sukaci gaba da dariya, suna cikin dariyar phone d'in Usman ya fara suwa a hankali yana d'agawa yaga Nuru ne, juyawa yayi ya kalli Ummul dake ta kiciniyar murza siterin motar tare da taima konshi, a hankali yace. "Ga lailamajanun yana kirana." Murmushi tayi tace . "Toh yauma zaku je zancen kenan?." Kai ya gyad'a mata tare da amsa kiran yana d'agawa Nuru yace. "Kai Gwanja ina kake ne? gani nazo gida Aliyu yace ka fita." Dariya yayi tare da cewa "Toh d'an anace naga jiya mafa kaje shine yauma zaka wani takura ni, toh yau nima na fara zuwa zance gani ga Baby na tana ta cemin, Ina sonka niko nace Allah d'ai yiba." Shiko Nuru tsaki yaja yace. "Kai da Allah ka same ni a k'ofar gidan su." "Toh" yace sannan ya katse kiran, hannu yasa ya d'an ture hannun Ummul dake kan nashi yana kallon titin yace. "Bari sai gobe zamu fita da rana zan koya miki yanzu muje in maida ke gida dan zanje gun Nuru inban jeba zaita damuna." "Toh tace sannan tace. " Ya Usman ina son fruits." Kai ya gyad'a sannan ya tsaya a gefen titin yaje ya saya mata sannan ya dawo suka tafi, a bak'in gate ya sauk'e ta da nufin zai juya, da sauri tace. "A a ya Usman zomuje na yanka maka fruits d'in kasha kafin ka tafi." "Ki bari sai na dawo." "A a wallahi ni dai kazo mu shiga inya so na gyara maka ka tafi dashi ko a cikin mota zaka ci." Binta yayi suka shiga cikin gida kai tsaye kitchen d'in Nenne suka shiga , gaban sink ta tsaya tare da wonke su tsab sannan ta jawo wata yar roba mai kyau ta zuba mishi, suna fitowa Aliyu ya kalli Ummul yace. "In anga kina kiciniya dai toh kinga kayan zak'ine, nanne za'aga k'wazon ki." "Eh d'in me ruwan ka da ni d'an sa ido kawai." Kitchen d'in ya shige yana cewa. "Uhum shazumami kawai kin iya shan zak'i kin iya yi mana kuka in cikin ki ya fara ciwo, kita b'are mana baki." Kanshi tayi da sauri zata kai mishi duka, shi ko zillewa yayi ya koma bayan Ya Adam dake harararta yace. "Ai gaskiya ce Aliyu ya fad'a kike wani fiffik'ewa ke zakiyi duka." Shi dai Ya Usman dariya yayi ya jawo hannun ta ya nufi parlour Hajjajo da ita yana cewa. "Ko Hamma Umar mai son kalota miki laifi bazaice fruits zai saki ciwon ciki ba, k'anwata sha abinki." ba tare da tunanin su Abba na cikan d'akin ba suka shiga tare da sallama. Suna shiga Hamma Umar ya d'ago kanshi fuska a tsuke ya d'an harari Ummul dake rik'e da Apple a hannun ta tana ci, baki ta tura tare da kauda kanta da sauri a ranta tana. "Mugu ko yaushe fuska a tsuke." Shi ko Usman cikin dariya yace. "Abba yau mitin kukeyi da Hajjajo da d'an jikinta a gefe ne." Kallon shi kawai su Abba sukayi zuk'atan su cike da alhinin irin son da Umar keyi mishi, shiko Usman ganin yadda suke zaune daga dukan alama magana mai mahimmanci sukeyi sai ya d'an zauna tare da gaida su, itako Ummul dama tuni ta fita ta tsaya a barandar ganin bai fito bane tace. "Ya Usman bari in kai maka robar cikin motar ko." "Toh muje nima gani nan zuwa." Juyawa tayi ta nufi harabar gidan nasu, shima yana gaida su ya fito yabi bayan ta, robar ta ajiye mishi sannan ta koma cikin gida, tana shiga Mustapha ya kira dan shaida mata ya isa lafiya, daga nan kuma sukaci gaba da hira, shi kuwa ya Usman wurin abokin shi Nuru ya nufa, A parlour hajjajo kuwa cikin zurfin tunani Abba yabi bayan Usman da kallo a hankali ya sauk'e ajiyan zuciya sannan ya kalli Hamma Umar cikin nitsuwa, shiko Hamma Umar kanshi ya sunkuyar, kai Abba ya juya ya fuskanci Daddy da Hajjajo ajiyar zuciya ya kumayi sannan cikin yanke hukunci yace. "D'an uwana Hussani da maifiyata Ku zama shaida a gareni na bada auren Ummul khairi ga d'an d'an uwana , na bada auren ta ga shi..... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 8⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Fans na fatan alkhairi a gareni baki d'aya ina mai Baku hak'uri kwana biyu zaku jini shiru sakama kon tafiyar da zanyi gobe zanyi tafiya YOLA 2 KANO kuma biki zani ba damar yin typing sai Allah ya dawo dani lafiya ina barar addu'arku gareni* *INA kuke masoyan yan gaskiya Firdausi Sodaggi tare da Hassana d'an larabawa Wannan shafi nakune INA al'fahari daku* *TABITAL FULAKU group GARKUWAR FULANI group AYSHA ALI GARKUWA fans GARKUWA AYSHA&UMMEE novels tare da BANDIRAWO fans kun zamoni na zamo Ku Kusani kab groups na inajin daku kamar yadda kuke ji dani bani da kamarku a duniyar gizo-gizo🤝😍😘* *"N*a bawa Umar auren Ummul khairi, ku sani na bashi auren ta na kuma yanke hukuncin za,ayi bikin nanda wani d'an lokoci domin aurar dasu ga juna shine mafita da zamu sama musu ." Daddy kam da Hajjajo kallon Abba sukeyi cikin jin dad'i Daddy sai murmushi yake yi ita kuwa Hajjajo kai take ta jinjina wa, gaba d'aya sai farin ciki ya cika zuk'atan su, Shi kuwa Hamma Umar tunda yaji furucin da Abba yayi, gaba d'aya yaji jikin shi na rawa gabb'an jikin shi kab kamar an sassare su, sai zufa yaji yana ketomai tako ina ido ya d'ago ya kalli iyayen nashi sai kuma atake yaji wata iriyar kunya mai tarin yawa ta rufeshi nauyin Abba yaji gaba d'aya ya kama shi, cikin tsananin kunya ya sunkuyar da kanshi k'asa yatsun hannushi ya rink'a murzawa tare da yin shiru sai bugun zuciyar shi da ya tsanan ta, Daddy ne ya kalli shi cikin kula yace. "Farouq kaji ta inda Allah ya kawo mana mafita ko?, tunda dama kai tunanin ka matar da zaka aura ta kasan ce mai tausayawa Usman ta taya ka kula dashi kar tazo ta rabaka da d'an uwanka, kaga a sauk'ak'e ita Ummul yar uwarsa ce kuma ko yanzu tana kula dashi." Shiru yayi bai d'ago ya kalli Daddy ba sai gyad'a mishi kai yakeyi, haka yasa Abba ya zuba mishi ido cikin kula yace. "Farouq." Shiru bai amsa ba sai gyad'a kai ya kumayi alamar amsawa, shima Abba kai ya jinjina tare da k'ara kiran shi a karo na uku yace. "Farouq." Jin Abban nata jerama mishi kiran yasa ya d'ago kanshi kad'an cikin raunin murya yace. "Na'am Abba." a hankali Abba yace. "Farouq d'ago kanka ka kalleni." Kai ya jinjina a hankali ya d'an kalli k'anin mahaifin nashi, sai ya kuma yin k'asa da idanun shi, kafad'an shi Abba ya dafa murya a tausashe yace. "Farouq kai da banne a cikin yaran mu kowa da halinsa kowa ana fahimtar ina ya dosa amman kai haka Allah ya halicce ka kana da zurfin ciki ba'a gane abin da kake so da abinda baka so kuma bakin ka baya furtawa, toh ka sani duk da haka bazan cutar da kaiba, dan kafin ka zama maraya mu muka zama marayu kuma d'an uwanmu Abbanka shi ya zame mana uwa da una bai regemu da komai ba yakan hak'ura da farin cikinsa dan ya sama mana farin ciki, haka zaisa Farouq bazan k'untata rayuwar kaba, yadda Ummul take y'ata haka kaima d'anane jininane ni da maifinka uwa d'aya uba d'aya Farouq ina sonka son da bana yiwa y'ay'an cikina, Farouq ni ubane a gareka kuma aboki kuma amini kuma mashawarci, Farouq bazan yimaka doleba sai da son ranka karkaji kunyar shaida min baka son Ummul in har baka sonta ka gaya min ,dan bazan yimaka auren cusheba bare na dole, ka furta min kana son Ummul? ko baka sonta?." Kai ya rink'a jujjuyawa yana sauk'e numfashi a ranshi yake juya kalaman Abba a fili kuwa cikin raunin murya yace. "A,a A,a Abba a,a ba kaina nake tunawa ba , Abba Ummul bata sona, ko cikin yayunta ni da ban ta d'aukeni kuma gashi tana da wanda take so, Abba me za'a cewa Mustapha? Ummul da Mustapha nake tunawa kar sanadi na a cutar dasu hakan zaisa Ummul ta k'ara tsanata bana son na zama bak'in jakada a Rayuwar Ummul da Mustapha." Sai kuma yayi shiru yana murza yatsun sa tare da kamo lips d'in shi na k'asa yana d'an ciza. Abba da Daddy kuwa ido suka zuba mishi yayin da Hajjajo kuwa gaba d'aya take kallon shi da suffar maihaifinshi , Umar Faruoq shi haka Allah yayi shi baya son shiga hakk'in kowa . Kai Abba ya jinjina sannan yace. "Farouq amsa min tabbaya ta, shin kana son Ummul ? ko baka sonta?." Kai ya k'ara sunkuyar wa cikin cushewar tunani a ranshi yake tuna. "Abba ya zanyi in kalli tsabar idanun ka nace bana son y'arka ta cikin ka?." A zahiri kuwa kai ya girgiza murya a raunane a hankali yace. "A,a Abba ya zanyi ink'i y'ar uwata." Nannauyan ajiyan zuciya Abba ya dire sannan ya kalli Daddy cikin jin k'arfin guiwa da kara yace. "Hussaini ina nemawa d'ana Umar Faruoq auren d'iyar mu Ummul." Murmushi Daddy yayi tare da yin hamdala yace. "Na bada auren Ummul ga d'ana Umar Faruoq." Hajjajo ko murmushi tayi da hamdala sannan ta sanya alkhairi a acikin abin, shi kuwa Hamma Umar kai ya d'ago a hankali yace. "Abba nagode Daddy Allah ya biyaku." Da sauri Abba yace . "A a Farouq godiya kuma a tsakanin mu ai nauyin mu ne mike sauk'e wa." Kai ya kuma sunkuyar wa murya a raunane yace . "Abba ya za'ayi da Mustapha? Abba me za'acewa Mustapha? Abba ya Ummul zata d'auke ni?." Gyara zama Daddy yayi sannan a nitse yace. "Farouq wannan magana bamu gaya maka itaba har saida mukaje muka samu iyayen Mustapha mu kayi misu bayanin Ummul zamu bada ita ga d'an uwanta, Alhamdulillah iyayen Mustapha masu mutun cine sun fahim cemu inda anan take suka kira Mustapha a gaban mu akayi mishi baya ni, tabbas Mustapha yana son Ummul kuma ita tana sonshi d'an Mustapha ya san haka d'an tunda mahaifinshi ya mishi bayani Mustapha kuka yake tamkar yaro, Amman kuma hakan bai hanashi ya fahimci abinda mik'e nufi ba, d'an haka yace , yaji kuma ya yarda amman don Allah kar a hanashi zuwa gun Ummul tunda ba'asan Rubutaccen AL'AMARI da zai wakana ba yace zaici gaba da neman ta in ita rebonshi ne zaka bar mishi ita, haka yasa yake zuwa gunta har yanzu kuma munce karya gaya mata yakuma yarda munkuma ce ya rege kiranta da zuwa duk ya yarda." Allah sarki Umar Faruoq mai sadaukar da farin cikin sa ga wani gaba d'aya sai yaji ya tsani kanshi dan yanaga ya shiga hurumin wasu ya tsaga soyeyyarsu, gaba d'aya jikin shi ya mutun a haka suka tashi taron su, Daddy ya tashi ya koma gidan sa shi kuwa Abba yayi part d'in sa a parlour shi ya samu Nenne tana zaune rik'e da carbi hankalin ta na kan tv tana kallon tashar sunnah tv, zama yayi gefen ta cikin sakin fuska da halin girma ya kalleta tare da cewa. "Khadija rege sautin tv nan akwai maganar da zamuyi." cikin girmamawa ta rege sautin sannan ta juyo gareshi cikin nitsuwa tace. "Fatan alkhairi." kai ya jinjina cikin girma da isa da gidan shi ya shaida mata yadda sukayi da y'an uwanshi kab. sannan ya d'ora da cewa. "Kinji hukuncin da muka yanke." shiru Nenne tayi cikin zulumin abinda zai biyo baya a hankali kamar cikin rashin fahimta tace. "Umar ko Usman?." cikin zuba mata ido yace "Umar dai ba Usman ba ko kina da magana ne?." Kai ta juya yayin da idanun ta sukayi tab da k'olloh cikin sanyi tace. "A a me zance ba komai sai fatan Allah ya sanya alkhairi Allah yasa sanadin haka zumunci ya k'ara k'arko." sai kuma tayi shiru sannan tace. "Lallai Mustapha yayi halin kirki, sai kuma ita Ummul." Cikin kula Abba yace. "Ummul kam ai dole tabi umurni na." Kai Nenne ta gyad'a tare da tarin zulumi. Daga nan sukaci gaba da hirar yadda bikin zai kasan ce. Shi kuwa Hamma Umar su Abba na fita ya koma kan 3 str ya konta yayi shiru tafin hannushi yasa ya rufe fuskar sa, gaba d'aya zuciyarshi ta cushe ta cika da tausayin Mustapha da Ummul shi kam gani yake tabbas ba'ayi musu adalci ba, d'aya rumtse idonshi sai ya rink'a ganin yadda Mustapha ke kallon Ummul zuwanshi na k'arshe, Hajjajo ce ta matso shi gefen shi ta zauna a hankali tace. "Umaruh Farouqu farin cikin ka iyayen ka ke bid'a shi yasa suka yanke wannan hukuncin da su sama maka dad'in rayuwa, ba k'inka sukeyi ba." ido ya d'an bud'e sannan yace . "Na sani basa nufin cutar dani." daga nan kuma ya mik'e jikin a mace yace. "sai da safe." "Allah bamu alkhairi." Part d'in su ya nufa yana zuwa ya samu Usman yana konce sanyi da 3qtr shi a jikin shi matso shi yayi a hankali ya kalli B'iyayen nashi ganin yayi bacci ne yajawo blanket ya rufeshi, sannan yayi addu'a ya shafa mishi sannan yaje yayi wonka yayi al'wala yazo suka konta.. A hankali Abba ya kammala shirye-shiryen auren Ummul da Umar hatta kayan d'akin Ummul Abba ya had'o mata a saudia ba abin daya rege, abin mamaki shi kam Hamma Umar daga ranan basu kuma maganar dasu Abban ba, Abin da ke bashi mamaki kuwa hatta kayan d'akin an kaishi gidan da yake zama a damaturu cikin gida jen ma'aikatan an shirya komai tsab ba abin da ya rege da bobu a gidan hatta kitchen d'in an shirya komai tsab. Ita ko Ummul duk abinda akeyi bata da labari, shak'uwa tsakanin Hamma Umar da Usman kuwa kullum k'aruwa yake Hamma Umar sam baya yarda ya kwana a damaturu yana tashi daga office nashi zai kama hanyar potiskum, Ummul da Mustapha kuwa suna soyewa son ransu shima Mustapha har manta maganar su Abba yakeyi wasu lokutan. Yau jumma tun da safe Ummul ta tashi da ciwon cikin da mararta kad'an-kad'an, haka yasa bata samu tayi aikin da Hamma Umar ya k'indaya mata ba, shi kuwa Umar Faruoq tun da sassafe ya shirya tsab shida Usman tea kawai suka d'an sha sannan suka fita a tare Usman ya nufi wurin aikin shi shima Hamma Umar ya nufi cikin damaturu, kasan cewar ya jumma'ace aikin ba yawa sosai. 11:00 Am kiran Adam ya shiga woyar Hamma Umar d'in, yana d'agowa yace. "Adam ya akayi ne?." "Yauwa Hamma Umar dama Abba ne ya aikoni da masu gyaran labulaye yace a canza labulayen toh munzo kuma baka gida gashi gidan a rufe." "OK gani nan zuwa yanzu ku jirani kad'an bari in k'arisa aikin dan tare zamu koma cikin potiskum d'in." "Toh" yace sannan suka koma cikin mota suka zauna. Jimawa k'adan Hamma Umar d'in ya iso ya bud'e musu gidan nashi suka shiga , a take su Abdul suka canza labulayen gidan kab sannan suka kimatsa komai suka shimfid'e carpet masu lau shi da taushi gaba d'aya gidan ya d'auki k'amshin da shek'i ga k'amshin sabon penti ga k'amshin sabbin kayan d'akin ga k'amshin kasan cewar Hamma Umar ma abocin tsabta da k'amshin ne komai yayi ras sai shek'i da k'amshin yake zubawa, shi kam Hamma Umar yana tunanin me Abba yake shirin yi tunda yasan har yau Ummul bata san da zancen ba haka dai ya bar abin a ranshi tunda shi bashi da yawan magana, su Abdul na gamawa suka d'auki hanya tare da Hmma Umar.. Suna zuwa gida sallan jumma'a suka tafi, Bayan an taso masallacin ne Dr Umar ya wuce chemist d'in shi, Abba kuwa da sauran gida suka dawo, Itako Ummul zuwa yanzu ciwon cikin ta ya fara tsananta, tana zaune a parlour Nenne tana d'an juya kai Aliyu ya shigo parlour kallon ta yayi cikin kula yace. "Sannu Anty Ummul ko inje in kira Hamma Umar ne?." a d'an wahalce ta harareshi tace. "Barni in mutun." Dariyan tsokana yayi sannan yace. "Kije Abba na kiran ki." Da sauri ta d'an zaro ido gami da dafe k'irji cikin tsoro tace. "Ni? da gaske Abba na kirana?." "Ehh wallahi da gaske ne, toh menene dan Abba ya kiraki ji yadda kike zaro ido." "A a wallahi Aliyu Abba baya kirana ko batun makaran ta ne Nenne yake gayawa ta gaya min, ni dai naji tsoron kiran nan nashi." "Toh koma dai menene kije maji daga baya." cewar Aliyu kenan. A bak'in kofar parlour Abban ta tsaya tare da yin sallama , Daddy ne ya amsa tare da cewa . "Ummul na shigo." Kai ta sunkuyar cikin jin tsoro ta shiga a hankali can gefen Daddy ta zauna yayin da zuciyarta ke luguje, a hankali ta gaida su, sannan tace. "Abba Aliyu yace kana kirana." Kallon ta yayi cikin k'aunar y'ar tashi a hankali yace. '"Ehh ina kiran ki." Sai kuma duk sukayi shiru, can dai Abba yayi gyaran murya tare da cewa. "Ummul ni wayene a gareki?." Kai ta d'ago cikin k'arin firgici a hankali tace. "Mahaifina." Kallon ta ya kumayi sannan yace. "A duniya bayan mahaifi yarki akwai wanda ya fini sonki?." Baki na rawa tace. "A,a babu." "Na tabbatar kina da sanin cewa shariya ta bani damar zab'a mik'a majin aure ko." "Ehh." ta bashi amsa hawaye na bin fuskarta. Shi kuwa gyaran murya yayi sannan yace . "Abin da ban saniba ko zaki iya min biyeyya kan zab'in da nayi miki." Zuwa yanzu kam ta k'asa magana sai kai take gyad'a wa tana wasa da yatsun ta. Cikin bada umurni Abba yace. " toh nayi miki miji, kiyi biyeyya a kanshi ko bana raye shine mijin ki, mahaifiyata da d'an uwana sune shaida, na bada auren ki ga d'an uwanki Umar Faruoq." Kalaman Abba sun maida Ummul kurma sun sata wani irin razani da firgici gaba d'aya jikin ta rawa yakeyi bugun zuciyar ta kuma kamar zai b'allo ya fito woje kunya yayi mata wani irin nauyi cikin rawan baki tace. "Hamma Umar Faruoq?." Kai Abba ya gyad'a mata tare da cewa. "Ehh shi d'in dai." Hannu tasa cikin tsoro ta kama kanta ta bud'e baki zatayi magana Abba ya dakatar da ita cikin tsuke fuska yace. "Tashi ki tafi bana buk'atar jin komai daga gareni ba shawara bace umurni nane wannan." Tanaji Abba na cewa tashi Amman ta k'asa ko d'aga yatsarta, sai da taji ya zuba mata tsawa, cikin firgici ta mik'e ta fita , tana fita kai tsaye part d'in Nenne ta ta nufa , tana zuwa a parlour ta samu su Ya Usman su ya Adam ya Sadik da Aliyu kai tsaye cikin bedroom ta shige, Usman na binta da kallon ganin yadda take a firgice. Tana zuwa ta zauna gefen Nenne dake kan sallaya cikin wani irin yanayin ta kifa kanta kan k'afafun Nenne cikin cushewar sauti ta saki wani irin galabaicen kuka mai cike da tausayi kuka takeyi mai tsuma zuciyar mai sauraro kukan take da sauti, Nenne kam tana ganin haka tasan me yasa ta kukan gaba d'aya sai zuciyarta ta cika da tausayawa y'ar tata, su Ya Usman kuma suna jin kukan da takeyi cikin sauri suka shigo d'akin , cikin tarin tausayawa Usman ya zauna gefen ta baki na rawa yace. "Ummul meke faruwa? meya sameki? meke miki ciwon?." Ba amsa sai kukan da takeyi, Nenne kuwa tsuke fuska tayi cikin fad'a tace. "Ke ni tashi a kaina tunda abin naki iskanci ne ana miki magana kina kukan banza bazan kiyi magana ba." Cikin kuka mai cushe zuciya ta d'ago kanta baki na rawa tace. "Wayyo Allah wayyo Nenne kiji abin da Abba yace min Nenne wallahi ina son Mustapha ina sonshi yana sona dan Allah Nenne ki bawa Abba hak'uri wallahi ina son Mustapha." Wani irin dogon tsaki ya Adam yaja cikin buga mata tsawa yace. "Ai Mustapha yafi miki kowa a duniya tunda har kike kuka da umurnin Abban mu, ni wallahi kin saman na k'ara tsanar sa." Juyowa tayi cikin kuka tace. "Ya Adam kasan da waye Abba zai had'a ni?". A hatsala yace. " Na sani mana kuma yafi Mustapha da komai." Cikin kad'uwa da bugawar zuciya Ya Usman ya kalleta tare da cewa. "Waye za'a had'a ki dashi?." Kuka ta saki tare da cewa. "Ya Usman waifa Abba da Hamma Umar zai had'a ni aure." Ido Usman ya zaro cikin wani irin yanayin yayi wani irin..... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* page 1⃣1⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Zan abbato mutanen sokkoto su y'an kwaraine basu da tsoggoma idan kaje ka sanya fad'a musu zasu rik'eka da kyau harda lallamah k'warai-k'warai na gane duniya mai sonka shike yi maka hiddima masoya na na sokkoto kun gaman gata gaisheku 🤝😍😘👍🏻🤝nakeyi domin kuke raba gardama👍🏻🤝 sokkotawa ina al'fahari daku domin baku da hassada a zuk'atan ku shiyasa na sadaukar da wannan shafi gareku sokkotawa🤝😘👍🏻* *Ha*nnushi ya tura kasan pillow dake gefen ta da niyar zai jawo laptop d'in shi daya bari a wurin, lalubawa yakeyi aman baiji inda laptop d'in yakeba dan d'akin yana da duhu gashi kan gadone mai rumfa duk yasha gyara da shimfid'a da labulaye sai ya k'ara duhun, Ita kuwa Ummul tana ganin shi dan ita ta dad'e a d'akin so duhun yabi idonta shi kuma yanzu ya shigo d'akin shiyasa yake ganin duhun sosai, tab'e fuska tayi cikin ko in kula tasa hannu ta turo laptop d'in nashi k'asa dai-dai sautin kan yatsunshi ta turo shi, shi ko da sauri ya sunkuya da nufin yasa hannu ya taro laptop d'in kar ya kai k'asa gudun karta lalace, amman ina cikin rashin sa'a ta fad'o kan yatsunshi tsinin aggil d'in jikin marfinta ya caki kan farcen babbar yatsarsa, cakar da a take farcen ya tsage lokaci d'aya jini ya fara zuba a take k'afar ta fara wani irin b'ari dan azabar daya ratsashi gaba d'aya yatsar kuma sai motsi take kamar zata fice a jikin shi, cikin wani irin azaba dayaji ya ziyarci k'ahon zuciyarshi ya dafe kanshi da k'arfi hannun shi sai rawa suke gaba d'aya jijiyoyin kanshi suka taso ida nunshi sukayi jazir ya kasa magana sai harshen shi ya d'an zaro ya rink'a d'an kad'awa yana furza numfashi tuni zufa ta keto mai ta sashoshin jikin sa, harshen yake d'an kad'awa yana fidda sautin. "Shihhhhhhhh ahhhhshhhhhh." Sai kuma k'afar tashi daya d'an d'ago yana yarfawa, Ita kuwa Ummul sai murmushi mugunta ta rink'a yi tanaji dariya nason kufce mata murmushin takeyi tuk'uru cikin jin dad'in azabtar dashi da tayi sai wani kad'a kai takeyi tana magana a ranta. "Kad'an ma kaji Hamma Umar wannan shine makullin wahalar da zakasha a hannun na, kaida azabtuwa kun kullah, Sai kayi kuka cur-cur da hawaye ka sai ka gommace kid'i da karatu sai ka sakeni saki mafi muni wanda zan haramta maka har sai inna nasake wani auren an sakeni." Kai ta jinjina taci gaba da maganar zuciyar da bata saniba na yanzun ya fito fili cewa take. "Tabbacin da nake dashi ko ince yak'ini na sani Mustapha bazai sakeni ba har Abadan zamu rayu tare." Da sauri Hamma Umar d'in ya bud'e idanun shi daya rumtse jin sautin Ummul d'in kan gadon ya tsurawa ido cikin wore idanun shi , fuskar ta ya tsare da ido cikin zafin nama ya mik'a hannushi kan gadon, ita kuwa ganin haka tayi wani irin dira daga kan gadon a guje tayi woje a parlour ta samu ya Usman da su Hajjajo da Inna tare da Anty Halima da Anty Shuwa k'anwar Nenne, cikin rawan jiki ta koma gefen ya Usman ta zauna cikin tura baki da tsuke fuska, Anty Halima ce ta kalleta cikin tuhuma tace. "Me kika aikata? kika fito a guje haka?." fuska ta k'ara tsukewa sannan ta kalli Anty Shuwa dake ta danna mata harara cikin son yin kuka tace. "Nayi ai ban sani bane." Hajjajo ta bud'e baki zatayi magana kenan sai kuma tayi shiru ganin Hamma Umar d'in d'aya fito cikin d'akin nata , tafiya yake yana d'ingisa k'afar tashi duk inda ya taka sai jini dake zuba gaba d'aya jijiyoyin kanshi sun taso kanshi a k'asa yake tafiya hannushi rik'e da laptop d'in nashi yayinda d'aya hannun kuma yake rik'e da iPhone d'in shi, Ya Usman ne da Anty Halima sukayi kanshi da sauri cikin rawan baki Ya Usman yace. "Hamma Umar me ya fasama yatsa yaushe ya fashe kalli yadda jiki ke zubafa." Anty Halima kuwa gaba d'aya jikin ta rawa yake ganin duk jini ya wonke mai k'afarsa cikin sanyi murya na rawa tace "Hamma Umar a tsaida jinin nan mana ya dena zuba." kai ya gyad'a musu cikin jarumta da dauriya ya nufi hanyar fita yana ce musu . "Ba komai fa." har yake bak'in k'ofar fita, Hajjajo da Inna sukayi kanshi da sauri cikin kula da tsananin k'aunar jikan nasu suka kalleshi, kusan a tare suke magana. "Kai Farouq me ya fasama k'afar? kayi magana kayi shiru ?." kai ya jinjina a hankali yace. "Tuntub'e nayi." fad'in haka da yayi ne yasa suka rink'a jeromai "sannu-sannu Amman kaji azaba kam ai abinda ya fasa farce ba k'ara min abu bane." Su tsoppin sun yarda Amman Anty Halima da Anty Shuwa kam sun gane sarai Ummul ce taji mai ciwon dan ganin yadda take zare ido da alamun rashin gaskiya Ita, kuwa Ummul har cikin ranta take jin dad'in ciwon da taji mishi, a wani sashin zuciyar ta kuwa tana mamakin yadda Hamma Umar d'in ya rufa mata asiri yak'i cewa Ita ta fasa mishi k'afar, dan ta tabbaya d'aya fad'a Ita kuwa da ta shiga 9 nema ba 3 ba. shi kuwa Hamma Umar ko inda take bai kallah ba ya fice yana d'ingisa k'afar, ya Usman kuwa karb'a laptop d'in Hamman nashi yayi ya rik'e cikin raunin fuskar sa kamar zaiyi kuka dan tausayawa d'an uwan nashi, har zasu fita ya juyo ya kalli Ummul d'in cikin raunin da yanayin tuhuma dan ya gane itace silar ciwon Hamman nashi, itama kallon shi takeyi cikin sanyi ta rumtse idonta, shi kuwa juyawa sukayi suka tafi. Suna zuwa part d'in su Hamm Umar d'in yayiwa yatsar tashi dressing sannan yawa kanshi allurar ya kuma sha magani. Ita kuwa Ummul suna fita Anty Shuwa da Anty Halima suka jata d'akin dake gefen na Hajjajo suka rink'a yi mata gyare-gyare tare da tsumata da irin tsumukansu na shuwa'arab , Anty Shuwa ce ta b'alle marfin wani roba sannan ta jijjiga tare da mik'ewa Ummul d'in cikin tsuke fuska tace. "Karb'a ki shanye yanzu ki bani robar." Kai Ummul d'in ta karya cikin kuka da gajiya da d'ure-d'uren da suke mata tace. "Ni dai amai nakeji dan Allah a barni hakanan." A fad'ace Anty Shuwa tace . "Sai kinsha muguwar banza yadda kike mishi mugunta haka zai rama kiji tsoron mutumin da baya magana inya tashi ramawa zaki yabbawa aya zakinta." kai Halima ta jinjina sannan tace . "Gaya mata dai Anty wallahi wata rana zakiyi nadama abinda kikewa Hamma Umar d'in." Haka suka rink'a yi mata fad'a da nasiha sunayi suna tsumata tare da dilketa da murjeta. Haka nan kullum Sai sun murjeta sun tsumata, ta fito tayi rasa sai wani shek'i take tamkar tarwad'a fatar jikinta kuma tamkar auduga komai nata yasha gyara sai wani k'amshin mai sanyi take fiddawa ko wucewa tayi k'amshin ta sai ya ratsa wurin gashin kanta kuwa ba'a maganar gyaran d'aya sha, an gyareshi gyara na mussamman k'afafun ta da hannayen ta kuwa an musu zanen Lalle na mu samman komai na Ummul ya fito rasa ta fito a shuwa'arab d'in sak. A gefen ago Hamma Umar kuwa , komai Ya Usman ne yake gudanarwa gaba d'aya ya gayyato abokon Hamma Umar d'in nashi ... Yau ta kama Jumma haji babbar rana Wanda ya kasance gobe asabar ne za'ayi d'aurin aure Ummul da Hamma Umar . Toh a rayuwar shuwa'arab akwai wata al'adar da sukeyi a duk lokacin da zasuyi bikin su , suna yin wannan al'adar tasune kamar gone za'a d'aura aure , kuma wannan al'adar tasu tana kunshe da wata al'adar kuwa Wanda a halin gaskiya a yanzu haka gaba d'aya shuwa'arab sunbar yin wannan al'adar ta biyun na farin dai sunyi Amman na biyun kam , a shuwa'arab d'in ma na zamanin yanzu da yawa basuma san al'adar ba dan tuni anbar yin al'adar duk da dai a zamanin da d'in ma a cikin aggwaye 100 da wuya a samu aggwaye 5 masu yin wannan al'adar domain al'adace mai nuni da d'auka alk'awari da kuma rik'o da amana suna kiran al'adar da sunan *Nad'in uwar gida* So shiyasa aggwayen yanzu basa wannan al'adar ta biyun kenan fa, Amman na farin kam har yanzu shuwa'arab sunyi kuma in an gama na farinne akeyin na biyun, so Yau jumma'a tun safe aketa shirin wannan al'adar tasu na. farin wanda dama asan dashi shi kuwa na biyu ba wanda yake da tabbacin za'ayishi a cikin shuwanma wasu basu san da wannan ba, tun safe aka k'afa tantuna a harabar gidan nasu aka shimfid'a kilisai na al'farma aka ajiye kujera na gani na fad'a kujera masu taushi gaba d'aya an zagaye wurin da kolliyoyin zamani tare dana al'adun shuwa'arab d'in, cikin kujerun kuwa a tsakiyar kujerun akwai na aggo da amarya wanda sunayen su ke rubuce a Kansu sai na k'awayen Amarya da abokin aggo suma duk sunayen su na rubuce akan kujerun nasu. Yadda ake al'adar tasu kuwa bayan an gama kimtsa wurin aggo zai fara zuwaya zauna da zugar abokan shi sai bayan ya zauna da mintuna kad'an sai a fito da amarya, fito da amaryarna kuma 'Yar uwar amaryar ce ta jini zata fito da amariyar rik'e da hannun ta , sai ta mik'a hannun amariyar ga hannun y'ar uwar aggo ko d'an uwan aggon, daga nan sai shiko d'an uwanshi ago yaja hannun Amarya ya kaita kusa da aggon ya ajiyeta, so y'an uwa da abokin arzik'i zasu tashi sunyi ta yiwa Amarya lik'in kud'i da gudumowowinsu, bayan duk an gama lik'inne sai shi kuwa aggo ya tashi yayi nashi lik'in, shike nan itace al'adar su ta farin . So haka aka tsaba wannan al'adar bayan an sauk'o sallan jumma'a Hamma Umar da abokanshi duk suka dawo gidan suka d'an huta sannan matayen su kuwa suna cikin gida , bayan anyi sallan la'asarne sannan aka fara shirin fita wurin taron, abokon Hamma Umar manyane masu cikar kamala abokai ne daku masu karatu kun sansu haka kuwa matayen su, haka sukayi shiga ta al'farma shiga irin ta shuwa'arab d'in sukayi baki d'ayan su suka fito rasa tamkar larabawa, Suma matayen su da k'awayen Amarya Ummul shiga sukayi ta shuwa'arab d'in gaba d'ayan su laffaya suka yane jikin su dashi suma dama gasu kyawawa. Haka yasa wurin taron ya zama tamkar a k'asar larabane , wani abin burgewa kuwa duk woni sak'o da luggu har cikin fulawowi na gidan an ajiye kaskon turaren wuta sai wani irin k'amshin ke tashi hakan yasa nishad'i a zuk'atan duk wani bani adam dake zaune a wurin. 5:00 pm zugar ago da abokanshi suka ido farfajiyar gidan Ya Usman ne a gaba yayinda sauran abokon ke binshi a baya , Hamma Umar kuwa yana tsakiyar su yasha sutura ta al'farma ya fito cikin haiba da cikar zati sajenshi sai wani irin shek'i yakeyi farar fatarshi ta fito ras tamkar balarabe sumar kanshi kuwa. yayi luf gwanin sha'awa ya murza hula a kan nashi yayinda gashin nashi yabi k'eyarshi da zagayen fuskar shi, idanun shi kuwa wani d'an siririn glass ne mai haske irin na Doctors ke manner a fuskar sa. dai-dai lokacin da suka fito a dai-dai lokacin kuma matayen abokan aggon suna suka fito , gaba d'aya wani taku suke a jere kamar yadda kujerun ke Jere kowa da matarsa a gefen Hamma Umar ne ya fara zama sai babban abokin shi , Hamma Yusuf da Ayshar sa sai Hamma Hassan da Fateemar shi sai kuma. Hamma Bashir da Ruk'ayyar shi Sai Hamma Mahmoud da Khadija shi sai kuma Hamma Aliyu Haydar tare da Minalin shi, A d'aya gefen kuwa wasu manyan abokan Hamma Umar d'in na gani da matayen su, Amadi da Nadiyar shi, sai Abuturrab da Batul d'in shi sai kuma Salim da Tawa Sai Abdullahi tare da Maryam d'in shi, daga gefen su kuwa Fauziyya ce da Al'ameen sai Aisar tare da Bintun shi sai kuma Abbah da Ruky pinkyn shi, ga kuma Ridwan da Zakiyya can kuma kusa dasu Ahmad Ana Muslim ne tare da khadijan shi sai kuma Assadiq da Safiyyar shi tare Hibbah da Faheem. Gaba d'aya sun zauna cikin nitsuwa da al'farma suna zaune cikin cikar haiba sun fito tamkar taurari sai shek'i sukeyi da wani irin k'amshin da suke zubawa zamane sukayi na masoyan gaske. Bayan sun zauna da kamar minti 5 Dangi da k'awayen Amarya da sauran mutane sukazo suka zauna, cikin nitsuwa da lumana, Jim kad'an, suka fara jiyo wani irin k'amshin na k'ara ratsa hancin su gaba d'aya sai wani irin shauk'i ya ziyar cesu ido suka lumshe tare da jin dad'in k'amshin dake k'ara bud'e su wanda Anty shuwace ke rik'e da kaskon turaren wuta, Anty Halima kuwa na biye da Ita a baya tana rik'e da hannun Ummul wacce tasha gyara iya gyara an yaneta cikin laffaya mai tsadar gaske ta fito a shuwa'arab d'in sak ta fito tamkar tauraruwar zarah dake kusa da wata, Anty Halima na rik'e da hannun ta suka iso farfajiyar gidan yayinda ita kuwa Ummul kanta ke sunkuye idanun ta na zubda wasu irin wahaye masu zafi da tafasa zuciya tafiya takeyi tamkar hawainiya, suna isowa Ya Usman ya mik'e cikin happy yaje gabansu ya tsaya cikin wani irin salon al'darsu ya d'an kife guiwarsa d'aya a k'asa sannan ya d'an d'ago hannunsh sama kad'an ya ware tafin hannushi cikin sanyi yace. "Halima samin hannun matar Hamma na cikin tafin hannuna ni zan kaiwa Hamman matarsa kusa dashi." murmushi Anty Halima tayi tare da kamo hannun Ummul d'in ta d'aura cikin tafin hannushi, wani irin nanauyan ajiyan zuciya ya sauk'e tare da rumtse idonshi da k'arfin, yatsun hannushi ya cusa cikin nata ya rik'o hannun ta sannan ya mik'e tsaye ya fara taku a hankali itama Ummul takun takeyi tamkar hawainiya a haka har suka isa gaban kujerar da zai zaunar da ita suna zuwa ya kamo kafad'unta ya juyota tana fuskantar shi yayinda ta bawa kujerar baya, cikin sanyi ya zaunar da Ita kan kujerar dake manne data Hamma Umar, a hankali ya fara tasowa daga sunkuye da yayi a kanta, Ita kuwa Ummul kanta ta kuma sunkuyarwa tare da sakin wani narkekken sautin kuka can k'asa, Sai kuma tayi shiru cikin sauri ta d'ago kanta tana kallon Ya Usman d'in nata jin kamar y'an watsa mata ruwa, abin mamaki da Ummul ta gani ba ruwan bane ya Usman ke watsa mata , Hawaye ne ke bin fuskar sa har yana diga cikin tafin hannun ta , ido ta zuba mai cikin yanayin tabbaya da tsantsar. mamaki a fuskar ta, shi kuwa cikin jarumta yasa tafin hannushi ya goge k'ollah dake zuba a idanun shi, murya na rawa yayi murmushin da yafi kuka k'una a zuciya murya can k'asa yace mata. "Allah ya d'aiyiba." itama murmushi tayi cikin zubda k'olloh murya a disashe tace. "Ya Usman ina son ka". ido ya lumshe da sauri cikin raunin murya yace. " Ummul nima ina sooonki." Ido Ummul kam ta kuma rumtsewa dan tasan ba haka suka saba cewa juna ba, Ita tasan in tace mai ya Usman ina sonka shiko sai yace Allah ya d'aiyiba Amman Yau kuma shima sai yace mata "Ummul nima ina sooonki " a madadin yace Allah ya d'aiyiba Sannan ga hawaye dake bin fuskarsa, tana cikin nazarin ne taji ya fara yi mata lik'in da Sabin kud'i na gudan dubu-dubu' gaba d'aya wuri aka fara tafi marok'a na . "Kaji k'anin aggo Usman d'an Maliki mai ruwan nare." lik'in sosai Ya Usman yayi mata yanayi yana zubda k'olloh cur-cur sai yasa tafin hannushi yana gogewa ganin haka yasa Ummul tayi murmushi cikin d'an d'aga murya kad'an yadda zai iya jinta tace. "Allah ya d'aiyiba min ya Usman dina." jin haka sai ya rink'a murmushi tare da kallon fuskar ta, a haka ya gama yi mata lik'in sannan Ya Adam da ya Sadik tare da Aliyu auta suma suka shigo sukayi mata lik'in , daga nan manyan abokan Aggo kuma jarumai suma suka fito sukayi lik'in ban girma, daga nan y'an uwa da abokan arzik'i sukayi nasu. lik'in, bayan duk an gama kowa ya koma mazaunin shi wuri yayi haske, cikin wani irin yanayi Hamma Umar d'in ya mik'e tare da juyowa gaban Ummul d'in sannan kanshi a sunkuye cikin sanyin muryar shi ya kalli marok'an yace. "Ku shaidawa Jama'a yanzu zanyiwa Ummul lik'in ne a matsayina, na babban Yayanta d'an uwanta." aiko a take marok'an nan suka rink'a shela suna fad'in. "Aggo yace a shaida muku yanzu zaiyi lik'in ga Amarya a matsayin shi na babban yayanta kuma d'an uwanta." gaba d'aya sai wuri ya ciki da shauk'i , abokan Hamma Umar da matan su sai murmushi suke, shi kuwa Hamma Umar lik'in kawai yake mata da rafa-rafa na dubu-dubu, haka ya rink'a zubawa Ummul kud'i tamkar ruwan sama, bayan ya gama ne sai ya kuma komawa kan kujera ya zauna, sannan k'awayen Amarya suka rink'a tattara kud'ad'en. Bayan sun gama ne Hamma Umar d'in ya sake tashi tsaye cikin cikar haiba da kamala gaban Ummul d'in ya kuma tsayawa cikin k'asaita yace. "Yanzu a matsayin aggo zanyi lik'in." marok'an ko tuni suka cika wurin da kirari suna. "Ummaru sand'a babuga mai nera Ummaru mai ado da zinari Ummaru Farouq mai K'amshin al'miski kunji Umaru Farouq babban adali doctor mai tausayi da jink'ai." Shi kuwa Hamma Umar Dolas ya zaro ya rink'a yiwa Ummul b'arinsu a kanta, Ya Usman kuma na tsaye a gefen shi rik'e da turaren mai suna *du'a'ul jannarh* mai tsananin k'amshin, bayan Hamma Umar ya gama lik'in sai ya kuma mik'a hannu ya karb'i turaren dake hannun Ya Usman, sannan ya d'an sunkuyo kan Ummul d'in ciki kallon fuskar ta ya fara fesa mata turaren yanayi yana k'ara matsota har ya isa gab da Ita sannan ya mik'ewa Usman turaren , a hankali ya rokk'fo gaban ta sannan ya sunkuye dai-dai kanta, mutanen wurin kuwa gaba dayasun maida hankalin su sukayi kan Hamma Umar d'in domin son ganin me zai aika ta, Hajjajo kuwa da Inna tuni sun fara mamakin abinda Umar d'in yake shirin aika tawa, sauran mutane kuma gaba d'aya kallon shi suke cikin tarin mamaki dan gano abinda yake shirin aika tawa, Ammin kuwa lokaci d'aya taji wasu siraran hawaye na bin fuskata tana kallon Abin da Babban d'an nata zaiyi, Abokan Hamma Umar kuwa ido suka zuba mai cikin mamaki su Hamma Yusuf duk an cika da mamaki sai k'ara rik'e hannun Ayshan sa yake. Itako Ummul gaba d'aya jikin ta sai kerma yake ido kawai ta zubawa Hamma Umar d'in fuskar ta cike da k'olloh, Nenne ma ido ta zuba mishi dan gano abinda zaiyi. Shi kuwa Hamma Umar cikin wani irin yanayi yasa hannushi ya cire hular kanshi sannan ya k'ara sunku yowa kan Ummul d'in tare da manna.... By *GARKUWAR FULANI*📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 9⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Alhamdulillah ala kulli halin nayi tafiya lfy na dawo lfy yanzu zanci gaba da typing insha Allah har k'arshe* ```NI na jinjina muku y'an KADUNA bamai rabani daku jama'ar KANO kui hak'uri ga shafinku ya iso mun jinjina muku reedars damu writers daku d'ayane bamai rabu daku sai Allah kui hak'uri ga pagenku ya fito kanawa sunce mini GARKUWAR a baya kinyi wani kuskure duk novels da kinkayi a social media dad'in su yayi ta kewaya nahiya sun shiga sak'ok'in Nigeria shin meyasa kika ware hausawa bakya yin novels da su sai FULANI? Hausawa ne sukayi min wannan tabbayar shaidar suna k'aunata gaba d'aya, NIKO NACE MUSU , dole naje duk inda rebo yake dan bani Rena masoya na kuma ban raina ranar da novel yayi mini ta sanadi an sannu garuruwa INA alfahari da Gombe Taraba ADAMAWA YOLA gida nake tun fari su sukayi mini GARKUWA😘 tunda nazo a cikin y'ay'an Adam duk ajizi an sanshi da kuskure kuyi hak'uri novelna na gaba da hausawa yana nan tafe, dan ni garin mosoya nisa bai mini da na fad'a kuma yanzu ina tuni Allah ya kaddara in zamto Zuma dana fito ai tayi mini sansani, yau hak'uri zan bawa hausawa dan sunfi so na tsaya tamkar gini, RABBI nufeni silar novel da zanyi mutan k'asarmu su zauna lfy, Forko mutan KANO zanai kira wanda fagen nema basa jira maza da mata Manya da k'ank'ana a gsky na sansu da Hattara sunce nazo naga yadda abin yake sannan na tabbaya ni sukayi jira na mori so da k'aunar da suke mini sannan sunce na dage fannin k'irk'ira🤝😘Kanawa wannan shafi naku ne``` *Y*ayi mata wani irin kallo cikin tarin mamaki da jin zafi a ranshi murya can k'asa yace. "Ummul duk wannan kukan kina yinshi ne dan an had'a auren ki da Hamma Umar? Ummul duk wannan zafi da tarin bak'in ciki dan an shigar da Hamma na cikin rayuwar ki ne kike haka?." Sai kuma yayi shiru tare da dafe k'ahon zuciyarshi a hankali cikin jin jiri ya koma baya kad'an ya zauna ido ya rumtse da k'arfi sannan ya jingina da jikin gini, numfashi ya rink'a furzarwa da sauri-sauri yana mai cushewar tunani. Ita kuwa Ummul cikin kuka tace. "Na tsaneshi na tsani Hamma Umar bana sonshi duniya da lahira ko fuskar sa bana k'aunar gani, Hamma Umar ba abinda yake jazamin a rayuwa sai bak'in ciki ya zame min bak'in jakada a rayuwa ta." K'ara ta saki da k'arfi tare da dafe fuskar ta jin wani irin zazzafan mari da ya Sadik ya zuba mata cikin huci da zafin rai ya nunata da yatsa murya a hargitse yace. "Ki kula kisan furucin da zakiyi ki san waye Hamma Umar wallahi a kanshi zamu iya miki komai, shi Mustapha ko tare kuka fito duniya bake ba shi." Kife kai Ummul tayi a bakin gado ta saki wani irin kuka mai cike da zafi a zuciya kuka mai cushe zuciya gaba d'aya jikin ta sai b'ari yake lokaci d'aya ciwon mararta da ciki da k'ugunta suka taso a tare, kuka take cikin tausayawa kanta da Mustapha. Gaba d'aya sukuwa shiru su kayi cikin jin sautin kukan ta, ya Usman ne yake tunani a ranshi tabbas Ummul akwai kuna a ranta akwai zafi da ciwon rabuwa da masoyi, sannan ga cushen mak'iyi da akayi mata, har cikin ranshi yake tausayawa mata, a sashin zuciyar shi kuwa, yana jin zafi da bak'in ciki da takaici yadda Ummul ta tsani d'an uwanshi mafi soyuwa a gareshi. Nenne kuwa itama shiru tayi tana jin sautin kukan y'ar tata har cikin ranta take tausayawa mata, amman a zahiri tafi jin dad'in auren Ummul da Umar akan ace da Mustapha dan ita Nenne tana son Umar da Usman tamkar yayanta na cikinta bata son abinda zai b'atawa Usman rai da yanayin ciwon sa bata k'aunar taga damuwa a fuskar Umar dan shi jigone mai burin samawa kowa farin ciki shi baya shiga sabgar daba tasaba, shi ba a gane matsalar sa dan ba fad'a zaiyi ba duk halin da yake ciki dan shi mutun ne mai kunya da zurfin ciki da kara da kawaici shiyasa bata son abinda zai cutar da Hamma Umar d'in, haka yasa take ji a ranta dole zata iya juya d'iyarta tayi mishi biyeyya. Ya Adam kuwa wata iriyar kunyace ta rufeshi ganin yadda a gaban Usman Ummul ke kuka kamar ranta zai fita dan an hada ta Aure da Hamma Umar, kunya yake ji ya Ummul zata nuna bata son d'an uwan shi alhalin shi a koda yaushe cikin nuna mata kulawa da gata yake. Ya Sadik har cikin ranshi yake jin tsanar Mustapha tunda a kan Mustapha ne Ummul take furta kalaman k'iyeyyar Hamma Umar d'in nasu haka kuma yake jin zai iya yiwa Ummul ko wanne hukuncin matuk'ar zatayi wa Hamma Umar d'in rashin da'a. Auta Aliyu kuwa abokin fad'in Ummul kuma kaninta mai tausayawa mata ganin yadda take kuka ba wanda yake lallashin ta gashi dama ya Usman ne mai kareta kuma yau shima fad'an ya shafeshi, kawai shima Aliyu sai hawaye yake zubda wa a hankali ya matso kusa da Ummul d'in murya na rawa yace. "Ayyah Anty Ummul kiyi hak'uri kibar yin kukan haka." Cikin tausayawa kanta da kanta ta fad'a jikin Aliyu kanta ta kife kan cinyar shi ta saki kuka mai cushewar sauti, shima Aliyu sai hawaye car-car yana jin tausayin ta a ranshi, cikin kuka tace. "Aliyu yau kowa baya sona duk an tsanani sabida Hamma Umar ! sannan an rabani da Mustapha sabida Hamma Umar ! Auta kalli yau ya Usman ma fushi yake yi dani sabida Hamma Umar! kalli ya Adam da ya Sadik ji suke kamar su kashe ni sabida Hamma Umar! Abban mu da Nenne duk basa sona a yau sabida Hamma Umar! Aliyu ba wanda ya tausayawa min sai kai." sai kuma ta saki wani sabon kuka. Ya Adam ne yayi kanta cikin nunata da yatsa murya a fad'ace yace. "Kifa dena cika mana kunne da kuka wallahi in ba hakaba zan tattakaki." Ya Sadik kuwa tsaki yaja cikin zuciya yace. "Kiyi duk yadda kika ga dama ya rege naki tunda bakya ganin alkhairi zab'in da iyayen mu suka yi miki, Mustapha ne dai bazamu bashi auren kiba." Daga nan suka fice ita kuwa Nenne tsaki taja ta fice ta shiga kitchen ta kama aikin ta, Aliyu kuwa tafin hannushi yasa yana gogewa Ummul d'in k'olloh dake bin fuskar ta, shi kuwa ya Usman zama yayi kusa da Ummul d'in daketa murk'ususu tana ta cike lips d'in ta zufa na keto mata tako ina sai kukan da takeyi cikin raunin da wahala. A hankali ya kalleta cikin sanyi ya d'an yi murmushi yace. "Ummul khairi banyi fushi da keba , ki sani ke tawace kamar yadda Hamma Umar yake nawa ni Usman Ku duk nawa ne ba Wanda zank'i a cikin Ku kiyi hak'uri k'anwata kiyiwa kanki da Hamma na addu'a Allah ya muku zab'in abinda yafi zamewa alkhairi a gare Ku." Kai kawai ta juya tana mai azabtuwa da ciwon cikin da tarin damuwa. Shi kuwa Usman haka yayi ta bata baki , Amman ina Ummul bata ma san yana yiba, ganin haka yasa. Usman ya fita kai tsaye parlour Hajjajo yaje, cikin sanyi yayi mata maganar abinda ke faruwa, kai ta d'an jinjina cikin k'arfin guiwa ta kalli Usman tace. "Ku kanta na d'an wani lokacin ne zatayi ta bari ta saduda ta zauna da Umaru cikin aminci, aini naji kukan nata zuwa ne bazan yiba, dan inta ga ana damuwa da kukan nata dayin lallashin ta toh bazata bariba ku fita sha'anin ta." Ido ya tsurawa Hajjajo cikin sanyi yace. "Hajjajo indai Hamma Umar na son wannan had'in toh ina farin ciki da auren nan domain farin ciki B'iyayen na shine nawa." Haka suka d'an tattauna kan zancen. Itako Ummul tunda suka waste suka barta take kuka kamar zata had'iyi zuciya ta mutu, Aliyu yayi ta lallashin ta amman ina dan abin ya had'e mata ga ciwon ga bak'in ciki, haka Aliyu sai ya fito yaje kitchen ya dawo gunta yana ta sintiri ya kasa zama. Haka har dere yayi Nenne kam ko ta kanta bata kuma biba dan inta tsaya kusa da ita tana jin tausayin d'iyar tata, ta dai sa abinci Aliyu ya kawo mata, ita kuwa Ummul yau abincin bazai ciwuba. 9:00 pm har yanzu Ummul tana kuka ne hannun ta dafe da mararta da k'ugunta akaro na biyu Aliyu ya shigo cikin tausayawa yace. "Ummul naje na gayawa Nenne baki da lafiya Abba kuma yace kije gun Hamma Umar ya duba ki." Kai ta kuma kifewa kan kago ta ci gaba da kukan da sautin shi baya fita dan muryar ta ta dashe, Ya Adam ne dake zaune a parlour Nenne jin Abinda Aliyu ya fad'a yasa shi mik'e wa ya shigo bedroom d'in cikin tsuke fuska da bada umurni yace. "Ke mike kije Hamma Umar d'in ya duba baki, kin zauna kin wuni kuka shin kukan zai miki magani ne? ki mik'e ko nace." Cikin kuka dabin umurnin mahaifin nata da Yayan nata da tsoron ya Adam d'in ta mik'e cikin wahala hannun ta damk'e da mararta ta fice tana kuka, kuma Ita da kanta ta san in Hamman ya mata Allurar tana jin sauk'i, cikin kukan ta nufi part d'in su Hamma Umar d'in. Shi kuwa Hamma Umar duk kukan da Ummul keyi yana ji dan lokacin da tafara kukan yana parlour Hajjajo jin kukan yayi yawane gashi yaji bala'in da su Adam ke mata yasa ya zame jikin shi ya dawo parlournsu cikin sanyi jiki ya konta kan kujera yasa tafin hannushi ya rufe fuskar sa, zuciyar shi cike da tausayin Ummul , yana koncen yaji sautin kukanta a hankali yana ratsa parlour cikin rawan murya yaji tana sallama, ido ya lumshe cikin jin zafin kukan da takeyi ga kunyar da ta rufeshi, a hankali ya amsa mata sallamar, Ita ko da zuwa yanzu ko tsawonta bata iya mik'ewa, a sunkuye ta shigo parlour hawaye cike a fuskar ta da tayi jazir da kuka ida nunta duk sun kumbura, a hankali ta durk'usa gaban kujerar da yake konce cikin kuka da rawan murya tace. "Abba yace inzo kamin al..! alluran da kake min." Shiru yayi zuciyar shi cike da tausayin ta gaba d'aya yake jin haushin kanshi tunda sana dinshi take irin wannan kukan. Ita kuwa ganin bai kulatan ba ta saki kuka mai cike da raunin gaba d'aya jikin ta rawa yakeyi, jin yadda take kukan ne ya mik'e cikin sanyi bedroom ya shige yana zuwa ya had'a allurar, sannan ya dawo parlour yana zuwa gabanta ya k'afa guiwowin shi a k'asa kan carpet suna fuskan tar juna, kanshi a sunkuye yasa hannushi ta bayan ta a hankali ya murza siket d'in atampa dake jikin ta, ita kam Ummul ido ta rumtse da k'arfi zuciyar ta cike da tsanarsa a ranta, fuskarta ya d'an kallah sannan ya zira bakin allurar a cikin jikin ta, k'ara ta saki cikin kuka da zafi ta fad'a jikin shi. Ido ya rumtse da k'arfi sannan yasa hannushi d'aya ya matso ta cikin sanyi da raunin murya yace. "Kar kiyi inji miki ciwon ki nitsuba ba zafi." kuka ta kuma fara cikin dashewar muryar, shi kuwa idoya lumshe sannan ya k'ara saita allura a hankali ya rink'a cusa ruwan a jikin ta, yanayi a hankali yana ce mata . "Sorry." Ita kuwa jin zafin yadda ruwan ke ratsata yasa ta ya matso shi ta rik'eshi gam, yana gamawa ya zare allurar sannan a hankali ya tureta baya ya janye jikin shi, ya mik'e kenan ya kalli Usman dake dafe da bak'in k'ofa ya zuba musu ido sai kallon suyake cikin wani irin yanayi. Ita kuwa yana tureta ta mik'e cikin jin jiri ta ratsa gefen ya Usman d'in ta wuce. Tana fita Hamma Umar ya kawo hannun Usman d'in cikin tsantsar kulawa , kan kujera ya ajiye shi sannan ya d'auki maganin shi yazo ya bashi yasha, a hankali yace. "Usman gobe zamuje gun Ammin mu." murmushi Usman yayi sannan yace. "Toh Allah ya kaimu." "Amin" yace sannan suka she ga bedroom d'in a tare sukayi shirin baccin su. Washe gari da safe bayan sun gama shirin su tsab sannan suka shiga cikin gida a parlour Nenne suka zauna bayan sun gaida Nenne suka fito parlour Hajjajo suka wuce suna zuwa Hamma Umar d'in ya shiga kitchen d'inta da niyar zai d'auki cup, Sai kuma yayi baya a hankali ya tsaya a bakin kofar yana jin abinda Ummul ke fad'a, ya Adam da Hajjajo dake bayan kitchen d'in ma suna jin abinda take fad'in ta window ita kuwa cikin sanyi taci gaba da cewa. "Nayi alk'awarin har Abadan..... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 🔟 *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *'Yan KADUNA duk Nisan da nayi musu Amman dani sai al'fahari suke in sunga novel na ko a fushi suke farin ciki gurbi nasa zai shige da zana jeni mu zauna so suke basu da niyar tsigen fiffige,💃🏻🤝😘 da gaskiya nunan k'auna suke dan sun kirani sunai mini magiya, na jinjina muku mutan Kaduna domin kuna da karamci hakan yasa na sadaukar da wannan page a gareku* *C*ikin kuka murya na rawa tace. "Habibi Mustapha nayi ma al'kawarin ni taka ce har Abadan bazan bari wani yayi nasarar rabamu ba, nayima alk'awarin zan adana maka kaina zan killace maka jikina ba wani mahaluk'in da zai zama hijabi a tsaka nin mu." Sai kuma tayi shiru tare da sheshshek'an kuka murya na rawa tace. "Hamma Umar zai rayu cikin bak'in cikin rayuwa tunda har ya kasance a sanadin shi za,a rabamu , bazai sake samun farin ciki da konciyar hankali ba gidan shi zai zame mai tamkar kurkuku zai rayu cikin k'unci da bank'in ciki ta yadda shida kanshi zai sauwa k'amin ba tare da neman shawarar kowa ba, Mustapha tun jiya duk wani tsoron Hamma Umar ya fita a raina na tsaneshi ji nake kamar na kashe sa." Sai kuma ta saki kuka mai sanyin sauti, shi kuwa Mustapha lallashin ta yake cikin raunin murya yake cewa. "Kiyi hak'uri Ummul ki daina kuka ki sani har Abadan kina cikin raina bazan dena sonki ba, amman kuwa duk yadda nake sonki bazan so sanadi na ki sab'awa iyayenki ba, Ummul kiyi biyeyya ga mahaifan ki." Cikin raunin tace. "Mustapha zanyi biyayya ga iyayena amman bazan yi biyeyya ga Hamma Umar ba zan d'and'awa zuciyarshi bak'in ciki mai tarin yawa sai yaji irin d'acin da ya jiyar dani, tabbas sai zuciyar shi ta raunatu jinin shi sai ya hau hankalin shi bazai sake konciya ba." Haka ta rink'a fad'in irin uk'uba da cin fuskar da ta tana darwa Hamma Umar d'in yana jinta, Hajjajo kuwa da ya Adam bushewa sukayi suna kallon juna cikin jin tsoron furucin Ummul d'in da mamakin yadda take k'ok'ari da niyar cusawa bawan Allah bak'in ciki. Shi kuwa Hamma Umar a hankali ya juya cikin sanyi fuskar sa a raunane lips d'in shi ya kamo ya ciza cikin jinjina kai ya juya ya fita, a parlour suka had'u da su ya Adam da Hajjajo cikin mamaki ya Adam ya kalleshi ganin daga kitchen d'in ya fito ita Hajjajo kallon shi take, shiko ganin kamar zasu zargi wani abu yasa ya d'an yi murmushi cikin yanayin sanyi ya gaida Hajjajo sannan ya kalli Usman dake tsaye gefen Hajjajo yana mik'a mata hannun shi da alamar ta d'aure mai agagon hannushi , Ita ko sai kiciniya take ta kasa, matso su yayi cikin sanyi ya matso ta ya d'an bugi k'eyar Usman cikin kula yace. "Kai komai baka iyaba agogo ma bazaka iya mak'alawa ba sai da taima kon tsohuwa." Murmushi yayi yace. "Toh Hamma Umar ai kaine ka b'atani haka komai kace bazan iyaba banda lafiya kai zaka min." Dariya sukayi baki d'aya shiko Umar murmushi yayi daga nan suka sallami Hajjajo suka fita suka tafi kai tsaye dicency super market suka wuce suna shiga suka yiwa Ammin su shopping komai na buk'atan rayuwa suka had'a mata kamar yadda suka saba, daga nan gidan su Ammin su suka nufa. Suna isa bakin gate ko parking Hamma Umar bai k'arisa yiba, Usman ya b'alle marfin motar cikin jin dad'i da raha ya d'an d'aga murya yana. "Ammi ! Ammina ! Ammiiiiii ! Ina kike ne?." Shi kuwa Hamma Umar murmushi yayi ya juya gun mai gadin ya mik'a mishi key d'in motarsa cikin sanyi yace. "Isah shigo da kayan cikin gida." cikin mutuntawa Isah ya karb'a, sannan shi kuma yabi bayan Usman d'in. Ita kuwa Ammi tunda tajiyo muryar Usman tayi wani irin murmushi mai cike da jin dad'i da k'aunar y'ay'an nata, ido ta lumshe tare da shak'ar kanshi turaren da ta sani na Hamma Umar ne, dan shi kafin ya isa wuri turarenshi keyin sallama. Kai ta jinjina tare da ture y'ar roban da ta k'wab'a lallen gargaji da nufin zatasa a k'afafun ta, tana k'ok'ari tashi taga Usman har ya iso, kawai sai ta koma ta zauna cikin yin dariya, cikin happy tace. "Lale marhabin da yaran kirki yara na gari y'an albarka abin alfaharin Ammin su." Da sauri ya k'arisa gaban ta cikin k'aunar mahaifiyar tasu ya zauna gaban ta , hannu ya mik'a mata itama hannu ta mik'a mishi sukayi musabaha, sannan ya zame gefen ta cikin lumshe ido da yana yin shogoba ya konta a hankali ya d'aura kanshi kan cinyarta tare da sauk'e ajiyan zuciya murya a tausashe yace, "Ammina ina sonki' Ammina munyi kewar ki." Kanshi ta shafa cikin kula da k'aunar irin ta uwa da d'anta tace. "Allah ya muku albarka." "Ameeen ya rabbi Habibi Ammin mu." Inna dake cikin d'akin ne ta fito jin muryan jikan nata da kuma k'amshin turaren babban jikan nata, cikin sauri ta fito, tana zuwa ta kalli Usman yadda yake zuba yarinta a gaban mahaifiyar tashi , dariya tayi sosai tace. "Shin wai kaika kam Usmanu baka ganin ka girma ne gankafa tsoho da kai." Kallon ta yayi cikin dariya yace. "D'a baya girma a gaban iyayen shi, na rasa d'umin jikin Abba na tun ina da shekara d'aya kinga ko dukda haka Hamma Umar na ya zame min madadin Abba na." Murmushi sukayi dukan su, dai-dai lokacin kuwa Hamma Umar yayi sallama cikin sanyi, fuska a sake Inna ta amsa mai gami da cewa. "Umaru sanda kafi mata yanga Umaru kafi k'arfin kabi mace sai dai ta bika Umaru sanda mai k'amshin al'miski Umar mai yawan kyauta da tausayi." Murmushi yayi cikin sanyi yace. "Bakya gajiya da surutu ne ke kam?." "Ya zanyi in gani ance ma kowa irin Kane mai tsadan magana." Kallon ta ya d'an yi cikin sanyi yace. "Allah ko Ammin Inna ce ta b'ata miki yaro da surutu kinga Usman ko duk surutun ta ya d'auka." "Ehh d'in na b'atashin." Shi kuwa Usman dariya kawai yake dan yasan dama za'a rina, itako Ammi murmushi kawai takeyi tana kallon fuskar d'an nata, shi kuwa Hamma Umar a hankalin ya matso gaban Ammin nashi cikin girmamawa da tsananin k'aunarta ya durk'usa a gabanta guiwa bibbiyu cikin sunkuyar da kai ya cire hular kanshi, ya k'ara matsota tare da sunkuyar da kanshi. a hankali Ammi ta d'ago hannun ta cikin sanyi ta dafe tsakiyar kan nashi sannan ta kalleshi cikin kula tace. "Allah yayi muku albarka rabbi ya karemin ku aduk inda kuke Allah ya tsare min imanin ku." a hankali ya d'ago hannayen shi duka biyu ya dafe hannun ta dake tsakiyar kanshi cikin sanyi yace. "Amin Amin Ameeen ya rabbil izzati , Ammi Allah ya kare mana ke." "Amin Amin" tace sannan ya koma ya zauna gabanta ya tonk'oshe k'afafun shi yana fuskantar ta, shi kuwa Usman yana konce kanshi na kan cinyarta shima yana fuskantar d'an uwan nashi. Wannan shine d'abi'a ko once al'adarsu Hamma Umar muddin suka zo gunta. Ita kuwa Inna sai murmushi take tana kallon d'iyar tata da yaranta, itako Ammi ajiyan zuciya ta sauk'e cikin sanyi tace. "Farouq ya jikin d'an uwanka?." kai ya d'an d'ago ya kalleta a hankali yace. "Ammi da sauk'i sai dai Usman sam baya son bin dokan likita komai ya samu ci yakeyi yayita d'ure-d'ure kuma yasan zuciyar sa nada rauni Ammi kiyi mishi fad'a bana son abinda zai cutar dashi." ya karishe maganar cikin raunin murya Hannu Ammi tasa ta kamo kunne Usman d'in cikin hukuntawa tace. "Baka ji ko?." k'ara ya d'an saki cikin d'an yarfa hannu yace. "Kai Ammi ninefa banda lafiyar amman kuma wai sai Hamma Umar zaki tabbaya ya jikina d'in, shiko ya fiye tsare-tsare." Dariya Inna tayi tace. "Baka dai ji shiyasa." .dai-dai lokacin yayan Ammin nasu ya shigo shima dariya yakeyi d'an yana matukar k'aunar yaran k'anwar tasu. Bayan sun gaggaisa ne, sukaci gaba da hira, Usman yana zaune gefen Ammin su yana bare banana yana mik'a mata tanaci inya bata d'aya sai ya kuma bawa Inna sannan ya mik'a wa kawun nasu pilet d'in, shi kuwa Hamma Umar zaune yake kusa da Ammin nashi yana rik'e da hannun ta yana yanke mata farce, abinda tunda Umar ya girma shike yanke mata farce, yakan shirya sam musamman dan yaje ya yanke mata farce kuma hakan shike yankewa Usman ma fartatunshi. Suna cikin hiran kawun nasu ya d'an yi gyaran murya cikin sanyi yace. "Umar kwana ki su Abban ku sunzo sun min baya nin batun auren ka da d'iyar Abban naki, mun tattauna maganar kuma yadda sukayi yayi dai-dai, toh shekara jiya sunzo sun shaida min asabar mai zuwa za'a d'aura auren sun kuma cemin sun gama komai za'a fara bikin nanda kwana 3 , toh Amman duk da sunce sun gama komai mukuwa mun had'a kayan lefen , yanzu haka Antyn ku sun tafi kai lefen ne shiyasa kukaji gidan shiru." Kai ya d'an d'ago ya kalli kawun nasu da Ammin shi sannan ya kalli Inna da Usman a hankali yace. "Dama nazone in shaida muku batun, ashe Abba har yazo." sai ya juya gun Ammin shi murya can k'asa yace. "Ammi ban nemi auren nan ba su Abba bani kawai sukayi shiyasa baki tab'a jin na miki zancen ba ko Usman ban gaya mishi ba dan nima a satin daya wucene suka gaya min, amman Ammi ya kika gani kina son abin ko a barshi?." Murmushi tayi tare da shafa kanshi cikin kula tace. "INA so Farouq ina al'fahari da wannan had'in fatana Allah ya baka ikon rik'e amanar da suka baka ka kular musu da d'iyarsu fiye da yadda suka kula da kai da d'an uwanka." Cikin rauni yace. "Insha Allah Ammi yadda kikace haka za'ayi." Shi kuwa Usman murmushi ya rink'a yi cikin jin dad'i da wani yanayin da zuciyarsa keyi ya kalli Hamma Umar d'in yace. "Ko zakayi zurfin ciki ga kowa a duniya ni ban canccanci kayi zurfin ciki a gareni ba." Kan Usman d'in ya dafa cikin sanyi yace. "Ba wani abu nawa wanda zan boye maka a duniya, Abba ne ya hanani in gayawa kowa shiyasa B'iyaye na ka gafar ceni." Rik'e hannu Hamman nashi yayi cikin happy yace. "A duniya zanyi fushi da kowa amman banda kai da Ammin mu ina farin ciki in nagan ka cikin farin ciki." Murmushi yayi sannan ya kalli kawun nashi cikin sanyi yace. "Kawun in nayi Aure zan d'auki Ammi na da Usman su koma gidana nima na samu ladan mahaifiya ta da k'anina." Kai kawun ya juya mishi alamar a,a sannan yace. "Banzan hanaka ba Umar amman kaga auren naku kamar auren cushene akayiwa yarinyar nan dan haka sai kaga ya yana yin zaman naku zai kasan ce." cikin sauri Ammi tace. "A duk inda kake kana samun ladana ni kam d'an uwanka kuma ai kaine jigonsa, nima zan kula da tawa mahaifiyar." Shiru kawai yayi dan shi kam a ranshi ya kudurta yana son mahaifiyar shi ta kasance kusa dasu. Daga nan sukaci gaba da hirarsu, haka suka wuni cikin farin ciki, sai dare suka tafi. A gida kula Ummul tunda matan su Kawun suka kawo kayan auren, yayin da su Mama matar Daddy da Anty Halima da k'annen Nenne suka tarbi bak'in Ummul ta shige d'akin Hajjajo ta rink'a wani irin kuka , haka ta wuni kuka baci ba sha ta k'aura cewa kowa ta k'aura cewa komai gani take duk ba masoyan ta bane . Haka tayi ta kuka har dare, Anty Halima ce ta shigo tare da Ya Usman cikin takaici tace. "Ummul kiji tsoron Allah ki tausayawa kanki yanzu wannan kukan maganin me zai miki?." Kuka ta k'ara sakewa cikin dashewar murya tace. "Anty kiji yadda Hamma Umar yake harkokin sa shi ko a jikin sa ni aka cusawa bak'in ciki, na tsani Hamma Umar bana sonshi ko a matsayin d'an uwa bare abokin rayuwa." Tsaki Anty Halima taja sannan ta juya ta fice tana cewa. "Tunda bakya jin magana kiyi duk yadda kike so, Aure ne dai saura kwana 6 nima daga gobe zanzo su Anty Shuwa kuwa suma gobe zasu zo dan su fara shirya ki." Tana kaiwa nan ta fice abinta, ita kuwa Ummul sai hawaye, Ya Usman ne ya matsota cikin sanyi yace. "Kiyi hak'uri kibar kukan Ummul kina soyamin zuciya da kukan ki, Ummul ko so kike zuciyata ta fashe." Shiru tayi cikin tausaya mishi baki na rawa tace. "Ya Usman kasha maganin ka." Murya a raunane yace. " ko nasha maganin ba zaiyi aiki ba in har baki bar kukan nan ba." Cikin tsoron halin da zai iya kasan cewa, tasa hannun ta share hawaye ta, murya na tace. "Nayi shiru ya Usman." "Toh" yace sannan ya kamo hannun ta suka fito parlour abinci ya bata ta d'an ci . Haka abu yake tafiya ba mai iya lallashin Ummul sai Usman kuma ba wanda take saurarawa sai shi bata cin abinci Sai in ya Usman d'in nata ne matsamata bata shiri da kowa sai shi shiko Usman shi kad'ai yasan cikin halin da yake rayuwa yana boye sirrinshi a zuciyar shi, abinda bamu saniba shin zuciyar Usman zata iya jurewa kuwa? . Yau talata tun da sassafe gidan su yake cike tib da bak'in haka yasa Ummul ta takure kanta cikin d'akin Hajjajo akan gadon ta mai rumfa, ko k'awayen ta tak'i su ganta, tana konce a hankali taji k'amshin turaren Hamma Umar d'in a take taji wani irin tsanarsa na ratsata, shi kuwa kai tsaye bak'in gadon ya nufa yana zuwa ya tura hannu shi a k'asan..... By *GARKUWAR FULANI* *RUBUTACCEN AL,AMARI* page 1⃣1⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Zan abbato mutanen sokkoto su y'an kwaraine basu da tsoggoma idan kaje ka sanya fad'a musu zasu rik'eka da kyau harda lallamah k'warai-k'warai na gane duniya mai sonka shike yi maka hiddima masoya na na sokkoto kun gaman gata gaisheku 🤝😍😘👍🏻🤝nakeyi domin kuke raba gardama👍🏻🤝 sokkotawa ina al'fahari daku domin baku da hassada a zuk'atan ku shiyasa na sadaukar da wannan shafi gareku sokkotawa🤝😘👍🏻* *Ha*nnushi ya tura kasan pillow dake gefen ta da niyar zai jawo laptop d'in shi daya bari a wurin, lalubawa yakeyi aman baiji inda laptop d'in yakeba dan d'akin yana da duhu gashi kan gadone mai rumfa duk yasha gyara da shimfid'a da labulaye sai ya k'ara duhun, Ita kuwa Ummul tana ganin shi dan ita ta dad'e a d'akin so duhun yabi idonta shi kuma yanzu ya shigo d'akin shiyasa yake ganin duhun sosai, tab'e fuska tayi cikin ko in kula tasa hannu ta turo laptop d'in nashi k'asa dai-dai sautin kan yatsunshi ta turo shi, shi ko da sauri ya sunkuya da nufin yasa hannu ya taro laptop d'in kar ya kai k'asa gudun karta lalace, amman ina cikin rashin sa'a ta fad'o kan yatsunshi tsinin aggil d'in jikin marfinta ya caki kan farcen babbar yatsarsa, cakar da a take farcen ya tsage lokaci d'aya jini ya fara zuba a take k'afar ta fara wani irin b'ari dan azabar daya ratsashi gaba d'aya yatsar kuma sai motsi take kamar zata fice a jikin shi, cikin wani irin azaba dayaji ya ziyarci k'ahon zuciyarshi ya dafe kanshi da k'arfi hannun shi sai rawa suke gaba d'aya jijiyoyin kanshi suka taso ida nunshi sukayi jazir ya kasa magana sai harshen shi ya d'an zaro ya rink'a d'an kad'awa yana furza numfashi tuni zufa ta keto mai ta sashoshin jikin sa, harshen yake d'an kad'awa yana fidda sautin. "Shihhhhhhhh ahhhhshhhhhh." Sai kuma k'afar tashi daya d'an d'ago yana yarfawa, Ita kuwa Ummul sai murmushi mugunta ta rink'a yi tanaji dariya nason kufce mata murmushin takeyi tuk'uru cikin jin dad'in azabtar dashi da tayi sai wani kad'a kai takeyi tana magana a ranta. "Kad'an ma kaji Hamma Umar wannan shine makullin wahalar da zakasha a hannun na, kaida azabtuwa kun kullah, Sai kayi kuka cur-cur da hawaye ka sai ka gommace kid'i da karatu sai ka sakeni saki mafi muni wanda zan haramta maka har sai inna nasake wani auren an sakeni." Kai ta jinjina taci gaba da maganar zuciyar da bata saniba na yanzun ya fito fili cewa take. "Tabbacin da nake dashi ko ince yak'ini na sani Mustapha bazai sakeni ba har Abadan zamu rayu tare." Da sauri Hamma Umar d'in ya bud'e idanun shi daya rumtse jin sautin Ummul d'in kan gadon ya tsurawa ido cikin wore idanun shi , fuskar ta ya tsare da ido cikin zafin nama ya mik'a hannushi kan gadon, ita kuwa ganin haka tayi wani irin dira daga kan gadon a guje tayi woje a parlour ta samu ya Usman da su Hajjajo da Inna tare da Anty Halima da Anty Shuwa k'anwar Nenne, cikin rawan jiki ta koma gefen ya Usman ta zauna cikin tura baki da tsuke fuska, Anty Halima ce ta kalleta cikin tuhuma tace. "Me kika aikata? kika fito a guje haka?." fuska ta k'ara tsukewa sannan ta kalli Anty Shuwa dake ta danna mata harara cikin son yin kuka tace. "Nayi ai ban sani bane." Hajjajo ta bud'e baki zatayi magana kenan sai kuma tayi shiru ganin Hamma Umar d'in d'aya fito cikin d'akin nata , tafiya yake yana d'ingisa k'afar tashi duk inda ya taka sai jini dake zuba gaba d'aya jijiyoyin kanshi sun taso kanshi a k'asa yake tafiya hannushi rik'e da laptop d'in nashi yayinda d'aya hannun kuma yake rik'e da iPhone d'in shi, Ya Usman ne da Anty Halima sukayi kanshi da sauri cikin rawan baki Ya Usman yace. "Hamma Umar me ya fasama yatsa yaushe ya fashe kalli yadda jiki ke zubafa." Anty Halima kuwa gaba d'aya jikin ta rawa yake ganin duk jini ya wonke mai k'afarsa cikin sanyi murya na rawa tace "Hamma Umar a tsaida jinin nan mana ya dena zuba." kai ya gyad'a musu cikin jarumta da dauriya ya nufi hanyar fita yana ce musu . "Ba komai fa." har yake bak'in k'ofar fita, Hajjajo da Inna sukayi kanshi da sauri cikin kula da tsananin k'aunar jikan nasu suka kalleshi, kusan a tare suke magana. "Kai Farouq me ya fasama k'afar? kayi magana kayi shiru ?." kai ya jinjina a hankali yace. "Tuntub'e nayi." fad'in haka da yayi ne yasa suka rink'a jeromai "sannu-sannu Amman kaji azaba kam ai abinda ya fasa farce ba k'ara min abu bane." Su tsoppin sun yarda Amman Anty Halima da Anty Shuwa kam sun gane sarai Ummul ce taji mai ciwon dan ganin yadda take zare ido da alamun rashin gaskiya Ita, kuwa Ummul har cikin ranta take jin dad'in ciwon da taji mishi, a wani sashin zuciyar ta kuwa tana mamakin yadda Hamma Umar d'in ya rufa mata asiri yak'i cewa Ita ta fasa mishi k'afar, dan ta tabbaya d'aya fad'a Ita kuwa da ta shiga 9 nema ba 3 ba. shi kuwa Hamma Umar ko inda take bai kallah ba ya fice yana d'ingisa k'afar, ya Usman kuwa karb'a laptop d'in Hamman nashi yayi ya rik'e cikin raunin fuskar sa kamar zaiyi kuka dan tausayawa d'an uwan nashi, har zasu fita ya juyo ya kalli Ummul d'in cikin raunin da yanayin tuhuma dan ya gane itace silar ciwon Hamman nashi, itama kallon shi takeyi cikin sanyi ta rumtse idonta, shi kuwa juyawa sukayi suka tafi. Suna zuwa part d'in su Hamm Umar d'in yayiwa yatsar tashi dressing sannan yawa kanshi allurar ya kuma sha magani. Ita kuwa Ummul suna fita Anty Shuwa da Anty Halima suka jata d'akin dake gefen na Hajjajo suka rink'a yi mata gyare-gyare tare da tsumata da irin tsumukansu na shuwa'arab , Anty Shuwa ce ta b'alle marfin wani roba sannan ta jijjiga tare da mik'ewa Ummul d'in cikin tsuke fuska tace. "Karb'a ki shanye yanzu ki bani robar." Kai Ummul d'in ta karya cikin kuka da gajiya da d'ure-d'uren da suke mata tace. "Ni dai amai nakeji dan Allah a barni hakanan." A fad'ace Anty Shuwa tace . "Sai kinsha muguwar banza yadda kike mishi mugunta haka zai rama kiji tsoron mutumin da baya magana inya tashi ramawa zaki yabbawa aya zakinta." kai Halima ta jinjina sannan tace . "Gaya mata dai Anty wallahi wata rana zakiyi nadama abinda kikewa Hamma Umar d'in." Haka suka rink'a yi mata fad'a da nasiha sunayi suna tsumata tare da dilketa da murjeta. Haka nan kullum Sai sun murjeta sun tsumata, ta fito tayi rasa sai wani shek'i take tamkar tarwad'a fatar jikinta kuma tamkar auduga komai nata yasha gyara sai wani k'amshin mai sanyi take fiddawa ko wucewa tayi k'amshin ta sai ya ratsa wurin gashin kanta kuwa ba'a maganar gyaran d'aya sha, an gyareshi gyara na mussamman k'afafun ta da hannayen ta kuwa an musu zanen Lalle na mu samman komai na Ummul ya fito rasa ta fito a shuwa'arab d'in sak. A gefen ago Hamma Umar kuwa , komai Ya Usman ne yake gudanarwa gaba d'aya ya gayyato abokon Hamma Umar d'in nashi ... Yau ta kama Jumma haji babbar rana Wanda ya kasance gobe asabar ne za'ayi d'aurin aure Ummul da Hamma Umar . Toh a rayuwar shuwa'arab akwai wata al'adar da sukeyi a duk lokacin da zasuyi bikin su , suna yin wannan al'adar tasune kamar gone za'a d'aura aure , kuma wannan al'adar tasu tana kunshe da wata al'adar kuwa Wanda a halin gaskiya a yanzu haka gaba d'aya shuwa'arab sunbar yin wannan al'adar ta biyun na farin dai sunyi Amman na biyun kam , a shuwa'arab d'in ma na zamanin yanzu da yawa basuma san al'adar ba dan tuni anbar yin al'adar duk da dai a zamanin da d'in ma a cikin aggwaye 100 da wuya a samu aggwaye 5 masu yin wannan al'adar domain al'adace mai nuni da d'auka alk'awari da kuma rik'o da amana suna kiran al'adar da sunan *Nad'in uwar gida* So shiyasa aggwayen yanzu basa wannan al'adar ta biyun kenan fa, Amman na farin kam har yanzu shuwa'arab sunyi kuma in an gama na farinne akeyin na biyun, so Yau jumma'a tun safe aketa shirin wannan al'adar tasu na. farin wanda dama asan dashi shi kuwa na biyu ba wanda yake da tabbacin za'ayishi a cikin shuwanma wasu basu san da wannan ba, tun safe aka k'afa tantuna a harabar gidan nasu aka shimfid'a kilisai na al'farma aka ajiye kujera na gani na fad'a kujera masu taushi gaba d'aya an zagaye wurin da kolliyoyin zamani tare dana al'adun shuwa'arab d'in, cikin kujerun kuwa a tsakiyar kujerun akwai na aggo da amarya wanda sunayen su ke rubuce a Kansu sai na k'awayen Amarya da abokin aggo suma duk sunayen su na rubuce akan kujerun nasu. Yadda ake al'adar tasu kuwa bayan an gama kimtsa wurin aggo zai fara zuwaya zauna da zugar abokan shi sai bayan ya zauna da mintuna kad'an sai a fito da amarya, fito da amaryarna kuma 'Yar uwar amaryar ce ta jini zata fito da amariyar rik'e da hannun ta , sai ta mik'a hannun amariyar ga hannun y'ar uwar aggo ko d'an uwan aggon, daga nan sai shiko d'an uwanshi ago yaja hannun Amarya ya kaita kusa da aggon ya ajiyeta, so y'an uwa da abokin arzik'i zasu tashi sunyi ta yiwa Amarya lik'in kud'i da gudumowowinsu, bayan duk an gama lik'inne sai shi kuwa aggo ya tashi yayi nashi lik'in, shike nan itace al'adar su ta farin . So haka aka tsaba wannan al'adar bayan an sauk'o sallan jumma'a Hamma Umar da abokanshi duk suka dawo gidan suka d'an huta sannan matayen su kuwa suna cikin gida , bayan anyi sallan la'asarne sannan aka fara shirin fita wurin taron, abokon Hamma Umar manyane masu cikar kamala abokai ne daku masu karatu kun sansu haka kuwa matayen su, haka sukayi shiga ta al'farma shiga irin ta shuwa'arab d'in sukayi baki d'ayan su suka fito rasa tamkar larabawa, Suma matayen su da k'awayen Amarya Ummul shiga sukayi ta shuwa'arab d'in gaba d'ayan su laffaya suka yane jikin su dashi suma dama gasu kyawawa. Haka yasa wurin taron ya zama tamkar a k'asar larabane , wani abin burgewa kuwa duk woni sak'o da luggu har cikin fulawowi na gidan an ajiye kaskon turaren wuta sai wani irin k'amshin ke tashi hakan yasa nishad'i a zuk'atan duk wani bani adam dake zaune a wurin. 5:00 pm zugar ago da abokanshi suka ido farfajiyar gidan Ya Usman ne a gaba yayinda sauran abokon ke binshi a baya , Hamma Umar kuwa yana tsakiyar su yasha sutura ta al'farma ya fito cikin haiba da cikar zati sajenshi sai wani irin shek'i yakeyi farar fatarshi ta fito ras tamkar balarabe sumar kanshi kuwa. yayi luf gwanin sha'awa ya murza hula a kan nashi yayinda gashin nashi yabi k'eyarshi da zagayen fuskar shi, idanun shi kuwa wani d'an siririn glass ne mai haske irin na Doctors ke manner a fuskar sa. dai-dai lokacin da suka fito a dai-dai lokacin kuma matayen abokan aggon suna suka fito , gaba d'aya wani taku suke a jere kamar yadda kujerun ke Jere kowa da matarsa a gefen Hamma Umar ne ya fara zama sai babban abokin shi , Hamma Yusuf da Ayshar sa sai Hamma Hassan da Fateemar shi sai kuma. Hamma Bashir da Ruk'ayyar shi Sai Hamma Mahmoud da Khadija shi sai kuma Hamma Aliyu Haydar tare da Minalin shi, A d'aya gefen kuwa wasu manyan abokan Hamma Umar d'in na gani da matayen su, Amadi da Nadiyar shi, sai Abuturrab da Batul d'in shi sai kuma Salim da Tawa Sai Abdullahi tare da Maryam d'in shi, daga gefen su kuwa Fauziyya ce da Al'ameen sai Aisar tare da Bintun shi sai kuma Abbah da Ruky pinkyn shi, ga kuma Ridwan da Zakiyya can kuma kusa dasu Ahmad Ana Muslim ne tare da khadijan shi sai kuma Assadiq da Safiyyar shi tare Hibbah da Faheem. Gaba d'aya sun zauna cikin nitsuwa da al'farma suna zaune cikin cikar haiba sun fito tamkar taurari sai shek'i sukeyi da wani irin k'amshin da suke zubawa zamane sukayi na masoyan gaske. Bayan sun zauna da kamar minti 5 Dangi da k'awayen Amarya da sauran mutane sukazo suka zauna, cikin nitsuwa da lumana, Jim kad'an, suka fara jiyo wani irin k'amshin na k'ara ratsa hancin su gaba d'aya sai wani irin shauk'i ya ziyar cesu ido suka lumshe tare da jin dad'in k'amshin dake k'ara bud'e su wanda Anty shuwace ke rik'e da kaskon turaren wuta, Anty Halima kuwa na biye da Ita a baya tana rik'e da hannun Ummul wacce tasha gyara iya gyara an yaneta cikin laffaya mai tsadar gaske ta fito a shuwa'arab d'in sak ta fito tamkar tauraruwar zarah dake kusa da wata, Anty Halima na rik'e da hannun ta suka iso farfajiyar gidan yayinda ita kuwa Ummul kanta ke sunkuye idanun ta na zubda wasu irin wahaye masu zafi da tafasa zuciya tafiya takeyi tamkar hawainiya, suna isowa Ya Usman ya mik'e cikin happy yaje gabansu ya tsaya cikin wani irin salon al'darsu ya d'an kife guiwarsa d'aya a k'asa sannan ya d'an d'ago hannunsh sama kad'an ya ware tafin hannushi cikin sanyi yace. "Halima samin hannun matar Hamma na cikin tafin hannuna ni zan kaiwa Hamman matarsa kusa dashi." murmushi Anty Halima tayi tare da kamo hannun Ummul d'in ta d'aura cikin tafin hannushi, wani irin nanauyan ajiyan zuciya ya sauk'e tare da rumtse idonshi da k'arfin, yatsun hannushi ya cusa cikin nata ya rik'o hannun ta sannan ya mik'e tsaye ya fara taku a hankali itama Ummul takun takeyi tamkar hawainiya a haka har suka isa gaban kujerar da zai zaunar da ita suna zuwa ya kamo kafad'unta ya juyota tana fuskantar shi yayinda ta bawa kujerar baya, cikin sanyi ya zaunar da Ita kan kujerar dake manne data Hamma Umar, a hankali ya fara tasowa daga sunkuye da yayi a kanta, Ita kuwa Ummul kanta ta kuma sunkuyarwa tare da sakin wani narkekken sautin kuka can k'asa, Sai kuma tayi shiru cikin sauri ta d'ago kanta tana kallon Ya Usman d'in nata jin kamar y'an watsa mata ruwa, abin mamaki da Ummul ta gani ba ruwan bane ya Usman ke watsa mata , Hawaye ne ke bin fuskar sa har yana diga cikin tafin hannun ta , ido ta zuba mai cikin yanayin tabbaya da tsantsar. mamaki a fuskar ta, shi kuwa cikin jarumta yasa tafin hannushi ya goge k'ollah dake zuba a idanun shi, murya na rawa yayi murmushin da yafi kuka k'una a zuciya murya can k'asa yace mata. "Allah ya d'aiyiba." itama murmushi tayi cikin zubda k'olloh murya a disashe tace. "Ya Usman ina son ka". ido ya lumshe da sauri cikin raunin murya yace. " Ummul nima ina sooonki." Ido Ummul kam ta kuma rumtsewa dan tasan ba haka suka saba cewa juna ba, Ita tasan in tace mai ya Usman ina sonka shiko sai yace Allah ya d'aiyiba Amman Yau kuma shima sai yace mata "Ummul nima ina sooonki " a madadin yace Allah ya d'aiyiba Sannan ga hawaye dake bin fuskarsa, tana cikin nazarin ne taji ya fara yi mata lik'in da Sabin kud'i na gudan dubu-dubu' gaba d'aya wuri aka fara tafi marok'a na . "Kaji k'anin aggo Usman d'an Maliki mai ruwan nare." lik'in sosai Ya Usman yayi mata yanayi yana zubda k'olloh cur-cur sai yasa tafin hannushi yana gogewa ganin haka yasa Ummul tayi murmushi cikin d'an d'aga murya kad'an yadda zai iya jinta tace. "Allah ya d'aiyiba min ya Usman dina." jin haka sai ya rink'a murmushi tare da kallon fuskar ta, a haka ya gama yi mata lik'in sannan Ya Adam da ya Sadik tare da Aliyu auta suma suka shigo sukayi mata lik'in , daga nan manyan abokan Aggo kuma jarumai suma suka fito sukayi lik'in ban girma, daga nan y'an uwa da abokan arzik'i sukayi nasu. lik'in, bayan duk an gama kowa ya koma mazaunin shi wuri yayi haske, cikin wani irin yanayi Hamma Umar d'in ya mik'e tare da juyowa gaban Ummul d'in sannan kanshi a sunkuye cikin sanyin muryar shi ya kalli marok'an yace. "Ku shaidawa Jama'a yanzu zanyiwa Ummul lik'in ne a matsayina, na babban Yayanta d'an uwanta." aiko a take marok'an nan suka rink'a shela suna fad'in. "Aggo yace a shaida muku yanzu zaiyi lik'in ga Amarya a matsayin shi na babban yayanta kuma d'an uwanta." gaba d'aya sai wuri ya ciki da shauk'i , abokan Hamma Umar da matan su sai murmushi suke, shi kuwa Hamma Umar lik'in kawai yake mata da rafa-rafa na dubu-dubu, haka ya rink'a zubawa Ummul kud'i tamkar ruwan sama, bayan ya gama ne sai ya kuma komawa kan kujera ya zauna, sannan k'awayen Amarya suka rink'a tattara kud'ad'en. Bayan sun gama ne Hamma Umar d'in ya sake tashi tsaye cikin cikar haiba da kamala gaban Ummul d'in ya kuma tsayawa cikin k'asaita yace. "Yanzu a matsayin aggo zanyi lik'in." marok'an ko tuni suka cika wurin da kirari suna. "Ummaru sand'a babuga mai nera Ummaru mai ado da zinari Ummaru Farouq mai K'amshin al'miski kunji Umaru Farouq babban adali doctor mai tausayi da jink'ai." Shi kuwa Hamma Umar Dolas ya zaro ya rink'a yiwa Ummul b'arinsu a kanta, Ya Usman kuma na tsaye a gefen shi rik'e da turaren mai suna *du'a'ul jannarh* mai tsananin k'amshin, bayan Hamma Umar ya gama lik'in sai ya kuma mik'a hannu ya karb'i turaren dake hannun Ya Usman, sannan ya d'an sunkuyo kan Ummul d'in ciki kallon fuskar ta ya fara fesa mata turaren yanayi yana k'ara matsota har ya isa gab da Ita sannan ya mik'ewa Usman turaren , a hankali ya rokk'fo gaban ta sannan ya sunkuye dai-dai kanta, mutanen wurin kuwa gaba dayasun maida hankalin su sukayi kan Hamma Umar d'in domin son ganin me zai aika ta, Hajjajo kuwa da Inna tuni sun fara mamakin abinda Umar d'in yake shirin aika tawa, sauran mutane kuma gaba d'aya kallon shi suke cikin tarin mamaki dan gano abinda yake shirin aika tawa, Ammin kuwa lokaci d'aya taji wasu siraran hawaye na bin fuskata tana kallon Abin da Babban d'an nata zaiyi, Abokan Hamma Umar kuwa ido suka zuba mai cikin mamaki su Hamma Yusuf duk an cika da mamaki sai k'ara rik'e hannun Ayshan sa yake. Itako Ummul gaba d'aya jikin ta sai kerma yake ido kawai ta zubawa Hamma Umar d'in fuskar ta cike da k'olloh, Nenne ma ido ta zuba mishi dan gano abinda zaiyi. Shi kuwa Hamma Umar cikin wani irin yanayi yasa hannushi ya cire hular kanshi sannan ya k'ara sunku yowa kan Ummul d'in tare da manna.... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1⃣2⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *H*ularshi ya cire daga kanshi sannan ya kuma sunkuyowa kanta, yayin da gaba d'aya mutanen wurin kuwa suka zuba mai idanu, shi kuwa Hamma Umar kanshi a sunkuye cikin lumshe ido ya manna mata hular tashi a kanta sannan yasa hannu biyu ya dai-dai ta zaman hular a kan Ummul d'in hular tayi ras, ita ko Ummul ido ta zaro cikin tarin firgici gano cewa Hamma Umar al'adarsu ta biyun zaiyi a take zuciyarta ta rink'a buga wa a saba'in, Ammin shi kuwa sai murmushi take a ranta tana al'fahari da d'an nata, Abokan Hamma Umar kuwa kallon shi suke cikin sha'awa da burgewa, Ya Usman kuwa k'irjin shi ya dafe da k'arfi sannan yasa hannun shi d'aya ya damk'o hannun abokin shi Nuru dake zaune kusa dashi a sashin zuciyar sa kuwa yana al'fahari da hallaci irin na Hamma Umar d'in nashi yana jin dad'in yadda a gaban dubban al'ummah zaiyi al'k'awarin da d'aukar amana, Shi kuwa Hamma Umar bayan ya gyara zaman hulan nashi a kanta sai ya kuma sa yatsunsa biyu ya zaro siririn gilashin dake manne a fuskarsa cikin lumshe ido ya kuma mannawa Ummul gilashin tare da ajiyeshi ras a fuskarta , ita ko Ummul zuwa yanzu hawayen ta tuni suke d'iga kan tafin hannun ta tol-tol, ganin haka yasa cikin furza sassauk'an numfashi Hamma Umar d'in ya d'an rok'k'ofo ya zauna gabanta suna fuskantar juna zama yayi dirsham a gabanta ya tok'k'oshe k'afafun shi sannan ya had'e guiwowin sa, A hankali ya sunkuyo kanshi yana kallon k'afafun ta da su kasha zane , hannun shi yasa a hankali ya d'ago k'afafun nata sannan ya zare takal manta ya ajiye gefe cikin kula ya tallab'o k'afafun nata da tafin hannun shi cikin tabbacin abinda zaiyi ya d'ago k'afafun nata ya diresu kan guiwowin shi sannan ya had'a yatsun k'afafun ya rik'e yana d'an matsawa kamar mayi mata tausa sai kuma ya sunkuyar da kanshi cikin yanayin bugawar zuciya dan tabbas yasan hakan da yayi d'aukan babban al'k'awarine firgincin dake ranshi shin ko zai iya cika al'k'awarin da ya d'auka?, mutanen wurin kuwa gaba d'aya aka kaure da tafi maroka na gud'a cikin yin kirari ga aggo Umar Farouq, dan ba wanda yayi tunanin Hamma Umar zaiyi wannan abun, Hajjajo kuwa hamadala ta rinkayi cikin jin dad'i Inna kuwa sai k'ollah dake bin fuskata a fili tace. "Farouq na Allah Umar Farouq adon gari Farouq mai zuciyar taimako Allah ya baka ikon cika wannan al'k'awarin da ka daukarwa kanka." Anty Halima kuwa da Anty Shuwa farin cikin su baya fad'uwa ita kuwa Nenne kuka takeyi sosai a ranta tana ganin al'barkacin sune ita da Abba Ummul ta samu wannan karramawar a gun Hamma Umar d'in, Matar yayan Ammin Anty Nafeesat ce ta kalli Hajjajo dake gefen ta cikin mamaki tace. " Hajjajo me Wannan abinda Umar yayi yake nufi?." Murmushi Hajjajo tayi cikin al'fahari da jikan nata, ta kalli Anty Nafeesat tace. "Anty Nafeesat Wannan abin da Farouq yayi shi muke kira da nad'in uwar gida sannan mutu ka raba , Anty Nafeesat wannan abin da yayi d'aukar al'k'awarine mai k'arfin gaske na rik'e mace da amana da gaskiya." Numfa sawa Hajjajo tayi tare da ciga da cewa. "Anty Nafeesat idan namiji yayi wannan abin toh ya d'aukarwa kansa indan zai kashewa kansa dubu 50 toh zai kashewa matarsa dubu 100 ninkin ba nashi kenan kuma ba abinda zaici ba tare d'aya ciyar da matarsa ba kodako tsagin dabino ne sannan ya bata matsayin sarauniya shin ki kalli yadda yake zaune a gabanta mana kuma ya d'ora k'afafun ta a kashi tamkar itace sarauniyar shi." Kai Anty Nafeesat ta jinjina cikin jin dad'in abin tace. "Allah ya bashi ikon cika alkhairi." "Amin Amin." Hajjajo da Inna suka amsa. Tafi da sowan da mutane keyi da al'k'awarin da Hamma Umar ya d'auka su suka kara cushe zuciyar Ummul dan ganin duk Hamma Umar ya saye zuk'atan mutanen wurin ita kuwa zuciyar ta tamkar ta fashe dan tsabar tsanar Hamma Umar d'in sai wani irin kuka ta saki mai cin rai, shi kuwa Hamma Umar ba abin da ya fad'o mishi a ranshi sai tunanin mahaifinshi dan al'adarta su ana gamawa aggo zai wuce gun maihaifin shine dan ya samishi albarka da addu'ar Allah ya tayashi rik'o, tunanin shi a yanzu shi gashi yayi al'k'awarin Amman bayida mahaifi a duniya bare ya samishi albarka ya kuma tayashi Addu'ar Allah ya taya shi rik'o, tuno hakan ne yasa rauni a zuciyar Hamma Umar ta yadda lokaci d'aya hawaye ya b'allo a fuskarsa hawaye ne ke zuba cur-cur dan tuno mahaifinshi , zuba hawaye suke har kan k'afafun Ummul dake kan guiwowin sa, kuka yake cikin raunin sautin da ba wanda ke jinshi sai ita Ummul d'in da yake zaune a gabanta sai kuma Ya Usman da ya haggo hawaye na bin fuskar B'iyayen nashi, Ammi ma dake zaune gefen a lokacin tunanin mijinta ya dawo mata yau gashi ana bikin babban dansu amman ba mahaifin su Allah bai nuna mishi ba sai ita kad'ai, itama sai kuka, Ya Adam kuwa dake tsaye gefen Hamma Umar ya fara jin sheshshek'ar Hamman nasu tuni shima hawaye ya fara bin fuskarsa, Abokan Hamma Umar kuwa tasowa sukayi suka rink'a yi mishi liki, Ya Usman kuwa tuni zuciyar shi take harbawa hakan yasa ya sake hannun Nuru ya nufi gun Hamma Umar d'in nashi, shiko Nuru da sauri ya mik'e yabi bayan Usman din yana. "Usman anya kuwa yau kasha maganin ka kuwa? jikin ka ko? Usman kana wasa da lafiyar ka fa wato yau Hamma Umar yana cikin baki bai samu ya baka maganin kaba shine kai kuma bazaka iya shaba sai ya baka?." cikin rawan murya fuska cike da k'ollah Ya Usman yace. "A a Nuru a,a Hamma na ya bani maganin nasha , Hama Umar baya manta bani maganin duk hidamar da yake ciki, Nuru kalli Hamma Umar na yana kuka da hawaye Nuru sake ni naje kusa da B'iyaye na, Nuru Hamma Umar baya barin hawaye ya zuba a idanuna ,.Nuru ya za'ayi niko na k'asa tsaida nashi hawaye ?." cikin tausayin su Nuru ya sake mishi hannun shi, shi kuwa Usman kutsawa yayi cikin mutane yana zuwa ya durk'usa gefen Hamma Umar d'in daketa kuka hannun Usman yasa ya rik'o na Umar d'in cikin kuka yace. "Kai tona Hamma Umar kaito na tunda ina raye ban iya k'anwar da duk wani abu da zai saka kuka a rana mafi daraja a gare kaba." jin muryar d'an uwanshi yasa ya juyo ya rugume k'anin nashi, suka rugume juna cikin rauni Hamma Umar yace. "Usman Abban mu na tuna yau gashi ina bid'ar addu'arsa gashi kuma baya raye." ganin yadda suke kukan ne jikin kowa yayi sanyi haka yasa Ya Adam ya jagoranci abokan Hamma Umar din suka koma cikin gida a gefen baki Anty Shuwa kuwa taja k'awayen Amarya suka tafi, Anty Halima kuwa cikin kuka ta kamo hannun Ummul dake kuka kamar ranta zai fita sukayi cikin gida, haka aka watse taron, Ammi kuwa dama tuni tayi cikin gida kai tsaye d'akin Hajjajo ta wuce tana wani irin kuka mai karya zuciyar mutane, Hamma Umar kuwa shida Usman suna tashi suma suka wuce d'akin Hajjajo, suna zuwa suka zauna gaban Ammin su ita kuwa Ammin ta k'asa magana sai kuka, Hamma Umar ne ya matsota kanshi ya d'ora kan cinyarta cikin kuka da rauni ya jawo Usman kuma jikin shi ya rugume shi baki na rawa yace. "Am! Ammi! Ammeee! ki dena kuka Ammi ki samin al'barka kimin Addu'a Allah ya bani ikon cika al'k'awarin dana d'aukar wa kaina, bani da mai tayani Addu'a bayan ke da d'an uwana Ammi kibar kuka karki sa Usman a rud'ani." Hannunta ta dafe kanshi... *Kuyi hak'uri da Wannan Yau bak'in ciki kamar na d'aki kaina na gama typing 1 page mai Reed more 7 wlh garin gyara nayi delete nashi da ker nayi wannan* By *GARKUWA FULAni* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1⃣3⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *K*anshi ta dafe cikin muryar kuka tace. "Farouq Allah yayi muku albarka kai da d'an uwanka Allahu rabbi ya jibanci lamuran ka hak'ik'a yau ina al'fahari da kai, kuma na tabbatar yau da mahaifinku na raye zaiyi al'fahari da kai , domin ka cika d'a na gari d'a na hallas tabbas yau kasa farin ciki a zuk'atan iyayen rik'onku kai da d'an uwanka domin wannan abin da kayi zai sama musu nitsuwa a zuk'atan su ta yadda zasu samu k'arfin guiwar cewa ko bayan ransu zaka kula musu da y'ar su bisa amana da gaskiya, naji dad'i da samun yara nagari Umar Farouq da Usmanu shehu Allah ya muku al'barka ya k'ara muku k'aunar juna Allah ya sanya al'khairi a rayuwar Ku." Murmushi suka rink'a yi zuk'atan su cike da farin ciki da aminci jin irin addu'oin da mahaifi yarsu ke musu, Hamma Umar kuwa k'ara jawo Usman yayi jikin shi , shi kuma kanshi ya kara kontarwa kan cinyar Ammin sun, Hajjajo da Inna ma Addu'a sukayi tayi musu da sanya al'khairi da sa musu al'barka. Anty Halima kuwa tunda ta kamo hannun Ummul suka koma cikin gida kai tsaye d'akin Nenne ta wuce da ita, tana shiga ta saki hannun Ummul taje bak'in gado ta kifa guiwowin ta a k'asa kanta ta kife kan cinyar Nenne cikin kuka mai cike da tausayi murya a raunane baki na rawa tace. "Nenne Hamma Umar ya bani tausayi Nenne kiga irin al'k'awarin da Hamma Umar ya d'auka a kan Ummul Nenne sai kinga yadda Hamma Umar yake kuka cur-cur da hawayen shi ya rugume ya Usman suna ta kuka sun bani tausayi Nenne sun tuno Abban su." sai ta kuma d'ago kanta cikin zubda k'ollah ta kalli Ummul dake ta kuka tamkar zata amayo da ranta cikin sanyi tace. "Ummul ke kukan dad'i kikayi naki kukan najin dad'i ne iyayen ki na raye gaba da baya, bawan Allah Hamma Umar shiko kukan rashin uba yakeyi domin shi yasan zafin rashin Uba dan shi kam ya Usman Hamma Umar d'in ya meye mai gurbin mahaifin su, Hamma Umar bawan Allah maraya duk da tarin k'iyeyyar da kike nuna masa bai hanashi yin al'k'awarin zai rike da amana ba." Daga nan kuma sai ta mik'e ta fice ta nufi part d'in Abban ta, ita kuwa Ummul kuka take da bak'in ciki mai yawa a ranta a fili take gani duk an tsaneta tunda babu ko mai lallashin ta inba Ya Usman ba kowa harara ke had'a su ganin yadda su Anty Shuwa ke cilla mata harara yasa ta mik'e cikin kukan ta nufi part d'in Hajjajo, a parlour ta samu su Hamma Umar d'in da ya Usman dasu Hajjajon da Ammin su, har yanzu Hamma Umar kanshi na kife kan cinyar Ammin yana kuka k'asa-k'asa dan gaba d'aya jikin shi da zuciyar shi Abban shi kawai suke tuno mishi a yau d'in, shi kuwa Usman kukan Hamma Umar ne yake sashi kukan, itama Ammi ta kasa d'aure zuciyar ta sai k'ollah dake ta bin fuskar ta, itama Ummul nata kukan take ta wuce bedroom d'in Hajjajo kai tsaye kan gadon ta konta ta kife kanta cikin pillow taci gaba da kuka, ita kuwa Anty Halima a baki k'ofar parlour Abba tayi sallama cikin muryar kuka, cikin sanyi ta shiga bayan Abba ya amsa mata sallamar , Abban ta samu shida Daddy suna zaune sai fufun goro kusan guda 12 da katon-katon na sweet da k'oren dabino dake gaban su, gefen Abban nata taje ta zauna cikin sanyi ta gaida su sai kuma ta fara magana cikin raunin murya tace. "Abba Hamma Umar! Abba Hamma Umar da ya Usman sunata kuka sun tuno Abban su, Abba Hamma Umar ya bani tausayin Ammin suma sai kuka takeyi, Daddy kuje ku rarrashe su, Hamma Umar ya bani tausayin yanata kuka ya Usman ma yana kuka." kusan a tare Abba da Daddy suka mik'e suka fita kai tsaye parlour mahaifi yarsu Hajjajo suka nufa Anty Halima na biye dasu a baya, suna shiga parlour suka zauna gefen Ammi da yaranta Daddy ne ya jawo hannun Usman cikin kula yace. "Ya isa kukan ya isa haka habba Usman k'afa san zuciyar ka bata da cikekken lafiya." A hankali Usman ya kalli Daddy cikin sanyi yace. "Daddy kalli yadda Hamma Umar yake kuka , hawaye na bazasu bar zuba ba muddin idanun Hamma Umar na zubda k'ollah." Abba ne ya kalli Hamma Umar d'in cikin sanyi yace. "Farouq Kaine nake ganin kana da k'arfin zuciya sai gashi ka k'asa iya daurewa ga yadda kake kuka kalli yadda kukanka yasa d'an uwanka yin kuka kalli mahaifiyarku yadda kuka sata a rud'ani, shin ka manta zuciyar d'an uwanka ne? Farouq a yanzu ba abinda mahafinku keso daga gareku da mu da mahaifiyar mu sai Addu'armu." da sauri yasa hannu ya share hawaye shi cikin k'arfafa zuciyar shi yace. "Abba na bari, Usman kayi hak'uri ka koyi dauriya kajiko d'an uwana?." Kai Usman ya rink'a juyawa tare da goge k'ollah, daga nan su Abba sukayi ta musu nasiha sannan suka fita tare dasu dan jin an kira sallan maggariba, har sun fita gaba d'ayan su , sai kuma ya Usman ya juyo cikin sanyi ya shiga d'akin Hajjajo kai tsaye bak'in gadon da Ummul ke zaune yaje ya zauna cikin sanyi ya zaro hankicif d'in shi ya mik'a mata, bata karb'a ba sai d'ago kanta tayi ta zuba mishi ido cikin kuka tace. "ya Usman shike nan Hamma Umar zai rabani da Mustapha har *Abadan* shike nan nayi ban kwana da farin cikina, ya Usman kalli al'k'awarin da Hamma Umar yayi dan tsabar mugunta ya Usman shike nan Hamma Umar ya zame min k'arfen k'afa Ya Usman kasan ina son Mustapha gashi Hamma Umar ya rabamu gashi Abba na ya kwace woyata shike nan ya Usman ko muryar Mustapha baza a barni Mayo ba, ya Usman Hamma Umar ya binne min rayuwa ba Mustapha ba karatu na." sai kuma taci gaba da kuka, shi kuwa Usman ido ya tsura mata , sannan ya d'ago hannun shi ya dafe kahon zuciyar shi cikin tsura mata ido yace. "Ummul kece sanadin bugawar zuciyata zaki kasheni ki huta ki sani idan na mutu kece sila." cikin tsoro da mamaki ta zaro ido woje baki na rawa tace. "Ya Usman ni kuma? ni dai? in kasheka kuma? sabida me zan kasheka?." Kai ya jinjina mata cikin sanyi yace. "Ehh kasheni kike son yi tunda na lura bazaki bar koke-koken nan ba, na kuma gaya miki bana son inji kina kuka, Kukan ki nasa zuciya ta tayi nauyi bana son kina kira min sunan Mustapha in kina ki ranshi ji nake zuciya tana harbawa da k'arfi, kamar zata fashe." da sauri tasa hannu ta karb'i hankicif d'in sannan ta goge k'ollah cikin rawan murya tace. "Nayi shiru ya Usman na bar kukan , bana son ka mutu." Murmushi yayi sannan yace. "Allah ya d'aiyiba." itama murmushi tayi sannan tace. "Ina sonka ya Usman." cije lips d'in shi yayi da k'arfi sannan ya juya cikin sauri yayi hanyar fita har yaje bak'in k'ofar fita sai kuma ya tsaya cikin sanyi yace. "Allah ya d'aiyiba, nima ina sooon ki k'anwata Ummul." daga nan kuma sai ya fita, part d'in su ya nufa yana zuwa ya samu abokan Hamma Umar d'in duk sunyi al'wala shima al'walan yayi sannan suka nufi masallaci, bayan sunyi sallan maggariba basu dawo ba saida akayi sallan ishah sannan suka dawo gidan. 9:00 pm Hamma Umar ne da abo kanshi suke ta hira a parlour shi hira sukayi sosai cikin shak'uwa da sabo Abdallahn Maryam ne yayi murmushi cikin tsokana ya kalli Hamma Haiydar din Minali yace. "Kai General Aliyu wai ina Hamma Yusuf d'in Aysha ne ban ganshi ba?." Amadin Nadiya ne yayi murmushi tare da cewa. "You ai Hamma Mahmoud d'in Khadija ma ban ganshi ba." Salim d'in Tawa ne yayi murmushi tare da cewa. "Toh sa idawa." Abun batul kuwa murmushi yayi sannan yace. "Mutun da matar sa ai sai adena sa musu ido." Hamma Bashir d'in Rukayya ne yayi murmushi tare da nuna Hamma Hassan d'in Fateema yace. "Kaima ko zaka zillene kayi gaba da matar ka?." Hamma Haiydar d'in Meenarl ne ya d'an yi murmushi sannan yace. "Kai Aisar d'in Bintu sai dariya kawai kake kuma kaima anjima za'a nemeka a rasa zaka tafi gun matar ka." Al'ameen d'in Fauziyya ya mik'e cikin raha yace . "Nima nayi gaba." Ridwan d'in Zakiya kuwa shima sai murmushi yake yana woya da zakiyarsa Ahmad ana Muslim kuma shima dariya kawai yake. Suna cikin hira da dariyar su Hamma Yusuf ya shigo hannun shi rik'e da robobin inabi dasu Apple da reke sai kwakwa da dibino, ajiye su yayi a tsaki yarsu ya zauna gefen Abuturrab cikin murmushi ya kalli Aisar yace. "Ga inabi nan kusha , Aysha ce ta kirani tace in seyo mata shine kuma na kawo muku ku d'ana." dariya sosai Abban Rukky pinky yayi yace. "Aysha ta kiraka ko kai ka kirata." murmushi Hamma Umar d'in Ummul yayi tare da cewa, " Ku dai kuci kar kuyi tone -tone." dariya sukayi baki d'ayan su sannan sukaci gaba da hirarsu, suna hira suna cin lodin fruits din da Hamma Yusuf ya kawo musu, can sai kuma Hamma Umar d'in ya mike cikin sauri Key din motar Aisar ya zara sannan ya fice da sauri yana fita yaje ya lodowa Ummul fruits d'in da yacin gaba d'aya sannan ya dawo gida, Parlour nashi ya shiga inda ya samu su Abu har yanzu suna hira, Amadi ne ya kalleshi cikin tsokana yace. "Kaima Ummul tayi kira ne kaje ko?." murmushi kawai Hamma Umar d'in yayi tare da juya kai sannan ya zaro woyar shi auta Aliyu ya kira, Jim kad'an Aliyu ya shigo rik'e da hannun Hannah yarin yar Hamma Haiydar da Meenarl, robobin fruits d'in Hamma Umar ya mik'a wa Aliyu cikin yana yin aike yace. "Gashi ka kaiwa Ummul kace abokin nane ya seyo mana mukaci shiyasa itama na seyo mata nata." "Toh" Aliyu yace sannan ya karb'i robobin yayi cikin gida, kai tsaye parlour Hajjajo ya nufa, yana zuwa ko ya samu Ummul d'in tana zaune fuska duk a jeme , a hankali ya ajiye mata fruits d'in cikin kula yace. "Anty Ummul sarkin son zak'i gashi wai inji Hamma Umar wai abokin shi ne ya seyo sukaci shine kema ya seyo miki naki." ido ta d'ago cikin tsuke fuska ta buga mishi harara sannan tace . "Bana so ka meyar mai da abunshi." Kallon ta yayi cikin sanyi yace. "Kai Anty Ummul kinfa san ba kyau meda hannun kyauta." K'afa tasa ta ture robobin, Shi kuwa Aliyu hannu yasa ya d'auki robaa inabi guda d'aya ya fice tare da cewa. " ni dai zanci." Hajjajo kuwa tire ta d'auko ta tattara fruits d'in duka ta lodasu kan tiren cikin yin hamdala , ta rink'a nuna wa mutane tana cewa. "Ku gani Ku shida Farouq ya fara cika al'k'awarin d'aya d'aukar wa kanshi." suko sauran mata sai sunyi ta yabawa halin Hamma Umar d'in, ita kuwa Ummul ji take kamar taje ta shak'e shi ya mutu ta huta da bak'in cikin sa, kamar wasa Hajjajo ta dage tana bin d'aki-d'aki tana nuna musu abinda Umar ya aiko wa Ummul harsu abba sai da taje ta nuna musu, Ummul kuwa haka ta kwana cikin k'unci shiko Hamma Umar yana tare da abokan shi.. Washe gari misalin k'arfe 11:00 Am dai-dai dubban al'umma suka shaida daurin auren Umar Ibrahim Umar Shuwa tare da Rabi'atu Hassan Umar Shuwa Ummul kenan, d'aurin auren d'aya samu halartan manya-manyan bak'i kama daga gwamnan Yobe Ibrahim gaidam dan Hamma Umar shine doctor dake duba lafiyar gwamnan nasu na jihar Yobe tare da sarkin su, bayan an gama d'aurin auren ya Usman ne yazo ya rugume Hamma Umar d'in cikin happy yace. "Ina cin farin ciki Yau Allah ya nuna min auren d'an uwana Allah ya tayaka rik'o." murmushi Hamma Umar yayi tare da cewa. " Amin." daga nan abokan shi suka rink'a yi mishi musabaha suna tayashi murna, cikin zugar mutanen dake tayashi muryar ne yaga Mustapha ya mik'a mai hannu cikin sanyi sukayi musabaha sannan Mustapha yace. "Hamma Umar inayi maka fatan al'khairi a Rayuwar auren ka kaida Ummul ina taya ka farin ciki a matsayinna na d'an uwanka musulmi." sai kuma muryar shi ta fara rawa sai hawaye cur-cur a fuskar Mustapha, cikin tausayawa Hamma Umar ya rugume shi a hankali yace. "Mustapha ka gafar ceni na shiga rayuwar ka kai da Ummul Amman bayina bane Mustapha wannan rubutaccen al'amari ne bani da niyar rabaku, su Abba ne suka had'a aurena da Ummul, ku gafar ceni Mustapha domin na zame muku bak'in jakada a Rayuwar ku Mustapha ka gafar ceni." Cikin rawan murya Mustapha yace. "Hamma Umar na yarda da kaddar ta fatana ka rik'e min Ummul bisa amana." kara rugume shi yayi sannan ya sake shi cikin sanyi Mustapha ya juya ya tafi, shiko Hamma Umar haka yayi ta sallama da abokan shi dan duk yaune zasu tafi tunda biki ya kare gashi kuma abokan duk y'an nesane, Hamma Haiydar har Kaduna zai koma Hamma Yusuf kuwa Taraba Hamma Mahmoud Adamawa Yola Hamma Hassan Gombe yayin da Hamma bashin kuwa zai koma kano, haka Hamma Umar da ya Usman suka tsaya a harabar gidan nasu suna ta ban kwana da bak'on nasu, bayan duk sun tafi ne, saura baki matama dake cikin gida duk sun tattafi sai y'an kad'an da suka rege. Da daddare bayan Anyi Sallan maggariba da ishah Abba ya Tara family d'in shi harda Ammi da Inna da sauran mutanen gidan bayan sun zazzauna Daddy ya bud'e musu taron da Addu'a , sannan daga nan Abba kuma yayita musu nasiha mai ratsa jiki da zuciya, Ummul kuwa zuwa yanzu kuka ya zame mata jiki. Bayan Abba ya gama musu nasihar ne ya mik'e tsawon sa gaban Ummul yaje ya tsaya cikin bada umurni yace. "Ummul taso kizo." mik'ewa tayi cikin zubda k'ollah, shi kuwa Abba hannun ta ya kama yaja har gaman Hamma Umar d'in cikin kula ya kamo hannun Umar d'in ya tsaida shi sannan cikin girma da jagoranci yasa hannun Ummul cikin tafin hannun Umar d'in a hankali yace. "Farouq ga matar ka rik'e hannun ta ku tafi gidan Ku." kallon Abban yayi cikin sanyi sannan ya manner tafin hannun shi ya rumtse hannun Ummul d'in kamar yadda Abba ya umur ceshi, shi kuwa Abba Ummul ya kalla cikin tsuke fuska yace. "Kibi mijin ki ku tafi Allah ya baku zaman lafiya." "Amin Amin." sauran mutanen dake wurin suka amsa, shi kuwa Hamma Umar hannun Ummul d'in ya jawo cikin yin k'asa da guiwowin shi suka durk'usa gaban Abba a hankali yace. "Abba nagode Allah ya k'ara zumunci." "Amin Amin." Abba yace tare da shafa Kansu , sannan shi kuma Hamma Umar ya sake jan hannun Ummul gaban Daddy ya mishi godiya a haka ya rink'a jan Ummul suna zagaya wa har suka iso gaban Ammi da Nenne kamar kullum Hamma Umar hannun shi d'aya yasa ya ciro hularshi sannan ya jawo ummul suka durk'usa a gaban su cikin sanyi yace. "Ammi ! Nenne ! nagode Allah ya saka muku da al'khairi." dafa kanshi Ammi tayi kamar ko yaushe sannan tace. "Allah ya sanya haske a wannan Aure naku Allah ya taya ka rik'o Allah yayi muku al'barka." haka tayi ta musu Addu'a sannan tayiwa Abba ma godiya da kyautar y'ar shi d'aya bawa d'an ta. Shi kuwa Umar yana rik'e da hannun Ummul yaje ya rugume ya Usman cikin sanyi da k'aunar k'anin nashi murya na rawa yace. "Kamin al'k'awarin zaka kula da kanka, kasha maganin ka karkaci duk wani abu green kaji B'iyaye na, nanda kwana 5 Kaima zaka koma gidana inci gaba da kula da kai." murmushi Usman yayi cikin yanayin shi na abin dariya yace. "Nayi ma al'k'awarin zan kula da kaina kafin nima na auru matata taci gaba da kula dani, kaima ka kula da matarka Allah ya d'aiyiba." gaba d'ayansu dariya sukayi sannan Abba yace. "Farouq ku tafi dare yanayi." "toh" yace sannan suka rekosu harabar gidan Usman ne ya bud'e musu mota bayan sunyi saida safe sannan Hamma Umar yaja motar suka tafi. Tunda suka shiga motar ummul taci gaba da kukan ta, shi kuwa Hamma Umar tuk'in kawai yakeyi hankalin shi na kan titi haka sukayi tafiyar tasu Ummul daga Potiaskum har cikin Damaturu kuka take batayi shiru ba, suna isa k'ofar gidan ba tare d'aya shiga cikin gidan ba yayi parking sannan ba tare d'aya kalleta ba ya fito gefen da take ya zagayo marfin motar ya bud'e sannan ya jawo hannun ta, ita kuwa sai fizge hannun take tana k'ok'arin kwancewa, shiko sai matse hannun yayi da k'arfi cikin sanyi ya jata zuwa bak'in gate d'in juyawa yayi ya kalleta cikin bada umurni yace. "Ki nitsu kisan abinda kikeyi karki kuskura ki shigar min gida da k'afar hagu , sannan kiyi Addu'a kafin ki shigar min gida, dan na lura akwai shaid'anu a tsakiyar kanki, so ki watsar dasu anan kan titi karki kuskura ki shigar min gidana da su." kai ta sunkuyar cikin zubda k'ollah dan ta tuno Nenne tama ta horeta da tayi addu'ar kafin ta shiga gidan, k'ollah ta zubda sannan a hankali ta d'aga k'afar ta dama wanda kusan a tare suka d'aga k'afafun nasu, a hankali sukayi addu'ar shiga gida sannan suka shiga cikin gidan. A gida kuwa bayan Hamma Umar yaja motar sun tafi, Usman ne ya dafe k'ahon zuciyar shi da sauri jin yadda zuciyar shi ke bugawa da sauri-sauri idon shi ya rumtse da k'arfi lokaci d'aya yaga wani irin duhu cikin k'arfin hali ya juyo ya kalli Nenne sai yayi murmushi ya bud'e baki a hankali yace , "Shike nan yau kam ni kad'ai zan kwana ba Hamma Umar, da safe kuma ba Ummul wazan tsokana?." Dariya su Ammi sukayi mishi sannan suka juya zasuyi cikin gida kenan a dai-dai lokacin Usman yayi wani irin numfashi tare da dafe k'irjin shi yayi taggal-taggal ya fad'i kan kujerun jiki ba..... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1⃣4⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Y'an uwa abokai k'awaye yayu k'anne yara manya maza da mata masoya na da sab'anin haka writers da reedars dan Allah don soyeyyar mu da Annabi ina barar addu'arku ga mahaifiyata bata da lafiya dan Allah kusa min ita a addu'arku da bakunanku masu albarka Allah ya bata lafiya rabbi ya tashi kafad'an ta Allah yasa zakkan jiki ne a wanan gab'ar kuma zan shaida muku ba tabbas kuci gaba da samun posting nan kullum in nasamu nayi fani'imal in ban yiba la'basa nasan zaku min uzuri, DEDDE Am Allah ya baki lafiya 😭👏🏻* *A baya nace Usman Accounter ne so na batane Usman Lecturer ne a Yobe state university so daga yanzu a lecturer sa zamu tafi dan shine aikin sa na gaskiya* *B*a numfashi ya konta kan kujarar ba inda yake motsi a jikin shi, gaba d'aya su Nenne da Abba dasu Hajjajo a tare suka juyo kanshi ya Adam ne yayi sauri ya tallabo shi jikin shi cikin tsananin firgici ya rink'a juya kanshi yana d'an tab'a fuskar shi cikin d'imuwa yana . "Usman ! Usman ! Usmaaaaaaan! ka tashi ka tashi Usman , Abba Daddy ku gani Usman baya numfashi." Sai kuma ya k'ara rugumoshi jikin shi cikin rawan jiki, Abba ne yasa hannu ya jawo Usman d'in jikin shi cikin k'arfin hali irin na manya ya cewa Daddy. "Hussaini kawo wuruwa." jiki na rawa Daddy ya shiga cikin gidan, Ammi kuwa tunda Usman ya fad'i gaba d'aya sai jikin ta ya fara rawa kar-kar ko ina na jikin ta ya sake k'afafun ta suka k'asa d'aukar nauyin ta zuciyar ta sai bugawa take tara-tara cikin wani irin rashin kuzari ta zame a wurin ta zauna ta jingina da kujaran da Usman yake kai cikin sanyi baki na rawa take cewa. "Ya Allah ka rufa min asiri Allah ka dub'eni da idon rahama Allah ka hanani ganin mugun abu Allah ka jinkirtawa wannan bawa naka kabashi lafiya Usman Allah ya hanani ganin gawarka ganin na mahaifinku ma har yau bai bar idanuna ba." Inna ce ta dafa ta cikin sanyi tace. "Kiyi mishi Addu'a Amina addu'arki gare shi ba hijabi insha Allah karb'ebb'iya ce ." jin haka sai zuciyar Ammi ta kara karaya cikin sanyi ta kontar da kanta a cin yar Innarta ta kamo hannun Usman ta rink'a wani irin kuka mai cike da fargabar faruwar wani abu, Hajjajo ma sai kukan takeyi ya Sadip da Aliyu ma gaba d'aya sun k'asa saida hawaye su Anty Halima kuwa cikin gida ta shiga tana kuka cur-cur, Daddy kuwa yana zuwa ya d'auko goran ruwan mai sanyi ya dawo Abba ya mik'a wa, yana karb'a ya b'alle marfin gorar sannan ya tuttulo ruwan sanyin a tafin hannun shi da k'arfi ya watsa a fuskar Usman d'in, a take sai yayi wani irin ajiyan zuciya mai k'arfi sai kuma yayi shiru numfashi sa na harbaqa , cikin kuka Ammi ta rik'o hannun shi tana. "Usman ! Usman! Usmaaaan!." sai kuma ta fashe da kuka, Shi kuwa can sama-sama yake jin sautin kukan mahaifiyar shi da sauran yan uwa, cikin tsananin mutuwa jiki ya bud'e idanun shi kuma sai ya lumshe su ganin baya ganin su sosai , su kuwa ganin haka yasa Ya Adam ya zaro woyarshi da sauri yace. "Abba bari in kira Hamma Umar yazo ya duba shi." jin hakan yasa Usman d'in ya k'ara bud'e idanun shi cikin rawan. Murya yace. "Ah,Ah a a Adam kar ka gayawa Hamma Umar komai ka barshi , naji sauk'i." meda woyar Adama yayi cikin jin dad'i ya kamashi ya rugume murya na rawa yace. "Usman meyasa kake wasa da lafiyar ka me kake tunawa me damuwarka a duniyar nan Usman?." cikin k'arfin hali ya d'an ture Adam sannan ya d'an jingina da jikin kujerar ya kamo hannun Ammin shi ya kalli Hajjajo da inna dake ta zubda k'ollah yace. "Kai da Allah ni ku dena min kuka lafiyata lau ji tsoffin nan fa aini ras na ke sai namu rakiya kafin nima a min rakiya zuwa gidana na gaskiya, Abba kace su dena kuka ni na worke." Sai kuma ya kalli Ammin shi cikin sanyi yace. "Ammi shi komai da kika gani a duniyar nan toh Rubutaccen al'amari ne so karki damu ki sawa ranki dangana insha Allah ba zakiyi kuka ba matukar Hamma Umar na yana raye, karki damu shi d'aya ne tamkar da mu biyu kinji ko Ammi na." kanshi ta shafa cikin rawan murya tace. "Ku duk ina fatan ku rayu har bayan rayuwa ta." dariya ya d'an yi sannan ya kalli Abba da Daddy dake binshi da ido cikin fidda numfashi mai nauyi yace . "Dan Allah Abba kar a gayawa Hamma na kunga kar hankalin shi ya tashi." Nenne ce ta kalleshi a hankali tace, "Kasha maganin ka yau?." Kai ya gyad'a mata sannan yace. "Hamma Umar ya bani kafin ya tafi." so haka yayi ta basu k'arfin guiwa ya kuwa hanasu su gayawa Umar, a haka sukayi ta mishi nasiha kan shan maganin shi, sannan Abba yace daga yau shi da Adam zasuke kwana tare, haka kuwa akayi, shi kuwa Usman, suna shiga d'akin nasu ya zame ya shiga toilet k'ofar ya maida ya rufe cikin tarin takaici dajin haushin kanshi da zuciyar shi ya kife kanshi jikin gini ya rink'a wani irin kuka maicin rai kuka yake yana d'an dukan saitin kahon zuciyar shi cikin kukan yake cewa. "Kai tona da Wannan zuciya tawa mai zuwa hurumin daba nataba." haka yasha kuka har saida yaji kamar numfashi sa zai yanke sannan yayi al'wala ya fito ya shimfid'a sallaya ya fuskanci gabar, Adam ne ya kalleshi cikin kula yace. "Usman zaka iya tsayuwa ? ka konta mana ka d'an huta." Murmushi yayi cin juya fuskar sa dan baya son Adam yaga idanuwan shi da sukayi jazir suka kumbura, cikin yanayin wasa yace. "Kai nafa fika lafiya kuma zanyi wa Hamma na da Ummul addu'ar Allah ya basu zaman lafiya dakuma 'yan biyu." dariya Adam yayi tare da cewa. "A a yan ukune ba yan biyu ba." Toh hakafa rayuwa tayi ta juyawa Usman kullum yakan b'uya yasha kuka har sai yayi gyatsa ya kuma ji numfashi sa na carkewa sannan ya fito, ba kuma wanda yasan halin da yake ciki. *Gidan Hamma Umar da Ummul kuwa* Bayan sun shiga cikin gida Hamma Umar na rik'e da Hannun Ummul d'in a haka ya jata har bak'in k'ofar shiga cikin asalin gidan bak'in k'ofar parlour ya tsaya key ya zaro a haljihun shi sannan ya bud'e k'ofar cikin bada umurni yace. "Kiyi Addu'a ki kuma shiga da k'afar dama." bata kulashi ba sai k'ollah da take zubda wa sannan tayi yadda yacen, suna shiga cikin Parlour Ummul tayi fizge hannun ta cikin kallon yadda Abban ta ya binne mata dukiya a parlour fuska cike da k'ollah tayi cikin bedroom da gudu tana zuwa shiga ta maida kamar ta rufe kan gado ta fad'a cikin disashewar murya taci gaba da sana'arta, shi kuwa Hamma Umar shiru yayi a parlour ya tsurawa k'ofar d'akin ido yana jin sautin kukan can k'asa-k'asa kai ya juya ya fito kai tsaye motar shi ya shigar cikin gida ya ajiye ta a harabar gidan sannan ya bud'e bayan motar ya d'auko lodojin da ya ciko da abubuwan cin da sha, kai tsaye parlour ya shigo kan dinning table ya ajiye ledojin sannan ya bi d'an corridor dake gefen d'akin da Ummul ta shigan nan ma wani d'aki ne babba wanda yasha gyara da shimfid'u daga dukan alamu dama nanne d'akin da yake rayuwa in yazo Damaturun daga can d'aya b'arin kuma nan ma akwai wani bedroom d'in dan gidane mai yalwar d'akuna parlour ne guda d'aya babba wanda ke d'auke da dinning area mai girma da tsarina sai daga gefen shi wani d'an corridor ne da zai sadaka da kitchen sai sito dake manner a gefen shi, ta bayan kitchen din kuwa d'an k'aramin wurine mai cike da tsirrai masu kyau , cikin parlour kuwa yana d'auke da 3 bedroom, so yana shiga d'akin sa wonka yayi sannan ya fito yayi shirin baccin sa, parlour ya fito cikin nitsuwa yana taku mai cike da haiba a hankali ya jawo kujara ya zauna a dinning table d'in kanshi ya jingina jikin kujerar sannan ya d'ora k'afafun shi kan table d'in yana d'an kad'a su a hankali ida nunshi ya lumshe tare da kamo lips d'in shi ya matse yana jin yadda Ummul ke yin kuka cikin sauti mai cike da rauni da wahala da alamun gajiya daga kuma jin sautin kukan da alamun zazzab'i a jikin ta, ido ya k'ara rumtsewa dan yana jin kukan nata na ratsashi dan window d'akin ta yana ta saitin dinning area d'in, cikin sanyi ya mik'e a hankali yaje bak'in k'ofar, cikin murya mai cike da tausayawa yace. "Khairi kiyi hak'uri ki dena kukan nan ya isa kizo ki bud'e k'ofar kinji kibar kukan kar ya saki zazzab'i ki fito kici abinci kinji ko Khairi?." kukan Ummul ta kuma k'ara yi cikin dishewar muryar tace. "Bazan fito ba, ka barni nayi kukana in banyi kukaba me zanyi ? bazanci abincin ba inya so yunwar ta kasheni kowa ya huta tunda dama ba,a sona." Shiru yayi sannan ya d'an yi ajiyan zuciya tare da cewa. "Khairi baki da lafiya fa ki bud'e kizo kici abinci kisha maganin inyaso kyaci gaba da kukan tunda shi kikeso ." bata kuma kula shi ba haka tayi ta kukan ta yayi ta lallashin ta a banza, haka ya hakura ya barta ya koma bedroom d'in shi ba tare da yaci abincin ba, ita kuwa haka ta kwana kuka har Allah ya wayi gari. Bayan Hamma Umar d'in ya dawo masallaci ne ya zauna a parlour tare da kunna TV ya kama tashar manara idan ya samu sun saka sautin karatu k'ura'ani tare da muryar Ahmad Sulaiman volume ya k'ara ta yadda sautin ya rink'a ratsa cikin gidan baki d'aya kan kujera ya konta ya lumshe ido yana bin sautin karatu hannun shi kuma rik'e da carbi, itako Ummul tunda tayi salla ta konta kan sallayar cikin jin zazzab'i ga ciwon kai kuma ta k'asa barin kukan, a haka tana kukan har bacci ya saceta, shi kuwa bai bar parlour ba sai 9:00 am ya mik'e ya shige kitchen nasu gas ya kunna tare da d'an tafa musu ruwan tea sannan ya sake d'uma kajin daya seyo ajiyan ya had'a musu komai yazo ya ajiye kan dinning d'in , d'akin shi ya shige wonka yayi sannan ya shirya cikin kananan kayan ya fito ras sai k'amshi yake zubawa, kai tsaye k'ofar d'akin ta yazo ya tsaya cikin sanyi yace. "Khairi ! Khairi ! tashi kizo kiyi breakfast." tana jinshi tayi shiru kamar bata jinshi , sai mik'e wa tayi ta zauna ta jingina jikin gado tana jin yadda yake kiranta tayi cib kamar bata d'akin, shi kuwa sai komawa yayi ta jikin window ta ya bud'e glass d'in sannan yasa hannun ya bud'e labulen ido ya zuba bata, itama idon ta zuba mishi cikin nuna kiyayyarsa a fili, kai ya jinjina cikin jin tausayin ta yace. "Khairi taso kizo kinji ko." "Bazan zoba bazan cin abince ba, Na mutuwa mane me ruwan ka?." Kai ya juya tare da cewa. "Meyasa bazaki ciba." a kufule tace . "Sabida na tsane kaa! bana son ka! bana son ganin ka! bana son ko jin muryar ka!." ido ya zuba mata cikin tsananin mamaki da al'ajabi bai tab'a zaton k'iyayyar da Ummul take Mashi yakai matsayin da zata kalleshi ido da ido tace mishi bata sonshi bata k'aunar shiba, muryar tace ta kuma katsemai tunani tana cewa . "Na tsane ka tunda ko yaushe a sana dinka nake azabtuwa." Kallon ta ya kumayi sannan a hankali yace. "Kina son kanki ai?." "Sosai ma dama ina son kaina kam mana." murmushi ya d'an yi sannan yace. "Toh ki fito kici abinci dan ki kula da kanki ni kuma nagode da k'iyayyarki gareni." "Bazan ciba ! ba kuma zan fito ba!." Haka Hamma Umar yake ta fama da Ummul Amman sam tak'i fitowa , zuwa yanzu kuwa kukan har ya gaji da ita dan ba itace ta gaji da kukan ba kukanne ya gaji da ita sai dai tayi ta diri ba hawaye shi kuwa duk kula da tattali yana had'a mata Amman ko fitowa tak'i tayi bataci komai sai ruwan da take sha da fari bata jin yuwar Amman zuwa yau da tayi kwana biyu a hakan sai take jin yunwar kamar zata kasheta inta tsaya sai jiri , tayi wonka kuwa yafi sau 3 wai duk ko zataji k'arfi Amman abin yaci tura a deren kwana na 3 ne ta k'asa bacci dan yunwar dake kwak'ularta. Shi kuwa Hamma Umar gaba d'aya kewar d'an uwanshi ya cika mar jiki da zuciya haka yasa kullum sai sunyi magana a woya a kalla sau 5 zuwa sau 6 duk lokacin shan maganin Usman in yayi sai Umar ya kirashi yace mishi kasha maganin a b'aggaren Ummul kuwa yana damuwa da halin da take ciki. A al'adun shuwa'arab d'in kuwa suna yin wata al'adarsu duk lokacin da akayi Aure aka kai Amariya gidan ta washe gari y'an uwanta zasuje karb'ar tukuici a gun aggo kuma Wannan tukuici ba'a badashi sai aggo ya kusanci matarshi so haka yasa wasu basa zuwa washe garin randa aka kai Amariya sukan bari sai randa tayi kwana 3 ko 7 kuma Wannan tukuici ba'a ba dashi ga amariyar da bata kai budurcin ta gidan mijin taba, so Hamma Umar kuwa yasan da wannan al'dartasu, so yau ya tashi da wuri ya kimtsa ko ina na gidan dan yana tsammanin y'an uwan Ummul zasu zo yau d'in tunda yau kwanan ta uku da zuwa gidan, bayan ya gama komai yayi wonkan shi fes ya fito ya shirya cikin wagamri mai kalar sararin samaniya ya fito ras sai k'amshi yakeyi. kamar kullum yazo bak'in k'ofar d'akin nata cikin sanyi yace. "Khairi ki zo ki bud'e k'ofar nan zakiyi bak'i su Anty Shuwa na zuwa." A hankali cikin wahala da jiri ta mik'e tazo bak'in k'ofar ta bud'e sai kuma ta juya ta koma ta zauna gefen gado tana ta haki hannun ta rik'e da cikin ta, shi kuwa Hamma Umar yana ganin haka ya koma parlour dinning area ya nufa yana zuwa, ya d'auki cup tea ya had'a mata mai kauri sannan ya juyo ya dawo cikin d'akin yana shiga kiran Usman na shiga woyar shi gefen ta yaje ya zauna sannan ya mik'a mata cup d'in cikin kula yace. "Karb'i kisha tea zakiji k'arfi." kai ta juya tare da matse ido ta samu ta zubda k'ollah, shi kuwa woyarshi ya zaro ya amsa kiran yana kallon fuskar ta, gaisawa sukayi da Usman sannan yace . "Kashe maganin ko?." "Eh nasha tun d'azun ma." sai kuma yayi shiru... can kuma yace . "Hamma Umar Ummul fa?." "Gata nan tana ta kuka tak'i cin komai kuma bata da lafiya , gata bari in bata woyar." "Toh" yace sannan yayi shiru yana jin Hamma Umar d'in yana cewa. "Ga Usman yana magana." Karb'ar woyar tayi cikin rawan jiki murya na rawa tace. "Hello ya Usman." A hankali cikin sanyi yace. "Na'ammmm Ummul." Tana jin muryar shi sai kuma ta fashe da kuka cikin kukan tace. "Ya Usman cikina ciwo , kaina ciwo jiri nake ji duhu nake gani ya Usman ni dai zan dawo gida." sai kuwa ta fashe da kuka. shi kuwa Hamma Umar shiru yayi ya zuba mata ido yana sauraron magarda takeyi, shi kuwa Usman a hankali yace. "Ummul kinfi son zuciyata ta fashe ko? Ummul bazaki bar kukan nan ba ko? Ummul kina son inyi fushi da ke ko?." Kai ta rink'a juyawa kamar tana gaban shi sai kuma tasa tafin hannu ta share hawayen ta murya a sanyaye tace. "Ah ah ya Usman bana so kayi hak'uri nayi shiru." Ajiyar zuciya ya sauk'e sannan yace. "Ban yarda ba nasan yanzu haka idanun ki na zubda hawaye kuma ba zakici abinci ba." da sauri tace. "Wallahi nayi shiru kuma na share hawayen kuma wallahi zanci abincin." "Kin tabbata ?." "Ehh wallahi." "Na tabbayi Hamma Umar?." "Ehh gashi ka tabbaye shi." Sai kuma ta mik'awa Hamma Umar d'in woyar tana cewa. "Bani zansha shayin." Mik'a mata cup d'in yayi sannan ya karb'i woyar tashi, yana kallon fuskar ta, shi kuwa Usman dariya ya d'an yi cikin sanyi yace. "Hamma na tayi shiru ko? ta karb'i tea d'in ? ta fara sha ne?" Murmushi yayi tare da cewa. "Ehh ." Dariya Usman ya kumayi sannan yace. "Hamma na kai baka saba lallashin wani d'an adam bayan ni a duniya ba shiyasa ka k'asa sata tayi shiru Hamma dole ka koyi lallashi fa tunda Allah ya had'a ka da Ummul." murmushi kawai yayi sannan yace. "Toh." Bayan ya katse kiran ne ya juyo ya kalli Ummul da tuni ta shanye tea d'in sai zufa keta tsatstsafo mata tako ina sai damk'e cikin tayi tana murk'ususuwa, mik'ewa yayi ya tsaida ta sannan ya rink'a jijjigata har saida yaji tayi gyatsa sannan ya meda ita kan gadon ya kontar da ita, d'akin shi yaje jim kad'an ya dawo hannun shi rik'e da magani , shida kanshi ya bata tasha sannan ta koma ta konta, shi kuwa rafan kud'i ya ajiye mata a gefen ta wanda zasu kai dubu 100 sai kuma wata y'ar counter near yar k'arama sarkace da y'an kunne sai zobe, zoben ya zaro sannan ya kamo hannun ta ya zura zoben a yatsarta dake kusa da y'ar karamar yatsar ta sannan yace. "Gashi insu Anty Shuwa sunzo ki basu wannan kud'in da sark'ar." Harara tayi mishi k'asa-k'asa sannan ta zare zoben ta jefar gefe, shi kuwa parlour ya koma ya zauna, ya zauna kenan su Anty Shuwa suka iso bayan sun gaisa ne sai ya fita shida ya SADIK daya kawo su. Su Anty Shuwa kam tunda suka samu Ummul a konce ba lafiya sai sukayi zaton ta zama cikekkiyar matar aure, yayin da Usman ma tunda Hamma Umar yace mai Ummul bata da lafiya kuma tana ta kuka sai ya d'auka Hamman nashi ya zama oggone a daren jiyan, so haka suma su Anty Shuwa amman Anty Halima ita ta gane sarai ba abinda Hamma Umar yayiwa Ummul kawai ya bada tukuicin ne. haka suka wuni suka yi tayiwa Ummul nasiha ta kuma ci abinci so ta samu tayi k'arfi, sai yamma lis suka tafi. bayan sun tafi kuma ta wore ras ta fito parlour dan a cewarta yanzu lokaci yayi da zata fara gasa Hamma Umar d'in. Da dere yayi Hamma Umar yana d'akin shi bayan ya yayi wonka ya fito yayi shirin bacci har ya konta sai kuma ya mik'e ya nufi d'akin ta yana zuwa ya zauna gefen ta a hankali ya.... *Dedde na Allah ya baki lafiya* By *GARKUWAR FUlANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1⃣5⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Alhamhadullih jikin Dedde na da sauk'i sosai ta samu lafiya nagode wa Allah daya bata lafiya kuma nagode muku masu kirana da masu turo min messages da yi mata addu'a a groups da masu bina pc, UWA uba wad'an da sukayi tattaki suka zo dubiya duk nagode da addu'oinku gareta ngd matuka Allah bar zumunci 🤝😘😍🤝* *K*allon ta yayi cikin mamaki ganin yadda take konce duk ta duk'unk'une wuri d'aya gaba d'aya ta takura kanta ga kayan jikin ta duk ta konta dasu hatta hijabin kanta bata cireba ta nad'e guiwowin ta har suna tab'a k'irjin ta sai hannun ta data sa ta kame kafad'un ta sannan ta cusa kanta cikin pillow da kaga ganta kasan bacci takeyi amman cikin tsoro duk ta takure hatta numfashi ta da kalan tsoro take fidda sautin shi, gyara zaman shi yayi yana fuskan tarta a hankali yasa hannu tare da kamo hijabin ya fara k'ok'arin zare mata shi a jikin ta, ita kuwa cikin baccin tsoron da tunda tazo gidan a haka take rayuwa cikin tsoro dan ita bata tab'a kwana ita kad'ai a d'aki ba a rayuwar ta gata da tsoro amman kuma k'iyeyyar Hamma Umar d'in ta hanata kusantan inda yake ta gommace ta rayu cikin tsoro, a hankali ta d'an motsa tare da k'ara jawo hijabin nata duk cikin bacci, shi kuwa ganin ta d'an motsa ne yasa ya d'an janye hannunshi yayi shiru yana kallon fuskar ta, can zuwa wani lokacin kuma ya d'an k'ara matsota sannan yasa hannun ya fara zaro hijabin har ya cire shi a kanta, dai-dai sanda ya cire ita kuwa ta bud'e idonta, gaba d'aya jikinta rawa yakeyi tamkar mazari sai wani irin zaro idanu tayi cikin tsoro ta mik'e tare da fizgewa tana tuttureshi, shi kuwa Hamma Umar kamota yayi da k'arfi ya maidata kan gadon pillow ya jawo sannan ya kontar da ita kan pillow sai kuma yasa hannu a hankali ya fara zuge zip d'in rigarta, ganin haka yasa ita kuwa tayi wani irin yunk'uri tare da sa hannu bibbiyu ta tureshi da k'arfi har saida kanshi ya bugi jikin gado da sauri ya dafe kanshi da hannun d'aya d'ayan kuma ya kamota ya rik'e gam, cikin sanyi yace. "Ina zaki je? ki nitsu mana zakiji wa kanki ciwo fa zoki konta ba abinda zai sameki gani a kusa da ke." hannu tasa tana ta kiciniyar b'amb'are yatsun hannu shi cikin tsiwa tace. "Bana so ka sake min hannun na ka fita harkata ba ruwan ka da ni ka barni inje duk inda naga dama kar woni zo ka mak'ale ni kace zaka min dad'in baki ni bana sonka bana son ganin ka." jawota yayi jikin shi cikin tsura mata ido yace. "Bakya sona fa kikace khairi nifa d'an uwan kine." "Eh bana sonka bana son ganin ka na tsanekaaa." lips d'in shi na k'asa ya kamo ya rink'a tsotsa a hankali yana jin zafin kala manta , sai kuma ya k'ara matsota tare da zare rigar sannan yasa hannun yana kunce d'aurin da tayiwa zanin ta, ita kuwa gaba d'aya sai wujijjigashi takeyi tana ta kici niyar kwace kanta amman ta kasa kawai sai ta sunkuyar da kanta tare da kafa bakinta a damtsen hannun shi ta datsa mishi cizo mai zafi dan gaba d'aya ta tsinke da Hamma Umar d'in, yana jin yadda ta dasa hak'oran ta a damtsen hannun shi zafin yana ratsashi madadin ya saketa sai ya k'ara matsota jikin shi ido ya rumtse da k'arfi cikin wani irin yanayi yace. "Zaki kasheni kike so? Ummu kiji tsoron Allah fa meyasa kika zab'i ki azabtar dani bayan kin san ni mijin kine." Ita kam ganin bata da k'arfin kwatar kanta yasa ta saki kuka mai cike da tsoro murya a birkice tace. "Ka sani wallahi ni bana sonka bana son ganin ka, ka fita hanya ta." Ido ya lumshe dan hak'ik'a yana jin ciwon yadda take cemai bata sonshi cikin sanyi yace. " Khairi bakya sona ko ?" "Ehh bana sonka." Kai ya jinjina sannan yace . "Kin dai san ni mijin kine ke kuma matata ce so kin san akwai hak'k'ina a kanki ko? kin kuwa san zaman aure mukeyi ni kuwa ba waliyi bane." tureshi ta k'ara yi cikin kuka tana Jan hijabinta tana k'ok'arin rufe jikin ta murya na rawa tace. "Ni bana sonka kuma ba zaman auren da zanyi dakai dan bazan karya al'k'awarin da nayiwa Mustapha ba ni ka sake ni." ajiyan zuciya ya rink'a sauk'e wa cikin yanayin cushewar tunani ga yanayin canji daya tsinci kanshi a ciki shi da kanshi bai san yana da wannan halittar ba dan a zaton shi da zai iya rayuwa ko ba mace amman gaba d'aya tunda akayi auren yake jin bak'in al'amura a jikin shi, saketa yayi cikin sanyi ya mik'e ya tsaya a bak'in gadon yana mai jin zafin kanshi data gwora da jikin gado da kuma cizon da tayi mishi, hannun yasa ya kamo hannun ta a hankali yace. "Ki dena kwana da bra a jikin ki yana haddasa ciwon k'irjin yana kuma iya jawo cancer ko ya sa miki toshewar numfashin, ki dena kwana da kayan masu nauyi a jikin ki, ki rink'a yin al'wala kafin ki kwanta ki kuma yi addu'ar bacci." Baki ta tab'e cikin jin haushin sa tace. "Nida jikina ba ruwan wani dani inyi yadda nike so kuma dole in kula da kaina tunda ina rayuwa da kai gida d'aya." Murmushi yayi gano wai danshi take kwana a hakan, hannun ta yaja har zuwa cikin bathroom a hankali yace. "kiyi al'wala." baki ta tura sannan tayi al'walar nan ma dan tasan hakan koyarwa ce ta annabi, bayan tayi al'walan suna fitowa ta zauna bak'in gadon cikin tsiwa tace. "Zanyi bacci fa." Kai ya gyad'a sannan yasa hannu ya kontar da ita blanket ya jawo ya d'an rufeta , hannun shi na cikin blanket d'in ya sunkuye kanta a hankali yace. "D'an d'ago bari in cire miki bra d'in." harara tayi mishi k'asa-k'asa cikin tura baki tace. "Ni ai ba karuwa bace." sai ta kuma ture hannun shi sannan ta juyo ta konta ta a kife, shi kuwa Addu'a yayi tare da shafe jikinta kamar yadda ya saba yiwa Usman , sannan ya kalleta ahankali ya juya ya fita, a parlour ya konta tare da son jin d'umin ta Amman yasan hakan bazai samu ba, haka ya kwana cikin halin takura. Haka rayuwa taci gaba da juya musu duk wata kulawa da gata Hamma Umar yanayiwa khairn shi yayin da ita kuwa take ta azabtar dashi , ta yadda baya samun ko magana mai dad'i ma bare ya samu hakkin shi dake kanta duk da yana yawan zuwa inda take amman haka ba abinda yake sama mishi sai azaba da bak'in ciki ko tafin hannun ta bai isa ya murzaba sai yasha bak'ar magana. Yau Monday kuma Yau kwanan su takwas da tarewa kenan, yau tunda sassafe Hamma Umar ya shirya komai tsab kamar yadda yasaba sannan ya shiga wonka sauri sauri ya shirya dan yau zai fita zaije gidan governor dan duba lafiyar shi duk da dai bai gama hutun auren nashi ba amman zaije dan duba lafiyar shi , bayan ya gama shirin shi tsab sannan ya fesa turaren shi mai tarin k'amshi laptop nashi da phone dinshi ya d'auko sannan ya fito parlour kan dinning table ya ajiye su , sannan ya jawo cups guda biyu tea ya had'a , sannan ya d'an juya rik'e da cups d'in ya nufi cikin parlour gaban Ummul d'in ya d'an tsaya cikin sanyi yace. "Khairi taso kisha tea sauri nake zan fita yanzu zan dawo." kallon shi tayi sannan ta kalli yadda tea d'in yake ta tiriri da alamun ruwan yana da zafi sosai ido ta lumshe cikin jin dad'in shawarar da shaid'an ya kawo mata fuskar shi ta kuma kalla cikin mugunta ta mik'e ta tsaya a gaban shi, hannu tasa ta karb'i cup d'in tare da tsura mishi ido, shi kuwa kanshi ya sunkuyar tare da d'an juya tea spoon d'in dake cikin cup d'in, itako murmushi mugunta tayi, cup d'in ta d'ago tare da watsa mishi ruwan zafin a fuskarsa , ba zato ba tsammani yaji ta watsa mishi tea d'in a fuskar da jikin wani irin zafi da rad'a d'i yaji yana ratsashi, jin zafin ruwan daya sauk'a a jikin shi yayi wani irin yunk'uri ya hankad'ata da k'arfi saida ta fad'i k'asa, sai kuma cup d'in hannun shima ya sub'uce yayi k'asa, hannun shi ya rink'a yarfawa yana d'an jujjuya kai yana jin zafin na ratsa fatarshi har cikin zuciyar shi yake jin zogin, a take fuskar shi tayi jazir sai zufa keta keto mishi tako ina, ita kuwa Ummul yana tureta tana fad'uwa ta kife kai tare da sakin kuka, kuka ta saki da k'arfi shi kuwa jin kukan yayi sauri yayi kanta yana zuwa ya d'ago ta ya sa hannu biyu ya rik'e kafad'un ta ido ya zuba mata cikin wani irin yanayi ya lumshe ido murya a sanyaye yace. "Kiyi hak'uri Ummulkhari bawai na tureki dan zafin ruwan da kika watsa min bane, a a wallahi na tureki ne dan kar ruwan ya fantsalu ya dawo jikinki ya k'onaki , kiyi hak'uri." Ido Ummul ta zuba mishi tare da k'ara sautin kukan nata tanayi tana mita, a cikin zuciyar ta kuwa tabbas ta cika da mamaki har cikin ranta taji mamakin yanayin da Hamma Umar keyi mata magana a yanzu bayan k'onashi tayi sannan kuma shike bata hak'uri har kuma yana cewa ya tureta ne dan kar itama ta k'one, kuma a zahiri da kaga fuskar shi kasan yana jin zafin k'unan amman bai bi ta kanshi ba ya tsaya bata hak'uri, shi kuwa Hamma Umar har cikin ranshi bawai ya tureta dan ta watsa mishi ruwan zafin bane kuma yaji zafin yadda ya ture harta fad'i har takai da tana kuka, a hankali ya kuma matsota yana kallon bakinta da take ta kuka da iya k'arfin ta ya lura so take ta tara mishi mak'otan su, kuka take tana. "Allah zai saka min ka rabani da kowa nawa kazo kana azabtar dani na tsane k...!" a hankali ya sunkuyar da kanshi cikin sauri ya manne bakin shi da nata lips d'in ta yayiwa rik'on taushi ida nunshi ya lumshi tare dasa hannun shi d'aya ya zagayo k'ugunta , ita kuwa ido ta zazzaro woje cikin tsantsar firgita da tsoro ga tarin mamaki Hamma Umar ne ke manne bak'in shi da nata , gaba d'aya ya rufe bak'in manata ya hanata kukan bare rakin da takeyi da son tara mishi mutanen, shi kuwa Hamma Umar idon shi a lumshe ya sab'ule lips d'in ta a bak'in shi cikin lumshe ido ya juya ya koma bedroom d'in shi , wonka ya sake yi sannan ya canza kaga , ya fito parlour kan dinning table yaje phone d'in shi ya d'auka kanshi a sunkuye yazo gefen ta ya tsaya yana jin yadda take yin kuka a hankali yace. "Ayyah Khairi kiyi hak'uri kibar kukan nan kinji bari inje in dawo ki gaya min me kike son in miki." mik'ewa tayi ta nufi bedroom d'in tana kukanta na rashin gaskiya, haka ya fita yana mai tuhumar kanshi daya gaza rik'e amanar daya d'auka. Tunda ya fita bai samu ya dawo ba sai 9:34 pm , yana shiga cikin gidan bedroom nashi ya shige wonka yayi sannan ya fito d'aure da towel a parlour ya d'an zauna jin gidan shiru kamar ba kowa a ciki, mik'a yayi tare da lumshe ido tabbas yana buk'atar kulawar Ummul amman haka ya faskara zuwa yanzu ya fara k'asa yin control d'in kanshi, a yanzu kuwa ya gane cewa shi mutunne mabuk'aci mai son kulawar matar sa, a hankali ya mik'e ya nufi d'akin nata cikin sa'a ya samu k'ofar a bud'e take a hankali ya murd'a hannun k'ofar tare da turawa , yana shiga ya haggota kwance kan gadon, k'ofar ya maida ya rufe cikin sanyi ya zauna gefen ta a hankali ya kwanta tare da sauk'e ajiyan zuciya jikin shi ya manna da nata a hankali yasa hannu ya jawota jikin shi , kan k'irjin shi ya kifeta a hankali ya fara shafa gadon bayan ta murya can k'asa cikin rad'a yace. "Ummul khairi ! Khairi ki tashi." ido ta bud'e cikin yunk'uri tare da yin mutsumutsu tana. "Wallahi bana so ni ka fita harkata." A hankali ya k'ara matsota bak'in shi ya saita cikin k'annen ta iska ya d'an hura mata cikin rauni da rawan murya yace. "Ki tausawa min Ummul khairi ki jik'aina ki tallafa min ki bani hak'k'ina Khairi karki zamto silar sani cikin wani hali." tureshi takeyi tana "Ni ba ruwana da halin da zaka shiga in saka cikin wani halin ko kasa kanka ka sakeni in auri wanda nake so kamai kaje can ka nemi wacce zata soka." cikin rawan murya kamar zaiyi kuka yace. "Khairi ki tausayawa mijinki Ummul nifa d'an uwanki ne zakiso na cutu plzz kiyi hak'uri ki amince dani Ummul bazan cutar da keba karki cutar dani ki barni na rab'i jikin ki , in ban rab'eki ba wa zanje in rab'a?." jin yadda yake magana yana cakud'ata da juyata yasa ta rink'a kuka tana birgima har saida ya saketa sannan ya zauna gefen ta yana mai karkarwa, ita kuwa ganin haka ta mik'e ta koma parlour. Daga wannan ranar haka suke rayuwa kullum da salon azabar da Ummul ke shirya wa Hamma Umar d'in shi kuwa gaba d'aya yana rayuwa ne cikin tarin bukarta yayinda hakan ya k'ara bawa Ummul damar juya shi haka kwana ki suna tafi mokonni sunja har sun fara irga watanni, Hamma Umar kuwa har yau baisan menene dad'in aure ba shi kuwa bai iya kai k'araba bare ya kai karanta, Anty Halima na yawan kiran Hamma Umar tace ya Ummul ta nitsu ko? sai yace mata ehh ba komai fa, ita kuwa Anty Halima bata gamsuwa hakan yasa tana yawan zuwa weekend toh hakan yasa kab ta lura da zaman da suke yi. ya Usman kuwa tunda akayi auren yak'i zuwa a cewarsa sai Ummul ta dena kuka, Hamma Umar kuwa rana d'add'aya ne baya zuwa cikin pataskum shida k'anin shi sunyi ta hira yana kula dashi kamar da sukan je gun Amminsu, su wuni. Yau Saturday tun safe Anty Halima da Hajjajo da inna da Aliyu suka shirya zasu je gidan su Hamma Umar d'in , Hajjajo kuwa ta dage sai dai Ya Usman ya kaisu , dolen shi a hakan badon yaso ba ya kalli Hajjajo tare da cewa. "Toh sai ku jirani na shirya ai Hajia Yawo." murmushi tayi tare da cewa. "Zamu jira jeka shirya, dan ni nafi yarfa da tuk'in ka kaida Umaru, Adam gudune dashi Abubakar ko motarsa kamar zai fire in mutun ya shiga." Murmushi kawai yayi ya tafi part d'in su, yana zuwa wonka ya shiga amman ya kasa sai kife kanshi da yayi a jikin gini ya rink'a wani irin kuka mai cin rai zuciyar shi na harbawa da k'arfi zuwa yanzu Ya Usman shi kad'ai yasan idan yayi tarin yakan ga jini amman yak'i gayawa kowa dan ya naga shi lokacin sane ya kusa. Haka yasha kukan shi sannan ya shirya ya fito suka tafi idanun shi na cike da begen ganin Ummul d'in. A gidan Hamma Umar kuwa yau kwana yayi cikin takura haka ya wayi gari a buk'ace bayan ya dawo masallaci d'akin shi ya wuce da niyar ko zai samu yayi bacci amman ina baccin yak'i zuwa, dole ya fito ya nufi d'akin nata yana shiga ya haggota tana zaune bakin gado cikin sanyi ya zauna gefen ta, shiru yayi yana kallon ta, ita kuwa tab'e baki tayi tare da harara shi k'asa k'asa dan ta rigada tasan damuwar shi ita kuwa ta naga ta nan zata cuzguna mishi, ajiyan zuciya ya sauk'e tare dasa hannun shi ya kamo nata cikin rawan murya yace. "Ina cikin matsala dan Allah ki taimaka min wallahi na fara cutuwa da rashin kulawar ki Ummul." cikin ko in kula ta mik'e taje gaban dressing Mirror ta tsaya tana gyara gashin kanta, mik'ewa yayi tare matsowa bayan ta suna kallon juna ta cikin madubin hannun shi yasa ya tattara gashin nata a hankali yace. "Ki tsammin aron lokacin ki da jikin na d'an wani lokacin ta haka zaki ceci lafiya ta." juyawa tayi a tsiwace zatayi magana kenan ya fizgota jikin shi, cikin rawan jiki ya had'e bakin su wuri d'aya, ido Ummul ta zare jin yadda Hamma Umar d'in yake mata wani irin hort kissi , cikin zafin nama ta tureshi ta koma jikin mirror ta tsaya tana rawan jiki tare da kallon yadda Hamma Umar d'in ya birkice gaba d'aya lips d'in shi sunyi jazir sai shek'i suke ida nunshi ma sai shek'i suke alamun sun ciko da k'ollah, ido ta kuma zarowa ganin ya zare jallabiyan jikin shi ya nufi kanta yana cewa. "Zan karb'i hak'k'ina Khairi tunda na lura baki da tausayi so kike ki kashe ni." kai ta rink'a juya mishi tana cewa. "Karka matsoni wallahi bana so." Bai kulata ba sai k'ara matsota yakeyi ganin haka yasa cikin sauri ta lalubo kolban turaren dake kan mirror, tana nuna mishi tana cewa. " karka isoni Hamma Umar ka fitan min a d'aki." bai kulata ba don shi a zaton shi ko buga mishi kolbar zatayi, ita kuwa yana iso ta cikin tsoro da mugunta ta saiti idanun shi ta dannan bak'in turaren feesssh sai cikin I.... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1⃣6⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *S*ai cikin idanun shi, da k'arfi ya rumtse idanun tare dasa hannu ya damk'e kanshi da hannu. bibbiyu kai d'in ya rink'a juyawa tare da yin layi cikin wani irin azaban da bazai misal tuba gaba d'aya jikin shi b'ari yakeyi duk ta inda hudar gashin jikin sa yake zuface ke tsatstsafowa kwayar idanun shi tamkar zasu zazzago su fad'o k'asa ji yakeyi tamkar rushin wuta aka cusa mai a cikin idanun, ba abin da jikin shi keyi sai rawa daya bud'e bakinshi zaiyi magana sai ya kasa sai lips d'in shi suyi ta rawa tamkar maijin sanyi a haka ya rink'a juyu a cikin d'akin har yaje bak'in gado lokaci d'aya kuma ya rink'a murza kanshi a jikin gadon dan azabar da yakeji, Ita kuwa Ummul da fari murmushi tayi ganin yadda ya rumtse idanun shi jikin shi na rawa, amman zuwa yanzu tsoro ya rufeta ganin yadda Hamma Umar d'in yake cikin azaba da gigita gefe ta tsaya jikin ta na rawa cikin tsoro a hankali ta fara cewa. "Hamma! Hamma!." Yana jinta amman bashi da damar amsawa ba abinda yake yi sai murzan kan nashi da yakeyi, cikin dauriya da k'arfin hali ya d'an bud'e idon ihu Ummul tayi cikin firgicin ganin yadda kwayar idanun nashi sukayi jazir tamkar zasuyi aman wuta sun fiffito woje sun hargitse, shi kuwa Hamma Umar bud'e idon daya d'an yi sai da yaji k'ahon zuciyarshi tamkar zata dare dan iskar da ta d'an shiga cikin ido cikin sauri ya sake rumtse idanun ya k'ara danna kanshi a kan gadon, Ummul kuwa gaba d'aya ta tsinke sai kuka ta saki da iya k'arfin ta tana kiran shi tana, "Hamma Umar ka tashi! ka tashi mu tafi hospital. " Ganin yadda gaba d'aya ya fara sakewa ne yasa ta sake sakin wani k'ara mai k'arfi. Dai-dai lokacin Ya Usman kuwa yayi parking a harabar gidan jin yadda Ummul ke kuka da k'arfi yasa cikin zafin nama ya fito da sauri ya nufi cikin gidan yayin da Aliyu ke binshi da gudu, suna shiga parlour Ummul kuwa tana fitowa a nufin ta zata d'ebo mai ruwan sanyi ya woke idon, ganin ya Usman d'in ne tayi sauri taje gareshi cikin kuka da tsananin tsoro da firgici ta rik'e hannu Usman tana buga k'afafun ta da k'arfi tana kuka murya na rawa take cewa. "Ya Usman Hamma Umar! ya Usman Hamma Umar." shi Usman har ga Allah a zaton sa ko laifin tayiwa Umar d'in ya d'an razanata shiyasa take kuka, Aliyu kuwa tunda yaga yadda take kukan kawai sai ya nufi d'akin da take ta nunawan, ya shiga ya haggo Hamma Umar d'in yadda yakeyi da gudu ya juyo parlour cikin tsoro yace. "Ya Usman Hamma Umar baida lafiya fa zo kaga yadda yake." dai-dai lokacin kuma su Inna da Anty Halima da Hajjajo suka shigo jin abin da Aliyu ke fad'a yasa suka nufi cikin d'akin, suna shiga Usman ya tallabo d'an uwanshi a jikin shi cikin rawan murya da bugawan zuciya yace. "Hamma na! Hamma Umar ! d'an uwana ! me yake faruwa da kai Hamma Umar kayi min magana Hamma Umar meke faruwa?." Anty Halima ce cikin rawan jiki ta kira doctor Abbas abokin Hamma Umar d'in, sannan ta juya ta kalli Ummul dake ta zare ido jiki na rawa alamun rashin gaskiya cikin tuhuma Anty Halima ta buga mata tsawa tare da cewa. "Ki baryi mana kuka ki gaya mana meke damun shi me ya sameshi?." jikin Usman ta kuma matsowa ta kalli Hajjajo da inna da suke ta kuka, Aliyu kuwa gaba d'aya jikin shi rawa yake ganin yadda jikin Hamma Umar d'in ke rawa, tsawa Halima ta kuma buga mata cikin watsa mata harara, k'ara rik'e hannun Usman tayi, shi ma Usman da yake rugume da d'an uwanshi cikin rawan murya yace. "Ummul me ya samu Hamma Umar? meke matsa ciwon?." k'ara rik'e hannun Usman d'in tayi cikin rawan murya tace. "Ya Usman idonshi ne yake mai ciwo." cikin mamaki da k'arin tuhuma Anty Halima tace. "Me ya samu idanun nashi? yaushe ya fara mishi ciwo? me a cikin idanun ? nasan dai Hamma Umar baida ciwon ido, Amman ji yadda yakeyi kamar Wanda maciciji ya tsirta mishi dafi a cikin idon, me ya samu idon ina tabbayarki kinyi shiru." baki na rawa tace. "Turarene a cikin idon." gaba d'aya kusan a tare suka zare ido woje cikin tsoro sukace "turaren kuma?." "Ehh." ta basu amsa tana rawan murya. jin haka Usman ya rugumoshi cikin sauri yace . "Aliyu jeka bud'e min mota mu tafi asbitin su." Aliyu har ya mik'e Hajjajo ta kalesu cikin sauri tace. "Usman ajiye shi maza d'auki makullin motarka yanzu kaje laying FULANI ka seyo mana madarar shanu wanda ba'a tafasa ba daga nan ka biya Islamic kemis ka seyo zam-zam." cikin juya kai Usman yace. "Hajjajo wad'an nan abubuwan me zasuyi mu tafi asibiti kar turaren nan ya kashe mai ido." Inna ce ta kalleshi cikin k'arfin guiwa tace. "Ajiye shi ka gudu yanzu ka seyosu." toh yace tare da kontar da Hamma Umar d'in sannan suka fita da sauri shida Aliyu, kai tsaye layin filoli sukaje sukayi sa'a kuwa suka samu d'anyen madarar shanun daga nan suka seyo zam-zam sannan suka nufi gidan, a gidan kuwa doctor Abbas yazo tun bayan fitan su Usman amman Hajjajo ta hana a sa mishi komai, dole Dr ya hakura yana jiran dawowan su Usman , su Inna da Hajjajo kam gaba d'aya basuyi tunanin ya akayi turaren ya shiga idanun shi ba, Anty Halima kuwa tun tuni ta zargi k'anwarta bare da taga kolban turaren a tsakiyar d'akin. Su Usman na dawowa Hajja tace, a had'a zam-zam d'in da madarar shanu a bashi yasha , haka suka had'a suka bashi yasha, a hankali ya fara jin zogin da zuciyarshi keyi yana raguwa, sannan ta kamo hannun shi cikin sanyi tace. "Farouq." cikin rawan murya yace. "Na'am." "Alhamdulillah." Inna tace sannan cikin jin k'arfin guiwa tace. "Halima je kitchen nasu ki kawo roba mai d'an girma." "Toh" tace tare da ficewa da sauri , tana kawowa Hajjajo ta ajiye mai robar a gaban shi sannan ta matso da koryar madarar shanun, cikin kula tace. "Ga madarar shanu k'asa hannun ka a ciki ka rink'a d'iba kana wonke idanun ka bud'e idon." "Toh." yace sannan ya sunkuya kan robar ya ciki tafin hannushi da madarar sannan ya sunkuyo da kanshi idanun shi ya manna cikin ruwan madarar shanun sannan ya bud'e kwayar idanun a cikin ruwan madarar, wani irin zafi yaji ya ziyarci ruhinshi da zuciyarshi, gaba d'aya saida ya rink'a karkarwa hannushi d'aya yasa ya kamo hannun Ummul dake durk'ushe a gefen shi wanda shi baisan waya rik'e ba, sannu su Hajjajo suka rink'a jera mishi ya Usman kuma yana zuba mishi madarar shanun a haka duk wanda yasa idanun a ciki sai ruwan madarar yayi bak'i a hankali har ya fara yin ja har ya zamo inyasa idanun a cikin ruwan madarar baya canza launi haka kuwa a take idanun nashi sukayi fari tas, har kaman sunfi da d'in fari, sannan aka mik'a mishi goran zam-zam ya k'ara woke idanun sai gashi sun fito ras, Dr Abbas ne ya kalli doctor Umar Farouq cikin kula yace. "Kana ganina kuwa?." Murmushi Hamma Umar yayi tare da cewa. "Sosai ma kuwa ganina normal har kamar yafi na da." ajiyan zuciya dr Abbas yayi tare da cewa. "Tabbas muna da manyan likitoci a kusa ga magani mai sauk'i gaskiya nayi mamaki tsoffi sun zama likiticin babban doctor Umar." dariya sukayi baki d'aya sannan Hajjajo ta kallesu cikin yin k'arin bayani tace. "Ko maciciji in ya tsirtawa mutun yawunshi a idanun haka akeyi kuma da izinin Allah mutun zaiyi ras haka kuwa ko turaren ko wani abu mai Carmichael zakaga gubar zatabi jikin nonon." Dariya Usman yayi cikin jin dad'i yace. "Aiko munga zahiri." da haka Dr Abbas ya tafi, sukuwa parlour suka dawo suka zauna suna ta jira, Anty Halima kuwa gaba d'aya hankalin ta na kan UMMUL da Hamma Umar ta lura sarai da yadda Ummul ke yawan satan kallon Hamma Umar d'in shi kuwa kamar baima san da ita a wurin ba, hakan yasa ta k'ara zargin Ummul d'in. Anty Halima ce ta shiga kitchen ta fara yi musu girgi, Sai daga baya ta kira Ummul dake zaune kan dinning table ita da Aliyu suna lallatsa laptop d'in ya Usman, ta shiga kitchen d'in ta kalleta a fakaice tace. "Sarauniya kece da bak'in nice da shiga kitchen ko kunya babu kin zauna kina danne-danne, ga maggi ki b'are min, sannan ki wonke fruits dinnan ki kaiwa su Hamma Umar d'in da su Hajjajo." "Toh.' tace cikin sanyi sannan ta fara b'are margin dan ta lura Anty Halima tana tuhumarta gashi sai harara take watsa mata, kuma ta sani in Anty Halima ta gane itace ta fesawa Hamma Umar turaren a idanun shi tohfa ta shiga tara tasan ya Adam zaiji in kuma yaji Abban su zaiji inko sukaji shikenan sai buzunta. tana gama b'are margin ta mik'a mata sannan ta wonke fruits d'in ta shiryasu a pilet guda biyu sannan ta nufi parlour dasu, tana fita Anty Halima ta jawo robar da ta sa mata magin a ciki da niyar zata sa a girkin nata, sai taji robar tana k'amshin turare, k'ara shinshinar robar tayi aiko k'amshin kam rasa taji shi, kai ta jinjina tare da cewa. " ba shakka zargina ya tabbata Ummul ce ta fesawa Hamma Umar turaren a idanun shi." kai ta kuma juyawa tare da cewa. "Ummul banso had'a ki da ya Adam ba amman kin jawa kanki dole in gaya mishi." Ita kuwa Ummul a parlour tana shiga taji Hajjajo da Inna suna. "Wai ni abin mamaki Farouq ya akayi ka fesa turaren a idanun ka? kaiba yaroba." baiyi magana ba sai latsa woyar shi da yakeyi, Ita kuwa Ummul gaba d'aya jikin ta ya d'auki b'ari tana jin tsoron kar Hamma Umar ya fad'i abinda ke faruwa a tsakanin su, Inna ce ta kuma kallon shi cikin tausayawa dan ita tasan Umar da zurfin ciki koma menene ba fad'a zaiyi ba a hankali tace. "Ko garin fese-fesen turaren nan shine yaje ya fesa a idanun shi, tunda shi mutun ne ko yaushe ka jishi da turaren a jikin shi." Usman ne ya girgiza kai cikin kula yace. "A a kam ba yadda za'ayi ya fesawa kanshi turaren a cikin idanun shi ai ba yau ya fara mu'amalan tuwa da turaren ba ." ido Ummul ta kuma zarowa dan ganin kamar duk sun ganeta, sai kallon Hamma Umar d'in take cikin yanayin ya rufamata asiri, stool ta jawo gaban shi shida ya Usman ta ajiye musu pilet d'in fruits d'in sannan ta d'an dago cikin rawan ido da suka ciki da k'olloh alamar ka rufamin asiri, shi kuwa fuska ya tsuke cikin kauda idanun shi a kanta, gaban su Hajjajo taje ta ajiye musu nasu sannan ta zauna tana fuskantar Hamma Umar d'in da alamun neman al'farma, Hajjajo ta kalleshi tare da cewa. "Farouq ana maka magana kayi shiru ya akayi ka fesa turaren a idanun ka." Kai ya juyo cikin sanyi yace. "Ummul ce....!" ido Ummul ta zaro woje cikin rawan jiki sai hawaye car-car a idanun ta, Su Hajjajo kuwa suma ido suka zaro cikin kallon shi sukace Ummul ta fesema turaren?. " Fuska ya tsuke tare da cewa. "Ni kam bance ba kaji tsohuwa fa ki tsaya kiji me zance mana." Usman ne ya tsura mishi ido sannan ya kalli Ummul dake ta rawan jiki ya kuma kalli Hamma Umar d'in da yake kallon ta sai yace. "Toh Hamma Umar muna jinka." Tsuke fuska ya kumayi sannan yace. "Cewa zanyi Ummul ce zata gaya muku yadda akayi na fesa turaren a idanuna." Ummul d'in suka kallah cikin son jin zance sukace . "Ummul garin Yaya akayi ya fesa turaren a idanun shi?." Tsuru-tsuru tayi da ido shi kuwa kallon ta yake yana d'an murmushi yana jiran me zata ce musu, abin mamaki sai yaga Ummul ta gyara zama ta tokk'oshe k'afafun ta ta d'auki apply ta fara ci a hankali sannan tace. "Hajjajo waifa yaje yayi wonka ne ya fito ya zauna gaban mirror toh sai nazo ina taje mishi sumar kanshi ina d'an goge mishi sumar da towel, shine shi kuma yana ta kallona ta cikin madubin ya d'auki turaren wai zai fesa a sumar kan nashi , ya kuma zuba min ido ta cikin madubin a haka ya fesa turare kam cikin manyan idanun shi." Gaba d'aya su Hajjajo kam dariya sukeyi Aliyu ma sai dariya yakeyi, Usman kuwa anan take ya gano akwai wani abu a k'asa, shi kuwa Hamma Umar mamaki ne ya rufeshi sosai yake kallon fuskar Ummul yana mamakin yadda ta zame kanta a abin ta kuma maida abin da salon so lallai mace bata kad'an, Ita kuwa Ummul kallon shi tayi tare da d'aga mai girma d'aya sannan ta tab'e baki. Anty Halima kuwa baki ta cije tare da juyawa ta koma kitchen d'in ta kwaso abinci ta kawo sukayi suka sha sunata jira da dariya. Haka suka wuni har yamma sannan suka shirya suka fito, a harabar gidan Ummul ta kalli ya Usman d'in cikin zubda k'olloh tace. "Ayyah ya Usman nima zan koma gida." lumshe ido Usman yayi yana maijin wani irin yanayi a ranshi a hankali yace. "Toh ai bani zaki tabbaya ba ki tabbaya mijin ki." Aliyu ne yayi maza ya karb'e maganar cikin tsokana yace. "Ba inda zakije Hajia zauna a gidan ki haka kawai ki koma gida kiyi ta takurani, mu yanzu gidan mu ba wurin zaman ki ehe, Allah ko Hamma Umar karka barta." hararan shi tayi tare da kai mishi duka, shi kuwa sai zillewa yayi ya shiga mota, Ita kuwa cikin zubda k'olloh tace. "Hamma Umar inje ko?." murmushi yayi tare da cewa. "A,a kam in kin tafi wazai tayani zama a gidan?." murmushi Hajjajo tayi tace. "Toh kinji ko? kai Usman shiga mu tafi." haka suka tafi suna yiwa Ummul dariya shiko Usman tun a cikin motar ya k'asa tsaida hawaye shi abin ya had'e mishi ga ciwon zuciya ga k'aunar abinda bazai samuba ga tausayin halin da d'an uwanshi yake ciki dan ya gane Ummul na azabtar mishi da d'an uwanshi a hankali ya fara jin numfashi sa na toshewa, a haka suka isa gida, bayan sun sauk'e Inna a gidan ta suna shiga part d'in su ya wuce kai tsaye kan gado ya fad'a kife kanshi yayi ya rink'a wani irin kuka mai cushe numfashi gaba d'aya jikin shi sai rawa yakeyi lokaci d'aya zazzab'i mai zafi ya rufeshi ciwon kai mai tsanani ya rink'a sarawa zuciyarshi sai har bawa take a d'ari 200, haka ya rufe kanshi. Anty Halima Ku suna shiga cikin gidan cikin sa'a ta samu ya Adam yana zaune a parlour Nenne suna hira da ya Sadik da Nenne Aliyu kuwa bayan Hajjajo yabi, Nenne tana ganin su ta mik'e taje tayiwa hajjajo sannan da dawo ta kai mata abinci da ruwa sannan ta dawo parlour ta gun yaran nata shiko Aliyu tuni ya konta a parlour Hajjajo, Nenne na shiga suka zauna sukaci gaba da hira har zuwa d'an wani lokacin, a hankali Anty Halima ta gyara zama ta fuskanci ya Adam da Nenne a hankali tace. "Nenne! ya Adam Ummul zata kashe Hamma Umar watarana in dai ba'a d'auki mataki a kanta ba." cikin kad'uwa Nenne ta nemi k'arin bayani, itako Anty Halima cikin nitsuwa ta yimusu bayanin zaman Hamma Umar da keyi da Ummul da irin azabtar dashi da takeyi. ya Adam kam hatsala iya hatsala ya hatsala gaba d'aya ranshi ya b'aci ji yake kamar ya fire yaje ya tattaka Ummul d'in, Nenne kuwa tamkar tayi kuka dan takaici, ya Sadik ne ya yayi magana . "Nenne Ummul bata da tausayi in an barta da tunanin ta zata lahanta mana d'an uwa, kawai ya Adam ya gayawa Abba asan matakin da za'a d'auka a kanta." rai a b'ace Nenne tace. "Ni so nake Ku dakamin Ita sai ta dawo haiyacin ta." haka sukayi ta fad'a bayan anyi sallan ishah ya Adam ya samu Abban su a parlour shi cikin nitsuwa ya mishi bayani, sosai ran Abba ya b'aci cikin takaici yace. "Adam ka shirya gobe bayan sallan la'asar zamuje gidan Farouq d'in zanyi maganin abin." Haka suka yita tattaunawa kan lamarin. A gidan Hamma Umar kuwa bayan su ya Usman sun tafi, Ummul ta juya cikin kuka tayi cikin gida a parlour Hamma Umar ya same ta, gefen ta ya zauna cikin sanyi ya rik'o Hanna yenta ido ya tsura mata a hankali yace. "Ummul meyasa kike son sani cikin damuwa Ummul nifa d'an uwanki ne nijinin kine fa, ki tausayawa min ki bar kukan nan ki taimaka min na samu nitsuwa dake a matsayin ki na matata." kwace hannun ta tayi cikin kuka ta nufi d'akin ta tana cewa. "Bana sonka na tsaneka." tana shiga ta rufe k'ofar, Shi kuwa haka ya kwana cikin tsananin begen ta da buk'atuwa, koda gari ya waye haka ya wuni a matse gaba d'aya ya k'asa fita ko kofar parlour har zuwa yanzu karfe 3:30 pm, wonka yayi sannan ya kimtsa cikin k'ananan kaya sannan ya fito parlour, yana zama yaji ana buga k'afa cikin rashin kuzari yaje ya bud'e k'ofar, cikin fara'a ya kalli Abba yace. "Abba barka da zuwa ." Sai kuma ya d'an matsa cikin girmamawa yace. "Abba shigo." Sai ya kuma kalli ya Adam murmushi ya d'an yi sannan yace. "Nayi fushi da kai ai tunda kowa yazo kai kak'i zuwa." Murmushi yayi shima tare da cewa. "Gashi nazo ." "Ba kazo badai ka reko Abba dai." A parlour suka zauna cikin happy yaje kitchen ya kawo musu ruwan da juice sannan yaje bak'in kofar Ummul cikin d'an daga murya yace. "Ummul fito munyi bak'i." Tana jinshi rashin sani yasa tayi shiru tana ta shafa mai da murza jikin ta da turaruka dan yanzu ta fito wonka, shi kuwa Hamma Umar gunsu Abba ya koma yana cewa. "Abba tana zuwa." haka wasa-wasa sai da Hamma Umar ya buga mata k'ofa kusan sau 3 ganin haka Abba ya tabbatar da abinda Halima ta fad'a, cikin hikima Hamma Umar d'in ya zagaya ta dinning area d'in su glass d'in window ta ya bud'e cikin yin k'asa da murya yace. "Ummul Abba ne da Adam suka zo." ido ta zaro cikin tsoro jiki na rawa ta jawo katon hijabin ta nayin sallah ta d'aura kan d'aurin zaninta da ta d'aura a k'irji, sannan tayi bak'in kofar zuciyarta na har bawa tara-tara a parlour kuwa ya Adam ne ya mik'e a hatsale yazo bak'in k'ofar cikin d'aga murya yace. "Zaki fito ko sai na shiga na tattakaki?." jiki na rawa ta bud'e k'ofar, tana fitowa ya Adam ya rink'a zuba mata maruka a fuska, Hamma Umar d'in ne ya daka mishi tsawa cikin fad'a yace. "Adam kana da hankali kuwa? me kakeyi haka." Ita kuwa Ummul gaba d'aya jikin ta b'ari yake hannun ta Hamma Umar yaja suka nufi cikin parlour a gaban Abba suka zauna gaba d'ayan su a k'asa kan carpet, Ita kam Ummul ganin kallon da Abba yake mata ga marukan data sha gun ya Adam sai ta mak'ale hannun Hamma Umar d'in tana b'uya a jikin shi, shi kuwa gaba d'aya baiji dad'in dukan da Adam ya mata ba, cikin kaushin murya Abba ya fara magana rai a b'ace. "Ummul wato ni ban isa da keba ko? wato ban kai na baki umarni ki bi shiba ko? Ummul bansan cewa kinfi karfina ba ashe ban isa da keba bansan cewa kinfi k'arfin yimin biyayya ba Ummul ni mahaifinki ni kike tozarta wa ko? ni kike watsawa k'asa a ido?." kuka ta saki cikin rawan jiki tare da k'ara mik'ale hannun Hamma Umar d'in, cikin kuka. "ta rink'a juya kai baki na rawa kuka takeyi sosai cikin tsananin tsoro tace. " Abba na tuba ka gafarce ni wallahi bazan sakeba Abba wallahi zanbi umarnin ka Abba ka isa dani." Kai ya juya cikin yin mata tsawar da saida ta kife kanta a jikin Hamma Umar d'in cikin fad'a yace. "Da na isa dake da bazaki bijirewa umarnina ba dana isa dake da dole kiyi biyeyya ga mijin dana zab'a miki Ummul ina gab da cireki cikin jerin y'ay'ana matuk'ar ba zaki yi biyayya ga mijin kiba." cikin kuka ta k'ara rik'e hannun Hamma Umar d'in cikin rawan baki tace. "Abba ka gafarceni karka tsine min Abba na tuba zanyi biyayya ga umarnin ka." sai ta kuma kalli Hamma Umar d'in cikin tsananin kuka tace. "Ayyah Hamma Umar ka bawa Abba na hakuri na tuba." sai ta kuma kife kanta tana yin kuka mai cikeda tsoro, haka Abba yayita mata fad'a daga k'arshe ya dawo yi mata nasiha ita kuwa sai kuka takeyi, cikin lallashin Abba yace. "Ummul ki sani nayi miki zab'i na gari don son da nike miki, Ummul ki sani al'jannarki tana k'ark'ashin diga-digin mijin ki Ummul zanyi al'fahari da kene in kin yiwa mijin ki biyayya Ummul kiji tsoron Allah ki sauk'e nauyin mijin ki daya rataya a kanki." haka Abba yayi ta mata nasiha, Ita kam Ummul kuka takeyi mai cin rai tana ga dole tayiwa Abban ta biyeyya, haka Hamma Umar kuwa ya rink'a bawa Abba hak'uri, sannan suka tashi suka nufi hanyar fita, har sun fita Adam ya sake dawowa cikin zare ido ya nunata yana cewa. "Wallahi karki ga yau Abba lallashin ki yayi ni kuwa aka hanani dukan ki next time in na sake jin wani abu wallahi b'allaki zanyi kowa ya huta." ya fad'a yana nuna yadda zai b'allatan kuka ta saki da k'arfi, jin kukan ta ne Hamma Umar ya kalli Abba cikin raunin yace. "Abba Adam fa." Murmushi Abba yayi sannan yace koma ciki reki yar ta isa, ka turo min Adam d'in." "Toh Abba mun gode Allah ya kaiku lafiya." yace sannan ya koma cikin gida, yana shiga Ummul na ganin shi da gudu ta dawo gefen shi hannun shi ta rik'e cikin kuka, shi kuwa Hamma Umar k'eyar Adam ya d'an buga tare da cewa. "Fita ka tafi Abba na jiranka , kuma bama son ziyarar ka indai haka zakayi in kazo." murmushi yayi ya fita yana cewa. "Kin dai ji abin da nace." yana fita Hamma Umar ya maida k'ofar ya rufe, cikin yana yin lallashin da tsananin shauk'i da jin wani irin yanayi na ratsashi ya jawo Ummul ya rugume... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1⃣7⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *T*a tsam a jikin shi hannun shi yasa yana shafa gashin kanta d'aya hannun kuma ya zagoyo bayan ta yayinda ya manna kanta a wuyan shi ya d'an d'aga kanshi sama kad'an yana jin yadda take fidda sautin kukanta cikin tarin bak'in ciki, itama Ummul yau rashin ya Usman mai lallashin ta a kusa ga abin kuka an mata ga ba kowa hakan yasa ta lafe a jikin Hamma Umar d'in ta d'an sa hannu ta zagoyo k'ugunshi da bayan shi ta manna k'irjin ta da nashi tayi luf ta d'an d'aura hab'ar fuskar ta a damtsen hannun shi k'afafun ta kuwa kan nashi k'afafun ta taka ta tsaya ta yadda gaba d'aya a jikin shi take mak'ale gaba d'aya jikin ta tsuma yake tanayin wani irin kuka mai sanyin sauti, shi kuwa gaba d'aya tausayin ta ke ratsashi har cikin ranshi musamman yazu da yaga yadda ta lafe a jikin shi shid'in da ta tsana tana kuka, k'ara rugume ta yayi yana sauk'e ajin zuciya tare da lumshe ido, a hankali ya fara d'aga k'afafun shi wanda nata k'afafun suke a kan nashi a haka ya rink'a tafiya da ita a hankali tana manne a jikin shi tayi luf sai kuka takeyi tana k'ara mak'ale shi, a hankali ya shiga cikin bedroom da ita a hakan, yana shiga ya maida k'afar ya rufe kai tsaye bak'in gado ya nufa da ita cikin sanyi ya matso cikin fridge dake kusa da bak'in gadon yana rugume da itan, ita kuwa tana tsaye kan k'afafun shi ya d'an sunkuyo goran Faro ya d'auka a hankali ya bud'e cikin nitsuwa ya d'an sunkuyo kanta yasa mata bak'in goran murya can k'asa cikin yanayin lallashi yace. "Khairi." ido cike da k'ollah ta kalleshi sai hawaye car-car, shi kuwa ganin hakan yasa mata ruwan sanyin a bak'in ta, ido ta rumtse tare da d'an kurb'an ruwan, saida ta d'an sha kad'an sannan ya zame makin goran ya ajiye a kan fringe d'in a hankali ya zauna bak'in gadon sannan ya jawo pillows yasa a bayan shi a hankali ya konta kan pillows d'in sannan itama ya gyara mata konciyarta a kanshi, ita kuwa har zuwa yanzu kuka takeyi sosai, kai ya rink'a d'an juyawa tare da tsotsar lips d'in shi, idanun shi a lumshe, a hankali yasa hannun shi ya zare hijabin jikin nata ya tureshi gefe, ya rege daga ita sai zanin jikinta, a hankali ya ture d'aurin zanin nata ya d'an yi k'asa ta yadda gadon bayan ta ya bayyana, tattausan tafin hannun shi ya kife a kan k'afa d'unta ya rink'a shafawa tare da d'an bubbugata kad'an-kad'an har zuwa kan bayan ta yanayi cikin alamun lallashi, hakan yasa ita kuwa ta k'ara narkewa a jikin shi cikin tausayawa kanta, a kanshi aka doketa a kanshi aka zageta kuma dashi kawai aka barta a gidan ita kuma tana son a lallasheta dole hakan kuwa tayiwa mahaifin ta biyeyya, shi kuwa jin yadda take fidda sautin kuka da yadda hawaye ke zuba a idanun ta yasa ya d'an d'agota suna fuskantar juna fuskar ta ya d'aura kan tashi fuskar gemun ta kan nashi gemun hancin su na d'an gogar juna hannu yasa ya k'ara matsota jikin shi a hankali ya zaro harshen sa cikin lumshe ido ya d'an laso lips d'in ta da suke ta rawa da shek'i dan kukan da ta keyi, sai kuma ta bud'e idanun ta da sauri ta zuba mishi ido , shima ido ya zuba mata cikin sanyi yace. "Khairi kibar kukan nan haka nan ya isa, kiyi hak'uri ki rugumi k'addarar ki, shin bakya ganin hak'uri shi zaiyi maganin wannan yana yin da muke ciki, Khairi ina son na zame miki gata matukar muna tare zan zame miki GARKUWA bana da nufin cutar dake, ya zanyi k'addara tasa nine silar rabaki da burin ranki, amman abinda nake so ki gane wannan abin da kika gani Rubutaccen al'amari ne tun ina cikin mahaifiyata Allah ya rubuta min kece matata nine mijin ki." sai kuma yayi shiru yana shafa bayan ta, ita kuwa cikin kuka tace, "Hamma Umar nima ina son yiwa iyayena biyeyya na kasa Hamma Umar bani ce nasawa kai k'iyayyarka ba na kasa sonka bana sonka, Mustapha nake so." Rugume ta yayi da k'arfi dan zafin da kalaman ta sukayi mishi cikin zafin ya had'e bak'in ta da nashi cikin lumshe ido yayi mata wani irin zazzafan kissi har zuwa wani d'an lokacin saida yaji tayi luk'us a jikin shi cikin rawan murya kamar mai son yin kuka yace. "Ummul Khairi wata rana ! watara na zaki..! zaki soni, insha Allah watara na zaki soni , na tabbata bazaki dauwa dimun wa da'imu da k'iyeyya ta a zuciyar ki ba, sai dai ko zaki sonki a k'urerren lokaci." kai ta rink'a juyawa murya na rawa tace. "An rabani da wada nake so an had'ani da wanda bana so." sai ta kuma kife kanta a k'irjin shi cikin kuka tace. "Hamma Umar kalli yadda ya Adam ya kumbura min fuskar a dokeni a zageni." hannun yasa ya shafa fuskar tata sannan ya mirgino ta gefe a hankali ya sunkuyo kanta fuskar ta ya rink'a shafawa a hankali cikin taushin murya yace. "Zan rama miki Khairi na kiyi hak'uri da mijin da Allah ya zab'a miki." hannun ta tasa ta kamo nashi ta mana a fuskar ta da tasha marukan ya Adam ciki sanyi ta saki kuka, shi kuwa Hamma Umar daga lallashi salon ya fara can zawa tuni ya fara koyar da ita darrusa masu ratsa jiki tana konce tayi zuru-zuru da ido gaba d'aya jikin ta sai rawa yakeyi hawaye kuwa kamar an b'alle bak'in pompo gaba d'aya ta firgita ga tsoro ga k'iyeyya a hankali ta fara tureshi cikin kuka da rawan jiki da murya tace. "Wayyo Allah na Hamma Umar bana sonka ka barni kar kayi min Katanga da Mustapha." hannayen ta ya kamo ya d'aura kan wuyan shi sannan ya cusa kanshi a k'irjin ta murya na rawa cikin rauni yace. "Bazan cutar da keba Khairi karki cutar dani kiyi hak'uri ki sama min nitsuwa ki tuna hak'ina yana kanki, ayyah Ummul ki amshi kaddararki kinga bamu san me yake boye cikin Rubutaccen al'amarinmu a nan gaba ba Khairi inci darajar aure mana Khairi ki tuna yanzu kika yiwa Abba al'k'awarin yin biyeyya ga zabin da ya miki." kuka ta saki da sauri mai cike da k'una cikin kukan ta k'ara k'amk'ameshi cikin sakin kuka mai d'auke da wuya damtsen hannun shi ta rik'e tare da cusa kanta cikin k'irjin shi, shi kuma Hamma Umar zuwa yanzu yayi nisan kiwo ya shiga duniyar dake cike da al'khairai bayaji baya gani bare ya fahimci halin da take ciki, a wannan ranar a wannan yamma cin daga lallashi Hamma Umar ya am she budurcin Ummul, gaba d'aya jinshi yake cikin tarin farin ciki da nishad'i jinshi yake tamkar an mishi bushara da al'jannah ba abinda yake iya furtawa sai k'amk'ameta ya keyi cikin sauk'e ajiyan zuciya yanata kissing nata tako ina tare da binta da shafa mai cike da tsantsar kulawa da farin ciki gaba d'aya ya kasa magana sai wani shunshunata yake tako ina, ita kuwa kukan abu da yawa take yi kukan wahala daya bata had'i da kukan takaici ga tarin tsanarsa da ta k'aji dan ya rabata da budurcin ta da ta dad'e tana yiwa Mustapha tana dinshi ga bak'in cikin dukan da ya Adam yayi mata ga tsoron fushin da Abban ta yake yi da ita, gashi ko numfashi ta fitar sai taji kamar tana fame ciwon da raunin da Hamma Umar d'in ya ji mata hakan yasa ta saki kuka cikin disashewar muryar tana kai mishi bugu tako ina cikin raunin da take cikin, tana kuka da rawan jiki tana. "Shi kenan Hamma ka cuceni ka zalum ceni na saneka nacema bana sonka!." baya iya gane halin da yake ciki bare ya sarara mata, ganin bai sarara matan ba ga wuya iya wuya tana sha hakan yasa ta rik'o wuyan shi cikin kuka da rauni murya na rawa tace. "Hamma ! Hamma kayi hak'uri na tuba kayi hak'uri Hamma kaina k'afafu na baya na cikina ciwo Hamma zaka kashe niii." sai kuma ta tura yatsun ta cikin sumar kanshi tana murzawa da k'arfi tare da murza kai idanun na zubda k'ollah sai wani irin numfashi take fizga da k'arfi, a haka har zuwa wani lokaci mai tsawo, sannan hankalin Hamma Umar ya fara dawowa jikin shi cikin rawan jiki ya zauna da k'er sannan ya jingina da jikin kan gadon jiki a mace ya jawota cikin shi ya rugume ta tsam a k'irjin shi kanta ya rink'a shafawa har zuwa gadon bayan ta, kanshi kawai yake juyawa yayin da tausayin ta ke ratsa mishi jiki da zuciya yana jin yadda hawayen ta ke zuba a kan k'irjin shi, k'ara matsota yayi cikin wata iriyar muryar da bata tab'a jinshi da ita ba yace. "Ana aspet ya zaujati na, ki gafar ceni Khairi na banyi nufin wahal dake haka ba yana yine ya juya dani har na k'asa control d'in jikina da zuciya ta ki yarda dani banyi nufin jikkata kiba." kukan ma gagarata yayi sai hawaye tana jin wata iriyar kunya mai tarin yawa da bak'in ciki yadda take manne jikin Hamma Umar a gida d'aya d'aki d'aya gado d'aya blanket d'aya sannan kan k'irjin shi fatarta da tashi fatar suna manne da juna duk wani sashi na jikinta ya zama mallakin Hamma Umar ba Mustapha ba , shi kuwa gaba d'aya ya gigice sai kissing nata yake tako ina murya na rawa yake cewa. "Khairi na nagode Allah ya miki albarka Allah ya faran ta miki kamar yadda kika faran tamin Allah ya sanya haske a rayuwar ki." sai ya kuma d'ago kanta ya manna bakin shi a nata yayi kissing na lips d'in ta sannan ya sumbaci goshin ta ya dawo wuyan ta har zuwa k'irjin ta inda nan take ya k'ara susuce wa, hannun shi ya murza kan fatar cikin ta, cikin tsananin happy yace. "Allah yasa nayi ajiyan baby, Khairi ina son inga gudan jinina Allah yasa kin samu ciki a wannan ranar Khairi zaki so d'an da zamu haifa ko? dan Allah shi kam ki sonshi d'an kine jinin kine karki tsane shi, zaki son shi ko??? ."... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1⃣8⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Jama'a ku tayani duba a cikin wad'an nan sunaye ina sukayi kama Aysha Ali Garkuwa da Safiya Abdullahi musa huguma ni dai a ganina basa kama toh amman me yake rikita wasu Reedars da suke zuwa gareni a matsayin nice Safiya Huguma? kuma abin mamaki ko nace musu ba ita bace basa yarda wai sai suce bana dai son yin magana dasu ne, hoh ni Aysha na koma Safiya GARKUWA ta koma Huguma Safiya fans naki na sani ciwon kai ki kawo agaji sun cika min gida duk sun shanye min d'an furana da nono mai sanyi na koresu sunki tafiya wai sai dai na kaisu hareki wayyo ni GARKUWA na karb'i bak'ina na karb'i na Huguma wallahi sunk'i yarda kan cewa ba Huguma bace ban san ina suke samo number ta ba ace musu tak'i ce, Reedars kunji Safiya Huguma itace mai Abadan GARKUWA kuwa itace mai Rubutaccen al'amari Allah yasa Ku gamsu da wannan bayanin na kan pagen ga Ku ruga a guje kuje ga Huguma na tabbata zata karb'eku cikin aminci wlh ni GARKUWA ba nice Huguma ba Safiya ki shirya amsar bak'in ki zan korosu da sandar Fulani zan basu tukuicin man shanu da nono🤝😍😘* *k*ai ta juya cikin wahala da galabai ta, shi kuwa k'ara rugume ta yayi cikin aminci da cikar farin ciki, murya a raunane yace. "Khairi d'an Allah kar k'iyeyya ta tashafi Abinda Allah zai azurta mu dashi." bata kulashi ba sai yunk'uri tayi da nufin tashi zaune amman kuma sai ta koma jikin shi da k'arfi ta fad'a kanshi cikin rawan jiki da murya ta saki wani sabon kuka hannayen shi ta damk'o da k'arfi har tana karkarwa murya a raunace tace. "Wayyo Allah wayyo Nenne na wayyo ya Usman Hamma Umar ya ketamin haddi ya kasheni." abin ma dariya ya bawa Hamma Umar wato ita a zaton ta zata iya tashi hartayi rashin mutunci sai kuma shegen raki da rauni, ruggume ta yayi yana murmushi fuskar cike da happy har cikin ranshi yake jin dad'i karb'e budurcin Khairi sarkin tsiwa yana ga yanzu kam zatayi mubaya'a ta hak'ura a zauna lafiya, kanta ta kife kan damtsen hannun shi cikin takaici ta datsa mishi cizo mai zafi, idon shi ya rumtse da k'arfi tare da sake mata hannun cikin rauni yace. "Ahhh shihhhhh Khairi cijeni in har cizon zaisa ki huce amman dan Allah karki sake cewa na keta miki haddi shin kin manta cewa, *ana zaujiki* ni mijin kine amman kike cewa na keta miki haddi." bata kulashi ba sai kukan ta kuma sakewa ganin haka ya mik'e zaune cikin tarin kunya ya jawo blanket ya rufe su dan shi da kanshi bai san meyasa yake k'asa control d'in kanshi ba a kan Khairi sai yayi abu yazo yana jin kunya shi da kanshi bai san ma cewa shi yana da shawa'a ba da har zata sashi zaucewa, ido ya lumshe ya jawo bosses d'in shi ya saka a hankali ya jawo ta jikin shi k'irjin ta ya manna kan nashi cikin kauda kai ya jawo zanin ta ya d'aura mata a jikin ta sannan, ya kontar da ita gefen shi ya d'an yi mata rumfa da k'irjin shi bakin su ya manne wuri d'aya tare da tallabo kanta yayi mata wani irin kiss mai cike da sak'onni masu kauda tunanin mutun, itama shiru tayi tana kallon fuskar sa shiko idanun shi a lumshe, a hankali ya zame bakin shin tare da bud'e idanun shi da tuni sun sake k'ak'k'an cewa sunyi jazir sai ya kamo lips d'in shi yana tsotsa tamkar yaro yana kallon ta cikin wani irin yanayi sai ajiyan zuciya yake sauk'e wa, itama idon ta rumtse sannan ta kamo lips d'in ta daya gama tsotsewa yanzu ta ciza ta ciki kuma taci gaba da tsotsar lips d'in, sunkuyo wa yayi tare da kauda kai hannun shi ya cusa cikin k'irjin ta bak'in shi ya kai dai-dai kunnen ta cikin rad'a yace. "Zo muje in miki wonka Khairi zakiji sauk'i." shiru tayi tana kallon fuskar shi d'aya kawar tana jin yadda yake murje mata k'irjin zuwa yanzu mamaki Hamma Umar yake bata ga wani irin tsoron shi da take ji, Shi kuwa ganin batayi magana ba ya sunkuyar da kanshi ya d'an laso lips d'in ta sannan ya juya ya nufi toilet ita kuwa ido ta tsura mishi tana kallon surar jikin shi tana mai cike da takaici wai Hamma Umar ne mijin ta , ruwan d'umi ya had'a sannan ya dawo ya d'auke ta cid'ak, suna shiga cikin toilet d'in ya tsayar da ita, sai kuma yayi maza ya ruggumota jin wani irin k'ara da ta saki sannan ya kalli k'afafun ta gaba d'aya sai rawa suke kamar mazari alamun bazasu iya d'aukar taba, k'ara ruggume ta yayi cikin tausawaya ya rink'a shafa kanta tare da cewa, *"Aaspet* sannu." rugume shi itama tayi tana yarfa hannu , k'ara matsota jikin shi yayi yana cewa. *"Bas bas bas* ya isa ya isa kiyi hak'uri *bitirajjaki* khairi, ki dakata." kuka takeyi har lips d'in ta na rawa dan azabar da takeji, kamota yayi cikin kauda kai ya kunce zanin sannan ya kamo hannun ta suka shiga cikin baf d'in ruwan d'umin a hankali ya zaunar da ita sannan shima ya zauna ya rink'a gasa mata jikin ta da ruwan d'umin yanayi yana cemata. *"ana aspet*" ita kuwa hannun shi kawai ta rik'e gam ta cusa kanta a k'irjin tana jin ruwan d'umin yana ratsata, a haka cikin lallama ya mata wonka tsab sannan yasa ta tayi wonkan tsaki shima wonkan yayi sannan ya jawo towel ya d'aura a k'ugunshi sannan ya dagota itama ta tsaya lokaci d'aya sai hawaye car-car a idanun ta, sunkuyo wa yayi yana kallon yadda har yanzu k'afafun ta na rawa a hankali yace. "Har yanzu kina jin zafi?." gini ta dafa ta fara tafiya a hankali tana yarfa hannu d'aya hawaye na zuba murya can k'asa tace. "Mugu kawai ka ketani ba ko imani kana kuma cemin har yanzu inajin zafi." ya jita sarai amman sai yayi murmushi ya d'ago ta ya kaita d'aki zanin gadon ya tattara ya duk'un k'une yana b'ata fuska dan baya son ganin jini a rayuwar sa tsikar jikin shi ke tashi, wani zanin gadon ya shimfid'a bayan ya gyara wurin ya zaro doguwar riga ya zira mata sannan ya kimtsa kanshi, yana gayawa ana kiran sallan maggariba d'an haka ya shimfid'a musu carpet yaja su sukayi sallan makariba tare da insha don lokacin ishan yayi, sannan ya mik'e ya shiga kitchen ferfesu ya had'a mata da tea sannan ya gasa mata nama ya had'o komai kamar mai jego yazo ya ajiye a parlour, cikin d'akin ya koma konce ya sameta kan carpet d'in tana ta rawan sanyi gaban ta ya tsuguna cikin kula yasa hannu ya shafa goshin ta da wuyan ta zafi jau yaji alamun zazzab'i, baiyi magana ba sai dagota yayi ya dawo parlour da ita zama yayi ya jawota jikin shi cup d'in tea d'in ya jawo a hankali yace. "Khairi dan Allah ki dena kukan kisha tea sai in baki maganin insha Allah zaki samu sauk'i." kai ta juya mishi alamun bazata shaba sai hawaye, matsota yayi jikin shi cikin tsuke fuska yace. "Zaki Sha ko sai nayi na biyu?." cikin rawan murya tace. "Hamma Umar zan mutu kayi hak'uri." "Toh kisha tea in baki maganin." tsoron shi yasa ta d'an sha tea d'in sannan taci naman kad'an daga nan ya bata maganin, sannan ya kunna TV a inda ya samu tashar Bollywood sun Sa film d'in *kal ho naa ho* sai ya jawota jikin shi ya rugume ta yana jin yadda take rawan sanyi jikin ta kamar wuta sai ajiyan zuciya take sauk'e wa, tana manne a jikin shi tana kallon tv a haka har bacci ya tafi da ita. 11:00 pm ya mik'e da ita a jikin shi dan yaji gari yayi shiru kai tsaye d'akin shi ya wuce da ita yana zuwa ya kontar da ita kan gadon shi daya sha gyara sannan ya dawo parlour ya kashe komai na wuta sannan ya koma d'akin shi, wonka ya sakeyi sannan yayi al'wala yazo yayi ta nafilfili har zuwa 12 sannan ya jawo qura'anin shi ya fara karatu cikin sauti mai sanyi murya cike da tauhidi da tajwidi gaba d'aya ya hallarto da kushi'inshi, haka yayi ta karatu har zuwa k'arfe 2 na dere sannan ya mik'e a hankali ya zauna bakin gadon yana kallon yadda taketa duk'unk'unewa alamun sanyin takeji, konciya yayi gefen ta cikin sauk'e ajiyan zuciya a hankali ya jawota gare shi, hannun shi yasa yana shafa fuskar ta da ta d'an kumbura tayi ja dan kuka, ita kuwa cikin baccin taji d'umin jikin mutun kusa da ita haka yasa sai k'ara matsoshi takeyi tana caku moshi, ido ya tsura mata ganin yadda ta tsuke bak'in ta ta manna shi kan k'irjin shi murmushi yayi ganin gaba d'aya ta cakumo wuyan shi, ta rik'e shi gam sai murza k'afafun ta takeyi a jikin shi, haka yasa lokaci d'aya ya fara dabur cewa jawota ya kumayi sannan ya cusa hannun shi cikin rigar ta ya rink'a d'an yi mata tausa, ita kuma sai mik'a takeyi tana lumshe ido, a haka ta k'ara tunzuro buk'atar shi, tuni ya susuce a kanta jiki na rawa ya zare mata rigar sannan ya rink'a murzata da juyata, cikin gigin bacci ta ji salon daya zarce tunanin ta a hankali ta bud'e idanun da sauri ta fara tureshi a firgice ta rik'o hannu shi murya na rawa tace. "Wayyo Allah Hamma Umar ka tausaya min mana kasheni kake son yi ko? zafi wallahi." rufe ta yayi da k'irjin shi a hargitse yace. "Ahh! Ahhh! bazaki mutu ba kiyi hak'uri ki nitsu bazan ji miki ciwo ba wallahi zakiji ba wuya." ina ita kam tureshi takeyi tuk'uru, shiko ya rigada ya gama d'imau cewa, dan haka bai sarara mata ba har saida ya samu nitsuwa , ita kuwa gaba d'aya ta sake bata ko numfashi mai k'arfi, haka ya kwana mak'ale da matarsa sai sanya mata al'barka yakeyi yana shafa kanta, bai san cewa ita kam Ummul bata cikin hayya cinta tana jinshi tana kuma ganin shi amman ta k'asa magana bare kuka sai hawayen dake bin fuskar ta ko yatsarta bata iya motsawa, A haka suka kwana sai da Asuba da yayi mata wonka ne ta dawo haiyacin ta tun a toilet d'in ta rink'a kuka tana magiya da rok'on shi, ya maida ta gidan su ita kam zata koma gun Nennen ta, a haka sukayi sallan Asuba suna idarwa ta tasa sabon kuka tana rawan jiki dan yunwa da wahala da bacci ga zazzab'i tace. "Wallahi ni gida zan koma ka medani gun Nenne na dan Allah Hamma Umar ka meyar dani gida." ta k'arishe maganar cikin rauni, shi kuwa ido ya zuba mata tare da cewa. "Meyasa zan medeki gida? en kin koma me zaki ce musu?, kin san Adam kuma inya ganki a gida kin san me zai miki kam ko?." kai ta tonk'oshe cikin raunin fuskar cike da k'ollah da tsoro tace. "Ayyah dan Allah Hamma ka kaini gun Nenne na ka hana ya Adam dukana plxx zanje gun Nenne na." sai ta kuma kife kai jikin gado ta rink'a sheshshek'a, ganin yadda gaba d'aya jikinta ya nuna bata da lafiya yasa ya matso gareta ruggume ta yayi a hankali yace. "Toh ya isa haka kibar kukan bari in had'a miki breakfast ko." zame jikin ta tayi ta zauna tana goge k'ollan dake bin fuskar ta, shi kuwa kitchen ya shiga ya had'a musu breakfast sannan ya ajiye musu a parlour , amman fir tak'i cin abin cin tuni mayafin ta na hannun ta ita dai a tafi, haka yasa shima baici komai ba wonka yayi ya shirya sannan ya dawo parlour, tana ganin shi ta mik'e tare da binshi da harara k'asa k'asa, shi kuwa ido ya zuba mata ganin k'atuwar jakar da ta ciko da kayan kamar wacce zata koma, gashi ko tafiya da k'er takeyi ba yadda baiyi ba ta ajiye jakar tak'i ta rege kayan ma tak'i, murmushi kawai yayi ya karb'a mata jakar suka fita sannan ya rufe gidan, suka shiga mota suka kama hanyar potaskum d'in, tunda suke tafiya ba wanda yayiwa d'an uwanshi magana. A gida potaskum kuwa gaba d'aya mutanen gidan kowa na y'an harkokin shi, Abba ma yau yana gida Ya Adam da ya Sadik da Aliyu duk suna parlour Nenne ita kuwa Nenne tana parlour Abba ya Usman kuwa yana parlour Hajjajo suna d'an tab'a hira duk da zuciyar shi bata da nitsuwa, gaba d'aya tunanin shi na kan Ummul lokaci guda numfashi sa ya fara cushewa , jin hakan yasa ya sallami Hajjajo ya fita dan yaje ya b'uya yayi ta kuka dan in numfashi sa ya fara cushewar da tunanin sai yayi ta kuka yake jin dama-dama, haka yasa kai tsaye ya nufi harabar gidan motar shi ya bud'e ya shiga ya rufe kanshi ya kifa kai a jikin siterin ya rink'a kuka mai ciwo a zuciya. 10:12 na safe Mati mai gadi ya bud'ewa Hamma Umar gate d'in gidan yana shiga gefen motar ya Usman yayi parking, kasan cewa glass d'in motar Usman tintek ne Hamma Umar bai ga Usman d'in a ciki ba, shi kuwa Usman ya gansu so baya son ya fito Hamma Umar yaga fuskar sa a yadda yayi kuka yanzu yasan zai saka d'an uwanshi a firgici yasan Hamma Umar zai gigice in ya ganshi shiko baya sun Hamma Umar ya gane yana da wata matsala. Su Hamma Umar d'in kuwa yana yin parking Ummul tasa hannu ta bud'e marfin motar da niyar zata fice, hannun ta ya kamo da sauri ya jawota jikin kujerar, gyara zaman shi yayi ya d'an juyo gareta tafin hannun shi ya manne da nata tafin hannun ido ya d'an zuba mata cikin sauk'e numfashi sannan ya kuma lumshe idon a hankali yace. "Khairi gudu na kikeyi ko? sauri kike kibar inda nake ko?." hannun ta rink'a k'ok'arin kwancewa ta k'asa dan ya hard'e yatsun ta cikin nashi yatsun kallon ta ya kumayi a hankali yace. "Ke baki iya sallama mijin ki ba ko?." a kufule cikin jin tsanarshi tace. "Eh d'in ban iya ba ba'a koyamin ba." murmushi yayi cikin zafin nama ya fizgota jikin shi tare da matsota sannan ya d'an d'ago fuskar ta, harshen shi ya d'an zaro tare da kad'a mata shi sannan ya lumshe yace. "OK haka nefa Ashe ban koya miki ba, karki damu toho yanzu in koya miki yadda akeyi." ido ta zaro ganin yadda ya ruggume ta baki ta bud'e da niyar mishi tsiwa, sai kuma ta zaro idanun woje jin yadda ya manne bak'in shi da nata yana mata tsotsar lolly pop, shi kuwa sai lumshe ido yakeyi, ya Usman kuwa tunda yaga Hamma Umar d'in nashi ruggume da Ummul a take yaji numfashi sa na fizga zuciyar shi na harbawa da k'arfi kamar zata faso k'irjin shi ta fito zufa ta fara keto mishi tako ina a take jijiyoyin jikin shi sukayi rud'u-rud'u k'irjin shi ya dafe da k'arfi jin kamar ana soka mishi allurai, ido ya rumtse da k'arfin dai-dai lokacin da Hamma Umar yake kissing d'in ta, wani irin tarine mai k'arfin ya turnu k'eshi gaba d'aya ida nunshi suka firfito hannun yasa ya to she bak'in sa wai dan kar Hamma Umar d'in yaji, amman ina tuni tarin ya kufce mishi tarin yakeyi sosai har numfashi sa na fizga da k'arfi tuni ya fara gigicewa yana buga jikin motar, shi kuwa Hamma Umar jin tarin a cikin motar B'iyayen nashi yasa ya zame bak'in shi daga jikin Ummul d'in cikin tsoro da mamaki yadda tarin ya sark'afe mishi da sauri ya nufi gaban motar har jikin shi na rawa ya bud'e marfin motar, yana bud'e wa Usman ya fad'o jikin shi, shi kuwa ruggume shi yayi da k'arfi tare da zaro idanun cikin tsananin tsoro da firgita gaba d'aya jikin shi rawa yakeyi ba abin da yake furtawa sai jujjuya kan Usman d'in yakeyi yana cewa. "Usmaaan ! Usmaaaaaan!." sai kuma ya k'ara matsoshi jikin shi ganin wani irin yunk'uri da Usman d'in keyi, shi kuwa Usman k'irjin shi ya rik'e tare da damk'o hannun d'an uwanshi yayi wani irin kakari da k'arfi har jikin shi na karkarwa , aman jini ya rink'a yi bak'ik'k'irin dashi guda-guda sai ya damk'o hannun d'an uwan nashi yayi kakari, ita kuwa Ummul gaba d'aya karkarwa takeyi da dafa jikin motar tayi tana tafiya a hankali har ta isa gaban su hannun ya Usman d'in ta rik'e da k'arfi cikin gigicewa da tsoro ta saki wani irin k'ara mai k'arfi kawai sai ta fad'a jikin Hamma Umar d'in a sune, shi ma ya Usman lokaci d'aya numfashi sa ya fara d'auke wa, Allah sarki Hamma Umar gaba d'ayansu ya had'a ya ruggume su cikin tsinkewar jijiyoyin jikin shi gaba d'aya ya zame ya zauna a k'asa kanshi ya rink'a murzawa a jikin motar Usman cikin wani sauti mai tsananin rauni yace. "Usmaaan kar kayi min haka Usman karka barni ni kad'ai Usman wazai meye min gurbin ka wayyo Allah wayyo d'an uwana wayyo Ammina ina kike Usman zai tafi ya barmu wayyo Abba d'an uwana zai tafi ya barni ni kad'ai ba Uba ba d'an uwa." ruggume Usman da Ummul d'in ya kumayi da k'arfi Abba ya rink'a kira da k'arfi dai-dai lokacin daya ga numfashi Usman yana ficew.... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1⃣9⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Wannan shafi naki ne kad'ai Firdausi Sodaggi ke da members naki na matan k'warai na baku kyautan wannan shafi gaba d'ayan shi🤝😍😘* *QAULIKI HAQQUN SAFIYYA HUGUMA👍🏻 ALMUSLIM AKUL MUSLIM🤝😘 ZADAKILLAHU FIKHRAN WA ILMAN👏🏻, WAYATTAQINALLAHU JAMI'AN👏🏻🤝😀🤝* *R*uggume su ya K'ara yi cikin tarin firgici yana tallabo kan Usman yana mannawa a k'irjin shi tare da rumtse ido da k'arfi yana fad'in. "ya rabbi ! Ya k'adir ! Allah kaine gatana kaine gatan dukan bayin ka Allah kaine mai rayawa da kashewa Allah kaine mai bada lafiya ya Allah ka jib'amci lamuran d'an uwana Allah ka rayamin d'an uwana, shima Usman k'amk'ame Umar d'in yayi cikin fitar hayya cinshi da azabar da yakeji, Ummul kuwa manne take a jikin Hamma Umar d'in tayi luf a sume, su Abba kuwa tun k'aran da Ummul tayi na fari sun ka fito cikin mamaki jin muryar Ummul d'in a gida ya Adam da Sadik kuwa jin muryar Hamma Umar yana kiran Abba da karfine yasa suka fito a guje gaba d'aya harabar gidan suka nufa, Hamma Umar kuwa gaba d'aya jikin shi rawa yake tsoro da firgicin zai rasa d'an uwan nashi gaba d'aya sai ya resa k'arfi jikin nashi haka ya zauna dir sham a k'asa yana ruggume dasu yana wani irin kuka mai cike da firgici da tsoro da kad'uwa gaba d'aya ya resa halin da yake ciki duniyar ta mishi duhu, su Abban suna fita da gudu sukayi inda suke jin sautin kukan Hamma Umar d'in da sautin fuzgar numfashin Usman d'in, suna zuwa Abba ya durk'usa gabansu cikin tarin firgici da ganin ikon Allah ya kamo hannun Usman cikin tashin hankali yake kiran shi. "Usman ! Usman ! Innalillahi." sai ya kumu kalli Adam da gaba d'aya jikin shi rawa yake cikin rawan murya yace. "Adam fito da mota mu tafi asibiti." sai ya kumma kalli Ummul dake kwance luf jikin Hamma Umar d'in tana sume cikin jin tsoron lamarin ya kalli Umar tare da cewa. "Umar meke faruwa da sune?." ina ya kasa magana sai k'ara ruggume Usman da ummul d'in yakeyi, shi kuwa Usman cikin tarin ya kamo hannun Adam d'aya juya zai fito da mota numfashi na fizga tare da zarewan idanu yace. "Ad..! Ada..! Adam Karku kaini asibiti Abbah Ku barni a gida." sai ya kuma carkewa da tari sai ya rink'a amayo da jini guda-guda bak'k'ik'irin dashi, cikin a man ya kamo hannun Umar d'aya gama mutuwan zaune yace. "Hamma na karku kaini ko ina ku barni a gidan ku maidani cikin gida." Hamma Umar kam kanshi ya kife a jikin Usman d'in cikin rawan murya da baki yace. "Usman d'an uwana ya za'ayi mu barka a gida a cikin wannan halin da kake kayi hak'uri muje asibiti." hannun Umar d'in ya rik'o dan ya fara jin numfashi sa na dawowa tunda ya amayar da bak'in jinin hawaye na bin fuskarsa zufa na ketomai tako ina cikin murmushi k'arfin hali yace. "Toh su asibiti zasu hanani mutuwa ne in lokaci na yayi? nasan dai mutuwa ce kuke tsoro kuma in lokaci yayi ba makawa Hamma Umar ka tunafa Abba ka sani tun ina yaro kuke fama dani ko yaushe muna hanyar asibiti ban workeba yanzu kuma ko anje ba lallai a samu nasara ba ko nasha maganin shi maganin abinda ya samu yake tayiwa in ya samu sauk'i sai ya k'ara sauk'i in ya samu ajali kuwa tofa ajalin yake tayiwa dan Allah Abba Hamma Umar ku maida ni gida bana son zuwa asibiti nan." Haka dole ba d'an suna soba suka koma cikin gida dashi, shi kuwa Umar Ummul ya ruggume sannan yabi bayan Abba dake tallabe da Usman, kai tsaye part d'in Hajjajo suka nufa a parlour suka zauna kan 3 str Abba ya kwantar da Usman shi kuwa Umar ya kwantar da Ummul kan 2 str , ya Adam kuwa dama tuni ya fita ya d'auko doctor dake duba Usman d'in. Bayan yazo ya duba shin yayi duk binciken da zaiyi ya gama sannan ya kalli Usman d'in dake konce a rigingine ya lumshe ido hawaye na bin fuskar shi sannan ya juyo ya kalli Hamma Umar dake zaune ya zuba mishi ido yana rik'e da hannun shi sannan ya kalli Abba dake k'ok'arin gyara wa Usman d'in konciya cikin kula doctor Ibrahim yayi ajiyan zuciya sannan yace. "Alhaji Hassan ko kuna lura da Usman sannan kunsan meke damun shi akwai matsalar da yake boyewa a zuciyar shi sannan kuma yasan zuciyar shi bazata iya d'aukar nauyin ba Usman akwai abin da yake matukar so bai samu ba, domin na duba na'urar dake cikin k'irjin shi tana zaune yadda ake so tana kuma taimakawa kamar yadda ta saba tana kuma harbawa jinin dai-dai misali kuma zataci gaba da aikin har nan gaba shekara 1 a lokacin zai cika shekara biyar da sata sannan za'a koma a canzata kamar yadda aka saba, yanzu wata matsalar ce ta daban kuwa ke damun Usman kuma zata iya jawo komai a rayuwar shi." yana rufe bak'in shi Usman ya bud'e idanun shi cikin salon sa na abin dariya ya fara magana cikin dariya da son badda matsalar tasa yace. "Uhummm wai ina son wani abu, toh niko mai zanso wanda Abba da Hamma Umar basu samamin shiba ni ba abin da nake so." Ido Nenne ta tsura mishi cikin tsananin tunani lokaci d'aya kuma ta fara tuno wani abin, Hajjajo kuwa ba abinda takeyi sai kuka, shi kuwa Hamma Umar ido ya tsurawa d'an uwan nashi cikin sanyi yace. "Me yake saka tarin da a man jini?." murmushi yayi tare da d'an shafa sajen shi yace. "You naga Anyi tayin maganin asibiti ba canji shine jiya naje na karb'o na wmzamai shine na jik'a nasha , sai gashi yana k'ok'arin fecewa dani barzaq." Murmushi ya kuma yi sannan yace. "Amman fa gsky naji sauk'i dana amayar da jinin." haka ya rink'a shashantar da abin shi kuwa doctor Ibrahim ya tabbar akwai matsala tare dashi. su ya Adam kuwa sun d'an samu nitsuwa ganin Usman d'in ya mik'e, Hamma Umar kuwa har yanzu zuciyar shi na cike da fargaba, Abba kuwa bayan doctor Ibrahim yabi suka fita tare yana k'ara mishi bayani, bayan su Abban sun fita ne Hamma Umar ya d'an juyo kusa da Ummul tafin k'afafun ta ya kamo yasa hannun shi ya rink'a murzawa yana jan yatsun k'afafun nata tare da kiranta. "Ummul ! Ummuuul !." sai kuma ya dawo ta kanta hannun shi yasa ta k'asan wuyanta yana d'an murzawa, nanma shiru sai ya manna hancin shi da nata sannan ya rufe bakinta da nashi, cikin lumshe ido ya rink'a fesa mata numfashin sa sannan yana zuk'o numfashin ta bak'in ta gaba d'aya nashi numfashin ya rink'a fesa mata cikin sa'a tafizgo numfashin sannan a razane ta kamo wuyan shi baki ta bud'e da nufin zata sake k'ara, sai yayi maza ya rufe mata bak'in da tafin hannun shi, haka yasa ta bud'e idanun ta sannan ta rink'a kallon su d'aya bayan d'aya, zame bakin ta tayi cikin sanyin muryar tace. "Ya Usman ! ya Usman ." ido ya d'an rumtse sannan yace. "Na'am Ummul ." jin muryar shi ta mik'e da sauri taku d'aya tayi ana biyun ta koma ta zauna ido na zubda k'ollah dan azaban ciwon da raunin jikinta ke mata, cikin sauk'e ajiyan zuciya Hajjajo tace. "Ke kuma meya sumar dake? sannan yanzu tafiya ma na gagararki." batayi magana ba sai kawai ta kama kuka, ganin haka Nenne tace. "Toh sarkin kuka ya isa haka taso mu tafi kiyi wonka sai kici abinci kiyi bacci." mik'e wa tayi cikin zubda k'ollah tafiya ta farayi cikin d'ingisa k'afafun ta tana d'an waresu tare da cije lips d'in ta, ganin haka tuni Nenne tayi gaba dan ta gano matsalar yartata itama Hajjajo shiru kawai tayi dan ta fahimci matsalar, shi kuwa Hamma Umar kanshi ya sunkuyar cikin tarin kunya da tausayin Ummul d'in sai hawaye yaji yana bin hab'arsa dan gani yake kamar ya gwada mata rashin tausayi tunda yasan yarinya ce, kunya yakeji ta rufeshi kamar k'asa ta tsage ya shiga, ganin hakan yasa su ya Adam duk suka zame suka fita itama Hajjajo kitchen d'inta ta shiga ta fara had'a wa Ummul had'in su na tsoffin shuwa'arab sannan tayiwa Usman d'in ma had'in shi na musamman ta kuma dafawa Usman abincin da zaici da kanta. A part d'in Nenne kuwa suna shiga kai tsaye bedroom suka wuce kan gado Ummul ta konta ta kife kanta tana kuka, ita kuwa Nenne toilet ta shige ruwan d'umi ta had'a mata mai k'unshe da sinadarai na gyaran jiki sannan ta had'a mata wani juk'o na musamman a cikin buta, tana fitowa taje kusa da ita cikin kulawa da tausayawa irin ta uwa da yarta ta kamo hannun ta ta zaunar da ita kafad'an ta ta dafa a hankali tace. "Ummul Allah ya miki albarka kiyi hak'uri mamana ki d'aure kinji ko ki denan kukan nan ya isa yanzu kin girma ya kamata kiyiwa kanki fad'a tashi kije kiyi wonka ki zauna cikin ruwan d'umin sannan kiyi amfani da ruwan butar nan." kukan ta kumayi cikin shogwob'a dan ganin Nennen ta na lallashin ta, da kukan ta shiga tayi wonkan sannan ta k'asa kanta lokaci d'aya taji jikinta duk ya wore, tana fitowa ta samu Nennen ta jona borner a ajikin wuta tana fitowa ta zuba mata wasu turaruka masu tsananin k'amshi sannan ta kalleta cikin kulawa tace, zoki tsuguna kiyi hayak'i da wannan." "toh " tace sannan ta matso gaban borner ita kuwa Nenne ta fita parlour, tsuguna wa tayi a kanshi hayak'in na shiga jikin ta wani irin k'amshi na ratsata, tana mik'e wa ta Jita garau hakan yasa ta kimtsa sannan ta koma bak'in gadon ta konta cikin jin wani irin baccin gajiya, Tana konciya Nenne na shigo wa had'in kaza ta karb'a mata wanda Hajjajo tayi mata sai ruwan tsumi mai dad'in sha, ajiye wa Nenne tayi sannan tace. "Taso kici abinci saiki kontan." ba musu ta sauk'o taci tasha dan tana jin yunwa, kuma yau tana jin dad'in yadda Nennen ta ke kula da ita wanda tunda ta nuna bata son Umar Nenne ta dena kulata sai yau d'in, tana gamawa ta koma ta konta tana kallon Nenne dake shirin shiga wonka cikin sanyi tace. "Nenne zazzab'i nake ji da ciwon kai." ba tare da ta kalleta ba tace. "Toh bari in gayawa Umar d'in yazo ya dubaki." fuska ta tsuke dan bata son abinda zai had'a ta dashi inuwa d'aya kuma gashi ta jawa kanta, bayan Nenne tayi wonkan ne ta shirya ta nufi d'akin Abba a tsakar gidan ta kalli Aliyu yana shirin shiga part d'in Hajjajo kiran shi tayi sannan tace. "Jeka kira Hamma Umar d'in ku kace Ummul bata da lafiya yaje ya dubata." "Toh" yace sannan ya nufi parlour Hajjajo yana zuwa ya samu Hamma Umar d'in yana zaune gefen Usman yana b'are mishi lemu, gefen shi ya zauna a hankali yace. "Hamma Anty Ummul bata da lafiya Nenne tace kaje ka dubata." kai ya gyad'a sannan yaci gaba da bawa Usman d'in kulawa, bayan ya gama bashi abinci ya bashi maganin sannan suka tafi part d'in su suna zuwa ya had'a mishi ruwan wonka, har cikin bathroom d'in ya rekashi kamar zaiyi mishi wonkan, murmushi Usman yayi tare da cewa. "Hamma yau wonkan ma zaka min ne?." "Kanaga ka girma ko?." kai ya sosa sannan yace. "Gaskiya dai Hamma na girma mai min wonka zai iya makancewa." K'eyan shi ya d'an buga sannan ya fita, shi kuma Usman wonkan yakeyi yana zubda k'ollah cikin tausayawa kanshi da d'an uwan nashi, bayan ya fito Hamma Umar ya shirya shi sannan ya kontar dashi kan gado ya zauna gefen shi yana shafa kanshi cikin sanyi yace. "Ammmi ta kiraka kana wonka nace mata kace min yanzu ka girma." ido ya lumshe yana jin dad'in yadda d'an uwan nashi ke kula dashi k'aunar shi na ratsa mai zuciya, ido ya lumshe cikin jin bacci yace. "Hamma ?." "Na'am Usman d'an uwana." kai ya jinji na sannan yace. "Ina sonka d'an uwana." kanshi ya rink'a shafawa yana cewa. "Usman duk duniya bani da tamkar ka ina sonka k'anina bani da buri a duniya daya wuce inga ka samu lafiya fatana a koda yaushe in ganka cikin farin ciki." ruggume juna sukayi sannan a hankali Umar ya kontar dashi sannan ya rink'a yi mishi karatu qura'ani a cikin kunnen shi murya cike da rauni, lokaci d'aya bacci ya tafi da Usman d'in, shi kuwa Hama Umar a hankali ya gyara mishi konciya sannan ya fito kai tsaye harabar gidan ya koma motar shi ya bud'e ya d'auki magungunan Ummul sannan ya nufi part d'in Nenne, yana shiga parlour ya samu ba kowa sai kuma yaji muryan Ummul dake magana da Anty Halima da woyar Nenne, cikin yin sallama ya shiga yana shiga ya zauna gefen Ummul d'in sannan yasa hannu ya karb'i woyar ya katse kiran , ita kuwa a fusashe ta juyo gare shi a nufin yin tsiwa, sai kuma tayi shiru jin yadda ya jawota jikin shi ya ruggume ta tsam a jikin shi sai sauk'e ajiyan zuciya yakeyi murya can k'asa yace. "Kun bani tsoro keda Usman in na rasaku bansan makomata ba Ummul Khairi ina tsoron abinda zai rabani daku, In babu Usman bansan ya rayuwa zata juya min ba." sai kuma ya k'ara matsota jikin shi d'umin jikinta na ratsa shi, ita kuwa tureshi takeyi tana k'ok'arin matsawa, jawota ya kumayi a hankali ya tallabo kanta kissing d'in ta yayi da kyau sannan yace. "Kiyi hak'uri my Khairi bazan sake wahala da keba." shiru tayi tana jin yadda yake fidda numfashin da sauri-sauri a haka har ya fara sauk'e ajiyan zuciya a hankali nitsuwarsa ta dawo jikin shi sannan ya bata maganin ya kontar da ita ya shafa fuskar ta sannan ya fita. A haka Hamma Umar ya wuni kula da k'anin shi da matar shi da derema haka ya kwana kula da Usman yayin da kewar Ummul ke cin jikin shi da zuciyar shi, koda gari ya waye haka ya wuni kula dasu, kuma Alhamhadullih duk sun mik'e musamman Ummul dan shi kam Usman k'arfin haline da son kontar da hankalin Hamman nashi, bayan Anyi salla isha ne Abba yace Hamma Umar su tafi tunda duk jikin su da sauk'i, bayan ya fita ne ya d'auko jakar Ummul ya bawa Aliyu ya kai mata cikin gida sannan yace . "In kaje kace tazo." "Toh" yace sannan ya nufi cikin gidan, a parlour Nenne ya samu su ya Adam cikin mamaki ya Sadik yace . "Jakar nanfa daga ina.?." "Ta Anty Ummul ce." Ya bashi amsa ya Adam ne ya kalli Ummul d'in cikin tsuke fuska yace. "Ba yanzu zaku tafiba?." Kai ta juya ido cike da k'ollah tace. "A a ni bazan komaba bani da lafiya." A hatsale ya bugawa Aliyu tsawa . "Maza ka meda jakar cikin motar Hamma Umar d'in ke kuma tashi kibi mijin ki ku tafi." shi kam Aliyu tuni ya juya da jakar ita kuwa hannun ta rink'a yarfa wa tana buga k'afafun ta tare da bud'e baki da k'arfi tana. "Ai Hamma Umar d'in ya yarda kuma bani da lafiya shike nan dan an tsaneni sai ayi ta korata a gidan mu." Kanta yayi da sauri yana zaro bel d'in k'ugunshi, ya Sadik kuma cewa yake. "Yauwa zaneta tunda bata jin magana." Ihu ta saki jin sauk'ar bel d'in a jikin ta a guje ta fita tana kuka, bayan Hamma Umar d'in ta tsaya tana tsalle da dire-dire tare da rik'e hannun shi , Abba ne ya fito dan jin kukanta yana zuwa ya kalli yadda takeyi sai murmushi yayi dan a fili yarintar Ummul take ganuwa, shi kuwa Adam tsawa yake buga mata yana. "Ki wuce ki shiga cikin mota." Abba ta kalla dan ko zaice ta dawo sai kuma ta shiga motar ganin yadda ya had'a fuska yana kallon ta, shi kuwa Abba cikin bada umarni yace. "Farouq shiga ku tafi. "toh." yace sannan ya shiga, Aliyu kuwa dariya yayi tare da d'aga tafin hannun shi ya saitasu da kanshi yana kad'a hannun tare da zaro harshen yana kad'awa Ummul cikin tsokana yace. "Bana gaya mikiba yanzu ke ba y'ar gida nan bane yanzu dagani sai Nenne na." ya k'arishe maganar yana rawa, Usman ne ya d'an roggoshi keyarshi yace. "Aliyu wato kaine d'an tada zaune tsaye ko." ita kuwa kuka tasa tana cewa. "Ya Usman ba kaga Aliyu ba." Murmushi yayi yace. "Muna sonki Ummul d'in mu ke y'ar gidan nance har Abadan." K'ollah ta zubda tare da cewa. "ya Usman kai kad'ai kake sona, nima ina sonka." Ido ya lumshe sannan yace. "Allah ya d'aiyiba." murmushi sukayi dukan su, shi kuwa Hamma Umar hannun Usman ya jawo ya d'an sunkuyo kanshi a hankali yace. "Ka kula da kanka d'an uwana ina son ka ina tsoron abinda zai cutar da kai." Murmushi yayi tare da cewa. "Nayi lafiya fa." Haka sukayi sallama suka tafi, Ita kuwa suna fita harabar gidan ta bud'e sabon shafin kuka, sunyi tafiya mai d'an nisa, Hamma Umar yana tuk'in hankalin shi na cikin tunanin halin da k'anin shi ke ciki, kamar a mafarki yaji Ummul tasa hannunta ta d'amk'o........ By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 2⃣0⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *H*annun ta tasa ta damk'o siterin ta rink'a juyashi tare da murza shi da k'arfi tana. "Allah ka tsaya ni in sauk'a ehe, ni bazan koma gidan kaba ka sauk'e ni a nan zan tafi gidan Anty Halima." murza kan motar take da k'arfin ta, tuni motar ta fara yawo a tsakiyar titi ga ababen hawa dake ta gaban su da bayan su da gefe, gaba d'aya motar kanta ya kufce, a firgice yace. Innalillahi Ummul kin san abinda kikeyi kuwa?." fizge hannayen ta yayi da k'arfi cikin tashin hankali ganin ya nufi kan wani mai a dai-dai ta yana k'ok'arin hawa kanshi ita kuwa tak'i sakewa sai murzawa take tana. "Ka sauk'e ni a nan bazan koma gidan kaba bana sonka na tsaneka." Ido ya zaro cikin tashin hankali ganin saura k'iris ya taka wani mai reke da yake gefen titin gaba d'aya mutanen wurin sai rik'e kai sukayi suna. "Innalillahi subahanallahi." shi kuwa Hamma Umar cikin firgici da tsoron ganin zata sashin kisan kai gaba d'aya jikin shi sai rawa yake yi, cikin b'acin rai ya fizge hannayen ta sannan ya tura ta jikin sit d'in ta koma ta bugi jikin marfin motar sannan ta sake tasowa tana k'ok'arin sake rik'e kan motar, tsawa ya buga mata cikin zafin rai ya ware tafin hannun shi ya zuba mata mari d'aya wanda saida taga taurari na yawa a sararin samaniya kunnen ta saida ya bada sautin kiuuuu sannan ta kuma jin yayi dum lokaci d'aya zanen yatsun shi suka taso a farar fatarta tuni fuskar tayi jazir gaba d'aya ta rasa ina take dan marin ya gigitata, shi kuwa da k'er ya samu ya tsaida motar jikin shi na rawa zuciyar shi cike da tsoron karta sashi kisan kai yayi parking a gefen titin cikin sauri ya fito ya nufi gun mai reken da mai a daidaitan hak'uri ya rink'a basu, da sun hatsala amman ganin yadda yake basu hak'uri yasa sukace. "ba komai Allah ya tsare gaba a rink'a kula." "Toh nagode." yace dasu sannan ya koma cikin motar ya shiga ya zauna fuska a tsuke tamkar bai tab'a dariya ba, jan motar yayi da gudu ya kama hanyar damaturun, ita kuwa tunda ya zabga mata marin ta kife kanta kan cinyoyin ta ta rink'a kuka mai cike da takaici, bai kulata ba, ita kuwa kukan taci gaba dayi tana sheshshek'a, a haka har suka isa cikin damaturu a inda suna shiga hadari na tashi iska mai sanyi ya rink'a busawa tako ina sai walkiya ake da d'an rugugi alamu irin hadarin karshen damuna ce, suna isa yayi parking sannan ya koma ya zauna ya jingunu da jikin kujerar yana jin yadda take kuka, a zahiri mamaki yake irin tsanar da Ummul ke mishi sannan itace da laifi itace da kuka kuma har cikin ranshi yaji zafin marin da yamata, ajiyan zuciya ya sauk'e sannan yasa hannu ya d'an dagota ya jingina ta da jikin shi hannun ta ya kamo cikin sanyi ya cusa hannun kan k'irjin shi sai kuma ya kalleta a hankali yace. "Kiji yadda kikasa zuciya ta bugawa dan tsoron karki sani nayi kisan kai Ummul nine ba kyaso amman k'iyeyyar har tana k'ok'arin saki in kashe wasu a banza." sai kuma yayi shiru sannan yasa tafin hannun shi yana shafa fuskar ta a hankali yace. "Kukan ki nasa zuciya ta tayi nauyi sabida sai inga kamar na k'asa rik'e amanar dana d'auka ne kiyi hak'uri ki gafar ceni banyi niyar tab'a lafiyar jikin kiba." tureshi ta rink'a yi tana janye hannun ta, shi kuwa rik'e hannun yayi a hankali ya bud'e d'an durowan gaban motar wani d'an k'ara min kontena ya d'auko bud'e wa yayi sannan ya d'auko wani zoben Diamonds sai shek'i yakeyi tamkar tauraro yatsarta ya d'an d'ago a hankali ya zira mata zoben cikin sanyi yace. "Kinyi kyau matata yatsarki ta haska zoben." fizge hannun tayi dai-dai lokacin da ruwan sama ya fara sauk'a , bud'e motar tayi ta fice cikin kuka ta koma can tsakiyar harabar gidan ta tsaya tana kuka, ganin haka ya fito ya rufe motar cikin sauri yaje gabanta hannun ta ya rik'o tare da cewa. "Kiyi hak'uri zomu shiga cikin gida kar ruwan ya tab'a mu, kinsan ni bana son ruwan sama ya tab'a ni zai sani zazzab'i." cogewa tayi fir tak'i shiga daya kamo hannun ta sai ta dasa mai ihu, ganin haka ya rufe gidan sannan ya wuce ya shiga cikin gida a zaton shi ko zataji tsoro ta biyoshi, Abu kamar wasa ya shiga, ita kuwa sai tsuguna wa tayi a wurin ruwan yana ta sauk'a a kanta duk ta jik'e tayi jilik sai d'iga takeyi ga tsawa da walkiya da akeyi, parlour ya fito rik'e da leima ya nufi gunta, yana zuwa ya jawota jikin shi cikin rawan sanyi yace. "Khairi kiyi hak'uri mu shiga cikin gida kar mura ta kamaki d'an Allah mushiga ciki bana so ruwan ya tab'ani." Jin haka ta fizgota leimar ta cillata gefe haka ko iska ya debeta yayi woje da ita, shi kuwa da sauri ya d'ago hular rigar shi da take konce a kafad'an shi ya rufe tsakiyar kanshi dan in ruwan sama ya bugi kanshi yana sashi zazzab'i da ciwon kai mai tsananin, hannun shi kuwa ya hard'e a k'irjin shi tuni ya jik'e cikin rawan sanyi da karkarwa ya jawota jikin shi a hankali yace. "Toh aikin rama mu tafi cikin gida kiyi hak'uri k'anwata." cikin kuka tace. "Ban rama ba kam, kuma bazan shiga gidan kaba sai in zan rama marin da kayi min." murya na rawan sanyi yace. "Na yarda mu shiga saiki rama." baki ta tura sannan tace "toh." hannun ta yaja suka shiga cikin gidan , suna shiga d'akin ta ya nufa da ita, a gaban mirror ya tsaya da ita, cikin rawan sanyi ya cire mata mayafin nata sannan ya zuge zip d'in rigar ta yasa hannu zai cire mata rigar tayi maza a juya tana hararan shi tana cewa. "Ka barni in cire abina da kaina ." "Na barki nima bari inje in cire nawa." sai kuma ya bud'e durowa ya zaro mata riga da wondo wondon iya guiwa sai rigar mai d'an fad'in wuya ta yadda kafad'an ta yake fita inya ta saka kayane mai tashi da sulbi, kan gado ya ajiye mata sannan ya fita ya koma bedroom d'in shi, yana shiga ya canza kayan shi sannan ya fito ya nufi kitchen tea ya dafa musu mai zafi wai maganin sanyin, d'akin shi ya koma da niyar d'auko woyarshi yana rik'e da cups d'in yana juyowa da nufin zai fita kenan ya ganta tsaye a bak'in k'ofar shigowan fuska a had'e tace. "Zan rama fa ehe." Ido ya tsura mata cikin mamaki ajiye cups d'in yayi kan mirror sannan ya juyo a hankali yace. "Toh zoki rama." shigo wa tayi ta tsaya a gaban shi ta d'an d'ago kanta tana kallon fuskar shi, shi kuwa kollon d'an tsawonta yake tunda ko fuskarsa in zata kalla sai ta daga wuya da kai, kuma wai shine tana ikirarin tazo ta rama marin daya mata, cikin ranshi kuwa jira yake yaga iya rashin kunyarta zata mareshin neko k'ak'a, ganin tana ta d'ago wuya da k'afafun ta dan ta isoshi tsawo ta kasa, sai ya d'an rok'ofo kanshi ya sunkuyar dai-dai tsawonta cikin rumtse ido yace. "Rama." fuskar shi ta tsurawa ido ta d'ago hannun zata yarfa mai marin sai kuma tayi maza tayi k'asa da hannun sai hawaye car-car a idanun ta, shi kuwa jin shirun ne sai ya bud'e idanun shi ganin tana kallon fuskar shi tana kuka yasa ya d'an yi murmushi cikin kula ya jawota jikin shi ya ruggume ta kanshi ya sunkuyar dai-dai kan hab'arta daya maran a hankali ya rink'a fese mata iskan bak'in shi mai sanyi sannan yasa tafin hannun shi yana share mata k'ollah, ita kuwa cikin kuka tace. "Ni dai sai na rama amman ba, a fuskar kaba." murmushi yayi a ranshi yace. "Gaskiyar bahaushe wata fuskar tafi k'arfin mari." fahimtar da yayi bazata iya ramawan bane, sai ya mik'o mata cup d'in tea shima ya d'auki d'ayan ya fara sha yana lumshe ido cikin lallashi yace. "Kisha tea sai na goyeki a madadin marin." ajiye cup d'in tayi tace ita bazata shaba kuma shima ya ajiye sai ya goye tan, murmushi yayi ya ajiye cup d'in yana jin sanyi na ratsashi, tsakiyar d'akin ya dawo kan carpet ya durk'usa ya mik'e tsawonshi kamar mai konciya sai kuma ya d'an taso ya k'afa hannun shi a k'asa sannan ya mik'e tsawonshi , cikin sanyi yace. "Toh zoki hau." murmushi mugunta tayi dan tanaga bazai iya d'aukar nauyin taba, da sauri ta matso ta zauna a tsakiyar bayan shi sannan ta tonk'oshe k'afafun ta ta d'an ware hannun ta sannan ta had'a yatsun ta haka👌🏻 tana ta murmushi mugunta , dai-dai lokacin woyarshi ta rink'a suwa ita kuwa sai gyad'a kai take tana lumshe ido, yana kallon ta duk abin da takeyi, a haka har zuwa wani d'an lokaci sannan ya manna jikin shi kan carpet d'in ya kwanta yana maida numfashi, itako murmushi tayi sannan ta mik'e zata tafi, sai ya rik'o hannun ta ya fizgota jikin shi ya matseta gam cikin maida numfashi yace. "An gaya miki ni dokine da zan goyeki a banza, nima saina samu maganin sanyin da kika samin." Baki ta tura tace. "Toh ai ba ladan mari bane, kuma ni bani da maganin sanyi." "Kina dashi mana." "Toh ina yake?." hanun shi ya cusa cikin jikin ta tare da lumshe ido yace. "D'umin jikin kine kawai zai cire min wannan sanyin inba hakaba zai sani zazzab'i." tureshi tayi ta mik'e sai kuma ta d'an yi k'ara jin yadda yake murza hannun shi a kan k'irjin ta, murmushi yayi ya mik'a hannun kan gado ya jawo blanket sannan ya jawota jikin shi kan carpet d'in ya kuma rufesu da blanket d'in, hannun shi yasa yana shafa cikin ta a hankali yace. "Ina son Baby daga gareni Khairi kiyi Addu'a Allah yasa yau nayi ajiya a nan." tureshi takeyi shiko sai murzata yakeyi a hankali yace. "Kiyi hak'uri in kasance dake." Cikin fad'a tace. "Bana so." da sauri yace. "Karya ne kina so kam." hawaye ta fara zubdawa tana jin yadda yake murzata da juyata, ita kuwa, tureshi take d'an yi duk da yau yana binta a hankali ba zafi sosai, amman sai kuka takeyi cikin raki tana cewa. "Bana sonka na tsaneka." duk da yana cikin duniyar nitsuwa Amman yaji zafin kalamta gare shi, a ranshi yake fad'in. "Ko cikin yanayin da ma'aurata suke ruggume juna dayin musayan kalaman soyayya shi a cikin yanayin ma Ummul tureshi take a madadin ta mak'ale shi sannan kalaman k'iyeyya take fad'a mishi a madadin na soyayya kuma kuka take na jin tsanarshi a madadin tayi kukan gamsuwa, haka ya zame jikin shi ya konta gefe sannan ya jawota ya ruggume ta da k'arfi yana fidda nannauyan numfashin a hankali yace. " wata rana zaki soni Khairi , fatana Allah yasa jinin na ya gauraye da naki, ki haifarmin d'ana nasan shi kam zai soni." manne wa tayi a jikin shi dan ya gajiyar da ita ga kasala daya k'ara rufeta numfashi ta rink'a maidawa a hankali, cikin ranta kuwa fad'i take. "Tabbas in nayi garaje Hamma Umar zai d'irka min ciki ya barni da matsala." a haka da wannan tunanin tayi bacci a jikin shi, shi kuwa ruggume ta yayi har saida yaji baccin ta yayi nisa sannan ya mai data kan gado shi kuma ya gyara wurin yaje yayi wonka yayi al'wala yazo yayi ta nafilfilin daya saba da karatu qura'an, sai k'arfe 2:30 ya konta ruggume da ita. Washe gari da safe bayan ya gaba komai ya shirya ya fita, yana fita itama ta fita kai tsaye kemis na bayan layinsu taje k'wayoyin family planning ta seyo tazo ta boye wanda kullum sai tasha, acewarta bazata haihu dashiba in yana son haihuwa ya saketa ya auro wata. Haka rayuwa taci gaba da tafiya kullum sai tasha maganin a boye duk da ba wani bashi kanta takeyi ba, bayan ta fara shan maganin da kwana goma kawai ranan ya shiga ya samu tasha maganin kenan tana rik'e da sachet d'in, sosai Ummul taji tsoro da mamakin yadda Hamma Umar d'in ya birkice mata tamkar zaiyi hauka bata tab'a ganin baccin ranshi kamar na wannan ranar ba, ya rink'a surface mata fad'a daga karshe ya kwashesu yace zai kai ya nunawa Abba , ganin haka tayi ta kuka tana bashi hak'uri tare da cewa bazata sake shaba, ganin yadda ta nuna bazata kuma ba yaji dad'i ya yarda ya barta bayan yayi ta mata nasiha. Toh fa bayan sunyi haka da kwana biyu ta lallab'a taje wani prvt hospital ta shirga k'ariyar ta kan cewa da yardar mijin ta suko tunda aikin kud'i ne ba wani dogon bincike suka sa mata y'ar robarnan da ake tsawa a hannu suka d'inke mata, suka amshi kud'insu ko a jikin su, koda ta dawo haka tayi ta wasan b'uya da Hamma Umar d'in har saida wurin d'inkin ya worke ras ta yadda bazai ganeba, shi kuwa kullum addu'ar shi Allah ya bawa Ummul d'in ciki yanaga duk abin nata zai ragu inta fara haihuwa dashi. Yau Saturday tun safe Hamma Umar baije ko inaba yana gida ko parlour bai fitoba yana d'akin shi , dan ya fara gajiya da azabtar dashi da Ummul keyi, ita kuwa Ummul tun safe ta shirya a nufinta in taga ya fito zai tafi potaskum zatace zata bishi, ganin shiru-shiru bai fito bane har bayan sallan la'asar saita fito a hankali ta nufi d'akin nashi, a hankali tayi sallama tare da tura k'ofar ta shiga, kan gadon ta hoggoshi yana kwance yayi rigingine ida nunshi a lumshe ba komai a jikin shi sai towel dake d'aure a k'ugunshi alamun daga wonka ya fito, shiru bai amsa sallamar taba, shigowa tayi cikin d'aga k'afafun ta a hankali bak'in gadon taje ta tsaya tana son ta tasheshi ta rasa ya zatayi ta tasheshin gashi gaba d'aya ganin surar jikin shi na bata tsoro, a hankali ta durk'usa a bakin gadon cikin kauda fuska ta fara magana. "Hamma! Hamma! Hamma ka tashi mana." yana jinta yayi shiru kamar maiyin bacci a ranshi kuwa farin ciki yake da shigowar ta d'akin nashi, ita kuwa tashi tayi ta zauna gefen shi a bakin gadon a hankali tace. "Hamma yau bazaki je gida bane? Hama weekand d'in ma baza'a fitaba ni ina son zuwa inga Nenne na." murmushi ya d'an yi gano yawo take son fita shiyasa take wani yin ladabin kura ga mai akuya, mik'a yayi a hankali sannan yasa hannu ya jawota kan k'irjin shi hannun shi yasa ya rink'a shafa bayan ta a hankali yace. "Zamuje mana in kina so." Mutsumutsu ta rink'a yi cikin had'e fuska tace. "Ehh ina so mana ka tashi mu tafi." towel d'in nashi ya rink'a murzawa tare da jawo blanket ya rufe su sannan ya k'ara jawota jikin shi a hankali yace. "Bazan iya tuk'in ba sai an bani maganin." hannu tasa tana ture hannu shi da yaketa b'alle boturan gaban rigar ta mai dogon hannu wai duk dan ta boye tabon abin family planning d'in ne, shi kuwa ido a rufe ya zare rigar tata, sannan ya kuma rink'a shafa wutanta ido a lumshe a hankali har ya isa kan damtsen hannun ta da akasawa robar, ido ya bud'e jin kamar d'an k'urji a cikin hannun nata gashi da alamun kamar tabo, da sauri ya tashi zaune cikin hamzari ya d'ago ta ya manna ta a k'irjin shi sannan yasa hannu ya kamo hannun nata ya d'an daga, da sauri ya tureta cikin wani irin yanayi ya kafa mata. By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 2⃣1⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *I*do ya tsura mata yana k'ok'arin k'ara jawo hannun nata, ita kuwa da sauri ta janye hannun gaba d'aya har jikin ta na rawa sai ta konta a kife ta cusa hannayen nata k'asan k'irjinta ta konta kan hannayen tayi luf tana d'an mai da numfashi, shi kuwa k'ara matsota yayi cikin yanayin tabbaya yace, "Khairi me a hannun ki?" bata kula shiba sai d'an mirgino wa tayi jikin shi cikin yanayin yaudara ta d'an konta kan k'irjin shi hannun tasa ta cusa a bayan shi, Ido ta lumshe tare dasa hannun tana shafa sajen shi har zuwa kan k'irjin shi tanayi tana lumshe ido, shi kuwa gaba d'aya ta zuba mishi kasala duk jijiyoyin jikin shi sun mace, ganin haka sai ta sake konta wa ta juya mishi baya ta kifu, shi kuwa sunkuyowa yayi ya rink'a kissing na tsakiyar bayan ta yanayi yana murzata gaba d'aya ya gigice ya gigitata a haka ya samu abinda yafi kwana 12 bai samuba, ita kuwa abinda ta saba fad'a mai shi take furta mai, "Bana sonka ni na tsaneka". hakan ya tunzura shi ya murzata har saida yaji ya huce ya kuma gamsu, sannan ya juya mata baya cikin maida numfashi yace, " Sai ki nemo wanda kike son yazo ya kaiki gidan ko". rai a b'ace ta jawo blanket d'in ta hard'eshi a jikin ta ta mik'e tana jan shi tana, "Sai Allah ya saka min tunda saida kayi tayin pakala iya son ranka sannan yanzu kace bazaka kaini ba". tana fad'in haka tana k'ok'arin fita d'akin, shi kuwa har cikin ranshi yake jin dad'i dan ya samu gamsuwa da ita kuma ta d'an sake mishi, abinda bai saniba boye laifinta take sonyi, itako har taje bakin k'ofar fita tace, " Ni kuwa bazan sake zuwa d'akin nan ba kuma mutun ko yazo min d'aki rufewa zanyi". Murmushi kawai yayi ya bita da ido, dan sakarcin Ummul yarin tane a ciki, ba gashi yanzu buk'atar tace ta kawota ba har ya samu shima tasa buk'atar ta biya so yasan gaban ma hakane. Haka rayuwa tayi ta tafiya, Usman kuwa a gefen shi ciwo ba sauk'i kullum sai gaba gaba yakeyi. Yau Saturday tun safe Usman bai lek'a ko k'ofar parlour suba, Nenne kuwa gaba d'aya hankalin ta na kanshi ganin har bayan la'asar bai shigo ba yasa ta mik'e ta nufi part d'in nasu, a hankali tayi sallama, shiru bai amsa ba dan yana zaune a k'asa a bak'in gado ya kifa kanshi a jikin gadon yana kuka mai cushe numfashi, a hankali Nenne ta rink'a jin sautin kukan nashi, tare da tari mai yanayin ciwon zuciya, a hankali ta shiga cikin d'akin kai tsaye bakin gadon taje ta zauna cikin sanyi tasa hannun ta tadafa kanshi, da sauri ya d'ago kanshi yana goge k'ollah dake bin fuskar shi, cikin k'arfin hali yayi murmushi , ido ta zuba mai cikin tuhuma tace, "Usman a zaton ka bansan meke damun ka bako?" kai ya jinjina tare da yin murmushi yace, "Nenne bani da matsalar komai". ido ta sake tsura mishi sannan tace, " Ummul ce matsalar ai". cikin sauri ya rink'a juya kai yana jin kunya na ratsashi ya za'ayi ya k'asa control d'in k'aunar Ummul a ranshi har mutane su gane yana son matar d'an uwanshi, ita kuwa Nenne kafad'an shi ta dafa a hankali tace, "Ban tab'a zaton shak'uwar ka da Ummul ya zama so a tsaka nin kuba har aka d'aura auren Ummul da Farouq duk a zaton shak'uwace kawai a tsaka ninku, Usman na fara Azargin kana son Ummul ne bayan Umar ya tafi da ita gidan shi, tun lokacin da ka fad'i ka suma na gane akwai abinda kake b'oyewa a ranka, ban gaskanta hakan ba sai randa kukaje gidan Ummul kuka dawo nanma kai ta aman jini sai kuma randa su Umar d'in suka zo manna ka birkice, sannan tunda suka tafi baka samu sukuni da kowa ba kuma doctor ya shaida mana akwai abin da kakeso kuma kana b'oyewa, Usman ni yanzu nasan Ummul kake so". tunda Nenne ta fara magana yayi shiru yana kallon ta, saida ta furta "Ummul kake so". sai ya kife kanshi kan cinyarta ya saki wani irin kuka murya a hargitse ya rik'o hannun ta ya rink'a juya mata kai a birkice yace, " Asiri na ya tonu naji kunya har gaban Ubangiji na tunda matar aure zuciya ta ke so ina zankai wannan zunubin? naji kunya a idanun duniya na rasa wacce zanso sai matar d'an uwana shak'ik'ina wanda bayi da b'uri a duniya daya wuce farin ciki na". sai kuma ya kuma kife kai yayi ta kuka mai tarin firgici cikin rawan murya ya durk'usa gaban Nenne a hankali yace, "Nenne ki rufa min asiri ki tayani b'oye wannan sirrin nawa kodako zai zama ajalina dan Allah karki gayawa ko daga ni sai ke ". itama Nenne kuka takeyi sosai dan Usman ya zama abin tausayi, a hankali tace, " kana ganin a haka zakaci gaba da boye abin a ranka ne?" Kai ya jinjina a hankali yace, "Nenne taima kona zakiyi kisa baki Abba da Hamma Umar su barni intafi India inbar k'asar gaba d'aya na tabbatar zan samu sauk'in abin a raina in nayi nesa da Ummul". kallon shi tayi a hankali tace, in dai haka zai sama maka sauk'i toh ba matsala". Haka kuwa akayi Nenne ta ajiye Hamma Umar da Abba tayi ta rokawa Usman d'in a barshi ya tafi ai yace ya samu lafiya kuma daga can zai k'ara ganin doctor, shi kam Hamma Umar har cikin ransa baya son tafiyar da d'an uwanshi zaiyi amman Abba da Daddy sun yarda dole shima ya yarda, shi kuwa Usman ya fara shirin tafiya cikin happy da kewar d'an uwanshi da Ammin su abar k'aunar su ji yake kamar ya fasa tafiyar dan gani yake kamar shike nan ya rabu dasu kenan har abadan, haka dai ya d'aure ya tafi. Gidan Alhaji Bello kuwa mahaifin Mustapha gaba d'aya rayuwar Mustapha ta juya ta canza Mustapha ya zama abin tausayi dan tabbas har cikin ransa yake son Ummul mahaifin shi kuwa ganin ya rasa Ummul d'in ne yasa yace zai had'a shi da y'ar k'anwar shi, yau tun safe aketa fama da Mustapha iyayen shi sun sashi a gaba kan batun auren amman sai ya d'ago ya kallesu fuska cike da k'ollah yace, " Daddy ni ba zanyi aure ba Daddy dan Allah kuyi hak'uri ni bana son auren ,bazan iya auren bafa". Ido Daddyn ya zuba mishi cikin sanyi yace, "Mustapha shin kana fushi da hukuncin Ubangiji ne? ya za'ayi kace bazaki yi aure ba bayan kuma kana da damar yin auren ashe dan ka rasa Ummul bazaka so y'ar uwarka Amina ba shin ko zakaci gaba da son matar aure?" kai ya rink'a juyawa yana zubda k'ollah yace, "Daddy bana son Amina kona aureta bazata ji dad'in zama da niba Daddy bana son cutar da ita". Mahaifiyar shi ce ta kalleshi cikin tausayawa tace, " Mustapha wata rana zaka so Amina na kuma tabbata zatayi ma biyayya tunda dama ita tana sonka kuma indai mun isa da kai toh ka aminci da auren nan". a hankali ya mik'e cikin rawan murya yace, "Shike nan Daddy na aminci indai hakan zai saku farin ciki". murmushi Daddy yayi cikin jin dad'i sannan suka bishi da Addu'a, shi kuwa yana fita d'akin shi ya nufa a parlour ya konta a k'asa yayi shiru yana tuno irin shirin da yakeyi na auren Ummul kawai sai ya rink'a kuka yana istgifari dan tuno cewa Ummul fa yanzu matar aure ce, haka akayi ta shirin auren Mustapha da Amina.. Gidan Hamma Umar kuwa tun randa Ummul taje d'akin Hamma Umar d'in ya kusance ta daga Wannan ranan , rayuwar Ummul ta fara canzawa wani irin abin al'ajabi da tsoro ya rink'a bibiyar Ummul, tun daga yamma cin wannan ranar Ummul ta farajin hannun ta da akasawa robar family planning d'in yana mata wani irin nauyi sannan sai taji hannun kamar ba a jikinta yaje ba gaba d'aya sai zuciyar ta ta rink'a tsinke wa wata iriyar kasala ta rink'a rufeta, a haka a daddafe tayi sallan maggariba da isha, cikin kasala ta zame ta konta kan sallayar da nufin zatayi bacci , Amman sai ga wani sabon al'amari mai ban tsoro kuma, bayan ta konta tayi Addu'a sannan ta lumshe ido a hankali bacci ya fara fizgarta, lokaci d'aya bacci mai dad'i ya d'ebeta, Amman cikin baccin sai taga Hamma Umar yana rik'e da jariri fari tas mai kyau yaron sai kuka yakeyi shi kuwa Hamma Umar sai ya mik'e mata jaririn ita kuwa sai ta ture ta juya ta gudu can gefen su, shiko Hamma Umar d'in sai yasa yaron a kafad'an shi yana lallashin jaririn yana ta zirga-zirga shiko jaririn sai kuka yakeyi da k'arfi, ganin haka ta tashi a firgice al'wala taje ta kumayi sannan tazo ta kumayi Addu'a sannan ta sake kwanciyar bayan kamar minti 30 bacci ya sake d'auke ta, still cikin baccin ta sake ganin Hamma Umar zaune cikin jarirai sai kuka sukayi da k'arfi duk sun cika gidan da kuka, a hankali ta rink'a ganin jariran sun dawo gareta sunata kuka shima Hamma Umar ya koma gefen su yana kallon jariran yana zubda k'ollah, haka ta sake farkawa a firgice, Toh fa haka Ummul take rayuwa ba bacci data rumtse idanun ta sai taga ana binta da jarirai suna kuka har abin ya fara zame mata ko a gyegyed'i takeyi sai tayi tajin kukan jarirai ga hannun ta kuma yamma nayi yake fara ciwo ta kuma k'i ta gayawa kowa Hamma Umar kuwa ko sabgarta ya dena shiga , sai ya kwana nafilfilin shi yana mai rok'on Allah ya azurtashi da haihuwa kullum Addu'ar sa Allah yasa Ummul ta samu ciki dan yana son haihuwa tare da ita sai azumi da yake yawan yi dan ya rege k'arfin sha'awarsa tunda yasan ba kulawar Ummul zai samuba, itako Ummul zuwa yanzu har tsoro take dere yayi da zaran yamma tayi bata da sauran kwanciyar hankali. Yau juma'a tun safe Hamma Umar yake d'akin shi yana ta karatun qura'an har zuwa 12 sannan yayi wonka ya shirya sab cikin fararen tufafi sai k'amshin turaren shi na du'a'ul jannah yake yi sannan ya fito hannun shi rik'e da sallaya a parlour ya samu Ummul zaune cikin yanayin bacci dan yau koda safen da zaran ta rufe ido sai taga ana mik'o mata jarirai gaba d'aya baccin sai yasa mata ciwon kai ga hannun ta da takeji kamar ba nataba gashi dai ba kumbura yayi ba amman jin hannun take kamar dutsi, tana ganin shi ta matso gaban shi cikin yin mik'a ido a lumshe tace, "Hamma Umar a bani maganin bacci mana". bai kalleta ba bai kuma yi magana ba har yaje bakin k'afa sannan yace, " sabida me? zan baki maganin bacci?" "Bana samun bacci ne shiyasa". " baki da lafiya ne?" "A a ni lafiya ta lau". Juyawa yayi ya d'an kalleta sannan ya girgiza kai ya fice, koda akayi sallan juma'a potaskum ya nufa kai tsaye gidan Inna ya nufa ranar ko lek'a gidan Abba baiyi ba dan tunda Usman ya tafi baya son zuwa gidan sosai, yana zuwa ya wuni da Ammin su sunata hira ya kira Usman d'in ma a woya sun dad'e suna hira, shine bai nufi hanyar damaturu ba sai bayan sallan ishah sannan ya kama hanyar, ita kuwa Ummul gaba d'aya ta birkice bacci na shirin zautar da ita sai zirga-zirga takeyi da zaran ta konta in tayi baccin minti 30 dai toh sai mafarkin jarirai, shi kuwa Hamma Umar yana isowa kai tsaye bedroom d'in shi kawai ya nufa, wonka yayi sannan ya konta rik'e da woyar shi yana magana da Ammin shi yana shaida mata ya isa lafiya, ita kuwa Ummul a hankali ta samu baccin ya saceta, bacci mai nauyi cikin nisan baccin ta fara juyo kukan jarirai ba adadi kukan sai k'ara matsota yake har taga jariran sun cika kan gadon nata sai kuma taga hannu wani mutun ya yarfa mata mari sannan ya nuna mata wani fili mai kyau inda ta haggo Hamma Umar yana zaune rik'e da jariri yana ta kallon ta yana murmushi tana cikin mamaki ina Hamma Umar a samo yaron nan sai taji an kuma yarfa mata marin tare da buga mata tsawa, " tashi kije ki karb'i d'an ki". A firgice ta farka da jin marin tayi kamar a zahiri, lokaci d'aya wani irin tsoro ya rufeta gaba d'aya jikinta sai zufa ke tsatstsafo mata hannun ta kuwa sai rawa yake kar-kar, sai kuma taji kukan kululluka a saman d'akin ta, haka yasa ta mik'e cikin tsananin tsoro da gudu ta fito parlour sai kuma ta nufi bedroom d'in Hamma Umar d'in tana shiga ta ganshi zaune kan sallaya hannun shi rik'e da qura'an da gudu taje ta fad'a jikin shi gaba d'aya jikin ta sai tsuma yakeyi hannun tasa ta ruggume shi da k'arfi kanta take ta cusawa cikin k'irjin shi tana to she kunnen ta, da sauri ya kalleta cikin mamaki ganin yadda take boye kanta a jikin shi yasa shima ya k'ara ruggume ta sannan ya rufe qura'an d'in ya ajiye kan mirror , ita kuwa Ummul sai kuka takeyi cikin tsananin jin tsoro, kanta ya d'ago a hankali yace, "Ummul meke faruwa ne?" baki na rawa tace, "Hamma tsoro nake ji Hamma kullum bana bacci mafarkin jarirai nakeyi suna kuka suna hanani bacci". Jawota jikin shi yayi ya kara ruggume ta cikin mamaki yace, " jarirai kuma? toh banda abin ki Khairi kukan jarirai kuma me abin tsoro a ciki?". K'ara mak'aleshi tayi tana, kuka tace, "Suna da yawafa kuma yau har dukana akeyi". ruggume ta yayi ya mik'e da ita kan gado ya kontar da ita sannan ya konta gefen ta ya ruggume ta yana shafa kanta cikin sanyi yace, " kiyi shiru kibar kukan ba komai kinji ko". Ido ta rumtse sai kuma ta mik'e da sauri ganin wani hannun yana sa wuk'a kan damtsen hanunta dai-dai inda akasa mata robar , hannun ta rink'a turawa Hamman tana kuka tana, "Hamma ka cire min Hamma zasu yanke min hannun Hamma ka cire min". Cikin mamaki ya kamo hannun yana duddubawa tare da cewa, " Zasu yanke miki hannun kuma? me a hannun naki?" shiru yayi dai-dai lokacin da yatsun shi suka sauk'a kan inda akasa mata robar, d'ago hannun nata yayi da kyau ya duba wurin cikin rawan baki yace, "Family planning kikayi ne?" kai ta gyada mai cikin zafin da taji hannun yana mata, tureta yayi da karfi lokaci d'aya idanu shi sukayi jazir gaba d'aya jikin shi sai rawa yakeyi murya a hargitse yace, " fita min a d'aki ki koma can d'akin ki kisan hujjar da zaki gayawa ubangijinmu kisan yadda zakiyi da jariran dake binki suna kuka ki gaya musu dalilinki na hanasu zuwa duniya Ummul kiji tsoron Allah ki tuba ki koma gareshi tun lokaci bai k'ure mini ba". sai kuma ya kamo hannun ya matse da k'arfi har saida tayi k'ara mai cike da gigita, tureta ya kumayi sannan yace, "Idan Allah yace ehh toh fa ke Ummul baki isa ki ce a,a ba ki sani idan Allah ya k'addara sai kin haihu dani wallahi wannan robar bata isa ta hana cikina shiga jikin kiba". ita kam Umml sai zare ido take tana kuka, gaba d'aya tsoron shi ya rufeta, shi kuma murmurshin takaici yati wanda yafi kuka ciwo sannan ya nunata da yatsa yace, " kina so kija da yin rabbi toh gashi kinga ishara tun ba'aje ko inaba kinga duk abunda kikeyi koni ban saniba Allah ya sani, wallahi ki shirya me zaki cewa Abba da Adam da Sadik kome zasuyi miki bazan hanaba kuma zan gaya musu abinda kikayi zan kuma kaiki gabansu in sunga damage su tsireki ki kuma je ki samu mahaliccin mu tunda bakya tsoron Allah". kuka ta kamayi sosai tana, "Wayyo Allah na dan Allah Hamma ka rufa min asiri wallahi ya Adam zai kusan kasheni gashi ya Usman baya nan ba wanda zai ceceni kayi hak'uri wallahi bazan sake ba ya Sadik zai karyani Abbana zaiyi fushi dani Hamma wallahi bazan sake ba". Cikin tsawa yace, " ki dai ji tsoron Allah, kuma ki shirya da sassafe zamu tafi abunki ya fara bani tsoro na lura baki da tausayi". yana kaiwa nan ya fita ya bar mata d'akin, binshi tayi a baya tana ta magiya da tuba, bai kulataba ya wuce d'aya d'akin ita kuwa a parlour ta kwana tana magiya bata kuma samu ta rumtsa ba. Washe gari bayan ya dawo masallaci yana shiga parlour tabi bayan shi murya a disashe tace, "Ayyah Hamma na dan Allah kayi hak'uri wallahi bazan sakeba kaji na rantse dan Allah karka gayawa ya Adam". bai kulata ba ya fara shiri , ganin haka ta lallab'a ta d'auki woyarshi ya Usman ta kira, yana d'agawa cikin sanyin murya yace, " Hamma na ina sonka yauma nayi mafarkin ka nayi kewarku zan dawo". Cikin sanyi tace, "Ya Usman dan Allah ka bawa Hamma Umar hak'uri karya kaini gida kasan ya Adam mugune zai karyani". Hannun shi yasa ya dafe k'ahon zuciyar shi dake harbawa cikin sanyi yace, " Allah ya d'aiyiba min k'anwata, me kikayi wa Hamma na har yasashi fushi yace zai hadaki da Adam Boss?" Cikin sakarcin ta gayawa Usman abin da tayin, tanayi tana kuka, shi kuwa Hamma Umar ido ya zuba mata cikin tsananin bak'in ciki, shi kuwa Usman gaba d'aya ranshi ya baci bai tab'a jin haushin Ummul ba akan batun auren su irin na yau rai a b'ace yaja dogon tsaki cikin fad'a yace, "Ummul ki sani in kin cutar da Hamma Umar toh kin cutar da zuciyata duk duniya bani da kamarshi amman kike gaya min bakya sonshi bazaki haihu da shiba Ummul d'an uwana kikeyi wa haka, bazan hanashi ba bazan bashi hak'uri ba ya kaiki duk inda zai kaiki kuma kiji a bakina, nida kaina zan gayawa Adam da Abba". jin haka saita kuma fashewa da kuka ta mik'awa Hamma Umar d'in woyar baki na rawa tace, " Dan Allah Hamma Umar ka bawa ya Usman hak'uri dan Allah karku gayawa ya Adam". Woyar ya karb'a cikin k'aunar juna suka fara magana, Usman ne ya d'an yi shiru sana yace, "Hamma yanzu forko dai ka cire mata robar daga nan kuma kayi abinda ya dace da ita". A hakali yace, " Me zan iya yiwa Ummul, Usman duk hukunci da zanyi yunk'urin d'auka a kanta zai kasance na gaza rik'e al'k'awari da amanar dana d'auka". shiru Usman yayi sannan yace, "Toh ni zan gayawa Adam dan ajamata kunne". yana kaiwa nan ya katse kiran, shi kuwa Hamma Umar mik'ewa yayi ya yawo hannun Ummul d'in kai tsaye harabar gidan ya fita da ita, cikin mota ya sata, sannan shima ya shiga yana shiga ya figi mortar kai tsaye ya kama hanyar potaskum, tana ganin haka cikin tsoro ta kwanta kan....... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 2⃣2⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Ina kike ne Nana Fa'ad wannan shafi naki ne ke kad'ai ban had'a ki da kowaba gaba d'ayansa nasa d'aukar da shafin nan a gareni har kullum ke ta daban ce ina al'fahari dake🤝😍😘* *Sisters kuyi hak'uri kwana biyu kun jini shiru banji dadine sosai Amman insha Allah zanke lallab'awa na rink'a yi mana typing ko kad'an -kad'an ne* *T*ana ganin haka cikin tsoro ta kwanta kan cinyar shi ta kifa kanta a jikin shi hannun ta zagaye kan kugunsa tana "Wlh bazan k'araba kayi hak'uri karka kaini gun Abba wallhi Ya Adam zai karya ni". cusa kanta tayi a k'irjin sa tana wani irin kuka tana cewa "Ayyah Hamma Umar dan Allah kayi min rai wallahi nayi alk'awari bazan sake ba, kaji kaina karka kaini gurin su Abba bana son fushin sa kuma Ya Adam zai dake ni" tana mai k'ara narkewa a jikin sa, shi kuma Hamma Umar wani kasala yaji tareda mugun tausayin ta amma haka ya b'ata rai yak'ara murtuke fuska yana driving koh kulata baiyi ba, ganin hakan hankalin ta ya k'ara mugun tashi ta k'ara narkewa a jikin sa sai wani shege masa take ta ta cusa hannun ta cikin suman kansa tana mai masa sosa cikin kissa tana mai had'a sajen sa da fuskan ta tana wani iri kuka had'e da shagwab'a tana cewa "Wallahi Allah Hamma Umar ka yarda dani nayi al'kwari bazan sake ba, idan na k'ara without any second thought ka kai k'arana na yarda amma yanzu dan Allah kayi hak'uri ka yafe mini Insha Allah bazan sake ba" tana mai masa sosa kamar tafiyan tsutsa a hankali cikin sumar kansa, ganin tana neman rikita masa brain muddin tacigaba bazai ma iya tukin ba nan take yayi reverse da motar ya juya ya kama hanyan komawa damaturu, ganin haka ta sauke naunauyar ajiyan zuciya tareda hamdala cikin ranta tace "Nagode Hamma Umar Inshaa Allah bazan kara ba" shi kuwa koh kulata baiyi ba yacigaba da driving nasa ita kuma ta gyara zaman ta a seat tareda lumshe idanuwan ta. Direct general Hospital dake cikin damaturu ya kaita. bayan yayi parking motar sa a parking lot ya kalleta yace " sai ki fito mu shiga ai", ba tareda ta musan tashiba ta gyara hijabin ta, mik'a mata farar hankerchief yayi wanda yake fitar da wani k'amshi mai dad'in gaske yace "Haka zaki fita salon a ganeh kinyi kuka koh? Maza karb'a ki goge fuskan ki" ba musu ta karb'a hankerchief d'in ta goge fuskan ta,bayan ta kimsa yace "Toh muje koh" ba musu ta sauk'o a motar suka jera suna tafiya abun sha'awa har office na abokin shi Doctor Nasir Fuskan tausayi tayi tana kallon shi tace "Ayyah Hamma Umar fallasa ni kake sonyi? Salon abokin ka yasan abunda na aikata?". Hararar ta yayi ya bud'e office yashiga ita kuma tabisa a baya. Sosai Doctor Nasir ya amshe su yana mai zolayar abokin sa ango, bayan sun gama gaisawa Hamma Umar yace "Yawwa ina wancan Doctor'n take neh?" Cikin rashin fahimta Doctor Nasir yace, "Wacce kenan?" "Doctor Rukayya" "Ohh tana nan bari na kirata tazo tayi assisting naku" Ciro wayan sa yayi ya kirata tazo, dagan nan ya had'a su. Bayan an had'a ta da Doctor'n tayi mata fad'a sosai tareda mata wa'azi tace "D'an adam kenan, wasu har kuka suke. Wallahi jiya wata mata da tazo shekarunta arba'in da biyar kuma tun tana shekaru goma sha tara tayi aure, bata tab'a family planning bata tab'a koh da b'ari ba. Jiya da tazo ta same ni sanda na zubda hawaye, kuka take sosai tana masifan son haihuwa kuma Allah bai bata ba, amma ke sai k'okari toshe ni'iman Allah kike bayan mijin ki naso, gaskia kin bani kunya kin ban haushi" Haka ta ta mata masifa har ta cire roban tareda bata wasu magani. Bayan sun gama taje ta samu Hamma Umar a cikin motar sa yana zaune already daman sunyi waya ta same shi a cikin mota. Yana ganin ta da Doctor'n ya fita a motar sa ya mata godiya sosai tana mai k'ara basa hak'uri irin halin 'yan matan yanzu. daga nan ya shige motar sa daman tuni har Ummul ta shige ta kwanta a kan kujera tareda lumshe idanuwan ta,wani irin ciwon kai take ji dalilin kukan da tasha, tsantsan tausayin ta yaji ya shafa laulausar fuskan ta yace "Sannu kin gaji koh?" D'aga masa kai tayi ba tareda ta basa amsa ba, restaurant ya wuce ya musu odering abinci a take away yazo ya zuba su a seat na baya ya sake tsayawa ya siyo musu icecream dayawa daga nan ya kama hanyan gida. Suna isa Ummul direct d'akin ta tashige shi kuma ya kwasa kayakin da ya siya ya shigar dasu, icecream d'in ya zuba su a fridge ya ajiye abincin dinning shima ya shige d'akin sa dan wanka. Bayan ya fito ya saka jallabiyar sa ya fesa jikin sa da turaruka masu k'amshi gaske yaje d'akin Ummul, yana shiga ya ganta a kwance akan gado but da gani alama tayi wanka dan ta canza kaya, zama yayi a gefen ta yana mai shafan fuskan ta yace "Ummul taso muje muci abinci tun safe fa ba abun da kika ci sai d'azu da kika sha coke a asibiti", ita kanta tasan tana jin yunwan haka ta taso a daddafe tace "Toh muje". Tasowa yayi shima ya kama kugunta suka fara tafiya har dinning, ya jawo mata kujera ta zauna, haka yayi serving mata abinci taci ta koshi,daga nan yace "Ummul bari naje masallaci kinji kinga yanzu za'a kira magrib bayan sallah'n isha zan shigo". d'aga masa kai tayi tace "Toh sai ka dawo". Ganin yanayin da tayi magana da k'yar ya matso kusa da ita yace "Lafiya kuwa Ummul? meke damunki?", wasu zazzafan hawaye neh suke sauk'a akan kuncin ta tace "Hamma Umar ciwon kai", kallon ta yake da tausayi fal kwance kan fuskan sa yace "Kinga illan yawan kuka koh? maza tashi ki shiga d'akin ki na kawo miki magani kisha" Haka ta taso yana rik'e da ita har d'akin ta ya zaunar da ita kan bakin gado, ya shige d'akin sa ya d'auko magani ya had'o da faro ya mik'a mata, duk yadda yakai da batason magani ganin yadda ya tsareta da kallo ba yadda ta iya haka ta amsa maganin tasha, daga nan ya wuce masallaci itama ta tashi tayi sallah a daddafe, ita bata tashi akan daddumar sallah'n ba har sanda aka kira sallar isha'i tayi, a yanzu dai ta d'an ji saukin ciwon kai d'in. Shiga toilet tayi tayi brush tabi lafiyan gado sabida tana wani irin jin bacci, cikin minti biyu bacci b'arawo ya d'auke ta. Shima kuma Hamma Umar ana idar da sallah'n isha ya dawo gida, d'akin ta ya shiga ganin tana bacci ya k'aro rufe kofar yazo shi parlour ya had'a tea yana kallon news, shine bai tashi a gaban TV ba sai kusan k'arfe goma, shiga d'aki yayi ya watsa ruwa ya canza kaya zuwa pyjamas da singilet tareda shafa turaren sa mai dad'in gaske du'u'rul jannah, zuwa d'akin Ummul yayi ganin tana baccin ta hankali kwance ya gyara mata blanket nata ya mata addu'a ya tofa mata had'e da mata peck a goshin ta ya fita ya ja mata kofar d'akin. Kwanciya yayi akan gadon sa yayi addu'a, wani irin yanayi yafara ji yana zuwa masa ganin surar Ummul da yagani yanzu, yaso ya kau da tuninin amma hakan yaci tura, ganin bazai iya bacci ba ya taso ya nufe d'akin Ummul ya yaye blanket d'in ya kwanta ya k'ara ja musu blanket, matsowa yayi kusa da ita yana mai cusa kansa a k'irjin ta ya rungume ta sosai, take yaji yana tsananin bukatar ta nan ya k'ara rikicewa ya fara zame kayan dake jikin ta. Ummul tana bacci taji kamar mutum a jikin ta a firgice ta tashi ta ture shi, wutan gefenta ta kunna gadon ya zagayu da wuta ganin Hamma Umar tayi idon sa sai lumshe su yake yace "Ummul hakki na zaki bani", Hararan sa tayi tace "Hamma Umar nifa na gaji bacci nake ji kuma ba abunda zan iya maka gwara ka tashi ka tafi ihhe", matsowa yayi daf kusa da ita ya kwanta akan cinyar ta ya zagaya kugunta da hannayen sa yace "Kiyi hak'uri Khairi ina cikin wani yanayi ki taimaka wa mijin ki,koh so kike Allah yayi fushi dake?" Hawaye neh suke sauk'a akan kuncin ta tace "Nidai ka barni ba abun da zan iya maka kayi hak'uri kaima kaje ka kwanta", ganin so take ta hanasa yace "Idan baki bani hakki nah ba gobe zan kira Ya Adam na fad'a masa abunda kikayi kuma na k'ara da cewa baki son bani hakki nah", jin haka yasa tayi mugun tsorata tana hawaye tace "Kayi hak'uri dan Allah karka fad'awa Ya Adam wlh zai kashe ni, Abba da Nenne zasuyi fushi dani yanzu kaga Ya Usman shima yana fushi dani kayi min rai" K'ara cusa kansa yayi a cinyar ta yana mai mata sosa a cikin ta yace "Idan baki so na fad'a musu toh ki bani hakki nah" Shiru tayi tana mai zubda kwalla, d'aga kansa yayi akan cinyoyin ta ya zagaya kugun ta da hannayen sa, had'a lips nashi da nata yayi yana mata tsotsan lollipop, haka yata kissing nata hannayen sa yana mai cusa wa cikin rigar ta haka har ya samu daman rabata da kayan jikinta, a haka suka shiga cikin duniyar ma'aurata, sanda ya samu nutsuwa ya kyale ta ita kuma ta gama shan wahala, har a ranta bata tab'a jin sonsa koh da d'igo d'aya a ranta ba, hawaye neh yake sauk'a akan kuncin ta shi kuma sosai ya rungume ta yana saka mata albarka, k'asa bacci yayi dan ba k'aramin jin dad'i yayi ba da samun nutsuwa, can kuwa ya cusa kansa a k'irjin ta yana mai shakan k'amshi jikin ta, gana fulanin ta wanda yake k'ara sa gashin jikin sa tashi, hannun sa yasa yana mai shafawa su yana lumshe idanuwan sa, a haka har bacci ya sace sa.. Kiran sallah'n ASubh na farko ya tashi yayi wanka yayi alwala yazo ya tada Ummul, sai wani mik'a take cikin muryan bacci tace "Ayya Hamma dan Allah ka barni na d'an k'ara bacci kad'an" "Hak'uri zakiyi Ummul kiyi wanka muyi sallah", ganin batada niyyar tashiwa ya cincib'e ta ya d'auke ta cak ya kaita toilet sai cikin bahon wanka wanda already ya had'a ruwa mai d'umi, wani d'an k'ara washh ta sake cikin kukan shagwab'a tace "Wayyoo Hamma ruwan fa zafi" "Hak'uri zakiyi shi zai saka ki samu k'arfin jiki". so yake ya mata wanka amma tace ita sam bata yarda ba ita da kanta zatayi, a haka ya fita a toilet d'in ya barta. Kusan minti ashirin tayi kan ta fito a toilet d'in ta fesa body spray ta saka doguwar riga tareda da zuga hijabin ta. Sallah yajasu bayan sun idar ta k'ara komawa bacci shi kuma ya d'au Al Qur'anin sa ya fara reciting a haka har gari yayi haske shima yaje d'akin sa ya kwanta nan da nan bacci ya d'auke sa. Shi bai farka ba sai kusan k'arfe goma sha d'aya , nan take ya shiga Kitchen ya had'a tea ya dafa musu indomie yakai dinning, sallama yayi ya shiga d'akin Ummul a lokacin kenan ta fito daga wanka daga ita sai towel a jikin ta, tana ganin sa ta had'a rai tace "Ina kwana" tareda d'auke kanta , zuwa yayi daf kusa da ita ganin yadda dogon bak'in gashin kanta a jek'e abun ba k'aramin yi masa kyau tayi da sha'awa ba, hannayen sa ya zagaya kugunta tareda hura mata iskan bakin sa yace "Morning Mata ta", hannun sa take son rabawa da jikin ta amma ta kasa, d'an guntun tsaki taja tace "Hamma dan Allah ka barni na shirya kaji", d'an k'aramin bakin ta yake kallo da yadda take tura shi, nan ya d'an tsuguna ya had'a fuskokin su tare suna mai shak'an numfashin juna, haka ya k'ara had'a dogon hancin sa da nata ya cusa hannayen sa cikin sumar kanta, haka ya had'a lips nasu tare yana masa tsotsa cikin kwarewa da wani irin salo wanda ya banbanta fiye dana kullum, sanda yasha bakin ta iya son ransa kan ya rabu da ita, yace "Idan kin gama ki fito kici breakfast", cikin konar rai tace "Bazan ciba bana jin yunwa " tana mai zubda kwalla. Cire wayan sa yayi cikin aljihun sa yace "yanzu zan kira Ya Usman na fad'a masa kina kuka kuma kinki cin abinci" Nan take ta share hawayen ta tace "Ayyah Hamma Umar kayi hak'uri karka fad'a masa kaga na daina kukan" tana mai goge hawayen ta "Bazan k'ara ba kuma zanci abincin dan Allah karka fad'a masa", shi kuwa Hamma Umar already yayi dialing number, yana d'auka wa suka gaisa yana mai tambayar lafiyan sa, Ya Usman cikin sanyin murya yace "Hamma Umar ina missing naka kuma ina sonka sosai sosai", Murmushi Hamma Umar yayi yace "Nima ina missing naka b'iyayye nah kuma ina sonka sosai", murmushi mai sauti Ya Usman yayi yace "Ina Ummul", shima murmushin yayi yace "Gata nan bari na mik'a mata ku gaisa", wanda ita kuma Ummul ta gama tsorata ita duk a tunanin ta zai fad'a sai kuma taga bai fad'a ba, karb'an wayan tayi shi kuma ya fece a d'akin, wani ajiyar zuciya ta sauk'e cikin sansayyar muryan ta tace "Ya Usman ina sonka", Usman dake kwance akan gado sanda yaji zuciyan sa kamar an tsoka masa kibiya yayi murmushi yace "Allah ya dayyiba kanwata", dariya sosai tayi tana mai k'ara jin kaunar yayan ta a ranta tace "Ya Usman gaskia baka kyauta mun ba ka barni anan kawai inata missing naka ni yaushe zaka dawo?" "Kanwata karki damu very soon zaki ganni bi'iznillah", sai jansa take da hira, shi kuma sai k'okari kau da hiran yake, ganin batada niyyar bari yace "Ummul nizan fita anjima zan kira ki", kukan shagwab'a tayi tace "Promise?", aziyan zuciya yayi yace "In Shaa Allah", haka ta katse wayan bawai dan tagaji da hira dashi ba, shirya wa tayi taje dinning taci abincin ta, shi kuwa Hamma Umar sai satan kallon ta yake, bayan ya gama ya shirya tsaf yace zashi aiki ya mata peck a forehead nata yace "Sai na dawo", tura bakin ta tayi tace "Allah kiyaye hanya" A yau aka d'aura auren Mustapha da 'yar uwar sa Amina, duk da baya so amma ba yadda ya iya mahaifan sa sun matsa kuma dole ya musu biyayya, da daddare Mama da Daddy suka kirasa d'aki suka masa wa'azi da nasiha mai ratsa jiki, Daddy yace "Kaga Amina amana ce aka baka dan Allah ka rik'e ta amana kar kace baka sonta In Shaa Allah wata rana zakayi alfahari da abunda muka zab'a maka", kansa a k'asa yace "Nayi alk'awari Daddy In Shaa Allah zan rik'e ta bisa amana" Da daddare Ummul tana kwance akan gadon ta tana game da wayar Hamman, Hamma Umar d'in yayi sallama yashiga sai zuba k'amshi yake, can kasa kasa ta amsa, zama yayi akan gadon ya jawo ta jikin sa yana mai shafa bayan ta, turesa tayi da iya k'arfin ta tace "Nifa gaskia bana so Hamma Umar bana sonka". barin ta yayi yace "Toh tunda kince bakiso zan kai karar ki ma Ya Adam". cikin tashin hankali tace "Haba Hamma kayi hak'uri dan Allah ai na fad'a maka na tuba". "Idan har baki so na fad'a toh ki bani hakki nah ". duk da bata so amma tsoran karya fad'a a gida ta amincewa bukatar sa har ya samu nutsuwa. A haka kullum yake mata idan taki ta basa had'in kai sai yayi threatening nata akan zai fad'awa su Ya Adam da Abba haka zata hak'ura ta bada kai bori ya hau haka kullum. Ya Usman a India kuma duk da yana seeking medical health amma kusan kullum sai yayi aman jini, haka zai kulle kansa a d'aki yata kuka har muryan sa ya dashe hawaye su daina sauk'o wa kan zaiyi shuru. A haka rayuwa ta cigaba masa sannan kuma ya fara shirin dawowa dan yayi kewar d'an uwanshi .. A kwana a tashi ba wuya yanzu sun kusan wata uku cur tareda Hamma Umar, a kullum idan taki ta amince da bukatar sa sai yayi threatening nata yace zai fad'a wa su Ya Adam, ta k'ara haske sosai sai dai ta d'anyi rama, ga wani son cin abincin da take yanzu tana cin abinci yanzu anjima kad'an zata fara jin yunwa, koh cikin dare idan taji yunwa zata tashe Hamma Umar ya had'a mata tea taci da snacks ta koma bacci, da sassafe tana sallah'n Subh zata ci abinci sai kuma ta koma bacci cikin kasala yau kam kamar abin yafi na kullum dan yau tunda ta tashi bacci take ta bin bayan Hamma Umar d'in tana rirrik'eshi dan jiri takeji dan tsabar yunwar dake kwakwularta, kallon ta yayi a hankali yace, "tsaya a nan Ummul bari in shiga kitchen in kawo miki abinda zakici". yana fad'in haka ya janye hannun shi ya shige kitchen d'in, ita kuwa a take duhu ya rufe mata idanun da wani irin jiri ya kwasheta lokaci d'aya k'afafun ta suka rink'a rawa sai ko tayi wani irin... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 2⃣3⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Kuyi hakuri sisters da jinkirin da muke samu na Rashin yin typing hakan ya farune bisa wasu larurai da sukasha kaina nasan ku kanku readers kun san ba haka na sabayi ba so nasan zakuyi min uzuri ngd da addu'ainku gareni Allah bar zumunci da k'auna* *I*tako atake duhu ya rufe mata idanu da wani irin jiri ya kwashe ta lokaci d'aya kafafuwan ta suka ringa rawa sai kuwa ta fad'i kasa a sume. Hamma Umar ba k'aramin birkice wa ba yayi daya fito a kitchen ya ganta cikin irin wannan halin, a rikice ya cincib'ota ya kaita d'aki ya kwantar da ita akan gado. Ruwa ya d'auko da sauri a fridge ya yayyafa mata nan take tayi wani irin ajiyan zuciya tareda bud'e idanuwan ta, cikin tashin hankali Hamma Umar yake tambayar ta lafiya tareda shafo fuskan ta, wani irin kuka ta fashe dashi tace "Yunwa nake ji ga kuma ciwon kai". Take ya d'auko mata Indomie'n da ya dafa ya mik'a mata, cikin five minutes sai gashi ta cinye shi tas ta wani tura bakin ta tace "Hamma Umar nifa ban k'oshi ba", bud'e baki yayi yana kallon ta da yasan Ummul bata iya cinye indomie k'anana biyu gashi yau ta cinye shi tas kuma tana kukan bai ishe taba, yace "Toh bari naje na k'ara dafa miki wani", turo bakin ta tayi tace "Ni yanzu wainan kwai nake so na.." bata k'arasa taji wani irin mai na zuwa mata take ta tashi tana son fita a d'akin taje toilet da gudu nan take Hamma Umar ya rik'e sai kawai ta fara aman a jikin sa, yi take har sanda ta amar da Indomie'n gaba d'aya a jikin sa, hankalin sa tashe sai sannu yake jero mata, a hankali ya kaita band'aki ya mik'a mata towel ta cire rigan jikinta ta wanke fuskan ta da hannun ta, bayan ya kwantar da ita akan gado shima ya fad'a toilet yayi wanka. Bayan ya fito ya saka jallabiyar sa sai baza k'amshi yake amma kallo d'aya zaka masa kasan hankalin sa a tashe, matsowa yayi kusa da Ummul dake kwance ta lumshe idanuwan ta, shafo fuskan ta yayi yace "Ummul bakya jin dad'i ashe, meh da meh yake miki ciwo?", hawaye tafara tace "Hamma ciwon kai kuma ni yanzu yunwa sosai nakeji ni gaskia ka kaini gida", shafa fuskan ta yayi yace "Yi hak'uri zan kaiki gida kinji yanzu meh kike so kici", shuru tayi na d'an wani lokaci tace "Bread da shayi", Allah ya so shi akwai biredi a gidan ya had'a mata da shayi taci. D'akin sa yaje ya d'au kayan aikin sa ya k'ara dawowa d'aki, cire allura yayi ya lallashe ta kan ta yarda ya d'au jinin ta, canza kayan sa yayi ya saka ash shadda wanda ya amshe sa ya masa kyau sosai yace "Ummul yanzu meh kike so kice dan ni zanje na bada jinin ki a lab suyi test" Take tace masa "D'anwake da alale", fita yayi ya siyo kan ya dawo har ma tayi bacci, ajiye mata yayi a d'aki a flask na tea ya fita. Direct lab ya wuce ya bada jinin ta ma wani abokin sa yace a mata test na Widal, Mp da PT emergency neh yanzu yake so. Cikin awa d'aya kaf aka gama masa tests d'in yana zaune a office na abokin sa aka kawo masa gaba d'aya uku tests result d'in. Karb'a yayi ya bud'e Widal result d'in yaga bata dashi gaba d'aya 40% da 80% wanda yake nunin batada typhoid, sannan ya bud'e na Mp yaga +1 tana da malaria'n amma ba sosai ba, a hankali ya bud'e result na pregnancy tests d'in idon sa yakai ga Positive, bai yadda da abunda yake gani ba har sanda ya k'ara bud'e idon sa da kyau harda goge idon sa, matar data kawo masa results d'in tayi dariya tace "Tabbas idon ka bai maka k'arya ba congratulations matar ka tana da cikin wata uku", nan take ya d'aga eyes nasa yana kallon ta nan take ya tashi a kujeran da yake zaune yayi sujada ya d'ago ya d'aga hannayen sa sama hawaye ya cika fal a idon sa yace "Allah nagode maka! Alhamdulillah Yaa Allah!" Take ya fita a d'akin yaje parking lot inda yayi parking motar sa, shiga yayi cikin motar yana murmushi yaja motar sai wani babban restaurant, abinci fried rice ya siya da Ice cream ya wuce gida. Da sallama ya shiga d'akin ta a lokacin Ummul tana kan sallaya ta idar da sallah, rungume ta yayi sosai ta baya yana mai shakan k'amshi ta, tura bakin ta tayi tace "Hamma Umar please ka barni k'amshi turaren ka na tada mun da zuciya", murmushi yayi ya raba jikin sa da nata yazo gaban ta yana kallon ta with so much tenderness in his eyes yana murmushi yace "Guess what?", tura bakin ta tayi tace "Hamma Umar I ain't good at guessing kawai ka fad'a mini menene?", k'ara rungume ta yayi sosai cikin rad'a a kunnen ta yace "Ummul kina da cikin wata uku" Zuciyan tane taji ya wani irin tsinkewa cikin k'arfi ta raba jikin ta da nasa hawaye fal kwance a kan kuncin ta tace "Na shiga uku nah ni Ummul Khairi", tareda aza hannu biyu a kaa, take ta fashe da wani irin kuka tace "Wallahi bana so bazan yadda ba sai dai a cire cikin nan, wallahi bazan bar cikin nan a jiki na ba", kallon ta yake yana ga yadda ta zauna ta mimmik'e k'afafu tana dukan cikin da k'arfi, ransa a b'ace yace "Hak'uri zakiyi Khairi dan ni wallahi inason cikin nan", tasowa tayi tana kuka taci gaba da dukan cikin da k'arfin da Allah ya bata tana, "Wallahi Allah sai dai ya zube ni bazan bar cikin nan ba sai dai ya zub'e" Tana mai buga cikin da hannun ta, nan take Hamma Umar ya rik'e hannun ta cikin lallashi yace "Ayyah Khairi yanzu baza kiyi hak'uri ki rungume k'addara ba, mata nawa suke neman haihuwa a duniyan nan Allah bai basu ba dan Allah kiyi hak'uri ki haifa min yaron nan ina matuk'ar son cikin nan fiyeda komai na rayuwa ta". Kuka take tana mai zubda kayan gaban dressing mirror'n ta tana wasar dasu a k'asa tana "Wallahi Allah bazan bar cikin nan ba, wayyo Allah na nashiga uku kowa baya so nah zasu d'aura min hawan jini, wayyo Allah nashiga uku", tana kuka sosai Kama ta yayi ya zaunar da ita akan gado yana mai rok'on ta Allah da annabi tabar masa cikin "Khairi dan Allah ki rufa mini asiri dan darajan manzon Allah S.W.A ki bar min cikin nan, a yanzu inason cikin nan fiyeda komai a rayuwa ta dan Allah Khairi". Cikin kuka tace "Bazan iyaba Hamma Umar kayi hak'uri nidai kam gaskia a cire cikin nan, idan kuma kaki koh ta yaya zan cire cikin nan" Haka zai ta lallashin ta har dare, tun safe data ci abinci bata k'ara ci ba, sosai take jin yunwa har jikin ta rawa yake yana karkarwa, Hamma Umar rik'e hannun ta yayi hawaye fal a cikin idon sa yace "Dan Allah Khairi kici abinci kiga jikin mi har rawa yake yi dan Allah", ganin yadda ya marairaice ga hawaye ciki a idon sa yasa ta d'an ji tausayin sa tace " Toh ka kawo min". Take ya taso jikin sa har b'ari yake yayi warming fried rice d'in ya kawo mata, sosai taci abincin tana gama ci ta fad'a toilet tayi wanka bayan ta fito tayi sallah, kwanciyar ta tayi a k'asa ba yadda baiyi da ita ta hau kan gado ba amma taki tace ita sam a k'asa zata kwana. Tsaban irin kukan da tayi koh minti biyar batayi da kwanciya ba bacci ya sace ta. Bayan tayi nesa a bacci ya d'auke ta cak sai kan gado tareda rufe mata jiki da bargo. Alwala yayi yafara jera nafiloli bayan ya idar ya d'au Al Qur'anin sa yana reciting. Shi bai kwanta bacci ba dai kusan k'arfe uku da rabi. Washegari da safe Ummul da wani irin yunwa ta tashi, Hamma Umar dake kwance akan cushion ganin ta tashi tana juye-juye ya taso ya same ta yace "Khairi lafiya kuwa", kuka ta fashe dashi tace "Ni Allah nagaji da cikin nan sai wani yunwa yake sa nakeji kamar wata mayya ni gaskia Allah bazan yarda ba sai an cire cikin", rik'e hannayen ta gam yayi yace "Eyyah Khairi hak'uri zakiyi kinji, ciki ai rahama neh daga Allah" Sabon kuka ta fashe dashi tace "Toh ni haka zan ta fama a yunwa kullum, ni kuma bason cikin nake ba gaskia dole ka cire shi". Sosai yake kallon ta idan tayi maganar zub da cikin ji yake kamar an tsoka masa kibiya a zuciya, shafo fuskan ta yayi yace " Yanzu bara na kawo miki shayi kici kinji?" D'aga kai tayi ba tareda ta amsa masa ba, tashiwa yayi ya had'a mata tea ya soya mata kwai ya kawo mata tareda bread. Sosai ta ci tana ci tana hawaye shi kuwa na kallon ikon Allah, bayan ta gama ci ya kwashe su flask d'in ya kai kitchen ya d'aura alwala itama haka sukayi sallah'n asuba. Suna idar wa ya fara karanta Al Qur'ani ita kuma tabi lafiyan gado ta kwanta dan wani irin bala'in bacci neh ke addaban ta, shi kuwa Hamma Umar sanda tana ta fito kan ya rufe ya kwanta a k'asa kan carpet shima cikin minti biyar bacci ya d'auke sa dan jiya bai samu yin bacci da wuri ba... Misalin k'arfe goman safe ji yake kamar ana bubbuga shi cikin mafarki, a hankali ya bud'e idon sa yaga Ummul hawaye kwance fal a kuncin ta, ganin ya bud'e idon sa cikin kuka tace "Hamma Umar ka tashi ka shirya ka kaini asibiti a zubar da cikin nan dan ni bazan k'ara kwana d'aya da cikin nan a jiki nah ba", pillow ya d'auka ya rufe kansa gaba d'aya dan sosai yake jin baccin, ganin haka ran Ummul ya b'aci sosai taja pillow'n tana kuka tace "Hamma wallahi wulakanci bashida kyau ina maka magana harda wani janye pillow koh? Ni ka tashi ka shirya muje asibiti a yanzu ji nake bazan iya k'ara koh awa biyu neh da cikin nan ba", tasowa tayi daga kwancen da yake yace "Kinsan wulakanci bashi da kyau amma baki san kisan kai yafi shi muni ba, abunda kike k'okarin aikatawa ke kanki kinsan kisan kai neh, kin sani amma kin taka sani, kiji tsoron Allah Khairi idan baki so nah ai bai kamata ya shafe d'an cikin ki ba, na yarda na amince baki so nah baki k'auna ta amma dan Allah", ya durkusa har k'asa "Dan Allah kiso d'ana Khairi, ina son cikin nan, ina matuk'ar son cikin nan, ki taimaka min ki taimakawa rayuwa ta, ina bala'i da masifan son cikin nan", d'auke kanta tayi daga ganin sa tana hawaye tace "Kai dai kayi hak'uri Hamma Umar, ni kuma wallahi Allah bana k'aunar cikin nan, bana so na k'ara kwana da cikin nan a jiki nah, kayi min rai a cire cikin nan, ina alk'awarin daka d'auka wa iyayen mu akan zaka rik'e ni amana and you'll never deprive me of my rights yanzu ka tabbatar min da ka cika alk'awarin nan, a zubar da cikin nan"... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL, AMARI* Page 2⃣4⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *K*ai ya rink'a juyawa ida nunshi cike da k'ollah murya na rawa ya durk'usa gaban ta hannun shi yasa ya dafa guiwowin ta cikin rawan murya yace, "Bazan iyaba Ummul bazan iyaba ina son cikina bazan zubda gudan jinina da kaina ba bazan yi kisan kaiba". sai ya kuma mik'e yana yarfa hannunshi, ganin haka ta mik'e itama tana yarfa hannun ta tana kuka tana binshi a baya tare da cewa, "toh ni dai ka maidani gida, na gaji da zaman gidan nan ka maidani gun Nenne na". jin hakan yasa yayi ajiyan zuciya dan yasan indai ya maidata gida bata isa tace a zubda cikin ba dan tana jin tsoron su Adam hakan yasa cikin kauda kai yace, "shirya mu tafi". Hannu ta yarfa cikin dire k'afafunta tace, "ni a shirye nake mu tafi kawai". "toh". yace sannan ya shige d'akin shi, wonka yayi ranshi cike da takaici, yana fitowa ya sameta a bakin gadon shi, bai kulata ba ya zauna gaban dressing mirror mai ya fara shafawa yana murza fatar jikin shi, a d'aya gefen kuma Ummul ce ta mik'e cikin tura baki tazo bayan shi hannun shi ta rik'e cikin jin bacci da kasala ta manna kanta a bayan shi a hankali tace, "Hamma mu tafi bacci nake ji". juyowa yayi ya jawota jikin shi cikin sanyi ya ruggumeta tsam a jikin shi yana shak'ar k'amshin ta, hannun shi ya cusa cikin rigarta yana shafa cikinta zuwa kan kirjinta murya can k'asa cikin daburcewa yace, "Ummul kiyi hak'uri kiso d'anki kiso gudan jinina ki barni in rab'i jikin ki ina begenki ki bani hak'k'ina". shiru tayi ta lafe a jikinshi tana jin yadda yake murje kirjinta da shafa cikin ta, ido ta lumshe cikin sanyi da kasalar daya k'ara sakar mata ta ruggume k'ugunshi ta manna kanta da fatan cikin shi, a hankali tace, "Hamma Umar tashi mu tafi, banda lafiya zan koma gun Nenne na ni a cire cikin". ranshi a b'ace ya d'an tureta sannan ya shirya tsab fuskarsa a tsuke suka fito, rufe gidan yayi sannan suka shiga mota, Kai tsaye hanyar potaskum ya nufa da ita. A gida kuwa Aliyu ne dasu Nanne ke zaune a parlour , Aliyu dake zaune a 1 str hannun rik'e da wayar ya Sadik yana game a wayar, itako Nanne tana kishingid'e a kan doguwar kujera suna hira da Ya Sadiq dake zaune rik'e da remote yana kallon TV suna d'an hira kad'an -kad'an, Suna isa harabar gidan Hamma Umar na tsayawa Ummul ta bude motar cikin kasala da jin bacci ta shige cikin gidan, kai tsaye tai parlour Nanne Sallamar ta ce tasa Nanne tashi zaune tana murmushi ta bud'a mata hannu, Ummul cikin shagwab'a ta fad'a jikin Nanne tace, "Nanne na ina kwana?". lafiya lau Ummul na, ya Damaturun ?". Sallamar Hamma Umar ce ta katse su, cikin sakin fuska Nanne ta amsa mai tana mai sannu da zuwa, Cikin nitsuwa da cikar kamala ya shigo parlour kanshi a sunkuye zama yayi a k'asa gaban Nanne yace, "Nanne ina kwana ? ya gidan?". murmushi tayi cikin jin dad'in ganin su ta amsa da, "lafiya lau Farouk ya hanya, ya aiki?". Kai yasake sunkuyar wa k'asa yace "Alhamdullah". sannan Ya Sadiq da Aliyu daya matso jikin Hamman na shi cikin so da kauna suka gaida shi ya amsa musu cikin sakin fuska tare da cewa, "Ina Adam fa?". Sadiq ne ya dan kalleshi tare da cewa, "Yanzu ya tafi d'akin shi, barin kira shi". Kai ya jinjiga yace, "kyale shi zamu wuni ai". Ummul dake kwance kan cinyar Nanne kuwa tuni tafara bacci cikin kasalar da take tare da ita, sukuwa hira suka ci gaba dayi. Can jimawa kad'an Hamma Umar ya mik'e tare da cewa, " Nanne bari inje mu gaisa da Hajjajo". Cikin zumud'i Aliyu yace, "Ko kaje ma yanzu tana sallar walaha, kasanta kamar tubabbiya, nima koroni tai". Dariya suka d'anyi duk kansu ban da Nanne da ta ran kwashi kan Aliyu tace, "tadai fika da surutun ka mara amfani ai ita hanyar tsira ta kama kaifa maiyin game ". Jin hakan yasa Hamma Umar d'in ya sake zamewa ya zauna k'asa tare da tok'oshe k'afafun shi sannan yayi k'asa da kai, a hankali ya furta, "Abba basu dawo ba? Munyi waya jiya yace suna maiduguri". Nanne dake shafa bayan Ummul ne tace, "Bai dawo ba, muna dai sa ran sai gobe insha Allah". Addu ar dawowa lafiya yayi masa, sannan suka amsa da, "Amin". Itako Ummul ta bud'e lumseshshun idonun ta da kyar tai mik'a a hankali ta kuma lafewa jikin Nennen tata ture ta Nannen tayi tare da cewa, "to d'aga min cinya in duba mai sunan ki ko ta idar sai kuje ku gaisa". Tana mikewa Ya Sadiq ya bi bayan ta yana cewa Aliyu, "Tashi muje mu k'arasa gugar Hajjajo". Fitarsu ne ya bawa Ummul damar tasowa ta matso gaban Hamma Umar d'in cikin kasala da mayen bacci ta durkusa ta had'a hannu wanta biyu guri guda tace, "Hamma narok'e ka dan Allah kayi hakuri ka rabani da cikin nan wallahi banaso cikin nan bana son haihuwa da kai". Idon shi ya rumtse da karfi tare da furza numfashi mai nauyi jiki a mace ya sa hannun sa ya lank'ayo kugunta ta fad'o jikin shi ya sa hannun shi ya Kara matsota sosai har numfashin su na had'ewa ya d'ago idanun shi ya tsura mata su cika sanyi ya sauke numfashi tare da lumshe ido ya kamo lips inshi yana tsotsa murya can k'asa yace, " Ummul khairina kiyi hakuri kibar mana d'anmu ya rayu a cikin ki kibarshi yaji d'umin cikin mahaifiyar shi". sake narkewa tai a jikin shi tasa hannu ta tallafo fuskar shi tace, "Haba Hamma dan Allah kaji tausayina mana nifa kasani bana sonka, ka zubda cikin nan dan Allah". Kanshi ya cusa cikin kirjinta yana goga fuskarsa akan dukiyar fulanin ta yana wani irin numfashi mai d'auke da tsan tsar k'una da rad'ad'i ga kuma sha'awar dake cin jinkishi da zuciyarshi murya na rawa yace, "Naji amman indai kina son a zubda cikin nan to ki fad'ama Adam da Abba idan sun amince shike nan sai a zubar ". Cikin tarin takaici Adam dake kokarin shigowa parlour yayi sallama tare da shigosa yana jin wani irin bak'in ciki da takaici ji yake kamar ya abka kan Ummul din har sai ya sumar da ita tunda ita bata gane nasiha tafi gane bugu, Itako Ummul tana jin muryar Adam d'in take yuk'ura tabar jikin Hamma Umar wanda ke zaune jiki a kasalance , Itako Ummul ganin yanda jikin Adam yai sanyi ga gumi na tsatstsafowa daga duka jikin shi yasa suka tabbatar da yaji zancen da sukeyi dan haka Ummul ta rink'a jan baya-baya Vikings tsoro tana kallon idanun shi yadda yake watsa mata harara gaba d'aya jikinta sai kerma yakeyi da sauri tajuya tayi cikin tsoro ta shige bedroom d'in Nanne ta turo kofa ta rufe ta haye gado tana tunanin yadda zasuyi da ya Adam, Shi kuwa Hamma Umar mik'ewa yayi cikin kasala da rauni yaje gaban Adam d'in hannu yasa ya dafa kafad'ar Adam yace, "kar inji wannan a bakin kowa". Cikin mamaki Adam ya zuba mishi ido tare da gyed'a kai dan abin ya d'aure masa kai, Shiko Hamma "good". Kawai yace ya fice yabar shi baki bud'e yana mamakin yanda Hamman nasu yazama, kai tsaye b'angaren Hajjajo yayi, yasame su dukkan su, cikin ladabi ya gaida Hajjajo, ita ko tana tsokanar shi yana murmushi yace, "Nanne bari inje gun Ammi". Itama fuska a sake ta amsa da, "ka gaidata, kace zan biyo muje gaisuwar". "toh". yace sannan ya fice ya tafi haka ya fita ya kama hanyar gidan su Ammin shi, Adam kuwa yana ganin Hamman nasu ya fita, yazo ya tsaya kofar dakin Nanne yana ta fada da alwashin koyama Ummul hankali yana, "wallahi ki bud'e k'ofarnan in kuwa kikak'i zan balla k'ofar na kuma shigo na tattakaki tunda baki da mutunci". tana jinshi sai rawan jiki take da tsoro tana k'ara b'uya a cikin blanket tana, Dan Allah kayi hak'uri ya Adam". a harzuk'e ya koma kan kujera ya zauna. a gidan su Ammi Kuwa yana isa yai paking a k'ark'ashin bishiyar kofar gidan ya fito yashige cikin gidan, da Inna yafara had'uwa tafito daga kichin tana ganin shi tayi murmushi cikin jin dad'i da k'aunar jikan nata tace, "kaga Ummaru faruq, mai tagwayen suna, kaga d'an Ammin shi da Nanne yayan shehu Usmanu, angon Rabi'atul Adawiyya likita bokan turai". Duk kirarin da Inna keyi ya na tsaye ya na kallon ta yana shafa sajenshi ganin ba zatayi shuru bane ya katseta da cewa, "To ya isa haka zo muje inbaki tukuici dan kinyi aikin maroka". hannun ta ya kama suka shiga cikin parlour inda Ammi ke zaune tana ninke y'an kayayyakin data data woke, sai murmushi takeyi tana jin dad'i da shauk'i da k'aunar d'an nata dariya ta d'anyi dan jiyo kirarin da Inna kewa d'an nata, suna shiga yasamu ya zauna a gaban ta ya cire hular shi kamar ko yaushe in yana gaban Ammin nashi , ya kwantar da murya yace, "Ammi na ina kwana?". hannunta takai ta shafa kanshi tace, "lafiya lau, ya aikin, ina Ummul dina?". K'ara matsawa jikin ta yayi yace, "lafiya lau Ammi na tare muka zo da ita bacci tai kafin in fito shiyasa bamuzo tare ba". sai kuma yasa hannu ya karb'i zanin hannun ta yaci gaba da ninkewa, Ido Ammin ta zubawa d'an nata tanajin kaunar shi na ratsata tace , "Umar inajin dad'in yanda kake tafi da rayuwar auren ka da k'anwarka amanar ka". Ajiyar zuciya ya sauke ya lumshe ido yana jin dad'in yadda Ammin nashi ke Al'fahari dashi da kuma yadda take gamsuwa da rik'on amanar daya d'auka, murya can k'asa yace "koyarwarki ce Ammi ina alfahari dake ko yaushe". Tattare kaya yayi yaje ya jere kowanne a mazauninshi sannan ya fito yad'akko abin yankan farce ya dawo ya russuna gaban Ammin sa, itako hannu ta mik'a mai yafara aikin shi na yankemata farce Kamar yadda ya saba dai-dai sanda ya gama yankan ffarcen Ammin nashi akayi kiran sallah dan haka yai alwala yawuce masallaci dan gabatar da sallah azhar, bayan an idar da sallan ne ya koma cikin gida gaban Ammin nashi ya zauna tare da zaro woyarshi yace, "Ammi bari in kira autanki ayi hira dashi". "toh". tace tare da yin murmushi. A b'angaren Ummul kuwa tun tana zaune har ta kwanta bacci b'arawo ya saceta shiko ya Adam da ya Sadiq daya shigo bayan fitan Hamma suna nan zaune a palour Nanne suna jiran fitowarta, baccin da tayi ne yasa bataji tafiyar su masallaci ba bare taking dawowarsu , Anan sukaci abinci cewarsu ko shekara zatai a d'akin suma zasu shekara a gurin. Ya Usman Kuwa mutan india, yana zaune a k'asan capet ya kifa kan shi a kujera hannu shi dafe da kirjinshi yana wani irin kuka mai cin rai da k'ona zuciya kamar yadda kukan ya zame mai sabo duk da ga tarin magungunan da ko ya shasu baya jin sauk'in zogin da zuciyarsa keyi kullum son Ummul da k'aunarta K'aruwa suke a zuciyarshi, kukan yakeyi kamar yadda ya saba har numfashin sa na fizga, Kid'an da wayar shi keyi ne yasa ya dago rinannanun idanun shi yakai hannu ya janyota daga kan table d'in dake tsakiyar palour, har kiran ya yanke yanata kallon ta yana k'ok'arin saita kan shi gudun kada yad'au kiran yayi abinda B'iyayen nashi zai gane yana cikin damuwa, Shiko Hamma Umar dake zaune gaban Ammi yace, "barin in sake kira". Bugu d'aya Usman ya amsa da, "Amincin Allah da rahamar sa gareka d'an uwana jinina". ba Hamma Umar ba hatta Ammi da tasawa wayar ido saida ta lumshe ido dan jin dad'in kalmar autan nata, aiko ita ta amsamai da, "Amincin Allah ya tabbata gareku y'a y'an albarka". wannan kalmarce ta tabba tarwa Usman da Hamman shi na tare da Ammin su, sai da ya k'ara dai daita kanshi sannan yace, "Ammina, Hammana, da y'ar tsohuwa Inna ina wunin ku?". Kafin su amsa kuwa ya sake katse su da cewa, "ina nan lafiya lau, dan nasan yanzu Hamma na zaita bincike ni da tuhuman ina shan magani". dukkansu sun manta da amsa gaisuwar tasa suka fashe da dariya sannan Inna tace, "wato dai angona kana nan da halinka na ban dariya ko?". sai da yayi gyaran murya sannan yace, "waye angon ki? kinga barni karki cikani da surutu gwara nayi magana da Ammina dan nayi missing voice d'in ta". Ammin ce ta katse shi tace, "Meyasa bazaka dawo ba in dai hakane, muna buk'atarka a kusa damu". Sai da ya sauk'e ajiyar zuciya sannan ya furta, "Afwan ya Ammi na ki tanadi abun dad'i dan nan da sati biyu zan taho". bai gama rufe bakin shiba Hamma Umar ya d'an juyo ya kalli wayar cikin nutsuwa da murmushi d'auke a fuskar shi ya ce, "Ajiye wasa B'iyayena, da gaske hakan zaka dawo?". Murmushi mai sauti yayi yace, "Insha Allah". Shima murmushin yayi cikin tsananin farin ciki da k'aunar d'an uwan nashi yace, " Alhamdullahi Usman yau naji dadin jin zaka dawo, Allah ya dawomin da kai lafiya nayi kewarka matuka". Da haka sukaita hira cikin so da k'aunar juna har lokacin sallah la asar sannan sukai sallama kowa yatashi dan gabatar da sallah shiko Hamma daga masallacin gida ya nufo dan ya sallami su Ammi shi. Yunwa ce ta tashi Ummul da rawar jiki da kyar ta mik'e ,a daddafe tai sallah la asar sannan ta zira kunnenta a bakin kofa, shirun dataji ya bata damar bud'e kofar ta leko kanta bakowa babu motsin kowa a palour dan haka da fito kai tsaye tai kicin, abinci ta zubo ta dakko ta fito kenan sukai arba da ya Adam jiki na rawa tai k'asa ta ajiye plate d'in ta durkusa jiki na kerma tace, "Ya Adam". Damgota da yayi ne yasata sakin wata irin gigitacci yar k'ara tana, "kayi hak'uri yaya, nadena, bazan sakeba". Aiko saukar marukan da taji yasa ta k'walla k'arar data janyo hankulan mutanen gidan ciki harda Hamma Umar wanda fitar shi daga mota kenan, da Nanne dake b'angaren Abba tana d'an gyare-gyare, da Hajjajo wadda suke zaune palour ita da Ya Sadiq da Aliyu da gudu sukayo b'angaren Nanne Hamma Umar ne a gaba, shigowar shi tai dai dai da marin da Ya Adam ya k'ara mata, a fusace ya janye Ummul bayanshi cikin fushi ya d'ago hannunshi tas, ya kifawa Adam mari , hakan yasa kowa k'amewa a inda yake sannan kowa da irin tunanin shi, Hamma Umar d'inne ya katse shiru cikin tsananin takaici yace, "metayi maka?". Kanshi a kasa yana rik'e da kumatun daya sha marin yace, "Hamma inaso inmata fad'ane akan maganar d'azu". Hannu Hamma Umar d'in ya d'aga ya dakatar dashi da cewa, "waya saka? na kawoma k'ararta ne?". Ya Sadiq ne ya matso kusada Hamma Umar d'in yace, "Hamma". Dakatar dashi yai yace, "ya isheni, kuban waje". fita su kayi dukkan su sukabi bayan Nanne da Hajjajo wanda tunda Hamma Umar ya mari Ya Adam d'in suka fita suka barsu, batare daya juyaba yasa hannu ya dawo da Ummul dake manne a bayan shi tunda ya karb'eta daga hannu Ya Adam ya ruggume ta tsam kamar za a kwacemai ita yana shafa bayanta ya sun kuyo da kanshi kan wuyan ta yana hura mata iska a kunne ta, dad'a narkewa a jikinshi tayi tana shashshekar kuka k'ara matseta yayi yace, "shiittt, ya isato, kinyi sallah ne?". da kai tabashi amsa, a hankali ya rabata da jikin shi yace, "muje mutafi gida". Maida kanta tayi kan kirjinshi tace, "Hamma yunwa nakeji". Matsawa yayi ya zaunar da ita akan kujera ya juya, kicin d'in ya shiga jim kadan yafito da plate d'in abinci da kofin shayi, zama yayi a kusa da ita ya ajiye plate d'in abincin a hannun kujerar ya rungumota ta kwanto jikin shi ya kafamata kofi shayin a bakinta aiko nan da nan ta shanye ya kuma mika mata abincin ta ta fara ci, sannan yajuya ya nufi b'angaren Hajjajo, Sallama yai ya shiga a gaban Nanne yazauna ya sunku yar dakai k'asa yace, "Nanne kiyi hakuri, bata da lafiya ne, shiya sa nakasa hakuri da hukuncin da Adam yayi mata, kuma ba wata babbar matsala bace shiyasa nace yabar maganar duka". yana maganane kanshi a kasa, itako Nanne fuska a sake tace, "bakomai babana, wannan ai tsakanin ka da k'annenka ne". Ajiyar zuciya ya sauk'e sannan yace, "zamu koma kar dare yayi". murmushi Nennen tayi sannan tace, "to barin d'akkoma man shanun ka". Hajjajo ce ta mik'e ta d'akko fura da kindirmon nono tace mai, "gashi in kunje shagwab'abbiyar matar taka ta dama muku". Kanshi a k'asa yace, "nagode". ya Sadiq ne ya karb'a yayi gaba Adam ma tasowa yayi Hamma Umar ya dafa kafad'ar shi cikin k'aunar juna suka nufi inda motar take, anan suka sami Nanne da Ummul tsaye dagani magana sukayi. Cikin k'aunar juna sukai sallama suka kama hanyar Damaturu. Tun a hanya Ummul keta marairaicewa tana kuka dan ta jibgu a hannun Adam, janyota yayi da hannu d'aya ya mannata a jikinshi lokaci-lokaci yana lek'a idonta yana murza tafin hannun shi kan fatar cikin ta yana lumshe ido, Kai tsaye gida ya wuce dan gaba d'aya Ummul na neman zautar dashi da yanda taketa shige masa jiki. suna isa yayi paking sannan ya fito ya zagayo inda taken hannu yasa ya kamo nata hannun d'agata yayi a hankali ya jingi nata jikin kujerar da take zaune ya kamo hannunta a hankali ya fito da ita ya sake bud'e k'ofar bayan ya dauko jarkar nono da ledar fura yarufe kofar ya juyo yace, " mujeto". baki ta tsuke cikin kuka ta noke hannu batare datace Komai ba, rusunowa ya d'anyi yana kallon fuskarta yace, "menene kuma? ai nace kiyi hakuri". Kai kawai ta d'agamai shiko ya aje kayan hannun nashi sannan ya matsota ita kuwa tana yarfa hannu fuska cike da k'ollah jawota jikin shi yayi ya ruggumeta yana maida numfashi. Ƙyana rungume da ita yasa daya hannun yad'au kayan ya jata sukai cikin gida, Kai tsaye d'akin ta ya wuce ya zaunar da ita bakin gado shima ya zauna yai kasa da murya yace, "kinga kiyi hakuri kiyi wanka kiyi sallah sai muyi magana". fuska ta sake raunatawa tace, "gun da ya Adam ya mareni kemin zafi". hannu yasa yana shafa gun yana hura iskar bakin shi agun itama tana k'ara manna hannun nashi a gurin tana dad'a shigemai, duk ta rud'ashi ta gigitashi bakin shi na rawa yafara magana cikin susucewa da wani irin Shauk'i da wani irin salo yace, *"Ummul ina sonki* so mai tsanani, bantab'a son maceba saike, wallahi Ummul da sonki nake rayuwa nasoki tun bakisan kanki ba, a jinina sonki yake wallahi duk abinda nake miki bantab'ayi da wata manufa ba face so da kulawa kiyi hakuri da duk b'atamiki danai *ina sonki* dashi na rayu". Yakare maganar da had'e bakinau guri d'aya yana ma harshenta tsotsa mai ratsa zuciya, gaba d'aya ya gigice ya zauce a kanta cikin rawan jiki da murya yasa hannu biyu ya tallabo habarta tare da k'ara manna lips enshi kan n...... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL, AMARI* Page 2⃣5⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Wannan shafi naki ne Anty Fauzah Allah bar zumunci da k'auna* *K*issing enta ya rink'ayi cikin wani irin salo mai ratsa zuciya gaba d'aya ya hargitse sai numfashi yake fesarwa a gaggauce cikin kula ya kontar da ita fuskarshi ya saita da nata hancinsu na gogar juna yayin da ya cusa hannun shi yana shafa cikin ta da k'irjin ta ido ya lumshe tare da laso jajayen lips enshi da suke shek'i cikin rad'a da tsantsar so yace, " Ummul ina sonki tun randa aka haifeki nasoki fiye da zaton zuciya ta, Khairi ki yarda dani kece farin cikina ki cire zargi ko zaton bana sonki ki sani kece farin cikina zan rayu da sonki a zuciyata har gaban Abadan Khairi ki jik'aina nima ki soni ki yarda dani a matsayin mijinki uban y'ay,anki". sai kuma yayi shiru yana kallon fuskarta yadda ta lushe ido hawaye na bin habarta, ita kuwa Ummul lumshe idon tayi tana kallon fuskar Hamman nata ta tsakanin gashin idanun ta, tana jin yadda ya kife tattausan tafin hannun shi kan k'irjinta yana mata salon so mai wuyar mancewa, a hankali ta k'arisa bud'e idanun nata jin wani damshi na d'iga kan wuyanta, cikin raunin zuciya ta Kalli fuskar Hamman nata dake zubda k'ollah, wani irin yanayi taji a ranta ganin yadda Hamma Umar keyi mata yana yin so, shi kuwa zuge zip d'in rigarta yayi cikin rauni da sanyi ya cusa kanshi a k'irjin ta a hankali ya rink'a murza kan nashi kan k'irjinta yana wani irin numfashi gaba d'aya jikin shi rawa yake yi ba abin da yake iya furtawa sai, "Khairi ina sonki so mai tarin yawa kece burin raina, Anti tamamu sururi, kece cikon farin cikina". sai kuma ya kuma kife kanshi kan k'irjin ta, gaba d'aya ya rikita Ummul ta kasa furtamai kalmar, "bana sonka". da take son fad'an sai cusa hannun ta tayi cikin sumar kanshi tana damk'e sumar tana dan yin mik'a, kiran sallan magrib da akayi ne ya dawo da Hamma Umar d'in hankalin shi, a hankali ya dago kanshi cikin sanyi ya tsura mata ido tare da cewa, "Uhibbuki fillah, ina sonki sabida Allah, ba dan wata manufa ko surar jikin kiba". sai ya kuma ruggumeta tare da cewa, "Kuma wallahi tallahi, As'attu li wajattu zawajiki, nayi farin ciki da samun auren ki, har Abadan bazanyi nadama ba, domin, kunti ba'adu jasadi, kin kasance wani sashi na jikina, har kullum ina cikin farin ciki tunda, kunti lagamee, kin zamo tawa". sai ya kuma shafa fuskarta sannan ya juya cikin sanyi ya nufi hanyar fita, har yaje bakin k'ofar sai kuma ya tsaya jin Ummul na cewa, "Toh ai ni bana sonka Hamma Umar bana k'aunar zama da kai na tsaneka tunda ka rabani da Mustapha". juyowa yayi cikin zafi da kishi murya na rawa yace, "Wat...! wata...! wata rana zaki soni Ummul na tabbatar wata rana zaki kasance mai tsananin sona khairi sai dai ban sani ba ko son zai amfanemu, amman tabbas zaki so Hamma Umar d'inki fiye da kowa a duniya". sai kuma yayi murmushi mai zafi ya fita ya nufi masallaci, ita kuwa kife kai tayi tana kuka tana dukan cikin ta daya fara girma tana, "bana sonka Hamma Umar bana son cikin nan ni bazan haihu da kaiba na tsaneka na tsani cikin naka". haka tai ta kuka har muryarta ta disashe, cikin kukan tayi wonka tazo tayi sallah bata tashi a wurin ba har saida akayi Ishah, sannan ta fito parlour ta zauna a k'asa kan carpet tana kallon TV tashan Bollywood, shi kuwa Hamma bayan an idar da sallan ishah d'in ne ya dawo gida, a parlour ya sameta sai ya kauda kai ya wuce bedroom enshi konciya yayi ranshi cike da tunani kala-kala, ita kuwa tana ganin ya wuce ta mik'e ta biyo bayanshi tana zubda k'ollah dan yunwar da takeji har jiri na d'ibarta, tana shigowa ta zauna gefenshi cikin tura baki tace, "yunwa nake ji jiri nake ji duhu nake gani ni zanci abinci". kallon ta yayi cikin nitsuwa yace, "plxx karkiyi kuka bari in kawo miki". Kai ta gyad'a tare da cewa, "toh Hamma in nayi shiru naci abincin zaka zubarmin da cikin ko?". Kai ya juya tare da cewa, "ehh zamuyi shawara". A haka ya kawo mata abincin da Nenne ta had'o musu ya zauna sukaci suka sha sannan ya taratara wurin, ita dai binshi da ido kawai takeyi, she kuwa wonka yayi sannan ya fito ya murza jikin shi da mai da turaruka, sannan ya had'o mata tea ya kawo mata, ba musu ta karb'a ta ajiye a gefenta sai kuma ta juya suna fuskantar juna cikin zak'uwa tace, "toh a cire cikin". murmushi yayi cikin hikima da tunanin dabararsa zatayi mishi aiki dan ya gama sanin Khairin akwai wauta, ita kuwa ganin yayi murmushine ta rink'a yarfa hannu da tutture k'afafu dan tanaga yama maida ta mahaukaciya Keenan, da sauri ya jawota jikin shi cikin hikima ya tura hannun shi cikin rigarta ya d'an murza cikin a hankali ya d'ago fuskarta cikin rad'a yace, "kina son in cire cikina ko? ". da sauri tace, "eeh a cire yana damuna ". ajiyan zuciya ya sauk'e cikin hikima da wayo da dabaru irin nasu na doctors yace, "ki dena kuka zan cire d'ana tunda bakya sonshi amman fa ba yan zuba dan in nace zan cireshi yanzu zaki iya mutuwa, kuma yarinyar ma zata iya mutuwa, kinga su Abba da Daddy zasu gane kuma Allah zaiyi fushi damu dan munyi kisan kai". da sauri ta kalleshi tare da cewa, "toh Hamma sai yaushe za, a cire cikin? ". murmushin jin dad'i yayi ganin hikimarsa tayi aiki a sauk'ak'e ruggumeta ya k'arayi cikin sauk'e ajiyan zuciya yace, "sai cikin yayi wata 7 sai in cireshi sai nasa d'ana a cikin kolba daga nan inci gaba da renon abina kekuma kinga shike nan kin huta, sai incewa su Abba bakwaini kika haihu". ido ta tsura mai cikin nazartar maganarsa, shiko sai shafa cikin yake yana lumshe ido, a hankali ya bud'e idon nashi jin tana cewa, "ni dai a a wallahi har wata bakwai gaskiya bazan iya ba". kallonta yayi cikin sanyi yace, "ai kamar yaune kinga fa yanzu cikin ya shiga wata na 4 kinga kenan wata 3 kawai zaki k'ara". da sauri tace, " a a ni a canza dabara". Ajiyan zuciya yayi cikin jin dad'i yace, " yauwa toh dabara ta biyun tafi sauk'i sai dai nasani bazaki yarda ba". da sauri tace , "fad'amin inji zan yarda". murmushi yayi sannan yace, "in kina son cikin ya zube da wuri sai kin yarda dani na rink'a yin pakala dake kullum safe da rana da yamma kuma ki rink'a taimaka min muyi sosai hakan zaisa bakin mahaifarki ta bud'e daga nan baby zata fad'o sai incewa Abba zuban gaskene kuma Adam bazai dakeki ba". cikin rashin fahimta tace, "Hamma mene kuma pakala da zamu rink'ayi safe da yamma da dere da rana?". k'ara matsota yayi cikin kauda Kai ya lumshe ido tare da cusa hannun shi kan mararta yana d'an shafawa yace, "Hmmmm baki san pakala ba?". "ehh ban saniba". zip d'in ta ya zuge cikin kasala yace, "Saduwa ne Pakala ki yarda in rink'a kusantar ki kullum a k'alla sau 3 ki kuma taimaka min muyi komai tare, in kin yarda dai ba mamaki cikin ya zube kafin wata 7 d'in". baki ta tura tace, Kai dai ka fiye jaraba kuma ka sani ni bana sonka". Kafad'unshi ya d'aga tare da cewa, "Toh kin huta sai ki jira wata bakwai d'in in baki yarda ba". Shiru tayi tana tunani shiko kan gado ya koma ya lumshe ido kamar maiyin bacci, ta dad'e a zaune tana nazari, sannan can ta mik'e a hankali ta koma kan gadon cikin sanyi ta zauna gefenshi murya can k'asa tace, "Na yarda Hamma". kauda kai yayi, yayi ta murmushi sannan yasa hannu ya jawota jikin shi, kayan jikin ta ya zare mata sannan ya zare nashi blanket ya jawo ya rufesu a hankali yasa hannun shi yana murza al'barkatun jikin ta, shiru tayi cikin lumshe ido, ganin bata taimaka maine yace, "ko dai bakya so ne in barki da cikin ki?". cikin kasala tace, "inaso mana ". murmushi yayi sannan yace, " toh ki tayani muyi tare duk abinda nayi miki kiyi min inba hakaba in fasa taimakon ". ba musu ta fara maida mishi martani, gaba d'aya sun gigice Sun shiga duniyar ma aurata ita kanta Ummul salon Hamman nata na yau ya wuce zaton ta, shiko Hamma Umar ya samu gamsuwa iya gamsuwa da y'ar k'anwarshi sai al'abarka yake samata. Haka suka kwana mak'ale da juna, koda gari ya waye yana dawowa masallaci kai tsaye d'akin Ummul d'in ya wuce ya kwashi garar kafi shayi dad'i, haka rayuwa tayi ta juyawa tana tafiya gaba d'aya yanzu Hamma umar ya jarabe ya yaraba Ummul d'inshi wasu lokutan har yana jin tsoron kar dai cikin ya zube dan shida kanshi yasan jarabarsa tayi yawa, cikin ko yana nan daram sai k'ara k'awari da lafiya da wintsil-wintsil da yake yawan yi, Ummul ko har kwanan gobe bata tabajin son Hamma Umar d'in ba haka kuma bata tab'ayin wani abu dan ta faranta mai raina. A gida kuwa randa Hamma Umar ya mari Adam suna tafiya, Adam ya koma parlour Nenne cikin takaici da jin haushin k'anwar tashi ya shafa kumatun shi ya kalli Sadik dake gefen shi rai a b'ace yace, "Ni Hamma Umar ya mara a kan na daki Ummul dan tayi mishi laifi". dogon tsaki Sadik yaja cikin ta kainci yace, "wallahi tallahi da a bare Hamma Umar ya auro Ummul wallah sai ince ta asirce mana d'an Uwanmu Kalli fa yadda ta maida Hamma kamar bawanta inajin bak'incin yarinyar nan wallahi duk randa na kamata sai na b'allata". ya k'arishe maganar yana nuna yadda zai b'allatan, Tsaki Adam ya ja cikin ta kaici yace, "Duk ta meda Hamma Umar shanyeyye soko ya zama tamkar sakarai". Aliyu ne ya dan yi k'asa da kanshi yace, "Ni ina jin tausayin Hamma, Ummul na wahal dashi". Ajiyan zuciya Nenne ta sauk'e cikin kallon yaran nata a hankali tace, "Ba Ummul ke wahal da Farouq ba soyayyar Ummul ce ke wahal dashi". cikin mamaki Adam yace, "Son Ummul Kuma Nenne Hamma Umar yana son Ummul ne ai ba sonta yake ba had'asu fa akayi ko kin manta ni dai inaga girman al'k'awarin daya d'aukane ke wahal dashi ko?". Kai Nenne ta kuma juyawa cikin sanyi tace, "Farouq yana son Ummul Adam baku gane hakan bane kuma sonda Umar keyiwa Ummul na asaline tun randa aka aifi Ummul". sai kuma tayi ajiyan zuciya taci gaba da cewa, "Tun randa aka haifi Ummul, Umar ya bata matsayi mai girma a rayuwar shi, bayan na haifi Ummul Umar shine mutun na forko daya d'aga Ummul yana d'agata ya ruggumeta cikin tsananin farin ciki sai kuma ya kalleni yace, "Nenne da d'a namiji kika haifa da anmin takwara Nenne yarin yar nan dana mijine da na samu magaji, amman yanzu ma bai b'aciba Insha Allah zata haifomin takwarana kuma Yerimana". inajin abinda Umar ya fad'a sai nayi dariya nace ai itama takace, haka daga wannan ramar Umar ke d'awainiya da Ummul renonta kab shi yakeyi a kwana a tashi har ta fara girma so shiko a lokacin an kaishi karatu India bayan ya gama ya dawo kuma, sai ya zama basa shiri da Ummul sabida shi mutunne mai nitsuwa ita ko Ummul tana da kaud'i da tsiwa ga yawan fad'an da takeyi da Aliyu tana cin zalinshi shiko Umar baya son zalumci da sowa kuma ya zama shine matsayin mahaifinku in Abban ku baya nan shiyasa yake bada kulawarshi akan Ummul sosai yayinda ita ko ta d'auki hakan a mizanin k'iyeyya,". kai suka jinjina su duka ita kuma taci gaba da cewa, "Kuma duk da haka dole ku d'auki mataki kan halin Ummul dan a samu ta gyaru, amman fa karkuyi a gaban Umar". toh a haka fa daga ranar suke cike da takai cin Ummul d'in a rayu kansu, kwanaki sun ja makonni sun ja watanni sun ja ya Usman kuwa kullum sai yasa ranar dawowa sai ya d'aga a haka har cikin Ummul ya cika wata 7 , yayin da a gefen Umar kuwa kullum cikin tashin hankali yake da matsamai da Ummul take akan a cire cikin ya samu dai yanzu ya lallab'a ta a kan sai cikin ya cika wata 7 da kwana 7... Yau Monday tun sassafe Hamma Umar ya shiryo da Ummul enshi suka nufo gida dan Ya Usman yau zai dawo a cewarsa yau kam bazai d'aga dawowar ba dan jin kewar Umar yakeji tamkar sun shekara 10 basu had'uba, Abin mamaki suna isa gida a harabar gidan Hamma Umar ya haggo Usman d'in ya nufo gunsu cikin sauri yana murmushi mai cike da farin ciki, Hamma Umar kuwa da Ummul har rigerigen fitowa sukeyi, a motar suna fita Ummul ta ruga a guje cikin ihun farin ciki da sowa da rakad'i tana, "Oyoyo ya Usman na ya dawo Hamma Umar Kalli ya Usman nawa ya dawo". shi ko Umar zuciyar shice ta rink'a bugawa da k'arfi yana kallon yadda Usman ya rame sai farin daya k'ara shiko, Usman ganin Ummul da yayi da k'aton ciki a take jikin shi ya Kama rawa cikin tsananin firgici da tsinkewar zuciya gaba d'aya gabban jikin shi suka rink'a rawa zuciyarshi na harbawa da karfi, dafe k'ahon zuciyarshi yayi a da-idai lokacin da Ummul ta fad'a jikin shi dai-dai lokacin kuma Hamma Umar ya k'araso garesu bud'e hannayen shi yayi ya had'asu gaba d'aya ya ruggume su, Lokaci d'aya yaji wani irin karaya a zuciyarshi abin mamaki saiga Hamma Umar yana kuka cur-cur ruggume da k'aninshi da matarshi kuka sosai yakeyi yana shinshina wuyan Usman , kukan Hamma Umar d'in ne ya k'ara tono dafin zuciyar ya Usman d'in cikin wani irin yana yi yace, "Hamma kuka Kuma? ". sai kuma tari ya sark'a fe mishi tarin yakeyi da k'arfi yana numfashi sama-sama, a gigice Hamman ya tallabo d'an uwan nashi dai-dai lokacin usman yayi wani irin yunk'uri da kakari sai ga.... *by* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL, AMARI* Page 2⃣6⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *INA KUNE MATAN group d'in TABITAL FULAKU tare da AYSHA ALI GARKUWA FANS da kuma GARKUWAR FULANI Group tare da GARKUWA AYSHA&UMMEE ina Al'afahari daku ina sonku har raina ko a cikin groups na ku din nan da banne a gareni Fatan Allah ya k'addara saduwarmu a jannatul firdausi🤝😍😘* *S*aiga tari ya k'ara turnu k'eshi tarin ya keyi sosai har ida nunshi na firfitowa woje gaba d'aya jijiyoyin kanshi dana hannun shi suka taso rud'u-rud'u, sai k'ara ruggume Hamma Umar d'in nashi yake yana wani irin murmushin k'arfin hali, ita ko Ummul gaba d'aya jikinta rawa yake ta rik'o hannun ya Usman d'in tana zaro ido murya a hargize tace, "Wayyo Allah na Hamma Umar kalli ya Usman". sai ta kuma fara kuka itama tana, "ya Usman har yanzu kana wannan tarin da aman jinin ko shin doctors basu duba lafiyar ka bane?". kai ya rink'a juyawa jikin cushewar numfashi da zufa dake tsatstsafo mishi duk ta inda hutar gashin jikin sa yake, hannun na rawa ya tallab'o hab'ar Hamma Umar da hawaye ke zuba tamkar an bud'e pompo idanun shi kamar zasu fad'o k'asa yana kuka harda sheshshek'a, ido ya kuma tsurawa Hamma Umar d'in nashi cikin dauriya Ya rink'a juya mishi kai cikin tarin yace, "A zatona zuciyar Hamma Umar na tana da k'arfin da zata iya jure mutuwata ma bare dan tarina, amman kach sai gashi ina rayema kana min kuka, ashe in namutu gatan da zakayi min kenan Hamma na? ashe bazaka iya cin jarrabawar da Allah zai maka ba, Hamma Umar ka dai sani dole watara zan mutu ko". Kai ya rink'a juyawa cikin kuka yana k'ara ruggume shi yana cewa, "Usman bani da kamarka kullum cikin fargaba nake nima da kaina bansan ya rayuwata zata kasance min ba inba kai, Usman bazanyi maka gatan kukaba bazan zubdama hawaye ba zan zamema mai gatan yima sutura da addu'a Usman inajin tsoron jinin da kake amayarwa". cikin sauk'e ajiyan zuciya dan tarin ya dan lafa sai ya kuma yi murmushi ya kalli Ummul ya kuma nuna k'aton cikin ta sai ya Kuma kalli Hamman nashi cikin salonshi na abin dariya ya d'an ture su yaja baya kad'an sannan yayi gyaran murya ya gyara zaman hulanshi ya dan bud'a kafad'a cikin salon girma yace, "Na zama Baba yanzu na wuce yarinta a dena jimin tsoron mutuwa ko namutu ga magaji na". sai ya kuma sunkuyowa saitin cikin yace, "Ni Baba zaka kirani". cikin jin dad'i Hamma Umar ya kalleshi tare da cewa, "ai dama kaine baban shi na bar makashi ni dai mahaifinshi ne kawai amman kaine babanshi". murmushi yayi cikin farin ciki sannan ya kalli Ummul da ta tura baki tana hararan cikin a hankali yace, "Allah ya d'aiyiba min Baby maman Baby". cikin zubda k'ollah tayi murmushi tare da kallonshi tace, "ya Usman ina sonka yayana". dariya yayi sannan yaja hannun Hamman nashi suka nufi cikin gaida, yana cewa, "Allah ya d'aiyiba". Kai tsaye parlour Abba suka nufa inda gaba d'aya gidan suke zaune a parlour sunata hira, suna shiga su duka uku suka zauna gaban Abba da Daddy cikin Happy Abba ya kallesu tare da amsa gaisuwar su, sannan ya kalli Hamma Umar yace, "Farouq ya gidan naka ba wata matsala ko?". kai ya gyad'a a hankali yace, "Abba matsalar dai cikin yayiwa Ummul nauyi". ya Adam ne ya watsawa Ummul d'in harara tare da cewa, "Toh ai haka kowa ke haifar yaranshi har in ba, ayi daceba yar ta nuna bazata yiwa iyayen nata biyayya ba". hararan da Hamman ya mishine yasa ya kame bakin shi, ya Sadik ma sai hararan Ummul d'in yake yana jin tana gaida shi yak'i amsawa, ya Usman kuwa Hajjajo ya kallah cikin murmushi yace, "Hajjajo kingafa na girma na zama baba da haka kar ki kuma cemin yaro". dariya sukayi baki d'aya sai kuma suka juyo gun Aliyu da yake hararan Ummul yana janye piket d'in abincin gaban shi yana cewa, "mitssss wallahi ke dai kin bonu da kwad'ayi kina ta kallona salon na kware ni ba baki zanyi ba tunda ai ke yanzu ba yar gidan nan bane". Hamman ne ya kalleta cikin kula yace, "Zakici abin cin ne". Kai ta gyad'a a hankali tace, "eh yunwa nake ji". Adam ne ya tsuke fuska tare da cewa, "Uban me ya hanaki kiyi girkin a gidan ki kici?". hawaye ta fara k'ok'arin zubdawa ganin haka Hamman ya mik'e tare da cewa, "Taso mu tafi gidan Ammina zata miki duk abinda kike so bar musu abincin gidan su". mik'ewa tayi dan tasan inya tafi ya barta zasu iya mareta, shiko Hamma Umar hannu yasa ya kamo na Usman sannan yace, "tashi mu tafi". dariya yayi sannan ya mik'e suka fita, Nenne ko kallonsu take cikin k'aunar yadda suke k'aunar juna tace, "ku gaida min Ammin kuce sai gobe Aliyu zai kawo mata aiken nata". "toh ". Sukace sannan suka fita, suka nufi gidan Ammin nasu, suna fita Abba ya kalli Adam dake bin bayan ummul da harara yace, "Adam me kuma Ummul ta aikata? dan na lura fushi kake da ita". zama Adam d'in ya gyara sannan ya kwashe labarin yadda sukayi da Ummul da Hamma Umar d'in ya fad'awa Abban, gaba d'aya parlour shiru sukayi dan yadda Abba da Daddy suka hatsala fad'a sukeyi sosai tamkar zasu bugi babu daga k'arshe fad'an ya dawo kan Nenne cikin tsananin fushi Abba yace, "khadija na lura kece kike d'aurewa Ummul gindi takeyin abinda taga dama shin dan na had'ata da d'an d'an uwana ai bawai yana nufin tayi ta tozartarmin da shiba, ashe ban saniba ban isa da Ummul ba toh wallahi zan d'auki mataki a kanta". ita kam Nenne gaba d'aya takaicin Ummul ya isheta, tunda gashi laifinta ya shafeta, dama in yaro yayi abu mara kyau tofa koya uwa zatayi sai anga laifinta, shiko Abba da Daddy kan Adam d'in suka haura da fad'a, "ai kaima baka da wani amfani tunda ka kasa d'aukar mataki a kanta kuma tunda na dawo baka gaya min ba sai yau yau d'inma saida na tabbaye ka, to daga yau ni na baka izini da Umarni in Ummul ta sake yin abu makamancin wannan kayi mata duka sai ta konta jinya tunda bata jin magana". Hajjajo ce taja tsaki tare da cewa, "yarinya sai taurin Kai kamar Arnan forko, a mata dukan shine maganin ta". ita ko Nenne, shiru kawai tayi tana jinsu sunata fad'a, haka dai sukayi ta fad'a daga bisani suka watse. A gidan Ammi kuwa suna shiga gidan ya Usman ya nufi parlour Ammin yana, "Ammmmmi! Ammi! Ammina ina kike ne ". Ammi dake kitchen cikin tsananin mamaki da jin muryar autan nata ta fito, Inna ma da sauri ta fito daga bedroom nata, a parlour suka sameshi yana ganin Ammin nashi da sauri ya k'arisa gaban ta cikin tsananin kewar juna ya ruggumeta itama kuwa sai murmushi take tare da hamdala, Hamma Umar kuwa da yanzu ya shigo tare da Ummul mamaki yake yadda shi Usman ba ruwanshi ba kunya ko nauyi yake ruggume Ammin tasu abinda shiko bazai iyaba, ita ko Ummul cikin sanyi ta matso kusa da Ammin a hankali tace, "Ammi ina kwana? ". Da sauri Ammin ta ture Usman sannan ta kama hannun Ummul suka zauna kan 3 str Inna ko ta zauna kan 1 str tana fuskantar su, shiki Usman d'aya gefen Ammin ya zauna kamar yadda ya saba, shiko Hamma Umar a hankali ya matso gaban Ammin ya zauna a k'asa kan carpet sannan ya rusunar da kanshi tare da cire hular kan nashi, ya sunku yar da kan nashi, murmushi Ammin tayi sannan tasa hannu ta dafa kan nashi kamar yadda suka saba cikin tsananin farin ciki tace, "Allah yayi muku Al'abarka Allah ya tsaremun ku da zuk'atanku da imaninku Allah ya jibanci lamuranku". "Amin Amin". suka amsa baki d'aya sannan shiko Usman ya juyo ya gaidata cikin happy tace, "Usman ya jikin naka "?. da sauri ya kalli Hamman nashi dake shirin yin magana sai ya kuma kalli Ammin yace, "Ni na samu lafiya plxx adena yawan cemin ya jiki, indai ba so kuke yaron da Ummul zata haifa shima ya fara cemin ya jikin ba". dariya sukayi baki d'aya sannan ya kalli Ummul d'in yace, "A cici akawo miki abincin ko? ". kai ta sunkuyar itako Ammi tana jin haka ta koma kitchen ta had'o musu abincin ta kawo musu, Inna ce ta kalli Usman tace, "Kai aggona tare zamuci fa dan yau amarci zamuyi". duk dariya sukayi, shiko Hamma Umar abin cin ya had'a musu a pilet sannan ya kalli Ummul da Usman yace, "ku sauk'o kuci abincin". sauk'owa sukayi suka fara ci dan ita Ummul da Ammi tamkar uwa da ya suke, shiru Ammi tayi ta zuba musu ido ganin Usman da Ummul kecin abincin shiko Umar sai in sunci ya k'ara musu sannan ya had'a musu tea a hankali tace, "Farouq kai bazaka ci bene? ". kai ya jinjina sannan ya kalli Ummul d'in da Usman yace, "Ammi na nafi buk'atar inga su d'in sunci". murmushi Usman yayi ya kalli Ummul dake ta faman d'uri ko a jikinta, itako Ammi sai ta had'a wani tea d'in sannan ta mik'owa Umar d'in tace, "karb'i kasha kai kullum kan kula da Usman kake k'arewa sam bak'a kula da kanka". murmushi yayi ya karb'a yana sha tare da cewa, "To Ammina nagode". itako Ummul tana gama cin abincin tayi mik'a tare da kallon Ammi tace, "Ammi bacci zanyi". cikin jin dad'i Ammin tace, "taso muje ki hau gadona kiyi baccin ki". haka taje ta konta, suko sukayi ta hira, anan suka wuni har yamma sannan suka sallamesu suka koma a gidan ma suka d'anyi hira bayan sallan ishane Hamma Umar d'in ya kwashi Ummul d'inshi suka koma gidan su cikin damaturu. Lokaci ya juya yanayi ya canza a cikin sati 3 da dawowar Usman yayin da yanzu cikin Ummul yake da wata bakwai da sati 3 tsakanin Hamma Umar kuwa da Usman wani irin shak'uwane da son juna me tsanani yake k'ara ratsasu Usman baya iya yin kwana 2 baije damaturu ba inko ya kwana 1 bai jeba toh Umar zai d'auko Ummul su zo, Itako Ummul da Hamma Umar zuwa yanzu abu yaci tura ko gaban Usman Ummul cewa take aje a cire cikin ya isheta ita ta gaji dashi, a gefen ciwon Usman kuwa Allah ne yasan halin da Usman yake ciki dan gaba d'aya shida kanshi yana jin rayuwarshi ce tazo k'arshe shiyasa yake jin son Umar a ranshi kar yaya yakan zauna yayi ta kuka yana tuna halin da Hamman na shi zai shiga randa labarin mutuwarsa ta riskeshi, yau ma kamar kullum bayan Adam ya fitane shiko ya tashi ido cike da k'ollah pictures d'in Hamman shi da na Ammin shi sai na Ummul ya tattarosu kan carpet ya zauna ya watsa pictures en a gaban shi kamar zaucecce ya fara magana da surutai, "Kaito na ni Usman tir da halin zuciyata mara d'aukar k'addara tir da zuciyar da take son matar d'an uwana mafi soyuwa a gareni d'an uwan da yake sona fiye da kanshi amman zuciyata ta gaza bar mishi matarshi tir da halina, Hamma kana gujemin mutuwa a ganina itace mafita fargaba na d'ayane, Hamma na ya zakaji randa idanun ka zasu ganema gawata wazai lallasarmin kai wazai dawo madadina a gareka Hamma zan barka da Ammin mu kai kad'ai ko ya Ammin mu zataji randa zata ga ba Usman sai Umar Ummul sonki shine mafi munin fargaba a gareni zuciyata ta kasa barin sonki a matsayin ki na matar d'an uwana wayyo ni Usman naji kunyar rayuwata, son matar aure me zance da uban gijina Allah kai kajarabci zuciya ta da son Ummul Allah ka yayemin kar d'an uwana Umar ya gane inason matarshi". a haka yayi ta kuka da surutai har zuwa wani d'an lokaci sai kuma kawai ya kife kai yayi ta kuka tare da tari mai tsanani cikin layi ya mik'e ya tattara pictures d'in, ya juyo Kenan idanun shi suka sauk'a kan fuskar...... *by* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL, AMARI* Page 2⃣7⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *A TRUE LIFE STORY* ```Masoya na makaranta ina mai baku hak'uri dan naga k'orafe-k'orafen ku amman ku sani cewa wallahi wannan littafi nawa RUBUTACCEN AL AMARI NE MIN IND'ILLAH wannan labarin Allah ne ya tsarawa mutanen wannan littafin rayuwarsu a haka ba k'age wlh duk abinda kukaji na Al'ajabi gaskiyane ya faru har kuma wanda zakuji a gaba hatta dai-dai da ruwan tea da Ummul ta watsawa Hamma Umar a ido wallahi gskya ne hatta soyayyar Hamma Umar ga Ummul da ciwon Usman, ku bini a hankali wallahi tallahi akwai darasi mai girma a labarin nan``` *A* kan fuskar Nenne ya dire ida nunshi, kallon shi itama takeyi tana juya mishi kai cikin zubda k'ollah, shi kuwa komawa yayi ya zauna ya kife kanshi jikin kujera ya rink'a kuka mai cin zuciya, kusa dashi Nennen ta zauna a kan kujera, jinta a kusane yasa Usman ya d'aura kanshi guiwowinta sannan ya ci gaba da kuka, hannun tasa kan kafad'unshi cikin sanyi tace, "Usman ashe bazaka yiwa kanka fad'aba shin haka zaka bar rayuwarka cikin garari Usman ka manta illar abin da kakeyi shin haka zakaci gaba da son matar d'an uwanka Usman kai har sai yaushe zaka ruggumi k'addarar ka ashe bazaka zamo mai yarda da k'addarar rayuwar kaba". Kai ya d'ago ya rik'o hannun ta sannan ya rink'a juya kai cikin rawan murya yace, "A, a Nenne a a na yarda da k'addarata na bar son matar d'an uwana na cireta a raina bana son Ummul Nenne Hamma Umar da Ammina nake tausayawa Nenne zan tafi tafiyar da ba dawowa zan bar Hamma na bari na har abadan, Nenne Hamma na baida aboki sai ni Hamma baida mashawarci sai ni Hamma baya gayawa kowa matsalarsa sai ni Hamma yafi sona fiye da kanshi, Nenne ya Hamma na zaiji randa babuni ya Ammina zataji wazai lallasarmin su wazai sasu dariya wazai shiga rayuwarsu a madani dan ya sasu farin ciki Nenne tausayin Hamma nane ke sani kuka da k'uncin zuciya". kuka sosai yakeyi hawaye har gemunshi itama Ammi kuka takeyi sosai dan tausayin halin k'addarar rayuwar Usman da Umar kuka ta kumayi dan tausayawa Umar yaro ya tashi cikin maraicin Uba amman duk da haka ya hana Usman maraici ya zame mai madadin Uba ga kuma wata sabuwar kaddarar da zata rabashi da Usman d'in Murya na rawa tace, "Haba Usman ka dena fad'in haka ciwo ba mutuwa ba kuma Insha Allah zaka rayu da d'an uwanka kuma Allah ne gatan bawansa Umar, Usman ka kontar da hankali ka". kai ya gyad'a tare da share hawayen nashi sannan ya kalli Nenne a hankali yace, "Nenne kukana kikaji har cikin gidane yasa kikazo?". kai ta juya cikin sanyi ta mik'o mai magungunan shi tace, "Abban kune ya bani maganin ka in bawa Aliyu ya kawo maka so dana fito sai na samu Aliyun ya tafi gidan Ammin ku shine na kawo maka dan kasha sai kuma na samu kana cikin wannan halin". Ajiyan zuciya ya sauk'e sannan yace, "Nagode Nenne da kike tayani b'oye sirrina dan Allah ko bayan raina kar Hamma Umarna yasan wannan matsalar tawa". kai ta gyad'a mai cikin zubda k'ollah tace, "Insha Allah bazai saniba". haka ta zauna tayi ta mai nasiha har saida taga ya d'an sake sannan ta bashi maganin yasha ta fice ta tafi, shiko wayarshi ya d'auka cikin k'aunar Hamman nashi ya kirashi yana d'agawa sai cewa yayi, "Hamma na ina sonka! ina sonka! ina soka! bana son kayi nesa dani ina sonka d'an uwana ina son Ammin mu bani da kamarku a duniya Hamma na duk son da nakewa Ammi wanda nake maka yafi yawa ina sonka fiye da kaina". Shiru Hamma Umar yayi jikin shi a mace da kalaman Usman a take yaji kamar an rufe mishi jikin shi da d'anyen fata wani irin sanyi ya ziyarci rayuwarshi hannun shi ya fara rawa tuk'in da yakeyi ya fara gararsa dan wani kasala da yaji cikin firgici yace, "Usman meke damun ka zuciyar ka ko? Usman ka gaya min meke damun ka". dariya Usman yayi cikin calikanci yace, "Ni Hamma matsalata da kai Kenan kai saurin tsoro gareka ashe dan nace ina sonka sai ya zama banda lafiya toni lafiyata lau aradu". murmushi Hamman yayi duk da har yanzu yanayin sanyin na jikin shi, a hankali yace, "Nima ina sonka ina sonka sama da yadda nike son kaina d'an k'anina". dariya sukayi baki d'aya a dai-dai lokacin kuma yayi parking a cikin gidan nashi sannan ya katse Kiran, ya shiga cikin gida. Kai tsaye bedroom nashi ya wuce, yana shiga ya fara rege kayan jikin shi wonka ya sha yana shiga Ummul ta shigo d'akin a bakin gado ta zauna tasa k'aton cikin ta a gaba, shiko fitowa yayi k'ugunshi d'aure da towel yana ganin ta ya matso gabanta hannun yasa ya shafa cikin ajiyan zuciya yayi tare da kallon idonta yadda suka kumbura alamar tayi kuka zama yayi ya jawota jikin shi a hankali ya mannan kanta a kirjinshi dake da d'an damshin ruwa jin sanyin jikin shi yasa ta k'ara manna kanta sannan ta fara magana cikin muryar kuka da rauni irin na masu tsofaffin ci, "Hamma sai yaushe zaka ciremin cikin Hamma kullum sai kace min sai gobe gobe sai goben shi gashi yanzu kullum k'uguna ciwo yake min dan Allah ka rabani da cikin nan naka". k'ara ruggumeta yayi cikin sanyi yace, "Ummul na kiyi hak'uri ki haifa mana shi da kanki kar in cireshi inya girma yaji kinsa an cireshi a cikin zaiyi kukan bakya sonshi kinga fa yau saura kwana uku rak cikin ya cika wata takwas kinga kenan saura wata d'aya ki haifamin shi ni zan raini abuna". Rigarta ta d'aga sama ta nuna mai cikin sai kuma ta fara kuka tare da yarfa hannu tana buga k'afa tana, "Wallahi ni dai na gaji nayi iya taimakon da zanyi kawai ka cire min cikin tunda kai kana son abunka ka ciremin shi wallahi ko nasha gishiri na fiddashi". k'ara ruggumeta yayi cikin sanyin da kalaman Usman suka sakar mai yace, "Toh na yard'a zan cireshi amman kiyi hak'uri sai gata dan gobe da safe zan kaiki potiskum gun Nennen ki dan zamuje Abuja nida govnr akwai wasu gwaje-gwajen da zamuyi mishi da wasu doctors d'in kwana d'aya zamuyi muna dawowa zanje in d'aukoki mu dawo sai na cire cikin ko". kai ta gyad'a cikin jin dad'i tace, "Toh na yarda". murmushi yayi cikin kasala ya k'ara jawota jikin shi a hankali ya shafa cikin sannan yace, "d'ana ina sonka ina son mamanka". sai ya kuma tura hannun shi kan kirjin ta da suka k'ara ciccikowa a hankali yace, "Khairi na a d'an barni nayi pakala mana wata k'il daga nan ma baby ya fito". baki ta tura tace, "Na gaji ni na gaji da wannan jarabar". kai ya sunkuyar tare da cewa, "ya isa na barki kiyi baccin ki ina dai kinci abinci? ". "eh". tace sannan ta konta gefenshi shiko al'wala yaje yayi sannan yazo yayi nafilfilinshi tare da karatun qura'an ya rok'owa d'an uwanshi lafiya sannan ya rok'awa Ummul enshi sauk'a lafiya tare da mata fatan samun gajeriyar nak'uda, Sai k'arfe 2 na dare ya konta. Washe gari da safe bayan sun gama shirin su, suka nufi hanyar potiskuma dan yana sauri zai dawo su tafi Abuja, suna isa gidan A parlour Hajjajo suka zauna gaba d'aya gidan sai ya Sadik dake kitchen din Nenne, bayan sun gaggaisa ne ya kalli Abba cikin girmamawa yace, "Abba zamuje Abuja nida govnr kwana d'aya zamuyi toh gida ba kowa shine na kawo Ummul gida sai na dawo goben zanzo in d'auketa". Kallon shi Abban yayi tare da cewa, "Toh Allah ya kaiku lafiya Allah ya bada sa'an tafiya". "Amin Amin". suka amasa baki d'aya sannan ya mik'e tare da cewa, "sai na dawo". kusan duk a tare suka ce, "Allah ya dawo da kai lafiya". "Amin". yace sannan ya fito har yaje bakin kofar fitan yace, "Ummul zo". ba musu tabi bayan shi ganin hararakin da take sha, kai tsaye parlour Nenne suka nufa, suna shiga ya jawota jikin shi ya ruggumeta kanta ya tallabo ya had'e bakinsu wuri d'aya kissing nata ya rink'ayi cikin salon so da k'auna, itako tureshi ta rink'ayi har saida ta zame bakinta tana haki shima yana hakin, cikin tsiwa tace, "Wallahi ka fiye jaraba da wannan jarabar taka ka d'irkamin cikin nan kawai ka tafi kana dawowa ka ciremin cikin nan na huta da fitina". duk maganganun da takeyi kab a kunnen Sadik da yake dafa indomi a kitchen d'in Nenne, shiko Hamma Umar shafa fuskarta yayi sannan yace, "ba matsala Ummul wata ran zakiso wannan d'an naki fiye da kowa a duniya". baki ta tura tace, "Bana sonka bana son cikin". kai ya kad'a sannan ya fita ya tafi, kai tsaye Damaturun ya koma bayan sun gama shiri da tawagar govnr suka nufi babban birnin taraiya. A gida kuwa Hamma Umar d'in yana fita, itako ta koma ta zauna kan kujera, shiko Ya Sadik shiru yayi a kitchen d'in har saida yaji tashin motar Hamma Umar d'in yana jin ya fita gidan, shima ya fito parlour Ammin kai tsaye gaban Ummul ya tsaya hannu yasa ya kamo nata ya tsaida ta, itako da take lumshe da ido jin an d'agota ta bud'e ido cikin firgici baki na rawa tace, "y...! ya....! ya.. yaya Sadik". k'ara ta cilla da k'arfi tare da dafe kuncinta dan jin wani irin gigitaccen marin da Sadik d'in ya sakar mata, shi kuwa da iya k'arfin sa ya rink'a zuba mata maruka a jere a jere ba k'ak'k'autawa marinta yake cikin fushi da jin haushinta yama manta tana da ciki ji yake kamar ya karya ta, tuni ya fasa mata baki, itako sai kuka take tana kiran , "Wayyo ya Sadik kayi hak'uri wallahi bazan sakeba wayyo Hamma Umar ka tafi ka barni zasu kasheni wayyo Nenne na wayyo Abba na wayyo ya Usman ". haka ta rink'a kuka da kururuwa ba wanda yayi yunk'urin k'arbarta sai da sukaji kukan yayi yawane suka fito duk sukazo, ganin marinta kawai Sadik keyi sannan ya gaya musu abinda yaji tana gayawa Hamma Umar hakan yasa gaba d'aya suka k'i kwatarta, sai Adam ma daya k'ara zuba mata maruka duk aka resa mai karb'arta a gidan Usman ma sosai yaji zafin yadda take nuna bata son d'an uwan nashi, shiko Sadik mammaketa yayi har saida fuskarta ta kumbura tayi jazir, sannan ya barta Abba ma yazo yayi ta fad'a kamar zai ari baki Nenne kuwa fushi tayi da ita tak'i ta kulata, Usman ma fushin yayi da ita, haka ta wuni a wannan ranar cikin kuka da k'unci ga zazzab'i mai zafi ga ciwan kai gaba d'aya ta jeme tak'i taci komai tak'i tasha komai sai kuka har muryarta ta disashe hatta cikin nata saida ya yayi k'asa motsinshi ya d'an ragu, hajjajo ce mai d'an bata abinci duk da itama fushin take da ita a haka ta kwana har washe gari har zuwa yamma bataci komaiba duk gidan sun juya mata baya hatta Aliyu fushi yake da ita. Shiko Hamma Umar a Abuja tunda sukaje bai samu sukuni ba haka yasa bai kirasuba sai dare daya kira Kuma sai akace Ummul tayi bacci hakan yasa basu gaisa ba koda gari ya waye ya kira duk woyoyin gidan basa shiga, haka yasa suna dawowa ko gidanshi bai komaba ya kama hanyar potiskum d'in, yana shiga cikin garin sai kuma yaji kewar Ammin shi da begen son ganin ta hakan yasa ya nufi gidan Ammin yana zuwa ya samesu ita da Inna da uncle ensu suna tsakiyar gidan suna ta hira, kamar ko yaushe gaban ta ya zauna ya tonk'oshe k'afafun shi sannan ya cire hular kanshi, itako Ammin ido ta tsura mai cikin murmushi da Happy tasa hannun ta kan gashin kanshi murya cike da k'auna tace, "Allah yayi maka Albarka Allah ya tsaremin kai da d'an Uwanka Allah ya sanya alkhairi a rayuwarku ubangiji yayi muku rahama duniya da lahira". Murmushi yayi cikin jin dadi yasa hannun shi ya dafa hannun ta dake kanshi yace, "Amin Amin Ameeeeeeeeeeeeeeeen ya rabbil izzati Ammina". sai kuma ya juya ya Kalli Uncle en cikin girmamawa yace, "Uncle ina wuni ya gida". "Lafiya lau Farouq ya hanya yanzu Ammin ka ke cemin jiya kazo ka sallameta zaka tafi Abuja". "Alhamdulillah". yace da uncle d'in sannan ya kalli Inna yace, "sarkin surutu yau ya naganki shiru ko dan banzo da ogan naki bane". dariya tayi sannan tace, "ai kaima oganane". kallonta yayi a hankali yace, "kin Kama gaibu gwara miki Usmanun ki". dariya sukayi duka shiko Hamma murmushi yayi sannan ya kamo hannun Ammin shi yace, "Ammina farcenki ya d'an taru bari in yanke miki". murmushi tayi tace, "toh Allah ya ma albarka Allah ya tsaftace rayuwarka kamar yadda kake tsabtace min farcena". "Amin Amin". ya amsa sannan ya yanke matasu ya kankare mata, bayan ya gama ne ya kalleta cikin karya wuya yace, "Ammina yunwa nake ji kuma yau abin cikinki nake son ci". mik'ewa Ammi tayi da sauri ta nufu kitchen, abincin ta kawo mai tare da roban wonke hannun, tuwan farar shinkafa da miyar ganye yasha man shanu da nama, gaban shi ta ajiye mai a hankali tace, "matso kaci ka d'ena zama da yunwa bana so". "toh". yace sannan ya bud'e abincin murmushi yayi yace, "Tab Ammi ai wannan yamin yawa gsky bazan iya cinyewa ba sai dai in zamuci tare zanfi jin dad'in cin". murmushi Ammin tayi sannan ta matso sukaci a tare sannan suka dan yi hira Inna da uncle suna ta musu dariya, sannan ya salla mesu ya tafita, har yaje kofar gidan ya dawo ya kalli Ammin nashi itama shi take kallo a hankali yace, "Na manta ban gaya miki ba na kusa na samowa autanki mata muyi mishi aure yafi zaman hakan matar zata kulan mana dashi". murmushi tayi sosai sannan tace, " toh Allah sanya Al,khairi". "Amin Amin Ammina kiyiwa k'anina fad'a ya rink'a kula da kanshi". "toh zan mishi kaima ka mishi ". A haka suka sallami juna, yana fita kai tsaye gidan Abban ya nufa. Bayan yayi parking kai tsaye ya kutsa cikin gidan parlour Nenne ya wuce inda ya samu ba kowa har zai juya ya fita sai yaji sautin kukan Ummul a cikin bedroom d'in, da sauri ya Koma cikin d'akin kan gado ya hangota konce tana ta rawan sanyi da kuka, cikin sauri da furgici ya k'aroso gabanta hannu yasa ya d'agota ruggumeta yayi cikin kad'uwa yace, "Khairi! Khairi na meke damun ki? Ina Nennen? ya gidan shiru basa nanne? ". ruggumeshi tayi cikin kuka ta d'ago kanta, da sauri ya tallabe kanta cikin tsoro yace, "meya samu fuskarki inasu Nennen? ". cikin kuka da tausayawa kanta ta, kwashe labarin abinda sukayi mata ta gaya mishi ta k'ara da cewa, "Nenne ma bata min magana Abba ma fushi yakeyi dani ko Aliyu sun hanashi yamin manana ya Usman ma fushi yake dani duk basa sona basa zama kusa dani yanzu duk suna parlour Hajjajo". hannun ta ya kamo cikin tsananin bak'in ciki da takaici waje ya fito da ita kai tsaye part d'in Hajjajo ya nufa da ita, kicinb'is sukayi da ya Sadik a tsakiyar gidan, yana ganin Sadik d'in yaja hannun Ummul d'in ya tsaya a gaban Sadik d'in cikin tarin bak'in ciki murya na rawa idanunshi sunyi jazir sai shek'in hawaye yakeyi cikin fad'a da d'aga murya yace, "Zo nan". jin muryarshi yasa gaba d'aya mutanen gidan suka firfito tsakiyar gidan dan basuma san ya dawoba, shiko ido ya zuba musu d'aya bayan d'aya cikin rawan murya da fad'a yace, "Sadik amman dai dama can haushina Kake ji ko? bazaka iya duka na bane shiyasa kai ma Ummul duka dan ka huce a kanta ko? ". Gaba d'aya shiru sukayi ganin yadda jikin shi ke rawa dan basu tab'a ganin wannan bacin ran a fuskar shiba, shi kuwa cikin fad'a yaja hannun Ummul zuwa gaban Adam baki na rawa yace, "Adam ka tsani Ummul ko meyasa baza kayi min adalci da kawaici ba ka tsane ni shiyasa ka tsani Ummul tunda aka Aura minta ko?". shi kam Adam da Sadik sai jujjuya kai sukeyi alamar a, a, shiko k'ara jawo hannun Ummul d'in yayi zuwa gaban Nenne cikin rawan murya da k'ok'arin maida hawayen shi yace, "Nenne ki rink'a ganina a jikin Ummul na tabbata a ko wanne hali kike zaki kulanmin da Ummul Nenne ya za'ayi kina ji kina gani a doki mutun hud'u Nenne Ummul a gareta Ammina a gareta d'an Uwana Usman a gareta d'ana da zata haifa a gareta ni kaina". Nenne kam kasa cewa komai tayi. shiko jawo Ummul d'in yayi gaban Abba dake tsaye a k'ofar parlour shi suka durk'usa cikin rauni da karya wuya yace, "Abba kayi hak'uri abin ne yayi yawa gara in fad'a musu yadda nake ji in sun tozarta ta, Abba nasan sonane yajanyo kai watsi da Ummul, Ayyah Abba in dai soyayya tace to na rok'ek'a dan Allah ka kulanmin da ita ka hana su Adam dukan ta Abba kallifa da tsohon cikin nan suka daketa in sun mata illafa me zasu cemin". ita kanta Ummul yau ta fara gano wani irin son da Hamma Umar ke mata hakan yasa ta cika da mamaki ziryan. Shiko Hamma k'ara jawo hannun Ummul yayi ya tsaya a gaban Usman, cikin tuhuma ya kafe Usman da idanu sai kuma hawaye car-car na bin fuskarsa, murya na rawa cikin kuka yace, "Ashe Usman bazaka iya kula da iya lainaba in bana nan ? Usman ashe baka damu da abinda ni d'an uwanka nake soba? shin in ban barmaka amanar Ummul ba wa zan barwa amanarta a wannan duniyar?, wallahi wallahi bazan yafewa duk wanda ya takura min itaba hankalina bazai kwantaba, Usman hakan yana nufun kenan in nayi tafiya zatasha wuya a gaban ka?." kai Usman ya rink'a kad'awa cikin kuka da tashin hankalin ganin yasa Hamman shi kuka cur-cur shima kukan ya rink'ayi yana matsowa jikin Umar d'in dan wani irin suka da zuciyarshi tayi a take jikin shi ya rink'a rawa, shiko Hamma Umar kamo hannun Ummul din yayi yace, "Khairi na mu tafi kai kuma Aliyu azatona ko kowa zai juyawa Ummul baya ai kai abokin kukanta ne dole ka lallasheta in kana son inji dad'i, Nenne wallahi gata d'aya zakumin inji dad'i ku kulanmin da Ummul in bananan Adam! Usman! Sadik! wallahi da kunsan yadda nake ji a kan Ummul da ko hararta baza kuyi ba". sai kuma yaja hannun ta ya nufi harabar gidan da ita tare da ce musu, "Adam! Usman! Sadik! kuci gaba zata dawo in yaso saiku kashemin ita ku huta". sannan yaja hannun ta suka fice suko gaba d'aya bayanshi sukabi da sauri Usman yana kuka har jikin shi na rawa yace, "Ayyah Hamma Umar kayi hak'uri ba hannuna a dukan Ummul Hamma bazan sake barin ayi mata komaiba kar kayi fushi dani d'an uwana ." Bai kulashi ba sai bud'e mota yayi yasa Ummul d'in a ciki ya zagaya zai shiga kenan Abba ya matsoshi a hankali yace, "Farouq kayi hak'uri". girgiza kai yayi cikin sanyi da zubda k'ollah yace, "a, a Abba raina nane ya b'aci kuma wallahi dazan iya tafiya da ita duk inda zanje da da ita zanje, amman bazaiyuwu ko ina muje tareba anan kad'ai zan iya barinta amman sunk'i samamin konciyar hankali". Sadik ne da Adam da Aliyu su kace, "Hamma kayi hak'uri ka gafarcemu". tsaki yaja ya bud'e motar zai shiga Kenan Usman ya ruggumeshi cikin kuka yace, "in kayi fushi dani ya zanyi?". shima ruggume Usman d'in yayi cikin rawan murya yace, "Ba komai! ba komai! ba komai! Allah zai zama gatanta tunda dukanku kun tsaneta, Kai kuma waya cema zan iya fushi da kai, bani da kamarka fa duk duniya ina sonka d'an Uwana". sai ya sakeshi ya shiga mota ya tafi yana juyowa yana kallon Usman shima Usman d'in binshi yayi da d'an sassarfa yana d'aga mai hannu alamar bye-bye tare da cemai, "Hamma na ina sonka". shima hannu ya d'aga mai yace, "Usman ina sonka". daga nan ya bar harabar gidan ya dauk'i hanyar damaturu, suna isa kai tsaye hospital ya wuce da ita yana zuwa shida kanshi ya duba lafiyarta a cikin asibitin sukayi sallah sannan ya dauketa suka wuce Restaurant abinci suka ci suka sha sannan ya wuce gida da ita. Bayan sun isane ya wuce d'akin shi yayi wonka ya fito kenan ita kuma Ummul ta shigo daga dukkan alamu itama tayi wonka, a hankali ta tako tazo gabanshi cikin sanyi ta fad'a jikin shi murya can kasa tace, "Hamma Umar ina son k.......... *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL, AMARI* Page 2⃣8⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *A* hankali tayi taku cikin sanyi ta matsoshi ta fad'a jikin shi tayi lub a k'irjin yayin da ta manna kanta a kafad'arshi ido ta lumshe cikin yanayin sanyin zazzab'in, shi ko Hamma Umar hannu yasa ya ruggumeta tsam a jikin shi sai ajiyan numfashi yake sauk'ewa ya lumshe idon shi yayi shiru yana jin bugun zuciyarta na harbawa kan nashi sai ya k'ara tallabo ta tare da shafa fuskarta, lumshe ido tayi a hankali tace, "Hamma Umar ina son kak'ira ya Usman ka lallasheshi, ka ganifa yana kuka muka barshi, Hamma kayi hak'uri karkayi fushi da ya Usman". jawota yayi suka zauna tsakiyar gadon nashi sannan ya zauna ya d'an jingina da jikin kan gadon ita kuma ya jawota jikin shi sannan ya d'an sunkuyo kanta yana kallon fuskarta kallo mai cike da wasu yanayin a hankali ya fara magana cikin lumshe ido yace, "Usman wani sashi ne na jikin Umar Usman rabin jiki nane Usman d'an uwanane da bani da madadin shi Usman aboki nane kuma amini nane kuma shak'ik'ina ne Usman wani babban jigone a rayuwa ta, Ummul kin tab'a ganin mutun yayi fushi da d'an uwanshi Ummul indai zanyi fushi da Usman toh zanyi fushi da karan kaina kenan Ummul ba fushi nayi da Usman ba a a hannun ka mai sanda nayi mishi". shiru tayi tana jin wani irin yanayi daya bak'onci rayuwarta tun sanda taga Hamma Umar d'in na kuka a gaban su Abba yana kuma yiwa su ya Adam fad'a, haka kawai ta tsinci kanta da k'ara ruggume shi sai kuma tayi luf a jikin shi kamar maiyin bacci, shima shirun yayi a haka har zuwa wani lokaci sannan ta d'an d'ago kanta ta kalleshi a hankali tace, "Hamma ka kira ya Usman kaji kayi hak'ari shifa ya Usman baimin duka ba". baiyi magana ba sai hannu yasa yajawo wayarshi dake kan dressing mirror sannan ya kira Usman d'in tare da sa amsa kuwa, shiru sukayi suna jin yadda woyar ke ruri bai d'agaba, a gida Kuwa su Hamma Umar d'in na fita Abba yayi tayiwa su Adam fad'a, Hajjajo Kuwa gaba d'aya mamakin Umar take, shiko Usman suna watsewa, kai tsaye d'akin su ya nufa yana zuwa kan gado ya fad'a cikin tarin k'uncin zuciya da zafi haushin kanshi da kanshi yakeji tunda ya kasa samawa Hamman shi farin ciki mutumin da kullum burin rayuwarsa yasashi farin ciki amman shiko yau sai kuka yasa d'an Uwan nashi gaba d'aya sai yaji ya tsani kanshi da kanshi cikin kuka ya rink'a cewa, "Hamma na kayi hak'uri ka gafarceni Hamma na bazan sake yin abinda zai bata ma raiba insha Allah nima zan saka farin ciki". yana cikin haka ne yaji woyarshi na suwa, hannu yasa ya amsa kiran tare da manna woyar a kunnen shi, shiko Hamma yana jin a ya d'aga cikin sauk'e numfashi yace, "B'iyaye na fushi kayi da nine? toh kayi hak'uri kaji ko d'an uwana Usman ka gafarce ni." kai Usman ya rink'a jujjuyawa tare dasa tafin hannun shi ya share hawayen shi murmushi yayi mai d'an sauti sannan yace, "In dai zanyi fushi da Hamma na kenan zanyi fushi da mutanen duniya baki d'aya Hamma na ni zan nemi gafararka ba kai zaka nemi nawaba ka gafarce ni Hamma na karkayi fushi dani". murmushi yayi jin dad'in Usman baiyi fushi dashi ba sannan yace, "Ni bakayi komai ba na yafe maka kaima ka yafe min sannan ka samu Adam da Sadik da Aliyu kace su gafarceni nima na yafe musu". dariya Usman yayi yace kai Hamma mune da laifi kuma mu za, a bawa hakuri har ka huce kenan". murmushi yayi yace, kai Usman da kana kusa dani da sai na rongwoshe ma kai na kuma matsema kunne tunda bakajin magana". dariya Usman yayi sosai dan yaji dadin hucewar da Hamman shi yayi, shiko Hamman a hankali yace, "Usman inajin kunyar Nenne da Abba nayi ta fad'a a gaban su watak'il na b'ata musu rai, dan Allah ka basu hak'uri kace su gafarceni". da sauri Usman ya katseshi da cewa, "Tab Abba fa da Nenne da katafi saida sukayi ta fad'a kamar su ari baki Abba harda marin Sadik, sai kace badasu akayi wa Ummul d'in hukunci ba duk suka ware kansu laifi ya koma kan Sadik da Adam nima da Aliyu sai muka zille kanmu". dariya sukayi baki d'aya sannan Ummul dake jinsu kuma tace, "Ya Usman ba cin zalina kukayi ba duk kun tsaneni ba mai sona dan kunga Hammana baya nan kukamin halin yan ubanci". dariya yayi yace, "ai ked'in ce bakya jin magana". ruggume Hamma Umar d'in ta k'arayi da k'arfi sannan ta d'ago kai ta kalleshi baki ta d'an tura tare da cewa, "ina jin magana mana ya Usman ka tabbayi Hamma shi yasan inajin magana". sai ta kuma kalli Hamman a hankali tace, "Hamma inada jin magana ai ko?". ruggumeta shima yayi sannan yace, "sosai ma kuwa Khairina tana da jin magana". Murmushin jin dad'i tayi shiko Usman dariya yayi ya katse kiran, ya kife kanshi cikin pillow numfashin sa na fuzga, shiko Hamma Umar ganin yadda Ummul ke mak'ale dashi a hankali ya jawo blanket ya rufe musu jiki hannu yasa yana shafa cikin nata, ita ko hannun ta ta kife kan kirjin shi tana d'an murza yatsarta a jikin shi, a hankali yace, "Khairi! Khairi! Khairi! ". shiru bata amsa ba, sunku yowa yayi ya lek'a fuskarta abin mamaki sai yaga tayi bacci tuntuni sai jikinta da ya k'ara zafi da zazzab'in haka yasa ya gyara mata kwanciyar ta a jikinshi sannan yayi musu addu'a ya shafa musu sannan ya d'auki woyarshi ya fara karatun qura'an, a haka har bacci yayi awon gaba dashi. washe gari lahadi da sassafe Hamman ya tashi kamar yadda ya saba ya kimtso komai sannan ya zauna da kanshi ya bata abinci Sauri-sauri dan duke da yau lahadi ne yauma zaije gidan govnr zai k'ara duba lafiyarsa, 9:20 Am ya gama komai ya fita kai tsaye gidan gomnatin jihar yana nufa. Itako Ummul a gida Hamman nata yana fita ta koma d'akin shi ta zauna haka nan ta tsinci kanta da yin abinda bata tab'ayi ba duk da zazzab'in da take ji amman taji k'arfin guiwar jikin ta d'akin ta fara tattarewa ta kimtsa duk abinda ya watsa kafin ya fita zanin gadon ta canza mai ta nad'e wannan d'in sannan ta share ko ina ta goge komai ta killaci d'akin sannan tasa turaren wuta mai k'amshi daga nan ta koma d'akinta ta gyara ta fito parlour su har dinning area da kitchen nasu kab ta gyara komai sannan ta shoga kitchen d'in, karo na forko kenan da tayi niyar tayi girki tare da rebon Hamma Umar d'in dan takanyi girki kam amman bata tab'ayi da rebonsa ba, shiko in zaiyi itace forkon ci kuma duk inda yake zai dawo ya mata abinda zataci ko yana office yakan dawo yayi girki ta kuma ci, amman yau da niyarta a cikin ranta zata yi girkin dan inya dawo ya huta, bayan ta kammala aiki ne ta koma d'akinta wonka tayi mai rai da lafi sannan tana fitowa karano na forko a da ta zauna tayi kolliya na gani na fad'a sannan ta zira doguwar riga a jikinta duk ta feshe jikinta da turaruka tare da murje humra a jikinta, k'arfe 2:00 pm ta fito parlour bayan tayi sallan azahar, a k'asa ta konta kan carpet tayi matashi da pillows d'in kujerun lokaci d'aya kuma gajiyar aikin da tayin ya rufeta sai mik'a takeyi, shiko Hamma Umar a gidan govnr yayi sallan azahar ana idarwa ya koma ya sallamesu sannan ya nufi gida, da saurinshi dan yana tunanin Ummul ba lafiya, yana yin parking ya fito ya nufi cikin gidan a parlour ya sameta tana konce abun mamaki ko ina fes gashi ta raggad'a kolliya sai shek'i takeyi, cikin mamaki ya zauna gefenta yana kallon dinning table nasu daya ga an shirya kuloli a hankali yace, "Hmmmmm Halima ce tazo? ". kai ta juya ba tare da ta fahimci manufar tabbayar ba, shiko a zatonshi Anty Haliman ce tazo tayi musu wad'an nan aiyu kan, k'ara matsota yayi yana shak'ar k'amshin jikin ta a hankali yace, "Kinyi kyau Ummu na wannan kolliya haka duk ni akayiwa ko?". hararan shi ta d'anyi sannan ta juya kai, shiko matsota ya kumayi yace. "Naga kamar kin gyara gidan kamar har da girki ko?", tureshi tayi sannan tace, "Kamace ma kenan? , kuma ai dama ina wonka ni dai ba k'azama bace girkin ma ai inayi dama banayin mai yawane yau kuma naga baka dawo da wuri bane kuma naga kamar ka gaji shiyasa nayi girkin da rebonka". wani irin murmushin jin dad'i yayi wanda har a fuskarsa za, a ga tsantsar farin cikin sa ajiyan zuciya ya rink'a sauk'ewa tamkar wanda aka cirewa abu mai nauyi, Ita kuwa mik'ewa tayi ta koma gefenshi a hankali tace, "ni fa yunwa nake ji". mik'ewa yayi da sauri hannun ta yaja sukaje suka zauna, kamar wasa Ummul ta had'a mai komai sannan ta sawa kanta, ta faraci ba tare da ta kalleshi ba, shi kam gaba d'aya ya cika da mamaki a haka sukaci abinci, sannan ya wuce bedroom nashi a nan ma yasha mamaki wonka yayi sannan ya zira jallabiya parlour ya fito ganin bata nanne ya lek'a d'akin ta sai yaga tana sallan la'asar haka shina ya wuce masallaci, koda ya dawo bata parlor kamar zai lek'a d'akin nata kuma sai ya fasa ya zauna dan yayi zaton ko tayi bacci, itako tana jin motsin shigowar shi ta mik'e a hankaki ta fito yana ganin ta ya zuba mata ido dan wani irin kyau tayi wanda bai tab'a ganin tayi irin wannan kyawun ba, kanshi ta nufa a hankali har tazo gaban shi, shiko sai ware ido yake yana kallon ta, kauda kai tayi sannan ta zame a hankali ta zauna a jikin shi, gaba d'aya yau Ummul ta cikashi da mamaki donko duk abubuwan da takeyi bata tab'a yinsu ba , ita kuwa lafewa tayi a jikin nashi tana rik'e da hannun shi duk motsin da zaiyi ta k'ara shigewa jikin shi ta kanainayeshi, ganin hakan shima ya wore hannun shi ya ruggumeta sannan ya tallabo kanta ya manna bakinshi kan nata, ido ya bud'e ya tsurawa ma tasu jin yau ba musu Ummul ta bud'e mai bakinta, idonshi kan nata idanun ya lalubo harshenta yana mata wani irin salo mai tafiya da hankali, itako sai lumshe nata idanun tayi tana k'ara narkewa a jikin shi, abu kamar wasa gaba d'aya salon Ummul na wunin yau ya canza ko motsi mai k'arfi ta hana shi yayi duk yadda zai juya tana mak'aleshi, shi kam har yanzu mamakin ta yakeyi. A haka har aka kira sallan magrib a hankali ya d'an d'agota cikin kula yace, "Ummul na muje muyi al'awala lokacin sallah yayi". tana jinshi amman sai tayi shiru a jikin shi tana k'ara manne tafin hannun ta da nashi, murmushi yayi tare da d'agota suna fuskantar juna murya can k'asa yace, "Ummul na yau dai kin fara son Hamman ki amman rigima ta hanaki ki gane bare ki gaya min inji dad'i". janye jikin ta tayi da sauri ta mik'e ta nufu hanyar bedroom nata tana k'unk'ini tare da cewa, "Ni dai a a, dan kawai na rab'eka to ni bana son k...!". karo na forko da ta kasa k'arisa cewa bata sonshi kenan sai kuma ta juyo suka kalli juna, murmushi yayi yace, "Ina sonki Ummul khairi na so mai tarin yawa zanci gaba da sonki har gaban Abadan". bata kulashi ba ta wuce cikin d'akin, shima masallaci ya wuce, bai dawoba har saida akayi sallan ishah sannan ya dawo, yana shiga d'akin ta ya wuce kan sallayan ya sameta tana zaune rik'e da qura,an tana karatu ganin haka shima ya zauna gefenta sukaci gaba da karatun bibbiyu inda suka karance suratul bak'ara bak'i d'aya sannan sukayi addu'oin masu tarin yawa, sai k'arfe 9:00 pm suka shafa addu'oin suka mik'e a tare, hannun ta ya kamo suka fito parlour abincin daya seyo musu bayan fitanshi masallaci ya zauna ya bata da kanshi taci kuma sosai, sannan aka fara darun shan magani wanda inda sabo Hamma Umar ya saba da darun Ummul a kan shan magani kullum sai tayi tamai gardama da rigina, haka dai da kyer ya samu tasha, sannan yaje da kanshi ya had'amata ruwan wonka saida yaga ta shiga sannan shima ya wuce d'akin shi, wonkan yayi sannan ya fito yayi shirin baccin 3 qtr ne kawai yasa sannan ya feffasa turare, kitchen yaje tea ya had'a dan shi baici abincin ba, d'akin nashi ya dawo ya zauna yana shan tea d'in suna woya da Ammin shi, bayan sun gama woyar ne ya koma bakin gadon shi ya zauna ranshi da jikin shi duk suna mamakin sauyawar Ummul hakan yasa gaba d'aya jikin shi yayi sanyi, ita kuwa Ummul bayan ta fito ta kimtsa har ta konta sai taji gaba d'aya d'akin nata ba dad'i yayi shiru, haka yasa ta mik'e ta nufi d'akin Hamman nata, sallama tayi cikin sanyi, a hankali ya amsa mata tare da bud'e mata hannayen shi ba musu ko wani gardama ta fad'a jikin shi tare da sauk'e ajiyan zuciya a jere a jere kamar wacce tasha kuka ta k'oshi, jin hakan yasa ya k'ara ruggumota a jikin shi a hankali yace, "Ummu na ina sonki". ido ta zuba mai tare da cewa, "Uhummmm". gyara zaman su yayi a kan gadon tare da shafa fuskarta ya kuma cewa, "duk duniya bani da kamarku". lumshe ido tayi tare da shafa sajenshi tace, "hahhhm nida waye? ". murmushin farin ciki yayi dan wannan wani ci gabane ace yau shida Ummul ne suke hira duk da ba amsa take bashiba sai dai tace Uhmmmm ko ahammm a hakan abin ya mishi dad'i gashi wai Ummul ke shafa wani sashi na jikin shi, ganin hakan yaci gaba da cewa, "Ammina da Usman da ke da Baby nan da zaki haifa min". "uhmmmmm". ta sake cemai, shiko jawota yayi suka konta suna fuskantar juna har lau hannun ta na kan fuskarshi, shi kuwa cusa hannun shi yayi cikin rigarta yana murza k'irjinta amman kuma bata hanashi ba saima hannun ta d'aya data saka ta kunce igiyar rigar baccin nata ta yadda k'irjinta ya fito fili, amman tak'i yarda su had'a ido sai k'irjinshi ta zubawa ido, ido ya lumshe cikin jin dad'i yace, "Ummul ina sonki, nima zaki soni ko? ". batayi manana ba sai lumshe idonta tayi, shiko mirginowa yayi ya k'ara shiga jikin ta a hankali yace, "Khairi kinsa wani abu kuwa wallah da takarduna zasu amfaneki da nabaki su kema ki zama Doctor Rabi'atu Hassan Umar, tunda na lura a fushin nan da akeyi dani a cikin laifukan nawa harda batun kara tunki da Abba ya hana a dalilina". bud'e idonta tayi a hankali tana kallon fuskarsa, shiko ruggumeta yayi ya d'agota ya d'aurata kan ruwan cikin sa ya d'an kaikace ta yadda basu matse cikin taba a hankali yace, "In kin haifi namiji duk sunan da kike so shi za'a saka, inko mace kika haifa duk sunan da nake so shi zan saka". hannu tasa tana shafa kanshi tace, "toh ko sunan Mustapha ka yarda in saka?". Murmushi yayi tare da laso lips nata yace, "Hmmmmm meyasa kikace ko sunan Mustapha ma na yarda?". a hankali tace, " babu ". kai ya juya cikin sanyi yace, "ai shima Mustapha d'an Uwana ne meyasa zank'i yarda, sharad'i d'aya ne kan sunan, ina sone ki sawa d'anmu sunan wanda kikafi so a duniyar nan baki d'aya in har shi mustapha kikafi so toh na yarda ai shima madadin k'ani yake a gareni, Khairi Mustapha da kike gani mutunci mukeyi sosai har aurenshi naje d'aurin aure". ido ta lumshe a hankali tace, "Kai waye kafi so a duniyar nan?". murmushi yayi a hankali ya zuba mata ido yana murza k'irjin ta da hannu bibbiyu cikin rad'a yace, "Ammina nafi so amman keda Usman ku nake sawa a Next of kind na a account na kune a wurin aikina ma keda Usman na saka". ya k'arishe maganar cikin rad'a sosai tare da cewa, "kar Baby na taji ba ita na saka a Next of kind tayi fushi da Daddyn ta". murmushi Ummul tayi dan ya bata dariya a hankali tace, "Hamma yaron dake cikin mamanshi kuma yana jin magana ne?". gira ya d'aga mata tare da cewa, "zaiji mana ". murmushi sukayi dukan su, farin ciki a zuciyar Umar kuwa baya fad'uwa bakin shi ya manne da nata harshen shi ya zirama ta a bakinta, ba zato ba tsammani yaji Ummul na kissing nashi, wayyo gaba d'aya Ummul ta gigitashi da kis d'aya tak sabida bata tab'ayi mishi hakan ba, duk ya susuce ya susutata, murya na rawa yace, "Khairi kin yarda na rab'i jikinki?". karo na forko da ta kasa cemai a a kenan sai rufe idonta tayi ta kasa magana sai k'ara shiga jikinshi takeyi, hakan ya bawa Hamma Umar damar d'ibar gara domin yau ita kanta Ummul tana taima ka mishi a harkar, haka ya bashi damar gamsuwa da ita ba musu, kuma yau Ummul bata iya furta mai kalaman da tasaba yi mishi ba in yana mu'amalantuwa da ita duk da dai har cikin ranta bawai tana jin tana sonshi bane, haka yayi ta murzata duk da cikin dake jikin ta, da kyer ya sararamata, sannan ya sake jawota sukaci gaba da hira duk da ba tanka mishi takeyi ba, a haka sukayi ta hira har zuwa k'arfe biyu na dere sannan ya kuma nuna mata cewar yana son k'ari, haka Ummul ta kasa hanashi ya murjeta son ranshi saida ya gamsu iya gamsuwa ya jawota jikin shi yana ta sa mata al'abarka ita ko tuni gajiya da zazzab'i mai zafi gaske ya fara rufeta lokaci d'aya ta fara karkarwa, jikin ta kamar uwata sai duk'unk'unewa takeyi a jikin shi ga zucuyarta dake harbawa da k'arfi kamar zata fashe, gaba d'aya Hamma kam ya rud'e k'aramin towel ya d'auko da d'an ruwan sanyi ya rink'a jik'awa yana goge mata jikinta har saida jikin yayi sanyi sannan ya bata magani tasha, lokaci d'aya jikinta ya sake ganin hakan ya jawota jikin shi, a take bacci ya saceta, shiko sai k'ara ruggumeta yayi yana kallon yadda d'an cikin ta ke motsi fuskarta kuwa tayi fari tas sai shek'i takeyi duk a wunin yau ta canza tayi fiyau, haka yayi ta kallonta har zuwa k'arfe 3 a lokacin ta farka ido ta zuba mai ganin yadda yake kallon ta, cikin baccin ta juya gareshi tasa hannu biyu ta ruggumo shi, murmushi yayi sannan ya gyara mata konciyar, sai can k'arfe 4 kuma ta sake farkawa nan ma har yanzu baiyi bacci ba kallon ta yakeyi kamar zai had'iye ta, nan ma juyi tayi a jikin shi cikin sanyi ta shafa sanjen shi har zuwa k'irjin shi a hankali ta sauk'o da hannun ta har kan mararshi cikin magagin baccin tace, "Hamma har yanzu bakayi bacci ba, me kake so ne? ". hannun ta ya rik'o a hankali yace, "Pakala nake so kuma naga kin gaji gashi baki da Lafiya ko zaki iya da buk'atuna?". a hankali tace, "Uhum". jawota yayi ya ruggume cikin jin dad'i yace, "Nagode Khairi Allah ya miki al'barka amman yanzu kiyi baccin ki sai na dawo masallaci sai ki bani kafi shayi tunda yanzu biyar ta kusa". kai kawai ta juya sannan taci gaba da baccin shikoh tashi yayi yaje yayi wonka sannan yazo ya d'anyi nafila ana kiran salla ya tafi massalaci, bayan ya had'a mata ruwan wonka ya kuma tasheta, itama wonkan tayi sannan tazo tayi salla ta d'an tab'a karatu zuwa k'arfe bakwai ta koma ta konta, shiko bakwai da rabi ya shigo gidan yana shiga ya lek'ata ganin tana bacci ya wuce kitchen kasan cewar yau Monday sauri sauri ya had'a musu breakfast sannan ya shirya musu komai kan dinning table, wonka yaje yayi a gaggauce yana fitowa k'ugunshi d'aure da towel ya nufi d'akin Ummul da nufin ya tasheta tazo taci abinci ya kuma bata magani, yana shiga ya wuce bakin gadon a hankali ya yaye blanket da ta rufe jikin ta, murmurs yayi ganin daga ita sai borgon duk zanin jikin ta d'in ya gudu hannu yasa ya shafo kirjin ta wanda hakan ya tayarmai da buk'atarsa, kawai sai ya rab'a gefen ta ya konta cikin sanyi ya fara lalubarta, koda ta bud'e ido batayi yunk'urin hanashi ba, haka ya murzata har saida ya samu gamsuwa sannan ya ciccib'e ta ya wuce da ita toilet nata, tare sukayi wonka, sannan suka fito d'akin shi ya koma ya shirya tsab sannan ya fito, koda ya fito parlour yayi mamakin ganin bata fitoba, dan haka ya wuce d'akinta yana shiga ya sameta sai rawan sanyi take kar-kar gaba d'aya zazzab'i mai zafi ya rufeta duk jikin ta kamar wuta, da sauri ya ruggumeta cikin tsananin k'auna da kulawa yace, "Ummu na sannu zazzab'in nan yana bani tsoro wallahi". ita dai ba magana sai hawaye da rawan sanyi ganin haka, yaje ya had'a mata tea sannan ya kwaso magungunan ta yazo ya bata, a Karo na forko kenan Ummul ta karb'i maganin tasha ba musu sannan ta shanye tea d'in ya kuma k'aro mata tea d'in tashanye tsab, sannan ya kontar da ita ya d'an rufe mata jikin ta kis ya manna mata a goshin ta sannan ya shafa fuskarta a hankali ya zaro babbar woyarshi ya ajiye mata gefen pillown ta cikin kula yace, "Ummu na fitar nan ta zame min dole ne badon hakaba da bazan fita in barki baki da lafiya ba amman karki damu yanzu zan dawo bazan dad'eba, ga wayata na ajiye miki zan fita da k'aramar dan zan kiraki inji ya jikin". kai ta gyad'a mai, jiki a mace ya juya ya fita koda yaje dinning table d'in ya kasa cin komai haka ya fita, tana jinshi ya rufeta ta baya tanaji har ya tashi motarsa sai kuma taji ya kashe motar, jim kad'an sai ta kuma jin ya bud'e k'ofar parlour nasu ya shigo, tana ganin shi yazo ya tsaya kanta yana ta kallon ta, sai kuma ya shafa fuskarta ya fita, a karo na uku ya kuma dawowa ya zauna gefenta a hankali yace, "Ummu ina sonki ciwonki na tayar min da hankali". kai ta juya a hankali tace, "meyasa kakeke ta zirga-zirga ka tafi mana ko meyasa kake kallo na?". mik'ewa yayi ya shafa fuskarta cikin sanyi yace, "wallahi kinmin kyaune yau d'in bana son d'auke idanuna a kanki". murmushi tayi tace, "Hamma kaima sai kaga yadda kayi kyau wallahi kamar oggo". murmushi yayi yana fita tare da cewa, "ai yau nake oggon Ummu yayan Usmanu d'an Ammi da baban Ibrahim jikan Hajjajo da Inna dan gatan Abba da Daddy da Nenne yayan Adam da Sadik da Halima da Aliyu". binshi tayi da kallon har ya fita, yana fita fita ya shiga motarsa ya tafi kai tsaye asibitin su ya nufa jikin shi a mace gaba d'aya ya rasa sukuni. A gida kuwa Usman ne ya kalli Adam dake gefen shi cikin sanyi yace, "Adam zan tafi damaturu zanje naga Hamma na tun shekaran jiya bamuga junaba yanzu zan tafi". cikin sanyi Adam yace, "Ni dai bazani ba sai Hamma ya huce ". haka yayi shirin tsab ya fito ya sallami su Nenne da Hajjajo sannan ya fito ya bud'e motarshi ya shiga. Ita Kuwa Ummul Hamma Umar na fita wani irin zazzab'i mai zafi ya rufeta a take taji wani irin yunk'u ri... .. *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 2⃣9⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *JAMU NA HOLARE BALD'E* *Y*unk'uri tayi cikin gala baita dan aman da takeyi tun bayan fitan Hamma Umar d'in nata amai d'in take tayi har jikin ta na rawa gaba d'aya ta gala baita intayi yunk'uri sai taji zuciyarya taja ta tsinke ras gaban ta na fad'uwa, a wahalce ta tashi cikin layi da rawan sanyin zazzab'in dake bibiyarta tattare wurin da tayi amai d'in tayi ta goge filin sannan ta kashe A/C dan sanyin da taji ya rufe ta sannan ta sassake labulayen windows nata har ta konta ta kuma mik'ewa da kyar taje ta rufe k'ofar bedroom nata d'in sannan ta dawo ta konta ta gudundune cikin blanket tana jin yadda d'an cikin ta ya tattare ya dawo k'asan k'ahon zucuyarta, yayi cus ya dena motsi, itako lokaci d'aya wani irin fargaba da razani da tsoro mai tsanani ya rufeta haka kawai taji jikinta kamar an rufamata d'anyen fata duk zuciyarta ta raunata a hakan cikin kad'uwa da ciwon wani irin bacci ya saceta. Shiko Hamma Umar da yake Federal Medical center duk da dama ba kullum yake zuwaba sai akwai imergency dan shi aikin shi duba govnr ne, so yauma imergency ne ya kawoshi, aiki sukayi cikin sauk'i shida abakin shi Dr Bashir Ibrahim, k'arfe takwas da mintu hamsin da biyu suka fito kai tsaye office nasu suka nufa dan office en a jere suke, suna tafiya Dr Ibrahim na bin bayan Dr Umar Ibrahim Umar d'in da ido ganin gaba d'aya yau komai yake jikin shi a mace duk motsin da zaiyi sai yace, "Sauri nake zan Koma gidana Ummul bata da Lafiya, kuma inaso muje gida nayi kewar Usman". murmushi Dr Bashir yayi cikin sanyi yace, "Dr Umar anya ko kana son kanka kamar yadda kake son Usman da Ammin ku da Ummul? ". kai ya gyad'a mai a hankali yace, "ina jin tausayin su ne". a dai-dai tsakiyar farfajiyar asibitin suka tsaya sukayi shiru suna kallon juna cikin kasa kunnuwa yayin da gaba d'aya illajirin mutanen dake wurin sukayi cirko-cirko suna baza ido da kasa kunne. Ta kasance yau Monday 27 February 2014 ranar da mutanen garin damaturu bazasu tab'a mantashi a kund'in tarihin rayuwar su da garin ba musamman zuriyar Alhaji Umar Shina k'arfe tara dai-dai na safiyar wannan rana *BOKO HARAM* sukayiwa garin Damaturun diran mikiya inda sukayiwa garin zobe wanda forkon shigarsu ta layin uguwarsu Hamma Umar suka shigo wato gidan Ummul kenan dake nyanya line dake gujba road damaturu, yayin da suna shiga suka rink'a sake bomb da harbe-harbe duk wanda suka kama suyi mishi kisan gillah, lokaci d'aya garin damaturu ya hargitse ya birkice sai gudu akeyi ana neman tsiratar da rai, 😭😭😭suko tsinannun Allah ta ala sai bi suke gida diga suna kashe Al'Ummar Annabi sannan sun datse hanyoyin shiga garin duk motor da tazo su tsare su kashe a bakin mashigar garin, a haka har suka kusan to gidan Hamma Umar. Shiko Hamma Umar a asibitin inda suke tsaye a take saiga motoci da mata maza manya da yara suna shigowa cikin asibitin da gudu dan b'oye rayukan kansu, abin mamaki sai Hamma Umar yaga gaba d'aya mafi akasarin masu shigowa asibitin yan uguwarsu ce duk mak'o tansu ne kab a cike cikin tsoro da firgici, ya kutsa cikin su, Dr Bashir ne ya rink'a binshi a baya yana cewa, "Dr Umar ina zaka je Dr tsaya mana". hannun shi ya fizge cikin tashin hankali da firgici yace, "Ummul! Ummul! Ummul! Bashir banga Ummul ba bashir kalli nan duk mak'otanmu ne gashi sun gudo banga Ummul a cikin suba". sai kuma ya rink'a kutsawa cikin mak'otan nasu yana tabbayarsu d'aya bayan d'aya, " ina Ummul kunga Ummul ne?". amman duk sai suce basu ganta ba, hakan yasa cikin tsoro da fargaba yayi parking lot nasu motarshi ya nufa, Dr Bashir d'in ne da sauran mak'otan nasu suka bi bayanshi cikin tarin tsoro suka rik'eshi a firgice Dr Bashir yace, "Dr Umar ka nitsu ina zaka je kana ga wad'anda suke canma sun gudo nan kaikuma kace zaka koma can plxx Dr Umar karka koma". ture Dr Bashir yayi cikin rawan jiki da murya yace, "Ummul bata da lafiya ga tsohon ciki bazata iya guduba kuma kasan kashe masu ciki sukeyi plxx Dr Bashir barni inje". Dr Bashir kam kai ya rink'a juyawa rik'e da hannun Hamma Umar d'in, mak'ocinsa ne ya matsoshi cikin rud'u yace, "Dr karka koma uguwarmu wallahi suna can suna ta kashe mutane". hannun shi ya fizge da k'arfi ya shiga motarshi yana cewa, "kace ana can anata kashe mutane Ummul kuma na can sannan kuce kar naje". yana kaiwa nan ya figi motar cikin firgici ya nufi uguwar tasu, yana zuwa ya samu uguwar a hargitse duk ko ina sai jini da gawarwakin mutane gaba d'aya jikin shi sai rawa yakeyi cikin tausayawa rayuwar mutan k'asarmu ta Nigeria ya rink'a ratsawa gefe-gefe yana kaucewa gawakin har ya samu ya isa cikin gidan nashi bai had'u da suba, parking yayi ya fito da gudu ya nufi kan y'ar barandar da zata sadashi da k'ofar shiga parlour nasu, key yasa ya bud'e k'ofar ya shiga hannun shi rik'e da woyarshi yana ta kiran Usman tun a cikin mota amman har yanzu da yake kiranshi a karona 13 bai d'aga ba har kiran ya katse, ganin haka ya zira woyar a aljihun shi ya k'arisa bakin k'ofar bedroom d'in Ummul d'in, turawa yayi jin k'ofar a rufe yasa cikin tashin hankali ya fara magana da d'an buga k'ofar yana cewa, "Ummu ! Ummu! Ummuna ina kike? Ummu na kizo ki bud'e min k'ofa Hamman kine". ita ko Ummul wacce tun sanda harbe-harben Boko Haram d'in suka tasheta a baccin daya saceta gaba d'aya jikin ta ya fara b'ari kar-kar d'an cikin ta ya k'ara komawa saman k'irjin ta numfashin ta ya rink'a korar juna sai wani irin zufa ke tsatstsafo mata tako ina, ta kasa ko motsi dan fargaba da bugawar zuciya tana jin yadda mak'onta su ke guduwa amman ta kasa tabuk'a komai, sai yanzu da taji muryar Hamman nata ne ta yunk'ura cikin rawan jiki taje ta bud'e k'ofar, yana ganin ta ya bud'e mata hannunshi, da sauri ta fad'a jikin shi, wani irin ruggume juna sukayi wanda basu taba jiyawa junan su irin wanan ruggumar ba, Hamma Umar kam da k'arfi ya matseta a jikinshi kamar wanda yaga mutuwa na biye da ita, itama da iya k'arfin ta tasa hannunta ta ruggumeshi murya na rawa tace, "Hamma mu buya". kai ya jinjina cikin rawan murya ya tallabo konta ido ya tsura mata cikin nata idanun yace, "Ummu naji tsoro karsu kashe min ke shiyasa na dawo Ummu na ina sonki inajin tsoron rabuwa dake zomu fita mu tafi asibitinmu yanzu na shigo layin nan basa nan sun gudu bayan sun kakkashe mana yan uwa musulmai". sai hawaye car-car a idanu su, a hakan ya jawo hannun ta ko mayafi basu tuna d'aukaba tunda yanaga mota zasu shiga, janta yake tana binshi a baya gaba d'aya jikin ta na rawa bata da kuzari ko kad'an a haka har sunzo k'ofar fita parlour sai kuma duk suka juya suna kallon cikin gidan nasu, sai ya kuma kamo hannun ta suka fito woje, taku d'aya sukayi a na biyu suka tsaya cak a tsakiyar barandar tasu, jikin Ummul rawa yakeyi har d'an cikin ta na yin k'asan maranta kuka ta saki cikin rawan murya ta nuna zugan Boko Haram da suka cika harabar gidan nasu wanda sunkai su 8 gaba d'ayan su rik'e da bindigogi da wuk'ak'e cikin tsoro ta k'ara rik'e hannun Hamma Umar d'in murya na rawa tace, "Wayyo Allah na Hamma na nashiga uku zasu kashemu". juyowa yayi cikin karfin hali ya kalleta murya a carke yace, "Ummu na Insha Allah zan kareki bazasu kashe min keba zan kareki keda d'anna Allah yana tare damu". suna cikin haka suka k'araso gabansu cikin rashin imani d'aya daga cikin su yace, "Kai meya dawo da kai? bayan kana ganin kowa yana guduwa kai kuma yanzu muna ganin ka ka dawo munga shigowar ka cikin gidan shine muka biyoka muje meya dawo da kai?". Allah sarki Hamma Umar cikin jarumta yace, "Matata na dawo in d'auka". harara suka watsa mishi cikin izzati sukace, "ita bata da k'afane da bazata gudu ba"?. cikin rashin karaya yace, "Bata da lafiya ne bazata iya guduba"". jin haka suka matso gaban su cikin rashin imani suka fizgo Hamma Umar d'in suka shak'e wuyanshi suna cewa, "Ai gwara daka dawo kaga zamu samu mu kashe ka mu rege arna". ita kam Ummul tunda suka fuzgo shi ta saki k'ara mai k'arfi ta matso kusa dasu cikin bushewar zuciya ta rink'a kaiwa wanda ya shak'eshin duka tana, "ka sake shi mugaye kawai azzalumai kuku bashi raine da zakuce zaku kasheshi mugaye Hamma na ba arne bane kune arna kafuran Allah ta ala". shiko Hamma Umar da k'afafunshi ya rink'a harbin na gabanshi da suketa dariyar mugun ta naushin su yakeyi sosai har ya kada uku daga cikin su, ganin hakan wand'a ya shak'enshi ya sakeshi cikin zalumci ya kalli sauran yace, "Ku kasheshi". nan sukayi kanshi gaba d'ayan su, Ummul kuwa kuka ta farayi da burburwa tana neman agajin Allah, shiko Hamma Umar kamar wasa ya rink'a dambe dasu Allah cikin ukonsa sai gashi ya jikkatasu duk da taron dengin da sukayi mishi, bai bar kare kanshi ba, ganin haka babban nasu yace, "ku sake shi". ba musu suka sake shi, hakan yasa Ummul ta taso da sauri tazo kanshi zata fad'a jikin shi sai babban nasu ya rik'eta ya bank'are hannayen ta cikin ta ya fito fili, K'ara ta saki da k'arfi tana cewa, "Hamma Umar". shima Umar cikin razani ya taso yayi kanta, dan sauri babban nasu yace, "wato Kai jarumi mai k'arfi ko, toh mun fasa bazamu kasheka ba, a gaban ka zamu kashe matar taka mu fasa cikin nata mucire abinda yake ciki, kai kuma zaka zama ganimar yak'inmu zamu musuluntar da kai kaima ka zama mayak'i d'an Boko Haram ". yana gama fad'in haka yace kai zo ka farka cikin nata, da sauri wanda yake bayan Hamma Umar d'in ya zaro wuk'a, ganin haka cikin rawan jiki da murya Hamma Umar ya sake guiwawin shi k'asa yana rawan murya yace, "Kuji tsoron Allah ku sani Allah na ganin ku mutuwa kuma tana matakata ko wanne mai rai sai ya d'and'ane ta, ku dena kafurtani *Ni Musulmi ne* karku kashe min mata karku cutar min da d'ana". dariyar mugunta suka saki baki d'ayan su suna k'ara bank'are Ummul ganin haka Hamma Umar d'in ya yunk'ura da k'arfi zai jawota, a dai-dai lokacin wanda yake bayan shi ya zaro wuk'a da nufin farka cikin Ummul, cikin rashin imani da tsoron Allah yasa wuk'ar a wuyan Hamma Umar a gaban Ummul suka d'anneshi sukayi mishi yankan rago 😭😭😭😭😭, Allahu Akbar Hamma Umar Allah sarki Ummul cikin wani irin firgita da gigicewa da fita hankalin ta tasaki wani irin k'ara mai firgatar da duk wani bani Adam dake wurin, juyowa tayi da k'arfi ta rink'a dukan wanda ya rik'etan dukanshi take a haukace tana, "Wayyo Allah na wayyo Hamma na Wayyoni Ummul naga ta kaina mugaye azzalumai Allah ya isa nima ku kasheni ku kasheni nace ku kasheni ko". dariya sukasa a mugunce wanda take dukan ya tureta ta zauna k'asa dirsham yace, "ai bama kashe mata sai maza". shi kuma wanda ya yanka Hamma Umar d'in yana rik'e da kafad'un Hamma Umar d'in k'ara sa wuk'an yayi a kan wuyan nashi zai k'ara yan kawan a dai-dai lokacin kuma jiragen helkobta na sojoji dake shawag'i a fad'in garin damaturun suka gilma ta kan gidan su Hamma Umar d'in kuma sun ga halin da suke ciki ganin haka boka Haram d'in suka hankad'o matashi a kanta sannan suka juya a guje suna fita, a gigice ta matsoshi cikin tsananin ihu da rud'ewa, shiko Hamma Umar cikin azaba da fizge-fizge dan jinin shi dake ta zuba amman da yake basu iso mak'ok'oron maganarshi ba a hakan yasa hannu cikin wahala murya can k'asa numfashi in ya fita baya dawowa yace, "Ummu na ki dena kuka matso matso in mutu a jikin ki Ummu na na yafe miki duk abinda kikayi min". sai kuma ya rink'a mimmik'e k'afafunshi jikin shi duk na rawa jinin shi nata zuba, ita kuwa Ummul matsoshin ta kumayi kanshi ta d'ago ta d'ora kan cikin ta cikin kuka tace, "Baza ka mutuba Hamma karka mutu ka rufamin asiri". a wahalce cikin magagin fitar rai murya na caccarkewa can k'asa yake, "Ummu karki sha komai kibar cikina ki haifamin shi, Ummu na kice kina sona". K'ara ruggume shi tayi a gigice tace, "Hamma bazan sha komai ba Hamma na ina sonka ina sonka Hamma na". sai kuma tayi shiru jin yadda ya had'a tafin hannun ta da nashi ya damk'e da k'arfe sai kuma yayi murmushi cikin sanyi da tafiyar numfashi da kyer take jin abin da yake fad'a, "Alhamdulillah Ummu". sai ya kuma saketa a hankali yace, "Am..! Amm...! Ammina Us...! U,,, Usman". sai kuma yayi mik'a a hankali yace, "LA'ilaha'illahu MuhammadS'A'W". daga nan sai Ummul ta jishi yayi shiru ya sake ko ina, nauyin shi ya k'aru fuskarshi tayi haske sai d'umin jininshi da takeji yana ratsa fatar cikin ta har zuwa cinyoyin ta, Daga nan lokacin rayuwar Ummul ko ta shiga wani yanayi kukan da takeyi ya tsaya cak, sai ta k'ara ruggumoshi a jikinta ta rik'eshi gam, ta kasa kukan sai tayi zuru da idanun ta, tana cikin haka taji motocin sojoji kai tsaye gidan suka shiga dan sojojin dake cikin jiragen ne sukayi musu umarni su shiga, suna shiga kai tsaye gaban ta suka je, babban sun ne ya durk'usa gabanta a hankali yace, "Sannu baiwar Allah me sunan ki". shiru batayi magana ba bata kalleshi ba idonta na kan wuyan Hamman ta da fuskarshi, a karo na uku sojan yace, "baiwar Allah kiyi magana mana musan taimakon da zamuyi miki me sunan ki? me sunan mamacin? ku yan inane ina za, a samu yan uwanku? ". duk bata amsa mishi ba, ganin haka yasa hannu zai jawo gawar Hamma Umar dake jikinta sai ta k'amk'ameshi da k'arfi, abu kamar wasa da kyer suka kwaceshi a jikinta, yana karbar shin ne I'd card 💳 d'in Hamma Umar d'in ya fad'o daga aljihun sa, ganin I'd card d'in ne yasa ya d'agoshi ya duba cikin mamaki yace, "Dr Umar Ibrahim Umar shine doctor Alhj Ibrahim Gaidam govnor jihar nan". jin haka yasa da sauri ya ruggume gawar Hamma Umar d'in cikin sanyin jiki yacewa sauran, " ku taho da ita mu tafi gidan govnr dasu". Haka kuwa akayi kai tsaye suka wuce g Government house dasu, ana shiga dasu kai tsaye har parlour Alhj Ibrahim gaidam suka wuce, mutuwar da ta girgiza illahirin mutanen gidan domin ko kwana biyu baiyi ba da zuwanshi, kuka cur-cur suka rink'ayi anan cikin gidan govnr kuwa akwai abokin Mustapha ganin Ummul yasa ya kira Mustapha ya shaida mishi, suna nan a zaune Ummul bata gane komai tasa gawan Hamman ta a gaba bata kallon kowa, Shi kuwa Mustapha lokacin da aka gaya mishi rasuwar yana gidan mahaifinshi dake bayan government house d'in cikin kid'ima ya d'auko Umman shi suka taho tare, suna shiga parlour Umman Mustapha ta matso jikin Ummul a hankali ta kamota, ita kuwa Ummul bata kalleta ba sai k'ara rik'e hannu Hamman nata tayi, a hakan taji muryar Mustapha tabbas taji muryarsa amman bata gane me yake fad'i ba, daga gidan govnr Alhj Ibrahim Gaidam d'in ya bada umarni a d'auki gawar Umar d'in a kaita gidan sarkin garin nasu wato Mai martaba Alhj Umar Bubaram ibin Wuriwa Bauya, haka kuwa akayi aka kwashesu aka nufi gidan sarkin dasu inda suna zuwa aka shigar da gawar sannan aka d'auki motacin sojoji guda 5 aka had'asu da motor Mustapha wanda Umman shi ke zaune a baya tana ruggume da Ummul wacce ta zazzaro ido tun sanda aka kwace gawar a hannun ta, a haka suka nufi patiskum bayan sun biya asibiti sun sanar nan ma Dr bashir da sauran abokansu suka mara musu baya a zaton su a can za, a sallaceshi, suna isa cikin pataskum d'in kai tsaye gidan su Abba suka nufa. A gidan kuwa tunda gari ya waye basu da wani nitsuwa kowa jiki a mace, har zuwa 11 na rana Adam dake konce a parlour Hajjajo cikin kasala ya mik'e ya fita ba tare da yayi mata magana ba, itama Hajjajo tana ganin shi amman batayi mishi magana ba, shiko Adam parlour Nenne ya lek'a inda ya samu Sadik na konce kan 3str Aliyu na zaune gefen Nenne amman su duk sunyi shiru, koda ya l'ek'a sun ganshi ya gansu amman ba wanda yayi magana, parlour su ya wuce yana zuwa ya samu Usman na zaune a tsakiyar parlour sai rawan sanyi yake, da sauri ya matso gaban shi baki na rawa yace, "Hah Usman baka tafi damaturun bane? baka da lafiya ne?". cikin rawan sanyi da mutuwar jiki yace, "Adam ban tafiba Adam bazan iya tuk'iba sanyi nakeji har cikin hanjina zuciyata na bugawa". cikin fargaba yace, "Usman baka da lafiya ne?". kai ya rink'a juya mishi a hankali yace, "Lafiyata lau amman bana jin dad'in yanayin yau kuma sanyi nakeji ina son inje gum Hamma na dan Allah Adam muje ka tuk'a motor muje gun Hamma". ba musu yace, " toh biri in d'auko hula mu tafi". "Yauwa to kayi sauri mu tafi". "To" yace sannan ya shiga cikin d'akin da nufin d'auko hular, A dai-dai lokacin kuma motacin sojojin suka tsaya a k'ofar gidan, suna tsayuwa Umman Mustapha ta kamo Ummul sukayi cikin gida, suma sojojin sukabi bayan su amman su sai suka tsaya a harabar gidan gamida cewa Ummun Mustapha in sun shiga tace ana sallama da mai gidan, shiko Mustapha gidan Ammin su Hamma Umar ya wuce dan yasan gidan nata. Ummun Mustapha na tallab'e da Ummul suka shiga cikin gidan a tsakiyar gidan ta tsaya a hankali tace, "Assalamu alaikum ". sai kuma tayi shiru a parlour Nenne Kuwa cikin bugawar zuciya Nenne ta amsa mata tare da cewa, " ku iso". Sadik Kuma da Aliyu mik'ewa sukayi da nufin zasu fita su basu wuri, Aliyu ne a gaba yana fita Sadik na binshi a baya, Umman Mustaphan kuwa kallon Ummul tayi a hankali tace, "Mu shiga ko Ummul". jin sunan Ummul ne Aliyu ya juyo da sauri, sai kuma ya zaro ido cikin rawan jiki ganin gaba d'aya rigar jikin Ummul d'in tana jik'e jilak da jini , a razane yayi wani irin k'ara, sai gashi ya fad'a k'asa a sume, k'aran da Aliyu yayi ne yaja hankalin mutanen gidan baki d'aya a guje suka firfito, Abba na fitowa ya kalli Aliyu a sume sannan yaga Ummul a tsaye jini na d'iga shima sai ya fad'i k'asa a sume, Adam kuwa yana fitowa Abban yaje ya kamoshi dan shi baima lura da Ummul d'in ba, Nenne Kuwa gaba d'aya jikin ta rawa yake kar-kar kamar mazari sai zufa ke zubo mata, Ya Sadik kuwa tsayuwa yayi tamkar an dasashi, ita kuwa Ummul sai yanzu ta d'ago kanta ta kalli ya Sadik d'in nata a hankali tayi taku taje gaban shi tana zuwa ta fad'a jikin shi, Sadik daya gama sakewa shima sai zamewa yayi ya zauna k'asa dirsham yana tallabe da ita, ita kuwa Ummul kifuwa tayi jikin ya Sadik din tana jizon lips d'inta da zuwa yanzu sun kuburo sintim sintim, cikin karfin hali Nenne tace, "Baiwar Allah make faruwa ina Umar?". shiru Umman tayi sannan ta kamo hannun Nenne suka zauna a kan kujerun dake wurin sannan ta kalli Sadik a hankali tace, "Sadik kawo Ummul nan". kai ya juya cikin kuka yace, "bazan iya ba". kukan Sadik yasa Nenne ma ta kife Kai ta fara kuka Adam ma kukan ya fara cikin tashin hankali yace, "Dan Allah ki gaya mana meke faruwa Ummul ina Hamma Umar ?". cikin sanyi Umman Mustapha tace, "Kullu nafsin za'ikatil maut". sannan ta dafa kafad'un Nenne taci gaba da cewa, "Lallai Umar namune amman Allah ne ya bamushi kuma ya fimu sonshi yau kuma ya kira Umar, Umar ya amsa kiran mahaliccin mu". gaba d'aya a tare suka mik'e cikin razani da kad'uwa, Usman kuma dake tsaye gefen Adam, kai ya rink'a juyawa da k'arfi sai kuma ya kalli Ummul dake jik'e da jini gabanta yaje ya durk'usa cikin razani yace, "Ummul gaya min inji a bakinki shi zaisa na yarda Ummul jinin waye a jikin ki? Ummul gaya min ina kika barmi d'an Uwana Ummul wannan jinin waye a jikin ki? ". Ba magana sai zamowa tayi daga jikin Ya Sadik ta fad'a jikin Usman d'in a hankali tasa hannu ta shafo jinin a hankali ta gyada mishi kai, cikin wani irin yanayi Usman ya mik'e tsaye sai kuma ya,........ *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 3⃣0⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Wannan littafi nawa gaba d'ayan shi sadaukarwane wa Hamma Umar, Dr Umar Ibrahim Umar shuwa Allah ya jik'anka da rahama😭😭😭* *Alhamdulillah Da forko zanyi amfani da wannan damar na mik'a sak'on godiya ta a gareku yan uwana Musulmai bayan na godewa mahaliccina tabbas lallai musulmi dan uwan musulmi ne kuma akwai soyayya da tausayin juna da k'auna a tsakanin mu musulmai hak'ik'a naga hakan kuma lallai in abu mara dadi ya samu dayanmu kamar ya samemu ne baki d'aya kamar yadda mutuwar Hamma Umar ta ratsa zuk'atanmu baki d'aya nida kaina Aysha ban san adadin addu'oin da bawan Allah nan ya samuba a cikin kwana biyun nan fatana Allah ya amsa addu'oinku gareshi Usman Ammi da Ummul suna godiya a gareku Ummul kuma tana neman addu'arku dan tun shekaran jiya bata da lafiya saka makon abun da ya zame mata sabo Ummu na Allah ya baki lfy🤝😍😘* *Abu na biyu ina baiwa masoya na hak'uri daga jiya da daddare zasuga suna magana bana amsa musu to na canza number ne sakamon yawan da Jama,a sukamin duk ta inda na lek'a kafafen yanar gizo-gizo sai naga sak'on ni bila adadin hakan yasa dole na canza number dan samun sauk'i toh dan Allah duk wacce taga tayi mgn ba amsa toh na canza number ne ngd matuka Allah bar zumunci da k'auna sisters bada ku na gajiba da bada amsa na gaji amman ku kam ana mugun tare domin kun zamani na zamma ku na godewa Allah daya bani ku masoyana tabbas jama'a rahamace Allah ne yamin wannan rahamar kuma ngdwa Allah na Alhamdulillah* *Y*a rink'a juya kai yana b'ari kar-kar kamar mai farfad'iya wani irin zufa ya keto mai daga tsakiyar kanshi har kan d'an babbar yatsar k'afarshi hatta cikin gashin kanshi sai d'igowa yake tol-tol, Hajjajo kuwa wacce tun ihun da Aliyu yayi ta fito amman ganin Abba a sume Aliyu a sume ga Ummul jiki duk jini, a take sai jijiyoyin ta suka sassake k'afafun ta suka kasa rik'e ta jiri ya rufeta cikin tashin hankali ta fad'i k'asa dirsham hawaye na bin fuskarta ta kasa tashi sai yanzu ta mik'e da kyar ganin halin da Usman ya shiga, tana xuwa ta kamo hannun shi tana k'ok'arin zaunar dashi amman ina sai taji jikin shi kamar an dasashi ganin haka cikin muryar kuka tace, "Usmanu! Usmanu! Usmanu ! ka ambaci Allah shi zai kawo mana agaji Usmanu kar kabar zuciyarka ta mance da Allah Usmanu wannan shine jarrabawarmu a wannan shekara a wannan wata a wannan rana muyi rashi mai girma ban sani ba waya kashe mana Umar". sai kuma ta k'ara rik'o hannun Usman d'in sannan cikin kuka ta kalli Adam dake yayyafawa Abba da Aliyu ruwa, a firgice Aliyu ya farfad'o cikin k'ara tare da rarumo Sadik dake gefen shi, karan da Aliyu yayi ne yayi dai-dai da farfad'owar Abba a razane ya mik'e dai-dai lokacin kuma sojojin dake harabar gidan suka shigo dan jin k'aran da Aliyu keyi, suna shiga Usman suka kama suka rik'e sabida ganin yadda yake tsaye, zau nar dashi suke k'ok'arin ya, cikin hard'ewar harce ya janye hannayen shi gaban Abba yaje ya tsaya hannun Abba ya kamo ya rik'e harce a nad'e maganarsa bata fita sosai kuma yadda bugun zuciyarshi tayi k'asa haka muryarshi numfashi a cushe ya nuna Ummul dake zaune ta zama mutum mutumi sai ida nun ta da sukayi jazir tamkar rushi sai lips nata da suka kumbura, a hankali yace, "A..! Ab...! Abb!... Abba wai jinin Hamma nane a jikin Ummul Abba kace ta gaya ma inda ta barmin d'an uwana Abba kalli matar nan wai cewa take d'an Uwana ya resu Abba wai Hamma fa suke cewa ya rasu". kife kai Abba yayi tamkar yaro ya rink'a kuka yana durk'ushe a gaban mahaifiyarshi, Aliyu kuwa kuka yakeyi da shid'ewa Nenne ma kuka takeyi da tsananin k'una ya Sadik kuwa kanshi ya rink'a murzawa yana kuka cur-cur Adam kuwa ruggumo Usman yayi yana kuka tankar ranshi zai fita, Umman Mustapha ma tuni kukan take, ganin haka sojojin suka kama Abba suma kansu kuka suke dan tausayawa rayuwar wannan family, cikin hikima sukayi wa Abba bayani, suka k'ara da cewa, "yanzu haka gawarshi tana gidan sarki ya kamata kuje ayi mishi sutura". Abba jikin shi sai rawa yake cikin kuka yace , "Mu tafi". juyawa sukayi har zasu fita Adam yaga yadda Usman yake tafiya numbfashin sa na yankewa ganin haka ya kamoshi da sauri a cikin kuka yace, "Usman ka zauna a gida Abba kace Usman karya je". Abba ya bud'i baki zaiyi Magna kenan Usman d'in ya d'ago ida nunshi da suka koma tamkar zasuyi aman wuta murya a nad'e yace, "Gun Hamma na kuke cewa kar naje idan banje gunshi ba ina zan shiga a duniyar nan wai yau ni kuke cewa kar naje gun d'an Uwana idan banjeba me zanyi". daga jin Maganar Usman an san baya hayyacin sa, haka yasa Adam ya rik'eshi suka shiga motocin sannan sojojin suyi gaba suko suka bisu a baya dan an hana zirga-zirga a garin suma dan da sojojin ne, Mustapha kuwa kai tsaye gida su Ammi ya nufa dan yasan gidan sun tab'a zuwa shida Hamma Umar d'in. Ammi kuwa tunda garin wannan ranar ya waye ta kasa yin komai gaba d'aya jikin ta a mace yake, a haka ta jawo radio ta kunna wanda yayi dai-dai da saka harbe-harben da yan BH sukayi a garin na damaturu sannan mai bayanin yaci gaba da fad'in uguwannin da suka fara shiga da kuma irin b'arnanr da sukayi, jin an kira uguwarsu Hamma Umar ba k'aramin tashin hankali da firgici ya sawa Ammi ba a take taji wani irin sanyi yana ratsata har cikin hanjin cikinta tsoro mai tsanani ya rufeta ido cike da k'ollah tib ta kalli mahaigiyarta cikin muryar kuka tace, "Inna ta uguwar su Farouq suka fara shiga Inna kinji sunfa kakkashe mutane". Itama Inna gaba d'aya jikin ta rawa yake cikin hargitsi tace, "Kira min wayar Umarun kira minshi maza Amina". jiki na rawa tayi ta kiran Hamma Umar d'in amman tuni abinda Ammi bata saniba an kashe mata d'anta, ganin Umar baya d'aga woyar sai kukanta ya k'aru sai kuma ta rink'a kiran Usman ina shima baya d'agawa hakan yasa hankalin ta ya tashi ta rink'a kiran mutanen gidan Abban amman duk basa d'agawa haka yasa ta koma ta zauna dirsham kan taburma a gaban Innarta d'in ta zauna kenan, Mustapha yayi sallama, shi kuwa Mustapha ganin tana kuka sai yayi zaton taji batun rasuwar Umar d'in sai ya tsuguna gefenta cikin kuka kamar yaro yace, "Ammi kiyi hak'uri hak'ik'a munyi rashi mai zafi amman Hamma Umar yafi but'atar addu'armu a kan kuka Addu'a zakiyi mishin Insha Allah muna zatama mai rahama Allah ya karb'i shahadarsa". Ita kam Ammi tunda taga Mustapha jikin ta ya rink'a b'ari kar-kar ta kasa tashi amman jin ya ambaci Hamma Umar yasa ta mik'e da sauri cikin razani a kid'ime zanin ta ta rink'a d'aurawa tana kuncewa tana sake d'aurawa sai karkarwa takeyi ganin haka cikin kuka Inna ta kamota ta rik'e tana cewa, "Innalillahi WA innailaihi rajiun". haka ta rink'a maimatawa har akayi sa'a itama Ammi cikin kukan daya kufce mata ta rink'a cewa, "LA haulawala k'uwta illabillahi aliyul azim hasbunallahuwani'imam wakil Allahu Akbar Allah Akbar innalillahiwa Inna ilaihirajiun Allah mai girma yau kuma da k'unar dana wayi gari kenan Mustapha yau kuma Boko Haram sun yanke min naman jikina kenan Mustapha ina Usman Mustapha Usman yana cikin wanne irin hali?". sai kuma ta kife kanta kan ciyar Innarta ta saki wani irin kuka mai cike da k'unci a zuciya, itama Inna sai kuka shima Mustapha ya kasa barin kukan, a haka Uncle ya shigo ya samesu wanda dama Abba ne ya kirashi ya gaya mishi, abin tausayi shima Uncle sai yasa yar uwarshi a gaba suna kuka tamkar yara Ammi kam kuka take har numfashin ta na tafiya, a hakan Uncle ya daukosu ya kawosu gidan Abban sannan shida Mustapha kuma da sauran abokan Hamma Umar dana ya Usman da abokan Adam Sadik da abokan Abba duk suka d'ugguma damaturun, suko Inna da Ammi suka wuce cikin gidan. A damaturu kuwa suna isa suka samu ana shirin yiwa mamacin wonka suna shiga Usman ya wuce kai tsaye inda yaga an mik'e gawar a shimfid'e ta a k'asa Adam ma da Abba da Sadik da Aliyu gaba d'aya sai sukasa gawar a tsakiyan su, shiko Usman hannu yasa ya d'ago gawar fuskar ya tsurawa ido cikin wani irin yanayi mafi rauni da muni ya rink'a kallon wuyanshi da aka yanka, ruggume gawar yayi da k'arfi, a hankali ya rink'a juya kanshi yana wani irin numfashi Adam kuwa kuka yake kukan tausayin Usman Sadik ma kukan yake Aliyu Kuwa a k'asa ya kife kanshi yana kuka, Shiko Usman cikin hard'ewar murya da juya kai yace, "Sun cuceni sun cuci rayuwata sun rabani da mutun mafi soyuwa a gareni ina ma ina wurin in fanshi ran Hamma na da nawa ran Ammi sun cuceki sun kashe miki lafiyayyen d'anki suka bar miki ni wanda zama danima larurace". sai kuma ya kalli Abba cikin wani yanayi da yafi kama da wanda baya hayyacin sa yace, "Ashe duk hirar da nike da Hamma na watsiyace ashe yana barmin abinda har in mutu bazan manta bane Abba Adam Sadik Aliyu ko jiya da dere Hamma na yace ince ku gafarceshi fad'an da yayi a kan Ummul". sai kuma ya ruggume gawar ya fara magana kamar zai bashi amsa cikin bushewar zuciya yace, "Hamma na ba jiya nake cema in na mutu zaka zama gatana na ko?". sai ya kuma kallin fuskar Hamman nashi yace, "Hamma na ka tuna kace min zaka zama gatana bazaka zubdamin hawaye ba zaka min wonka kamin sutura sannan zaka dauwama dimun wa da'imun kana min addu'a har sai randa kabar numfashi, to Hamma na Insha Allah zanyi maka wannan gatan har zuwa lokacin da nima zan biyo bayan ka". sai kuma ya kalli Adam yace, "Adam taya ni in yiwa Hamma na wonkan k'arshe a duniya". Adam yana kuka da majina suka kamo gawar suka matso inda aka tanadi abubuwan buk'ata dan yin wonkan gawar, Abba kam da Sadik zama sukayi suna ganin duk ta inda aka juya kan Hamma Umar sai yayi lagwas shiko Aliyu kuwa kuka yake da zafin rabuwa da d'an uwa, shiko Usman nad'e k'afafun wondonshi yayi cikin bushewar zuciya ya rink'a wonke wuyan nashi da sauran wuraren da jinin ya taba sannan yayi mishi wonka yadda addinin musulunci ya tanadar, bayan sun gama ya shiryashi tsab cikin likkafanin shi aka kawo makara motor da babu taya motar da ta zame mana dole shigarta bayan an sashi a cikine aka fitar dashi akayi mishi sallah bisa koyarwar annabi sannan aka d'auki Hamma Umar aka nufi gidanshi na gaskiya da shi, inda Usman da Adam su suka sashi a makoncin sa, Allah Akbar ko wanne d'an adam k'arshen sa kenan, an gama binne shi ne ya Usman ya d'aga hannu yayi ta karanto addu'oi bayan sun gama ne aka fara juya baya ana tafiya, a dai-dai lokacin ne Usman yaji wani irin suka da zogi a kahon zuciyarshi wanda ya fara ganin duniyar tana juya mai, da kyar yake d'aga k'afafun shi har suka fita cikin mak'abartan suka shishishiga motocin su suka nufi Potiskum. A gida kuwa Ammi da Inna suna shiga suka samu Anty Halima da matar Daddy da sauran yan uwansu duk sun taru suna zaune a barandar Nenne, Ammi na shiga Nenne ta ruggumota suka had'a kai wuri d'aya suna wani irin kuka, Halima kuwa da Anty Shuwa gefen Ummul suke zaune wacce tunda tazo batayi magana ba sai idonta da yake a zazzare, cikin kuka Halima tace, "Allah sarki Ammi wayyo ya Usman Ummul tashi ki cire rigar nan Ummu kar kiyi Ammi taga wannan jinin zai iya kawar mata da hankalin ta". shiru bata kula Halima ba sai kallon Nenne da Ammi take Hajjajo da Inna ma kuka suke kamar zasu shid'e, Ammi kuwa da Nenne sunyi kuka har idanu su sun rufe, sai can Ammin ta kalli Ummul dake gefensu tana ta zaro ido tamkar idanun zasu firfito, a hankali Ammin ta kalli Ummul d'in da k'aton cikin ta wanda jikin ta duk Jini, kife kai tayi ta kuma sakin kuka, amman Ummul sai kallonta takeyi kamar bata santaba ganin haka cikin kuka Ammin tace, "Nenne kuka rahama ne kuka wani sauk'ine a garemu kusa min Ummul tayi kuka inba haka ba zai zauna a zuciyarta ku samin yarinyar nan tayi Kuka Ummul ki zubda k'ollah". amman ina Ummul Allah bai bata damar kukaba, har Allah yasa su Abba da Usman dasu Adam Sadik da Aliyu suka dawo, suna shigo wo gidan Usman yazo ya kife kanshi a jikin Ammin shi yana magagi harce a nad'e yace, "Ammi sun kashe miki lafiyayye sun bar miki nakasheshshe wanda rayuwarsa bata da tabbas Ammi zan kai kararsu". cikin kuka ta ruggumeshi tace, "Usman ya zamuyi da *RUBUTACCEN AL, AMARI* wanda Allah ya tsara mana Usman ina zaka kai kararsu waya gansu". harce na k'ara nad'ewa yace, "Allah Ammi Allah ya gansu kuma zan kai k'ararsu gun adalin sarki Allah zan had'asu da Allah ya bimin hak'kin jinin yan uwana musulmai Allah zaiyi mana hisabi dasu zubarmin da jinin Hamma na da sukayi Ammi babu kotu ko lauya ko alkali da zaiyi wannan shariyar sai Allah dan haka zan dawwama ina kai kararsu gun Allah zasuga saka makon aiyu kansu a ranar da gabbansu zasuyi bayanin rayukan da suka kashe Allah ya isar mana ana cutar damu musulmai a k'asarnan ana kashemu tankar kiyashi Allah ya isa! Allah ya isa! Allah ya isa jinin d'an uwana". gaba d'aya sai gidan ya kuma cika da tasbihai dan samun sanyin zuk'atansu ita kuwa Ummul sai binsu take da kallo, Aliyu ne wanda tunda suka shigo yake kuka sai yanzu Sadik ya kamo hannunshi suka k'araso cikin gidan suna shiga Aliyun ya fad'a jikin Ummul d'in yana kuka mai tarin k'una shi kuwa Sadik cikin rawan murya yace, "Ammi mun kai Hamma Umar gidanshi yanzu addu'arki yafi buk'ata". daga wannan kalmar Ummul bata kuma sanin inda takeba ko a wanne halin takeba, ta sume cit suma mafi munu domin harda k'ok'olwarta tayi sanyi, daga nan aka kwasheta akayi asibiti da ita Dr Bashir shike duba lfyar ta, yayin da Usman Kuwa yake ganin suma hutune a wannan halin da yake ciki ba kuka ba suma sai tarin k'unan zuciya ga fargabar halin da Ummul take ciki. Har tsawon kwana uku Ummu bata farfad'o ba hakan yasa yan uwa cikin wani sabon tashin hankali ganin haka Dr Bashir ya bada shawaran a fiddata woje, haka kuwa akayi cikin kwanaki aka shirya fita da ita k'ark'ashin d'aukar nauyin gwamnatin jihar tasu aka fidda ita, Egypt inda aka kai tsaye suka wuce Magrib Medical Center Cairo, ita da Ammin Hamma Umar sai ya Adam tare da jagorancin Dr Bashir, koda suka je Ummul saida tayi kwana 8 a sume sannan ta farfad'o koda ta farfad'o d'in kuma bata magana sai kallon mutane kawai, duk bincike anyi da magani amman ba magana a haka aka sallamesu dan doctors sunce a koda yaushe zata iya magana, an sallamesu da sharadin watan haihuwar ta na tsayuwa su dawo dan bugun zuciyarta yayi k'asa sosai bazata iya haihuwa da kantan ba, a haka suka dawo gida dan hankalin mutanen gida ya konta. randa Hamma Umar ya cika sati uku da rasuwa a ranar suka dawo, suna dawowa koma yazo yanawa Ummul magana amman ba amsa, bata ko d'ago kanta ta kalli kowa sai in Ammi ce tayi magana, haka gaba d'aya farin cikin su ya koma ciki. A daren ranar ne bayan duk an shiga an konta Ammi na zaune da Usman a gefen Ummul da ta konta tana kallon su ba magana, Usman ne ya kalli Ammin cikin rauni yace, "Ammi cikin kam baida matsala ko? ". Ammin ta bud'e baki kenan zatayi magana Ummul tayi wani irin gigitaccen...... *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 3⃣1⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *MOH ALLAH WUJI FURD'ATA* *DEDDE Na Ummu uwata ta kaina mahaifiyata abin k'aunata abin Al'faharina yau kuma kirarinki da kikemin na yarintata na tuno lallai bani da tamkarku kida Abba na domin a yau Kirarin da kikemin zai iya kasan cewa a horkon ko wani shafina na littafaina inada kike cemin* *KIN KINI KAN KAD'A DAMONI NA DAMONI GID'D'O MO FINA LARA GAID'O MO FINA SUKOYO LADDE ALLAH YAMAD'UM! KI D'OIDI YALETE! KI B'IB'B'E SAMMMETE! B'ENDUKI YAMETE! YORIKI TENETE! DAMONI NA DAMONI GID'D'O MO FINA LARAMO GAID'OMO FINA SUKOYO LADDE ALLAH YAMAD'UM ALLAH WANNE BARKA BOD'D'I DEDDE Allah fintine ba seto arana* *wata kalmar sai a bakin Fulani* *Wani Abu sai Uwa da Uba wannan kirarin duk ni kadai Aisha Aliyu garkuwa mahaifiyata da mahaifina kemin da sanya min albarka tun ina karama har zuwa yau Ya Allah ka sakawa iyayena da mafi kyawun sakamako ya Allah ka yiwa iyayena jagoranci har cikin jannatul firdausi DEDDE NA DA ABBAN ina sonku fiye da kowo har kaina Allah ya barmin ku😍😘😍😘* *T*ayi wani irin firgitaccen zabura cikin tsananin razana ta yunkura da karfi zata tashi tana wani irin gurnani, ganin haka cikin karfin hali da firgici Ammi da ya Usman sukai saurin rik'ota suna mata addu'a, ita kuwa gaba d'aya jikinta rawa yake kar-kar hatta d'an cikin ta sai motsi yake da k'arfi ta zazzaro ido tana waige-waige kamar me neman wani abu, dakyar ya Usman ya kamo kanta da hannu biyu ya kwantar da ita a kan cinyar shi dan yadda take fisge-fisge Ammi bazata iya control enta ba, ita kuwa Ammin sai shafa bayanta takeyi a hankali kwalla cike a idon ta tana furta, "hasbunallahu wa ni'imal wakil". Shiko ya Usman yana ruggume da ita a jikin shi gaba d'aya jikin nashi sai kerma yake a karo na forko da yaji rauni da tausayin kanshi da kanshi ga taussyin halin rayuwar da Ummul ke ciki a zahiri yasan kuka rahama ne in dai da k'una a zuci amman shi kuka ya k'aura cewa rayuwarsa tunda Hamma enshi ya bar duniya baya gane halin rayuwar da yake ciki dazaran k'unan rai da k'uncin rayuwar sun tokare mai zuciya sai yayi ta aman jini yana murza kai da k'irji inko dere yayi sai ya tashi ya kwana nafilfili da nemawa d'an uwanshi rahamar Allah a hakan ne Adam ya gano wani abu daya shiga rayuwar Usman da zaran ya kad'aice sai ya rink'a juya kai yana mirgina kan nashi kan kafad'un shi kamar yadda yayi tayi lokacin daya zauna gaban gawar Hamma Umar abin a hankali ya zamewa Usman wani narkarwa ciwo mai zafi a ranshi da rayuwarshi da zaran ya tuno yadda yaga gawar d'an uwanshi sai kawai yayi ta juya kai jiki na rawa hakan yasa yanzu da zaran hankalin shi ya tashi ko ranshi ya baci sai ya rink'a wannan abun, so yanzuma da Ummul take ta fisge-fisge da gurnani yana ruggume da ita duk da ba wanda yake gane me take fad'a hakan yasa sai ya rink'a juya kai yana murza k'afafunshi dan zafin da zuciyarshi ke mishi, ita kuwa Ummul sai gurnanin takeyi Ammi kuwa duk sai zuciyarta ta d'anyace ta tasasu a gaba ta kife kanta tana kuka mai cike da dafi a zuciya, Ya Adam ne ya k'araso cikin d'akin da sauri ya d'ago Ya Usman wanda ya kife kai a kan bakin gado yana jan numfashi da a wahalce, Abba da yanzu ya iso da su Nenne da Hajjajo da su ya Sadik sai Aliyu suka shigo saboda jiyo k'arar da Ummul tayine, cikin karfin hali Abba yace, "Adam, d'aukemin Usman daga nan". Usman najin haka cikin rawar murya da juya kai ya fara magana, "Abba ku kyaleni dan Allah kubarni inkula da amanar d'an uwana ku barni in kula da amanar da Hamma na ya barmin". sai kuma yasa hannu biyu ya rik'e kanshi yana juya kan a wahale yana k'ollah murya na rawa yace, "Nanne ina zankai Ummul ? mezan mata ta sami sauki? Ammi ina soro kar d'an d'an uwana ya cutu ya zanyi na kare mutunci da lafiyar Iyalan Hamma na?". sai kuma ya kife kai ya saki wani irin kuka mai k'arya zuciyar mai sauraro kuka yake har numfashin sa na cizga duk jikin shi sai b'ari yakeyi tamkar mazari, Aliyu ne ya dafa kafad'ar shi cikin matsanancin kuka yace, "ya Usman tashi muje muyi nafila muroka mata sauki, Hamma Umar yace min duk damuwa tanada magani a gun Allah, kutashi muyi musu addu'a zata samu sauk'i kullum Hamma Umar nace min Aliyu duk tsanani yana tare da sauki, nasha in sameshi yana kuka in nace mishi Hamma Umar me yasa ka kuka? sai yace min Aliyu Usman baida lfy ina kukane wa ubangijina ina nemawa Usman lafiya a gun mai bada lafiyar, dan haka muma muje mu nemawa Ummul lafiya a gun mahaliccinmu". Yana kaiwa nan yaja hannun ya Usman suka fice suka nufi part insu al'wala sukayi sannan su fara nafilfili tare da karatun qura'an, haka kowa na gidan yai alwala suka dukufa nemawa Ummul sauki gurin Allah, Ammi kuwa na rungume da Ummul tana shafa bayanta a hankali tana tofa mata addu'o 'i har tasami bacci wanda takan razana duk mintina kad'an. Haka rayuwa tacigaba da tafiya cikin rashin wal-wala da kuncin zuciya yayinda kowanne ke buya yayi kuka san ranshi daga Abba, Hajjajo, Nanne, Adam, Sadiq, Aliyu, wanda b'angaren Ya Usman kuwa abun sai rahamar Allah kullum yana cikin aman jini ba k'ak'k'autawa kuma yanzu ya samu sauk'i yana iya kuka hakan yasa da zaran ya fara kuka kuma sai tari sai aman, Ammi kuwa tamik'a lamuran ga Allah tadage wajen kula da Ummul wadda tazamo tamkar mutum mutumi duk da ansami cigaba a yanayin ta takan d'an sha tea duk da sai Ammi tasha rarrashi wonka kuwa sai Usman ya zauna gabanta yayi ta lallashi wani lokacin ya kife kai yayi ta kuka kafin ta yarda Nenne ko Ammi su mata wonka abu kamar wasa a zahiri Ummul ta zama tamkar zaucecciya komai sai an sata kuma tun randa Hamma Umar ya rasu har yau Ummul Allah bai bata bakin manana ba kullum kuma in dere yayi toh tashin hankali ya tashi kab zuriyar tasu basu da konciyar hankali da zaran an shiga za'a konta sai Ummul tayi ta firgice-firgice tana razana tana son guduwa sai ta rink'a b'uya ko tana k'ok'arin shiga duk inda taga luggu, Usman kuwa haka zai zauna yayi ta kuka yana ga ya kasa tallafawa iyalan d'an uwan nashi a haka ciwon zuciyarshi ya tashi. Yau Jumma'a da yamma, ya Usman ne zaune gefan Nanne ya Adam yana tsaye Aliyu kuwa yana durk'ushe gaban Ummul sai kuka yakeyi duk sun zubawa Ammi da take bawa Ummul ruwan zam-zam da aka tofawa addu'oi wanda yanzu shine ruwan shanta, domin samun sauki da sassaucin kuncin zuciya, d'an ture hannun Ammi tayi sai kuma ta rink'a binsu da kallo d'aya bayan d'aya kai ta sunkuyar tana kallon k'aton cikin ta da d'an yaketa wintsil-wuntsul a hankali ta mik'awa Aliyu dake zaune yasata gaba yana kuka, hannu alamar ya d'agata da sauri fuskarshi cike da mamaki yace, "In d'agaki?". dakai tamai alamar eh, aiko cikin jin dadi yamike yasa hannu ya d'agota ta mike sannan yasa hannu yana gyara mata d'aurin zaninta yana mai zubda k'ollah, Ya Usman kuwa cikin saurin ya je bayanta ganin tana tangad'i kamar zata fad'i, cikin k'arfin hali tafara takawa wanda hakan yasa dukkansu dake d'akin jin dadi kasan cewar tun dawowarsu basuga hakan daga garetaba, a hankali suke tafiya Aliyu na rik'e da hannunta har suka fita daga d'akin, da hannu taiwa Aliyu nuni da hanyar inda Hamma Umar ke zama dan duba marasa lafiya dake zuwa gida, haka sukaita tafiya sanayi a hankali har suka isa gurin, d'an juyowa tayi ta yafito ya Sadiq da suketa binsu a baya tunda suka fito ta nunamai carpet dake jingine agun da hannun ta, shiko jiki na rawa yace, "in shimfid'a?". Kai ta kad'a, aiko ya shimfida nan da nan, kwace hannunta tayi dagana Aliyu ta juya kamar tana neman wani abu, Ya Usman dake tsaye a bayanta kamar body guard' yace, "me kike so?". itako Ummul Ammi ta nuna da hannu takuma nuna mata carpet da aka shimfid'a, cikin sanyin jiki Ammi ta zauna kan carpet d'in, Ummul tasa hannu ta rik'o hannun Aliyu shiko yasa daya hannun yakuma rik'ota ya taimaka mata ta zauna sannan ta matsa kad'an ta jingina bayanta da jikin Ammi, ta sauke nannauyar ajiyar zuciya ta lumshe ido sannan ta kalli Ya Usman daya zuba mata ido tamai nuni da ya zauna. zama yayi sannan taiwa Ya sadiq nuni shima ya zauna, ta kalli Aliyu tamai alama da hannunta daya yazo yazauna kusa da ita haka taiwa kowa nuni suka zauna harda Hajjajo, Ya Adam yasa tafin hannunsa ya goge hawayansa a dai dai lokacin da Ummul taimai nuni daya zauna shima, Haka suka zauna agun itako Ummul tanata kallon su da dai-dai kamar bata tab'a ganin suba saida aka kira magrib sannan suka koma cikin gida. Kwanci tashi cikin Ummul ya isa haihuwa dan haka aka shirya komawa kasar egypt da taimakon adalin gwamnan gwamnoni, gwamna daya d'au rayuwar talakawan jahar shi da muhimmanci gwamnan jahar yobe. Anyi tafiyar ne da Ammi, Abba da ya Usman sabida yanada buk'atar ganin likita akan yawan aman jinin da yake kowane lokaci, isar su da kwanaki uku aka gama bincike kan zuciyar Usman inda cikin ikon Allah doctor ya shaida musu za'a cire na'urar dake tallafa zuciyar Usman domin sanadin wani tsoro da tsinkewar zuciya daya samu yasa zuciyar ta harba cikin tsoron to daga nan yanzu ita da kanta take aikin harba jinin kuma in anbar na'urar zata iya maida zuciyar ta cushe dan haka cirewa za'ayi, abin ba k'aramin Al'ajabi ya bawa Ammi da Abba da Adam ba haka Abba da Ammi suka sa'a hannun, ita kuwa Ummul bayan magun guna da allurai da likitoci keta bata ne akai shirin shiga yimata aiki saboda babu halin haihuwa dakanta sakamakon sanyin da zuciyar ta tayi dan bugun zuciyarta tayi k'asa sosai haka yasa rana d'aya za'ayiwa Usman da Ummul aiki Abba kam da Ammi da Adam sai Addu'oi sukeyi Abba ya kira Daddy da Uncle dinsu Usman da sukaje saudi ya shaida musu su tayasu da Addu'a. K'arfe 8:00 dai-dai babban likitan da zai jagoranci aikin yakira Abba da Adam a office din shi, bayan yad'anyi rubuce rubucen shi ya d'ago kanshi ya sauke farin glass dinshi kasan hancin shi yace, "Alh Hassan, zamu shiga aiki da yaranka muna kuma bukatar addu'ar ku kasancewar ita yarinyar aiki zamu me cike da hatsari domin kuwa bamuda tabbacin zuciyarta zata tsaya yanda muke bukata har mu gama aikin". Abba yai ajiyar zuciya yace, "to Allah ya bada sa'a". Likitan ya mik'o musu form da zasu saka hannu dan yin aikin, Abba yasa hannu ya janyo takardar ya juya ya kalli Adam da ya sunkuyar da kai k'asa ya dafa kafad'ar shi yace, "Adamu kadaure kasa hannu aima k'anwarka aiki ni zansa hannu akan aikin Usman". a razane ya Adam ya d'ago yana kallon Abba da takardar, a hankali Abba yasake d'agamai kai da lumshe ido cikin sanyi Adam yasa hannu ya janyo takardar yad'auki biron sannan ya d'ago kai ya kalli likitan daya zubamai ido yana kallonshi, cikin tausayawa likitan yace, "Insha Allah zamuyi aiki cikin nasara". shi kam Adam ido cike da k'ollah yasa hannu tsoro tab zuciyarshi yana jin tausayin Usman a ranshi yana jin tsoron kar wani abu ya faru da su kuma a zuriyar tasu, hannu na rawa Adam yasa hannu a takardar yana zubar da kwallah, likitan yasa hannu yaja takardar yace, "good, be prayerful". da haka yatashi yafita sukabi bayanshi jiki ba kwari, karfe 9:00 dai-dai aka shiga da Ummul d'akin tiyata ya Usman kuwa aka shiga dashi d'akin dashen zuciya, akabar Abba da Ammi , tsaye suna karanto kowacce irin addu a da suka iya zuk'atan su cike da zulumi. Har k'arfe 11:30 suna ta zirga-zirga bawanda yake magana kowanne da irin tuna ninda yake a ranshi, bude k'ofar dakin da akema Ummul aiki ya tattaro hankalinsu, ya Adam ya dafe kirjin shi da hannu yabi bayan likitan daya wucesu yanufi office d'inshi, a lokacin kuma aka fito da ya Usman shi an gama aikin nashi, Adam kuwa a office d'in doctor saida ya zauna a kujerar shi sannan yad'anyi murmushi yace, "congratulation". Allah yayi ikon shi da taimakon y'an uwana likitoci anciro baby boy, yaro yana cikin koshin lafiya sannan insha Allah itama zata farka babu wata matsala". cikin jin sauk'in razanar Adam ya dago rinannun idanunshi dasukai jawur yace, "Alhamdullah Masha Allah". Sanna ya mike ya fito ya nufi d'akin da yaga Abban na shiga wanda ya haggo ana shigar da Usman, suna shiga kuma sai ga ita Ummul an shigo da ita haka aka kontar dasu d'aki d'aya gadon Usman na gefen na Ummul Ammi kuwa waje ta fita ruggume da yaron tana kukan abubuwa da dama kukan tuno d'anta kukan fargabar halin da Ummul da Usman ke ciki kukan tausayin yaro maraya tun yana ciki an kashe mai uba haka tayita kuka gwanin ban tausayi. Bayan awanni shida Ummul na kwance kan gadon hutu na asibitin, shiko Usman yana kwance kan d'ayan gadon dake kallon nata yasanya jinjirin gaba yanata kallo dan yariga ta farfad'owa, yayinda Abba ke zaune a kan kujera a gaban gadon Usman kusa dashi kuwa Dr Bashir ne suna kallon yanda Ummul kedan motsa k'afarta a hankali, Ammi ko tana zaune bakin gadon da ummul ke kwance tana rik'e da hannun ta idon ta ya na kanta, yun kurin bude idonta tafarayi a hankali tanajin yamata nauyi, da hannu Ammi taiwa Dr Bashir nuni aiko tare suka taso sukayo bakin gadon, Tana bud'e idonta da kyar ta d'aga hannun ta da kyar ta shafi cikinta dan jin yayi mata wayam aiko saita d'an kara zaro idonta tabud'e baki da kyar murya nara voice a disashe a hankali tace, "In in inaaaa cikin?". Hamdala suka rink'a jerawa cikin tsananin happy dan tunda Hamma Umar ya rasu sai yau Ummul ta iya magana, ya Usman kuwa juya kanshi yayi a hankali wasu irin hawaye masu zafi suna bin fuskarsa, Ammi ce ta mik'e da sauri ta d'auko babyn da yaketa bacci a gaba Usman shiko Usman sai kallon yaron yake cikin tsananin k'auna yana jin son yaro fiye da kowa a duniyar nan, a hankali Ammi tace, "gashi nan Ummul, ga d'anki wanda Allah ya azurtaki dashi keda Faruoq na amman ke Allah ya nunawa shi shi kam Umar ya rasu da begen wannan rana ya rasu da kumfar rashin ganin d'anshi Ummul ga d'anki maraya zai tashi maraya kamar yadda iyayenshi suka tashi marayu". Daga kwance tasa hannu ta d'ora akan yaron ta kuramai idanu tanajin k'aunar shi na ratsa zuciyar ta da dukkan jikinta sai kuma tayi kurui tana kallon Usman dake konce yana hawaye cikin sanyi yace, "Ammi yaron nan bazaiyi maraiciba Insha Allah bazai yi kukan rashin mahaifiba Ammi da izinin Allah indai ina raye yaronan bazai zubda k'ollah". sai kuma ya rink'a kuka yana rik'e da hannun Abba, shima Abban kuka yake Ammi kuwa zuwa yanzu hawayenta sun fara k'agewa, Adam ma gaba d'aya ya zama mai raguwar zuciya abu kad'an sai Kuka amman shi tausayi Usman ke addabar rayuwarshi, haka Dr Bashir kuwa da sauran doctors din sukayi ta kula da Usman da Ummul da jaririnta k'ato fari tas kekyawa, sukaita kula dasu cikin ikon Allah kuwa Ummul da Usman duk Alhamdulillah jiki yayi kyau Ummul kuwa tun randa tayi magana bata kuma yiba. Doctors sun bada tabbacin zuciyar Usman zata iya aikin da ake but'ata amman a guji b'acin ransa sosai sukayi kashedin gudun b'acin ran shi, a gefen Ummul Kuwa sunce kar a damu da rashin maganarta sunce a koda yaushe maganarta zata iya dawowa amman kuma a duk randa suka tsinci Ummul na kuka toh karsuyi yunk'urin hanata a barta domin a cewarsu yin kukan zai iya maida tunaninta dai-dai har ta fara magana kuma sanyin da zuciyarta tayi harda rashin kukan. Bayan kwanaki shida dayin aikin aka sallamesu da sharadin kulawa da bawa Ummul da Usman magunguna don cigaba da samarwa zuciyoyin su lafiya, da haka suka tattaro suka dungumo sai gida Nigeria. Randa suka dawo gaba d'aya zuriyar Shuwa sun cika da farin ciki domin samun lafiyar Usman da Ummul ga jariri da ya zamo magajin Hamma Umar kowa zaizo da Happy amman abin fargaba har yanzu Ummul bata mgn, Nenne takan buya tayi ta kuka, Ummul kuwa in banda bawa yaro nono da da tasashi a gaba tayi ta kallo ba abinda takeyi da kanta sai an tasa a gaba wani lokacin sai ta wuni ta kwana bataci komaiba inko yaronta na kuka sai tai ta rawan jiki ta gigice, in tak'i cin abinci da wonka Usman yakan zauna a gabanta yayi ta magiya har ya fara zubda k'ollah to da zaran taga yana kuka sai ta zauna ta fara cin abincin. A haka rayuwa tayi ta juyawa har sukayi kwana 9 da dawowa, yau asabar da safe bayan sun gama aiyu kansu, Abba da kanshi ya shiga d'akin da Ammin ke zaune da Ummul a nan ya samu Usman da Nenne da Adam Ummul ruggume da yaron, bayan sun gaisa cikin kula Abba ya kalli Usman yace, "ni kam Usman me sunan yaron ne har yau baka gaya min ba? ". cikin mamaki Usman yace, "Abba baka yiwa yoron huduba bane dama ni yamin ka gaya mai sunanshi ai". a hankali Abba yace, "A a Usman ya za'ayi haka yaro yau kwana 14 kuma ashe ba'a mai huduba ba". Ammi ce ta kallesu a hankali tace, "mahaifiyarshi ta mishi huduba tun randa yayi kwana uku amman har yau bata gaya min sunan shiba". usman d'in ya zuba mata ido cikin sanyi yace, "Ummul kiyi hak'uri mana ki ruggumi k'addararki ki rink'ayi mana magana yanzu tsakanin ki da Hamma kiyi mishi gatan Addu'a ki bawa d'anshi tarbiya to amman a hakan zakiyi wad'an nan abubuwan"?. shiru tayi tana jinshi karo na forko da ida nunta suka ciwo da hawaye tab, Abba ne ya kalleta a raunane yace, "Me sunan yaron?". murya can k'asa cikin rauni da tsananin k'una a zuciya tace, "Washe garin za'a kashe Hamma na yace min in namiji na haifa ya bani dama nasa sunan wanda nafiso a duniya wanda duk duniya bani da kamarshi". sai kuma ta saki wani irin kuka ta ruggumo yaron tana kallon shi, Usman ma kukan ya fara a hankali yace, "Ummul me sunan yaron?". cikin tsananin kuka tazo ta durk'usa gaban Abba murya a disashe tace, "Abba ina sonshi Abba ina sonshi ina sonshi Abba duk duniya bani da kamarshi Abba ina son Hamma Umar Abba ina zan ganshi Abba sun kashe min Hamma na a gabana Abba ina son Hamma Umar". sai kuma ta kife kanta a cinyar mahaifin nata cikin rauni da tausayawa rayuwarta, shiko Abba a hankali yace, "Me sunan yaron kika saka? ". cikin tsananin kuka tace, "Sunan shi *Umar Faruoq*". tana fad'in haka Usman ya........ *Sadaukarwa ga Umar Ibrahim Umar Hamma Umar* By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 3⃣2⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *MOH ALLAH WUJI FURD'ATA* *Kin kid'i kankad'a damoni na damoni giddo mo fina laramo gaid'omo fina sukoyo ladde Allah yamad'u benduki yamete ki b'ib'b'e sammete joruki tenete ki d'oidi yalete* *U*sman ya d'ago jajayen idanuwan shi yazuba matasu sannan ya mik'e yana layi yaje bakin gadon ya sa hannuwanshi biyu a d'auko Umar faruq ya rungume sosai a jikin shi yana zubda hawaye mai tsanani da zafi da k'una a zuciya yana shafa kan yaron dake cike da suma bak'ik'k'irin daya kwanta luf, ita kuwa Ummul cikin kuka taci gaba da cewa, "Hamma Umar ne rayuwa ta nafi sonshi a kan kowa a duniya, shikad'ai nakeso shine komai nawa na rasa a lokacin da nake tsananin buk'atarshi". Tana magana ne cikin matsanan cin kuka, bakajin komai a gun sai shashshek'ar kuka da duk wanda kegun yakeyi, shiko Usman yana k'ollah ne idanuwan shi na kan Umar faruq yana mai wani irin kallo kamar a lokacin yafara ganin halittar jariri, Itakuwa Ummul cikin kuka taci gaba da cewa, "Ammi wallahi ina sonshi, bazan k'ara son wani mutum a duniyar nan bayan Hammana, ina kaunar shi fiye da kaina Inamai matsanan cin so da duk duniya bamai iya fahimta". sei ta kuma jan gwiwoyinta data zuba k'asa har gaban Ya Adam dake ta faman zubda k'ollah tace, "Yaya na kafi kowa yimin fad'a bakamin wasa amman na kasa ganewa, kuma baka son damuwa ta, nasan kayi iya k'ok'arinka ka d'orani ka turbar gaskiya, amman taurin kaina da rud'un shaid'an yasa nak'i gane abinda nasan gaskiya ne gashi hakan ya jazamin nadama ta har abadan na cutar da kaina da kaina naga illar rashin yiwa iyaye biyeyya, nagode dakaita k'ok'arin nunamin hanyar gaskiya". Hannu yasa ya kama hanna yenta duka biyu ya d'an matsesu sannan yace, "Ummul nasan kina son shi naga sonshi a idonki amma inaso ki nunamai soyayyar da kikemai inaso ya amfana da ita ta hanyar yimai addu a Ummu ki dena zubda mai hawaye". kai ta rink'a gyad'awa cikin rauni da tsananin nadama, saita kuma juya ta kalli Abba dake tsaye yana kallonsu ido cike da k'ollah, sannan ta dawo da kallon ta ga Ya Adam dake murza yatsunta a hankali tace, "Ya Adam Abbana yamin zab'i mafi al'khairi zab'i mai cike da al'kairai a rayuwata amma ina shaid'an ya hanani ganewa nayiwa iyayena taurin kai gashi zan dauwama cikin nadama da dana sanin rashin biyayya haka zan k'are rayuwata na kasa yiwa iyayenmu d'a'a kaitona Allah ya wadaran halina bani da wani abun koyi lallai duk yarda tayiwa iyayenta ba dai-daiba tana tare da nadama ya Adam na tsani kaina na cutar da Hamma na na b'ata ran mahaifanmu". sai kuma ta kife kai wani irin matsanan cin kukane ya kwace mata wanda ya hanata k'arasa kalaman ta ta kife kanta a gwiwar Ya Adam jiki na rawa tana cewa, "Wallahi ina son shi, inason Hamma Umar Yazanyi Hamma Umar yaga soyayya da kaunar da nakemai, ya Adam kullum Hamma Umar yana cewa Ummul zaki soni, zakisoni lokacin da soyayyar bazata amfane muba ashe wannan lokacin ne Hamma na yake ganemin dana sani dana nuna mishi so da yake son in nuna mai lallai wannan shine kuskure mafi muni da yarinya tayi dan iyayenta sun mata auren dole". kuka takeyi sosai tana cike da madama, Aliyu ne yataho jiki ba kwari yasa hannu biyu ya d'agota ya durkusa gabanta a hankali yace, "Aunty Ummul kiyi hak'uri, Hamma yace nine abokin shawararki abokin kukanki kuma me rarrashinki kiyi hak'uri kidena kukan nan kinga kinsa Ammi da Nanne kuka ga Abban mu shima yanayi kinga Hamma junior zaiji sautin kukan mu ki dena auntyna dan Allah". Cikin galabaita da ajiyar zuciya ta kwantar da kanta a cinyar Aliyu tana sheshshe k'ar kuka tana nannad'e kafafun ta, hannun Aliyu yasa yana shafa bayanta yana bubbugawa tare da share mata k'ollar cikin lallashi da haka bacci yayi gaba da ita, su kuma Abba ya zauna yayi ta musu nasiha Usman kuma sai ajiyar zuciya yake sauk'ewa yana ruggume da farouq, a haka rayuwa tayi ta juyawa rana d'ad'd'ayace basa zama suyi kuka a hankali mutuwar ta fara shiga jikinsu, lokaci yaja kwanaki sun tafi tuni Farouq ya cika kwana arba'in. A bangaren Mustapha kuwa a kullum koda yaushe tunanin shi nakan Ummul da yaronta dan haka ranar Asabar suka shirya da umman shi suka nufo potiskum dan duba lfy Ummul da jaririnta, dai dai lokacin da motar Mustapha na shirin shiga harabar gidanne motar Dr Bashir ta sako kai dan fitowa wanda shima zuwa ganin Ummul da yaronta ya zame masa jiki a duk lokacin da baida aiki, daga cikin mota suka gaisa da Mustapha sannan ya wuce cikin gidan shiko Dr bashir ya fita, Kayane na gani na fad'a da suka had'a da sabulai man shafawa powder, pampers, wipers da sauran kayan jinjiri Mustapha ya lodo kamar me bud'e shagon mother care, duk na Umar faruq wanda Aliyu ke kira da junior, Bayan ya gaisa da su Ammi da Nanne Aliyu yamai jagoranci zuwa palourn bak'i sannan ya kawomai abin sha sannan ya fita, a cikin d'akin Kuwa Ammi ce ta maida hankalin ta kan Ummul dake zaune bakin gado cikin sigar lallashi da bada umarni da kulawa tace, "Ummu na ki kaiwa Mustapha yaron nashi ko". Dakai ta amsa tad'au katon hijab ta saka sannan Umman Mustapha dake rik'e da Farouq ta mik'a matashi ta karb'a ta fice, sukuma sukaci gaba da jajantawa juna irin jarrabawar da suka fuskanta. Mustapha dake zaune yana latsa wayar shi sallamar Ummul tasa ya aje wayar a gefe yamik'e tare da amsa sallamar yamik'a hannu ya karb'i Farouq dake ta bacci sannan ya koma ya zauna yad'an dago kai yana kallon Ummul dake tafiya kamar mara lakka a jiki har ta sami kujerar dake fuskan tar wadda yake zaune ta zauna tai k'asa dakai tana wasa da yatsun hannun ta sannan yamai da kallon shi ga Umar faruq, Shiru ya ratsa na y'an muntina sannan Ummul tai k'arfin hali tace, "ina kwana". Saida taji shirun yayi yawa sannan ta d'ago kanta a hankali tasauk'e idanun ta kan fuskar Mustapha dake rungume da Umar faruq kallon yaron cikin tsananin k'auna da tausayawa maraicin shi, lokaci d'aya tausayi shi ya rufeshi tuno Hamma Umar kawai sai idanun shi ya fara zubda k'ollah, da sauri ta maida kanta k'asa ganin hawayen Mustapha sai wani irin raunataccen kuka mai zafi ya kubce mata, Mustapha da kyar ya dai-dai ta nutsu warshi sannan yace, "Khairi dan Allah kiyi hak'uri banyi haka dan na saki kukaba please ki dena zubdawa Hamma Umar hawaye Insha Allah muna zata mai rahama gatan da zakiyi mishi addu'a ce". ai kamar ya dad'a tunzura ta tacigaba da kukan da sauri ta mik'e ta fita daga palour cikin kuka a zahiri ko fuskar Mustapha bata son gani ji take sanadin shine tayi duk wani kuskure da taurin kai shiyasa da zaran ance mata yazo sai ta resa meke mata dad'i, gashi shima in yazo kullum sai Farouq ya sashi Kuka tana fitan, Mustapha yasake rungume Umar Faruq ya lumshe idanuwa yanajin kaunar yaron na ratsa duk wata gab'a ta jikin shi, Dasu Ya Adam sukaita hira har lokaci yaja sannan yaje sukai sallama dasu Ammi suka kama hanyar damaturu. Yau asabar wanda yayi dai-dai cika watanni 4 da Farouq yayi, misalin k'arfe takwas Usman yafito daga b'angarensu sanye da farar jallabiya yanufi b'angaren Nanne kai tsaye d'akin Ummul ya shiga yasame su zaune da alama nono Ummul keba Umar Farouq ta yadda yaga tai maza ta sauke rigarta, k'asa yayi da kai ya tsugunna ya kuma gaida Ammi sannan ya dago kai ya kalli Ummul yace, "kawo shi". mik'a shi tai batare da ta dago kantaba yasa hannu ya karb'e shi sannan yace, "kinci abinci ne?". Kai ta girgiza alamar a a d'an juyawa yayi ya kalli Ammi kafin yayi magana Ammin tace, "kaga abincin nan zataci kenan yaron yafarka daga bacci, to nabashi ruwa yasha nace taci sannan ta ba shi nonon, amma saina ga hankalin ta bai kwanta da hakan ba, shiyasa nabata shi yasha tukuna". Murmushin karfin hali yayi ya kalli Ummul ya jijjiga kai ya juya rungume da yaron shi, a parlour su ya zauna ya kwantar da Faruq kan cikin shi ya zubamai ido saikuma ya fashe da kuka mai cin zuciya da k'unar rai yana kad'a kai wanda hakan yazama al'adarsa yana dawowa daga aiki zai d'auki Faruq yaje yasashi a gaba yaita aikin zubda k'ollah yana tuno d'an uwanshi Hamman shi abin begenshi. Ammi ce zaune tana kallon farcen hannun ta taga yanda suka fito sukai tsayi nan da nan ta tuna gudan jininta wanda tunda yayi wayo shike yanke mata farce dan haka ta manta da lokacin da ta yanke farce ta a rayuwar ta, hannu tasa ta d'auko abin yankan farce sannan ta koma ta zauna kan carpet ta fara gwada yankewan sai abin ya murd'e mata lokaci d'aya begen Farouq d'inta ya rufeta mutuwar ta dawo mata sabuwa kawai sai ta kifa kai jikin gado tasaki matsanan cin kuka mai cike da tausayi. A part d'in su ya Usman Kuwa, ya Adam na kwance rigin gine ya d'ora dan lelensu Umar Faruq a kan cikin shi shikuma Ya Usman ya zuro hannu yana daga kwance yakama k'afar faruq yanata murza k'asan k'afar a hankali shiko Farouq sai dariya yake yana wulla hannaye, Ya Sadiq ne ya shigo sanye cikin farar shadda yanata zuba kamshi yai sallama suka amsa sannan yace, "Ya Adam dan Allah kabani junior zamuje unguwa". Kai Adam d'in ya d'an d'ago yakalleshi yace "ina zakuje?". cikin mik'a hannun yace, " D'azu dana fita zan sayoma Nanne turare ne naga wani takalmi na yara me kyau shine nakeso inkoma da Farouq in sayo masa". aiko yana rufe baki Ya Usman ya mik'e yace, "muje nima zanje, kuje mota bari inje gun Ummul koda akwai abinda takeso a seyo mata". Yana fad'in haka ya nufi cikin gidan, Shigar dayayi tambayar Ummul ne yasa yaga Ammi ita kadai a d'akin ta kifa kai hannunta rike da abun yankan farce tana kuka mai cin rai, cikin rauni da sanyin jiki ya zame ya zauna kusa da ita yasa hannu ya karb'i abin yankan farcen kawai sai ya fashe da kuka mai ban tausayi ya kasa yanke mata farcen da rufe idonshi sai ya rink'a tuno yadda Hamman shi ke yanke mata farcen. shirun da Adam da Sadiq sukaji suka gaji da jirane yasa suka shigo dan duba me ya tsaya yi, aiko samun su sukayi suna kuka ba me rarrashin wani cikin su ganin haka, Sadiq ya zube guiwowin shi a kasa ya dafa kafad'ar Usman shima Adam ya rab'a yazauna bakin gadon sannan yafara bawa Ammi da usman hakuri da lallashin har saida suka samu suka hakura, sannan Usman yakama hannun Ammin shi ya yanke mata farce sannan yankan farcen Umar farouq, daga ranar yanke music farcen ya zame mashi abun yi duk k'arshen sati. Ranaku na shud'ewa wattanni sun tafi har Farouq yayi wata 7 B'ngaren Ummul kuwa kullum cikin kuka dasa mutane kuka tana fad'in irin yadda takejin Hamma Umar da soyayyar shi mai k'arfi a zuciyar ta yayinda ya Adam ya Sadiq Aunty Halima dake zuwa daga gidan ta duk kwanaki biyu suka dage wajen kula da y'ar uwarsu dan samar mata da farin ciki. Kamar kullum yauma zaune suke a palour nanne suna ta hira Aliyu zaune gaban Ummul yana b'are mata lemo yana bata labarai masu ban dariya su ya Sadiq na tayashi, Nanne ce ta fito daga bedroom nata ta zubawa yaran nata ido cikin kulawa tace to ina Yayan ku Usman? ya Sadiq yace, "yanzu yad'au Faruq yafita dashi". ajiyar zuciya tayi tace, "daman yanzuma fitowa nayi ince a d'aukeshi daga koyan tsayuwar kar ya gaji". Da haka ta wucesu tanufi bangaren su Usman, abinda take zato ta gani, Usman zaune yasa Farouq dake ta wutsil wutsil a gaba yana aikin kuka, zama tai gefen shi a hankali tace, "haba Usman, nad'auka zaka sassauta wannan damuwar da kake, nad'auka nasihar da mukaima jiya nida Inna da Hajjajo zata sa ka sassauta wa ranka, dan Allah kayi hak'uri ka ruggume k'addararka ka dena kukan nan haka, addu'a Hamman ka yakeso daga gareka a yanzu ba kukaba, kagafa d'anka yanzu yayi wayo yana buk'atar wasa , kuma kaga yafi sabo dakai kaduba yanda yake kallonka ya gane muryarka dayaji yake woige-woigen neman ka amma kuma saika sashi gaba ka rink'a kuka". D'an d'aga kai yayi ya kalli Umar Farouq da girman sa da wayon shi keba kowa sha'awa dan yarone bulbul dashi fari tas kamar balarabe ga dimple dake kumatunshi inka gan shi kace yayi shekara amma watan shi 7 ne, shi Kuwa Usman sauke ajiyar zuciya yayi sannan ya d'auki yaron ya rungume yana shafa bayan shi, Ita Kuwa Nanne kanshi ta shafa tace, "Allah yayi maku albarka". hawaye ya zubda masu zafi sannan yace, "Amin Nenne". Haka rayuwa taita tafiya da Ummul da dad'i ba dad'i dakuma samun kulawa ta musamman daga iyeyenta yayunta kaninta da uwa uba ya Usman wanda duk lokacin shi natane ita da yaron shi wanda komai nashi ke kanshi inko yajiyo kukan shi har yana gudu da tun tub'e dan so da k'auna, sau da yawa yakan cewa su Adam idan suna hira, "inajin nafison Faruq junior a kan kowa a duniya ciki harda Hamma na dan so kala da yawane a kan Junior son da nakewa mahaifinshi ma ya dawo kanshi". Daga b'angaren Mustapha kuwa abin ba a magana da duk k'arshen sati yana hanyar potiskum yayin da mahaifiyarshi ke rakoshi bayan sati biyu ko uku, Dr Bashir ma ba a barshi a bayaba domin kuwa baya wuce sati bai ziyarci Ummul da Umar farouq ba. Haka abin yake agun Inna da daddy abun saidai hamdala dan kuwa Ummul da d'anta suna ganin gata tako ina matsalar Ummul d'aya rashin abin kaunarta hasken idanuwanta Hamma Umar wanda har yau bata dawo dai-dai ba ita da Usman Ammi kuwa yanzu tasa dangana a ranta. Ranar wata asabar misalin k'afe hud'u na yamma ne Mustapha ya iso gidan su Ummul kamar yadda ya saba duk sati, da Aliyu yafara had'u a farfajiyar gidan yana zaune kan kujerar roba yana karatu cikin girmamawa yataso ya karb'i lodojin hannun shi yakuma gaida shi sannan yamai jagora zuwa palour sannan ya wuce ya sanar da Ummul, ba afi minti ashirin ba Ummul ta shigo sanye da hijabita k'ato har k'asa tana rike da Umar faruq da yaketa zullowa yanason sauka tai sallama ya amsa mata cikin kulawa sannan tasami kujerar gefe ta zauna, Farouq ko yanata kiciniyar sauka Mustapha yai d'an murmushi yace, "sauke shi mana". Bata d'aga kantaba ta sauke Farouq aiko kamar yana jira ya rarrafa da saurinshi kasancewar shi mai kuzari da lafiya kuma yana ji da k'arfi ya je wajen Mustapha, aiko shima hannu ya bud'e yana zuwa ya d'auke shi yana dariya tare da d'agashi sama yana sumbatar goshin sa, Sheshshek'ar kukan Ummul ne ya tsagaitar da Mustaphan daga wasan da yakema Farouq ya d'ago kan shi cikin damuwa da kid'ima a hankali murya can k'asa yace, "Khairi wallahi da kin san yadda nakeji akan kukan nan naki wallahi dakin taimaka min kin dena". sai kuma yayi shiru tare da cire glass d'in idon shi ya mik'awa Farouq da yaketa kokuwar karb'a sannan yaci gaba da cewa, "Ummul bana jurewa banajin dad'i kuma bana iya bacci ko cin abinci aduk lokacin da natuna wannan kukan da kike, kiyi hak'uri khairi dan Allah ki daure". Haka yayi ta aikin rarrashi kamar yadda ya saba duk sati dako duk yanda zaiyi Ummul bata cewa komai sai aikin kuka a haka ya zauna yana ta lallashin ta cikin salon tsumin tsohon so, Wani irin abune ya ziyarci zuciyar Usman daya shigo daga unguwa ganin motar Mustapha da yayi a cikin gidan wanda shima ya rasa dalilin hakan ya resa meyasa yake jin zafi a ranshi in Mustapha yazo gidan, da kyar ya tsaida motar shi ya bud'e cikin mutuwar jiki da sanyin gwiwa kai tsaye yanufi b'angaren su bedroom ya shige sannan ya fad'a kan gado yana kuka mai cin rai yana furta, "yazanyi yazanyi da raina, Allah ka ceceni ka kawomin d'auki Ummul har gobe ina sonki aurenki ne kad'ai zai bani damar kula da amanar d'an uwana Ummul ina sonki ina son d'ana Farouq bana son a rebamu". Shiru yayi dan yaji motsi wanda ya tabbatar mashi da akwai mutum a d'akin da sauri ya d'ago kai...... *Sadaukarwa GA Dr Umar Ibrahim Umar shuwa (Hamma Umar)* *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* page 3⃣3⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *MOH ALLAH WUJI FURD'ATA, MOH ALLAH HOKKI B'URI MOH BABA HOKKI* *Wannan shafi naku ne matan kirki masoyan kirki yan uwa a musulunce SADNAF tare da SURBAJO tawa ina Al'fahari daku Allah ya sanya alkhairi a rayuwarku da yaranku Allah ya raya mana yaranmu Yusuf namu ya auri ikram tamu muyi tuwona maina 🤝😍😘* *Y*a d'ago kanshi idanun shi da suka canza kala zuwa jawur ya sauk'e sure akan fuskar ya Adam, dayake tsaye ya hard'e hannayen shi a kirjin shi yana kallon shi cikin tuhuma, sai kuma ya tako a hankali jiki ba kwari yataho ya zauna kusa da shi, hannun yasa ya dafa kafad'ar shi yazuba mai ido cikin tuhuma da tausayi yace, "Usman me kake fad'a?". hannu yasa ya goge k'ollar daketa bin fuskar shi cikin sanyi yace, "bakomai Adam". "a a Usman kar muyi haka dakai dan Allah, kayi hakuri kad'auke ni matsayin Hamma Umar abokin shawara, meyasa zaka b'oyemin damuwar ka? nifa d'an uwanka ne kuma mai k'aunarka please ka fad'amin menene?". Zame hannu Adam yayi daga jikin shi cikin kauda kai yace, "Adam nacema bakomai". ido cike da k'ollah yana gir-giza kai yace, "naji Usman naji abinda kake fad'a fa, kayi hakuri kamin bayani mana". jajayen idanun shi ya zaro cikin gajiya da maganar yace, "Adam tashi kabar gurin nan tunda nacema ba komai ai ba komai d'in ne". sai da Adam ya mik'e tsaye sannan yace, "gaskiya akwai damuwa Usman kadai b'oyemin ne amma hakan bazai sa nabarka cikin damuwa ba dan haka zanje in fad'ama Abba abinda kunnena yajiye min". Yana kaiwa nan ya juya yafuce, shiko Usman ganin haka yabi bayan shi da sauri a palour ya sameshi yana shirin fita, da sauri ya kamo hannun Adam d'in kan kujere ya jawoshi suka zauna murya can k'asa yace, Adam please karka gayawa kowa maganar nan". ido Adam ya rumtse wasu hawaye masu zafi suka zubo a fuskarshi ranshi cike da tausayi Usman a hankali yace, "Usman meyasa kake son b'oye min matsalar ka wacce kasan zan iya magan ceta". shiru yayi cikin lumshe idanun shi murya can k'asa yace, "Ina son Ummul Adam ina sonta ina son zama da ita da yaro na, bana son b'acin ranta bana son suyi nesa dani nafi son na renesu da kaina nafi son na kula da jinin Hammana da kaina bana son Farouq yayi agolanci bana kuma son rabashi da mahaifiyarshi bana son ya taso kamar yadda nida Hamma na muka taso ba Uba uwar kuma bata kusa damu bana so Farouq ya tashi a gida na kuma ace ba mahaifiya shi bace ta reneshi, kuma bana son b'acin ran Ummul ko abinda zai tayar mata da hankali gashi ta tsani aure bata son a mata maganar aure sai tayi ta kuka kukanta na sani cikin k'unci sai in rink'a ganin na gaza samawa iyalen Hammana farin ciki ne bana son b'acin ran ta ina jin ciwon biyu in tana kuka, Adam kamin alkawarin zaka rik'e min wannan sirrin nawa muyita addu'a har muga abinda Allah zaiyi mana da ikon shi a hankali farin cikin Ummul zai dawo". Juyowa Adam yayi cikin kuka ya rungumi d'an uwan nashi suka cigaba da kuka mai cin rai har zuwa d'an wani lokaci, a haka sunata kuka babu mai rarrashin wani haka suka gaji suka kai shiru, a hankali Adam ya kwantar da kanshi akan cinyar Usman d'in murya na rawa yace, "Ya Usman to haka zamuyi ta zama da wannan damuwar? har sai yaushe farin cikin mu zai dawo? shin fushi mukeyi da hukun cin mahaliccin mu kenan? shin bazamu gane cewa wannan rubutaccen al'amari ne daga Allah ba ko so muke mu raunata imanin mune haka zamu rayu kullum ba walwala, addu'ar da muke yiwa Hamma itace so mu daure mu bar kuka, ka auri Ummul ka reni Farouq da kanka tunda aure dai abin yine tunda da lafiyar ka?". Cikin sanyi da rauni ido cike da k'ollah, Usman ya shafa kanshi murya a raunane yace, "A a Adam bazamu zauna cikin k'unci ba done wata rana zamuyi farin ciki ai ya rigada Allah ya sama bayinshi mantuwa a ransu ba dan mantuwar da Allah ya sa mana ba da ciwon mutuwar wani zai jawo na wani ba dan danganar da Allah ya samin ba da ciwon mutuwar Hammana ya kasheni Adam kalli rubutaccen al'amari yau ni Usman mai hujejjiyar zuciya ina raye nida kowa ke zatawa mutuwa amman bata d'aukeni ba sai ta d'auke Hamma na wanda ba'a tuna maiba kuma ta hanyar da ba zato ba tsammani, Adam zamuyi ta addu a Allah zai mana maganin damuwar mu nagode naji dadi da samun d'an uwa mai rik'emin sirrina". Murmushi k'arfin hali Adam yayi sannan ya tashi yakoma bedroom ya fad'a bandaki ya sakarma kanshi ruwa, shiko Usman tashi yayi ya d'auko qura'an ya fara karatu cikin rauni da halarto da kushi'i tun yana yi yana zubda k'ollah har yaji zuciyar shi ta fara sanyi a hankali yaji k'unshin ranshi na gushewa, Qura'ani kenan mai girma maganin hawan jini maganin ciwon suga maganin jutar daji maganin Iblis da junnu da mugun bani Adam duk tsanani sauk'in shi nan cikin qura'ani sai dai in mutum bai lizamceshi ba. A parlour bak'in Kuwa Mustapha yanata aikin rarrashi a hankali ya taso yamatso kuda da kujerar da Ummul ke zaune ya zama yayi a gaban ta ya tonk'oshe k'afafun shi a cikin sanyin murya da tausasawa yace, "Ummul narok'eki kiyi hakuri kiji tausayi na ki sassautawa zuciyarki Khairi na kinfi kowa sanin yanda nake jinki a zuciya ta kukan ki yana k'onamin zuciya, kiyi hakuri kibani dama indawo miki da farin cikin ki Ummul ina sonki wallahi ina miki son da bana yiwa kaina Ummul rayuwa ta zata cikane kawai idan ina tare dake". Yanda yaga Ummul ta d'ago kanta cikin razana ta zuba mai manyan idanuwan ta da suka canza kala zuwa jawur yasa yai shiru ya zuba mata nashi idanun. Kalmar da Ummul taso fad'amai ta "bana sonka". ce ta kasa fito sakama kon tunawa da tayi da yanda taita furtawa Hamman ta kalmar wadda gashi yanzu tazamo mata sana diyyar b'acewar farin cikin ta a yanzu wanda bata tab'a yin nadamar wani abu a duniya kamar shiba, wani irin abune yataso mata ya tokare mata zuciya dakyar ta samu ta fisgo wani irin nannauyan ajin zuciya wanda ya fito da kuka mai k'una da zafi, ido a rufe ta rab'a gefen Mustapha da sassarfa tayi cikin gida, shiko Mustapha binta yayi da kallo harta fita sannan ya juya jiki babu k'arfi ya koma yad'auki Umar Faruq daketa wasanshi ya rungume yanajin wani irin so da kaunar yaron da mahaifiyar shi Ummul a ranshi sannan ya fito, Ita kuwa Ummul da gudu tafad'a cinyar Ammi tasaki kuka mai k'arfi jikinta duk na rawa, a gigece Ammi take tabbayar ta, "menene Mama na kiyi hakuri ki fad'amin mana meke faruwa?". Aliyu daya biyo bayanta ya zuba gwiwa a k'asa shima hawaye na bin fuskarsa ganin yadda Ummul ke wani irin kuka kamar ranta zai fita ko ina jikinta rawa yake, Nanne da ya sadiq suma da gudun suka shugo, Nanne ma tuni jikinta yad'au rawa zuciyar ta na bugawa ganin yadda Ummul tafita hayyacin ta dan kuka, ya Sadiq d'in ne ya matsota ya dago kafad'arta ya janyota jikin shi, aiko shima tuni zuciyar shi tayi rauni dan jin zafin jikinta da yanda jikinta ke rawa cikin sassauta murya yace, "Ummu na meya sameki ne?". K'ara tusa kanta tayi a cikin cinyoyinta ta k'ara sakin kuka mai k'arfi, Su Usman kuwa sai yanzu suka fito shi da Adam zasu shige part d'in Nanne, a farfajiyar gidan sukaci karo da Mustapha wanda ke rik'e da Umar Farouq, aiko yana ganin Abban shi Usman ya mik'o hannu shima Usman da murmushi yakai hannu ya karb'e shi sannan ya mik'ama Mustapha hannu suka gaisa cikin sakin fuska sannan suka gaisa da Adam yai musu sallama ya shafa kan Farouq tare da cewa, "bye bye bobona". Amman yajuya ya nufi motarshi cike da damuwa da kunar zuciya da jin zafin kukan da Ummul take yi. Su kuwa da sauri suka k'arasa bangaren Nanne jiki na rawa dan jiyo kukan Ummul da sukayi cikin k'unar rai da firgici Usman yake salati idanuwan shi sun rufe da kyar ya matsa jikin gini ya jingina yana sauke numfashi da kyar, ya Adam ne ya k'arasa gurin ya dafa kafad'ar ya Sadiq yace, "meke faruwa ne? meya sameta?". Kai kawai Sadiq ke juyawa dan haka Adam ya tsuguna ya d'auko Ummul daga jikin Sadiq ya gyara zama ya kuma matsota jikin shi sannan yasa hannu ya kamo fuskarta cikin rarrashi yace, "k'anwata kiyi hakuri ki sanar damu damuwar ki, kinga dukkan mu hankalin mu ya tashi, kinga yaronki yana kallonki kada kisa mufara zargin kanmu da rashin cikawa Hamman mu al'kawarin rashi baki kulawa, daure ki fad'a mana". sai kuma yasake sa hannu ya d'ago kanta yace, "kallemu Ummul dukkanmu zamu iya jure duk wani abu dan mu samar maki farin ciki ki daure ki fad'a mana koma menene?". Cikin kukan ta sauke nan nauyar ajiyar zuciya sannan tasake cusa kanta jikin Ammi murya na rawa tace, "Ya Adam dan Allah ka hana Mustapha zuwa gidan nan, wallahi bana sonshi, ba zan sake son kowaba bayan Hamma na bazan so kowaba bare ma Mustapha wanda soyayyar sace tasa na kasa ganin soyayyar da Hamma na yake min na tsani Mustapha dan shine sanadin bijirewa Abbana duk da bai zugani ba kuma ya nusar dani da inbi zabin iyayena amman taurin kai da zuqar shaid'an tasa nak'i masoyi na auren Hamma na ya isheni ni nagama aure bana son ganin shi bana son ganin fuskar shi,bazan aure shiba bazan auri kowaba a barni da auren Hamma na dan Allah". Kafin kowa yayi magana Usman dake tsaye jikin bango ya sauke ajiyar zuciya ya mik'awa ya Sadiq dake kusa dashi Faruq sannan ya matsa kusa da ita ya tsugunna ya kamo hannun Ummul itama d'ago kai tayi tana kallon shi cike da rauni da tsantsar nadamar illar rashin bin umarnin iyaye tace, "Ya Usman". da sauri yasa yatsa akan lips d'inta dasu kayi jawur sabida kuka a hankali yace, "Na sani Ummu na kiyi hakuri zamuyi duk yadda kike so amma saikin daina kukan nan sai na dena ganin hawayen ki". Kai ta d'agamai sannan yayi murmushi yace, "Yawwa k'anwata Allah miki albarka". dukkan su suka amsa da "Amin". Mustapha kuwa yakasa zaune yakasa tsaye zuciyarshi takasa samun sukuni yanajin bazai iya rayuwa inba Ummul haka nan yayita fama da tunani da damuwa kullum saiya kira wayar Aliyu yace yakai ma Ummul suyi magana, amma idan Aliyu ya kawo sai tak'i karb'a shima wani lokacin baya kawowa sai yace tana bacci dan shima bayason damuwar ta. Farouq nada watanni 17 ya k'ara wayo da kyau yana yawon shi ko ina sannan Ummul ta yayeshi, Ummul da ya Usman kuwa kullum shakuwar su k'ara k'arfi take indai yana gida bai fitaba to suna tare a palour Nanne ko na Hajjajo, Ummul bata tab'a rasa wani abuba dan koda yaushe Usman na cikin tarairayar ta da tambayar me take buk'ata inko ya fita zai dawo to da tsara barta kala-kala yanzu Farouq ya cika shekara biyu har ya shiga na uku. Wata ranar Jimmy'a da yamma Abba da Daddy suka shigo palour Hajjajo suka inda suka sami yaran nasu dukkan su suna ta hira suna shiga Farouq yaje gaban Abba da gudu ya taho yana oyoyo Abba, cikin happy Abban ya bud'e hannu wan shi Farouq ya fad'a ya d'agashi sama yace, "sarkin wasa ya akayi". Daddy ne yayi murmushi yasa hannu ya karb'e shi tare da yace, "zo nan in tafi dakai gidana". wuri suka samu suka zauna bayan sun zauna ya Usman ne yafara gaida su suka amsa sannan kowa ya mik'a tashi gaisuwar. saida suma suka gaida Hajjajo sannan Abba ya kalli Usman cikin kulawa yace, "Usman naji d'azu wani abokina yana waya da yaranshi yana fad'a musu ankirashi ance anfara saida admission form na NCE a nan FCE(T) shine nace inna sameku zamuyi shawara tunda k'anwarku tak'i maganar aure ko zaku saya mata saita fara kara?". gyara Zama Usman yayi sannan yace, "to Abba zamuyi shawara insha Allahu zamu sanar daku duk abinda mukayi mungode". Daddy ya jinjina kai yace, "to Allah yayi maku al'barka". Dukkansu suka amsa da "amin". sannan suka d'an tab'a hira jimawa kad'an suka tashi suka fita, suna fita Ummul da zuciyarta tafara bugawa tunda Abba yafara magana ta mike jiki ba kwari ta fita, Usman ma mik'ewa yayi yabi bayanta Adam kuwa ya zuba musu idanu cike da tausayin yadda Usman d'in yake fama da soyayyar k'anwar tashi. Shiko Usman yana shiga yasame ta zaune kan kujera yasami gefenta ya zauna a hankali cikin tattausan lafazi yace, "Ummuna meyasa su Abba na fita kika taso kika baro gurin mutane kikazo nan ke kad'ai ? kinsan bana son damuwar ki kuma banaso ki b'oyemin komai". d'ago kai tayi tare da yin rau-rau da ido alamar zatayi kuka murya na rawa tace, "Ya Usman wlh bana son karatun na hakura da komai a rayuwa ta zan zauna in dauwama ina yiwa Hamma Umar addu'a, banajin dad'in komai a rayuwa ta bani da wani sauran farin ci daya wuce inga ina yiwa Hamma na addu'a, dan Allah kacewa Abba bana son kara tun wanda nayi a baya ya isheni, yayi hak'uri ya barni". tana gamawa ta kwab'e fuska zatai kuka, Da sauri yasa hannu ya tallabo hab'arta cikin tattausan lafazi yace, "farin cikin ki zai dawo bazamu dawwama cikin k'uncin rayuwa ba Ummuna ki bani dama ni Usman zan dawo da farin cikin ki ta yadda Hamma na zaiyi Al'fahari dani". lallashinta ya rink'ayi da kalamai masu taushi da sanyaya zuciya, itako Ummul sai cigaba da zubda k'ollah take tana d'an narkewa, dakyar yasamu ta hakura sannan yace, "ba wanda zai kaiki makara tar anan zamuyi zaman mu ko har sai Allah ya dawo mana da farin cikin mu?". Dakai ta amsamai sannan ta matsoshi ta kwantar da kanta a kafad'ar shi numfa shin ta na fita a hankali tuni Usman yafara zaucewa a hankali yakai hannu ya d'an tureta sannan ya rumtse ido yana shafa kanshi zuwa wuyan shi yanajin kaunar ta na tsuma ko ina na jikin shi, cikin sanyi yace, "Allah ya d'ayyiba". kai ta d'ago ta zura mai ido cikin murmushi tace, "Ya Usman ina son ka". ido ya bud'e da sauri sannan ya k'ara matsowa kusa da ita a hankali yace, "Da gaske kina sona?". kai ta gyad'a mai tare da kad'a harce tace, "ehh mana ina sonka". kai ya juya cikin k'arfin hali yace, "Allah ya d'aiyiba nima ina sonki so na hak'ik'a, Ummu ina sonki zan aureki mu reni Farouq da hannun mu, ina sonki ina shawa'awar rayuwa da ke a k'ark'ashin inuwar aure bisa sunna Ummu ina sonnnn ki zan dawo miki da farin cikin ki nima ki tallafawa rayuwa ta". Ido ta zazzaro tare da fuska tsuke cikin zubda k'ollah murya a carke tace, "Na shiga uku ya Usman". sai kuma ta mik'e da sauri ta gudu d'akinta ita da Ammi, a haka tasu hirar ta watsent a palour Nanne, inda ita ko Nenne duk taji abin da suke cewa dan tana cikin kitchen, shiko a nan ya zauna ya kasa tashi inda ya sametan, sai lokacin sallah la'asar yatashi tafiya masallaci, sai ya shiga d'akin nata dan yasan Ammi tana parlour Hajjajo, yana shiga ya d'ago ta yasa hannu ya shafa fuskarta yakai yatsan shi kan lips d'inta ya lumshe idanuwan shi da suka canja launi sannan ya juya ya fice tare da cewa, "Ina son ki Ummu so irin na aure ban saniba ko nima zaki tsanene kamar Hamma sai randa na mutu ki soni". yana fita itema tashi tayi tashige toilet wonka takeyi tana kuka ta rasa matsayin Usman a gareta shike tayata batun kartayi aure yau kuma shike cewa zai aureta me sunanta inta aureshi ta auri yaya ta auri k'ani yau ya Usman ke mata zaurancen saida Hamman ta ya rasu take sonshi a haka tayi ta kokenta, sannan ta fito dan yin Sallah. Ranar wata lahadi Ummul na kwance a cinyar Aunty Halima datazo tun safe tanayi mata kitso, Aliyu ne ya shigo ya zauna gaban Ummul yace, "Aunty Ummul Dr Bashir yazo yana palour yana jiranki, kamar bazata amsaba saida ta d'au lokaci sannan ta ce, "ina zuwa, ina Farouq fa?". cikin jin dad'i Aliyu yayi y'ar dariya yace, "ai muna ball yana ganin motar yatafi da gudu saida na rik'eshi motar ta tsaya yana fitowa na sakeshi yatafi da gudu gunshi". Aunty Halima ce ta d'anyi murmushi tare da cewa, "ya ganeshi kenan?". Sadiq ne dake kwance kan kujera yana latsa wayar shi yace, "ai Farouq ko sau biyu kazo gidan nan a na uku sai yanuna ya ganeka, balle Hamma Bashir da duk sati sai yazo indai yana gari". murmushi sukayi baki d'aya sannan ita kuma Ummul ta d'auko hijabi tasaka tafita. zaune tasame shi a k'asan carpet yabud'e ledar da yazo da ita yana b'arewa Farouq sweet din dayasaba kawo mishi, sallama tai tasami guri ta zauna sannan cikin nutsuwa ta ca, "ina wuni?". da fara'a d'auke a fuskar shi ya d'ago kai yace, "lafiya Ummul khair ya mutanen gida?". Kanta a k'asa tace, "suna lafiya". shiko Farouq cikin kici-kici yasa hannu ya k'ara d'aukan sweet d'in nashi sannan ya mik'e cikin gwarancin sa na yarinta yace, "Abpa Ayeeh". gaba d'aya ya sasu dariya har Ummul saida tai d'an yi murmushi balle Dr Bashir dayaketa kyal-kyalawa shiko cikin gudu dib-dib da kuzari yayi waje abin shi yana, "Abppa Ayeeeh jo cuwit". Cikin son yaron Dr Bashir ya dawo da kallonshi ga Ummul yace, "Wai me yace ne?". k'asa tayi da kai a hankali tace, "cewa yayi Bah Ali". dariya yasa keyi yace, "Aliyu zai kaiwa kenan?". da kai ta amsamai, murmushi yayi tare da sauk'e numfashi sannan ya tashi yakoma kan kujera ya zauna ya dai-dai ta nutsuwar shi sannan ya fuskanci Ummul cikin kulawa da wata irin murya da shima ya rasa inda ya samota yafara magana, "Ummul khair yau zuwana yanada banbanci da kowanne zuwa da nakeyi, sabida wannan zuwan ina tafe da magana mai muhimmanci wadda ta dad'e a zuciyata tana hanani sukuni". tunda ya fara magana Ummul ta tsinci kanta cikin fad'uwar gaba mai tsanani, shiko bai gusheba yaci gaba, "Kiyi hakuri ki daure da kisaurari kalamai na sannan kuma zan baki lokaci da zakiyi tunani akai, amma dan Allah Ummul kada kisa damuwa a ranki akan abinda zakiji sannan dan Allah ki tausa shi zuciyar ki saboda kukanki yana k'onamin zuciya". saida yad'anyi shiru kamar mai tunani sannan yace, " Ummul ina sonki, inason kizamo uwar y'a y'ana, ina sha awar zama dake a k'ar k'ashin inuwar aure". Duk kalaman da yake yak'i kallon Ummul, itako tuni jikin ta ya mutu tunaninta ya tsaya cak tanajin wani irin zafi a ranta. Katseta yayi da cewa, "kiyi tunani akan maganata zan dawo naji amsa". yana fad'in haka ya mik'e jiki a mace shida kanshi ya tuno abokin shi a haka ya fice, yabarta tana share k'ollah, yana fita a farfajiyar gidan yaga Usman da abokinshi Nura cikin jin dad'i suka fara gaisawa anan Ummul ta fito daga palour ta wucesu tunda ta wuce Usman hankalin shi ya koma kanta dan yadda ya ganta ya tabbatar akwai matsala dan haka sunayin sallama da Dr Bashir ya kalli abokin shi Nuru yace, " kajirani a d'aki ina zuwa". Bai jira amsar Nuraba ya shige cikin gidan da sauri, A bakin k'ofar parlour Nenne ya tsaya cake Dan abinda kunnen shi yajiyo maine ya hanashi k'arasawa ciki ya jingina jikin k'ofar yana sauraren Ummul data fad'a cinyar Aunty Halima tana cewa, "ku gaya musu banason kowa bazan auri kowaba bazan iyaba dan Allah kuce su kyaleni". Ya Sadiq dake kwance kan kujera ne ya mik'e zaune cikin b'acin rai yace, "wlh banason wanda muna zaman mu zaizo ya tada hankalin yarinyar nan, mutane basusan damuwar mutumba ke kuma Ummul ai aure wajibi ne a gareki zaman shekara biyu da wata 9 ya isa haka dole kiyi aure kam". sai kuma ya taso ya matso inda Ummul d'in take ya d'ago kanta yace, "kyaleshi Ummuna kiyi shiru kinji". sannan ya mik'e zai fita Usman dake lab'e yana sauraronsu juyowa yayi da sauri cikin k'unar zuciya yanufi b'angaren su yana tafiya da kyar. A palour ya sami Nura da Adam suna hirar ball yayi sallama ya fad'a kan kujera ya fidda dogon tsaki ya lumshe ido, Nuru ne dake kusa dashi ya dafa kafad'ar shi yace, "aboki na ya a kayi ne? ". d'ago kai yayi ya kalli Nura sannan ya maida kallonshi ga Adam daya zuba mai ido yace, "Wai dan Allah yazanyi ne mekuma yake shirin samuna wacce irin rayuwa zanyine?". Adam cikin yanayin tausayawa d'an uwan na shi yace, "Wai tambayoyin nan na meye haka? me a kayima?". saida ya rik'e kirji sannan yace, "Adam wai Dr Bashir ne yacewa Ummul yana sonta". Adam da shima yaji bugun zuciyar shi ya k'ara k'arfi yace, "Usman dan Allah ka ka gayawa Abba ko kuma kabarni in fad'a musu Abban kana son Ummul Insha Allah nasan nanda wata biyu Abba zai aurama ita." da sauri suka d'ago kai cikin sanyi dan ganin wanda ya shigo...... *Sadaukarwa ga Dr Umar Ibrahim Umar Shuwa( Hamma Umar)* *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 3⃣4⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RESA TUM MARA TUM HEB'A TUM SEYA TUM JOD'E BE GAYOMA WOD'I NAFU* *I*do suka zubawa Daddy tare da shafa Kai da sauri Usman ya sauk'e kanshi k'asa, Adam kuma ya yunkura zai tashi sai kuma ya koma ya zauna ganin shiko Daddy ya saki labulen daya d'ago ya juya ya fice, batare dayace musu komai ba, saida suka tabbatar da ya tafi Adam yatashi ya lek'a sannan ya dawo yazauna cikin zolaya yace, "Allah yasa Daddy yaji zancen da mukai". Nura ya gyara zama cikin wasa yace, "basai in fara kiran abokina da angoba". dukan wasa Usman yakaimai yana murmushi. Shiko Daddy kai tsaye gidan shi ya wuce haka ya kwana da tunanin abinda yaji yaran nasu na tattaunawa wannan yasa gari na wayewa tun da suka fito daga masallaci suka d'unguma b'angaren Hajjajo, samunta sukai tana lazimi a kan sallaya ganin haka suka samu gefe suka zauna har takai inda zata tsaya ta d'aga hannu sama tai addu'a suka shafa tare sannan suka gaisa cikin so da k'auna, kallonsu tayi da alamar tambaya, Daddy ne ya sake tonk'oshe k'afa yafara magana cikin nutsuwa yace, "Ummie jiya bayan nafita daga nan sai naje b'angaren yaran nan dan zan aiki Adamu to ina zuwa kunnena yaji Adam yanata rok'on Usman, wai yabar shi ya fad'a mana yanason Ummulkhair". da mamaki Hajjajo ke kallonsu shiko Abba cikin jin dad'i yace, "Alhamdullah Masha Allah, in haka ta kasance tabbas muna farin ciki dan naji dad'in wannan magana sosai". Sannan ya maida duban shi ga Hajjajo da itama da ganinta kasan taji dad'in maganar yace, "Ummie kinji ko? yanzu izininki kawai muke nema dan aiwatar da abinda ya dace tunda dama ita Ummu tak'i kowa kuma inaga shak'uwarsu da Usman zatayi tasiri wurin sa ta amince dashi". Ita love Hajjajo sunkuyar da kai tayi tana b'oye k'ollar data fito mata wadda ta fito da manufofi biyu tace, "namuku izini, kuyi duk abinda ya dace, Allah yai muku albarka yasa k'udirin mu yazamo alkhairi amman a nemi yardar Ummu dan yanzu ita ba budurwa bace ku bata dama tayi zab'in da ranta keso gudun kar a maimaita abinda ya faru a baya". had'a baki sukai suka amsa da, "Amin". sannan Daddy ya kuma gyara zama tare da cewa, "Insha Allah baza a maimaita abinda ya faru a baya ba dan tabbas munga illar auren dole da illar auren cushe duk da muna da damar da zamuyi mata zab'i kuma mun mata amman zuciyarta bata soba gashi sai a k'arshe rayuwar ta katse mana cikin nadama ita kuwa sanin din kafiyarta ta d'auke farin cikin rayuwar". cikin sanyi Hajjajo tace, "Allah ya tsare na gama". "Amin Amin Ameeeeeeeeeeeeeeeen ya rabbil izzati ". suka amsa a tare, Matsowa Abba ya sakeyi kusa da d'an uwan shi yace, "Hussain ina nemawa yarona Usman auren yarinyarka Ummulkhair". Hannunshi Daddy ya rik'o cikin jin dad'in yadda d'an uwan nashi kemai kara akan yaransu yace, "Nabaku nabaku Ummulkhair bisa amana da k'auna Allah yasa ayi cikin sa'a kuma Allah ya sanya alkhairinsa". Hajjajo da Abba suka amsa da, "Ameen". Haka sukai ta tattauna yanda zasu tsara, daga k'arshe Abba ya d'auko wayar shi ya latsa yasa a kunnen shi, Usman dake zaune kan sallaya yaji wayarshi na k'ara yamik'a hannu Adam dake kan gado kwance yasa hannu yad'au wayar ya mik'amai dasauri Usman ya amsa kiran yasa a kunne ya russuna kamar yana ganin me kiran yace, "Assalamu alaika, Abba ina kwana?". Adam dajin Usman yace Abba ya mik'e daga kwanciyar da yake ya zauna tsakiyar gadon ya zubawa Usman ido wanda ya saurara yana jin abinda Abban ke fad'a yana jiran karin bayani, "To". Usman yace sannan ya sauke wayar ya kalli Adam yace, "Abba na kiranmu a palour Hajjajo". daga haka ya tashi ya ajiye wayar yafice, cikin happy yayi d'an k'ara tare da cewa, "yes". sannan ya sakko daga gadon yafita cikin zumud'i da addu ar Allah yasa abinda yake zato ne. A palour Hajjajo Usman yayi sallama suka amsamai yasami k'asa gefen Abba ya zauna sannan Adam ma ya shigo yasami gefen Daddy ya zauna,Usman ne yafara gaida Hajjajo sannan yakuma gaida iyayen nashi sannan Adam ma yayi tashi gaisuwar sai kuma suka saurara cikin nutsuwa Abba yafara magana dacewa, "Usman banji dad'in yadda kuka waremu kaida d'an uwanka Adam kuke b'oye damuwarku ku kad'ai ba, duk da nayar da komai lokacine kuma ga lokacin yayi dan haka inaso ka shaida sannan d'an uwanka ya shaida kamar yadda mahaifiyata ta shaida d'an ni mahaifinka na nema maka auren y'ar d'an uwana Ummul khairi". sanyi, dadi, fad'uwar gaba gabaki d'aya suka ziyarci zuciyar Usman da haka ya kasa jin komai da gane komai da suke fad'a, Abbane ya dawo dashi daga duniyar daya tafi ta hanyar dafa kafad'ar shi yace, "Allah yamaka albarka Allah ya baka ikon kula da d'an d'an uwanka". Cikin nutsuwa da kwantar da kai k'asa Usman murya a sanyaye yace, "Daddy nagode Allah ya saka da alkhairi". sai kuma yakai dubanshi ga Adam da dad'i ya cikawa ciki yanata murmushi yace, "Adam katayani godiya gun Abba". Shiko Adam washe baki yayi kai kace shi akaima kyautar matar yace, "Daddy mun gode Allah ya k'ara girma". Usman yasake matsawa kusa da Abban yai k'asa da murya cikin biyeyya da yace, "Abba nagode Allah ya k'ara arzik'i, amin godiya gun Daddy". sai kuma ya d'anyi shiru kai ya kuma sunkuyarwa a hankali yaci gaba da cewa, "Sannan inaso in nemi wata alfarma agurin ku". Abba ne ya sa hannu ya shafa kan Usman yace, "a shirye muke mu samar maka da farin ciki kada ka damu ka fad'i duk abinda kake so insha Allahu zamuyi maka danko munada yak'inin bazaka nemi abinda bazamu iyaba". sauke ajiyar zuciya yayi sannan murya na rawa yace, "Abba dan Allah kumin alfarma kubani dama in nemi yardar Ummul, da kaina kar ayi mata dole a bari ta amince dani da kanta, Daddy inaso inganta cikin farin ciki sannan hakan shizai bani damar k'arasa kula da ita da yarona cikin jin dad'i, ina nufin zatafi jin dad'i idan anyi komai da yardar ta". Shirune ya ratsa palour na y'an mintina sannan Daddy yai gyaran murya tare da cewa, "Usman Allah yayi maka albarka, hak'ik'a wannan kalaman naka sunkai ayi maka uzuri kamar yadda ka buk'ata kuma hakan ya dad'a tabbatar mana da cewa kaine kad'ai zaka iya dawo mata da farin cikin ta, Allah yamaka albarka Allah yabaka ikon kulawa da iyalinka". "Amin". Suka amsa sannan Abba yace, "to duk abinda zance Daddyn ku yafad'a dan haka indai babu wata maganar sai kuje kuyi abinda zakuyi, Allah yayi muku Albarka ya jikan yayanku yakai haske kabarin shi". duka suka amsa da, "Amin". Daddy yace to Adam kayi mana addu'a mu tashi, daga haka taron ya tashi kowanne zuciyar shi na cikin nishad'i. Suna fita Adam ya kama hannun Usman yace, "congrat bros". Murmushi yayi yace, "nagode". Adam yasake matse hannun Usman dake rik'e a hannun shi yace, "nidai naso kabari ayi auren nan kasan yadda Ummul take balle yanzu yaza ai kace saida amincewar ta". a hankali ya janye hannun shi ya shafa kanshi ya kalli Adam cikin lumshe ido da sauk'e sassanyar numfashi yace, "Adam hak'ik'a inason kasancewa da Ummul ina son rayuwa da ita k'ark'ashin inuwar sure, amma kasani a yanzu soyayya hud'u nake mata, nafarko inamata so irin na ma a bota soyayya da kauna wanda Allah ne ya dasamin hakan a zuciyata, na biyu inason Ummul soyayya ta yaya da k'anwarsa, na uku itace abinda Hammana yafiso da k'auna, sannan itace tafara haifamin d'ana jinina, kaga wad'annan suke jana kuma suke bani tabbaci da kwarin gwiwar insha Allah zanyi nasarar samar mata farin cikin data rasa a baya". ajiyar zuciya yayi sannan yacigaba da cewa, "Zan jure duk wata damuwa akan haka, nasan burinka insami farin cikine amma inaso kacigaba da tayani addu'a Allah ya sanya sona a zuciyar Ummu". Magan ganun Usman ne suka kashe wa Adam jiki ya sa hannu ya rungumo shi suka rungumi juna suka juya zasu tafi b'angarensu Keenan, muryar Nanne c ta tsai dasu suka juyo inda take, ita ko cikin jin dad'in ganin su a haka tace, "y'ay'an Abba me kuka samu ne? na ganku a cikin nishad'i". K'asa sukai suka tsuguna a tare suka ce "ina kwana". Ammice ta amsa da, "lafiya lau". Kasancewar indai Ammi naguri Nanne bata amsa gaisuwar da za ai daga farko, sannan suka sake gaida Nanne ta amsa cikin sakin fuska tace, "kuje abinku muma zamu gaida mai sunan Ummul ne". Da haka suka shige sukuma suka kama hanyar b'angarensu. Dab da zasu shigene Usman yasaki hannun Adam daya rik'o yace, "kaga jeka ni bazan iya komai ba saina dubo Noor hayati name da my son". dariya Adam yasa harda rik'e ciki, shiko Usman ko kallo bai ishe shiba ya juya yai tafiyar shi. Hargowar Farouq yajiyo tun kafin ya shigo, yana k'arasowa ya sauke idanuwan shi kan Ummul dake zaune a bakin gado rik'e da rigar Farouq a hannu ta shagwab'e fuska kamar zatai kuka, inda take kallo shima ya kalla Farouq ne tsaye ya mak'ale kafad'a ya turo baki gaba yana zare ido, abin nasu dariya yaso bashi amma saboda gudun rigimar Ummul ya b'oye dariyar yazauna bakin gadon kusa da Ummul yace, "meya had'aku ne?". Kafin tai magana Farouq ya taho yafad'a jikin Usman yace, "Abee imma ne". k'ara rungume shi yayi a jikin shi yace, "Ummuna wai menene?". Itama k'ara shagwab'e fuskar tai tace, "tun dazu kowanne kaya na d'auko sai ya gudu yace bashi ba ni har nagaji". Murmushi Usman yayi yana jinjina aikin gaban shi na rarrashin y'an shagwab'a biyu sannan yasa hannu yakarb'i rigar daga hannun Ummul yace, "yaron kirki yi hakuri kasa wannan yanzu anjima kad'an sai in canja maka wasu ko?". d'aga kai yayi yace cikin gwaranci, "ambuma". hannu Usman ya mik'o ya mak'ale yatsu guda biyu yace, "e". aiko dariya Farouq yasaka sannan yasa yatsanshi tsakanin na Abeen nashi ya raba yatsun da Usman d'in ya had'a, sannan ya mik'a kai Usman ya sakamai rigar yajuya ya fice da gudu, ido suka rakashi dashi sannan Ummul tasuke ajiyar zuciya tai k'asa da kai tace, "Ina kwana". Ido ya zuba mata na tsahon 20 second sannan yace, " waya ce maki a haka ake gaida masoyi?". d'an turo baki tayi ta turo lips d'inta gaba ta mik'e zata fice daga d'akin, cikin zafin nama ya rik'o hannunta abinda yajine ya ratsa dukkan sassan jikin shi yasa yayi saurin sakin hannun nata itako tacigaba da tafiya, ganin hakan ya dafe kirjin shi da hannun shi d'aya yace, "washh". da sauri ta juyo ta dawo kusa dashi ta zauna tad'ora hannunta akan nashi tai rau-rau da idanu kamar zatai kuka tace, Ya Usman meke damunka? k'irjin ko? ". zame hannun ta yayi daga nashi yace, "so, soyayyarki ce take damuna Ummul soyeyyar kice take son min illah a zuciyata da jikina". Yanda ya kafeta da idanuwan shi masu zuba kasala yasa tai k'asa dakai ta marai raice fuska cikin sanyin murya tace, " dan Allah kadena min haka kaga kaban tsoro nazaci ciwo kakeji". murmushi yayi cikin jin dad'i tare dayi mata wani solon kallo mai cike da k'auna sannan yace, "Ummuna bakyaso inji ciwon ne?". Dakai ta amsamai alamar "eh". sannan ta tashi zata fice, da sauri ya taso yasha gaban ta ita kuwa ta rink'ayin baya-baya har ta isa jikin gini, ido ya tsura mata cikin laso lips enshi murya can k'asa yace, "Ina sonki so mai tarin yawa ina son rayuwa dake da Farouk na wuri d'aya ki kijik'ana ki tausayawa tuzurun yayanki Ummul na gaji da zama ba mata na matsu da yin aure ki tausayi min nida Farouq kar muyi maraici biyu ba Hamma na kema kuma kiyi nesa damu baza muji dad'in rayuwa ba". k'ara matsowa kusa da ita yayi cikin yin k'asa da murya yace, "Ummuna ina son aure wallahi na fa gaji da zaman gidan ina son mace kusa dani hak'uri na ya fara gazawa kiyi hak'uri ki yarda dani ki bani dama zan dawo miki da farin cikin ki kinji Ummuna". rab'awa tayi gefen shi cikin jin tsananin kunya da tsoron ya Usman d'in dan ta lura baida sauk'i ficewa tayi ta barshi a d'akin, shiko murmushi yayi yamik'e yafice. A ranar bayan ya tashi daga aiki, kai tsaye ya wuce Ahlul bhait communication ya seyowa Ummul d'inshi waya k'irar Iphone 6, sannan ya nufi gida yanajin farin ciki sosai a ranshi dan ya tabbatar ta woyar zai k'ara samun damar isar da sok'onnin soyeyyarshi. A gida kuwa yana isa kai tsaye part d'in kakarsu ya nufa, zaune ya samesu a palour Hajjajo yana shiga ya d'an rusuna ya gaida Hajjajo da Ammi da Nanne, sannan ya zauna a k'asan carpet, Sadiq ne yafara gaida shi sannan Aliyu Ummul ce k'arshe sannan ya dubi Nanne yace, "Ina Farouq fa? Murmushi Nenne tayi sannan tace, "Sun fita yanzun nan da Adam, kasan shi dason yawo". hannu yasa cikin ledar daya shigo da ita yaciro kwalin wayar ya mik'awa Aliyu dake kusa dashi yace mik'ama Ummul saika saka mata sim card d'in , murna Aliyu yake yasa hannu biyu ya karb'a ya mik'ama Ammi ta juyata tace, "to angode Allah yayi albarka". sai ta mik'ama Nanne tace, " Gashi asamana albarka Ummu na tayi woya". hannu tasa ta karb'a tayi godiya sannan tamik'a ma Hajjajo, da sauri Hajjajo takama kwalin da kokawa, sai kuma Aliyu yayi saurin kwacewa yace, "ke tsohuwa karki mana b'arna fa ya Karo'arma sai da dambe". Yamutse fuska tai tace, "garani ai". dariya sukayi sannan Ammi ta tashi tana gaba Nanne na binta suka fice, Cikin zumud'i Aliyu ya had'a waya yana washe baki ya mik'awa Ummul dake zaune tana wasa da yatsun ta kaita girgizamai alamar bataso, Shiko Usman da tunda ya shigo ya keta satar kallon ta sai yayi saurin kauda kansa kamar baiga me sukeba yatashi yafice, Shi kuwa Aliyu dawowa yayi kusa da Ummul d'in yace, "Haba Aunty meyasa kike hakane? yanzu dayaga kinnuna bakya so ai bazaiji dad'i ba, kuma bakya ganin zata d'ebe miki kewa da tunani, aduk lokacin da kike ke kadai, dan Allah ki karb'a kisa albarka". Batace komai ba sai idanu data zubamai tana zubda k'ollah cikin sanyi ta fara kuka murya can k'asa tace, "Aliyu kai gani kake akwai wani abu da zai mantar dani Hamma Umar ne Aliyu gani kake woya zata ciremin dana sanin dana saka rayuwata a cikine Aliyu gani kuko a shekara uku zan manta yadda aka rebani da Hamma Umar ne Aliyu bayan qura'an ba wani abu da nake rik'ewa inji sanyi a raina waya zata tuno min da Hamma na dan ita ce kyautar da ya bani a randa zai rasu zai fita ya ajiye min woyarshi k'asan pillow na yace min Khairi na ga wannan zai d'ebe miki kewa kuma zan rink'a kiranki inji ya jikin ki". sai ta kuma fashewa da kuka ta rik'o hannun Aliyu murya na rawa tace, "Inama woya zata iya had'ani da Hamma Umar da na gaya mishi ina sonshi so na hak'ik'a ina sonshi son da bana yiwa kaina da zan dauwama ina mishi zantu kan so amman ina Hamma na yayi min nisa Aliyu ina son Hamma Umar wallahi ina sonshi Aliyu nayi nadama a rayuwata nayi laifi mai munu ina ganin sakayyar rashin yiwa iyaye biyeyya ina ganin illar taurin kai ina ganin munin tsanar masoyi da nabi zab'in iyayena da bazanyi dana sani ba da bazanyi nadama ba". Cikin zubda k'ollah Aliyun yace, "Abun da Hamma Umar yafi so shine ya Usman Anty Ummu in kinso ya Usman Hamma Umar zaiyi farin ciki ki yarda da Ya Usman ku had'u ku reni Farouq ku rabashi da agolanci ki karb'i kyautar ya Usman ko dan kar ranshi ya b'aci kin san matsalar sa dan Allah ki amshi woyar kinji ko". shiru tayi ta tsura mai ido dan Aliyu kamar k'awa yake a gareta kuma abokin shawara kuma abokin kuka kamar yadda Hamma Umar ya fad'a ganin tayi shiru ne, shiko yasake cewa , " kin yarda?". saida ta k'ureshi da ido sannan cikin kosawa da nacinshi tace, "eh". Hajjajo da kamar jira take Ummul ta amsa tamik'e tace, "gulmammiya kawai kin sa kanki cikin nadama da taurin kanki". sannan itama tayi shigewar ta bedroom d'inta tabarsu a wurin ita da Auta, Aliyu ya k'ara matsowa kusa da Ummul yace, " kinga idan na bud'e miki Whatsapp zaki rink'a chat damu, sannan facebook kirink'a ganin labaru kinga ai zakiji dad'i". Kallonshi kawai take yana dannawa yace kinga ga number ki nasaka maki number duk y'an gidan nan harda Abba, itadai ta zuba ido tana kallon cikin wayar a haka ya seta komai harda whatsapp da facebook ya sanya mata hoton Farouq akan dp ta sannan ya kira mata Aunty Halima tana d'auka yace, "number aunty Ummul ce, kisa asata a groups da kike dan d'ebe mata kewa". Itama murna tayi sosai sannan tai addu'a take tabada number Ummul da aka sata a group na Hausa novel Aliyu ma yayi adding nata a family group nasu wanda shine admin, har magariba ta samesu agun sannan suka tashi suka fito a hanya Aliyu ke cewa Ummul, "Idan kinje kin nutsu zakiga number ya Usma saiki kira kice kin gode kinji Anty na?". Bata cikiyi wa Aliyu musuba dan shiya zama kamar k'awarta haka yasa ta gyad'a mai kai alamar toh. K'arfe 9:30 na dare Ummul tana kwance ganin zata fara aikin ta na tunani da kuka da take duk darene yasa ta janyo wayar ta kunna sannan ta lalubo number ya Usman ta danna kira aiko bugu d'aya ya d'auka daman yanada niyyar kiranta sallama yayi ta amsamai sannan shiru ya biyo baya, a hankali ta katse shirun da cewa, "ya Usman nagode". wata irin ajiyar zuciya ya sauke, tare da lumshe ido a hankali yace, "Nima nagode da kika amshi keutata, Ummu ina sonki ina son auren ki kiyi hak'uri ki yarda da k'addararki ta sirens dan inba mutuwa ba ba abinda zaisa ni Usman k'anin Umar nace zan aureki da haka shima wannan ki sanyashi a cikin littafin k'addarar rayuwarmu Ummu na ina sonki ki shigo rayuwata ki zame min gurbin Hamma na nima na zame miki gurbin sa, Ummu wallahi da gaske ina murad'in yin aure na gaji da zaman kad'aici ina son samun me d'ebemin kewa da kawarmin da buk'atuna ko zan samu sukuni a rayuwa ta Ummu ina da buk'atar ki kusa dani". saurin cire wayar tayi daga kunnenta ta katse kiran, tana jin zuciyarta na bugawa da k'arfi salon maganganun Ya Usman d'in nata suna bata tsoro dan a hankali ta fara fahimtar yana yin irin tasa halittar Kuma, Kamar zata ajiye wayar sai kuma ta bud'e data, aiko sak'onni sukayi ta shigowa saida ta bud'e na sauran groups d'in sannan ta dawo kan wanda taga sakon shi sunfi yawa mai suna 'COOL NOVELS ' na Hayatu Baba Zubairu, ta bude magan ganu tarink'a gani anayi a group din daga dukkan alamu a kan novel suke tattaunawa, wata tace daga cikin members na group d'in tace, "Gaskiya Meenal ta Hamma Haiydar ce". wasu suce, "A barwa Dr jabeer". wasu suce General Aliyu ai shine jarumin amman kuma Allah yasa kar Abdul yaci nasarar ketawa Meenal haddi". Saida tayi ta dubawa sannan taga suna maganane akan wani novel dataga antura page d'aya mai suna, *'BANDIRAWO'* na marubuciya nan *AYSHA ALIYU GARKUWA,* fita tayi tayiwa Aunty Halima magana data tura mata novel d'in saboda ta faro daga farko, aiko nan da nan ta turo mata, saida takai k'arfe 1:50 tana karantawa har ta iso inda aka tsaya sannan ta tashi tayo alwala tayi nafiloli day'an addu o i sannan ta kwanta. Tunda ta karanta littafin *Bandirawo* tafara tunani da kuma son taga itama labarin rayuwarta yazama littafin da jama a da dama zasu karanta kuma su ilmantu da sanin illolin rashi biyayya ga iyaye da rashin karb'ar k'addara sannan da sanin muhimmancin mutum mai hakuri da illar cutar da masoyi sannan jama a da dama zasuji labarin d'an kad'an daga cikin illar da boko haram sukayi ga zuciyoyin al'umar dake arewa maso gabashin Nigeria tana son yan mata su d'auki darasi a rayuwar ta tunda ita kam ta rigada tayi kuskure da nadamar yin tirjiya ga zab'in iyayenta amman tana son labarin ta ya zama izina ga yan mata da su guji yiwa iyayen su tirjiya dan nadama zata biyo baya tana son taga irin muhawarar da mutane zasuyi a kanta da abin da ta aikatawa Hamma Umar tana son taga an fad'i laifinta ko zata k'ara dauwama cikin dana sani da yiwa Hamman ta addu'a. Aliyu tafara bawa shawara sannan sukaiwa Ya Sadiq da Adam shawarar hakan shima ya gamsu amma yace mata ta sanar da ya Usman kafin ta ai watar da komai dan shine babba kuma shi zai bada shawara mafi dacewa dan haka tai niyyar sanar dashi buk'atar ta. Ranar asabar misalin k'arfe sha d'aya na rana Ummul tayi wanka tad'au doguwar rigarta ta saka tai rolling kanta da mayafin rigar ta feshe jikinta da turare mai kamshi sannan ta zauna bakin gado ta d'auki wayar ta a hankali tai dialing number Ya Usman sannan ta kara a kunnen ta, Usman dake zaune gaban laptop yana d'an danne danne ya d'aga wayar yasa ki murmushi mai sauti dayasa Adam dake latsa wayar shi juyowa yana kallon shi, ciki jin dadi ya amsa kiran ya karata a kunne yayi k'asa da murya yace, "Assalamu alaiki ya noorul hayati na". Ummul ta amsa da, "Wa alaikassalam, ya Usman ka fitane?". saida ya sake kashe murya yace, "waneni infita banyi sallama da ruhina ba, inzone?". Dasauri tace, "a a ina zuwa". bata jira amsar shiba ta katse wayar ta tashi ta fito. Juya kai Usman yayi ya harari Adam cikin wasa yace, "meye ka zuban ido, kake wata dariya kamar mara gaskiya". k'asa da kai Adam yayi yana danne dariyar dake shirin fitowa da k'arfi yace, "ni menace?". tsuke fuska yayi yace, "Daman me ka isa kace, fita zaka yi daga d'akin Ummuna zatazo". Adam baisan lokacin da dariyar ta kwace mashi ta fitoba, shiko Usman yunk'ura wa yayi ya kawomai dukan wasa Adam ya kauce yace, "kuda zakuyi maganar ku a palour ina ruwana ina nan". Kai ya kad'a yace, "Allah saika fita d'an sa ido kawai". Wayarshi ya d'auka yasauko daga gadon yana dariya yace, "intai tsami naji". "inba tagi tsaminba kuma kai sai kayi tsamin ko". Adam yana fita yasami Ummul bakin k'ofa tana sallama ya amsa cikin kauda kai sannan suka gaisa ya wuce yanufi b'angaren Nanne. Usman yana jin ta ya fito yana amsa sallamar ya k'arasa inda take tsaye ya kamo hannunta, ta biyo bayan shi saida yazo ya zaunar da ita a kujera sannan shima ya zauna gefen ta yad'an matse hannun ta dake rik'e a hannun shi yace, "kinyi kyau Baby". janye hannunta tayi daga rik'on da yayi mata tace, "ina kwana?". sosa kai yayi sannan yace, "lafiya lau sweetheart musamman ma dana tashi cikin sa ar ganin kyakykyawar fuskar ki". Kauda kai tayi gefe cikin jin kunyar shi sannan murya can k'asa tace, "Ya Usman daman inaso muyi wata magana ce". komawa yayi jikin kujera ya jingina ajiyan zuciya ya sauk'e tare da yin magana cikin rad'a yace, "Ina jinki ya habeebati me bum'arki?". Shiru tayi dan wata iriyar kasalar da voice d'in Ya Usman d'in ya sakar mata cikin sanyi tace, "Labarin rayuwar mu nake son a rubuta shi ya zama novel ne dan inaga akwai darussa da wasu mutane zasu samu da izina da WA'azantarwa a ciki shine ya Sadiq yace in fad'a maka". D'ago kai tayi danjin yayi shiru na d'an lokaci aiko da sauri ta maida kanta k'asa dan yanda taga irin kallan da yake mata tamkar zai cinye ta duk ya susuce a kanta a hankali cikin zurfin nazari yace, "Tabbas akwai darasi a rayuwar mu kuma babu wani aibu ga abinda mutum zaiyi dan nuni da tunatar da wasu wani Illa ko alfanu ko gargad'i ko izina ga Al'umma, dan haka ina goyan bayan hakan". Sai kuma yasa hannu yasake kamo hannun ta yace, "Abin damuwar shine waye zai rubuta tunda kinga mu ba iyawa mukayi ba". D'an murmushi tayi ta d'ago kanta dan jin dad'in yanda yabata goyon baya tace, "ai akwai group da Aunty Halima ta sakani a Whatsapp to shine akwai Admin na group d'in dana fad'amai har na bashi labarin kuma yace, akwai marubuciyar danaga novel d'inta zai mata magana akan labarin, toh amman ya mata magana , amman yace min ta nuna gaskiya ita bazata karb'i aikin labarin nawa ba tace, ai yanzu haka ma tana typing novel nata mai suna *Bandirawo* bata gamashi ba kuma tace ko ta gamashi tana da wasu aiyu kan rubuce-rubucen da yawa, nima ya bani number ta na mata magana amman ta nuna gaskiya nayi hak'uri bazata yiba, toh na gayawa Yahaya hayat d'in yadda mukayi yace kar in damu Insha Allah zai k'ara rok'onta kuma zai tura mata labarin yana kyautata zaton in taga yadda labarin yake zata karb'a kuma zata gyarashi ta yadda zata maidashi littafi mai zaman kanshi ta yadda ask'on da ake son isarwa zai isa ga Al'umma ya kuma cemin aikin typing wuyane dashi bare maida labarin gaskiya ya zama littafi aikine mai but'atar nazari da fasaha dan abu kad'an zaisa a kauce tsarin labarin, don haka kaima kayi mata magana kuma mu gayawa Abba da Ammi in sun yarda ba matsala yace sai, zuwa anjima zaimin magana in sun gama maganar da ita". Idonshi a lumshe yace, " to Allah yasa ta karb'a dan na lura hakan zai saki farin ciki kuma yanzu zanje in gayawa Abba da Ammi jirani yanzu zanje in dawo sai mu kirata". Murmushi ta k'arayi tace, "nagode ya Usman". Shiko mik'ewa yayi ya nufu cikin gida Kai tsaye part d'in Abba ya wuce inda ya sameshi shida Daddy da Ammi da Nenne suna maganar batun auren nasu, A nan ya zauna yayi musu bayanin yadda sukayi da Ummul batun rubuta labarin ta, murmushi Abba yayi shida Daddy da Ammi sukace sun yarda Allah ya sanya al'khairi rubutun Allah Kuwa yayiwa marubuciyar albarka komai za'ayi da yardarsu sun yarda a rubuta labarin ko suna yensu a saka kuma kar a canza labarin, sosai Usman yaji dad'i cikin happy ya juya ya fita kai tsaye part ensu ya koma, yana shiga ya zauna gefen Ummul nashi sannan ya d'anyi baya ya jingina da kujera yace, "amma fa gaskiya Ummul auren mu shine cikar burina da kuma k'arshen littafin Ummu na ina sonki ina sonki kusa dani ina da buk'atarki kusa dani". kauda kai tayi cikin sanyi tace, "Toh yanzu mu kira Aunty Aysha Garkuwa kayi mata magana da kanka". "To" yace sannan ya Karb'i woyartata yasa Hf cikin sanyi ta fara magana a hankali tace, "Anuty Aysha kiyi hak'uri na matsa miki Ummul ce wanda kukayi magana jiya dama ya Usman ne yake son kuyi maga". cikin tausayawa GARKUWAR FULANI ta fara magana dan yahaya hayat ya tura mata labarin ta karanta cikin tausayawa rayuwarsu tace, "Ayyah Ummu sannu Allah ya jik'an Hamma Umar Allah yasa ya huta rabbi ya karb'i shahadarsa Allah yasa Al'jannace makomarsa muko in tamu tazo Allah yasa mu cika da imani da kalmar shahada, Allah ya bawa Ya Usman lafiya da nisan kwana Allah ya raya Farouq k'arami". "Amin Amin Ameeeeeeeeeeeeeeeen ya rabbil izzati". suka amsa a tare ita kuwa garkuwa tuni take kuka cur-cur tunda ta karanta labarin nasu ta kasa tsaida hawayen ta, cikin sanyi ya Usman yace, "Mun gode da Addu'arki ga d'an uwanmu Aysha Ummul tace min kince baza ki amshi aikin labarin namu ba gashi yanzu tana kuka kuma mun gayawa iyayen mu sun yarda Insha Allah anjima zan had'aki da Ammin mu ta gaya miki da kanta". cikin sanyi da rauni tace, "Ba komai ya Usman na yarda in dai naji daga bakin Ammi na yarda zan rubuta labarinku ina gama *Bandirawo* kafin Sallan layyah bayan sallah zan fara labarin ku, zan ajiye duk labaraina sai na gama rubuta labarin ku dan tabbas labarin Ummul akwai izinah a ciki darasi mai girma a ciki". Godiya suka rink'ayi ita kuwa Ummul sai kuka takeyi, bayan sun katse kiran ne Usman yasa hannu a hankali cikin wani irin salo ya j......... *SADAUKARWA GA DR UMAR IBRAHIM UMAR SHUWA (HAMMA UMAR)* *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 3⃣5⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Kin kid'i kankad'a, damuni na damoni, gid'd'omo fina laramo, gaid'omo fina sukoyo, ladde Allah yamad'u, ki b'ib'b'e samme te, ki d'oidi yalete, b'end'uki yamete, yoriki tenets,* *Ina mik'o sak'on ta aziyata ga yan uwana Fulani ma zauna Numan dake jihar Adamawa Yola Allah ya isan mana ya saka mana cikin gagga bisa kisan gillan da k'abilar B'acamawa sukeyi mana, Allah ya jik'an wadanda suka kashe Allah ya karb'i shahadarsu Allah ya saka mana yadda suke tozarta mu Fulani ma zauna cikin rigogi suma Allah ya tozarta su Allah ya isa Allah ya isa Allah ya isar mana kuma shi zai saka mana zalumin ci da ake mana, ina kuma kira ga ugiyar TABITAL FULAKU ta jihar Adamawa tare da Ugiyar MI YETTI ALLAH da su hamzarta shiga cikin wannan Al'amari domin kawo k'arshen wannan zalumcin da akayi mana shekaran jiya da jiya a kwana biyu ace an kashe mutun kusan arba'in wannan zalumcin dame yayi kama😭😭😭😭* *A* hankali ya janwo ta jikin shi ya d'ora kanta a kan kijinshi sannan yasa hannun shi ya ruggume ta sai wani irin numfashi yake fitarwa a hankali yana lumshe ido da sauk'e ajiyan zuciya yana mai jin k'aunar ta da wani irin sonta, itako sai lafe tayi a jikin shi tana kuka mai cin zuciya dan tuno Hamma Umar d'inta da tayi, yayinda shikuma yakejin kukan ta har cikin ranshi gaba d'aya ta hargitsa shi yana jin tausayi kanshi da kanta cikin lallashi yace, "wayyo Allah ba Ummu na dan Allah ki rufamin asiri kidena kukan nan zuciya ta tana harbawa da k'arfi". Sake cusa fuskar shi yayi a wuyanta yasa bakin shi a saitin kunnen ta cikin sigar rarrashi da rad'a ya hura mata iska mai sanyi cikin kunnen nata murya a narke yace, "Ki taimakawa zuciyar data dad'e tana muradin samunki, ki tausayawa ran daya dad'e yana kwad'ayin ganin farin cikinki ki jik'aina kidena zubda hawayen ki, kiyi min son da ako yaushe kika tuna Hamma na kiyi mishi Addu'a, Wallahi Allah Ummul kece burin raina, kece zab'ina, Kece farin cikin ruhina kuma muradina, zanso kiban dama in gwada miki yadda nake azab tuwa da cuter k'aunar ki da rad'ad'in rashin d'an uwana kece kad'an zaki samamin farin ciki, ina kaunar ki k'auna mai tarin yawa, wallahi Ummul idona baya gani sai ko wacce mace da sigar aure sai ke, kunnuwa na basa jin zak'in muryar ko wacce mace sai muryarki, Noor qalbee wallahi idan nace ina ganin sauran mata kamar maza kar kiyi mamaki wallahi bazan iya rayuwa babu keba". ya k'arishe maganar tare da sa hannun shi ya shafo wuyanta numfashin shi na fita da kyar muryar shi na rawa yace, "Ummuna kaunar ki zatamin illah in dai ban same kiba, dake nake kwana dake nake tashi numfashi na da bugun zuciyata duka nakine, bazan iya jure rashin kiba, ki taimakeni ki yarda da aurena wallahi hakanne kawai mafita guna kinji ka'nwata abar k'aunata". Zuwa lokacin Ummul tafa ra tsorata da Usman gaba d'aya yanason b'atar mata da hankali, sai wani irin fesa numfashi yake yana lumshe ido da laso lips enshi kamar wanda yake cikin maye, ganin yadda yake ta k'ara matsowa jikin ta yasa ta d'an juya kai ta fuskarta ta fuskanci tashi hakan yasa hancinsu ya had'u guri guda sannan ta sauke ajiyar zuciya da hakan yasa iska fitowa daga bakinta kamar da gangan tayi, aiko Usman najin iskar kasala ta sauka mai jikin shi ya mutu hakan yasa shi sassauta rik'on dayayi mata ya koma jikin kujerar ya jingina yana lumshe ido yana bud'esu da kyer gaba d'aya ya sake sai wani irin shu'umin kallo yake mata, Ita kuwa hakan yasa tasami dama ta fusge jikinta daga rikon dayayi mata da k'arfi cikin sassarfa tafice daga parlor tana kuka cikin sanyin sauti. Kai tsaye d'akin su ta nufa tana shiga tafad'a kan gado tacigaba da rairo kukan ta, dakyar Ammi dake gefenta ta rarrasheta cikin kukan da tuno Hamman ta tayi lamo akan gadon kamar mai bacci, ganin tayi shirune Ammin ta fita ta barta. A parlour kuwa dakyar shima ya yunk'ura a daddafe yashige bedroom din ya fad'a kan gado hannun shi rik'e da marar shi yayita mirginawa yana juyi hawaye na bin fuskarshi pillow ya jawo Ya rungume da k'arfi yanajin wani irin yanayi na shigar shi, yad'au lokaci a haka sannan ya tashi dak'yar yafad'a bathroom yasakarwa kanshi ruwa sannan yafito ya shirya tsaf ya d'au mukullin mota yayi b'angaren Nanne . Kwance yasami Ummul kan gado kamar me bacci Ammi kuma da shigowarta d'akin kenan tana ajiye kayan data shigo dasu ya rusuna k'asa yasake gaida ta amsa tayi sannan tasami bakin gadon ta zauna saida yayi kamar zai tashi sai kuma ya zauna yace, "Yauwa Ammi akan maganar rubuta littafin da Ummul takeso d'azu munkira ita marubuciyar munyi magana shine nace mata zan had'aku da ita tasake ji daga bakin ki saboda tad'au abin da muhimmanci duk da dai daga yanayin yanda mukai magana da ita baza a samu wata matsalaba kuma bisa ga dukkan alamu Ummul ta k'ara samun Aunty dan bakiga yadda tayita rarrashinta d'azuba". Nan da nan Ammi taji k'aunar marubuciyar na ratsata kasancewar a yanzu bata da burin daya wuce ganin samun kwanciyar hankalin Ummul d'in ta da murna tace, " To madallah kirata muyi magana kaga sai nasake mata godiya". D'an d'agowa yayi ya lek'o kan gadon yace, "Khairi mik'omin wayar ki". Dana sauri Ammin tace, "Haba Usman kace in mik'omaka mana saika tayarmin da ita daga baccin tun d'azufa kuka take yi da kyer na samu tayi shiru". A hankali ta d'an d'ago kanta wadda daman tana jin duk zancen nasu ta d'auko wayar tayi ta mik'o mai, Kanshi a sunkuye yasa hannun zai karb'i woyar cikin hikima ya had'e wayar da hannun ta ya rik'e yana murza yatsunshi biyu kan yatsunta cikin salon lallashi da so, da sauri ta zame hannun ta tana kallon Ammi, Itako Ammo batama ga abinda suka yiba, Dialling number yayi bata jima tana ringing ba ta d'auka sannan ya mik'awa Ammi ta karb'a tasa a kunnen ta sannan tace, "Assalamu alaikum". Cikin muryarta mai sanyi da saisaita zuciya ta amsa sallamar sannan tace, "Wa alaikissalam ina kwana". gyara zama Ammin tayi tana fara a tace, "lafiya lau d'iyar albarka, ya yaranki ? da mai gidan ? ya kuma gurin manya?". Cikin ladabi ta amsa da, "lafya lau Alhamdulillah". cikin girma Ammi taci gaba da cewa, "Y'an nan Ammin Ummul ce". jin hakan Garkuwar cikin tausayawa tace, "Ayyah Ammi kece ya hakurin mu na rashin Hamma Umar? Allah ya jik'an shi yamai rahama yasa can yafi masa nan ku kuma Allah ya k'ara maku juriya da hak'urin rashin shi". Cikin sanyi Ammi ta amsa mata da, "Ameen nagode Allah ya bada lada". sannan tayi ajiyan zuciya tare da ci gaba da cewa, "Usman ya sanar dani yadda duk kuka yi akan rubutun littafin kuma yace kinaso ki k'ara tabbatar da sahihancin labarin shiyasa nasa baki kuma nake fatan zaki karb'i abun dan taimakawa". Shiru tayi dan sauraren amsarta inda cikin girmamawa tace, "Insha Allah Ammi babu matsala zanyi iya k'ok'arina inga munbada sak'on da labarin yake d'auke dashi, duk da ina da wasu ayyukan banda wanda nakeyi a yanzu amma da yardar Allah zan aje komai idan na k'arasa wanda nake aiki akai yanzu Insha Allah shi zan fara." Cikin jin dad'i tace, "To y'ar nan Allah yamiki albarka ya jib'anci dukkan lamuranki yakuma biyaki da gidan aljannah". Daga ita har Usman da Ummul da, " Amin Amin Ameeeeeeeeeeeeeeeen ya rabbil izzati ". suka amsa cikin sakin fuska Ammi tasake cewa, "To sai hakuri da k'anwar taki gatanan kuka koyaushe takasa daina shi sai ki cigaba da d'orata kan hanya dan tabbas had'uwar ta dake ya kawo canji a yanayin ta da". "Insha Allahu" Garkuwa tace sannan Ammi taciga da cewa, "Yauwa Aisha nagode sosai Allah ya bada sa a Allah yabaki ikon aikin alkhairin da kikayi niyya Allah ya miki al'barka". "Ameeen". da haka sukayi sallama Ammi ta mik'awa Ummul wayar ta mik'e tana kallon Usman cikin k'aunar d'an nata tace, "Fita zakayi ko?". yana inda yake zaune yace, "eh me kike buk'ata? in kawo miki?". tana tafiya tace, "bakomai Allah ya kiyaye ka ya dawo dakai lafiya". Yana sosa kai kamar mara gaskiya yace, "Amin". Tashi yayi yakoma bakin gadon ya zauna ya k'ura mata mayan idauwan shi sannan cikin rad'a yace, "Wai ina yarona ne?". Kanta a k'asa tana wasa da yatsunta tace, "Yabi Daddy tunda yazo gaida Hajjajo". K'ara sunkuyowa kanta yayi cikin lumshe ido yace, "To amma dai bawata matsala ko?". Murya na rawa tace, "bakomai". hannu shi yasa ya ruk'o nata yana d'an murza yatsunta a hankali yace, "To aimin rakiya mana irinta masoya". nan da nan ta kwab'e fuska ta tayi rau-rau da ido alamar zatayi mishi kuka, Ganin haka ya sake daburcewa jiki na tsuma mik'ewa yayi sannan ya sunkuyo dai-dai kunnen ta ya tsurawa k'irjin ta ido murya a cushe yace, "Kiyi baccin ki mai dad'i tare da mafarki na ina lasar wad'an nan lips en na ki masu taushi Ummu na ina begen randa zaki zamo mallaki na". Fusge hannun ta tayi ta rufe idonta cikin kinda da mamakin ya Usman d'in, shiko ko ajikinshi dan daman haka yake baya b'oye abinda yakeji, juyawa yayi har yaje bakin k'ofa yace, "please ki ajiye wayarki a kusa". Sannan yasa yatsunshi biyu a kan lips d'in shi yai kissing d'insu ya hura mata da bakin shi sannan ya fice. Kai tsaye yawuce FCE(T) inda yake koyar da masu koyan computer duk juma a da asabar. Office d'in Mallam Bashir Bala abokin aikin shi yashige kai tsaye kasan cewar nan yake zama in yaje saboda yakan jene sabida nemanshi da sukai yarink'a taimakawa, bayan sun gaisa Malam Bashir yace, "To bari inje kafin ka huta". Yana fita shiko ya d'aga kafafuwan shi ya d'ora akan kujerar dake kallon wadda yake zaune ya ciro waya yakira number Ummul ya saka a kunne, saida ta kusan katsewa sannan ta amsa murya can k'asa tai mashi sallama, "wa alaikissalam Hubby, ykk". Jin abin tai wani iri sabida ganinta yanzun nan yafita amma yana tambayar ya take, shiya dawo da ita daga tunanin da take da cewa, "Allah yasa ba bacci kika fara na tasheki ba, kiyi hak'uri wallahi soyayyar ki ce take d'ibana nake kasa jurewa shiyasa zakiga ina irin wannan abu buwan". baki ta tura tare da cewa "hmmm". Kawai shikuma yaci gaba, "Gaskiya Baby ki dena min rowar muryarki dan Allah ki karb'eni kiban dama nashigo rayuwarki na cika zuciyar ki da farin ciki pls". Yasan da wuya tabashi amsa dan haka yaci gaba da cewa, "Kice wani abu dan Allah, indai kinaso nayi aikin danazo yi". shiru dayajin ne yasa d'an sauke k'afar shi k'asa yazura takalmin shi ya mik'e yana mak'ale da wayar yafara tafiya yana cewa, "Ganinan dawowa tunda bazaki min magana ba nima babu abinda zan iya yi gwara indawo inta zamana a gida". Dai-dai nan yabud'e murfi motar shi yashiga ya rufe kofar, k'arar rufe motar yasa ta tabbatar dagaske zai dawo da sauri cikin sanyin murya tace, "Ya Usman dan Allah karka dawo". Komawa yayi ya jingina da jikin kujerar motar yayi murmushin jin dad'i yace, "kin barni na fito bakimin addu'a ba kuma yanzu nakira kink'i kimin magana gashi duk a matsa nake wane irin aiki kikeso nayi a hakan?". Katseshi tai da, "Kayi hakuri Allah yabada sa'a ya kiyaye ka". Wani irin sanyi yaji a zuciyar shi yasa hannu yabud'e motar ya fita ya maida murfin ya rufe sannan yace, "Amin, to ko kefa, yanzu ne zanyi aiki ki kulamin da kanki saina fito". "Adawo lfy". tace sannan ta katse kiran tabi wayar da kallo tana jinjina hali irin na ya Usman shi sam ya fiye zalama daga dukkan alamu shi ba irin Hammanta bane mai hak'uri. Shak'uwa mai k'arfice take shiga tsakanin Ummul da sabuwar Auntyn ta Aysha Aliyu Garkuwa, wanda sukan yi waya sannan suna dadewa suna chat, hakan na debewa Ummul kewa kuma tasami nutsuwa saboda irin rarrashi da shawarwari datake samu daga gareta saidai kusan koda yaushe dukkansu da kuka hirar tasu take k'arewa musamman idan GARKUWAR tayi mata wata tambaya game da rayuwarta ta baya, ranar wata asabar Ummul ke fad'awa Auntyn nata zasu tafi Saudi dan gudanar da aikin Hajji ita da Ammi da Ya Sadiq kuma zasu tafine ta international air dan haka Dubai zasu wuce sannan daga can su dawo k'asa mai tsarki. Addu'a tayi mata sannan suka rabu. Kamar yau aikin hajji ya k'are dan haka suka d'unguma sai Dubai inda zasu kwana kafin da safe suwuto gida Nigeria, Wannan yaba Ummul damar bud'e data ta tayi sa a Auntyn ta tana online taji dad'in ganin ta saboda hakanan taji tana buk'atar su tattauna akan abunda yake damunta, sallama ta yimata bayan su gaisa sosai ne Ummul tafara tambaya kamar haka, " Aunty dan Allah dagaske ne yanzu idan nasake aure shikenan na rabu da Hamma Umar na rabu da aurensa na tashi a matsayin matar Hamma Umar?". Tambayar ta bawata tausayi duk da tasaba da shirmen Ummul d'in, cikin sigar lallashi data saba da yimata tace, "Meya kawo wannan tambayar dear?". Shagwab'ewa tayi kamar zatai kuka tace, "Ya Usman ne yadameni kan maganar aure nikuma gaskiya banason kowa kuma banaso inzauna da kowa sai Hammana Aunty Aysha wallahi ina son Hamma na duk duniya yanzu shi nake so". Ajiyar zuciya tasauke sannan tace, "Haba Ummuna, tun kafin kiyi tafiyar nan muke magana guda d'aya kuma kinga dukkan mu burin mu mu samar maki da farin ciki wannan shiyasa zakiga kowa nada burin kiyi aure saboda auren shine kad'ai hanyar da zaki sami nutsuwa kuma kisamar wa Hamman ki kwanciyar hankali dan in kinyi aure zaki rege zubarmai da hawaye, kuma ta hanyar auren Usman ne zaki samu farin ciki mai d'orewa, k'anwata auren Usman shine kwanciyar hankalinki dana iyayenki dakuma na yaronki kai harma dana Hamman ki Allah yamai rahama". "Amin" ta amsa sannan taci gaba, "Zai kasance cikin farin ciki kina kulamai da d'anshi da k'anin shi sannan iyayenku su kasance cikin farin ciki kuma su manta da duk abinda ya faru a baya da yafe maki kuskurenki na bijire musu da kikayi a baya". Sannan taci gaba cewa, "Ki d'aure zuciyar ki nasan dole zakiji babu dad'i kuma dole akwai ciwo a zuciyar ki amma ki daure kiyi hak'uri kinji k'anwata ki yarda da auren Usman". Hannu tasa tashare k'ollah dake zubowa daga idonta sannan ta fara typing amsa, "To Aunty Aysha insha Allah zanyi hakan sabida farin cikin Hamma na da iyayena, nagode da kulawarki gareni". hakanan daga nan kuma hirar takoma rarrashi saboda kukan da dukkansu sukeyi. K'arfe 12 na dare jigin su yasauka a filin sauka da tashin jirage na Aminu kano a cikin birnin kano, a Tahir guest palace suka kwana sannan da safe suka d'auko hanyar Potiskum, ya Usman da ya Adam ne sukaje d'aukosu haka suka dungumo misalin k'arfe 10:08 suka iso gida, Sunsami kowa cikin k'oshin lafiya Umar Farouq tunda suka iso ya haye jikin mahaifiyarshi yanata bata labari na abubuwan da suka faru bata nan haka suka wuni cikin nishad'i sai bayan sallah isha'i ya Usman yamaida Halima da yaranta gida shima Adam yamaida Aunty Shuwa da Inna tunda unguwarsu d'aya, Adam na dawowa yawuce b'angarensu dan yana buk'atar hutu, shiko gogan Ummul daman Allah-Allah yake bak'in su tafi ya gana da masoyiyar shi tun yana mota yakira wayarta tana d'auka yace, "Ki jirani a palour Nanne baijira amsartaba ya katse kiran. A parlour ya sameta tana kwance akan kujera yana shiga da sallama tamik'e zaune ta amsamai kusa da ita yaje yazauna yasauke ajiyar zuciya sannan ya kure ta da ido cikin tsananin so yace, "gaskiya kin rame baby, dama nayita tunanin hakan". d'an murmushi tayi sannan ta sunkuyar dakai k'asa tace, "ya Usman tunda naje a wuraren Ibadan nake tarewa ina yiwa Hamma na addu'a da nema mishi rahamar Allah ko cin abinci bana son fita, ranar na d'an fara gyagyad'i sai nayi mafarkin Hamma na yana nuna min kai yana cemin inje gareka kar in bari ka zubda hawaye". sai kuma tayi shiru tana zubda k'ollah, sai kuma tace, "ya Usman ka gafar ceni". A hankali ya sake matsota yakamo hannayen ta duka biyu ya rik'e da kasalalliyar murya shi yace, "bantab'a jin b'acin rai akan duk abinda kike fad'a kinyi ba, nasha fad'a miki komai kikayi birgeni yake kuma komai kyau yake miki nagode da kulawarki ga d'an uwana". Shiru sukayi dukkansu yanata matsa hannunta dake rik'e a hannun shi ya katse shirun da cewa, "Fatana ki yarda da aurena". sai kumu yasa hannu ya d'ago fuskarta tare da cewa, "Kamar kinada magana ko?". K'asa tayi dakai murya na rawa a hankali tace, "inaso ". da sauri yace, "kina son me"?. ido ta lumshe cikin zubda k'ollah tace, "Ince son ince maka na amince da maganar auren". Kasa k'arasawa tayi tafashe da kuka, jiki na rawa ya janyota jikinshi ya had'ata da kirjin ya ruggume ta da k'arfinshi ta yanda har tana jiyo bugawar da zuciyar shi takeyi ido ya lumshe yanajin wani irin yanayi da bai tab'a jiba hakan yasa yakasa daurewa shima yafara k'ollah, kamar ya tuna wani abu yasa tafin hannu shi ya goge k'ollar idon shi yasake matso ta yace, "Yi hakuri kinji, kinga narasa mezance maki dan murna amma dai nasan yau matsalata ta k'are". Sakinta yayi ya sauka daga kujerar ya durkusa yayi sujjada yayiwa Allah godiya sannan ya juyo yazauna gabanta ya d'ora kanshi akan cinyarta kamar k'aramin yaro yasauke nannauyar ajiyar zuciya yace, " inasonki ina k'aunarki". A hankali takai hannun ta d'aya kan gashin kanshi ta tusa yatsun ta ciki tana d'an tureshi, runtse ido yayi da k'arfi yanajin wani irin abu da baitab'a jiba kuma bazai iya kwatan tawaba, itace ta dawo dashi daga halin dayake ciki dacewa, "Naji dad'in samun Aunty Aysha Garkuwa domin ko yaushe shawararta irin ta Ammi da Nenne ce kuma in nabi ina jin dad'i". d'ago kanshi yayi ya kureta da ido hakan yasa tai shiru cikin kunya tafara wasa da yatsunta, shi kuwa sake tashi yayi ya zauna gefen ta sannan ya ruk'o hanna yenta murya a raunane yace, "Nasani my life nasan wannan yafaru da ikon Allah da taimakon ta hak'ik'a ni dai GARKUWA tayi min rana". sai kuma ya d'an fizgota cikin tsananin shauk'i yace, "inna fad'a miki toh ki rik'e mini duk tsanani da wuya zana sakar miki sona kiyi rik'ona don Allah kar naga kin gajiya, in dai kikayi haka so zai habaka zamuga kyen tafiyar, da shak'uwa aka samu yarda har so yassanya muna kama da juna". shiru tayi tana jin salon son ya Usman d'in ta mai cike da kalamai masu sanyi gaba d'aya ya kashe mata jiki sai k'ara narke mishi takeyi cikin Shauk'i ya tallabo fuskarta ido ya kashe mata tare da kashe murya cikin rad'a yace, "Bisa dukkan alama an yabamini Kumar nasan zanga kyen yanayi domin kinmin halin mutuntawa duk kin gwada mini su tunda kin amince na zama mijin ki ni kuwa dole na k'arfafa so da k'auna nayi miki rik'on da ba shayi, gurin zaman auren mu in kyautata miki domin muyi zama na faran tawa juna rai". cikin jin kunya murya can k'asa tace, "Ni nace maka kwarai ina so dan haka karka fidda rebo, me kake so ya zama alamar sona a gareka don akwai sabo a tsaka ninmu inko yarda ta kake buk'ata to ka sanya a ranka ka samu, dan kai gudane da bani da kamar ka nida Hamma na da Farouq a zuk'atan mu". Murmushi yayi cikin jin dad'i yace, "Ummu na ina da matsala fa ban sani ba ko zaki iya d'aukar nauyin yawan buk'atata gaskiya gwara na shaida miki tun yanzu kar sai munyi aure kice na matsa miki ko na fiye jaraba, kuma ko a Shari'ance dama in gaya miki kisan irin mijin da zaki aura". kanta ta sunkuyar cikin jin tsananin kunya hakan yasa ta kasa maga sai kai ta gyad'a mai murmushi yayi cikin tsananin jin dad'i yace, "Dole in gwada miki farin cikina gaskiya kinyi na yaba miki al'k'awari kuma zan rik'e miki wurin zaman aurenmu wallahi bazan matsa mikiba zan sakaki a cikin farin ciki zuciyar ki na cire mata bak'in ciki da duk wani k'unci tunda kema kin yimin halacci domin kinyi rik'o da amana tunda kin amince dani". ido ta lumshe cikin sanyi da jin kasala da kalaman ya Usman d'in nata, a hankali tace, "Lallai shak'uwa tana sanya yarda a tsakanin mu tabbas idan nace maka a zuciya ta kai na zab'a ka gaskatani ka bani dama, amman in dai sone har gobe Hamma nane kawai nake so a raina ya Usman sai kayi hak'uri dani". Ajiyar zuciya ya sauk'e sannan ya kamo hannun ta ya tsaida ita cikin mayen so da juyewar idanu yace, "zan rayu dake cikin aminci son da kikeyiwa Hamma na ma kawai ya wadatar dani ko baki soniba ba matsala tunda kinso d'an uwana Kuma nasan nima wata rana zaki soni". Haka suka kasance cikin hirar su ta soyayya duk da bakomai take amsamai ba amma saida suka raba dare suna hira sai k'arfe 3:15 ya rakata har bakin kofar d'aki ta shiga yanajin kamar kada su rabu sannan ya juya ya tafi part ensu. Yana shiga bedroom ensu yasami Adam yayi d'ai-d'ai a gado yana baccin gajiya kasa hak'uri yayi yasa hannu yad'an bugi k'afar shi, da k'yar ya bud'e ido yad'ago kai yace, "yadai?". zama yayi kusa dashi a kan gadon yace, "Tashi kasha labari naci zab'e Dr Bashir da Mustapha duk sun fad'i jam'iyata ta kafu k'ark'ashin jam'iyar Hamma na naci albarkacin d'an uwana duk da baya raye amman a sana dinshi nake farin ciki". "a a dan Allah ka barni nai bacci na kaban labarin da safe". Adam yafad'a yana gyara kwanciya, da sauri shiko ya rik'oshi ya k'arasa zaunar dashi yana cewa, "Gwarama ka tsaya kaji wlh dan bazan barka kayi baccin nan ba". Adam da yakeson yacigaba da bacci yace, "To menene?". "Ummul ce". yace shiko katse shi yayi da cewa, "ai dama nasani koyaushe maganar kenan". hannu yasa ya toshemai baki yace, "Kai ba irin wannan labarin bane, yau da bakinta tace ta amince da aure na". "congrat Allah sanya alkhairi". daga haka ya juya yaci gaba da baccin shi, shiko mik'ewa yayi yaje yayi wanka da alwola yazo yayi ta nafiloli da karatun Qur'ani har aka kira sallah asuba. Tunda suka fito daga masallaci sallah asuba Abba ya fahimci da magana a bakin yaron nashi dan yanata bin bayan shi yana sosa kai, kamo hannun shi yayi suka nufi b'angaren Abban, ya zauna a kujera shikuma yazauna k'asan kujerar ya ton k'oshe k'afa saida suka gaisa sannan yafara sosa k'eya kamar mara gaskiya, "Haba d'an Abba ya aka yine ? ai babu wannan b'oye-b'oyen tsaka nin mu fad'amin me kakeso?". K'ara sunne kai k'asa yayi yana murza yatsun kafar shi cikin sanyi yace, "Daman mun gama magana da Ummul ne shine ". Sai kuma yayi shiru dariya Abban yayi mai sauti ya dafa kafad'ar shi yace, "To shikenan nagane anjima zamuyi magana da Ammin ku sai kuma insanar da Hajjajo inyaso idan Daddy ku ya shigo anjiman sai mu mik'a musu sadakin su kaga sai su samana rana ko?". Baisan lokacin daya kamo hannun Abba ba yana cewa, "nagode nagode". Saikuma ya saki hannu yana sosa kai. "To jekai azkar d'inka". "to ". Kawai yace yamik'e a kunyace ya fice. Shi kam Abba mamaki yake dan yana rena shekarun Usman gashi baida wani girman jiki amman ya lura yana son auren sosai, Dr Bashir kuwa yau da wuri ya tashi dan zaizo yayiwa Ummun shi sannu da dawowa, a gefen Mustapha ma harda Ummanshi suke shirin zuwa yau din suwa Ummul barka da dawowa Lafiya, Shi kuwa Usman yana shiga part ensu a parlour ya zauna cikin jin bacci ya kira Ummil d'in tana kan sallaya woyar na gefen ta juyowa tayi ta d'an kalli Ammi dake karatu, a hankali ta yi mishi sallama, yana jin muryar ta cikin, wani irin yanayi yace, "wash Noor Hayateeeeeeeeeh bacci nake ji kuma kuma b........... *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 3⃣6⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *MOH ALLAH WUJI FURƊATA* ```A madadin Member's ɗina na Group ɗin TABITAL FULAKU nake miƙa saƙon gaiduwar ta'aziya ta ga HALIMA Ummu Maryam kano tare Mu'allima Bauchi Allah ya jiƙan iyayen ku Allah yasa sun huta rabbi ya sanyayya konciyan ƙaburburansu Mu'allima Allah ya baki haƙurin rashin mahaifiyarki da kikayi a deren jiya Halima kema Allah ubangiji ya baki haƙurin maihaifiyarki da kika rasa shekaran jiya Allah yasa sun huta muko in tamu tazo Allah yasa mucika da imani``` *M*iƙa yayi cikin kasala da jin bacci murya can ƙasa yace, "Washhh Ummu na bacci nakeji, kuma begen ki ya hanani baccin, gashi ina jin sanyi". shiru tayi bata amsa mai ba a ranta kuwa mamaki ya Usman ɗin yake bata shi kuwa iska ya furzar a hankali sannan yaci gaba da cewa, "Inama an daura mana aure Ummu na in samu d'umin jikin ki". shiru tayi batace komai ba saidai cike take da kunya, shi kuwa lumshe ido yayi yaci gaba da cewa, "Laisa liyal'huzni inkunti ma'ee=in kina tare dani bani shiga kunci, amma yanzu narasa yadda zanyi". Dakaji yanda yake magana kasan bacci ke damunshi sai faman mik'a yake da hammah yana magana cikin shogoɓa yana maƙale da woyar yaci gaba, "Uhhmmmm wash bacci nakeji Ummuna kuma begenki ya hanani lumshe ido". A hankali ta buɗe baki cikin sanyi ta huramai iska a kunnen shi sannan cikin rad'a tace, "yanzu ina kake?". ldo ya lumshe sannan cikin shogob'a yace, "ina palour". Murmushi ta ɗanyi jin yadda yake magana sannan a hankali tace, "To tashi ka koma bedroom ka konta a hankali saika lumshe idonka". Tashi kawai yayi yanufi bedroom ɗin yana shiga ya kwanta kan gadon ya lumshe ido a hankali ya furta, "Nayi yadda kikace ɗin". Ɗan murmushi takuma yi shogob'ar shinna tana bata mamaki a hankali cikin raɗa tace, "Gani a gefenka, ga hannuna ka riƙe". Hannu yasa ya damk'e filon da yake kai a hankali yafurta, "Shhhhmm Ummuna Insha Allah sana iyshu ma'aki ma'a habbah=insha Allah zan rayu dake tare da soyayya". jin haka yasa tafara sauke numfa shi tana murmushi tana kuma hura mai iska a kunnenshi a haka yafara bacci ita kuwa taci gaba, "Kayi bacci cikin nutsuwa hannuna na riƙe da naka kanka yana cinyata hannuna ɗaya na yawo a cikin suman kayin ka zuwa kunnen ka, ina son kayi bacci kar ya saka ciwon kai". Shirun dataji dakuma jiyo saukar numfashin shi a hankali yasa ta kira shi ta tabbatar da yayi bacci dan jin bai amsa kiran da tayi mai ɗinba, haka yasa ta katse wayar ta konta cike da tunani har bacci ya d'auketa. Gari na k'arasa wayewa Ammi tazo ta tasheta dan tayi break saida tayi wonka tai kwalliya sannan taje tagaida Nanne, bayan sun gaisa tace, "Ga abincin Usman can ki ɗauka ki kai mishi". Amsawa tayi sannan tajuya ta je ta had'a mai komai akan tire ta ɗauka ta fita hannun ta riƙe da hannun Faruq. A ɓangaren Usman ma yana tashi yashige yayi wanka ya shirya tsaf ya feshe jikin shi da turaren hugo mai ƙamshi yana fitowa palour kunnuwan shi suka jiyemai abinda yafi son ji, Sallamar da tayi ya amsa sannan ya buɗe hannuwan shi ya ɗan tsuguno da fara a fuskar shi yace, "come on Daddy boy". da gudu Farouq yaje ya faɗa jikin shi shima yamaida hannun shi ya rufe sannan ya ɗagashi sama yana kissing ɗinshi tako ina cikin ƙauna shima yayi kiss ɗin shi a kumatun shi cikin gwaranci shi yace, "Ana Ubbuka Abee". Dariya yayi yana saukeshi ƙasa yasa hannu yana lakace mai hanci yace, "Ana hubbuka ya bunayya". Wucesu yayi yaje ya haye kujera yaɗau remote d'in tv yafara wasa. Shi kuwa dawo da kallon shi yayi kan Ummul dake kokarin ajiye tiren a tsakar palour ya zuba mata manyan idanun shi, tana ajiyewa tasami guri a ƙasan a tsakiyar carpet tazauna sannan ta kalleshi ta ɗanyi murmushi yadda taga ya ƙure ta da ido dakai tamai alamar yazo ya zauna, aiko kamar rakumi da akala yataho da hannu ta nunamai inda zai zauna, saida tasa hannu taɗau flate tafara zubamai abincin sannan ta ɗan kalleshi cikin sanyin murya tace, "katashi lafiya?". Shima lumshe idanu yayi sannan ya buɗesu ya namata wani irin kallo murya can ƙasa yace, "Inafa lafiya Ummu na bayan a baccin ma zuwa kikayi, kikayita jagolgoleni duk kin turmusheni kin sani cikin wani yana yin". ya ƙarishe maganar yana kashe mata ido ɗaya da ɗan ɗaga mata girar sa, kunya sosai maganar shin ta sakar mata sunkuyar dakai tayi ta ajemai abincin da tea data haɗa mai a gaban shi tace, "Kacinye duka sai in baka kyauta". Ɗan ɗago kai yayi yace, "kefa?". kai kawai ta girgizamai alamar a a, kallon ta yayi cikin tsigar so da ƙauna yasa hannu ya ɗauko ɗaya cup ɗin ya haɗa tea mai kauri sannan ya ɗan kurb'a cup ɗin ya miƙa mata a hankali yafurta, "Ki shanye ba zafi sosai". karɓa tayi tana kallon idon shi shiko lips d'inta da suka sha jambaki sai shek'i suke ya kurawa ido a hankali yace, "Wannan janbakin dada hali zan tsotse shi dan ya rufemin pink lips d'inkin nan masu kyawun gani". Baki ta ɗan tsuke tana ɗan yimishi kallon ƙasa-ƙasa bai jira tayi magana ba yace, "l'ilam uhibbuki hubban azeem=kisani ina sonki so na hak'ik'a, bansan wanne irin murna zan yiba idan aka ɗaura mana aure, bansan wsnne iri so nake mikiba Ummu na, Anti faƙat fee hayatee=kekad'aice a rayuwata". Ɗan ɗago kai tayi tace, "Kamar cewa nayi kaci abinci ko? sannan ka tsaya surutu nikuma nafiso inga ka kaci abincin sannan kasha maganin ka". Karya wuya ya ɗanyi cikin wani sabon salon shauƙi yace, "Aaahhhh hubby zanci amma kinga wannan kallon? hmmmm". sai kuma ya haɗiye maganar da yayi niyar furtawan sannan yaja flate d'in yafara cin abincin cikin nutsuwa, Farouq daketa tsalle kan kujera ne ya sub'uce kamar zai fad'o dasauri suka tashi dukkan su sukayi gunshi hannu kowanne yakai dan riƙoshi aiko hannunsu ya haɗe wuri guda gun ɗaukan Farouq ɗin, Shiko Usman haɗe hannun ta dana Farouq ɗin yayi ya riƙe ya na murzawa a hankali itako ƙasa tayi da kanta, sun daɗe a haka sannnan suka koma suka zauna ya k'arasa cin abincin, itako ta tattare kayan ta ɗauka suka fita tare, suna fita suka haggo Dr. Bashir yafito daga motar shi, Cikin gida Ummul ta shige b'angaren Nanne shikuma Usman ya k'arasa gurinshi riƙe da hannun Farouq, suka gaisa ya tsuguna yakamo hannun Farouq ya ɗaukeshi, Usman ne yamai jagora har palour baƙi yazauna yana wasa da Farouq shikuma ya juyo yafito yana fitowa yaci karo da Abba na shirin shiga palour ɗan russunawa yayi yace, "sannu da fitowa Abba". Kallon shi yayi yace, "Dr na ciki ko?". "eh". yace sannan yasake cewa, "To ka jirani a palour Hajjajo zamuje gidan Daddy inna fito". da "to". ya amsa yawuce parlorn Hajjajon. Shiko Abba da sallama ya shiga palour suka gaisa cikin girmamawa, a hankali Abba yawa Dr Bashir bayani sannan yabashi hakuri akan abinda ya faru dakuma nuna mai jin dad'in shi akan yadda ya nuna soyayyar shi ga Ummul dakuma burin kulawa da Farouq, shiko Dr har zuciyarshi yaji daɗin yadda Abban yamai bayanin yakuma yi addu'ar al'khairi har zuciyar shi yakejin ya haƙura da ita kuma zaici gaba da kulawa da ɗansu Farouq, dahaka sukayi sallama ya fita ya tafi. Inda yayi parking motar shi anan Mustapha yayi parking kusa dashi yana fito suka gaisa cikin mutunci sannan shi Dr ya tafi, shiko Mustapha ya nufi cikin gidan, Aliyu ne ya tarbi Mustapha sannan ya kaishi palour ya zauna shikuma yashiga dan sanarwa auntyn shi Ummul zuwan shi. Gabanta na faɗuwa kanta a ƙasa ta shiga palour tasami guri tazauna cikin nutsuwa dajin kunya ta gaidashi kallonta yake kamar ya ɗauketa ya tafi da ita dan so da ƙauna, cikin wani irin salo murya a raunane yace, "Andawo lafiya? ya ibada Allah yasa karb'ab'b'yace". "Alhamdulillah, Amin". tace sannan suka ɗanyi shiru na wani lokaci da kyar tabuɗe baki tace, "Ya Mustapha daman inaso zamuyi magana sannan ina fatan zaka fahim ceni?". Gyara zama yayi yace, "Haba khairi kinsan ina gane duk abinda yafito daga bakinki kuma ina yarda da shi kuma kin san maganar ki abar fahimtace a gareni, fad'i maganarki". sake sunkuyar da kanta tayi tafara magana a hankali, "Dafarko zan maka godiya da irin kulawar da kake bamu kuma naji dad'in hakan sosai bani da abin cewa sai dai ince da kai jazzakallahu bil jannatul firdausi, abu na biyu kuma inaso in baka hakuri akan maganar da kayimin kafin nayi tafiya". Tuni zuciyar shi tafara bugawa da ƙarfi sai sake ƙureta da idanu yayi, Ita ko kai a sunkuye taci gaba da cewa, "Haƙiƙa kai cikakken masoyine kuma mai soyayya dan Allah sannan mai ɗaukan ƙaddara da yarda da ita a duk yadda tazo maka dan naga hakan a baya kai namiji kayi biyeyya ga iyayen ka ka ruggumi ƙaddararmu abin da ni mace ya kamata nayi shi amman taurin kai da zugar shaiɗan sun hanani ruggumar ƙaddara ta nayi ta cutar da masoyi na gashi yanzu rayuwata zata ƙare cikin nadama da dana sanin rashin bin umarnin iyaye kai kuwa na tabbata zaka samu farin ciki a rayuwarka tunda kayi biyeyya ga zaɓin iyayenka, Ya Mustapha inaso in faɗamaka na amince da auren ya Usman saboda dalilai da dama amma nasan zaka fahim ceni kuma ka kasance mai yimin addu'a a koda yaushe". shiru ta ɗanyi har zuwa wani ɗan lokacin muryarta ta fara sarƙewa cikin zubda ƙollah murya na rawa tace, "Zan auri ya Usman ko dan na sa farin ciki a zuciyoyin iyayena, zan auri ya Usman cikin aminci ko dan na goge laifin da nayiwa iyayena a baya na ƙin yarda da zaɓin su, zan auri ya Usman ko dan na reba Farouq da agolanci na kuma kasance tare dashi dan duk inda nayi aure ya Usman zai karɓe min Farouq, zan auri ya Usman dan zaiyi farin ciki farin cikin ya Usman kuwa shine abu mafi soyuwa a zuciyar Hamma na, zan auri ya Usman ko dan na kula dashi da lafiyarshi wanda kullum shine fargabar Hamma na, zan auri ya Usman ko dan ƙaunar da Ammi take min, zan auri ya Usman dan mu rayu tare mu cirewa Farouq maraicin mahaifin shi, zan auri ya Usman ko Allah zaisa Hamma na yayi farin ciki dani, zan auri ya Usman don Allah da zuciya ɗaya, Mustapha na cutar da Hamma na akan soyeyyar ka amman Hamma bai taɓa fushi dani ba bare yayi fushi da kai Mustapha yanzu bana son kowa a duniya sai Hamma na ya Mustapha inama-inama Hamma na zai dawo gareni inama tafiya yayi ta dawowa inama ace ni suka yanka suka barshi a raye na tabbata da shi zaimin wonkan gawa da shi zai sani cikin ƙabarina ya Mustapha a gabana suka yanka Hamma na yankan rago ya Mustapha Hamma na ya sadaukar da rayuwarshi a kan tawa ya Mustapha wallahi wallahi tallahi ina son Hamma Umar ina sonshi ina sonshi, kaito na ni Ummu tabbas naga illar rashin yiwa iyaye biyeyya kaitona da zuciya ta kaitona da taurin kaina kaito na da ƙin yarɗa da ƙaddara ta a haka zan ƙare rayuwata cikin dana sani da nadama ashe maganar da Hamma na ke cemin gaskiya ce yana cemin tabbas wata rana zaki soni fiye da kowa a duniya amman ban sani ba ko son zai amfanemu ashe gaskiyarshi a ƙurerren lokacin zan soshi, ya Mustapha washe gari za'a kashe min Hamma na na fara sonshi na yarda dashi bisa gaskiya amman suka zo suka rabani dashi". sai kuma ta kife kai tana kuka cur-cur cikin sauti mai cike da rauni da nadama, Shiko Mustapha gaba ɗaya duk ya ruɗe tausayin ta na ratsashi tabbas ranshi ya cika da raunida kukanta ya raunata zuciyar shi lokaci ɗaya hawaye suka rinƙa zubo mai a take yashiga matsanan ciyar damuwa cikin rawan murya yace, "Haba Khairi na fahimce ki kuma nagamsu naji daɗi daya kasance ɗan uwana ne yazama zaɓinki domin kuwa inajin duk wani ɗan gidan nan a matsayin ɗan uwana na jini, kuma ina ƙaunar su, har kullum burina shine dawo maki da farin cikin da kika rasa, a koda yaushe fatana in sa hawaye ya dena zuba a idanuwan ki Ummu tabbas Hamma Umar mutunne mai cikar daraja, nasan kukan da zakiyi shi zaisa kiji sanyi, amman dan Allah ki daure ki dena zubda mai ƙollah kiyi ta mishi Addu'a kiyi fatan Allah ya sadaku a al'janna, ni dama fatana in kawarwa Farouq tunanin maraici, Allhamdulillh nasan zaku sami haka a gurin Usman sama da abin da zaku samu a gun kowa, kuma na yarda da ƙaddararmu a karo na biyu dana kuma neman aurenki ban samuba Ummul na haƙura dake amman ki sani ke nafara so a rayuwata, nima nagode da kulawar ki gareni ƙanwata". Hakanan yaci gaba da yimata hira da nasiha a matsayin yayanta duk da bayajin dad'in zuciyar shi da jikin shi amma yana ɓoyewa dan kada itan ta damu itako da eh ko a a kawai take amsamai har yadauki ɗan lokaci sannan sukai sallama yatafi jiki ba ƙarfi. A palour Hajjajo Ummul tayi sallama sakamakon kiran da Abba ya aika Aliyu yayi mata, dukkansu suka amsa sallamar tasami gefen da Hajjajo take tazauna a ƙasa gaida Daddy da Abba tayi sannan Hajjajo da Usman sai ya Adam, Daddy ne ya kalli Usman da sigar tsokana yace, "To angon yafara bud'e mana taron da addu a". Kanshi a ƙasa yana dariya k'asa-k'asa ya ɗaga hannu sukai addu'a suka shafa sannan Daddyn yaci gaba da cewa, "Mamana wannan taron nakine, yanzu Abbanku yazomin da sadakin su sannan yace suna so ayi auren cikin ƙan ƙanin lokaci dan haka nace a kirawoki kiji da kunnenki sannan inbaki sadakin ki". Kanta na ƙasa batace komai ba Daddy yasa hannu yaciro kud'in ya miƙa mata tare da cewa, "Gashi mamana yi bismillah ki karb'i sadakin ki". Sake sukuyar dakai tayi ta b'oye fuskarta a cinyar Hajjajo kunya kamar ta tsaga ƙasa ta shige, hakan yasa Daddy da Abba dariya irin ta manya sannan Abba yace, "To wani ya wakilceta". Hajjajo ce takai hannu takarɓa tana cewa, "kubani idan bataso". duk dariya sukayi sannan sukayi addu'a suka tashi Abba yafi kowa murna yanata sanyasa y'artashi al'barka. Kamar kullum idan dare yayi Usman ke zuwa su sha hirarsu da Ummul enshi yauma haka yana dawowa daga masallaci, wanka yayi ya sha kwalliya sai zuba kamshi yake Adam dake kwance kan kujera a palour yanajin fitowar shi daga bedroom yasa dariya k'asa-k'asa aiko kamar a kunnen shi yajuyo yace, "Me kakewa dariya?." ,hannu yasa ya toshe bakin da hannun shi yana b'oye dariyar yace, "Kai malam nifa abu nake kallo a waya". Kwafa yayi yafice sai palour Nanne. Da Ammi yafara haɗuwa tana fitowa zatayi ɓangaren Hajjajo ɗan raɓawa gefe yayi itako ta kalleshi cikin kaunar ɗan nata tace, "hmm Usman manyan gari". Sunne kai yayi ƙasa yana sosa ƙeya, sannan ta wuce, shima ya shige, a palour suka zauna sunata zuba soyayya yanata rikita ta da kalamanshi masu daukar hankali cikin hirar sukai amfani da wayar ta suka kira Garkuwa kiran na shiga shiya fara magana, "Barka da dare Anutyn Ummu". "Barka dai ,ya kuke yasu Ammi da su babana Aliyu Auta?". da fara'a yace, "Suna lafiya lau kowa na gaidaki". "Na gode matuƙa". "Daman cewa nayi bari nayi maki godiya akan irin shawarwarin da kike bawa Ummuna sannan in sanar dake yau ta karb'i sadaki na sannan ansaka rana nan da sati biyu". "Alhamdullah gaskiya naji dadi sosai nakuma tayaku murna Allah yasa ayi a sa'a, bani ita nayi mata murna". hannu biyu tasa tarufe ido tana murmushi shiko sai cewa yayi, Kin ganta tana jinki tarufe ido wai kunya takeji, Anutyn Ummu gaskiya kiyi mata faɗa ta rege kunyar nan gudun karta takura mana rayuwa kuma dan Allah ki mata nasiha ta rege kuka dan naga tana jin maganarki". Murmushi tayi sannan tace, "Ummu yau kuma ni ake kunya to shike nan saina jiki anjima a online dan zamu tattauna inason karin bayani akan labarin kinga zamu fara". Da haka sukayi sallama sosai Usman yaketa zuba godiya, Basu jimaba ya rekata ƙofar ɗaki ta shige shima yatafi ɓangaren su. Shirye-shirye aka fara domin kuwa sati biyu kawai aka saka ranar auren dan haka Aunty Shuwa da Aunty Halima suka zage gurin gyara Ummul da taimakon Ammi da Hajjajo kullum cikin tsumata suke da tsumakansu na shuwa'arab sosai suke tsumeta naci dana sha dakuma na zama a ciki suna murjeta tuni ta murje ta ƙara fari da kyau ko ina na jikin ta ya ciko tib sai sheƙi takeyi fatar nan tata kamar ta jariri kuma ita da kanta tasan ta tsumi da tsumin mutan Yobe. Wata ranar asabar da tayi dai-dai da saura kwanki bakwai d'aurin auren Aunty Shuwa ta jiko abunda suka saba bawa Ummul kullum tafito palour Hajjajo inda suke zaune ita da Aliyu da Aunty Halima sai Nanne da Ammi da uwar gaiya Hajjajo, aiko tana ganin ta da cup ta ɓata fuska ta marairaice kamar zatayi kuka tajuyar da kai tace, "Ni gaskiya nagaji wallahi cikina a k'oshe yake yanzufa Aunty Halima taban wani nasha". Itama Anty Shuwa ɗaure fuska tayi ba wasa tace, "Kuma wannan ma yanzu zaki shanye shi ba, ni banson shirme ki amsa kishs kawai". Bubbuga ƙafa tafarayi a ƙasa tana yarfa hannu da ƙunƙuni ƙasa-ƙasa dai-dai lokacin shigowar Usman da Adam da Sadiq sun dawo daga gaida Inna, Dasauri Usman ya ƙaraso cikin palour yace, "Wai meye, Halima ce ko?". Ɗauke kai Aunty shuwa tayi kamar bata jiba itako Aunty Halima cewa tayi, "kai ya Usman to bani bace itada Auntyn ta". ɗan juyawa yayi ya kalli Aunty Shuwa data ɗaure fuska babu alamun wasa tace, "kyaleni da ita, abu nabata wai bazata shaba ta k'oshi". ɗan leƙa cikin kofin yayi sannan ya tambaya, "Magani ne?". "eh maganin ciwon ciki ba". Inji Halima, ganin yadda yajuyo yana kallonta yasa Nanne tashi ta fice dan ta gane sarai Usman ya gane maganin menene ake batan, dan tasan halin shi zai iya faɗan komai, a hankali ya ƙarasa inda take zaune yace, "Ummu na yi haƙuri kisha mana kinji kinga yanada amfani". Noƙe kafaɗa tayi alamar taƙi a hatsale Aunty Shuwa tace, "Matsamin dan Allah intafi ana baki kinawa mutane yanga wazai amfana? ni ko Halima ko ke?". Dasauri yamiƙe ya karɓi kofin ya tsura mata ido fuskar shi babu alamun wasa yace, "Ke wallahi sai kinsha ko in ɗura maki, wannan ai shirme ne, au tukun ma wai shin ko dai baƙin ciki zakimin?". da jin haka Ammi ma ta tashi ta fice tabarsu ganin taƙi karɓa yace, "Sadiq riƙe min cup ɗin Allah saina ɗura maki zakiwa mutane asara da baƙin ciki inke bakya so ni inaso kuma dole kishi". Yana faɗa yana matsowa kusa da itan sanin halinshi yasa ta miƙa hannu Sadiq ya miƙa mata kofin tana ɓata fuska takai bakinta, "Gwara miki dan wallahi ba abinda zai hana in d'ura maki shi". Saida ta shanye tas sannan tasauke kofin tana dama fuska kamar zatai amai, kallon Aunty Shuwa yayi wacce kunya ta rufeta har ta kasa ɗaga ƙafarta wato Usman yama gano me ake bawa Ummu, shiko ko a jikin shi yace daga yanzu in taƙi sha dan Allah ku kirani". Yajuya zai fita Hajjajo datake kallon ikon Allah tace, "fitsararre". Juyowa yayi kafin yaba ta amsa idon shi yasauƙa kan Ummul da taketa kakarin amai kallon ta yayi tare cewa, "Kada kiyarda ki amayar da abinnan dan sai an ƙara maki wani". Ficewa yayi suko duk sukayi shiru suna kallon juna itako tashi tayi tafice tana buga ƙafa. Yau asabar da misalin ƙarfe 10:30am na safe dubban jama a suka shaida daurin auren USMAN IBRAHIM UMUR SHUWA da amaryar shi RABI'ATU HASSAN UMAR SHUWA ciki da abokan Hamma Umar wanda dayawa suka sami gayyata daga Dr Bashir da kuma Mustapha shima da mahaifinshi, Ango kuwa Usman lokaci ɗaya tunanin ɗan uwanshi ya faɗo mai a take ida nunshi suka fara zubda ƙolla mai tsananin zafi yana tuna a yau ds Hamman shi na raye da zaifi kowa farin ciki da yau zaiga gata mai tarin yawa cikin kuka yake gaisawa da abokan Hamman nashi, bayan ya shiga cikin gida kuwa Ammin shi ya tasa a gaba suna wani irin kuka mai cike da ƙuna a zuciya da kyer aka samu Abba da Hajjajo suka tausasu. Haka abin ya kasance a cikin gida mata nata nasu hidimar ga matar Dr Bashir da matar Mustapha da Ummanshi, ita kuwa Ummul yau mutuwar Hamman ta takuma dawo mata ruggume Farouq tayi ta durƙusa gaban Adam da Sadik tana kuka mai tarin nadama da dana sani, Shima yaro ganin yadda mahaifiyarshi ke kuka sai ya fashe da kuka mai ƙarfi ayyah Adam shma gaba ɗaya ya kasa control en kanshi sai hawaye cur-cur ya kasa magana Aliyu kuwa jawo Farouq yayi ya riƙeshi gam a jikin shi suna kuka, Sadik ne da Anty Shuwa sukayi ƙarfin halin lallashin su da yi mudu nasiha, saidai Amaryar kam da kyer aka samu aka rarrasheta saboda kuka da takeyi mai tsanani dan tunawa da masoyinta Hamma Umar. Haka jama'a sukayi ta tayasu murna har zuwa dare aka fara watsewa. Ango yanata sintiri dan yana son ya lallashi Ummul enshi da kanshi kuma shima yana buƙatar ta tausayawar ta a gareshi dan yau gaba ɗaya begen Hamman shi yake, karo na 3 yashigo yasami Nanne da Ammi sai Aunty Shuwa da Aunty Nafisa yasami gefe yazauna gaisawa sukayi tare da ƙara yimai addu'a kai yafara sosawa yakalli Aunty Shuwa cikin rauni yace, "Ina take?". Haɗe fuska tayi sannan kuma abin nashi ya bata dariya ya kuma bata tsusayi a hankali tace, "To anace tanada bak'i". D'agowa yayi ya kalleta sannan ya saci kallon Ammi daketa ƙoƙarin maida ƙollar ta a hankali yace, "Dere yayi fa kuma zamuje wani wuri da ita Ayyah dan Allah a bani matata". Ammi ce ta karb'i zancen da cewa, "A,a baza a baka ba Usman, ainan ba gidan ka bane kuma da bakinka kace sai kaje course kadawo zata tare". Da hannu ta nuna mai hanya alamar ya tafi, marairaice fuska yayi kamar zaiyi kuka yace, "Nanne". Bai ƙarasaba tace, "Jeka kayi wanka ka huta babu mai hanaka matarka". Ɗan murmushi ya ido cike da ƙollah yatashi yafice yana ƙoƙarin cire babbar rigar jikin shi, Ammi ta kalli Nanne tace, "Bafa zan yarda da wannan tsarin ba". ƙasa Nanne tayi dakai cikin girmamawa tace, "Kiyi haƙuri Addana dan tun ɗazu Abban su yace kada a hanashi matar shi , dan duk su biyu kukan da sukeyi na abu ɗaya ne tuno Umar ne kuma su duka kowa zai tsaida hawayen shi dan ɗaya yayi shiru, kuma ai banga laifin hakan ba tunda mutune dayawa suna aure su tare gidan iyaye nasu kinga shima yanada damar hakan kuma kinga yama kusa yin tafiyar". Aunty Shuwa ce ta kalli Ammi tare da cewa, "Ammi ki kyale ɗan Abba yasha sha anin shi dan wallahi dagashi har Ummul sun ban tausayi ga yadda ƙaddara ta haɗasu bawan Allah Farouq shima yau yayi kukan rashin Uban da bai saniba". Itako Ammi baki ta d'an rumtse hawaye na bin fuskarta tace, "Hmmm to Allah yayi musu albarka Allah ya jiƙan Umar Allah ya mishi rahama Allah ya raya abun da ya bari". "Amin Amin Ameeeeeeeen ya rabbil izzati" suka amsa baki ɗayan su, Aunty Nafisa matar Daddy wacce tunda aka fara magana tayi shiru tace, "Au shiyasa naga Adam da Halima sunata shirya Ummul ɗin". Ammin ce ta miƙe tana tafiya tace, "eh mana ai duk bakinsu ɗaya har da Adam kamar mace, nidai baruwana kuma bame takuramin yarinya. A ɗakin su Usman kuwa Adam ne da Nuru sukayi ta lallashin Usman, miƙewa sukayi jin muryar Anty Halima wacce ta shigo ruggume da Farouq Ummul na biye da ita a baya, A hankali tace, "Ga Farouq tun ɗazu yake kuka sai a kawoshi gun Abeen shi". hannu Usman yasa ya karɓeshi sannan ya ruggemeshi suko Anty Halima da Adam da Nuru fita sukayi suka bar part ɗin gaba ɗaya. Shiko Usman suna fita yasa hannun ya ruggum..... *By* *GARKUWAR FULANI* [12/5, 9:42 PM] ‪+234 808 364 9787‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMRI* Page 3⃣7⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *MOH ALLAH WUJI FURƊA TA FULLO BE FULAKU KOSAM EH DAN GOL* *Wannan shafi naki ne ke kadai k'anwata ta kaina Queen Hafsi Allah bar zumunci da k'auna dear 🤝* *H*annu yasa ya jawa Ummul ɗin ta faɗo jikin shi cikin sauƙe ajiyan zuciya ya haɗasu da Farouq ya ruggume su tsam a jikin shi yana jin wani irin yanayi mai cike da tarin rauni, tabbas wani abu sai mutuwa inba mutuwaba ya za'ayi ya auri Ummu matar ɗan uwanshi gaba ɗaya begen ɗan uwanshi ya rufeshi zuciyarshi ta cika da rauni a hankali wani irin kuka ya kufce mai, kuka mai cin zuciya har jikin shi na rawa sai ƙara ruggume ta yake yana sheshsheƙa hawaye na bin fuskar shi, itama Ummu sai kara lafewa tayi a jikin shi tacigaba da kukan dama tun safe take yinshi, Kuka suke sosai bame rarrashi wani a cikin su sai ruggume juna sukeyi suna kuka mai cike da ƙuna a zuciya, sun ɗau lokaci mai tsawo suna cikin yanayin tuno da jigonsu gaba ɗaya zuƙatansu sun cika da rauni, Cikin kukan Ummu ta ɗago kanta fuska cike da ƙollah ido ta ɗan firfitar ganin yadda numfashin ya Usman ke fusga yana neman ɗaukewa sai karkarwa yake ida nunshi sunyi jazir ƙirjinshi na bugawa da ƙarfi , janye jikinta ta tayi hankali ta miƙa hannun ta karɓi Farouq dake ta bacci daga hannun shi tamatsa a hankali ta kwantar dashi akan 2 seater, sannan tadawo jikin shi ta ruggume shi a hankali takamo hannun shi ta jashi suka zauna kan 3 seater, ruggume shi tayi cikin kuka da rawar murya tafara magana a hankali tace, "Hamma Umar baida wani fargaba daya wuce ya ganka cikin tashin hankali, kullum burinsa ya ganka cikin farin ciki, fatan Hamma Umar baya wuce samun lafiyar ka ya Usman, ko a lokacin da zai rasu sunan ka dana Ammi ya kiramin amman Allah bai bashi damar karisa min maganar da yake son faɗa minba sai yayi kalmar shahada, Abunda ban saniba wata ƙil amanar ku zai barmin ko cemin zai na kula da kune ban saniba". Tana kaiwa nan suka daɗa rungume juna suka sake fashewa da kuka jiki na rawa ya kuma matseta a jikin shi murya na rawa yace, "Ummu na ni kam Hammana yabar min amanar ki keda Farouq randa yayi zuwanshi na karshe a gidan nan, saida duk ya bar mana wasiya amman a lokacin bamu ganeba, Ummu kituna meyace min nida Adam". sai kuma ya sake matsota jikinshi yana zubda ƙolla sannan yaci gaba da cewa, " Hamma na cemana yayi, "Da inada damar tafiya da Ummul duk inda zanje, da ko ina zanje zan tafi da ita, sai dai kach bani da damar yin tafiya da ita dole in barmaka ita Usman kaine ɗan uwana kuma dole ka kula da family na, Ummu kin tuna abinda yacewa Adam yace Adam zantafi da ita amman zata dawo in tadawo duk maison ɓata min rai ko tozar tani to ya ɓatawa Ummu rai niya ɓatawa! Ummu kin tuna abinda Hamma yacewa Aliyu, yacewa Aliyu kai kuwa Aliyu a zatona kaine abokin kukan ta kaine abokin shawarar ta Aliyu ko duk zasu dakarmin Ummul a zatona kai zaga zame mata katanga abun jingina azatona kai mai tayata kuka ne". Sai kuma ya sake ruggumo Ummun cikin tarin ƙunci ya sauƙe nannauyan ajiyar zuciya yace, " Kin tuno me yacewa Sadik Cemai yayi "Sadiq inta dawo ka kasheta don dole zata dawo badon ina soba dole zata dawo cikin ku ba yadda na iya, ya kuma cewa Nanne Ummul fa madadin mutum 3 ce ni Usman da Ammin mu dakuma ɗan cikin ki ya ware kanshi a lissafi ashe zai tafi ya barmune bamu saniba tafiyar da bazai dawoba ashe duk maganganun shi wasiyace a garemu, Ummu dana sani dana hana Hamma na tafiya a wannan ranar, ashe shike nan mun rabu har abadan, ashe shike nan yayi zuwanshi na ƙarshe a gidan nan, Ummu ki tuna a ranar Hamma yace min, Usman nauyin farin cikin Ahlina yana kanka in bananan". Sake matsota yayi yaci gaba da kuka har yana shiɗewa, Cikin tsana nin kuka itama ta ruggumoshi tana cewa, "Ya Usman kayi hakuri mubar yiwa Hamma na kuka muyi mishi addu'a zaifi farin ciki damu, kabar kukan nan Hamma bayason kukanka nima banason kukan ka, ya Usman ina sonka ina son farin cikin ka ka dena kuka". Cikin kukan ya tallabo kanta ya kalleta da kumburarrun idanun shi ya sakar mata murmushin dayafi kuka ciwo a hankali yace, "Allah ya ɗaiyaba min Ummuna, nima ina sonki". Itama murmushin tayi wanda hawaye ke bin fuskarta a hankali tasa tafin hannunta tashare mai hawayen, shima haka yasa hannu ya share mata nata ya ruggumo ta yana sauƙe nannauyan numfashi a hankali yace, "Ummuna zan dawo miki da farin cikin ki keda Farouq ko Hammana zaiyi farin ciki dani". Shiru tayi tana kallon shi cikin jin tausayin shi, Shiko ido ya lumshe cikin sanyi yasa hannun shi yana shafe fuskarta tare da gashin kanta hannun yasa ya ƙara jawota jikin shi cikin salon lallashi yasa hunnun shi yana shafa jikinta yana sunsunarta tare da goga sajen shi a kumatun ta, a hankali ya rinƙa fese mata iska mai sanyi cikin kunnen ta, hannun shi yarinƙa cusawa cikin rigarta yana yiwa kirjinta wani irin salo mai wuyar faɗuwa yana sunsunar wuyanta yana wani irin numfashi gaba ɗaya ya gigitata ya gigita kanshi, itama sai sake narkewa take jikin shi tana mika tana ɓoye fuskarta a jikinshi cikin tsananin kunya, haka suka kasance cikin yanayin rarrashin juna da kyar ta zame jikinta, ta koma gefe tana gyara rigarta da ya cukuikiye a hankali takai dubanta ga agogon dake manne a palour 12 dai-dai shiru tayi a wurin tana satan kallon shi yadda ya kife kanshi a jikin kujerar yana maida numfashi gaba ɗaya yayi wani iri, da kyar itama ta saita kanta a hankali tace, "Ya Usman tashi ka rakani zan koma cikin gida kar Ammi ta farka taga Farouq baya kusa da ita". riƙo hannun ta yayi murya na rawa yace, "a,a dan Allah kibar shi mu kwana anan". miƙewa tayi tana girgiza kai, "a,a gaskiya nidai tafiya zanyi wallahi ni kunya nakeji bazan iya kwana anan ba". Shima miƙewa yayi ya kamo hannun ta ya lonƙoso kai yace, "Ki taimaka min habibty zan shiga wani hali in kika barni cikin wannan yana yin ina buƙatarki kusa dani, ki kaishi saiki dawo in kinga kowa yayi bacci kinji plssss". Dakai ta amsa mai alamar "Toh". dan ya Usman yana bata tausayi kuma tana tsoron karta kuma irin kuskuren da tayi a baya A hankali ta ɗauki Farouq ɗin ta fita kai tsaye ta wuce ɗakin su inda ta samu tuni Ammi tayi bacci. Kwantar dashi tayi akan gado a kusa da Ammin, sannan taje tayo wanka tashafe jikinta da turaruka masu ƙamshi da sanyaya zuciya sai kuma itama tazo ta kwanta gefen shi, Addu'a tayi ta tofa mashi ta tofe kanta sannan ta kwanta tajanyo wayarta ta buɗe data dan taga ya Usman nata kiranta kuma bata son ɗagawa kar Ammi ta tashi, tana buɗe datan saƙon shi ta gani, "ina jiranki a kofar Nanne ki fito mutafi kinga kowa yayi bacci". Amsa tamaida mai, "kayi haƙuri kaje ka kwanta saida safe". "gaskiya bazan iya baccin ba kizo ki taimaka min in kuma bakizo ba kuka zanyi tayi har gari ya waye, daman ni nasani ba mai sona sai Hammana". Jiki na rawa ta kashe wayar gaba ɗaya ta lallaɓa dan kar Ammi tafarka ta fice, a bakin ƙofar palour ta taddashi tana fita yasa hannu ya ɗauketa cak ya ruggume ta a jikin shi, bai sauketa ko inaba sai sai akan gadon shi, A hankali ya kontar da ita cikin wani irin yanayi ya konta gefenta a hankali ya jawota jikin shi yana maida numfashi hannun shi ya cusa cikin rigar baccin jikin ta yana mata wani irin salo mai taɓa zuciya a hankali yake sarrafata da salo mai cike da so da ƙauna haɗe bakinsu guri guda yayi yana mata wani irin tattausan kiss, hannun shi nakan kirjin ta yana murzawa dukkansu sun rikice sunyi nisa cikin duniyar masoya a haka sukai ta fama har bacci ya ɗaukesu suna ruggume da juna cikin happy. A zabure Ummu ta farka, aiko tare suka mike yana daɗa matseta kamar zaa kwace mai ita, "Ya Usman kabarni intafi kafin kowa ya farka kaga an fara kiran salla ". Wani irin kallo yake mata kamar zai haɗiye ta baice komaiba ya saketa, dasauri ta fice bayanta yabi da kallo badan yasoba banɗaki yashiga yayi wanka sannan ya fito ya fara nafilillin shi. Gari na wayewa misalin 8:00 Usman ya shirya tsab yaje yagaida Abba da Hajjajo sannan ya shiga ɓangaren Nanne, a kitchin yaji motsin Nanne dan haka ya tsaya ya gaidata sannan ya wuce ɗaki, zaune yasami Ummul a kan sallaya Ammi kuma na bakin gado ta zuba mata idanu, kamar jira take ya shiga tana ganin shi ta zuba mai ido cikin son gano halin da ɗan nata ke ciki, Shiko Usman a hankali yazo ya zauna a gefen ta yana gaida ta, ɗago kai tayi tana kallonshi, sai kuma ta sunkuyar da kanta ido cike da kolla a hankali ta fara zub da hawaye sai sautin kukanta dayake fita a hankali dasauri sukayo gabanta suka durkusa suna tambayar ta ko meya sameta suma idonsu tab kollah, cikin kuka tace, " Usman wato wannan shine gatan da zakuyiwa Umar kenan ko Usman? sai ku taru kuyita mishi kuka? An haɗaku aure dan a nazaton zaku samawa juna sanyi da sassaucin zafin rashi shi amman ashe bamu saniba hakan an baku damar ku zauna kuyi ta mishi kukane". Usman ta kuma kalla da duk jikinshi yayi sanyi tace, "Usman bakaso hankalina ya konta ko? Kasan bana son tashin hankalin ku kaida Ummu kuma shine kake ƙarawa ga yadda fuskokin ku suka kubbura, Usman har sai yaushe zamu bar kukan rashin Umar? Usman ai kukan rashin shi bazai kare manaba har sai randa muka konta damarmu daurewa zamuyi mubar zubda ƙollah muyita mishi Addu'a, amman hakan ya gagara da sai ka tasa Farouq a gaba kaɓuya kayi ta kuka yanzu kuma Ummul zakake tasawa a gaba kana kukan kenan?". Shiru sukayi cikin sanyi da yarda da nasihar Ammin, A haka Abba da Adam suka shigo suka samesu suma suka ɗora tasu nasihar har saida sukaga sun sake suka je sukayi break cikin wolwola. A ranar bayan sunci abincin dare ne suka zauna a palour Nanne dukkansu suna kallon news a tashar TVC News suna zaune kowa da abinda yakeyi amman ita Ummul gaba ɗaya hankalin ta na kan tv sai Aliyu dake zaune gefenta ta saman hannun kujerar da take zaune Usman kuwa yana gefen ta a kan kujerar suna cikin hirar kawai sai sukaga Ummul ta miƙe cikin tsananin razana da firgici gaba ɗaya jikinta sai rawa yake cikin gigita ta damki hannun Aliyu dake kusa da ita sannan ta nuna tv da hannunta ɗaya baki na rawa murya a hargitse take nuna tv tare da cewa," "Ammi gasu Ammi sune ya Usman kallesu wallahi sune Ammi sune suka k..". Bata ƙarasa maganar ba tayi baya a sume ta faɗa kan Usman, wanda ya taso tunda yaga yanda jikinta ke rawa, dukkan su kanta sukayo kowa yana addu'a da jimamin damuwarta da gudu Sadiq yaɗebo ruwa ya mikawa Ammi jikinta na rawa ta yayyafa mata sannan ta shafa mata a fuska, Lokaci ɗaya tayi wata irin ajiyar zuciya sai takuma razana tana ɗago kai idanu wanta a zazzare cikin tsoro Ammi tace, "Wai meke razanata ne haka fa in baku mantaba hakan yafaru da ita cikin azumi ta suma". sai ta kuma kallon ta cikin tausayawa tace, "Ummu na faɗamin me ke faruwa?". Cikin firgici jiki na rawa tare da rera kuka mai cike da ƙuna a zuciya ta nuna fuskokin da ake nunawa a tv tace , "Ya Usman kallesu sune suka yankamin Hamma na a gabana sune suka kasheshi wallahi har abadan bazan manta waɗan nan fuskokin ba bazan manta fuskokin suba wallahi sune". Gaba ɗaya jikinta na rawa, sosai Usman yasake matsota ya tare mata fuskar ta daga kallon tv shima yana rumtse idanun shi da ƙarfi dan har abada bazai so ƙara kallon waɗannan mutanen da suka kashe mai Hamman shiba, Adam dayake tsaye jikin shi yana rawa yafara musu bayani, "Hakane cikin azumi wani azumi daya wuce ankama waɗanda suka kai harin bomb a Jos! Kano da Zaria a gurin da ake verification na malaman makaranta, an kamasu ne a hanyar komawar su a Daɗin Kowa ta jahir Gombe, wannan da take nunawa yanzu dashi a cikin su yanzu kuma dasune akayi musaya suka bada y'anmatan Chibok da aka sace sukuma aka badasu wa uƙiyar tasu". Sadiq ne yakar ɓi zancen da cewa, "Ammi waɗannan dukkansu y'an asalin nan potiskum ne fa wata ƙil". Usman da tunda aka fara maganar baice komaiba sai addu'a da yaketa tofa mata, ganin har yanzu bata dawo hayyacin taba yasa yamiƙe hankali itama ya ɗagota duk jikinta na rawa suka fita yanufi ɓangaren shi da ita tana makale dashi tana rawar jiki da zazzaro idanuwa, Suko su Ammi da su Adam ɗin gaba ɗaya haka suka zauna sunata jajantawa da yiwa Hamma Umar ɗin addu'a. A ɓangaren su Ummul kuwa kukan taketa yi a kiɗime, ganin haka yasa Usman ya wuce da ita part nasu kan kujera ya jawota suka zauna rarrashin ta ya rinƙayi amman ina ya rigada Ummu ta buɗe shafin kuku dan ganin fuskokin waɗanda suka kashe mata ɗan uwanta kuma mijin ta, jawota jikin shi yayi a hankali ya tallabo haɓarta cikin sanyi da zubda ƙollah ya haɗe bakin shi da nata wuri ɗaya kissing ɗinta ya rinƙayi cikin salon son tsaida kukan nata daga nan ya gama rikitata da salon soyayyar shi mai tsanani duk da kuwa shima yanayi yana zubda hawaye, haka suka kwana ranar ma yanata ririta ta da son sama mata nitsuwa, sai dai duk yanda yaso daya samu damar raɓarta bata bashi damar kusantar taba shikuma baida niyyar takurata haka dole ya haƙura kamar yadda ya haƙura jiya, Asubar fari ta tashi ta gudu kamar yadda tayi jiyan. Usman ne yasami Abba da Daddy a safiyar litinin a palour Hajjajo yake sanar dasu cewa tafiyar shi zata kama cikin satin nan zuwa ranar juma a, kuma zaitafi da matar shi dakuma yaronshi Farouq duk da ba daɗewa zaiyi ba aiki ne kawai zaije na watanni uku yadawo, Addu'a sukayi mashi cikin jin daɗi sannan Abba yace, "Usman bazan hanaka ɗaukar matar ka da yaron kuba amma inaso ka fahimci hakan zai iya taɓamai karatu shi kada kayi tunanin dan yanzu yafara bazai sami matsala ba amma kaga ko zuwa kayi ka sakashi makaranta acan watanni 3 kawai zaiyi kasake ɗaukoshi kudawo kaga canje-canjen makaranta baida daɗi ga yaro dan haka kayi hakuri kutafi kubarshi anan yana zuwa makaran tar shi har kudawo ku sameshi ina ganin baza a sami wata matsalaba tunda daman yasaba da iyayen ku gakuma Adam da Sadiq sannan ga abokinshi Aliyu". Kanshi a kasa idonshi yafara ƙollah ya daure ya danne halin da yake ciki gudun kada su Abba su gane a hankali yace, "To Abba shikenan saimu barshi". sai ya kuma ɗan gyara zama cikin sanyi yace, "Abba dama Ummu tace min tana son zuwa gun AYSHA ALIYU GARKUWA marubuciyar dake rubuta labarin tannan to dama mun gama shiri kafin mu tafi Malesia sai munje garin su Garkuwar toh shine nake so in zamuje can ɗin kam a barmu mu tafi da Farouq dan itama Aysha tana son ganin Farouq ɗin". Daddy ne ya ɗan kalleshi cikin murmushi yace, " ba damuwa Usman Allah yayi muku albarka yasa ayi tafiyar a sa'a Allah ya kuma dawo daku lafiya". Da "Ameeen duka suka amsa sannan sukayi ta tattaunawa kafin suka watse. Ɗaki Usman ya koma yafaɗa kan gado yanajin wani irin zafi a zuciyar shi idanuwan shi na zubar da kollah a hankali yajanyo wayar shi yakira Ummul tana ɗagawa yace, "Kisameni a ɗaki". yana faɗin haka ya katse kiran, jin muryarshi yasa jikinta yin sanyi dan ta fahimci akwai damuwa tattare dashi dan haka ba ɓata lokaci ta fita ta nufi ɗakin nashi. Sallama tayi a parlour taji babu motsin shi dan haka ta murɗa kofar bedroom ɗin a hankali da sallama ta shiga, kwance yake yana kife a haka ya amsa sallamar ta yaɗago hannu ya kamota sannan ya juyo ya janyota jikin shi zamewa tayi ganin ƙollah a idanun shi tasa hannu ta goge mai a hankali tace, "Menene kuma?". Shima tashi yayi ys zaune ya ɗora kanshi akan kafaɗarta duk ya narke a jikin ta cikin shogoɓa yace, "ba komai Ummuna". hannu tasa ta shafa sajen fuskarshi tare da cusa hanun ta cikin suman kanshi tana ɗan murza yatsunta a ciki murya can ƙasa cikin raɗa tace, "Da komai kam ya Usman, daman tunda naji Abba yaje yana faɗama Ammi da Nanne yanda kukayi akan tafiyar nan kuma naga kiranka sannan naji muryarka nasan abunda kake wa kukan". Hannu tasa tashafi gefen fuskarshi tare da shafa wuyanshi zuwa ƙeyan shi ta ƙara manna kanshi a ƙirjinta cikin tattausan lafazi tare da sanyin murya tace, "Yanzu saboda sunce kabar Farouq ne kake kuka? Baka yarda da kulawar da zasu bashi bane? dan Allah ya Usman ka rege son da kakewa Farouq dan Allah kada kabari wani daga cikin iyayenmu yaga raunin zuciyarka akan wannan abun, domin baza suji daɗi ba, ni dakai zamuyi ƙoƙari mu danne damuwar mu musawa zuciyoyin mu haƙuri tunda ba rabamu dashi akayi gaba ɗayaba watanni 3 kamar yaune kadaure kaji ko? ya Usman na ko sokake nima nakasa jurewa nayi kuka har su gani?". Ɗago kanshi yayi yana juya mata kai alamar a,a duk ya wani maraice mata tamkar yaro sai fama nuƙurƙusanta yake da salon sakalcin sa da Hamma Umar ya sakal tashi, a hankali yasa hannu yakamo fuskarta ya zuba mata idanu sannan cikin karya murya yace, "Nabari Noor ƙalbee na nadena zan jure badan raina yaso hakan ba Ummu bana son duk wani abu da zai nisan tani da Farouq". ganin zai sake tada rigimar tasa yasa ta ɗan tureshi ya konta sannan ta ɗan kifa ƙirjinta kan nashi a hankali ta ɗan murza haɓarta a kan sajen shi cikin salon kawar mai da damuwar tace, "Naji ka gayawa Abba zamuje garin su Anty Aysha ko?". kai kawai ya iya gyaɗa mata dan tuni ta rikatashi ta yadda ko maganar zata bashi wuyan yi, ita kuwa lips enshi ta kalla sannan tasa yar yatsarta tana zagaye lips en nashi cikin happy ta lumshe ido tare da cewa, "To yaushe zamu tafi? in munje kwana nawa zamuyi?". hannu yasa yana shafa bayan ta a hankali cikin cushewar voice yace, "Hmmmm hahhhh gobe zamu tafi kuma kwana biyu zamuyi, in muna dawowa zamu biya Yankari muyi kwana ɗaya in mun dawo da kwana ɗaya zamu wuce malesia". murmushi tayi tare da subbatar lips enshi sai kuma tayi maza zata janye jikin ta, amman ina tuni Usman ya samu damar yi mata tsotsar Lolly pop a haka sukaita lallashin juna sannan suka rabu ta koma cikin gida ta fara shirin zuwa garin Fulɓe gun Antyn ta Garkuwa. Washe gari da safe suka kama hanya dan tafiya ce mai nisa a tsakani, inda Garkuwa kuwa take ta farin ciki da zuwansu tana ta shirya musu tarba ta musamman, Alhamdulillah sun zo lafiya ga Garkuwa ga Ummul ga Usman ga Farouq ɗan Hamma Umar, sunsha hira sosai Inda sukayi kwanakin su cikin jin daɗi sannan suka shirya suka koma jiharsu ta Yobe sun koma lafiya sun bar Garkuwa cikin kewar Ummu da Farouq da Usman Allah ya ɗaiyiba. Shirye-shirye suke dan tafiyar su kasancewa zasu tafi ranar juma a su tashi zuwa kasar malesia. Ranar juma a misalin 12:00 am jirginsu ya tashi zuwa Dubai inda dagacan kuma suka hau jirgin Qatar air ways zuwa kasar malesia, sun sauka a filin sauka da tashin jirage na jalah sultan isma'il, kuala lumpur. daga nan suka ɗauki hanya da jagoran cin wasu abokan aikin ya Usman dake can da zama zuwa jalal pentaling tafiyace mai nisa sukayi saida suka wuce masjid Jamet da flea market sannan suka ɗauki hanyar pentaling street, anan ne suka tsaya a fest shin kee beef noodles suka sai abinci sannan suka wuce soho city inda duka sauƙa a ɗan madaidaicin gidan da aka basu, wanda yake da 2 bedroom sai parlour su mai d'an girma sai kitching da dinning area gida dai ɗan dai-dai buƙatar su kuma akwai komai na kayan more rayuwa, da duk wani kayan bukata a gidan, a gajiye suke dan haka sukayi wanka suka ɗanci abincin da bai musu daɗiba suncine dan yunwa suka kwanta bacci. Haka suka kwana cikin ɗan gajiya sai asuba suka tashi sukayi wonka sannan sukayi sallah suna idarwa suka ɗanyi karatu har zuwa 7:30 nasu na can wanda yayi dai-dai da kusan ƙarfe biyu kenan a ƙasarmu nan, a hankali Ummu ta ɗanyi miƙa tare da yin hamma a hankali ta yuƙura zata tashi, da sauri Usman dake kallon ta cikin wani irin salo ya ɗan jawota jikin shi sannan ya kuma miƙewa yana ruggume da ita ya koma kan gado da ita yana kontar da ita, shima ya raɓa gefen ta ya konta a hankali y............ *By* *GARKUWAR FULANI* [12/5, 10:03 PM] ‪+234 808 364 9787‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 3⃣8⃣ *Na* *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Wai-wai na kusa nayi tuya na manta da albasa Amman na tuno takwarancy tawa AISHA ALIYU TSAMIYA sa ranki a inuwa bazanyi littafi har na gama ban baki kyautar shafiba Insha Allah haka bazata tab'a faruwa ba dan ke tawace dan haka wannan shafi gaba d'ayanshi naki ne kiyi yadda kikaga dama dashi ana tare🤝☺😉😍😘* *A* hankali ya kontar da ita sannan yasa mata pillows a bayanta ta yadda ta d'an taso sama kad'an kamar ya jingina nata, A/C ya kuma k'arawa gudu sannan ya zare jallabiyar jikin shi ya ajiye gefe, sai kuma ya haura kan gadon cikin wani irin salo ya rab'a jikin ta kanshi ya manna a tsakiyar k'irjin ta sannan yasa hannun shi duka biyu ya zagayo k'ugunta ido ya lumshe tare da sauk'e ajiyan zuciya yana mai fidda numfashi a hankali idon a lumshe ya rink'a murza fuskarshi a kan dukiyar fulaninta yana mai k'ara k'wak'wumota joking shi tamkar zai had'iyeta, janyota jikinshi ya k'arayi ya fara yi mata wani irin salon shafa da kissing ɗinta tako ina sai shushunar wuyanta yakeyi yana murza kanshi a k'irjinta zuwa k'asan wuyanta, tuni yafara rikitata gaba d'aya ya kaita tsakiyar duniyar masoya a hankali ta fara mik'a tana d'an lumshe ido sai kuma ta cusa yatsunta cikin tarin sumar kanshi tana d'an murza yatsunta tare da d'an kame jikin ta, ganin zai zautar da ita tasa hannun ta manna k'irjinta tana d'an tureshi, yayin da shiko take hakan kamar wani salon romancing take mai gaba d'aya yagama susucewa duk ya daburce ya d'imauce ya zama tamkar zaucecce, cikin rawan jiki yasa hannu yana zame rigar jikinta kanshi kuwa ya kife a k'irjin ta, nanfa jikin shi yafara rawa yana shafa k'irjinta a hankali cikin wani irin bak'on yanayi da bai taɓa jiba sai jan numfashi yake da k'arfi yana murzata a jikin shi yana mai sauk'e ajiyan zuciya. Ita Kuwa Ummul ganin yana neman wuce gona da irin yasa ta fara zubda k'ollah cikin rauni a zahiri take ganin kamar amanar Hamman ta take son ci a ranta take ganin sam auren Usman bai dace da itaba yau gashi ya Usman yana shirin kasan cewa a matsayi da Hamma Umar ya kasance a gareta a shekaru 3 da suka wuce cikin sanyi, tasaka hannun ta duka biyu a k'irjin shi tana ɗan tureshi da janye jikin ta daga rilkon da yamata, shi kuwa sai k'ara mak'aleta yake yana k'ara manna kanshi a k'irjin ta yana isar da sak'onnin shi masu wuyar fad'uwa, Jiki na rawa tak'ara tureshi da k'arfi tana jujjuya kai ido cike da k'ollah, Da kyer tasamu ta zame jikinta daga gareshi jiki a mace ta mirgina tayi juyi ta d'an zame k'asan gadon ta dunk'ule jikin ta a guri ɗaya ta manna kanta a jikin gadon ta d'an kifa guiwowinta k'asa gaba d'aya jikinta sai rawa yake tana faman zubda k'ollah tana k'ok'arin jawo blanket d'in ta rufe jikin ta, Jiki na tsunami shima ya mirgino k'asan kusa da ita jiki babu kwari idanuwan shi duk sun canja sunyi jazir sun cicciko da k'ollah sai shek'i sukeyi alamar a ko wanne lokacin zai iya zubda k'ollah, k'irjin shi na bugawa da sauri da sauri duk tsikar jikin shi ta mimmik'e, Idanun shi da suke cike da k'ollah ya zuba mata naɗan wani lokaci sannan cikin disashiwar murya mai cike da rauni murya na rawa yace, "Ummu na kiyi hak'uri ki taimaka min, wallahi ina wahala sosai a duk lokacin da kika gujeni ina cikin wani yanayi please ki Jik'aina, Wallahi a yanda nake ji yanzu zan cutu in baki matso gareni ba, kinsani namiki uzuri a gida saboda a tunanin kunyace tasa kike guduna kinaga a gida muke, Sannan haka kika yimin a yola wanda nayi zaton in munyi nesa da gida zaki tausaya min, amman har muka dawo kin kasa amsata a matsayi mijinki duk da hakan nayi miki uzuri nace duk kunya ce, to yanzu munyi nesa da duk wanda zakiji kunyar gaba d'ayama bama k'asar tamu amman kuma kalli yadda kike min, haba Ummu na kiyi hak'uri kibani hak'k'ina mana please wallahi a takure nake". Ya k'arashe maganar cikin sigar lallashi, Itako Ummu wacce tunda ya sauk'o k'asa ta rumtse idonta da k'arfi ganin yadda ya matsota ba komai a jikin shi sai blanket da ya jawo ya rufesu, Kuma duk maganar da yake hannun shi na kan k'irjinta, jin yayi shirune ya k'ara matsota ya manna bakinshi a k'irjinta, yasa ta bud'e ido cikin rauni da muryar kuka tace, "Hamma na, ya Usman bazan iya amincewa da kowanne namiji a duniya bayan inba shiba, Ya Usman inajin kunyar hakan, bazan ci amanar shiba". Ta k'arashe maganar cikin kuka mai tsanani. A hankali yasa hannun shi ya rungumo ta tsam a k'irjinshi, cikin tsananin mutuwar jiki yafara shafa bayanta zuwa wuyanta yana d'an murza k'irjinta a nashi k'irjin yana d'an hura mata iska a kunne tare da d'an bubbuga bayan ta har saida yaji ta sassauta kukan, sannan ya ɗagota ya maidata kan gado ya kwantar da ita yaja mata bargo sannan ya manna mata kiss a goshinta, Sannan yajuya jiki babu k'arfi ya shine bathroom ruwa ya sakarwa kanshi yana yi yana zubda k'ollah a haka yayi rink'a tsayuwa cikin ruwan har saida yaji hankalin shi ya dawo jikin shi sannan ya fito ya shiga kitchen ya had'a musu breakfast. Bacci take sosai har yagama abinda zaiyi ya shirya tsab, Sannan yaje yasake manna mata kiss a goshi ya gyara mata lulluɓin bargon yafita wurin aikin da yazo yin. Sai wajen 12:00 pm agogon kuala lampur ta tashi daga baccin, wanka tayi sannan tayi break, tana gamawa ta shiga kitching tadafa musu abinci, Sannan tadawo palour ta kunna Tv ta kwanta kan 3 seater tabuɗe data wayarta tafara chat da yan uwa, har k'arfe 3:00 pm tana ta chat salla ke tada ita duk da kuwa da Aliyu ne kad'ai take chart d'in sai kuma Aunty Aisha Garkuwa, Dawowar Usman yasa tayi musu sallama ta tashi ta nufi inda yake tsaye ya buɗe mata hannuyen shi, a kunyace taje ta d'an faɗa jikin shi tana mai rumtse ido, rungumeta yayi da k'auna yana kissin wuyanta tare da tallabo kanta yana d'an lasan lips enta, A haka suka ɗauki lokaci mai d'an tsawo sannan tazame jikinta ta kama hannun shi suka shige bedroom, Wanka yayi sannan sukaci abinci suka cigaba da hirarsu har lokacin sallah magrib, basu tashi daga sallayar ba har saida sukayi sallah isha'i sukayi addu'o'in su sannan cikin lumshe ido Ummul ta d'an kalleshi murya can k'asa tace, "Ya Usman zanyi bacci yanzu dan Allah ka tasheni anjima inason ganin posting ɗin Aunty Garkuwa yau har yanzu batayi posting ba wata k'il sai anjima zatayi". Ido ya zuba mata cikin tsananin begin ta sannan yace, "Yanzu duk baccin da kikayi ɗazu bai ishekiba? to zonan muyi wata magana kafin kiyi baccin". Matsowa tayi tashige jikin shi tana mak'ale wuyan shi, Shima hannnshi yasa ya daɗa rungumeta yana mai cusa hannun shi cikin rigar ta kamar mai raɗa yace, "Ummu na dan Allah ki saurareni kuma inaso ki fahimceni duk da k'issar nan ta kasance ne a tsakanin yan uwa mata amman zata wakilci yan uwa maza, Annabi mohammad (S A W) ya aurawa sahabin shi Usman bin affan y'arshi sayyada Ruqayyat (r a) tayi wafati sannan yasake ɗaukar k'anwarta Sayyada Ummulkhursum ya aura mashi haka itama Allah ya karb'i rayuwarta sannan a hakan Annabin mu abun koyinmu yace, "Da inada wata y'ar dana k'ara aura mishi". Kinga idan muka duba wannan babu wani haramci ko abun kunya cikin aurena dake madadi baya da wani aibu a musulunce". Sake tura fuskarta tayi a kirjin shi, Da k'arfi yayi wani irin gwauron numfa shi ya rumtse idon shi yanajin kamar ya buɗe kirjin shi ya sakata a ciki dan so da k'aunarta dake ratsashi, Ido a lumshe yaci gaba da cewa, "Hubby duk abinda zamiyi bazai zama cin amanar Hamman muba sai dai yayi farin ciki damu domin ta hanyar aure muke tare wanda duk abinda zanyi dake sunnace zan raya babu batun cin amanar Hamma na a ciki, Nasani da wahala amma ki daure kiyi hak'uri kisauke nauyin dake kanki kiban dama na rab'i jikinki kibani hak'k'ina ki dena sawa ranki amanar d'an uwana zanci". D'ago kanta tayi tana kallon shi, suna haɗa ido ya ɗaga mata gira tare da kashe mata ido d'aya, da sauri tasake maida kanta ta cusa fuskar ta a kirjin shi, sake matsota yayi, suna rungume da juna cikin rad'a yace, "Nafa gaya miki tun ba yauba kin sani mijinki mai yawan buk'ata ne". Shigowar sak'onni a wayar Ummul yasa yaɗan sassauta rik'on da yayi mata ya janyo wayar yana dubawa abinda Ummul ke jirane ya shigo posting en GARKUWA sai kuma sakonni da dama da suke ta shigowa a jere-a jere na jaje da ta'a ziyyar Hamma Umar a kowanne group da take, kallon shi take dan tana son gano abinda yake gani, hannu tasa ta karɓi wayar shikuma jiki a mace ya tashi yashiga Wanka ya shiga. Ita kuwa Ummul yana shiga bedroom en ta gyara konciyar ta kan 3 str forko kan sunan Garkuwa ta shiga inda ta samu yau bata turo mata page d'in yau d'inba sai gargad'in da tayi mata na karfa ta karanta page d'in *Rubutaccen al'amari* na yau d'in, tana ganin haka sai ta lumshe ido tana jin hawaye mai zafi group en Aysha Ali garkuwa fan's ta shiga inda tana shiga ta samu page d'in a forko, hannu d'aya tasa ta dafe k'irjin ta sannan ta fara karanta page d'in, tana farawa hawayen da take matsewa ya tsiyayo a hakan taci gaba da karanta page en inda yake tuna mata wannan ranar da bazata tab'a mantawa ba a zahiri karatu takeyi amman a bad'iri ganin abun take kamar yanzu yake faruwa karatun take tana kuka mai tsananin ciwo a zuciya kuka mai tafiya da numfashi tana zuwa dai-dai inda aka yanka Hamma Umar d'in nata ta wurgar da woyar a tsakiyar parlour kan carpet kife kanta tayi a jikin kujerar ta saki wani irin raunaceccen kuka mai toshe numfashi tanayi tana cusa kanta jikin kujera tana, "Allah ya isa Allah ya isana sun cuceni sun maida min d'ana maraya sun kashe mai uba tun bai fito duniya ba, Allah ya isa a gabana sunka kashe min d'an uwana jigona farin cikina sun cuci Ya Usman sun maidashi baida d'an uwa sun cuci Ammi sun kashe mata d'anta sun yashe min farin cikin rayuwata sun barni cikin nadama har k'arshen rayuwata". haka ta rink'a kuka da surutai a hankali numfashin ta ya rink'a cushewa lokaci d'aya ta fara fita hayyacin ta. Shiko Usman yana fitowa wonka 3 qutr ya saka sai d'an shert nashi mai taushi mai ya d'an shafa sannan ya fisa turaru kanshi masu sayin k'amshi yana gama kimtsawa ya fito parlour. Yana fitowa ya nufi inda taken dan ganin halin da take ciki yasa shi k'arasawa gurinta da sauri yana zuwa yasa hannu ya ɗagota idanta yagani sun canja kala gaba ɗaya jikinta ya saki ga zafi da yayi kamar wuta tana fisgar numfashi da kyar, rungumeta yayi sosai a jikin shi yana firgice duk jikin shi na rawa yace, "why Ummu na why? saida Aunty Garkuwa tace karki karanta page ɗin nan gashi kin bayyana kanki mutane dole suyimiki gaisuwa kuma nasan dole akwai matsala in kika karanta Ummuna meyasa kika karanta". Da karfi take nemo numfashin ta tana janyoshi tana mik'e wa kamar numfashin ta zai fita, a rikice yaɗau waya yakira abokin aikin shi dake kusa dashi, kukan dayaji Usman nayi ne yasashi fitowa daga gidan shi, kafin ya shiga suka haɗu da Usman ɗin rungume da ita bata ko numfashi wuce shi yayi shima yabi bayanshi sukayi gurin ajiye motocin, Kai tsaye asibiti suka nufa dan ceto rayuwarta, Tunda suka fara tafiya Usman ke jijjigata yana wani irin zubda hawaye masu cin zuciya yana, "karki barni Ummu please, ki tausaya min ki tashi kinji Ummu na ki dena kukan, bazamu iya rayuwa babu keba please, kinga Farouq yana sonki karki cutar da kanki". Da isarsu likitoci suka dukufa ceton ta shiko yana zaune rungume jikin abokin aikin nashi yanata rarrashin shi, Auwal Sulaiman shine abokin aikin ya Usman waya yayiwa matar shi dataje ta ɗauko wayoyin Usman sannan ta rufe gidan yakira abokin shi zaije ya karɓo ya kawo masu asibitin. A cikin ɗakin kuwa saida suka saka mata robar da zata taima kawa numfashin ta sannan suka yi mata allurai, Sai bayan mintuna 40 sannan numfashinta yadawo dai-dai sannan sukayi mata allurar bacci dan samun nutsuwar ta bayan tayi baccin ne suka fita. Da sauri Usman ya mik'e daga jikin Auwal amma sai ya dawo baya kamar zai faɗi Auwal da abokinshi ne suka rik'e shi sannan suka nufi ɗakin likitan, zama sukai likitan ya musu bayani kan a kula da ita sannan a kiyaye abinda zai ɓata mata rai dakuma tsoratar da ita domin zuciyar ta takai mataki na k'arshe a rauni wanda komai k'an k'antar abu zai iya tayar mata da hankali ya haifar mata da matsala, Saida yagama musu bayani sannan yace zasu iya shiga gurinta amma kada suyi surutu dazai tayar da ita daga baccin. Auwal da Abokin shi ne suka yiwa Usman sallama bayan sun shigo sun duba Ummul daketa bacci a wahalce sannan suka tafi. Shiko ya Unman zama yayi akan kujera ya zuba mata idanu yanajin wani irin tausayin ta na ratsa shi, hannu yasa ya kama nata hannun yaita kallon ta yana share k'ollah dake zubomai lokaci zuwa lokaci, wayarta ya ciro daga aljihun shi ya buɗe, yawan sak'on nin daya gani ne kuma dukka na masu mata gaisuwa ne daga groups da Aunty Garkuwa ta sakata yasa yafara amsa sakonnin a hankali ido na zubda k'ollah yake amsawa da, "Ameen Ngd". Yaɗauki lokaci mai tsawo yana amsa duk sak'onnin da ake turowa ta groups da p/c wanda shi kanshi bai san adadin suba, Sannan ya rufe data ya kwantar da kan shi jikin gadon da take kwance hannun shi ya d'an fike a kan goshin ta sannan d'aya hannun kuma yana rik'e da hannun ta d'aya a haka bacci ya saceshi. A hankali Ummul take buɗe idonta har suka gama buɗewa idon ta k'urawa sumar kan Usman daya fara bacci, tausayin shi ne ya kamata sosai dan tabbas tasan ya Usman yana sonta gashi ita kuwa ta kasa sakarmai jikinta ta sama mai nitsuwa yana bata tausayi dan ya resa mai kula dashi na hak'ik'a ido ta lumshe a ranta take fad'in, "Zan kula da kai kamar yadda nasan Hamma Umar nason a kula da kai zan saka cikin farin ciki kamar yadda d'an uwanka yake fatan ya ganka cikin farin ciki". hannunta ta cusa cikin sumar kan nashi tana murzawa tare da mishi salon lallashi a hankali tana shafawa, kamar a mafarki yaji kamar ana mai susa ɗago hannun shi yayi yakai kan sumar tashi hannu Ummul yaji dan haka yayi sauri ɗago kanshi sukayi tozali da ita, A hankali ta sakar mai murmushi tana d'an lumshe ido, Hannu yasa ya shafi fuskarta sannan ya d'an taso ya sunkuyo kanta ya haɗa goshinsu guri guda harshe yasa ya d'an laso lips enta a hankali yace, "Hubby karki sake min haka please zuciya ta zata buga in mutufa". Girgiza mai kai tayi sannan tafara magana da saida ya matso da kunnen shi kusa da bakinta sannan yaji abinda take cewa, "Ya Usman Insha Allah bazaka mutu ka barni cikin maraici biyu ba bazaka mutuba ina sonka zamu rayu tare mu bawa Farouq tarbiya da kanmu ya Usman ina sonka har abadan bazan sake yin rowar kalmar soba zan dauwama ina cema ina sonka' mutafi gida na samu lafiya ka kontar da hankalin ka mu koma gida na kula da farin cikin ka kaji?". Lonk'oso kai yayi cikin lallashi da jin dad'i yace, "Kiyi hak'uri likitan zai dubaki yace inkin tashi nayi mishi magana kinga sai muji ya zaice karki damu Ummu na zamu koma Insha Allah muna tare". Kai ta gyad'a mai shiko ya sumbaci bakinta ya fita, tare suka shigo da likitan ya sake duddubata sannan yasake jan kunnensu kan ɓacin ranta sannan yabasu damar tafiya gida. Yau kwanan su biyu da dawowa asibiti Ummul ta k'ara worworewa, bayan ta fito wonka ne ta zauna gefen gado tana shirin konciya bacci, Usman ya shigo shima wonka yayi sannan ya kimtsa blanket ya jawo sannan ya juya zai koma parlour, ido Ummu ta zuba mai tana kallon shi har yaje bakin k'ofar fita tace, "Ya Usman". "Na'am". yace da ita ba tare da yajuyo ya kalleta ba, ita kuwa keyanshi ta zubawa ido cikin mamakin yadda tun randa suka dawo asibiti ya Usman yake komawa parlour ya kwana a can zuwa yau kuwa abun ya fara soya mata zuciya, shiko jin shiru batayi magana bane yace, "lafiya dai ko? ". shiru tayi tana rau-rau da ido alamar zatayi kuka sai kuma ta daure a hankali ta mik'e tazo bayan shi murya can k'asa tace, "Ina zaka je? ". "Parlour zan tafi mana bacci zanyi". "Nan kuma cikin d'akin ba wurin bacci ne? ko dai zama kusa da nine baka so? ". ta k'arishe maganar tana zubda k'ollah, a hankali ya juyo suna fuskantar juna jin yadda muryarta ke rawa kai ya d'an kawar sannan yace, "Toh ya zanyi? Ummu ya zanyi da raina dolece take sa nakeyin nesa dake Ummu nifa ba waliyi bane, kinga dole inbar zama kusa dake tunda in na zauna kusa dake dole na buk'aceki ke kuwa yanzu baki shirya zama da niba toh ya zanyi kinga dole nayi nesa dake". Jikin shi ta fad'a tare dasa hannunta ta ruggumoshi tana kuka tana juya kai tace, "Kayi hak'uri ya Usman ka gafar ceni Insha Allah bazan sake irin kuskuren da nayi a baya ba ni na shirya zama da kai". Ajiyan zuciya ya rink'a sauk'ewa tare da ruggumota a jikin shi cak ya d'ageta sai kan g...... *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* page 3⃣9⃣ *Na* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *MOH ALLAH HOKKI B'URI MOH BABA HOKKI* *Hahaha 😎😀😜👸🏻 ina kuke ne BAREBARI bayin FULANI toh kuzo ku matso kusa kun san mu FULANI sarakunane masu adalci a gareku toh yau dan haka bisa adalcinmu a matsayi na uwar giyiyarku na Baku kyautar wannan shafi nawa nabakushi gaba d'ayan shi kuyi yadda kukaga dama dashI in kunga dama ku seda wannan shafin ku saro kanwa kud'in😜💃🏻SIRATI SIRTA MOD'O TO SALDORI TAGGA MOD'O babarbare cinna kane tunba wurin idonba💃🏻😜😂 maza kuyi mubaya'a dan GARKUWAR kuce ke gaidaka* *K*an gado ya direta a hankali ya kontar da ita, Sannan shima ya haye kan gadon gefenta ya d'an rab'a ya haɗe jikin shi da nata wuri guda sai kuma ya rink'a sauk'e ajiyar zuciya yana lumshe ido da furzar da numfashi mai sanyi, k'arar da wayar shi keyine yasa Ummul lek'a wayar dake kan side drower gadon, sai kuma taɗan zame jikin ta gani baida niyyar ko kallon wayar yasa tayi k'arfin hali murya can k'asa kamar mai rad'a tace, " ya Usman Abbane fa". Sakinta yayi yasa hannu yaɗauko wayar ya koma kan pillow ya kwanta yana sauk'e numfashi sannan yakai idanunshi da suka k'ank'ance kan wayar ganin sunan Adam yasa ya aje wayar yajuyo gareta yana shirun ruggumo ta, da sauri ta yunk'ura zata gudu shima cikin hamzari ya kamota ya fara mata cakul-kuli yana cewa, "Daman dan ki gudune yasa kikace Abba ne ko?". Dariya take har tana shiɗewa tana zulle-zulle tana d'an tureshi, jin wayar na sake yin ringing yasa ya kyaleta ya ɗauki wayar yasa a kunne sallamar da Adam yayi ya amsa sannan dagacan Adam ɗin yace, "Ga su Ammi da Nanne zakuyi magana". "Uhummmm". yace a tak'aice sannan yasa wayar a handsfree ya ajiye woyar akan pillow sannan yasa hannu ya tallafo Ummul ya haɗata da jikin shi yana shafata da lumshe ido a hankali yace, "Nanne na". Ammi ce ta katse shi dacewa, "Ina autata Ummu?". Da sauri cikin happy ta d'an ture kan Usman da yake tsakin wuyanta da kafad'arta yana shak'ar k'amshin cikin d'an d'aga murya tace, "Gani nan Ammina ina wuni?". Gaisuwa sukayi harda Aliyu sannan Nanne tace, "Usman daman matar Mustapha ce ta haihu jiya akayi suna, tomu bamu jiba sai jiyan Ummie shi ta kira take faɗa min ansami Umar Farouq, Mustapha yayiwa Hamma Umar enku takwara, jiyan lokaci ya k'ure shine yau zamu je muyi barka gashi Adam da Sadiq sun haɗo mana kayan barka zamu tafi yanzu muje muga Umarun mu". Tana maganar Usman yakai duban shi ga Ummul yaga ta shagwaɓe saura kaɗan tasa kuka, bakin shi yasa kan nata yai mata kiss sannan ya ɗaga yatsan shi yasa kan bakinta yana jujjuya mata kai hannun shi d'aya kuma yana cikin rigarta, sannan ya amsa da cewa, "Alhmdulillah, kai amma mungode sosai lallai Mutsapha yayi mana halacci tabbas ya cika d'an uwa musulmi, ku gaidashi in kunje sosai nima zan kira nayi barka da godiya kafin mu dawo muma muje". Aliyu ne ya katse maganar sanin halin Ummul zata iya kuka akan maganar yace, "Aunty Ummu albishirin ki?". Kamar bazata amsa ba saida Usman yakai hannu zai mata cakul-kuli tayi maza ta rik'e hannu shi tana zaroshi daga kan k'irjin ta a hankali tace, "goro". Cikin raha Aliyun yace, "Bakiga yadda Abba ya gyara ɓangaren ya Usman ba, yace yanzu yazama na Ammin ki". tuni ta mik'e zaune tasaki dariya tace, "Haba, Yanzu ta koma can tabar d'akin mu?". Sai kuma ya d'an kad'a kai cikin halin shi na tsokana yace, "Ina kuma ai badan zamu je unguwa bama da yau zamu rakata zata koma gidan Innar ta itama, tunda dama ke kika hanata tafiya da shagoɓa, yanzu kinyi tafiyarki kin mak'alawa miji dad'i kin manta damu, dan haka itama tafiya zatai". Adam ne yasa hannu ya ɗan bigi kan Aliyun cikin wasa, Itako harta faɗa jikin Ya Usman tana ta tumurmusheshi zata fara halin, da sauri Usman yace, "kai Aliyu ina wasa dakai ne? zaka samin ita kuka ko?". Ammin ma cikin Dariya tace, "Karkiyi kuka Ummuna, babu inda zanje zolayarki yakeyi harma na koma part d'in Usman d'in yanzuma a nan muke, ai inda kike so nan zan zauna Ummu na sai kun dawo harda Innata zaku tare". A hankali tasa tafin hannunta ta goge k'ollah dake shirin zubo mata taci gaba da cewa, "Amma fa idan na tambaya kina yawan kuka kuma bakicin abinci to zan tafi zan koma gun Innata". Tasowa tayi daga jikin Usman ta sunkuyo kan wayar yayin da ta kife k'irjin ta kan fuskar Usman tace, "Ammi banayi kuma ina cin abinci da yawa ko?". Tajuya tana tambayar Usman daya zura hannun sa cikin rigarta yana shafa kirjinta zuwa saman wuyan ta yana ta murza fuskarshi kan k'irjin yanayi yana lumshe ido, murmushi yayi cikin jin dad'i da tsananin shauk'i ya d'an gyad'a kai tare da cewa. "Ehhhhyyy Ammi ta d'an rege kuka yanzu kam". cikin jin dad'i Ammin tace, "Yauwa yarinyar kirki". Ita kuma a shagwaɓe tace, "Ammi kar kuje da Aliyu gidan Mustapha tunda yana tsokana ta". Adam ne yasa hannu yaɗau wayar sa tare da cewa, "To sarkin shagwa ɓaɓɓu da sakalci sai anje dashi tunda ba motarki bace". "ba inda za aje dashi tunda yana tsokano min ita". cewar Ammi, Usman ne ya katsesu da cewa, "Ina Boy ne ban jishi ba?". Murmushi Adam yayi yace, "Yatafi daɗi mota mana sun fita da Sadiq tun ɗazu". dariya sukayi dukansu Da haka sukai sallama kowa na cikin jin daɗi. Shiko Usman ɗaga Ummul yayi suka shige bayi alwala sukayi sannan suka fito, ya jasu suka gabatar da sallah nafila raka'a 2 sukai addu'a ya kama kan ta yayi mata addu'a sannan ya cire mata hijabin ya ɗauketa cid'ak sai kan gado . Hannu yasa yarabata da rigar jikinta sannan ya jawo blanket ya rufesu a hankali ya jawota jikin shi cikin lumshe ido ya manna bakin shi kan k'irjinta yana tsotsa kamar yaron da ya samu alawa yana shafa ɗayan da ɗaya hannun shi wani irin numfashi yakeyi tuni yafara sarrafata da salon shi dayasa gaba ɗaya ta birkice sai mik'a take tana fitar da numfashi a hankali, tuni ya rikice yana shafa ko ina na jikinta yana lasar ko ina tare da isar da sak'onnin shi, nan da nan tafara hawaye tana d'an tureshi ganin yana neman zautar da ita, shiko hankalin shi yatafi duniyar daya daɗe yana neman kai kanshi dan haka baiga kollar taba bare ya sahirta mata. Saida komai ya lafa Usman ya gama samun gamsuwa iya gamsuwa sannan ya janyota jikin shi ya rungumeta kamar zai sakata cikin jikin shi ya rink'a sunsunar wuyanta yana sauke numfashi yana jin wani irin farin ciki na ratsa zuciyar shi da gangar jikin shi yana jin wani shauk'i da daɗi kamar wanda akayiwa bushara da aljannah sai cusa kan shi yake a wuyanta hannun shi na shafa duk sashin jikinta murya na rawa cikin shauk'i yake samata albarka dan jinta yayi tamkar budurwa dan ya wadatu da ni'imar jikinta. Sai ririta ta yake yana kissing nata tako ina yana mata Addu'oi, "Ummuna Allah ya miki albarka Allah ya sanya rayuwarki cikin farin ciki kamar yadda kika sani cikin farin ciki yau kin kawarmin da duk wani k'ishi dake tare dani Allah ya miki al'barka ya Habeebaty". Itako sai daɗa narkewa take a jikin shi cikin tarin gajiya dan ya wahal da ita sosai gata dama uwar rak'i sai lafewa a jikin shi take gaba ɗaya jikin ta ya sake ko motsa yatsanta bata iyawa gaba ɗaya ta sakalce mai ta lumshe ido sai lokaci lokaci take buɗe su a hankali tana rufewa, Haka yayita lallashi da faɗa mata kalaman soyayya masu tsuma zuciya. Saida suka ɗauki lokaci mai d'an tsawo a haka sannan shima yaji yafara samun k'arfin jikin shi dan haka cikin halin shi na tsokana yace, "To wai kukan nan na menene bayan kin gama zuk'eni ko hannuna da kyar nake iya ɗagawa, amma ni banyi kukaba saike da kika zama sarauniya a zuciya ta da jikina". Maganar ce tasa taɗan ɗago kanta a hankali ta buɗe idon ta da kyar ta kalle shi, kashe mata ido ɗaya yayi yace, "k'ari nakeso kuma nasan kema wannan kukan k'arin kikeso". Sake cusa kanta tayi a kirjin shi tayi lamo tana jin bugun zuciyar na harbawa kan nata zuciyar, jin taɗanyi shiru tana sauke numfa shi a hankali yasa ya ɗan sunkuyo kai ya lek'a idonta yaga ta rufe idanu kamar mai bacci yace, "Kai bacci ma zakiyi baki isaba ɗaukata zaki ki kaini bathroom tunda kin gama moreni". Yana faɗa yana shafata da salon shi na tsokana, maida ita yayi ya kwantar da ita a hankali a kan pillow ya tashi yashiga bathroom ya haɗa mata ruwan wanka sannan ya fito yazo yasa hannu ya ɗauketa yajuya sai kuma ya tsaya buɗe idonta tayi dasuke rufe tunda ya kwantar da ita kan pillow karaf suka haɗa ido, da sauri ya kashe mata ido ɗaya tare da ɗaga nata gira yace, "Gaskiya indai na kaiki banɗakin nan sai na k'ara dan bazan tab'a gajiya dake ba don haka zan k'ara saboda nauyin ki dan yanzu kin fara zama y'ar lukuta mai nauyi". Shogoɓe mai tasake yi ta narke a jikin shi hanunta sak'ale da wuyan shi baki ta d'an tura ido na zubda k'olla murya can k'asa dakaji kasan an gajiyar da ita a hankali tace, "Hummmmm ya Usman kayi hak'uri na gajifa bazan iyaba wallahi jiri nake ji ka wahal dani da yawa". Sake kashe mata ido yayi ya laso lips enta yace, "Kuma in kika bari k'ollah nan ta zubama saina k'ara Ummu na ina sonki yau kin sani farin ciki kin jiyar dani dad'in rayuwa". Da haka yawuce ya sata cikin ruwan, duk yadda taso ya fita yak'i haka nan ta hak'ura sukai wanka tare ya sake ɗagota ya kwantar da ita kan gado bayan ya goge mata jikinta ya fesheta da turare sa ya samata rigar bacci shima ya shirya ya hawo gadon ya kwanta ya rungumeta kanta na kan damtsen hannun shi da haka bacci yayi awon gaba dasu. Haka nan da wayo da tsokana da barkwanci Usman yake samun nutsuwa sosai da Ummul a koda yashe yaso sannan yana kula da ita sannan yana k'okarin bata kayan itace tunda yaji ance suna gyara mace da k'ara mata ni'ima. Sati uku kenan da Usman yasami damar raɓar matar shi, koda yaushe yana manne da ita indai ya dawo daga aikin dayaje yana bata kulawa sosai itama tana jin daɗin yadda yake mata saidai salon shogoɓa kam bata fasaba duk da dazaran ta fara yake sakata dariya da barkwan cin shi. Ranar wata juma'a Usman daga gurin aiki suya wuce masallaci yayi sallar juma 'a sai da akayi magrib sannan ya dawo gida, makullin hannun shi yasa ya buɗe k'ofar ya shiga yanda yaga palour a yanda yabar shi yasa ya juya ya kalli kan dining table gani yayi babu komai hakan yasa gaban shi faɗuwa kirjin shi yafara bugawa ya ajiye jakar hannun shi yayi bedroom ɗin yana shiga yanda yahango Ummul kwance a nannaɗe cikin bargo tana rawar sanyi yasa yayi saurin hawa gadon ya janye bargon ya rungumota, zare ido yayi nan da nan jikin shi yakama rawa jin yanda jikinta yayi zafi ga numfashinta na fita da kyar, k'ara matsota yayi ya mannata da kirjin shi cikin rauni da sanyin murya yace, " Ummuna meya faru Hubby?". sai kuma yasa hannu ya share mata k'ollah dake zuba daga idonta yace, "Yi hak'uri Baby na bari mutafi asibiti". A take kuma sai tayi wani irin yuk'uri jikinta na rawa ta k'ank'ame shi idanuwan ta a rufa a hankali tace, " Ya Usman kirjina". Hannun shi ɗaya yasa ya dafa kirjin yace, "Kiyi hak'uri zai daina". Daukan ta yayi yakai cikin mota ya kwantar mata da seat sannan ya dawo yaɗauki wayoyin shi da nata yaja k'ofar ya rufe sannan ya koma motar ya zauna, tukin yake yana ɗan kallon ta har suka isa asibiti, saida aka basu ɗaki aka kwantar da ita sannan likitan yaje yayi gwaje gwajen shi yakuma ɗibi jininta yaba nurse ta tafi lab dashi dan gwadawa likitan ya juya zai fita ya dafa kafaɗar Usman dake tsaye yana kallon shi yace, "i will call you when i got the result". Dakai Usman ya amsa mai likitan na fita ya matso ya zauna bakin gadon ya rik'e hannunta ɗaya yana shafa kanta a hankali har bacci ya ɗauketa. Ba afi mintina 30 ba Nurse ta shigo hannun ta ɗauke da faranti da kayan aiki akai tace mai likita na kiran shi fita yayi dasauri ya nufi office din dr, Ita kuwa ta kama hannun Ummul tafara aikin ta. Yana shiga likitan yaimai nuni da kujerar gaban shi ya zauna jikin shi sai rawa yake dan yanajin tsoron kar zuciyar tace keda matsala bayaso ace wani abu ya taɓa zuciyar ta, shima likitan ya fahimci halin da yake ciki na firgici dan haka bai tsaya yimai dogon bayaniba yace, "congratulation mr Shuwa you pregnant your wife last 2 weeks". wani irin kallo yakema likitan kamar baitaɓa ganin shi ba saikuma ya maida kan shi ya jingina jikin kujerar da yake zaune ya lumshe idanu yasauke ajiyar zuciya sannan ya ɗago yana hamdala tare da yiwa likitan godiya ya fita. Ita Kuwa Ummu bacci take ga drip da Nurse ɗin ta saka mata yana tafiya a hankali, tsayawa yayi ya tsurata mata ido k'olla na zuba daga idon shi yasa hannu ya shafi gefen fuskarta yana Al'ajabi da lamarin ubangiji Ummu na d'auke da cikin shi bayan ta haife na Hamma Umar enshi tabbas lallai wanna shine *Rubutaccen al'amari* gaba d'aya zuciyar shi ta cika da rauni sai zubda k'ollah yake, A hakan ya shige bathroom na ɗaki yayo alwala yafito ya shimfiɗa sallaya yayi sallah isha'i sannan yacigaba da nafilillinshi yana addu'a idanun shi nata fitar da k'ollah, yana zaune kan sallayar kira ya shigo wayar shi wanda yasan bai wuce Adam ko Sadiq ba dan sukanyi video call a irin wannan lokaci wato k'arfe 01:30am agogon Kuala lampur sannan 9:30pm a Nigeria, janyo wayar yayi ya amsa ganin gudan jinin shi d'an d'an uwanshi Umar Farouq zaune akan cinyar Adam a kan gado da shirin baccin shine yasa yaji sanyi a ranshi yasaki murmushi shima Farouq dariya yayi yasa hannu ɗaya ya rik'e airpist ɗin dake kunnen shi cikin gwarancin sa yace, "Masa'ul khair Abeey". wani sanyi yasake ji a ranshi yana fara'a yace, "masa'unnur ya bunayya, hw's ur day". Domin dukkansu haka suke magana da Faruq suna haɗamai hausa, turanci, larabcin shuwa arab, kanuri, shiko Aliyu harda indianci yake cakud'a mai dan haka shima Faruq yake fahimtarsu insunyi, cikin gwari-gwarin ya kalli Usman yana murmushi yace, "Abeey bah shadik ayi bacci wau adun bah Adam am fana". Dariya yayi mai sauti yace, "OK Baba Sadik yayi bacci yau a gun Baba Adam zaka kwana?". kai ya gyad'a mai cikin jin dad'in Abeeyn shi ya gane maganar sa, shima Usman dariya yayi tare da cewa, "Yau tunda gurin bah Adam za'a kwana ya sunan ka na gaskiya?". gyara zama yayi sannan yace, "Uwan Faruoq Adam Cuwa". Dukkansu dariya sukai yadda ya ke cewa Umar Uwar shuwa kuwa cuwa dariya sosai sukeyi har Adam da yake mak'ale da kunne ɗaya na airpiest ɗin dan haka Farouq yake ko fita za ayi dashi tofa duk wanda ya ɗaukeshi a lokacin shine mahaɗin sunan shi kuma ko abu kabashi a lokacin duk wanda zai tambaye shi sunan shi na gaskiya to dana me bashi abin zai haɗa, sake tambayar shi yayi yace, "Bobo na d'azu nakira ance katafi unguwa to a unguwar da kukaje ya sunan ka na gaskiya? ". Saida ya juya ya kalli Adam sannan yasa hannu ya janye airpiest ɗin dake kunnen Adam ɗin dan kar yaji abinda zaifaɗa yayi k'asa da murya yace, "Uwan Farouq Abba Daddy cuwa". Hakan na nufin da Abba da Daddy sukaje unguwa haka Usman yayita mai tambayoyi yana amsamai suna dariya sannan yace, "Abeey Ummiena". tashi yayi daga kan sallayar yaje ya nunamai fuskar ta yace, "tayi bacci, inta tashi da safe zata kiraka ku gaisa ko Bobona, yanzu kabawa bah Adam saika kwanta kai bacci, i love u". Shima a gwarance yace , "i wov u Abeey". ya fad'a yana ɗaga hannu ya cire abin daga kunnen shi ya mik'awa Adam ya juya yayi kwanciyar shi shiko Adam saida ya gyara mai lulluɓa sannan yaɗau wayar yafita palour. Saida ya zauna a kujera sannam yace, "Meya faru? naganku a asibiti haryanzu bata daina kukanba ko?". Cikin damuwa yake maganar, "Ba kuka tayiba Adam nadawo na sameta kwance da zazzaɓi sai kuma tacemin kirjinta nima naɗauka ciwon zuciyar ne amma da mukazo sai akace ba shi bane". Ajiyar zuciya Adam yayi sannan yace, "meke damunta to?". yana sosa kai da wata y'ar dariya yace, "Abee zaka zama kaima". "yes that's my bro, dan Allah karka faɗawa kowa nizan faɗa". Murmushi yayi a zuciyar shi yace, "Kai kaɗai zan iya faɗawa wannan ". Da haka sukayi sallama ya mata fatan samun sauk'i sannan ya katse wayar. Sai da safe aka sallamesu dan jikin yayi kwari sosai sai shogoɓa da raki, haka suka koma gida tanata narke mashi shikuma yasamu aikin yi sai lallaɓata yake yana rarrashi a cikin ranshi kuwa yana tuna randa yaganta da cikin farouq da yanda yake lura da Hamman shi da duk motsin da zatayi akan idonshi sai sannu yake mata, yakanyi k'ollah yana gogewa a ɓoye dan karta gani, Itama kuma hakan ne a ɓangarenta da Usman da yaɗan kauce zata goge k'ollah tana tuna burin zuciyar Hamma Umar d'inta. Yau da Asuban fari Usman ya kira Adam wanda shima dai-dai shigowarshi daga masallaci sallah asuba kenan yace, "Adam ka haɗamu video call dasu Abba kuma inaso ka tabbatar kowa yana gurin har Daddy". Bai tsaya jin abinda Adam zaice ba ya ajiye wayar yakoma bedroom ya ɗauko dogowar rigar Ummul da ɗan k'aramin mayafin rigar yafito palour itako Ummul tana kwance kan 3seater ya ɗagota ya jinginata jikin kujera ya saka mata doguwar rigar daya ɗauko ya lulluɓa mata ɗankwalin daman y'ar shimi ce a jikinta da wando 3quater itako kallon shi kawai take, Adam ko yasami su Abba da Daddy a palour Hajjajo ya sanar dasu sakon Usman nason magana da kowa a guri guda kiran kowa na gidan akai Ammi kuwa kawai a zaune take amma jikinta sai rawa yake kirjinta na bugawa da k'arfi. bugu ɗaya Adam yayi Usman ya ɗauka ya jingina wayar da kujerar dake kallon su shima Adam jingina tashi wayar k'irar samsung tab E yayi yanda kowa zai gani sannan ya koma ya zauna. Shiko Usman komawa yayi ya zauna gaban Ummul a k'asa ya tonk'oshe k'afafun shi ganin haka jikin Ummul da Abba dake kallon su yafara rawa Nanne ma k'irjinta na bugawa tai k'arfin hali tace, "Usman meza kai haka kul karkayi wannan alk'?". Ammi ce ta ɗagawa Nanne hannu alamar ta kyale shi kanshi a k'asa yakamo k'afafun Ummul wacce tuni tasa mai kuka tana girgiza mai kai tana k'ok'arin janye k'afarta, da k'arfi ya rik'e k'afar ya ɗora kan cinyar shi batare daya ɗago kaiba cikin sanyi da k'auna da begen tuno Hamman shi yace, "Ni Usman Ibrahim Umar Shuwa nayi alk'awarin kulawa da matata da k'arfina da dukiyata da lafiyata da zuciyata da kuma raina". wani irin razana Ummul tayi zuciyarta tayi wata irin bugawa shiko dasauri yatashi ya katse kiran yadawo ya rungumeta dukkan su suna wani irin kuka mai cin rai saida suka ɗau lokaci a haka sannan tazame jikinta bakinta na rawa a hankali tace, "Ya Usman kaima haka zakayi min? bazan jumreba bazan iyaba dan Allah ka janye wannan alk'awarin wallahi ina sonka inason ka ina son Hammana kar kuyimin haka please banaso in rasaka ina sonka ya Usman". Hannu yasa ya kwantar da kanta a k'irjin shi cikin rauni yafara cewa, "bazaki rasani ba Ummul ni nakine kamar yadda Hammana yake naki, Insha Allah babu abinda zai faru sai al'khairi kidena tunanin abinda yafaru da Hammana zaifaru akaina kowa yanada sanadin shi insha Allah nizan k'arasa abinda Hammana ya fara na kyautata rayuwarki da saki farin ciki, zan rayu dake Ummuna zan baki duk irin kulawar da Hamma na yaso baki". haka yayi ta rarrashinta suna manne da juna. Sukuwa a gida kowa kuka yake sabida tunawa da Hamma Umar da kuma tausayawa Usman da Ummul, Ammi ce cikin k'arfin hali irin nata tace addu'a ce tsakaninmu da waɗannan yara domin jininsu ɗaya kuma haka Allah ya tsara musu rayuwarsu tabbas wannan shine Rubutaccen al'amari daga Allah, Daddy ne yace, "Wai ni kam meya kawo wannan abun kuma a yau?". Adam da shikadai ne keda amsar tambayar yace, "Daddy jiya a asibiti suka kwana Ummul ba lafiya amma likitan yace ba ciwon zuciyar bane wai tanada cikine, inaganin shiyasa Usman yin hakan". Hamdala kawai sukeyi dukkansu Ammi da Nanne kuwa suka tashi suka fita kowa da abu biyu a lokaci guda a ranshi murnar samun k'aruwa da kuma tunawa da kamilin ɗansu Dr UMAR IBRAHIM UMAR SHUWA.... *By* *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* page 4⃣0⃣ *Na* *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *MOH ALLAH WUJI FURD'ATA* *Nandis ngd matuka Allah bar zumunci da k'auna dear Allah k'ara basira naga novel mai suna sai NAGA AYSHA GARKUWA karki damu zakiga garkuwa amman bakisa number kiba kuma inada mgn dake so ina son number ki, kuma kar kici gaba da typing sai munyi mgn ngd bandirawo🤝😍😘* *Wannan shafi nawa gaba d'ayanshi tukuicine ga masu suna AYSHA ina k'aunar wannan suna mai daraja ina son duk mai wannan suna ina al'fahari da sunan ina k'ara yiwa iyayena addu'a da sunka samin wannan suna mai daraja sukamin zab'i mai kyau a lokacin da bansan kainaba ya Allah ka sakawa iyayenmu da ma fificiyar sakaiya Allah ya basu jannatul firdausi Amin Amin Ameeeeeeeeeeeeeeeen ya rabbil izzati* *B*ayan duk sun tashi a taron nasu Adam ma ya mik'e ya koma part enshi bayan an idar da sallan azahar, misalin k'arfe 2:00 Adam ya shigo ɓangaren Nenne yadda suka saba samun Nanne da Ammin a wannan lokacin hannun shi rik'e dana Farouq suna shiga ya sami kan 3seater ya kwanta yaɗan matsa shima Farouq ya hau ya kwanta a gabanshi ya lumshe ido sannan yace, "Ammi wai kina nemana inji Aliyu?". fuska a sake tace, "eh sonake ka kiramin Usman". Mik'ewa yayi ya ɗaga Farouq yace, "my boy jeka ɗauko mana waya a ɗaki". Da gudu ya fita bai jimaba sai gashi da wayar Nanne ce tayi ɗan murmushi tace, "masha ruwa magirmi, su Adam anyi ɗan aike har wani dadi kukeji ku aiki Farouq gashi baida k'iuya". Shiko Farouq kai tsaye ya mik'awa Adam wayar ya koma gefen shi yayi kwanciyar shi, Ringing tayi kamar zata katse sannan Usman ya ɗauki wayar murya can k'asa yace, "Ya akai gwauro?". dariya Adam yayi sannan yace, "Ammi ce keson magana da kai". Tashi yayi ya zauna ya ɗago Ummul dake kwance jikin shi ya mannata da k'irjin shi sannan ya jingina da jikin gadon ya ajiye wayar yasa handsfree ya ajiye sannan yace, "Ammi ina wuni?". Cikin murmushi tace, "lafiya lau ya Ummu na?". "Alhamdulillah tana lafiya Ammina". "Masha Allah". Tace sai kuma ta d'anyi shiru zuwa d'an wani lokaci sannan tayi ajiyan zuciya tare da yin magana a hankali tace, "Usman am sai yaushe zaku dawo? wallahi hankalina zaifi kwanciya in tana kusa dani ga Farouq ma yana kewarku, ka dawomin da yarinyata kusa damu zan kula da ita". Da sauri ya jawo woyar ya kashe handsfree ɗin yaɗauka yasa a kunne dan gudun kar maganar Ammi ta ankaro da Ummu ta fara regima akan a koma cikin sanyi da rauni kamar zaiyi kuka yace, "Ayyahh Ammi wallahi ba komai fa zan kula da ita sosai dan Allah kiyi hak'uri ban gama aikin da nazo yiba kuma bazan iya zama ni kadai ba". Ajiyar zuciya tayi sannan cikin jin tausayi d'an nata tace, "To naji, amma dan Allah ka lura min da ita ni gaba ɗaya gani nake bazaka iya kula da itaba dan kaima da kanka Usman yaushe ka koyi kula da kanka". murmushi yayi dan sanin gaskiya ta fad'a dan Hamman shine ke kula dashi ajiyan zuciya yayi yanaso ya kauda zancen dan ganin yanda Ummul ta k'ureshi da ido yasan zata iya yimai rigima yace, "Gata nan ma Ammi". Saka mata wayar yayi a kunnen ta aiko shagwaɓewa tayi tace, "Ammina ina wuni?". saida ta gyara zama sannan tace, "lafiya lau Mamana ya jikin? kina cin abinci ko? kin bar kuka ko? kinga kiyi hakuri ki rink'a cin abinci kinji kuma ki rink'a shan magani saboda ki rink'a samun k'arfi ko Ummu na?". Sake narkewa tayi tasa hannu ta ture hannun Usman da yaketa faman shafa cikin ta yana lumshe ido sannan tace, "To ". hira suka d'anyi sannan sukayi sallama ya katse wayar dama ya k'osa, Janyota ya sakeyi ya manneta da jikinshi ɗan ture shi tayi tace, "kai ya Usman kai baka gajiya ne? tun ɗazu ka hanani bacci sai tumurmushe min jiki kake yi". Baice komaiba sai sake tura kan shi da yayi a tsakanin k'irjinta yana goga fuskar shi. Hannu yasa ya cigaba da shafa cikinta dake lafe a jikinta kamar bataci komai ba, ture hannun shi tayi cikin shogoɓa tace, "Wallahi shima ɗan nan da zai iya daya gudu saboda wannan shafe-shafen naka". Dariya maganar ta bashi saida yayi dariyar me isar shi sannan yace, "Waya cemiki ɗane? to nidai y'a mace nake fatan na harba, sannan waya ce miki miji na gajiya da matarsa bari in gwada miki aikin rashin gajiya". Janyota yasakeyi ya matseta yafara lasar lips enta da harshen shi yana matsa ta, ganin da gaske yake ta narke fuska ta marai raice tace, "Kayi hak'uri saina huta". Rik'e hannu yayi sannan ya janyota kan kirjin shi ya kwantar da ita shima ya lumshe ido a hankali kamar me raɗa yace, "Inaso in faɗa miki wata magana amma saikin min al'kawarin bazakiyi kukaba". D'ago kanta tayi ta kalli idon shi sannan ta maida kanta ta kwantar tace, "bazan yiba tunda bakaso, daman nima bana sanin inayin kukan". Rungumota ya kumayi yace, "Yauwa kinsan Garba ɗan gidan Bah yahaya na kusa da gidan Daddy ko?". Tana ɗaga kai tace, "Abokin Farouq nagane shi ai yana yawan zuwa gun Farouq yana son Farouq sosai ko yaushe sai yazo ya daukeshi wani lokacin ma in Farouq na kuka sai kaga shima yana kuka, in Ammi na mai fad'a ya dena kuka, sai yace yana tausayawa Farouq ne". Ajiyar zuciya Usman yayi yasa hannu ya shafa kanta sannan yace, "Kinsan yana universty maiduguri, to ɗazu Sadiq ya kirani inagun aiki yake cemin ɗazu yaga yaron yake tambayar shi baije registration ba yaga tare suke tafiya da Aliyu, shine yake cemai daman Hamma Umar ne ya samar masa admission ɗin kuma shine yake biyamai kuɗin dan haka yanzu ya hak'ura saboda mahaifin shi bashi da k'arfi bazai iya biya maiba shikuma baya aikin komai balle yaci gaba da d'aukar nauyin karatun shi da kanshi". Shiru sukayi dukkansu naɗan lokaci sannan yaci gaba da cewa, "Ummu kinga Hamma baitaɓa faɗamin yana wannan aikin alkhairin ba, yayi tsakanin shida mahaliccin sa, dan haka shine nace Sadiq yacewa Adam yamai komai gobe ya tafi makaranta". Sai lokacin tasa hannu cikin dabara ta goge k'ollah daya zubo mata ta tana daga kwance jikin shi tace, "Ya Usman nima Hamma Umar bai taɓa faɗamin ba saidai ina mamakin yanda Garba yakeson Faruoq kuma kullum sai yaje gun shi ya ɗauke shi, amma dan Allah inaso kaimin wata alfarma". ido ya lumshe tare da manna hancinshi kan nata yace, "Kinfi k'arfin komai a gurina Hubby". Kissing k'irjin shi tayi tace, "Dan Allah kabarni in k'arasa aikin da Hamma na ya fara, kubarni inci gaba da biyawa Garba komai na karatun shi". ta k'arashe maganar murya na rawa, gyara kwanciyar shi yayi itama ya gyarata ya kwantar da ita sosai a k'irjin shi yasa hannu ya rungumeta a hankali kamar me raɗa yace, "To daman ai yanzuma ke kikayi, kinsan kece Hammana kuma kece ni, nikuma yanzu komai nawa kece kuma nakine". hannu yasa yana shafo k'irjinta yana lumshe ido yanason kawar da maganar dan kar Ummul ta fara tunani da kuka a cikin rad'a yace, "Irin wannan kayan gara da daɗi da kike bani ai dole komai nawa ya kasance naki". Dukan k'irjin shi tayi sannan ta rungume shi tana dariya, Dama abinda yakeso kenan ya ganta cikin Happy dan haka ya lumshe ido yaja bargo ya rufesu, hannu tasa a hankali tafara wasa da kan niples ɗinshi tana ɗan murzasu tare da sauk'e mai kasala, kamar a mintsine shi ya d'anyi zillo yasa hannu ya rik'e hannunta murya can k'asa yace, "kwaɗayyeyiya kawai". d'ago kanta tayi taga yayi kamar bashi yayi maganarba ya tsareta da idanu shogoɓe fuska tayi tana murza k'afafuwan tana ɗan dukan k'irjin shi da hannun ta gaba ɗaya ta rikita shi ta tasomai da fitinar daya kwantar mintina kaɗan dasuka wuce dakyar yasa hannu ya matsota jikin shi murya na rawa yace, "To wai menayi Kuma?". bata dena abinda taken ba tace, "bakai bane kacemin kwaɗayeyyiya ba". dariya yayi mai sauti sannan yace, "Ke bakiji maganar a dai-dai bane kwaɗayeyye nace fa, aidai kinsan indai zaki taɓamin niples ɗina to kwaɗayina saiya tashi koda yanzunnan na kaudashi, to da kika taɓa nefa sai naji abin na motsi shine nacemai kwaɗayeyye, ni badake nakeba nine makwad'aicin". Yana gama faɗar haka ya janyota ya tusa hannun shi a k'irjinta nan da nan tabada kai bori yahau suka koma aikin da basufi awa biyu da gamawaba. Haka rayuwa taita tafiya Usman na ririta matar shi da babyn cikinta yana bata kulawa ta musamman hakan yasa hankalinta yafara kwanciya wanda har takan iya wuni guda batare da tayi kukaba. Watanni ukun da zaiyi suka ciki dan haka sukai shiri komawa gida Nigeria cikin aminci da d'an cikin ta da ya fara girma. A gida kuwa kowa na murnar dawowarsu Abba da Daddy kuwa tuni sun k'awatar masu da gidansu dake kusa da gidansu komai yakammalu kowa na farin cikin dawowarsu musamman Ammi da tayi kyewar y'arta da shogoɓarta Hajjajo da Inna ma sai Happy suke da d'okin ganin jikokin nasu, Adam da Sadiq ne suka ɗaukosu daga Abuja kai tsaye gida suka kawosu inda auka tarar da duk familyn su na nan suna jiran isowarsu, Kowa yaji daɗin ganin yanda Ummul ta gyaru tayi kyau tak'ara cika ga haske da shek'in da fatarta keyi ga d'an cinkin ta ya taso, Usman kuwa yana manne da Farouq dayaketa zubamai surutu cikin gwaranci sa, shiko Usman yanayi yana satar kallon matar shi yana k'arajin k'aunarta na ratsa duk jikin shi. Haka suka wuni cikin y'an uwa anata raha da hira. K'arfe tara na dare Ammi ta tashi Ummul data fara bacci a palour tace ta koma bedroom ta kwanta badan Usman yasoba shima yaje ya kwana ɗakin Adam amma yakasa bacci sai juyi yake yana missing matar shi. Washe gari diTun bayan sallah asuba malamai suka fara karatu dan sauk'e qur'ani a gidan Usman dake kusa da gidansu domin neman kariya dakuma samun albarka a gidan, basu wuce 12pm ba suka kammala akayi addu'o'i. Sai bayan sallah isha'i sannan Ammi da Hajjajo da Aunty Halima sai Anty Aysha Garkuwa suka raka Ummul gidanta. Satinsu guda da dawowa aka shirya bikin buɗe makarantar da suka assasa kafin su tafi mai suna *Dr Umar Faruq learners academy* dake tudun wada layout daura da masallacin juma'a na jibwis k'ark'ashin kulawar k'ungiyar Fityanul Islam ta jaha reshen k'aramar hukumar potiskum. bikin yasami halartar manya daga ma'aikatar ilimi ta jaha dakuma wakilan sarakunan Potiskum da fika, yaran dake sanye da farar riga da dark blue wando dogo sai farar hula sunyi kyau matuk'a ciki harda *Umar Farouq Umar Shuwa* Makarantar zata koyar da yara duka ɓangare biyu wato boko da arabic a farashi mai sauk'i a duk k'arshen zango na karatu, Anyi taro an watse lafiya da fatan Allah ya yiwa makarantar albarka. Haka rayu take tafiya Usman na kulawa da Matar shi da d'anshi dakuma cikin Ummul daya girma, Shiko Faruq yazama mai gida Uku gidan Abba ga gidan Daddy dakuma gidan Abeenshi Usman. Yau lahadi wanda ya kasance ana cikin bikin auren Rukayyat da Nuru abokin Usman kuma yaune aka gama shagalin bikin bayan abokai sun reko aggo Nuru sun gama komai sannan Usman ya d'auki Ummul enshi suka nufi gidan su, Suna isa Ummul ta wuce dakinta Wonka tayi cikin jin gajiya ta zauna gaban dressing mirror tana murje jikin ta da turaruka masu k'amshi tana kallon cikin ta da ya fara motsi a y'an k'wanakin nan ajiyan zuciya tayi tare da yin murmushi tana, "barka na yau da Farouq yana guna da bazai barni na hutaba da surutun shi". tana d'aure igiyar rigar baccin ta taji woyarta na suwa, saida ta gama kimtsawa sannan ta dauki woyar ganin ya Usman ta dan karya wuya ta amsa kiran, "Ummuna ina kikene kin barni ni d'aya". a hankali tace, "Gani nan zuwa Hamma Usman na". tana fad'in haka ta katse kiran sannan ta fita ta nufi parlour shi, zaune ta sameshi kan kujera yana ganin ta ya nuna mata cinyarshi alamar tazo ta zauna ba musu ta matso gareshi ta zauna kan cinyarshi suna fuskantar juna, hannun shi yasa yana zare igiyar rigar baccin nata, kamo hannun tayi sannan ta tallabo kanshi bakinta ta manna kan nashi tamai wani irin zazzafan kiss sannan tasa hannun ta wore rigar tata cikin lumshe ido ta jawo kanshi ta cusa a tsakiyar k'irjin ta yayinda tasa yatsunta kuma cikin sumar kanshi tana mai wani salon romancing mai rud'a tunani, gaba d'aya ta gigitashi sai juya kanshi yake a k'irjinta duk ta inda yaga dama hannun shi kuwa na shafa cikin ta da ker ya budi baki a hankali yace, "Um....! Umm...! Ummu na Allah ya miki albarka kin gama min komai a rayuwa ta tunda kike samamin farin ciki". Kai ta d'an d'ago ido cike da k'ollah tace, "Hamma Usman dole na gyara yanzu na tunda na b'ata bayana nayi kuskure a baya bana fatan kuma maimaita kuren da nayi danko gashi har gobe ina dana sani, ya Usman da nayi biyeyye yadda *'YAR FULANI* tayiwa bappan ta biyeyyah da na tabbata bazanyi dana saniba amman da nak'i yiwa iyayenmu biyeyya yanzu *MI WASMITI* *NAYI NADAMA* mai tarin yawa naga illar bijirewa zabin iyaye tabbas na yarda *NAMIJI BAYA KAD'AN* dan naga jarumta da girman shawarar da Aliyu k'anin bayana yayi ta bani a lokacin baya tabbas da nabi shawarar Aliyu da a zaman aurena da Hamma Umar da *A TAUSAYWA JUNA* yayi tasiri a kanmu amman taurin kai da zugar shaid'an sun hanani tausayawa *BANDIRAWO* na k'iyeyya tasa na manta cewa Hamma Umar fa *BANDIRAWO* nane na kasa yarda k'addarata ashe a hankali *RUBUTACCEN AL,AMARI* na bibiyar rayuwata, Hamma Usman kalli yadda *rubutaccen al, amari* da k'addara yadda suka had'amu aure Hamma Usman ina son Hamma Umar ina mai addu'a aduk wani motsina da numfashina *Hamma Usman ina sonka*". Murmushi yayi cikin jin dadi da tarin k'auna ya rugumota yana murza k'irjin ta murya can k'asa yace, *"ALLAH YA D'AIYIBA* *Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah* Na godewa Mahaliccina daya bani rai da lafiya da damar rubuta wannan littafin daga forko har zuwa k'arshe inda na tubk'e bakin zaren labarin Alhamdulillah Abinda nayi dai-dai Allah ya taramu a kan ladan abinda nayi kuskure bisa ajizanci na d'an Adam Allah ya gafarta min. Masoya na ina alfahari daku zanyi kewarku zakuyi kewata dan ina son hutawa sosai kafin na faro sabon novel na watakil mai suna *FULB'E Nigeria* ba mamaki kuma na canza sunan, Godiya mai tarin yawa agareku masoyan Hamma Umar tabbas kunsa zuriyar Shuwa farin ciki da addu'oin da kukayiwa dansu Usman yace a mik'a godiyarsa gareku *Afwan Afwan Afwan ina mai neman gafararku mace ko namiji Babba ko yaro na kusa dana nesa wanda nasani da wanda ban saniba wanda muka tab'a magana da wanda bamu tab'a magana ba wala Allah ko akwai wani abu da ya bata muku rai a cikin labarin ga dan haka ina mai neman yafiyar duk wanda na sosawa rai a zahiri banyi komai da nufin batawa kowaba Ina fatan samun yafiya daga ko wanne sashi ku yafe min tun ina raye inko na nabar duniya masoyana Addu'arku nake buk'ata ni na yafewa kowa* Moh Allah wuji furd'ata Fullo be fulaku Moh Allah saini sunata Moh Allah hokki b'uri moh baba hokki *By* *GARKUWAR FULANI🐄🐪🐫 Fauziyya Fiji ga salon mu🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀😆😂😘😘😍🤝😂😆😆* *Bissalam* Copied By VISIT www.aihausanovels.com.ng For More Novel. AIHAUSANOVELS is website consists of hausa novels note, the reason of launching this site is to Entetaint, Motivate and Educate our readers. We provided hausa novels of many type, Such Adventure, love, romance, fiction, non-fiction, mystry, fantasy, action e.t.c from hausa Authors We provided a new and old novels both softcopy and hardcopy from our Author with thier permission. AIHAUSANOVELS shafin yanar gizo ne wanda yake ɗauke da littattafan hausa, dalilin bude wannan shafin shine domin Kayatar masu karatu da kuma ilimantar da su.