Showing 81001 words to 84000 words out of 250533 words

Chapter 28 - Kurkukun Kaddara Book 2 Middle Steps By Boss Bature.

18 Feb 2025

116525

a palour”
“Okey ina son yin magana da ita, ko zaka Iya kai mata wayar” Tuntsirewa Junaid Yai da dariya yana faɗin”a’a Sai dai ka yi magana dani, sai in faɗa mata”
“Pls ka kai mata wayar, “ maƙe kafaɗa Junaid Yai kamar yana agabanshi”ni dai a’a, Ka faɗamin sai in faɗa mata saƙon”

“Shekarunka nawa”? Ga dukkan alamu wanda ya kira wayar ya fahimci ƙaramin yaron ne ya ɗaga tun daga kan voice ɗinsa.

“Huɗu Biyar shidda” Sautin dariyar mutumince ta ratsa kunnan junaid.

“No wonder ashe babban mutun ne kai, zamu iya zama abokai” maƙe kafaɗa junaid yai”to aini yarone kai kuma babba”.
“Okey yanzu faɗamin Ina yayarka Angel”? Kwa6e fuska junaid yai cikin muryar shagwa6a yace”ta 6ace 6era ya cinyeta ita da daddynta da daddyna sun mutu nima mommyna ta faɗa min” sosai mutumin Ya fashe da dariya, jin wautar Junaid

“Ka hana Ni Yin magana da mommynka, gashi kanata cinye min kati”
“Ae nace ka faɗamin saƙon sai In gaya mata” mutumin yace”Okey, ka faɗa mata DADDYN UNAISAH NE ya Kira”!

“To zan faɗa mata Sai anjima” Yana kai ƙarshen magana Yai rejecting call ɗin tunkafin mutumin yai mashi sallama, Pillow Ya janyo ya zuge zip ɗin Ya curo ring box ɗin Yana Kallon zoben
“Na Angel ne wannan, Bazan bashi ba Allah tun da ya cinye min chocolate ɗina” Yana magana yana ta6e la66ansa.

Shigowa Mahboob Yai cikin palourn Hannun shi ruƙe da Kyautar wani abu Mai faɗi an rufe shi da wrap sheet mai Ƙyalƙyali, Karasowa Yai agaban sofas din da Uncle Abdallah Yake zaune Ya sauke gift ɗin kafin ya miƙa mashi key ɗin motar, Kar6a Uncle Abdalla yai”nagode sannu da ƙoƙari” muryarshi ƙasa ƙasa Ya amsa da”yawwa” Juyawa yai da sauri Ya nufi Sashen kitchen ganin Ana na zarya kai abinci a dining.


Tunkafin a buɗe Kyautar kowa Ya ƙagara da son ganinta, musamman zahra ta ƙura idanuwanta kamar na mazuru.
Ummi na murmushi tace”masha Allah wannan kyauta tunkafin abuɗe mun fara zumuɗin ganinta” Mami tace”ni kaina a ƙagare nake Allah”
A hankali Uncle Abdallah Yake warware wrapping sheet ɗin, slowly Kyawawan idanuwanta dara dara suka Fara Bayyana, da mamaki su ke Kallon juna cikin rashin fahimtar wacece wannan Kyakkyawar Matashiyar.

Lokacin da ya warwaro wrapping sheet ɗin dai dai Saitin hancinta ya ƙarasa 6an6are ledar gaba ɗayanta, adai dai time ɗin Mahboob da Ana sun fito daga kitchen Hannun shi ruƙe da glass Na lemu Karaf Idanuwanshi suka sauka akan Hoton zanan fuskar Angel, Nan take ya saki glass ɗin hannunshi gaba ɗaya ya tarwatse ruwan lemun dake acikinsa ya tsiyaye saman tiles.

Tsabar Al’ajabi da mamakine Yasa Aneelerh da mami Yunƙurawa a sukwane suka miƙe tsaye Suna ƙare ma Zanan Kallo Yasha fenti kamar horonta aka ɗauka.

Gaba ɗaya sun Rasa bakin magana, zanan yayi bala’en Yin kyau, fuskar Angel ta fito raɗau Kyakkyawar matashiyar balarabiya bugu da ƙari buzuwa a 6angaren Mahaifinta” Zahra Ko sai faman Yarfa hannu take yi tana ambaton Wow wow Tabarakallahu ahsanul khalikin! Gaskiya koma wanene portrait artist ɗin da ya zana hoton nan ba ƙaramin ƙwararre bane ya baje basira”

Ummi tace”Masha Allah, Yarinyar ba ƙaramar kyakkyawa bace, kamar tajuddeen Ya yi kakinta, Kamanninta sak Kalar nashi, Hasken fatarne ta ɗauko Na mahaifiyarta benazir”

Lamarin ya ɗaurewa Ana kai Ganin yadda Mahboob Ya fasa glass cup ko ajikin shi, Hankalin sam baya atare dashi, Zanan Fuskar Angel Ya tafi da Imaninsa, dama can tun fil azal Mahboob Mayen mata ne.

“Mahboob Meke damunka ne? Baka ga 6arnar da ka yi ba ne’?

Ba tare da ya kalli fuskar Ana ba Ya furta”dama akwai matan Hurul aini A duniya”?

Girgiza kai Ana ta yi Fuskarta ɗauke da murmushi ta nufi dinning, don ta jera kayan tray din hannunta.

Farin Ciki Ya hana Aneeleeh furta kalma, agaban zanan da ke a jingine jikin hannun sofa, ta zuƙunna saman gwiwowinta, yatsun hannayenta na kerma ta ɗaura su saman fuskar Angel, Lokaci ɗaya ta fashe da matsanancin kuka ta kifa kanta saman zanan

“Haba Aneelerh menene abun kuka? Ke da za ki yi farin Ciki”? Mami ce tayi maganar

Hajiya adama ta miƙe ta nufi Aneelerh ta ɗan ranƙwafa ta ɗaura hannunta saman kafaɗarta.

“Share hawayen ki Aneelerh, banaso pls, Ni ban Kawo maki zanan nan don ki yi kuka ba, saboda farin Cikin ki yasa Nasa aka yi min shi, nasan zaki ji daɗi sosai” Abie yace”in dai ko bazaki daina kukan nan ba, zansa su koma da zanan” sai lokacin ta ɗago da rinannun idanuwanta da suka kaɗa jawur ta kalli fuskokinsu cikin shessheƙar kuka tace”Nadaina, wlh kukan farin cikine Ya kubce min, Inason Angel sosai, na kasa jurewa ne, da na ga zanan nan sai naji na ƙara ƙagara da son ganinta a shekarunta Na yanzu” Mayar da idanuwanta ta yi a kan hoton

“Allah sarki my Angel, ɗiyata ƙanwata kuma ƙawata abokiyar firana, Na yi missing ɗinki sosai bazan ta6a mantawa dake ba har abada” Kifa kanta tayi saman hoton Hawaye suka cigaba da wanke fuskarta, ta yi matuƙar karya masu zuciya.


*Middle step A gidan Alhaji ubaid*


Tun lokacin da Dr. shureim Ya kammala kimtsawa ya zauna gefen gadon shi ya natsu yana kallon hotunan abar ƙaunarsa, Ƙarfe Goma sha Biyu Na bugawa, Kiran Alhaji musa Ya shigo wayarsa.

Da sauri Yai picking call ɗin Ya kara a kunnanshi

“Shureim Ina Jiran ka a palour!”

Abun da Ya furta mashi kenan, Ajiyar zuciya ya sauke Tare da miƙewa Ya fito daga Bedroom ɗinsa, Yana mai jin kewar ɗakin nashi, tafiya yake yi tamkar bayason Taka ƙasa, Ji yake kamar In yabar gidan zai ƙara nisanta kanshi da ita ne, duk irin yadda yake zumuɗin barin gidan hakan bai hana wani sashe na zuciyarshi ƙin amince masa ba, Saboda acikin gidan ne, abar ƙaunarsa ta kafa tarihi acikin zuciyarshi.

Lokacin da ya ƙaraso palourn, A zaune ya samu Alhaji musa da Uncle ubaid, Sai Mahaifiyarshi laila Da Mai aikin gidansu zainab, Hannunta ruƙe da shopping bag.

Yanayin fuskokin su Ya nuna alamun rashin jin daɗin tafiyar shi, musamman mai aikin gidansu zainab da kuma Mahaifiyarshi Layla, tana a tsaye ta ruƙe qugu fuskarta babu annuri ko misƙala zarratin zallar 6acin raine.

Shi ko Alhaji ubaid sai faman sakin fara’a ya ke yi babu alamun zaiyi kewar ɗan nashi idan ya tafi.

Idanuwan dr. Shureim akan na mahaifiyarsa, da sauri ya nufi inda take atsaye, hannu biyu ta sanya ta rungumo shi a ƙirjinta, hakan da tayi mashine yasa shi jin hawaye sun cicciko idanuwanshi.

Bubbuga bayanshi take yi a hankali tana faɗin”Shureim ɗina, zanyi missing ɗinka sosai, naji takaicin tafiyar nan duk da ba wani wuri zakaje me nisa ba, sai dai sam hankalina bai kwanta da tafiyarka ba, Naci burin In gatantaka In baka kulawa ta musamman tuntuni, sai dai rashin zamanka agida da kuma gudunmu da ka ke yi, shi yasa ban samu damar yin hakan ba, Yanzu kuma na samu na shawo kanka, an nuna anfini iko da kai za’a rabani da kai,’ tun da ta fara magana Alhaji musa Ya haɗe rai fuskarshi a tamke ba annuri, don yasan dashi take magana.

“Mommy ki samin albarka ita nake buƙata daga gare ki, Sannan ki kwantar da hankalinki, Ni musulmine kuma nayi imani da Allah dashi na dogara, aduk inda zan kasance Allah yana atare dani, ballanta kuma agidan Uncle ɗina ne ba nisa zanyi ba, nasan za ku dinga zuwa akai akai kuna ganina, Nima kuma zan dinga zuwa gida” Maganar Dr. shureim ta yi matuƙar karya mata zuciya, Allah na gani tana son ɗanta sosai, Muryar Alhaji musa ce ta katse su”shureim bamu da isashen lokaci, ka wuce mu tafi”

Ɗagowa Yai daga jikin mahaifiyarshi ido cikin ido suke kallon Juna, Canza harshe ta yi zuwa larabci kafin taci gaba da magana

“Shurem hankalina bai kwanta da kawunka ba, Ni ban yarda dashi ba, Bai ta6a nuna damuwa akanka ba, tun lokacin da ƙaddarar nan ta risƙe ka har ka fara shaye shaye a ƙarshe ma kabar ƙasar gaba ɗaya, musa bai ta6a bibiyar rayuwarka ba, babu ruwanshi dakai Ƴa’ƴanshi kaɗai Ya sani, Ta ya ya hankalina zai kwanta da zuwan ka gidan shi? Allah kaɗai yasan mugun nufin shi akan ka” Tana magana tana shafa sumar kanshi da ta sauko saman wuyanshi, babu wanda Yasan me ta ke cewa, dama da biyu ta yi mashi maganar da larabci don saboda tasan basa Jin Yaren, mai aikinsu kaɗaice ta ke ji saboda itama balarabiyace, jikin zainab duk yai sanyi da jin maganar Hajiya layla, baiwar Allah duk ta damu da Shureim gani ta ke yi kamar idan ya tafi wani abu zai faru dashi.

Muryarshi araunace Ya soma magana da harshen larabci”Mommy kidaina wannan tunanin dan Allah bana so, ki kwantar da hankalin ki, Uncle musa bazai Ta6a cutar dani ba, duk da bai damu dani ba a lokacin baya, yanzu ya nuna yana ƙaunata zai Iya yiwuwa ko dan saboda tausayin halin da nake aciki ne, Nafi so ki yi mashi kyakkyawan zato mommy”

Gyaɗa kai ta yi “Shikenan shureim zan cigaba da yi maka addu’a akan Allah ya kare mun kai ya tsaremun kai daga sharrin duk wani abun cutarwa” Cikin harshen labaraci ta dinga jero addu’o’i tana tottafa masa Yana amsawa da ameen.

Bayan ta kammala ya ɗago da ido Ya kalli zainab, idanuwanta sun cicciko tab da kwalla.

Matsawa ya yi kusa da ita, fuskarshi ɗauke da murmushi yace”auntyna zan tafi asanyamin albarka” yai maganar tare da duƙar da kanshi, Hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba, Ƴan hawayen da ta ke matsewa tuni sun soma shararowa saman kuncinta.

Tafin hannunta ta ɗaura saman arab turban ɗin dake naɗe akanshi, a tsanake take jero addu’o’i tana tottofa masa a ƙarshe ta ƙara da cewa”Allah yasa Silar komawarka can ka samu farin Ciki na har abada” Ya amsa mata da ameen ameen”Allah ya saukeku lafiya shureim” ya ƙara amsa mata da ameen

Daga Haka Ya juya ya nufi Mahaifinshi Alhaji Ubaid.

Fuskarshi ɗauke da murmushi yake duban shureim”daddyna, asanya min albarka”

Da buɗar bakin Alhaji ubaid sai cewa yai “Shureim sai ka ce zaka Bar ƙasar, irin wannan bankwana haka! Na lura Jikinka duk Yai sanyi, Ko kamanta Abuja ne zaka je gidan ƙanina”? Harara Hajiya layla ta jefa ma Alhaji ubaid a fakaice.

“Lokacin da ka ke ƴan guje gujenka ba tare da sanin kowa ba, Ka ke barin ƙasar nan sai yau don zaka tafi gidan uncle ɗinka kake Neman albarkarmu”?

Da mamaki akan fuskar Dr Shureim ya ke kallon Alhaji ubaid, Ran Hajiya layla ya 6aci A harzuƙe tace”Dan Allah Ya isa haka! Me yakawo wannan maganar? Saboda kawai yace ka sanya mashi albarka? Idan baza ka sanya mashi ba sai ka ƙyale shi Ya tafi, dama albarkar uwa aka fi buƙata, bata uba ba”

Runtse ido shureim Yai, Maganar daddynsa ta ta6a mashi zuciyarshi tuni ƙwalla sun Ciko idonshi, Hatta zainab ta ji ɗacin maganar Alhaji ubaid ji take kamar ta kikkifa mashi maruka a kuncinsa.

Still da murmushi akan fuskar Alhaji ubaid ya ke dubanta, kafin ya maida dubanshi ga shureim.

“Ka ji abunda Mommynka tace, babu buƙatar albarka ta, Don haka zaka Iya tafiya” cikin jin ƙunar rai Yace”daddy na roƙe ka, Ka sanya min albarka ina buƙatar taka”! hawaye tuni sun wanke fuskarshi, Jinjina kai Alhaji Ubaid Yai, Kafin Ya janyo Dr shureim Ya rungume shi, Yana tofa mashi albarka, Hankalin shi ba ƙaramin kwanciya ya yi ba.

Miƙewa Alhaji musa yai daga saman sofa ɗin da ya ke azaune, ko kallo basu ishe shi ba, Cikin takun nan nashi na izza, ya juya ya fuce daga falon don shi arayuwarshi Ya tsani 6ata lokaci.

Tsoki Hajiya layla taja aranta tace”abanza, Uban Ji da kai, ai ni da za ka burgeni, ka kama Hanya ka yi tafiyarka, kabarmin ɗana”

Ruƙo Hannun dr shureim Alhaji ubaid Yai, Yaja shi suka nufi Hanyar fita falon, Da sauri Zainab Tabi su Hajiya layla kam zama tayi dirshan saman sofa tana faman cije le6e.

Abakin Engry hall na gidan, Zungureriyar motar da zata ɗauki Alhaji musa zuwa airport tayi parking, Hamshaƙiyar gaske Ƴar ubansu mota mai numfashi.

Yana daga kishingiɗe a ɗaya daga cikin back seat na motar, tamkar yana acikin bedroon ɗinsa saboda tsabar haɗuwarta, slowly murfin motar ke zugewa Dr shureim na ƙoƙarin shiga ciki, Muryar Zainab ta katse masa hanzarinsa.

“Namanta da wannan, kai na haɗamawa” juyowa yai tare da kallonta, Ledar hannunta ta miƙa masa, fuskar shi ɗauke da murmushi ya kar6a Yana yi mata godiya, kafin daga bisani yayi masu sallama, yasa kai cikin motar, daddaɗan Sanyin a.c ya ra6i sassan jikinsa shi kanshi Ya yi al’ajabin haɗuwar motar.

Mutun Biyune agaban motar, Driver ɗinsa da kuma p.a ɗinsa wani gabjejen mutun mai ƙirar Ƙarfi daga gani yana gym saboda ko’ina na jikinsa a murɗe Yake, wankan suit ne a jikinsa Baƙi wulik baida fara’a a fuska.

Kaitsaye Airport Suka nufa, already An shirya mashi privet jet dinsa, Bayan shigarsu cikin jirgin wanda Tsayawa zayyana Haɗuwarshi 6ata lokaci ne, abune da hankali bazai ɗauka ba, saboda an kashe dukiya kamar ba asan zafin nemanta ba, Kai kace saman bishiya ake tsinko kuɗin ana amfani da su. (😂)

Dr. shureim Yaga aljannar duniya, Bayan tashin jirgin Cikin mintuna da basu wuci arba’in ba Suka ƙaraso Airport ɗin Abuja, Tun kafin jet ɗinsa ya ƙaraso airport ɗin tuni Escords ɗinsa sun hallara abakin motocin su cikin shiga ta baƙaƙen suits domin tarbarsu da kuma basu tsaro.

*EX-PRISONERS❤*


Tun Bayan da suka kammala Cin abinci kowan nan su yai kulu wash rabu hani’an, Nurse ta shigo ɗakin ta kwashe kayan abincin da suka ci ta fuce da su waje.

Gaba ɗayansu suna A saman gadon zazzaune Sai Yanzu su ka samu damar ƙarewa ɗakin kallo.

“Angel menene wancan”? Parveen ce ta yi maganar tana nuna mata plasma tv dake manne a jikin bango.

“Tv ce da ita ake yin kallo”
“To ki kunna mana mu gani mu ma” girgiza kai Angel ta yi”a’a Parveen ku bari sai munje gidan daddyna tukunna”

ta faɗi hakanne don tasan muddin ta kunna masu kallo zasu birkice mata ne, a ƙarshe ay abun kunya, tun da basu ta6a gani ba.

Tambayoyi suka dinga jera mata kamar ƴan jarida, komai na ɗakin sai sun tambayeta menene shi ya akeyin amfani da shi, ita kanta ba komai ta sani ba saboda ba kalar ɗakinsu na gida bane, Iya abunda ta sani take amsa masu.

“Zan shigo toilet” Batul ce ta yi maganar, saukowa ta yi daga saman gadon ta nufi ƙofar da take tunanin ta toilet ce ta tura da hannu ta shiga, tun da ta shiga take bin ko’ina da kallo sauƙin ma toilet ɗin su na prison na zamani ne, da ko anga ƙauyanci sai dai da banbanci sosai, don wannan akwai sink da bathtub hada shower ga mirror da sauran Kayan amfani.

Agaban madubi Batul ta tsaya tana kallon fuskarta, bata ta6a ganin Kyanta irin na yau ba yatsun hannunta ta tura cikin Curly hair ɗinta tana cakuɗa shi.

Acan bedroom ɗin Bayan shigarta toilet, zuciya da saƙe saƙe Angel sai ta dinga ayyanawa aranta ga Batul can ta kunna Ruwan zafi amaimakon na sanyi” Jiki Na rawa ta sauko daga saman gadon ta nufi toilet ɗin, ko neman excuse babu ta shigo toilet din kamar an jeho ta.

Jin motsin shigowar mutun yasa Batul Juyowa a firgice don ganin wanene. Kusan atare suka sauke Ajiyar zuciya

“Dama ba wani abu za ki yi a toilet ɗin ba”?
Murmushi Batul ta sakar mata”Inaso ne in ƙare ma ko’ina kallo,”

“In dai wannan ne kada ki damu zan yi maku bayanin komai, amma Yanzu ki fito mu koma ɗaki” Amsa mata ta yi da toh ta juya ta nufi Angel ta ruƙo hannunta suka fito, shugowarsu ɗakin ke da Wuya Aka buɗe ƙofar, Dr Daniel brown ne tare da Nurse rebecca.

Fuskokinsu ɗauke da murmushi, cikin harshen turanci ya soma yi mata magana.

‘Masoyiya Angel da ƴa’ƴanta, fatan na same ku Lafiya” Amsa mashi sukayi da lafiyalou
“Ya jikin naku? Ko akwai inda ke yi maku ciwo “? Atare suka girgiza mashi kai

“Okey, Starting tomorrow, you’ll be receiving injections for three days, and you’ll also be taking regular medication to improve your health.” cikin kulawa dr brown ke yi masu magana idonshi akan fuskar Angel.

Murmushi ta sakar mashi”mun gode sosai da kulawarku agare mu, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku”

“Kada ki damu, aikin mu ne, Ko akwai wani abu da kuke buƙata”?

Cikin raɗa Batul ta yi ma Angel magana a kunne”muna son ganin Haris da Danish”

“Doctor, can we see our brothers?” kamar mai jin shakkar shi ta yi maganar.

Jinjina mata kai Yai alamar eh, Kafin ya ɗaura idonsa akan Nurse rebecca” Ki kai su ɗakin Ƴan uwansu”
“Okey sir” Mayar da idonshi yai kan Angel” pls muna so ki samu natsuwa sosai, ki kwantar da hankalinki dana ƴan uwanki, akwai magana da zamuyi dake tare da sojojin da suke ceci Rayuwarku, sunce da zarar kin farka a sanar da su, Ni kuma na bari sai zuwa gobe idan kin ƙara wartsake wa duk da naga jikin naki da ƙwari”

shiru Angel ta yi tana faman zazzare mashi gray eyes ɗinta aranta ta ayyana komai suke son sani? fatanta Allah ya bata ikon amsa masu tambayoyin da zasu Yi mata

“Haɗin kanki mu ke buƙata Masoyiya Angel” murmushin yaƙe ta sakar mashi wanda bai kai zuci ba.

Bayan fitar shi daga ɗakin, Nurse ta kalli faces ɗinsu”zamu Iya tafiya” A hanzarce suka sassauko daga saman gadon suka bi bayanta, tun da suka fito daga ɗakin gabansu ke faɗuwa ganin haɗaɗɗen wurin da suka tsinci kansu a cikinsa, Asibitin Har ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login