Kurkukun Kaddara Book 2 Middle Steps

Chapter 36 of 83

Kayan Jikin su, Su Angel an dage da yin sallah da addu’a, har tsakar dare tana tashi yin night prayers, yawanci addu’o’inta akan Danish ne, ta roƙi Allah da ya kare mata shi, idan farkawarshi Alkhairi ce Allah Yasa ya tashi cikin amince, idan kuma farkawarshi ba Alkhairi bace Allah yasa yaita sharar baccina har zuwa su koma Nigeria zaifi masu sauƙin su Yi control dinshi, duk da yanzu ta fara fargaban kada su zo Nigeria A nemi Ruwan zam zam arasa tabbas ba ƙaramar matsala za’a samu ba, damuwarta yanzu akan Sojojin ce shiru basu dawo ba, Kuma bata Ji daga bakin dr laura Ya ake ciki ba, Shin za’a maidasu ƙasarsu ne ko kuwa a’a, Ta dai zubawa sarautar Allah Ido 👀

Sam ta kasa runtsawa, tun wuraren ƙarfe tara na dare ta farka, saboda mugun bugun da ƙirjinta ke yi mata, tabbas tana ji aranta wani abun ne ke shirin faruwa.
Miƙewa Tayi zaune saman gadonta, ta jingina Bayanta Jikin pillow, idanuwanta suna a lumshe, sanyin A.c sai ratsa fatar jikinta Yake yi wata irin kasala take Ji da matsanancin faɗuwae gaba.
“Masoyiya Angel, Lafiya kika farka daga bacci? Na lura kamar wani abu ke damunki”
Muryar Nurse Jessica ce ta fargar da ita, har saida ta ɗan zabura don bata yi tsammanin jin Muryar mutun a kusa da ita ba.
Slowly ta wurga eye balls ɗinta akan fuskar nurse ɗin, tana daga zaune saman chair ta kusa da gadonta, hannunta ruƙe da wayarta, fara ce sol, uniform ɗin jikinta light blue ne kalar nasu, ta ɗaure jar sumar kanta da ribbom.
Nauyayyar ajiyar zuciya Angel ta sauke tare da cewa”sister, nagode da kulawarki agareni, nakasa runtsawane saboda inason ganin yan uwana ko zaki Iya taimaka min”?
Smiling gently nurse jessica tace”Na lura kina son ƴan uwan nan naki, cos tun ranar dana fara kula da ke, sau uku kike zuwa room ɗinsu Kina duba su, faɗamin ko dai akwai damuwane? Ko tsoro kike ji kada mu sace maki su”? Da zolaya nurce jessica tayi mata maganar
Cikin jin kunya Angel takama ƴan kame kame tana faɗin”am.... Ba haka bane just inason su sosai, mun shaƙu da juna, shiyasa bana samun natsuwa idan ban gansu akai akai ba”

Nurse jessice tace”Kuna burgeni sosai, inaso Inga ƴan uwan masu son junansu, masu haɗin kai, ta hakanne ake cin ribar zaman duniya, idan har kana da ɗan uwa mai share maka hawayenka, mai nuna maka ƙauna wanda baya gajiya dakai tabbas ka gode ma Allah, zai yi wuya ka rasa madafa a duniyar nan, babu wanda zai yi gigin cutar dakai muddin kuna da haɗin kai a tsakaninku, amma idan Ya kasance kuna ƴan uwa baku da haɗin kai, danasani zai biyo baya cos dayawa rashin kulawa keja har damuwa tayi ma ɗan uwanka Illa, ya akaita abunda zakuyi danasani gaba dayanku”

Angel ta natsu Tana sauraron Kalaman Nurse Jessica, Haƙika kalamanta sun ta6a mata zuciya, sai taji ta ƙara ƙaunar ƴan uwanta, ta ɗanyi mamakin yarda nurse ɗin take sakar mata fuska suke Yin fira, saboda ta ta6a Jin ana faɗin turawa sun tsani baƙar fata suna nuna masu wariyar launin fata, sai dai tayi tunanin ba duka aka taru aka zama ɗaya ba, sannan kuma su basu da banbanci dasu, hasken fata, launin ido da kuma sumar kai, shiyasa suka zama ɗaya.

“Ki tashi muje in raka Ki ɗakunan ƴan uwan naki, Nima Inason ganin su, musamman twins ɗin nan” murmushine Ya bayyana akan fuskar Angel jin abunda nurse ɗin tace, tuntuni ta faɗa mata, ba twins bane Jamimah da azeeza ɗaya ta girma ɗaya amma taƙi yarda, ba ita kaɗai ba hatta sauran nurses ɗin da likitocin kallon twins suke Yi masu acewarsu Basu da banbanci, Komai nasu kala ɗaya.

da zumuɗi Angel ta sauko daga saman gadon, light blue uniform ɗinta ne a jikinta, sai da ta fara zuwa gaban closet ɗin ɗakin ta buɗe ta ɗauko Hijabin da aka bata Nayin sallah ta zura a jikinta.

Hannunsu ruƙe cikin na juna ita da nurse ɗin suka fito daga ɗakin, hasken electric bulbs Ya haskaka Asibitin tamar da rana, a tsanake suke Yin tafiya suna tattaunawa a tsakaninsu, ɗakin Gabriel suka Fara shiga, tayi mamakin ganinshi idon shi biyu Shida nurse rebecca, ta kunna masu kallo sun natsu abunsu.

Jin motsin shigowar Mutun yasa suka kai eyes dinsu ga ƙofar, murmushi ne ya bayyana akan faces dinsu

Mayar masu da martanin murmushin nasu Angel tayi”ɗan uwana, Baka Yi bacci ba? Fadamin meya hana ka Yin bacci”!
Kafin Ya bata amsa nurse rebecca tace”Ni na hana shi, Ko bakisan mun fara soyayya bane, Gabriel baka faɗa mata ba”? Gaba daya suka sanya dariya, jessica tace”har kinyi kamu kenan” ɗaga mata gira tayi”yap, taya zan bari damar nan ta wuce ni”? Firarsu ba ƙaramin nishaɗi take sanyasu ba, Angel tuni ta haye saman gadon gabriel, Ruƙo hannunshi tayi acikin nata,
“My sister, meya hana Ki yin bacci”? Ƙasa ƙasa da murya ta furta”Danish, Hankalina Yaƙi kwanciya da rashin farkawarshi, Yaufa kusan One week kenan a lissafina, Gabriel bansan ya zanyi ba, Ni nafi so Mu koma nigeria....”katse mata maganar yai da cewa”ai kin faɗamin dr laura tace zata taimaka mana mu koma can ko?

Ɗaga mashi kai Tayi”eh, amma har yau shiru, banji daga gareta ba, Kuma kaga sojojin basu ƙara dawowa ba”

Ganin kamar duk ta damu yasa shi kwantar mata da hankali”Wani jinkirin alkhairi ne Angel, wata’ƙil ki ga gobe anzo mana da kyakkyawan labari, don haka Mu ƙara haƙuri kada mu damu kanmu komai zai tafi dai dai My lovely sister” Yai magabar Tare da jan kumatunta da hannunshi, Hakan ba ƙaramin dariya Ya bata ba.

“Masoyiya Angel, zamu Iya tafiya “? Muryar nurse Jessica ce ta katse masu tattaunawar tasu.

Peck tayi mashi saman cheek dinsa”ka kwanta ka huta,” ta ambaci hakan tare da saukowa daga saman gadonshi ta nufi nurse jessice taja hannunta suke fuce bayan sunyi masu sallama.

Room ɗin Batul suka shiga, A kwance suka same ta saman gado, ta ƙudundune da bargo, da alama tayi zurfi abaccinta, Basu shiga ɗakin ba suka wuce ɗakin Jemimah, Itama baccin take Yi, ta wawware ƙafafuwanta ta saki baki da hanci, nurse din dake kula da ita, Tana acikin ɗakin har gaisawa sukayi da ita kafin suka nufi ɗakin Azeeza, Kamar yarda suka samu jemimah haka suka sameta a kwance bacci yai daɗi, murmushi Angel tasaki kafin suka ƙara gaba zuwa ɗakin Parveen, Hallau dai mai hali Baya ta6a canzawa, bata Yi mamakin ganinta a zaune gefen gado ta tasa abinci saici take Yi, An kunna mata tv tana kallon mbc channel Suna Yin cartoon tom and jerry, Sai tiƙar dariya take Yi kamar zata kifa kanta saman table din gaban gadon, babu alamun bacci a idonta, sam bata ji motsin shigowarsu ba, plate ɗaya ne agabanta shaƙe da chicken wings, gefen plate ɗin kuma Apple juice ne, Duniya Ta yi mata daɗi, Gyaran muryar da Angel Tayi mata ne yai silar Jawo Hankalinta ga dubansu, bakinta cunkushe da nama ta furta “Angel”

Nurse ɗin da suka zo atare da ita sai murmushi take saki, Da alama parveen ta burgeta, ba tun Yau ba, duk in tazo dubata sai ta sameta tana Cin abinci, da wuya ka same ta bakinta babu abun taunawa.

Farin Cikine Ya bayyana akan fuskarta, Da sauri ta ƙarasa suka rungume juna ita da Angel.

Shafa sumar kanta Tayi”Parveen kowa Yai bacci banda ke, kina nan kinata cin abinci Ko gajiya bakya yi, so kike ki karya masu jari ko”? Da zolaya tayi maganar, bayan ta raba jikinta daga na Angel, Just 4days Har kumatu ta ƙara.
“Ai nurse ɗinne Yace min duk in ina buƙatar wani abu Inyi mashi magana...” zaro ido Angel Tayi hada ruƙe ha6a tace”Eyehh! Wato saboda yace maki haka shine kuma ko da wani lokaci sai kince mashi zaki ci abinci, Angaya maki nan Restaurant ne? You’re a patient bai kamata aga kina cunkushe cunkushen abinci, kamar me fama da cutar Yunwa” sam Sun manta da nurse din da ke abayansu, Da turancin Angel Keyin maganar, hakan Yasa ta fahimtaci abunda suke tattaunawa, sai faman sakin murmushi take Yi tana binsu da kallo.

“Angel ai su ba ruwansu, komai mutun yake so suna yi mashi, baki ga yarda nurse din Ya ke ji dani ba, Shine ma Ya kunna mun abun nan ba ƙaramin Daɗi naji ba” ta yi magana tana nuna mata plasma tv

Watsa Hannu Angel Tayi”Okey, Koma Ki cigaba da cin abincinki, pls Ki samu ki kwanta ki huta, ki kula mun da kanki” murmushi parveen ta sakar mata

“Thank u sis, Allah yabar mana Angel ɗinmu” Nurse jessica ta tsaresu da ido, gwanin ban sha’awa take kallon su
Sallama sukayi Ma parveen bayan sun fito daga ɗakin suka nufi ɗakin Hannah, Yarinya ƴar madara, hankalinta kwance take sharar baccinta, Rabin jikinta duvet ne.

Bayan sun ƙara gaba ɗakin Naufal su ka shiga da ɗakin Javed, Kowan nan su bacci Yake Yi, daga ɗakin Javed suka nufi ɗakin Haris, Bawan Allah ba laifi Jiki Yai kyau, yana samun kulawa fiye da sauran ƴan uwanshi saboda lalurar shi.

Sunyi tunanin bacci yake yi ganin shi kwance ya rufe idanuwanshi, Har sun Juya zasu fuce muryar shi ta katse masu hanzarinsu

“Angel!” Atare suka Juyo suna kallonshi, Ya buɗe idanuwanshi da suke a lumshe, farin Cikine Ya lullu6e Angel, da sauri ta nufi gadon shi daga gefe ta haye, taimaka mashi tayi ya mike zaune, ta rungume shi a chest ɗinta, hannunta asaman bayanshi tana shafashi

“Haris ɗina Ya jiki naka da sauƙi ko”? Muryar shi, ƙasa ƙasa Ya masa mata”da sauƙi Angel, bana jin ciwo a jikina sai dai har yanzu ina yin mafarki akan Deejana, ina ganinta a prison suna azabtarmin da ita, tana kuka tana roƙona akan in taimaki rayuwarta’ cikin rauni na murya yai maganar

“Ka kwantar da hankalinka haris, Mafarki ba gaskiya bane, sau dayawa mafarki Shaidanne yake assasa shi, wani daga Allah ne wani mafarkin kuma ya danganta daga Yarda ka ƙwallafa abu aranka, shiyasa nace ka dage da yin addu’a, in sha Allah haris in dai Deeja tana araye zaku haɗu ne,”

Nurse ɗin ta zuba masu ido tana kallon su, bata san me suke tattaunawa ba a tsakaninsu, saboda sunyi amfani da harshen hausa.

Still Haris bai ɗago kanshi daga saman chest ɗinta ba ji yake kamar deejanshi ce

“Wlh Angel inason deejana, Kuma inayi mata addu’a, Ko yanzu da kika sameni na rufe idanuwana, addu’a nakeyi mata, Ni bazan ta6a gajiya dayima deeja addu’a ba, Har nunfashina na ƙarshe”

Tuni idanuwan Angel sun cicciko tab da ƙwalla, (Ƙaunar dake a tsakanin haris da Deeja, daga Allah ne, irin son da ake kira true love, Inason ka kana so na badan wani abu ba❤ Allah Ya bamu masu sonmu tsakani da Allah🙏)

Shafa sumar kanshi Angel Ta yi da hannunta, Jin shessheƙar kukan shi Ba ƙaramin Karya mata zuciya yai ba

“Haris pls don’t cry, kasan bana son jin kukan ka, ko ba danni ba, nurse da ke kula dakai bazata Ji daɗi ba, Suna iyakar bakin ƙoƙarinsu wurin ganin sun sanyaka farin ciki duk don ka rabu da ciwon zuciyar dake damunka” a hankali ya ɗago da kanshi Idanuwanshi sun ɗan kumbura.

“Angel, nadaina bazan ƙara ba” tafin hannunta ta ɗaura saman fuskarshi tana share mashi hawayenshi

“Zan tafi Yanzu nurse tana Jirana, Amma kafin nan kayi min murmushi mana” daƙyar ya ƙaƙaro murmushi kan fuskarshi, Hakanan taji gabanta Ya faɗi ƙura ido tayi akan face dinshi kamar tana son gano wani abu sai dai ta kasa gane menene shi.

Ganin yadda take kallonshi yasa yace mata Lafiya Angel’? Girgiza mashi kai Tayi bakomai, ka kula mun dakanka, Sai Allah Yakaimu” daga haka ta sauko daga sama gadon, suka fice daga ɗakin shi ita da nurse jessica.
Last room da suka Nufa ɗakin Garkuwa, tunkafin su ƙarasa take Jin faɗuwar gabanta na ƙaruwa, ji take yi kamar idan ta shiga ɗakin wani abu zai faru, Da bismillah abakinta ta kutsa kai dakin nurse jessica tabi Bayanta, kamar matacce haka suka same shi kamar kullum Sai sharar baccin shi Ya ke yi, Lamarin Danish ba ƙaramin ɗaurewa likitoci kai Yai ba, tsawon kwanaki mutun Yana yin bacci yaƙi tashi? Tun abun na damunsu har sun haƙura sun zubawa sarautar Allah ido.

Saman chair nurse ta zauna idonta akan face din Danish

A hankali Angel ta zauna gefenshi Tana ƙare mashi kallo, Ji take yi tamkar ta fasa ihu acikin kunnuwanshi wata’ƙil idan Yaji zai farka, sai da tasan ko Tayi abanza, Allah shine shaidarta, ta matsu a ƙagare take da son farkawarshi kamar ta yi hauka
Sam ta manta da nurse dake a ɗakin, ta natsu tana kallon shi kamar zata Haɗiye shi, A hankali Ta ɗaura small pink lips ɗinta farar fatar cheek dinsa ta manna ma kiss.

Murmushin gefen fuska nurse jessy ta dan saki, abun ba ƙaramin ƙayatar da ita yai ba, kamar ta samu tv haka take kallonsu.

A hankali Angel ta kwantar da kanta saman faffaɗan chest dinshi ta kasa kunne tana sauraran heart beat dinsa

Muryarta cikin raɗa take Yin magana”My man pls wake up, nayi kewarka kamar zan zauce, dan Allah ka taimaki rayuwana ka farka danish, a matse nake duk na takura da rashinka, pls idan kana Jina Ka amsa min” hauka ta soma yi mashi asaman jikinsa tabi duk ta hayeshi, shessheƙar kuka tadinga yi mashi duk don ya farka sam babu hawaye akan face dinta, ɗagowa tayi da kanta, gray eyes dinta akan fine face nasa, eyes lashes dinsa ta ƙurawa ido masu kyau da tsari.

Bakomai take tunawa ba face Farkon haɗuwarsu a prison, a karo na farko da Ta yi tozali dashi saida gabanta Ya faɗi saboda zazzafan Kyanshi, Murmushi tasaki tunawa da maganar farko data fara haɗasu lokacin da tana zazzaga masu masifa akan afaɗa mata ubanwa ya kawota prison
Muryarshi ta ratsa kunnanta, tamkar ana busa sarewa
“Bansan wacece ke ba, amma na lura kamar kina son wuce gona da iri, yakamata ki kiyaye harshen ki, wannan tsohuwar da ki ke gani tamkar uwa take agare mu, tun da mu ke da ita bata ta6a cutar damu ba, muna samun kyakkyawar kulawa daga gare ta, don haka bazamu bari zuwan ki ya zama silar tarwatsewar farin cikin mu ba hope u understand me!” a lokacin takai maƙura A zafafe Ta juyo ta kalle shi tsabar mamaki tamkar ba daga bakinshi maganar ta fito ba, duk da bugun da zuciyarta tayi mata na ganin kyanshi hakan bai hanata zazzaga mashi masifa ba.

“Sannu isasshen me walkin sa! Kai kuma a suwa ɗan wake a hotel? am talking you are talking? duk wanda ke son zaman lafiya acikin ku, kada ya kuskura ya shiga gona ta, domin ni ba irin ku bace! Wlh uban mutun zanci kuma a zauna lafiya!”

Batasan lokacin da dariya ta kubce mata ba, Rayuwa kenan, Idan mutun ya kasance ƙaddararka baka isa ka canza shi ba, bata ta6a tunanin zasu sasanta tsakaninsu ba, saboda rashin jituwarsu sai gashi a yanzu sun shaƙu da junansu ita da sauran ƴan uwanta prisoners.

Nurse Jessica Har tafara Gajiya da zama bacci na shirin kwasarta a saman kujera, sam batason ta katse Angel donta fahimci ba ƙaramin so take Yiwa ɗan uwan nata ba, duba da yadda ta haye saman jikinshi tana sambatu hada murmushi da dariya.

Soft lips ɗinsa ta ƙurawa ido tamkar anyi mixing din launinsu da pink

“Masoyiya Angel Yakamata mu koma ɗaki ko”? Muryar Nurse jessica ce ta fargar da ita, Amsa mata Tayi da toh Kafin ta miƙe ta ɗan dukar da kanta saitin fuskarshi sumar kanta ta yi mashi rumfa, A hankali ta ɗaura small mouth ɗinta saman Forehead dinsa Da Niyar ta manna mashi peck ba zato ba tsammani taji ya damƙi waist dinsa ruƙo bana wasa ba, Agigice Take kallon face dinsa wani abun mamaki bai farka daga baccin ba, tashin hankalin da ba’a sama shi data, Nan take Jikinta Ya hau Yin kakarwa ido Ya raina fata, wata irin zuface ta soma tsastsafo mata ta cikin hudar gashin jikinta.......




*Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*



First bank



3196407426,



*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*


_~*BossLadiesWriters*~_


_*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_


~Middle step~


_The Prisoners E20🔥💫_



*Daga alƙalamin Boss Bature*






Hankalinta a matuƙar tashe take kallon fuskarshi, Numfashinta na hauhawa zuciyarta na bugawa da sauti mai ƙarfin gaske tamkar zata tsaga ƙirjinta, tsabar tsoratar da ta yi, Nurse Jessica da ke a zaune ta rasa gane meke faruwa ne? taga dai tun da Angel ta yi mashi rumfa taƙi motsawa, kamar an daskarar da ita, idanuwanta ba su hango mata hannun Danish da ya damƙi Qugun Angel da shi, sakamakon Sumar Kanta da Hijabin jikinta sun lullu6e shi.


“masoyiya Angel, Ke nake Jira, kusan ƙarfe goma na dare, Yakamata Muje ki kwanta ki kwanta ki huta” Cikin Kulawa ta yi mata maganar Tana leƙen fuskarta sai dai bata samu damar ganinta ba, saboda wuyan Hijabinta Ya zame tuntuni sumar kanta ta zazzago gefe da gefen fuskarta, ta rufe su.


Yunƙurin kubcewa tayi daga ruƙon nashi sai dai ko gizau wannan bai yi ba, kuma bai motsa ba, Ya matseta A jikinshi, tamkar an ɗaureta da igiyoyi, duk da sanyin A.c na room din hakan bai hana ta zubda gumi ba, zufar dake wanko fuskarta kaitsaye take sauka saman fatar face nasa, idanuwanta azazzare, yayin da acan cikin zuciyarta ta ke ta ambaton”INNA LILLAHI WA’INNA ILAIHIRRAJI’UN”! Ba ƙaƙƙautawa.


Muyar Nurse Jessica ce ta ƙara fargar da ita”Lafiya kuwa Angel? Ya akai naji Kinyi shiru? Ko kinyi bacci ne a jikin shi” ta ƙare maganar tare da yunƙurawa ta miƙe daga saman chair ɗin ta nufi gaban gadon ta tsaya tana ci gaba da yi mata magana, tsabar yadda la66anta ke yin kerma

Download complete TXT · Novel page