Kurkukun Kaddara Book 2 Middle Steps
Chapter 38 of 83
abun”
Kamar wani ƙaramin yaro haka take tarairayarshi, da hannu ta dinga bashi grilled chicken din yana ci, Idan ka kallesu a yadda suke zaune sai ka sha mamaki saboda girman da yai ma Angel, Bata wuci Ya lullu6eta da faffaɗan kirjinshi ba, amma saboda sabo da juna, da kuma shaƙuwa da ƙaunar dake a tsakaninsu bata ganin girman shi.
Ɗaya daga cikin abunda ke burgeta, idan ta tura mashi abincin abaki yadda yake motsa tattausan full lips nasa da kuma motsin Adam’s apple dinsa, komai nashi ƙayatar da ita yake yi kamar yarda itama ta ke burge shi, a ƙarshe sai suka koma suna feeding din junansu tana bashi abaki, Shima yana bata abaki.
Abunda basu sani ba, Har safiya tayi gari ya ware babu wanda Ya lura a cikinsu, tuni sun kammala cin abincin, sun shagala suna kallon juna.
*ABUJA NIGERIA A GIDAN ƊAN IYA*
A round ƙarfe 10 na safe agogon Nigeria, tun bayan kammala sallar Asubahi da ta koma bacci bata farkaba ba saboda Jiya sun sha fira da Aneelerh sun kusa raba dare kamar ƴa’ƴan Aljanu, shiyasa yau take ta sharar baccinta kamar matatta, ta wawware ƙafafuwanta saman mattress, ta saki baki da hanci, sai jan minshari ta ke yi kamar ragon sallah, daɗin bacci hada yawu a gefen bakinta, Gajeran wandone a jikinta sai ƴar farar half vest data zura, sumar kanta babu kitso zallar gashinta a hargitse ba gyara.
Tayi zurfi acikin baccinta, Wayarta dake ajiye saman side drawer ta buga uban ringing, Babu alamun zata farka har kiran ya katse, wani ya kuma shigowa, sautin ya cika ko’ina banda kunnan zahra dake yin bacci.
Shigowa cikin ɗakin Aneelerh Tayi, jikinta asanye da doguwar riga, ta yi rolling mayafi akanta, kaitsaye ta nufi drawer din ta miƙa hannu ta ɗauki wayar tana faɗin”Allah ya shirya zahra, wannan bacci haka kamar matatta, ana ta kiran mutun awaya wama ya sani ko arziƙi ne ke kiranta...” Waro ido waje aneeleeh tayi ganin sunan mutumin dake kiran Aneelerh, Ya fito 6aro 6aro saman screen din, bakowa bace face Hajiya Saratu Obinna, Jiki na rawa ta haye saman gadon takai hannu tana bubbuga ƙafar zahra”banza, ki tashi arziƙine ke kiran ki, zahra ki tashi kada muyi asara” yamutsa fuska zahra tayi muryarta kamar ta mashayin giya ta furta”dallah wanene ke takuramin, ni a ƙyaleni inyi bacci na, ba dama mutun ya ɗan kwanta ya runtsa sai an samu wani uban anacin ya tada shi’
cikin magagin bacci take yin sambatun. kiran har yayi rejecting, zuƙunnawa Aneeleeh tayi saitin kunnan ta da karfi ta furta”Shashasha Hajiya saratu obinna ce ke Kira” A haukace Zahra ta zabura Ta miƙe tana faman mutsustsuke ido, A fujajen take fadin”Wai dagaske? Ina wayar? Gaba ɗaya tabi ta ruɗe jin an ambaci sunan Hajiya saratu obinna, sai faman zazzare ido take yi.
Miƙa mata wayar Aneelerh ta yi “yo har yayi rejecting, Tun ɗazu nake ta ƙoƙarin tada ki, Kinƙi ki farka gashi yanzu kin ja mana asara....” bubbuga katifa zahra tayi da hannu tsabar takaici hada hawaye akan fuskarta”Aunty aneelerh, kin karyamin jari, meyasa da kika tada ni naƙi tashi baki shiga toilet kin ciko bokiti da ruwa kin watsa mun ba”?
Babu wasa akan face dinta ta yi maganar, Sakin Baki aneeleeh tayi tana kallonta
Zahra ta ci gaba da yin kuka tana faɗin “Nashiga uku, wayyo Allahna, ni wlh bakiyi min adalci ba, wama ya sani ko kujerar Hajji za’a raba mana,” sosai ta fashe ma Aneelerh da kuka. Lamarin ya ɗaure mata kai, ta rasa ina zahra da mahboob suka gado shegen son kuɗi, sai dai tafi tunanin ta 6angaren mahaifinsu ne.
Lallashinta ta soma yi”Kiyi hakuri sister kukan Ya isa haka, wata’kil ta ƙara Kiran ki,” cikin shessheƙar kuka tace”taya za’ae ta sake kira na, bakisan halin masu kuɗin nan ba, basu ɗaukar raini, za ta yi tsammanin dagangan naƙi ɗaga kiranta, Wayyo Allahna aunty Aneelerh, nayi wa arziki ƙulli, har ƙiyamil laili nayi akan Allah ya bude mun kofofin samu, da kuma miji nagari a sabuwar shekarar da zamu shiga...” dariyace kumshe abakin Aneelerh.
Dafa kafaɗarta tayi”Sorry My lovely sis, Yanzu abunda za’ae, Ki kira Layinta mu gani ko zata ɗaga” kar6ar wayar tayi daga hannun Aneelerh, Yatsun hannunta har kerma sukeyi sam babu natsuwa, kiran layin ta soma Yi, tamkar zata fashe da kuka ta kalli Aneelerh”line busy, dama ni nasani, wlh basa ɗaga kira, idan ba su suka kira mutun ba”
Aneelerh tace”mu ɗan ƙara haƙuri, zuwa anjima sai mu ƙara jaraba kiran layinta, yanzu ki tashi ki shiga toilet ki ki gyara jikin ki, zan Jiraki anan,” cikin shessheƙar kuka ta amsa da toh, kafin ta sauko daga saman gadon ta nufi toilet ta shige.
Bayan shigarta da mintuna biyar Aneeleeh tana zaune tsakiyar gadon tana jiran fitowarta, zuciyarta acunkushe take da tunanin baby junaid ɗinta tayi kewarshi, tun shekaran Jiya Uncle abdallah da hajiya adama suka koma gidansu, anyi rabuwar mutunci sun nemi alfarma Junaid ya zauna wurinsu na tsawon 2 weeks, zai dawo gida, sannan duk weekend za’a dinga kai masu shi, yanzu haka yana acan gidan nasu, tsawon kwana uku da yayi acan kullum ne sai ya matsa masu akan su kira mashi Mommyn nasa, wani lokacin tun kafin ta farka daga bacci kiran su ke shigowa wayarta saboda jarabar junaid.
Tayi zurfi cikin tunaninta, Wayar Zahra ta soma yin ringing, Kafin ta wurga idonta kan inda zahra ta ajiye wayar saman drawer, da ƙarfi taji sautin buɗe ƙofar toilet, Ras taji gabanta Ya fadi ganin zahra ta watso aguje, jikinta duk kumfa daga ita sai gajeran towel tayi ɗaurin gaba da shi, hatta fuskarta kumfar sabulu ce, miƙa hannu tayi ta rurumi wayar, tsabar zumuɗin ganin wanene ke kiranta, fatanta Allah yasa hajiya saratu obinna ce, cikin sa’a idonta yai mata nuni da sunanta akan screen, sai ƙoƙarin ɗaga kiran takeyi kumfar hannunta ta hana touching din yin aiki, kamar zata fashe da kuka, sai da aneelerh ta taimaka mata wurin answer mata call din tukunna ta samu natsuwa, a Hands free ta sanya kiran don suji me zata je
Cikin girmamawa zahra tayi mata sallama”Assalamu alaikum” kamar tana agabanta.
On the other hand sautin muryar hajiya saratu ya karaɗe kunnuwansu
“Wa’alaikum salam”
“Ina kwana hajiya, fatan kun tashi Lafiya, wlh bana a kusa da wayar ne, kunata kira bansamu damar ɗagawa ba, da yake na ɗan shiga toilet ne”
Aneeleeh dake zaune saman gado, dariyace ta kubce mata da sauri ta cakumi pillow ta toshe fuskarta dashi don kada sautin Ya fita, bakomai ne ya sanyata yin dariya ba face yadda zahara keyin waya kamar ƴar maroƙa, ga kumfa a jikinta.
“Bawani abu ai, nayi maki uziri, dalilin dayasa na kira layin ki, last time da kukayi mana decoration aikin ku ya yi mana kyau, muna so za’a ƙara Yi mana wani next week, sannan muna so za’a fidda mana anko wanda zai dace damu”
Da sauri zahra ta kar6e da cewa”in sha Allah hajiya komai kuke so za’ayi yadda ya dace, hada ƙunshi da kitso idan akwai mai buƙata”
Hajiya saratu tace”okey, You can send me the list of your services and I’ll add what I want to the list, through text message zaki tura min”
“Toh hajiya in sha Allah, Mun gode sosai, da kiranmu da ku kayi, kuma in sha Allah zaku same mu masu biyayya ga duk abunda kuke so,” bayan sunyi sallama da Hajiya saratu, Zahra ta sauke nauyayyar Ajiyar zuciya, Ta fasa ihu Tana faɗin”Alhamdulillah! lokacin Yin arziki na Yayi, wai yau ni ce Aunty saratu ta kira awaya? nayi mamaki wlh, matar tana burgeni bata ɗaukar raini, akwai harkar arziƙi.
Ta saki baki sai sambatu take yi, Kumfar Jikinta duk ta bushe har ƙasan tiles ruwan ke zuba, sautin dariyar Aneelerh ne Ya fargar da ita, da sauri ta jefa wayar saman mattress din, ta ruga da gudu ta faɗa toilet tana dariya.
Daƙyar Aneeleeh ta samu ta tsagaita da yin dariyar. Ta ɗago da kanta daga jikin pillow ta jingina bayan jikin head board.
“Aneelerh” muryar Mamie ce ta ratsa kunnanta, zumbur ta sauko daga saman gadon ta nufi kofar ɗakin, shigowa ɗakin Mamie Ta yi suka ci karo da ita”oh dama kina anan? Inata kiranki na duba ko’ina ban ganki ba” Aneelerh na murmushi tace”mamie kema kinsan bani da wurin zuwa a gidan nan inba ɗakin Ƴar uwata zahra ba”
“Okey, ina zahran”?
“Ta shiga toilet yin wanka, amma takusa fitowa
Mamie tace”Okey, idan ta fito, muna jiran ku a dining, ku zo muci abinci”
Ta amsa mata da toh, bayan fitar mami ɗakin, komawa ta yi gefen gadon zahra ta zauna, bada jimawa ba zahra ta fito chest dinta daure da towel, da zolaya Aneelerh tace”Lashe money an fito lafiya”? Tuntsirewa zahra tayi da dariya tana fadin”aunty aneelerh kuɗi duniyane, Dole inso kuɗi, saboda sune maganin talauci, maganin ƙasƙanci da wulaƙanci, idan kina da kuɗi kin fi ƙarfin raini wlh, girmama ki za’a dinga yi kamar wata basarakiya, taya mutum bazai so kuɗi ba? Yanzu fa ko a dangi masu kuɗi sune masu faɗa aji, idan baka da kuɗi toh baka da banbanci da Allon bango”
Fashewa Aneeleeh tayi da dariya, zahra ta zaƙe sai kora mata jawabi ta ke yi dangane da kuɗi.
“Zahra wasu kuɗinfa ba alkhairi bane, suna kai mutun ga shagalar duniya har ya halaka”
“Aunty Aneelerh, nima ai bana roƙon Allah yabani kuɗi kaitsaye batare da nace Allah yabani masu albarka ba, kuma ni burina inyi arziƙi don al’umar annabi su amfana da ni, Ina kwaɗayin inga na taimaki marasa ƙarfi....”.
“Zahra Allah ya dubi kyakkyawar niyarki, inayi maki fatan Alkhairi”
“Ameen auntyna”
Shaf shaf ta kammala shiryawa, cikin riga da skirt, ta dawo gefen Aneeleerh ta zauna bayan ta ɗauki wayarta
“Ki tashi muje muci abinci, su mamie suna jiran mu a dining”
“Inaso ne in fara turama aunty saratu list na abunda mukeyi, zaki Iya zuwa kada su ji mu shiru” miƙewa Aneelerh tayi daga gefen gadon ta fuce daga ɗakin.
Through text message ta tura mata saƙon kamar haka
Here’s a list of services that “Zahra’s World of Beauty” could offer:
- Bridal makeup and hairstyling
- Event planning and decoration
- Haircuts, color, and styling
- Manicures and pedicures
- Facials and skin care treatments
- Massage and body treatments
- Waxing and other hair removal services.
Bayan ta kammala rubuta sakon a ƙalla saida ta maimaita shi yayi sau ashirin gudun kada ace tayi kuskure kafin ta tura mata, fuskarta ɗauke da murmushi ta ajiye wayar saman pillow, ta miƙe ta nufi falo domin Yin breakfast, fatanta Allah yasa Hajiya saratu ta mayar mata da martanin saƙon da wuri, taci buri sosai akan zuwa estate dinsu, ko dan ta haɗu da Owais idan Allah yasa lokacin ya dawo ƙasar.
*KURKUKUN ƘADDARA*
*AN YANKA TA TASHI☠️👹*
Babban ɗakin tarone mai girman gaske, wanda akeyiwa laƙabi da fadar matsafa, Mallakin shuwagabannin kurkukun ƙaddara, ta ko’ina manya manyan matsafane maƙil acikin fadar, zazzaune saman kujeru dake a jere tsakiyar fadar, kowannansu yana sanye cikin shiga ta baƙaƙen dogayen riguna masu huluna, sunyi 6adda kama ta yadda mutun bazai ta6a Iya ganin koda ziririn gashin kansu bane, Hannayensu da ƙafafuwansu baƙaƙen safunane, Yayin da fuskokinsu sun sanya masu mask me suffar ƙwarangwal gwanin ban tsoro, saƙo da lungu ta fadar, Wasu Gabza gabzan giants ne daga masu ƙaramin miƙami har izuwa manyansu masu star uku a gaban kakinsu, wata irin ƙira garesu mai matuƙar ruɗarwa, rikitarwa da razanarwa da kuma tsoratarwa, kallonsu kaɗai zai Iyasa zuciyar mutun ta buga, Ga tsawo da Allah yayi masu tun daga kan tsayuwarsu zaka tabbatar babu ɗigon imani akansu.
Daga can saman karagar fadar, wasu jigunannun arm chairs ne guda shidda ƴan ubansu, mutane shiddan dake zaune saman kujerun dogayen rigunane launin jajaye na maza a jikinsu masu huluna, baka ta6a Iya tantance suffarsu saboda sun 6oye ko’ina na jikinsu, hannyensu na ruƙe da Sanda wadda aka ƙerata da zallar zinari, daga gabansu zungureran teburi ne, samanshi maƙil Yake da kayan ciye ciye dana shaye shaye daga ciki hada Jinin mutun da farfesun naman mutun ga zungura zunguran kwalaban giya, da Kayan marmari nau’i kala kala, da gasasshen nama na dabbobi daban daban.
Komai na fadar matsafan tun daga kan ƙofofi da tagogi da fentinta da jan carpet din dake shimfiɗe ƙasanta, gaba ɗaya Launin baƙi da Ja ne, saman rufin fadar wasu haɗaɗɗun fitilune masu haskaka cikinta.
Zanunnukan dake a jikin bangon fadar, na kan ƙwarangwal ne, da yatsun hannun shaiɗanu masu akaifu zaƙo zaƙo da sauran zanunnuka masu ban tsoro.
Daga gefe ɗaya tacan 6angaren da Arm chairs din nan suke Tanƙameman madubine wanda suke Kira da Allon tsafi, gaba ɗaya Hankalin matsafan yana akan Allon tsafin nasu, fadar tayi tsit tamkar mutuwa ta gifta, ga dukkan alamu wani abu suke kallo wanda yai silar ɗauke masu hankulansu..........
(Nima kuma na ɗauke alƙalamina)
*Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_~*BossLadiesWriters*~_
_*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_
~Middle step~
_The Prisoners E21🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
A ƙalla sun shafe mintuna suna kallon Allon tsafin, ga dukkan alamu sun girgiza da ganin abun da idanuwan su ke gane masu, Hankulan su sun yi matuƙar tashi, abun ya yi mugun ɗaure masu kai, bakomai bane suke kallo acikin Allon tsafin face Garkuwar kurkuku tare da Angel, duk wani motsinsu akan idonsu tamkar video haka suke ganinsu, lokaci ɗaya Allon tsafin yayi duhu hoton fuskokin su ya 6ace.
Kowan nan su ya sauke Ajiyar zuciya, sun natsu suna jiran jin bayani daga bakunan shuwagaban nin su.
Ɗaya daga cikinsu ne yai gyaran murya, da wata irin kakkausar murya mai sautin gaske tamkar bata mutun ba, ya soma Yin magana Cikin harshen su na shahararrun matsafa ni kuma ina fassara maku.
“Wannan ne Karo na farko da muka yi babban kuskure arayuwar mu, wanda idan bamu miƙe tsaye mun nema ma kanmu mafita ba, to tabbas za’ayi nasara akan mu, Ko a tarihi ba’a ta6a samun prisoners ɗin da suka tsira daga kurkukun ƙaddara ba, su ne na farko kuma sune na ƙarshe, da farko sunyi nasarar ƙetare kurkuku da taimakon Garkuwarmu, Na biyu sun ku6uta daga dajin evil forest da taimakon shi, Babu wani mahaluƙin da ya isa ya iya ƙetare kurkuku da dajin evil forest salin alin ba tare da ya Rasa ranshi ba, amma saboda suna atare da garkuwar prison mun rasa cin galaba akansu saboda mu kanmu bamu isa mu Iya ja da shi ba, babu wata muguwar halittar data Isa ta tunkaresu muddin Yana atare da su, rashin baccin da baiyi ba shine Yaja har muka gaza tunkarar su, lokacin da baccin Ya ɗauke shi munyi nasarar yi mashi abunda ya dawo gare mu sai dai wani abun al’ajabi ya ku6uta daga hannunmu Ya koma ma gangar jikin shi, kamar yadda kuka gani a allon tsafin mu, shin me ya jawo hakan”? Yai tambayar yayin da yake gyaran zaman shi.
Mutumin dake a gefenshi, Ya ɗaura da cewa”Yarinyar da ke atare da shi itace silar komai, kamar yadda yazo mana a allon tsafin mu, Cewa itace za ta yi silar tarwatsa tarihin kurkukun ƙaddara, gangancin da mu ka yi shine Haɗa su wuri ɗaya da garkuwar mu, sakamakon shaƙuwar da sukayi a tsakanin su, taja shi ga faɗawa tarkon sonta, mu kan mu bamu ta6a tsammanin Garkuwar prison zai Iya kamuwa da matsanancin so irin haka ba” dakatawa yai da yin maganar yana motsa yatsun hannunsa, kafin ya cigaba da cewa
“Sai dai har yanzu bamu rasa power ɗinmu ba, Garkuwa namu ne har abada, mu ke ruƙe da masarrafin da zamu Iya sarrafa linzamin shi, mu kaɗai ne mu ke da iko da shi, ba zamu ta6a yin danasanin Ɗaura shi amatsayin magajin kurkukun ƙaddara ba, kuskure ɗaya da muka tabka shine sakacin da mu ka yi da har ya samu nasarar guduwa daga kurkuku, Ni ban damu da sauran Yaran da suka ku6uta ba, saboda basu da amfani a wurinmu, mun ci moriyar su, mutun ukun ne sune rauninmu, Na farko Garkuwarmu dole sai da shi za’a Iya Cin galaba akanmu, Na biyu ƙaddarar kurkuku, yarinyar ta fi sauran hatsari tun da har ta Iya Jan hankalin garkuwarmu, wanda nayi imanin da ace babu ƙauna a tsakanin shi da yarinyar ba zai ta6a taimakon sauran ƴan uwan shi don su gudu daga tarkon mu,” Ya faɗa yana mai jan dogon numfashi Ya fetsar da shi, ya cigaba da faɗin “Itace silar komai, kuma itace kaɗai zata Iya sarrafa shi bayan mu, idan kuwa hakan Ya faru zai Iya fallasa mana sirrin mu ya kuma taimaka wurin ruguza kurkukun ƙaddara”! Da ƙarfi Ya ambaci hakan Yana mai nuna fusatar shi.
“Yarinya ta ƙarshe itace bugun zuciyar kurkukun ƙaddara, kamar yadda ya zo mana a allon tsafin mu, idan har muka samu nasarar Cire Zuciyarta daga ƙirjinta zamu samu ƙarfin Iko fiye da wanda muke da shi a yanzu, Ita kuma ƙaddarar kurkuku dole mu dawo da ita cikin mu idan har muna son ta zamar mana ƙaddara mai kyau, barin ta awaje shi zaisa ta zamto mummunar ƙaddara agare mu” Tamkar mayunwacin zaki haka yake kora masu jawabi yana fitar da huci.
Bayan ya rufe baki Na gefen shi ya soma magana da wata irin murya ta dattawa waɗanda suka Shahara a fagen zalunci.
“Tun fil azal, Banso Muka damƙa amanar mu ga tsohuwa tamira ba, dama tun lokacin Sai da na musa akan hakan, Ni dama nasani Jinin Habibullah ba zasu ta6a zama amintattun mu ba, sai gashi sun yaudaremu sunci amanar kurkuku, sun kashe mana Zafreen ɗaya daga cikin shuwagabannin mu, babu wanda ya ta6a tsammanin zasu Ci amanar mu ita da ɗanta Salsabeel, sai da suka bari mun basu yarda mu su kuma suka butulce mana, haƙiƙa Nayi takaicin
Kamar wani ƙaramin yaro haka take tarairayarshi, da hannu ta dinga bashi grilled chicken din yana ci, Idan ka kallesu a yadda suke zaune sai ka sha mamaki saboda girman da yai ma Angel, Bata wuci Ya lullu6eta da faffaɗan kirjinshi ba, amma saboda sabo da juna, da kuma shaƙuwa da ƙaunar dake a tsakaninsu bata ganin girman shi.
Ɗaya daga cikin abunda ke burgeta, idan ta tura mashi abincin abaki yadda yake motsa tattausan full lips nasa da kuma motsin Adam’s apple dinsa, komai nashi ƙayatar da ita yake yi kamar yarda itama ta ke burge shi, a ƙarshe sai suka koma suna feeding din junansu tana bashi abaki, Shima yana bata abaki.
Abunda basu sani ba, Har safiya tayi gari ya ware babu wanda Ya lura a cikinsu, tuni sun kammala cin abincin, sun shagala suna kallon juna.
*ABUJA NIGERIA A GIDAN ƊAN IYA*
A round ƙarfe 10 na safe agogon Nigeria, tun bayan kammala sallar Asubahi da ta koma bacci bata farkaba ba saboda Jiya sun sha fira da Aneelerh sun kusa raba dare kamar ƴa’ƴan Aljanu, shiyasa yau take ta sharar baccinta kamar matatta, ta wawware ƙafafuwanta saman mattress, ta saki baki da hanci, sai jan minshari ta ke yi kamar ragon sallah, daɗin bacci hada yawu a gefen bakinta, Gajeran wandone a jikinta sai ƴar farar half vest data zura, sumar kanta babu kitso zallar gashinta a hargitse ba gyara.
Tayi zurfi acikin baccinta, Wayarta dake ajiye saman side drawer ta buga uban ringing, Babu alamun zata farka har kiran ya katse, wani ya kuma shigowa, sautin ya cika ko’ina banda kunnan zahra dake yin bacci.
Shigowa cikin ɗakin Aneelerh Tayi, jikinta asanye da doguwar riga, ta yi rolling mayafi akanta, kaitsaye ta nufi drawer din ta miƙa hannu ta ɗauki wayar tana faɗin”Allah ya shirya zahra, wannan bacci haka kamar matatta, ana ta kiran mutun awaya wama ya sani ko arziƙi ne ke kiranta...” Waro ido waje aneeleeh tayi ganin sunan mutumin dake kiran Aneelerh, Ya fito 6aro 6aro saman screen din, bakowa bace face Hajiya Saratu Obinna, Jiki na rawa ta haye saman gadon takai hannu tana bubbuga ƙafar zahra”banza, ki tashi arziƙine ke kiran ki, zahra ki tashi kada muyi asara” yamutsa fuska zahra tayi muryarta kamar ta mashayin giya ta furta”dallah wanene ke takuramin, ni a ƙyaleni inyi bacci na, ba dama mutun ya ɗan kwanta ya runtsa sai an samu wani uban anacin ya tada shi’
cikin magagin bacci take yin sambatun. kiran har yayi rejecting, zuƙunnawa Aneeleeh tayi saitin kunnan ta da karfi ta furta”Shashasha Hajiya saratu obinna ce ke Kira” A haukace Zahra ta zabura Ta miƙe tana faman mutsustsuke ido, A fujajen take fadin”Wai dagaske? Ina wayar? Gaba ɗaya tabi ta ruɗe jin an ambaci sunan Hajiya saratu obinna, sai faman zazzare ido take yi.
Miƙa mata wayar Aneelerh ta yi “yo har yayi rejecting, Tun ɗazu nake ta ƙoƙarin tada ki, Kinƙi ki farka gashi yanzu kin ja mana asara....” bubbuga katifa zahra tayi da hannu tsabar takaici hada hawaye akan fuskarta”Aunty aneelerh, kin karyamin jari, meyasa da kika tada ni naƙi tashi baki shiga toilet kin ciko bokiti da ruwa kin watsa mun ba”?
Babu wasa akan face dinta ta yi maganar, Sakin Baki aneeleeh tayi tana kallonta
Zahra ta ci gaba da yin kuka tana faɗin “Nashiga uku, wayyo Allahna, ni wlh bakiyi min adalci ba, wama ya sani ko kujerar Hajji za’a raba mana,” sosai ta fashe ma Aneelerh da kuka. Lamarin ya ɗaure mata kai, ta rasa ina zahra da mahboob suka gado shegen son kuɗi, sai dai tafi tunanin ta 6angaren mahaifinsu ne.
Lallashinta ta soma yi”Kiyi hakuri sister kukan Ya isa haka, wata’kil ta ƙara Kiran ki,” cikin shessheƙar kuka tace”taya za’ae ta sake kira na, bakisan halin masu kuɗin nan ba, basu ɗaukar raini, za ta yi tsammanin dagangan naƙi ɗaga kiranta, Wayyo Allahna aunty Aneelerh, nayi wa arziki ƙulli, har ƙiyamil laili nayi akan Allah ya bude mun kofofin samu, da kuma miji nagari a sabuwar shekarar da zamu shiga...” dariyace kumshe abakin Aneelerh.
Dafa kafaɗarta tayi”Sorry My lovely sis, Yanzu abunda za’ae, Ki kira Layinta mu gani ko zata ɗaga” kar6ar wayar tayi daga hannun Aneelerh, Yatsun hannunta har kerma sukeyi sam babu natsuwa, kiran layin ta soma Yi, tamkar zata fashe da kuka ta kalli Aneelerh”line busy, dama ni nasani, wlh basa ɗaga kira, idan ba su suka kira mutun ba”
Aneelerh tace”mu ɗan ƙara haƙuri, zuwa anjima sai mu ƙara jaraba kiran layinta, yanzu ki tashi ki shiga toilet ki ki gyara jikin ki, zan Jiraki anan,” cikin shessheƙar kuka ta amsa da toh, kafin ta sauko daga saman gadon ta nufi toilet ta shige.
Bayan shigarta da mintuna biyar Aneeleeh tana zaune tsakiyar gadon tana jiran fitowarta, zuciyarta acunkushe take da tunanin baby junaid ɗinta tayi kewarshi, tun shekaran Jiya Uncle abdallah da hajiya adama suka koma gidansu, anyi rabuwar mutunci sun nemi alfarma Junaid ya zauna wurinsu na tsawon 2 weeks, zai dawo gida, sannan duk weekend za’a dinga kai masu shi, yanzu haka yana acan gidan nasu, tsawon kwana uku da yayi acan kullum ne sai ya matsa masu akan su kira mashi Mommyn nasa, wani lokacin tun kafin ta farka daga bacci kiran su ke shigowa wayarta saboda jarabar junaid.
Tayi zurfi cikin tunaninta, Wayar Zahra ta soma yin ringing, Kafin ta wurga idonta kan inda zahra ta ajiye wayar saman drawer, da ƙarfi taji sautin buɗe ƙofar toilet, Ras taji gabanta Ya fadi ganin zahra ta watso aguje, jikinta duk kumfa daga ita sai gajeran towel tayi ɗaurin gaba da shi, hatta fuskarta kumfar sabulu ce, miƙa hannu tayi ta rurumi wayar, tsabar zumuɗin ganin wanene ke kiranta, fatanta Allah yasa hajiya saratu obinna ce, cikin sa’a idonta yai mata nuni da sunanta akan screen, sai ƙoƙarin ɗaga kiran takeyi kumfar hannunta ta hana touching din yin aiki, kamar zata fashe da kuka, sai da aneelerh ta taimaka mata wurin answer mata call din tukunna ta samu natsuwa, a Hands free ta sanya kiran don suji me zata je
Cikin girmamawa zahra tayi mata sallama”Assalamu alaikum” kamar tana agabanta.
On the other hand sautin muryar hajiya saratu ya karaɗe kunnuwansu
“Wa’alaikum salam”
“Ina kwana hajiya, fatan kun tashi Lafiya, wlh bana a kusa da wayar ne, kunata kira bansamu damar ɗagawa ba, da yake na ɗan shiga toilet ne”
Aneeleeh dake zaune saman gado, dariyace ta kubce mata da sauri ta cakumi pillow ta toshe fuskarta dashi don kada sautin Ya fita, bakomai ne ya sanyata yin dariya ba face yadda zahara keyin waya kamar ƴar maroƙa, ga kumfa a jikinta.
“Bawani abu ai, nayi maki uziri, dalilin dayasa na kira layin ki, last time da kukayi mana decoration aikin ku ya yi mana kyau, muna so za’a ƙara Yi mana wani next week, sannan muna so za’a fidda mana anko wanda zai dace damu”
Da sauri zahra ta kar6e da cewa”in sha Allah hajiya komai kuke so za’ayi yadda ya dace, hada ƙunshi da kitso idan akwai mai buƙata”
Hajiya saratu tace”okey, You can send me the list of your services and I’ll add what I want to the list, through text message zaki tura min”
“Toh hajiya in sha Allah, Mun gode sosai, da kiranmu da ku kayi, kuma in sha Allah zaku same mu masu biyayya ga duk abunda kuke so,” bayan sunyi sallama da Hajiya saratu, Zahra ta sauke nauyayyar Ajiyar zuciya, Ta fasa ihu Tana faɗin”Alhamdulillah! lokacin Yin arziki na Yayi, wai yau ni ce Aunty saratu ta kira awaya? nayi mamaki wlh, matar tana burgeni bata ɗaukar raini, akwai harkar arziƙi.
Ta saki baki sai sambatu take yi, Kumfar Jikinta duk ta bushe har ƙasan tiles ruwan ke zuba, sautin dariyar Aneelerh ne Ya fargar da ita, da sauri ta jefa wayar saman mattress din, ta ruga da gudu ta faɗa toilet tana dariya.
Daƙyar Aneeleeh ta samu ta tsagaita da yin dariyar. Ta ɗago da kanta daga jikin pillow ta jingina bayan jikin head board.
“Aneelerh” muryar Mamie ce ta ratsa kunnanta, zumbur ta sauko daga saman gadon ta nufi kofar ɗakin, shigowa ɗakin Mamie Ta yi suka ci karo da ita”oh dama kina anan? Inata kiranki na duba ko’ina ban ganki ba” Aneelerh na murmushi tace”mamie kema kinsan bani da wurin zuwa a gidan nan inba ɗakin Ƴar uwata zahra ba”
“Okey, ina zahran”?
“Ta shiga toilet yin wanka, amma takusa fitowa
Mamie tace”Okey, idan ta fito, muna jiran ku a dining, ku zo muci abinci”
Ta amsa mata da toh, bayan fitar mami ɗakin, komawa ta yi gefen gadon zahra ta zauna, bada jimawa ba zahra ta fito chest dinta daure da towel, da zolaya Aneelerh tace”Lashe money an fito lafiya”? Tuntsirewa zahra tayi da dariya tana fadin”aunty aneelerh kuɗi duniyane, Dole inso kuɗi, saboda sune maganin talauci, maganin ƙasƙanci da wulaƙanci, idan kina da kuɗi kin fi ƙarfin raini wlh, girmama ki za’a dinga yi kamar wata basarakiya, taya mutum bazai so kuɗi ba? Yanzu fa ko a dangi masu kuɗi sune masu faɗa aji, idan baka da kuɗi toh baka da banbanci da Allon bango”
Fashewa Aneeleeh tayi da dariya, zahra ta zaƙe sai kora mata jawabi ta ke yi dangane da kuɗi.
“Zahra wasu kuɗinfa ba alkhairi bane, suna kai mutun ga shagalar duniya har ya halaka”
“Aunty Aneelerh, nima ai bana roƙon Allah yabani kuɗi kaitsaye batare da nace Allah yabani masu albarka ba, kuma ni burina inyi arziƙi don al’umar annabi su amfana da ni, Ina kwaɗayin inga na taimaki marasa ƙarfi....”.
“Zahra Allah ya dubi kyakkyawar niyarki, inayi maki fatan Alkhairi”
“Ameen auntyna”
Shaf shaf ta kammala shiryawa, cikin riga da skirt, ta dawo gefen Aneeleerh ta zauna bayan ta ɗauki wayarta
“Ki tashi muje muci abinci, su mamie suna jiran mu a dining”
“Inaso ne in fara turama aunty saratu list na abunda mukeyi, zaki Iya zuwa kada su ji mu shiru” miƙewa Aneelerh tayi daga gefen gadon ta fuce daga ɗakin.
Through text message ta tura mata saƙon kamar haka
Here’s a list of services that “Zahra’s World of Beauty” could offer:
- Bridal makeup and hairstyling
- Event planning and decoration
- Haircuts, color, and styling
- Manicures and pedicures
- Facials and skin care treatments
- Massage and body treatments
- Waxing and other hair removal services.
Bayan ta kammala rubuta sakon a ƙalla saida ta maimaita shi yayi sau ashirin gudun kada ace tayi kuskure kafin ta tura mata, fuskarta ɗauke da murmushi ta ajiye wayar saman pillow, ta miƙe ta nufi falo domin Yin breakfast, fatanta Allah yasa Hajiya saratu ta mayar mata da martanin saƙon da wuri, taci buri sosai akan zuwa estate dinsu, ko dan ta haɗu da Owais idan Allah yasa lokacin ya dawo ƙasar.
*KURKUKUN ƘADDARA*
*AN YANKA TA TASHI☠️👹*
Babban ɗakin tarone mai girman gaske, wanda akeyiwa laƙabi da fadar matsafa, Mallakin shuwagabannin kurkukun ƙaddara, ta ko’ina manya manyan matsafane maƙil acikin fadar, zazzaune saman kujeru dake a jere tsakiyar fadar, kowannansu yana sanye cikin shiga ta baƙaƙen dogayen riguna masu huluna, sunyi 6adda kama ta yadda mutun bazai ta6a Iya ganin koda ziririn gashin kansu bane, Hannayensu da ƙafafuwansu baƙaƙen safunane, Yayin da fuskokinsu sun sanya masu mask me suffar ƙwarangwal gwanin ban tsoro, saƙo da lungu ta fadar, Wasu Gabza gabzan giants ne daga masu ƙaramin miƙami har izuwa manyansu masu star uku a gaban kakinsu, wata irin ƙira garesu mai matuƙar ruɗarwa, rikitarwa da razanarwa da kuma tsoratarwa, kallonsu kaɗai zai Iyasa zuciyar mutun ta buga, Ga tsawo da Allah yayi masu tun daga kan tsayuwarsu zaka tabbatar babu ɗigon imani akansu.
Daga can saman karagar fadar, wasu jigunannun arm chairs ne guda shidda ƴan ubansu, mutane shiddan dake zaune saman kujerun dogayen rigunane launin jajaye na maza a jikinsu masu huluna, baka ta6a Iya tantance suffarsu saboda sun 6oye ko’ina na jikinsu, hannyensu na ruƙe da Sanda wadda aka ƙerata da zallar zinari, daga gabansu zungureran teburi ne, samanshi maƙil Yake da kayan ciye ciye dana shaye shaye daga ciki hada Jinin mutun da farfesun naman mutun ga zungura zunguran kwalaban giya, da Kayan marmari nau’i kala kala, da gasasshen nama na dabbobi daban daban.
Komai na fadar matsafan tun daga kan ƙofofi da tagogi da fentinta da jan carpet din dake shimfiɗe ƙasanta, gaba ɗaya Launin baƙi da Ja ne, saman rufin fadar wasu haɗaɗɗun fitilune masu haskaka cikinta.
Zanunnukan dake a jikin bangon fadar, na kan ƙwarangwal ne, da yatsun hannun shaiɗanu masu akaifu zaƙo zaƙo da sauran zanunnuka masu ban tsoro.
Daga gefe ɗaya tacan 6angaren da Arm chairs din nan suke Tanƙameman madubine wanda suke Kira da Allon tsafi, gaba ɗaya Hankalin matsafan yana akan Allon tsafin nasu, fadar tayi tsit tamkar mutuwa ta gifta, ga dukkan alamu wani abu suke kallo wanda yai silar ɗauke masu hankulansu..........
(Nima kuma na ɗauke alƙalamina)
*Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_~*BossLadiesWriters*~_
_*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_
~Middle step~
_The Prisoners E21🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
A ƙalla sun shafe mintuna suna kallon Allon tsafin, ga dukkan alamu sun girgiza da ganin abun da idanuwan su ke gane masu, Hankulan su sun yi matuƙar tashi, abun ya yi mugun ɗaure masu kai, bakomai bane suke kallo acikin Allon tsafin face Garkuwar kurkuku tare da Angel, duk wani motsinsu akan idonsu tamkar video haka suke ganinsu, lokaci ɗaya Allon tsafin yayi duhu hoton fuskokin su ya 6ace.
Kowan nan su ya sauke Ajiyar zuciya, sun natsu suna jiran jin bayani daga bakunan shuwagaban nin su.
Ɗaya daga cikinsu ne yai gyaran murya, da wata irin kakkausar murya mai sautin gaske tamkar bata mutun ba, ya soma Yin magana Cikin harshen su na shahararrun matsafa ni kuma ina fassara maku.
“Wannan ne Karo na farko da muka yi babban kuskure arayuwar mu, wanda idan bamu miƙe tsaye mun nema ma kanmu mafita ba, to tabbas za’ayi nasara akan mu, Ko a tarihi ba’a ta6a samun prisoners ɗin da suka tsira daga kurkukun ƙaddara ba, su ne na farko kuma sune na ƙarshe, da farko sunyi nasarar ƙetare kurkuku da taimakon Garkuwarmu, Na biyu sun ku6uta daga dajin evil forest da taimakon shi, Babu wani mahaluƙin da ya isa ya iya ƙetare kurkuku da dajin evil forest salin alin ba tare da ya Rasa ranshi ba, amma saboda suna atare da garkuwar prison mun rasa cin galaba akansu saboda mu kanmu bamu isa mu Iya ja da shi ba, babu wata muguwar halittar data Isa ta tunkaresu muddin Yana atare da su, rashin baccin da baiyi ba shine Yaja har muka gaza tunkarar su, lokacin da baccin Ya ɗauke shi munyi nasarar yi mashi abunda ya dawo gare mu sai dai wani abun al’ajabi ya ku6uta daga hannunmu Ya koma ma gangar jikin shi, kamar yadda kuka gani a allon tsafin mu, shin me ya jawo hakan”? Yai tambayar yayin da yake gyaran zaman shi.
Mutumin dake a gefenshi, Ya ɗaura da cewa”Yarinyar da ke atare da shi itace silar komai, kamar yadda yazo mana a allon tsafin mu, Cewa itace za ta yi silar tarwatsa tarihin kurkukun ƙaddara, gangancin da mu ka yi shine Haɗa su wuri ɗaya da garkuwar mu, sakamakon shaƙuwar da sukayi a tsakanin su, taja shi ga faɗawa tarkon sonta, mu kan mu bamu ta6a tsammanin Garkuwar prison zai Iya kamuwa da matsanancin so irin haka ba” dakatawa yai da yin maganar yana motsa yatsun hannunsa, kafin ya cigaba da cewa
“Sai dai har yanzu bamu rasa power ɗinmu ba, Garkuwa namu ne har abada, mu ke ruƙe da masarrafin da zamu Iya sarrafa linzamin shi, mu kaɗai ne mu ke da iko da shi, ba zamu ta6a yin danasanin Ɗaura shi amatsayin magajin kurkukun ƙaddara ba, kuskure ɗaya da muka tabka shine sakacin da mu ka yi da har ya samu nasarar guduwa daga kurkuku, Ni ban damu da sauran Yaran da suka ku6uta ba, saboda basu da amfani a wurinmu, mun ci moriyar su, mutun ukun ne sune rauninmu, Na farko Garkuwarmu dole sai da shi za’a Iya Cin galaba akanmu, Na biyu ƙaddarar kurkuku, yarinyar ta fi sauran hatsari tun da har ta Iya Jan hankalin garkuwarmu, wanda nayi imanin da ace babu ƙauna a tsakanin shi da yarinyar ba zai ta6a taimakon sauran ƴan uwan shi don su gudu daga tarkon mu,” Ya faɗa yana mai jan dogon numfashi Ya fetsar da shi, ya cigaba da faɗin “Itace silar komai, kuma itace kaɗai zata Iya sarrafa shi bayan mu, idan kuwa hakan Ya faru zai Iya fallasa mana sirrin mu ya kuma taimaka wurin ruguza kurkukun ƙaddara”! Da ƙarfi Ya ambaci hakan Yana mai nuna fusatar shi.
“Yarinya ta ƙarshe itace bugun zuciyar kurkukun ƙaddara, kamar yadda ya zo mana a allon tsafin mu, idan har muka samu nasarar Cire Zuciyarta daga ƙirjinta zamu samu ƙarfin Iko fiye da wanda muke da shi a yanzu, Ita kuma ƙaddarar kurkuku dole mu dawo da ita cikin mu idan har muna son ta zamar mana ƙaddara mai kyau, barin ta awaje shi zaisa ta zamto mummunar ƙaddara agare mu” Tamkar mayunwacin zaki haka yake kora masu jawabi yana fitar da huci.
Bayan ya rufe baki Na gefen shi ya soma magana da wata irin murya ta dattawa waɗanda suka Shahara a fagen zalunci.
“Tun fil azal, Banso Muka damƙa amanar mu ga tsohuwa tamira ba, dama tun lokacin Sai da na musa akan hakan, Ni dama nasani Jinin Habibullah ba zasu ta6a zama amintattun mu ba, sai gashi sun yaudaremu sunci amanar kurkuku, sun kashe mana Zafreen ɗaya daga cikin shuwagabannin mu, babu wanda ya ta6a tsammanin zasu Ci amanar mu ita da ɗanta Salsabeel, sai da suka bari mun basu yarda mu su kuma suka butulce mana, haƙiƙa Nayi takaicin