Showing 195001 words to 198000 words out of 250533 words
Chapter 66 - Kurkukun Kaddara Book 2 Middle Steps By Boss Bature.
ya furta hakan yasa ta watsa da gudu cikin falon bata nufi ko’ina ba sai saman benan da zai sadata da macijin, da gudu big guy yabi bayanta, cikin shessheƙar kuka take fadin”dan Allah kada ku kashe shi, wallahi ba maciji bane, ɗan uwanane danish”
damƙo hannunta big guy yai, tadinga kiciniyar ƙwace kanta ranta amtuƙar 6ace ta soma zazzaga masu masifa tana fadin”wallahi babu inda zanje, nace maku dan uwanane, ku ƙyale shi ku daina harbinshi tunda bai cutar da kowaba, wayyo Allah na danish ɗina”
Sautin koke kokenta Ya cika gidan, hatta sauran mazauna gidan baba obie saida suka jiyota, ɗaya bayan ɗaya masu aikin gidan suke fitowa daga makwancinsu, Pravin bai jima da shiga ɗakin hajjaty ba ya jiyo sautin Kukan mutun agidan, sai gashi ya fito hajjaty na abiye dashi, Hajiya saratu kuwa jin sautin kukan Yasa ta fito daga ɗaki ta shigo falon, koda tayi arba da unaisa ga jami’ae da kuma shirgegen macijin dake bin bango, hannayenta biyu ta ɗaura akai tana ambaton Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un! Maciji acikin gidan nan? Wacece wancan Yarinyar? Ya akai ya shigo? Aruɗe ta furta hakan
Kowa Ya shiga ruɗani, Jami’an sun dage sai antaya mashi Harsashi suke Yi, Ganin suna ƙoƙarin yi mashi illa yasa Unaisa tayi wani irin kukan kura, ta bangaje big guy da iya ƙarfinta na ƙarshe, ta haura sama da gudun gaske, duk yadda suka so su kawar da ita sun gaza yin hakan har saida tayi nasarar ƙarasawa inda yake, tsawa suka dinga dakata mata suna korarta daga gabanshi amma taƙi matsawa, macijin yabi ya nannaɗe kanshi Ya dunƙule waje guda saman floor, lullu6e shi tayi da bazar rigarta, tana kuka tana fadin”danish dan Allah ka saurareni, ka taimaki rayuwata, bana so na rasa ka, ka canza halittarka ka tabbatar masu da cewa kai mutunne ba maciji ba, idan ba haka ba zasu Iya kashe mun kai” cikin jin ƙunar rai take Furta maganar, ta ƙanƙameshi kamar zata maida shi jikinta, jami’an sun natsu suna kallon ikon Allah, Hajiya saratu sarkin tsoro sai faman baza idanuwanta take Yi, baba obie Yana la6e bayan Mai girma sharafuddeen, Senate Ya ruƙo hannunshi dake tayin kerma, A hankali Hateem Ya zare farin glass din dake asaman fuskarshi Ya ruƙe ahannunshi, komai ke faruwa akan idanuwanshi, tamkar amafarki suke kallon lamarin, an rasa wanda zai janyeta daga jikinshi. Abunda ya ɗaure masu kai babu alamun macijin zai cutar da ita.
Duk da baya iya furta mata magana, ranta yana bata cewar yana son ya rikiɗa ya koma mutun sai dai ya kasa yin hakan, jikinshi ya ɗau zafi sosai, cikin sanyin murya ta soma yin magana, hawaye naci gaba da wanke fuskarta
“Ɗan uwana rabin raina, dan Allah ka canza halittarka, idan ba haka ba babu wanda zai yarda cewa kai mutunne zasu ci gaba da cutar min dakai” ta faɗa tana ƙara kankameshi a Jikinta.
umarni Owais Ya ba jami’an akan su daina yunƙurin harbinshi, amsa mashi sukayi datoh, ya fadi hakanne saboda ya fara kokwanton mutunne kamar yarda ta faɗi, a faɗace hajiya saratu tace”akan me zaka basu umarnin su daina harbinshi? idan ya cutar da wani fa”? Ko kallo bata ishe shi ba, muryar baba obie Na rawa ya furta”Ku kashe macijin nan, bana son ganinshi, ku kawar mana da shi”
“Baba ka kwantar da hankalinka, Ni na yarda da maganar yarinyar ba maciji bane mutunne” mai girma sharafudden ne yai maganar.
A harzuƙe Obie Yace”tayaya mutun zai zama maciji? hakan bazai ta6a yiwuwa ba, Ni bazan ta6a yarda ba, ku kawar mana dashi kawai, idan baso kuke zuciyata ta buga ba, Ita kuma waccan Yarintar mai kasada ƴar wacece? Ku ɗauke ta mana daga Jikinshi kada ya sare ta”yai maganar yana nuna Unaisah da sandar hannunshi.
Duk yabi ya furgice masu, big guy ne ya kutsa ta cikin jami’an Ya nufeta, muryarshi ƙasa ƙasa tamkar tame Yin raɗa ya furta”Unaisah, ki tashi mu tafi gida, za’a dawo maki dashi” maƙe mashi kafaɗa tayi, la66anta duk sun bushe sun faffashe.
“Babu inda zanje, Ina atare dashi, Idan nayi nesa dashi, ba zaku Iya sarrafashi ba, zai Iya guduwa ya nufi wani wajen” magiya ya dinga yi mata akan ta miƙe amma taƙi tashi, hakan Yasa Chief owais motsawa ya haura saman benan Ya nufe su, Darewa jami’an suka dinga yi suna bashi hanya har ya kaiga ƙarasawa inda suke, faffaɗan tafukan hannaye shi ya ɗaura saman unaisa ya ɗaɗɗagota tare da ɗaurata saman broad shoulder dinshi, juyawar da zaiyi da niyar ya tafi da ita, giant snake din Yai wata irin girgiza da gudun gaske yabi bayan owais daya ɗauketa.
Jami’an suka saita shi da bindiga owais Ya hana su harbeshi yace masu su barshi akwai dalilin dayasa yayi hakan, Yana tafiya macijin Yana bin bayanshi, kasancewar ya ɗaurata saman kafadarshi tana Iya kallon giant snake din daketa ta faman jan ciki Yana nufosu, hawayenta tamkar zasu ƙare muryarta shaƙe take ambaton sunan Danish.
Ganin macijin zai sauko down yasa Hajiya saratu ta watsa da gudu zaninta har yana kwancewa ta ruƙo shi ta nufi hanyar part dinsu aguje ta shiga ɗaki ta datse kofa, tabi tagogi duk ta rufesu, a karshe cikin toilet ta shige tayi locking kanta.
Hankalin baba obie yai matuƙar tashi sai ƙara ƙankame jallabiyar mai girma sharafuddeen yake yi, Hateem kuwa ko kadan baiji tsoron macijin ba, tsabar mamakine Ya hana su furta magana, kowa ya baza ido yana kallon ikon Allah, duk inda owais yai da ita sai macijin yabisu, fucewa yai daga falon Ya nufi motarsu da su ka yi parking dinta abakin entry hall, Ya buɗeta Ya shigar da unaisah aback seat na motar, ya buɗe front seat a mazaunin driver Ya zauna yai mata key, da gudun gaske Ya fusgi motar, ta cikin glass din motar take kallon macijin daketa binsu da ƙarfi Ya daka uban tsalle Ya haura saman motar Yai kwanciyarshi.
Ajiyar zuciya ta sauke ganin yana atare dasu, bai nufi ko’ina ba sai sashen da gidansu yake, ta gate din Baya ya shigar dasu a bakin entry hall chief Yai parking din motar, Ya fito Ya buɗe back seat din Ya cuccu6i unaisah Ya ɗaurata saman kafaɗarshi Ya nufi Babban falo da ita, hankalin shi kwance tamkar baisan da zaman macijin ba, saukowa yai daga saman motar yabi bayansu da gudun gaske yake jan jiki.
Cikin takun sauri Owais Ya haura upstairs da ita, kafin Ya ƙarasa second floor, macijin Ya riga shi isa, wani wawan tsalle ya daka Yabi ta jikin bene Ya faɗo tagabansu, ƙoƙari yake ya nannaɗe ƙafafuwan owais sai dai yakasa yin hakan saboda owais bai bashi damar ruƙe mashi ƙafa ba, sai kakkauce mashi yake Yi, a haka ya ƙarasa bedroom din Danish Ya shiga daga ciki, Ya kwantar da ita saman gado, Shigowa ɗakin macijin Yai yana faman huci kamar zai kai mashi hari, saman gadon Ya haye Yana faman bin mattress din. Owais dake a tsaye ya goya hannayenshi saman wide chest dinsa, Ya natsu yana kallonsu.
Giant snake din Ya nannaɗe jikinshi agaban unaisah ya ɗago da kanshi Yana kallon owais, duk a tunaninshi wani abu zaiyima unaisah shiyasa Yabiyosu, shi kuma owais daya fahinci Baya iya cutar da ita shiyasa yai dabarar daukota sai gashi yaci nasara akanshi”
Fitowa yai daga ɗakin Yaja ƙofar Yai locking dinta, Yabarsu su biyu adakin Ya nufi down.
Hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba, zuciyarta sai dukan uku uku takeyi, tsananin tsorone Ya kamata, amma saboda ƙaunar da take yi mashi takasa motsawa, duk tasha jinin jikinta, muryarta na rawa ta furta sunan shi”danish ɗina” juyowa macijin yai da kanshi Yana dubanta, jikinta na kerma saboda ƙarfin hali ahaka ta miƙa mashi hannunta, jan jiki ya somayi yana nufarta, saman kirjinta ya nannaɗe kanshi, wani irin sanyi taji ya ratsata, lokaci ɗaya tadaina jin bugun da ƙirjinta keyi mata, asaman fatar shi ta ɗaura hannunta, a hankali take shafashi duk don ta kwantar mashi da hankalinshi, ita kaɗaice zata Iya fahimtarshi a halin da yake ciki.
Walking quickly chief Ya nufi Ƙofar fita daga part din, Kafin Ya ƙarasa Muryar Boss man ta katse mashi hanzarinshi”yalla6ai” cak Ya tsaya da tafiya ya waiwayo yana dubansu, su biyune suka fara shigowa shida big guy, daga bayansu sauran jami’an isod ne da suka Biyosu, hankalinsu duk ba a kwance yake ba, musamman Boss man da yaji labarin abakin big guy shigowar shi kenan gidan duk wannan budurin da akeyi baida masaniya yana a part dinsa.
Fuskar chief owais ta canza zuwa yanayi na damuwa.
“Yalla6ai Ina macijin yake”? Big guy ne ya jefa mashi tambayar.
Daƙyar Ya iya buɗe baki Ya furta”yana adakin shi, tare da yarinyar na kullesu” waro ido waje sukayi suna kallon shi
Muryar boss man na rawa ya furta”kana nufin tare da Angel ka rufe su aɗaki? Idan ya cutar da ita fa”? Gaba ɗaya yabi ya ruɗe.
Big guy yace”ka kwantar da hankalinka, Ni na fahimci hikimar yin hakan, da ace bai daukota ba macijin bazai dawo gidan ba, bamusan inda zai shiga ba, amma yanzu kaga mun kulleshi aɗaki ta dalilinta”
Cikin rashin fahimtar kalaman big guy Boss man yace”bazai yiwu ba, Ƴata fa aka kulle aɗaki ɗaya da maciji, Idan ya kashe min itafa” dafa kafaɗarshi Owais Yai da hannu ɗaya”kadaina kiranshi maciji, mutunne, bazan iya yin abunda zai cutar maka da ƴarka ba, Kamar yarda kake jinta nima haka nake jinta, fatan ka fahimce ni” gyada kai Yai still hankalinshi bai kwanta ba.
“A wani daki ka kulle su”?
Atakaice owais Ya furta”A dakin shi” jiki na rawa boss man Ya watsa da gudu ya nufi upstair.
Chief owais Ya maida dubanshi ga Big guy, “Things are starting to get out of control, and I don’t know what to do now. But I want to see his brother, maybe he can control him. kaje ka zo dashi” ya faɗa in a cool voice, amsa mashi yai da toh, da sauri Ya juya ya fuce daga ɗakin, Kallon sauran jami’an yai”ku koma bakin aikin ku, ku tabbatar kun kula sosai” Cikin girmamawa suka amsa mashi da toh, juyawa sukayi da sauri kowa Ya nufi hanyar komawa bakin aikinsa.
Shafa sumar kanshi yai da tafin hannun shi nadama, yanke shawarar komawa gidan obie yayi, yasan suna can hankali duk Ya tashi, ba lallai su iya runtsawa ba.
Cikin takun sauri Ya fita daga part din, Ya nufi ɗaya daga cikin motocinsu, wani jami’i ne Ya nufeshi da sauri Ya buɗe mashi motar ya shiga a mazaunin baya, shi kuma ya zauna a driver’s seat, yai ma motar key ya tashe ta, suka nufi cikin Obie estate......
Unaisa tana akwance idanuwanta sun kumbura suntum, kumatuntu sunyi jawur saboda kukan da tasha, busassun hawayene saman fuskarta, ta lumshe idanuwanta akan giant snake din daya ɗaura kanshi saman kirjinta, karatun qur’ani take raira mashi cikin disasshiyar muryarta daƙyar sautin ke fita, macijin Yayi lamo sai ƙara narke mata yake Yi, ga dukkan alamu yana sauraronta.
Da karfi tajiyo muryar boss man Yana kwaɗa mata kira daga waje Unaisah, Unaisah!!.
A hankali tasoma ƙokarin raba jikinta daga na macijin, ta lalla6a ta sauko daga saman gadon tana cigaba da yin ƙira’ar al’qur’anin, agogon bangon ɗakin ta kalla almost 10 na dare.
A jikin glass door din Boss man Ya jingina yana leƙensu.
Ƙarasowa tayi gaban ƙofa suna fuskantar juna, batasan sa’adda ta fashe mashi da kuka ba, Cikin shessheƙar murya take fadin”kaga irin ƙaddarar da ta sami ɗan uwana ko? Nayi ƙoƙarin na fahintar dasu cewa mutunne amma sunƙi su gane, sai harbinshi suke Yi da bindiga”
Tsananin tausayine ya kamashi ganin yadda ta canza saboda damuwa.
Cikin kwantar da murya yace”Yana ina “?
Matsawa tayi daga bakin ƙofar, karaf idanuwanshi suka sauka akan giant snake din dake nannaɗe saman gadon kamar bacci yake yi.
“Unaisa bai cutar dake ba”? Tambayar daya jefa mata kenan, Girgiza mashi kai tayi”a’a baiyi min komai ba, dan Allah ka taimaka mashi, nasan kai kaɗaine zaka Iya fahimtana,”
Jinjina kanshi yaɗanyi”okey, Ki kwantar da hankalin ki, kidaina kuka bana son ganinki cikin damuwa”
Fuska amarairaice tace”dole in damu boss man, rayuwar ɗan uwana abun tausayice, bazasu ta6a ƙyale shi ba, tun yana jariri suke cutar dashi har izuwa girmanshi sunƙi su ƙyale bawan Allahn nan, mugaye in sha Allah bazasu ta6a yin nasara akanshi ba”
Idanuwanshi tuni sun cicciko tab da ƙwalla
“Dan Allah ka taimaka mashi, akwai ruwan zamzam da ake bashi na addu’a ina da tabbacin idan yasha zai dawo dai dai”
Cikin sanyin murya yace”A ina za’a same shi”?
“Ɗan uwanmune Ya bani address din gidan da zamu ɗauko, namanta takardar acikin aljihun uniform dina, ai kace min kayan suna a hannunku, idan ka duba zaka ga wandona launin baƙi, mu uku keda kalar kayan dani da batul saina danish, pls ka bincika ka dauko ta, Allah yasa bata faɗi ba, nasan ma zaiyi wuya asamu zam zam din koda an samu takardar adreshin”
“In sha Allah za’a nemo zam zam din, ki koma ki zauna amma pls kada ki bari ya cutar min dake” amsa mashi tayi da toh” ajiyar zuciya ya sauke, tamkar karya tafi yabarta haka yake ji, duk da Ya yarda Yaron bazai Iya cutar da ita ba, tunda gashi ya same su asaman gado ɗaya batare daya sare ta ba, shi tausayin yaron ma yake Ji.
Juyawa yai da sauri Ya nufi down stair.
Komawa tayi saman gadon ta haye, ta kwanta daga gefenshi taci gaba da yi mashi karatun qur’ani.
Da matsakaicin gudu motar chief ta ƙaraso bakin entry hall na shiga babban falon gidan baba Obie, dasauri jami’en Ya fito daga motar Ya zagaya other side Ya buɗe mashi murfin car din, Ya zuro kafarshi Ya nufi Cikin gidan da sauri, Kamar yadda yabarsu haka ya same su a tsaitsaye cirko cirko , damuwace ƙarara akan fuskokinsu, hankalinsu bazai ta6a kwanciya ba idan har ba gawar macijin suka gani ba.
“Owais”! Obie ne ya ambaci sunan shi da mamaki akan fuskarshi.
Dagowa yai da kyawawan idanuwanshi ya daurasu akan faces dinsu, kamar yadda yake kallonsu haka suma suke binshi da kallo, Kamar yaune rana ta farko da suka fara ganin juna”
“Owais Ina macijin”? hateem ne ya jefa mashi tambayar.
Calmly ya furta”mun fitar dashi daga gidan” ajiyar zuciya kowan nan su ya sauke, Senate lateef Yace”Wacece yarinyar dake atare dashi? Munji tana kuka tana fadin ɗan uwanta ba maciji bane shin dagaske ne”!
Jinjina kanshi yai alamar eh, ya ƙara da cewa”Ƴar uwarshi ce, ba maciji bane mutunne kamar kowa, ƙaddara ce ta afka mashi”
“Wai kana nufin ɗan mutunne ya rikiɗa ya koma maciji”? His excellency deen ne Ya jefa mashi tambayar, gaba dayansu sun ruɗe da jin maganar,
Abdul razak Yace”bazai yiwu ba, owais kodai ka fara shaye shaye ne? In bahaka ba ta ina mutun zai Iya komawa dabba kamar maciji? Ai sai dai idan ya kasance ba mutun bane shi”
Obie duk Yafi su firgita jikinshi yaƙi daina yin kerma
“Owais bana son ganin macijin nan, ku tabbatar kun fitar dashi daga gidan nan, Idan ba haka ba zai Iya cutar da rayuwar ahalina”
“Baba ka kwantar da hankalinka, zuwa gobe in sha Allah zan shigo muyi magana, nasan yanzu ko nayi maku bayani ba lallaibane ku fahimceni ba, ni kaina hankalina ba a kwance yake ba”
Girgiza kai obie yai”owais idan kaga na kwantar da hankalina to macijin nan baya acikin gidan nan, Ni ban ta6a ganin tashin hankali irin na yau ba, wai yaushema ka dawo kasar? Ita yarinyar dake tare da macijin ƴar wacece? A ina take zaune”?
Shiru yai yana duban face dinshi, sam bayason yawan surutu, abu kadan ke hasala shi, baisan amsar da zai basu ba, don ya fahimci hankulansu ba akwance suke ba.
Gyaran murya mai girma sharafudden Yai, hankalin owais ya dawo kan mahaifinshi”kada ka damu, ka koma bakin aikin ka My son, Ni na fahimce ka, kaje kawai zuwa gobe zamu nemaka donka zo ka warware mana rudanin da muke aciki” lumshe ido owais yai haƙika yaji dadin maganar mahaifinshi, dama yasan shi kadaine zai Iya fahimtar halin da yake aciki
Kafin Ya juya saida ya fara kallon Obie, wanda tuni idanuwanshi sun kaɗa jawur, tausayin tsohon ne Ya kama shi, yayi matuƙar yin kewar kakanshi.
Matsawa yai kusa dashi Ya rungume shi saman faffadan ƙirjinshi, baba Obie Ya kankame owais tamkar zasu koma mutun ɗaya.
Cikin sigar lallashi yake yi mashi magana”nayi kewarka baba, kana araina, nasan ban kyauta maka ba, amma in sha Allah idan komai Ya lafa zuwa gobe zan shigo gidan” cikin sanyin murya obie Ya amsa mashi da toh, ji yake tamkar karya tafi yabarshi, yana matuƙar ƙaunar jikannan nashi.
Iyayenshi dake kallonsu, murmushi ne saman fuskokinsu.
Raba jikinshi yai daga na baba obie, yakai hannu Ya shafi dogon gemun shi, da zolaya ya furta”kakana nakaina, nifa da jarumta nasanka, kai ɗin Namijin duniya ne, dan Allah kada ka bani kunya, kada ganin macijin nan ya hanaka rintsawa adaren yau, kayi bacci ka huta gobe jikanka zaizo gareka, sabon cake zamu yanka atare”
Farin ciki Ya cika obinna, yayin da yake duban owais, yana dariya yace”ka wahalar dani, bakasan irin kewarka da nayi ba, Na ƙwallafa raina akan son ganinka, ka manta dani owais, gobe idan kazo har tsallan kwaɗi zan sanyaka” dariya Iyayenshi suka sanya, Owais yace”kowani horo zakayi min bazan musa ba, Na cancanci fiye da hakan, Ni zan tafi, ku kulamin da kakana, Make sure he sleeps peacefully tonight.” ya faɗa yana duban iyayenshi, fuskokinsu dauke da annurin farin ciki, owais ba ƙaramin burgesu yake Yi ba, saboda yana son mahaifinsu.
Juyawa yai da sauri ya nufi ƙofar fita daga falon, idanuwan kowan nansu akan bayanshi, Harya ɗaga kafa zai fuce, muryar prime minister ta dakatar dashi
“Owais! ina son yin magana dakai” a hankali Ya juya