Showing 246001 words to 249000 words out of 250533 words
Chapter 83 - Kurkukun Kaddara Book 2 Middle Steps By Boss Bature.
kammala yin wanke wanken, ta mayar da hankali akan fuskar zahra
Mahboob Yace”kar dai kice zakiyi min rashin mutunci wallahi sai inyi zuciya inje in nemi auran ɗaya daga cikin jikokin baba obie”
Dariya suka saki gaba dayansu bayan sun tsagaita Aneelerh ta dubi mahboob”Ya ake ciki? Kunyi magana da Ana”?
Ɗaga mata kai yai alamar eh, zahra tace me ya faru ne ko bata da lafiya”
Nan mahboob Ya kwashe komai Ya sanar dasu dangane da halin da Ana take aciki.
Shiru sukayi jikin kowa yayi sanyi, musamman Aneelerh, ranta Ya dan 6aci bata ji dadin ƙin gaya matan da tayi ba.
“Idan kuwa hakana Ana bata kyauta min ba,Yanzu har akwai abunda zata 6oye min duk irin shaƙuwar dake atsakanin mu?”
“Aunty Aneelerh please kada ranki ya 6aci, na riga da nayi mata faɗa, abun da ya dace ku harhaɗa mata kudin da zata turama ƴan uwan nata”
Zahra sarkin tausayi tace”nida da halima wallahi da sun dawo gidan nan da zama.....” wata uwar harara Mahboob Ya watsa mata”saboda ke zaki ciyar dasu ko”? Fashewa sukayi da dariya.
Aneelerh tace’baka da dama mahboob, yanzu fa ka gama fadin a harhada mata kudi aturawa ƴan uwanta shine kuma don tace su dawo nan da zama kake tada jijiyoyin wuya daga maganar taimako”
Yamutsa fuska mahboob yayi”abun da nake nufi Aunty Aneelerh, ɗan adam ba abun yarda bane, muna iya mu taimake su su kuma su butulce mana shine abunda nake jiye mana, kawai dai ƙwara in taimakon zamuyi masu mu tura masu can su ƙarata”
“Ka faɗi gaskiya mahboob, nima nayi wannan tunanin, Yanzu me yakamata muyi”? Acewar Aneelerh.
Zahra tayi karaf ta kar6e dacewa”kowa ya kawo abunda yake dashi hada kai mahboob nakama sai yafi yawa tunda kaine jagaba atafiyar”
Harararta yayi”zahra ki daina wannan maganar, ni bawai bazan bada ba, idan na bada ai ba faduwa nayi ba, duk wanda ya taimaki wani shima Allah zai ji ƙansa, ga lada da mutun zai samu, kawai dai ni bani da kuɗinne Yanzu.....” ya fada yana soso keyarshi.
da zolaya zahra tace”hmmm, Ana fa ba musulma bace, ta ina zamu samu lada idan muka taimake ta”?
Banza yayi da ita baice komai ba, Aneelerh tace”babu ruwanmu da wannan, don Allah zamuyi da kyakkyawar niya, kidaina wannan tunanin” gyaɗa kai zahra tayi”shikenan naji, zan bata wani abu cikin kuɗin dana samu, Mahboob Idan kana da acct number dinta ka tura min” Aneelerh tace”Ina da ita, Idan muka koma ɗaki zan tura maki, Nima zan sanya nawa kudin”
Farin ciki ne tsantsa akan fuskar mahboob, Yaji daɗi zasu taimaki Ana batare da ko sisin shi ba.
“Allah yabarmun ku sisters dina, zahra Allah ya baki miji nagari mai sonki mai ƙaunarki, and aunty Aneelerh ubangiji Allah ya bayyanar mana da mijinki da ƴan uwansa , Allah ya raya mana baby junaid dinmu....” addu’o’i yadinga yi masu suna amsa mashi da ameen, kafin Ya juya zai fuce daga kitchen din
“Mahboob” kiran sunanshi da Aneelerh tayine ya dakatar da shi daga yin tafiyar ya waiwayo yana kallonta
“Please idan ka fita ka faɗama su mami, zuwa anjima Hajiya adama zata zo kawo mana baby junaid nasan bata sanar da ita ba”
“Aunty Aneelerh ashe yau muna da babban baƙo agidan namu, mutumina zai dawo, zamu dasa daga inda muka tsaya”
Murmushi Aneelerh tasaki, zahra tace”wallahi har na kosa in ganshi,Yau zaisha daƙuna duk saina sale mashi fatarshi” Aneelerh na murmushi tace”inaso zamu shirya masu abincin da zasu ci, tun da Ana bata jin dadin zuciyarta mubarta ta huta sai muyi aikin atare”
Zahra tace”Lafiyalou, dama na kwana biyu banyi girki ba, har cake zan haɗama baby junaid dina”
Sun jima suna yin fira a kitchen kafin daga bisani suka fuce zuwa ɗakin domin yin sallar azhar da aka fara kira.
*OBIE ESTATE🌃*
Idan muka koma 6angaren dattijon arziƙi, tunda garin Allah ya waye Hankalinshi ba akwance Yake ba, gaba ɗaya yabi ya furgice masu sun rasa gane kanshi, ko jiya da dare bai runtsa ba, sambatu yadinga yi masu yana firgita yana fadin ga macijij nan zai sare shi, Ina owais dinshi Yana gani za’a cutar da shi bazai kashe macijin ba, mutun biyu da suka taya shi kwana a ɗaki his excellency Deen ne tare da His excellency abdul razak, su kansu basu yi bacciba jiya saboda halin da baban nasu yake aciki, hatta sallar asuba agida sukayi ta yaƙi fita daga ɗaki, kuma ya hana su tafi subarshi, bawan Allah ba ƙaramin jiki yaji ba, hada ruɗun tsufa ke damun shi, daƙyar suka samu nasarar sanya shi yin baccin dole.
A yanzu haka Yana daga kwance saman gadonshi Ya ɗaura kanshi kan pillow, deen da Abdul razak suna a zaune saman arm chairs din dakin idanuwansu akan fuskar baba obie.
Jin motsin buɗe kofane Yaja hankalinsu ga kallon mai shigowa
Senate lateef ne, fuskarshi babu walwala.
Daren jiya da damuwar abunda ya faru ya kwana
Miƙa masu hannu yai suka gaisa da ƴan uwan nashi
Kafin ya dubi baban nasu dake kwance kan gado yace”Bacci yake yi ko idon shi biyu”?
His excellency Deen ne yace”bacci yake yi, daƙyar muka samu Ya runtsa” ajiyar zuciya senate lateef ya sauke kafin yace”banji dadin abunda ya faru jiya ba, gashi har yana neman zautar mana da mahaifinmu, wai taya ma akai har maciji ya shigo part din nan”? Rai amatuƙar 6ace yayi maganar
His excellency Abdul razak Yace”abun da yafi ɗaura min kai shi Owais din Yace ba maciji bane mutunne ya rikiɗa....”tunkan Ya ƙare maganar Senate lateef yace”inko dagaske ne wannan maganar to kuwa ba mutun bane dama, Aljani ne sannan ita wannan ifritun yarinyar mai kasada dana gani atare da shi wacece ita!”? Kafin wani ya bashi amsa sallamar Pravin ta katse masu hanzarinsu,
Shigowa yai cikin shiga ta black suit.
Cikin girmamawa pravin ya gaishe da su, bayan sun amsa masu fuskokinsu babu walwala, pravin ya soma yin magana
“Baba bashi da lafiya ne? naga da asuba bai halarcin masallaci ba”
“Baka ga abun da ya faru jiya bane”? Acewar senate lateef.
“Nagani, kar dai ace shi ne ya hana shi sukuni”? Cikin nuna kulawa yayi maganar.
His excellency abdul razak Yace”ai kuwa dai shine, don jiya ko bacci baiyi ba tsabar firgici, yanzu haka ma da kake ganin shi a kwance daƙyar muka samu yayi bacci’
“Abu baiyi daɗi ba” pravin ya faɗa yana ɗan girgiza kanshi”ubangiji Allah ya bashi lafiya” atare suka amsa mashi da Ameen.
Senate lateef ya ɗaura da cewa”ni yanzu so nake naji daga bakin shi Owais, ya faɗa min wanene macijin menene alaƙar shi dashi”
“Bari na kira shi awaya, ai jiya yace zai shigo yai mana bayani amma shiru kake ji wai malam yaci shiru” Deen ne yai maganar tare da curo wayarshi daga aljihu ya danna ma Chif Owais Kira, kusan sau uku tana yin ringing bai yi picking ba.
“Bai ɗaga ba, may be baya akusane da wayar” ya fada yana kokarin maida wayar cikin aljihun, kwatsam kiran owais ya shigo wayar tafara ruri, ajiyar zuciya ya sauke tare da duban su yace”shi ne ke kira,” ya fada tare da yin picking din kiran Ya kara wayar a kunnanshi, bayan sun gaisa deen yace”muna ta tsammanin zuwanka gida shiru baka shigo ba, ga babanku nan kwance ba lafiya saboda abun da ya faru jiya ko runtsawa baiyi ba sai firgita yake yi”.
On the other hand chief Owais ya furta”I will come later, insha’Allah,”
“Okay, we’ll be waiting for you, sannan inason sanin Ina macijin nan yake? Naji kace mutunne”
Muryar chief owais tamkar bai son furta maganar yace”please uncle can i text you” deen yace okey ba damuwa”, rejecting call din yayi, kafin wani ya furta magana ƙarar shigowar saƙo Ya dakatar da su.
Karanta sakon Deen ya soma yi duk sun ƙura mashi ido suna jiran jin me zaice masu, musamman pravin har wani zoƙa kai yake yi yana leƙen wayar Deen.
Ɗagowa yai da alamun mamaki akan fuskarshi yace”tabɗijancan, wallahi dagaske macijin mutunne wai shaidanun aljanune a jikinshi, yanzu haka ya rikiɗa ya koma mutun acan gidanshi yake zaune,........” aruɗe suke kallon shi.
“Wai ko kunsan Prime minister namu shine ya tura da jet din da zai ɗauko sheikh imam daga sudan saboda kawai ya taimaka ma macijin ya dawo halittarsa”?
Jin wannan maganar ba ƙaramin firgita senate lateef yayi ba ranshi a6ace ya furta”what? Bangane me kake nufi ba! Yaushe akayi hakan?batare da sanin mu ba!” a kausashe ya furta maganar,, a sukwane his excellency abdul Razak Ya miƙe Yana fadin”Anya ka karanta saƙon nan dai dai, bani wayar na duba, ya furta hakan tare da kar6ar wayar Deen Yana duba sakon, bayan ya gama yace”ba shakka, kuwa owais dinne ya rubuta da kanshi, magana ta tabbata prime minister namu shi ya tura da jet din daya dauko sheikh imam daga sudan don kawai a duba yaron, muna nan zaune muna jinyar ubanmu shi yana can wajen taimakon yaron da bamusan wanene shi ba, bamu haɗa alaƙar komai da shiba, bansan meke damun prime minister ba, daga shi har owais din shegen son taimakonsu shi zaija su jefa family dinmu cikin matsala ......” kafin Deen Ya ƙare magana senate lateef daya gama fusata yana huci yace”Wallahi basu isa ba, ni bani buƙatarma jin wani ƙarin bayani daga garesu, Yaron nan bazai zauna a estate dinmu ba, tunkafin aje ko’ina harya fara mallake zuciyar ɗan uwanmu hakan na nufin da wata manufa ya shigo family dinmu, zai iya yiyuwa wasu mugayen ne daga maƙiyan jam’iyarmu sukayi amfani da shi don su tarwatsa family dinmu, ku duba kuga fa duk gidajen dake a estate dinmu bai shiga kowanne ba, Ya tsallake nasu Ya faɗo gidan babanmu saboda shine target dinsa.....” a harzuƙe senate lateef Ya ƙare maganar.
Kanwa uban Ƴan Zigi Pravin Ya haɗe girar ƙasa da sama yace”Ni dama tun Jiya hankalina bai kwanta da shigowar macijin nan ba, Ai daga jin yadda abun ya faru zaka shaida makircine aka shiryama baba, so suke kawai su kashe shi, in ba haka ba taya za’ai ace wai mutun ya koma maciji ai sai dai idan sihirine da shi, munafuki kawai wallahi bazamu yarda ba, Yaron nan bazai zauna mana a estate dinmu ba, dole ne owais Ya kore shi daga estate dinmu, sannan A yanke alaƙarshi da kowa na family dinmu idan ba haka ba zaija mana masifar da bazamu Iya shawo kanta ba” Rai a6ace pravin yayi maganar Yana kallon fuskokinsu.
Jinjina kai kowan nan su yayi alamar gamsuwa da bayanin pravin,
His excellency abdul razak Yace”Ai bazamu ta6a yin gangancin nan ba, mu jira owais din ya shigo anjima, shima hateem din Zanyi waya da shi”
Pravin yace “yamakata atara kowa har shi kanshi yaya sharafuddeen din yazo yaji abun da owais ke shirin janyo mana a family, wallahi jiya Saratu batayi bacci ba, saboda fargabar macijin nan, sambatu ta dinga yi min tana kuka tana fadin gashi nan zai sareta, duk tabi ta haukace ta rikice min aɗaki, daƙyar nashawo kanta da ayar Allah”
Aruɗe Senate lateef yace”kunji ko? Tun yanzu ana kokarin ganin bayan ahlinmu”
Damuwa ƙarara akan fuskar Deen yace”Pravin kana nufin saratu batayi bacci ba jiya saboda macijin”? Batare da ɗar ba yace”bata yi ba yaya, yadda taga rana haka taga dare, ni na zauna ina yi mata fifita saboda zufar dake tsastsafo mata gafa ac a daki amma haka ta dinga zubda gumi”
Hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba, gaba ɗaya sunyi amanna da maganar pravin
Murya na rawa his excellency abdul razak Yace”Yanzu awani hali take ciki? Tayi bacci da safe?
Girgiza kai pravin yai fuskarshi da alamun jimami yace”batayi ba idonta biyu ko abinci takasa ci,”
“Inason ganinta pravin” acewar abdul razak”
Pravin yace toh, bari naje nazo da ita ya juya jiki na 6ari ya fuce daga ɗakin.
Yana fitowa daga dakin su ka yi kici6us da Hajjaty, ta ɗauki wankan bubu gown ta lace a jikinta, ta ca6a uban ado, ƙamshin turarenta ya buɗe ko’ina, mayafin rigar asaman kafaɗa ta daurashi, doguwar suman kanta ta zubo har gadon bayanta, Hannayenta biyu ruƙe da faffaɗan tray daga saman shi an ɗaura jerin kayan abinci.
Wani mugun kallo da pravin ya watsa mata saida gabanta Ya faɗi, duk tabi tasha jinin jikinta, sarai tasan ya hanata yin kwalliya idan har bashi zatayi mawa ba amma taƙi jin maganarshi.
Sai faman ƙyafƙyafta idanuwanta take yi, tayi mashi kyau sai dai yaji haushin adon data ca6a.
“Kin manta gargaɗin da nayi maki? Baki jin maganata ko”? muryarta na rawa ta furta”am sorry dear, na saba ne” guntun tsoki Yaja “yanzu ahaka zaki shiga dakin obie, bayan kinsan bashi kaɗai bane aɗakin, Balagaggun ƴa’ƴansa duk suna aciki, duk kamun kansu bazasu iya jure shaƙar ƙamshin turaren jikinki ba batare da kin jefa su yanayi ba, ko kallon ki su ka yi sai sun ayyana wani abun aransu....” shiru tayi mashi ba tare da tace komai ba, numfasawa yayi kafin ya ɗaura da cewa”bazan bari ki shiga ɗakin ahaka ba, sai dai ki haƙura da kai masu abincin ki koma ɗaki ni sai in kai masu”
muryarta tamkar zata fashe da kuka tace”dan Allah dear ka barni in kai masu, Jiya fa bansamu damar gaishe dasu ba”da shagwa6a tayi mashi maganar, nan take kasala tafara kama shi, matsawa yayi dab da ita, ya ruƙo mayafinta data ɗaura kan kafaɗarta, ya janyoshi zuwa saman kanta ya lullu6e mata sumar kanta da kirjinta saboda yana jin kishin agane mashi majiyar dadin shi, ƙoƙarin manna mata kiss yayi saman red lips dinta, kamar daga sama yaji ance”Daddy!” A firgice pravin ya ɗago yana faman zazzare idanuwanshi Jin muryar zayn, su biyune hannayensu ruƙe cikin na juna shida Zaid, fuskokinsu da alamun ruɗani, kafin ƙarasowarsu pravin yayi saurin ɗaukar juice dake acikin jerin drinks din tray din hannun hajjaty ya buɗe murfin ya watsa mata ruwan lemun gefen galenta, baiwar Allah jikinta sai kerma yake yi, mugun tsoron Zayn take yi, tasan muddin ya gane abun da pravin ke ƙoƙarin yi mata sai ta yaba ma aya zaƙinta, ajiya juice din pravin yayi, ya dai daita natsuwarshi, ya nufesu fuskarshi dauke da murmushi ya ware masu hannayensu da niyar yayi hugginsu dinsu,
Sai dai sunƙi bashi haɗin kai, wani irin matsiyacin kallon zayn yake watsama hajjaty data juya masu baya.
Adabarbace pravin yace”kun ganmu atsaye ko? na fito daga ɗakin baba ne na bankaɗeta batare dana ankara ba” kallon tuhuma Zayn yayi mashi kafin yace”daddy mayafinta fa naga ka ruƙe a hannunka akan wani dalili”
“Baka ji mena ce ba, bugeta nayi har tray din hannunta ya girgiza lemu ya 6arar mata jikin gyalenta shine fa na ruko gyalen ina ƙoƙarin goge mata” yayi maganar tare da juyawa ya ruƙo bakin gyalen hajjaty yana nuna masu,
Ajiyar zuciya zayn ya sauke, zaid yace”daddy barka da safiya, ya gajiyar jiya” ya faɗa tare da yin huggin dinsa, pravin yadan bubbuga bayanshi”Alhamdulillah My son, Ina fata kun tashi lafiya, Yau ba zaku shiga office bane” cikin kulawa yayi maganar, hankalinshi na kan zayn, ya lura yafi ɗaukar zafi halinsa ɗaya dana jatumarsa wurin iya masifa.
Ɗago da kai zaid yayi daga kan shoulder din daddyn nasu yace”mun tashi lafiya daddy, ba zamu je aiki yau ba sai zuwa next week, mun ɗauki hutu saboda zuwan Ƴan uwanmu” jinjina kai pravin yayi”hakan yayi, kunyi tunani,” ya faɗa still idonshi akan fuskar zayn daurewa yayi tare da ce mashi”Son ba magana? Ka tsareni da ido kana kallona ko akwai wani abune”
Ta6e baki zayn yayi, kafin yace”bakomai, daddy ni me zance? Tun da ga zaid nan yana yi maka magana dani dashi duk abu ɗayane”
Hajjaty tuni ta shige ɗakin Obie, batare da sun ankara ba.
Dafa kafaɗar shi pravin yayi”kaima ina buƙatar yin magana dakai, bai kamata kana faɗamin haka ba, Ni mahaifinka ne yakamata kana tuna wannan” ya faɗa tare da janyoshi yayi huggin dinsa, zayn fa ji yake kamar ya haɗa jikinsa da allon bango, shifa sam mahaifinsu baya burgeshi baisan dalilin dayasa yake jin haka ba, kamar bashi ya haife shi ba” bayan sun raba jikinsu zayn yai ƙoƙarin furta”am sorry daddy, idan na 6ata maka rai,” murmushin gefen fuska pravin ya sakar mashi”kada ka damu, inayi maka uziri saboda har yanzu kallon ƙaramin yaro nake yi maka, akwai sauran kuruciya atattare dakai,” dan zaro ido zayn yayi”dady nine ƙarami”? Pravin yace ƙwarai kuwa, ko ka manta shekarunkane? Idan ka manta bari na tuna maka you’re just 2O something years, wata’ƙil don kana ruƙe da muƙami a company shiyasa kake jin kanka wani babba”
Dafe kai zayn yayi da hannunshi, arayuwarshi ya tsani ana fada mashi shekarunshi, haushi yake ji, zaid dai sai faman murmushi yake saki, yana jin dadin tsokanar da daddynsu yake yima zayn.
“Jiya a ina kuka kwana ne”?
“Muna agidan daddy deen, munyi fira tare dasu justice, shine yace mu tsaya ayi firar yaushe rabo” zaid ne yayi mashi bayani
Pravin yace”naji dadin jin haka amma ya akai Justice ya tsaya yin fira da ƙannansa maimakon ya tuntu6i Zaki shi da yake sa’ansa” da biyu yayi maganar yana kallon zayn, haɗe girar sama da ƙasa yayi”daddy, zolayar ta isa haka, nima zan ƙara shekarunne nan bada jimawa ba” dariya zaid da pravin sukayi, bayan sun tsagaita da yin dariyar pravin yace”bakusan abun da ya faru jiya da dare a part din baba”
A ruɗe suka furt”meya faru daddy”? Nan fa ya labarta masu kaf abunda ya faru tun daga shigowar macijin, da firgicin obinna, Hankalinsu yayi matuƙar tashi.
“Daddy kana nufin mommy batayi bacci ba saboda macijin? Sannan baba shima bai runtsa ba? Kuma naji kace chief owais ne Ya kau da macijin yaushe yazo ƙasar? Taya akai macijin ya samu