So Da Buri Book 1

Chapter 22 of 43

girkinta sai ta girka musu abinci ta basu…
Sadiya taci kuka ranar da aka karb’e Jalila kamar ranta zai fita! Ita kuwa Jalila murna ma ta dinga yi ta dawo wajen Maman ta.

Maryam duk wani kulawa haka ta had’a Yaran nan guda hud’u take basu kamar ita ta haifesu duka….Jalila ta taso da k’aunar Huda a ranta dan babu wadda takeso kamar Huda! Abu kad’an ‘k’anwata’ komai ita dai k’anwarta, ko abu taci a makaranta sai ta rago ta kawowa k’anwarta.
Lokacin da aka saka Huda a makaranta kuwa taga gata wajen Jalila da Junaidu wanda tun a lokacin Junaidun yake cewa “shi kam inama ana auran k’anwa to da zai auri k’anwarsu Huda” Gata kala kala ba wanda baya nuna mata, ita ma Jalila yadda take ji da Huda kamar tsoka d’aya a miya! In ka tab’a Huda to ko d’an gidan uban waye kai sai taje har d’akin uwarka da jibgeka…dan one thing about Jalila bata da kunya kuma bata da tsoro ko kad’an! Dan ma Mama tana taka mata burki.

Ya Jaafar ne kawai baya shiga harkar Hudan sosai, saboda shi daman chan akwai shi da son girma kuma miskiline na ajin k’arshe. Shekarunsa suna d’an yin sama ya daina yi musu dariya ma kwata kwata, ko
hira akeyi haka nan shi sai dai ya shige d’aki.
Shiru shirun sa ya fara damun Mama dan haka ta saka mishi ido, ai kuwa nan ta gano ashe yawan baccin da yake yi shaye shaye yake yi tuk’uru.
Hankalin Mama ba k’aramin tashi yayi ba dan a lokacin kwata kwata shekarun Jaafar 15 kuma koma ba dan ta shekarun ba shaye shaye ba abu bane mai kyau. Shiyasa ta dage ta tsaya tsayin daka da addua da komai da kyar aka samu ya shiryu ya daina.


Tsakanin Maryam da Ya Usman kuwa! Soyayyar sati uku kawai ya nuna mata bayan aure daganan ya birkice ta kasa gane kansa…
Haka kurum sai ya tisa ta a gaba wai sai ta fad’a mishi wa tafi so tsakanin shi da Abba!
Wasu lokutan a rana d’aya sai ya buka’ceta sau hud’u idan ya ga dama ko sama da haka a cewarsa ‘sai yayi wanda yafi na Abba yawa!’
Gaba d’aya waensu irin abubuwa yake yi marasa ma‘ana wanda sam ta kasa gane kanshi kwata kwata.
Tabbas Ya Usman yana sonta ta yarda da hakan amma wasu lokutan har hanata abinci yake yi wai yana so ta ji yadda yaji a lokacin data gudu ta barshi dan a wannan lokacin har kwana hud’u ya sha yi bai ci abinci ba…..

Hanyar gidansu Abba kuwa ko waye ata arean bata isa ta bi ta je ba, ko dubiya ne ko kasuwa taje in dai yaji labarin sun wuce ta hanyar gidansu Abba to sai tayi sati tana shan azaba a hannunsa. Babu abinda ya fi sosa mata rai kamar yadda Ya Usman yake nunuwa k’iri k’iri kaff a fad’in duniyar nan babu wadda ya tsana sama da Huda!
Haka kurum sai yayi ta kyarar ta yana hantarar ta, wani lokacin har duka!
Tun Hudan bata gane ba har ta gane, dan sai da ya zamana ko
muryarshi ne idan taji da gudu haka zata shige d’aki….
Hakan ya sanya hatta Jalila da Junaidu da suka fahimta suma sai daina kula shi,har sai da Maman ta gane ta bud’e musu ido tace “basu isa gaba da Mahaifinsu ba”, tukunnan
ba yadda suka iya suka sak’k’o amma idan yana yiwa Huda abu wani lokacin har kuka suke yi.
Lamarin Ya Usman ya kai idan gida akwai mai suna Abba to zai hana Maryam mu’amala da y’an gidan kwata kwata!
A cewarsa wai ‘da gangan take zuwa gidan saboda idan an kira sunan Abba ta dinga tuna Abba…’

Abubuwa kala kala dai…tun abin yana damunta har ta hak’ura ta rungumi y’ay’anta ta yaye lamarin shi a kanta.


A b’angaren Sadiya kuwa sai da tayi shekara 9 tana shan azaba a hannun Garbati, k’arshe ma rufe mata baki yayi ita da iyayenta suka daina neman saki a wajenshi, Allah ma ya taimaki Sadiyan bata yarda ta haihu a gidanshi ba saboda dama tace ‘bata ga guri ba!’.
Su Jalila sukan je su dubata su kai mata kayan abinci da zannuwa, da farko da Maryam suka fara zuwa amman tun zuwan farko da ta saka Yara suka yi mata ihu shikenan Ya Usman da yaji labari ya hanata zuwa kwata kwata.
Sai da zama ya Kare tukunna Allah ya karb’i ran Garbati a hanyar shi ta zuwa Niger (minna) ganin Mahaifiyarsa….

Yaranshi ne kad’ai suka yi kukan rashinsa amman matan sa da y’an unguwa har ga Allah murna suka yi domin kuwa kai tsaye zaka kira Garbati da mai mugun hali gashi duk wani hali na mugunta ya sani ya kware a kai.

Tana gama idda ta fara yiwa Usman zirya..
Haka kurum za taci kwalliya ta ta zo gidan wai ta zo ganin y’ay’anta! Shi dai Usman ba ma ya bi ta kanta dan yace ‘daman a rashin Maryam ne ya hak’ura ya zauna da ita!’.

Idan tazo gidan ta dinga habaice habaice kenan, ko
Jalila ba kulata take yi ba sai
Maryam tayi da gaske tukunna suke gaisheta, Jafar ne kawai yake biye mata.
Ana cikin haka aka yiwa Mijin Zainab transfer shima ya dawo Kano, lokacin Yaranta uku mata biyu Aisha (momy) da khadija sai auta muhammad, itama dayake malamar makaranta ce sai ta nemi transfer aka kaita makarantar mata ta nan gandu take koyarwa.

Ai kuwa tun daga nan duniya ta yiwa Mama zafi, domin kuwa k’awancen Zainab da Sadiya sake k’ulluwa yayi dayake itama Zainab d’in nan kusa Mijinta ya kama haya ba nisa, dan haka kusan kullum suna tare.
Haka nan za suzo gidan suyi ta neman ta da fad’a!
Ita dau ba kulasu take yi ba.

Bilkisu a lokacin Yaranta biyu
Itama ta kammala karatunta na law tana aikin ta!
Kowa dai da y’ar sana’ar shi ko wani means of samun kud’i dan hatta Sadiya business d’in kaya take yi, amma ita Maryam a duk lokacin da tace tana son yin karatu ko sana’a tashi d’aya Ya Usman zai ce “a’a!!
Salon tayi kud’i ta gujesa!.”

Ranar da abun ya isheta daman ko kayan sallah baya yi musu ita da Huda idan ka gansu kullum cikin tsumma, Baba Bashir da Baba Talatu ne suke dan k’ok’artawa suyi musu sai ko Bilkisu,
hakan yasa ta d’auki waya ta kira Baba Talatu tana kuka tana gaya mata.
Ashe Shuwa na gefen ta a lokacin suna tare
Baba Talatu batayi auni ba taji Shuwa ta karb’e wayar!
Maryam zata iya cewa ta manta rabon da taji muryar Shuwa amma maimakon magana mai dad’i sai kawai Shuwan ta rufeta da fad’a ko gaisuwarta bata tsaya amsawaba, tace hau fad’a tana cewa
“Ai ta riga tabar gini tun ran zane! Lokacin da su Zainab da Bilkisu suka yi nasu karatun a lokacin daya dace ai ita saurayi tabi, sai yanzu god’ai god’ai da itane zata wani ce tanaso zata koma makaranta??!.

Kawai ta zauna idan Usman d’in yaga dama yaayi mata to, idan kuma bai yi mata ba ta hak’ura, sannan tama daina k’ok’arin had’a kanta ‘jahila! mara aikin yi! Da su Bilkisu masu ilimi masu aikin yi dan indai tace haka zata yi to kuwa wahala zata sha!.”…
Tana gama fad’in haka ta kashe wayar.


Haka rayuwa taci gaba su Shuwa ko k’ofar gidansu har yau har gobe sun hana Maryam zuwa ballantana Huda, ko Bilkisu ta je gani idan emergency ya taso sai dai su had’u a waje ko a gidan Baba Bashir..
Sunce ‘ai tun ranar data saka k’afa tabi Abba suka cireta a matsayin y’arsu, su bama su da ita ba.…..

Ana haka rana d’aya kawai Usman Ya mayar da Sadiya aka d’aura aure.
Da farko su Baba Bashir sun so hanawa amman yadda ya nuna kamar idan bai auri Sadiya a ranar ba to tabbas zai iya mutuwa! Ne ya sanya kawai aka d’aura musu aure ta tare…

Tun daga wannan lokacin kuma Ya Usman d’in sai ya zamana kamar irin tsoron Sadiyar ma yake yi
,baya son ganin b’acin ranta baya iya hanata abu.
Tana dawowa gidan ta janye y’ay’anta duk wahalar su da Maryam taci ba ayi shekara uku ba gaba d’aya hankali Jalila ya koma kan Mahaifiyarta, tun bata kulata har ta fara kulata daga baya data gane uwar ta kuma sai ta fara yiwa Maryam rashin kunya da rashin mutunci kala kala tun bama data lura da Maryam d’in bata so a tab’a Huda ba, nan ta samu abunyi…

Saboda ita aka cire Huda daga makarantar islamiyyar
da suke yi aka chanjamata
boko kuwa sai da suka san yadda suka yi k’iri k’iri aka hanata zuwa..

Junaidu tun yana dukan Jalila har Sadiya ta bud’e mishi ido ya daina.
Haka kurum sai su rufe Huda da duka babu laifin tsaye babu na zaune..

Maryam bata samun sauk’i a kaf fad’in duniyar nan sai in tana karatun Alqurani ko kuma idan Bilkisu da Yaranta sun zo
Sakina itace Babba watanni uku Hudan ta bata amman irin Yaran nanne masu garin jiki
shiyasa ta zama kamar ma ta girmi Hudan, sai k’anwarta
Sumayya.

Sakina irin Yaran nan ne da basa barin takwana, takan zo wasu lokutan tayi weekend a gidan itama Hudan takan je musu,
ammanfa duk ranar da Sakina tazo sai an kwashi y’an kallo ita da Jalila duk da kuwa Jalilan mugun duka take yi mata amman takanci nasara itama akanta itama wasu lokutan.
Akwai ranar da suka yi wani dambe! Jalila tayi mata duka ita kuma da taji zafi ta rarumi dutse ta bugawa Jalilan a kai wanda har saida ya kaita ga suma.

Ya Usman da Sadiya kuwa suka d’aukowa Sakina y’an sanda, su kuma y’an sanda da son banza suka zo zasu tafi da ita.
Suna shirin sakata a mota kenan daman Babansu ya taho d’aukarsu kuma Mama ta kirasa dan haka ya k’araso a rikice.
Ya ji haushin abun sosai dan haka fad’an ya koma na manya akai baram baram da shi da Ya Usman.
Tun daga nan suka hana Yaran su zuwa gidajensu.
Shiyasa ko lokacin da Bilkisu tace zata d’auki Huda Shuwa ta hanata a cewarta ba zata bari matsalar Maryam ta shafi aurenta ba.................


………………………………

Mama bataji shigowar Sakina da Ummu ba, dafa ta d’in da
Ummu tayi ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin data lulaaa..
A hankali ta juyo gareta tana kallonta fuskarta sharkaf da hawaye.
Numfashi Ummu ta fesar kafin ta tsugunna a gabanta sannan ta shiga share mata hawayen har sai da taga tayi shiru tana sauk’e ajiyar zuciya…

Motsa hannun da Huda tayi ne ya katsewa Ummu maganar da take shirin farawa.

..A hankali take bud’e idanuwanta da suka chanza kala suka k’ank’ance.
Tana gama bud’ewa hawaye suka shiga zubo mata.
Rad’ad’i take ji har yanzu a wajen da Ya Ja’afar ya daketa da katako ga ciwon kan da take ji kamar zata mutu!.
Sakina ce ta hau kan gadon ta zauna ta wajen kanta kafin ta kamo hannunta ta kuma shiga share mata hawaye tana cewa “ta yi hak’uri tayi shiru karta k’arawa kanta ciwon.”
Da kyar dai itama Hudan tayi shiru.
Bayan Likita ta shigone ta chanja mata d’aurin ruwa sannan tayi mata wasu allurai tace “ba zai yiu a sallamesu yau ba sai dai gobe”

Kasancewar dare yayi sosai hakan ya sanya Mama ta lallab’a su Ummu suka wuce gida.
Ya junaidu kam sai da ya tabbatar sun kintsa ya nemo musu duk abun buk’ata tukunna ya wuce
shima.

Washegari da sassafe su Ummu suka zo musu da breakfast, bayan sun biya gidan Hajiya sun ajjiye Sumayya dan itama jikin nata sai a hankali.

Kamar jiya yau ma har dare Ummu tana wajensu, saboda zazzab’in da ya sake lullub’e Hudan ya sanya Likitocin suka fasa sallamarsu aka kuma k’ara mata allurai masu nauyi da magunguna ta wuni tana barci. Sakina Ummu ta sake aikawa taje gida tayo musu girki ta dawo.
Suna zaune wajajen 8 daman kamar Mama ta sani tana ta cewa Ummu ta tashi su tafi sa dawo gobe amman tak’i!
Kawai sai ga kiran Hajiya Shuwa, Ummu na d’auka ko gaisuwarta bata amsaba ta hau zazzaga mata bala’i
tana cewa “taya zata tafi ta bar mara lafiya haka!?
Tabi duk ta wani d’aga hankalinta akan wata Huda, koma meye ya sameta ai sune suka jawa kansu!
Tayi maza ta dawo yanzun nan idan ba hakaba ranta sai ya b’aci!”.
Sarai Mama taji abinda Hajiya tace saboda wayar Ummu irin mai volume d’in nan ce
amman sai ta nuna kamar bata ji ba.
Ummu kam jikinta duk yayi sanyi ko tambayar jikin Huda Hajiya bata tsaya yiba tace a taho a barsu su suka sani.
Haka nan dai jiki duk ba kwari, ta d’auki jakarta bayan ta tabbatar ta biya komai kuma tabar musu isheshshen kud’i a hannu da alk’awarin gobe da sassafe za su dawo In sha Allah.

Suna shirin fita Junaidu kuma yana shirin shigowa da ledoji a hannunshi. Gaisawa suka yi da Ummu sannan yayi mata sai da safe ya shigo.
A gefen gadon wajen k’afafunta ya nemi waje ya zauna bayan ya gaida Mama.

A hankali yake kallonta yana jin wani zafi a ranshi kafin yace mata “ya jikin?”.
Sai da ta gaisheshi bata damu da rashin amsawar shi ba tace masa “da sauk’i”

Shiru d’akin yayi babu mai cewa komai kafin a hankali Hudan tace “Mama zan yi sallah.”
“To”
Maman tace sannan ta mik’e ta fara k’ok’arin d’aga Hudan wadda azaba tasa ta fara yin wani kuka mara sauti abin tausayi.

Runtse ido Junaidu yayi kafin yace “Mama idan ba zata iya ba gara kawai a nemo kwano da ruwa, tayi alwala anan tunda daman yanzu jikin nata zai yi tsami sosai.”
Hakan kuwan akayi da kyar ta iya zama sannan ta samu tayi alwala tayi sallar.
Bayan ta idar ne ya janyo ledojin da ya shigo dasu ya fara bubbud’ewa….
D’ayan fresh milk ne da su maltina, sau d’ayan kuma gasassun kaji ne mai yawa, da zafin su sai maik’o da kamshi suke yi.
Mik’ewa yayi ya d’auko plate da cup, kazan ya fara zuba mata kamar rabi, har ya d’auko
fresh milk zai zuba mata sai kuma ya d’ago manyan idanuwanshi ya kalleta yace
“Me zaki sha??”
Cike da jin kunya, dan ya kamata tana kallon kazar daya zuba mata
ta nuna mishi Maltina.
Murmushi yayi sannan ya ajjiye fresh milk d’in ya d’auki Maltina ya zuba mata kafin ya sake mik’ewa ya dawo kusa da ita ya ajjiye plate d’in akan cinyarta, cup d’in kuma a kan drawer gefen gadon, shi kuma ya tsaya a kanta kafin yace “Bismillah”
Har ga Allah so yake yad’an zauna kusa da ita amman kuma yana jin kunyar Mama.

Da kyar ta iya cin rabi, daga nan tace masa “ta k’oshi” dan ji tayi cikinta har ya cika taf!
Amma da farko lokacin da yana zubawa kamar tace masa ya juye duka.

Gyara tsayuwar shi yayi sannan yace “ko ta cinye ko ya d’ura mata!”
Ba yadda ta iya haka ta dinga turawa saida yaga tana k’ok’arin yin amai tukunna ya kyaleta.

Gaba d’aya Mama itama a takure take, kayana kunya da nauyi duk ya kanainaiyeta.

Har ga Allah idan aka tsareta ba zata iya nuna makusa guda d’aya a tare da Junaidu ba.
Yaron yana da hankali, gashi yayi karatun shi yanzu haka ma masters yake yi, part time.
Yana kuma sana’a dan yana da zuciyar nema, sanna ta san yana son Hudan tsakaninsa da Allah,sosai.
To amman matsalar d’aya itace iyayen shi, da ace Junaidu ba d’an Sadiya da Usman baneba da ita da kanta zata tsaya tsayin daka ya auri Huda.
Tsakanin d’aa da uwa sai Allah dan ta d’auki lesson akan Jalila, duk runtsi wata rana dole yabi maganar Mahaifiyar shi kuma itama Hudan dole ta yiwa Sadiya biyayya tunda uwar Mijinta ce……ta san Huda ba k’aramin wahala zata sha a hannun Sadiyar ba…
Ita kuwa tana ganin wahalar da Huda ta sha daga yarintarta kawo yanzu yaci ace ta samu kwanciyar hankali a gidan aurenta!
Apart from all this ma, ta san Sadiya da Usman ba zasu tab’a yadda da auren ba sai dai wani tsananin rabo..

Sallamar Baba Bashir da Baaba Talatu ce ta katse mata tunaninta..ta yi saurin d’agowa
tana kallon k’ofa.........

BULAMA ✍️






So da Buri
Free Book
21


Murmushi Mama tayi kafin ta mik’e ta shiga yi musu ‘sannu da zuwa’.

Baba Bashir ta jawa kujera ya zauna, Baaba Talatu da d’an gidan Ya Jamilu mai sunan Madu su kuma ta shimfid’a musu darduma.

Bayan sun gaggaisa ne Kaka (Baba Bashir) ya ke tambayar Mama “mai ya faru?,d’azu Bilkisu ta kira take ce musu Hudan na asibiti.”
Shiru Maama tayi dan ita harga Allah bata san ta ina zata fara ba, gashi tanajin kunyar su.

Junaidu ne yayi gyaran murya, ya hau zayyano musu duk abunda ya faru.

Ai kuwa nan Kaka ya hau fad’a! Ta inda yake shiga bata nan yake fita ba
A take ya sa aka kira mishi Baba yace masa “yazo yanzun nan yana son ganinshi a asibitin da aka kwantar da Huda.”
Bayan kamar minti biyu Baba ya kira Junaidu ya tambayeshi “ko ya san sunan asibitin?” nan ya fad’a mishi harda number d’akin.

Suna zaune Baaba Talatu itama tanata bawa Mama baki
Baba ya turo k’ofa da sallama a bakinsa ya shigo.
Tun kafin ya zauna Kaka yace
“Wato Usman ban isa da kai ba ko?
Wato na hana su Sadiya zaluntar Yarinyar nan shine ka b’ullo ta hannun Ja’afar ko!?
Tayaya ma zaka bari shi da ba ishashshiyar nutsuwa garesa ba ya bugi Yarinya haka?!
Haba Usman, katako fa mai k’usoshi a jiki ya maka mata, a ciki!!!.

Yaro gaba daya duk ya bi ya haukace? Yo hauka mana, idan ba hauka ba wa zai yi wannan ta’asar saboda Allah?
Sannan ku kuma kai da uwar sa sam baku son kuji laifinshi.

Lokacin da yake hannun Maryam ai tun farkon fara lalacewar shi sai da ta nutsar da

Download complete TXT · Novel page