So Da Buri Book 1

Chapter 34 of 43

ya sameshi, a wani had’add’en garden haske ta koina tarr!!kamar rana.
Daidaita kanshi yayi sannan ya d’an saki fuska kafin ya k’arasa wajenshi.

Ko gaisuwarshi kuwa Granpa bai amsa ba ya rufeshi da fad’a!
Ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, sannan daga k’arshe yace “idan ba zai iya bane ya bar mishi company d’inshi ai daman ragowar ma ba shine yake kula mishi da su ba!
Wannan d’in dama dan yaga a tsakaninsu (jikokinsa ) yake son bawa mutum d’aya shiyasa yake d’orasu a kai saboda yana so yaga ko zasu iya, but tunda yaga kamar ba lalle su iya d’inba!
Kawai zai chanja shawara ya bawa Yahaya ko Yusuf
dan ba zai yiu ya d’auki something that is so dear to him ya bayar a wrong hand ba! Company d’in is very dear to him ne it’s like something da suka yi shi da brother d’inshi.
Bayaso Company d’in ya samu matsala ta koina shiyasa yake son bawa individual dan sai anfi kula da shi ta hakan, sab’anin idan mutum ya san ba nashi bane shi kad’ai, to ba lalle ya zage damtse kamar yadda zai yi idan nashi ne shi kad’ai ba.
Yana buk’atar jajirtacce tsakanin shi(Auwal), Aslam ko Arshaad!
Yana ganin su Dad yanzu girma ya fara zuwa musu, besides kuma duk akwai companies d’in da ta mallaka musu each, ba lalle su iya ba.
To kuma gashi su d’in (jikokinsa) da ya kwallafa rai gashi suna k’ok’arin bashi kunya!
Meye amfanin su?
wish d’inshi na passing company d’in to an individual from generation to generation ya tashi a aiki kenan?
Gaba d’ayan su basu da amfani daga shi har Arshaad, har gara ma Aslam wanda dukda tarin aikin da yayi
mishi yawa hakan bai sa ya nuna gazawa ba a b’angaren kula da branch na company d’in nasu da yake a chan! Aiki yake yi tuk’uru bil hakk’i da gaskiya!
Su kuwa a nan daga b’arawo sai mai son jiki.”

Sai da Granpa yayi mishi tatas!! tukunna ya tashi ya barshi a wajen ko kallonshi bai kuma yi ba, ballantana ya tsaya sauraron hak’urin da yake ta faman bashi.

Auwal ji yayi kamar ya shak’e kanshi da kanshi tsabar takaici!
He tried so much for all this amman sai da abu ya kusan zuwa gangara zai fara nuna gajiyawa a time d’in da ya kamata ya zage damtse?!
Tabbas maganar Babansa (Daddy) da yake cewa
“babban companyn Granpa…
Ya tab’a cewa kyautar shi zai yi a mutum d’aya tak!
To amman ba lalle a tsakanin su brothers su uku zai bawa ba, tunda company d’in flour n su a hannunshi( Yusuf) yake, na textiles kuma Dad (Yahaya) ne akai a chan Abuja shiyasa ma bai cika zama ba, na oils kuma Abba (Ya’akub) ne dudda yanzu an cireshi an sake bawa Daddy( Yusuf) d’in shiyasa ma aiki yayi mishi yawa.

To wannan babban na MAI TURARE and Co. wanda har a Uk suna da branch
tabbas kyautar shi zai yi amman a tsakanin jikokin su uku, duk mai rabo.”

Gaskiya ce kenan?

A hankali Auwal ya sauk’e ajiyar zuciya, yace
“Daa chan, da na d’auki maganar under probability ma nayi k’arfi da k’arfe wajen ganin na mallaki company d’in, ballantana yanzu da naji daga bakin oga kwata kwata ai sai inda k’arfi na ya k’are!.”

Juyawa yayi ya kalli hanyar da Granpa ya bi ya wuce..
Murmushi yayi kafin yace
“Old man, you may be older but I’m smarter..
Lokacin da zaka sauk’o daga fushin nan ma, baka sani ba.”
Yana gana fad’in haka ya juya ya wuce tare da plans barkatai a ranshi.

Ko da yaje kwanciya ma sai da ya gama shirya yadda zai wanke kanshi a wajen Granpa ta hanyar yin aiki tuk’uru ba tare da an saka shi ba ma!
Dan ya samu ya dawo da martabar shi a idon Granpa, sai wajen 12:30 bayan ya zab’i dandatsetsiyar shaddar da zai saka gobe idan zai je wajen Jalila, tukunna na ya kwanta........


1:00am a airport tayiwa Arshaad, duk da kuwa sun yi waya ba da jimawa ba yace mishi “sun samu delay gashi akwai transit so sai 2:30 flight din zai yi landing a Kano!.”
Amman tun 12 ya shirya da kyar ya bari 1:00 d’in ma tayi, ya fita.

Kamar yadda Aslam ya fad’a masa ‘2:30 am’ d’in tana yi, Arshaad d’in ya isa wajen arrivals ya tsaya.

Har ya d’an fara gajiya dan ya fi 20 minutes a tsaye kuma sai kiran shi yake yi baya d’auka!
D’ago wayar shi yayi a karo na ba adadi da niyyar sake kiran nashi sai kuma ya sauk’e wayar yana kallon setin shi ya hau murmushi….

Sanye yake cikin normal sleeve golden color ta ciki, ta waje kuma ya d’aura slim fit suit a kai white colour, takalminshi da wandonshi suma duk white sai agogon hannunsa ne shi
kuma ya kasance gold jaguar special edition!.
Dogo ne, dan ya fi Arshaad tsayi..
Sannan kyakkyawane
ajin farko!
Hasken fatarshi bai kai na Arshaad ba, amman dai shima ba bak’i bane ba.
Yana da doguwar fuska wadda take zagaye da lallausan saje da gashin baki, baki wuluk!
Yana da madaidaitan idanuwa masu oval shape da straight cikakkiyar gira, hancinshi dogo ne sosai kamar yadda yanayin fuskar tashi take..
Sai d’an mitsitsin bakinshi wanda ya k’arawa fuskar tashi tsari da ainahin kyau mai aji!.

Tafe yake yana jan d’an matsakaicin trolley d’inshi yana amsa waya. Magana yake yi amman kamar baya so yayi…da alama ma bai lura da Arshaad d’inba

K’arasawa yayi towards
inda yake dede lokacin yana hanging up call d’in.
Ji yayi anyi hugging d’inshi kawai, wanda ko bai ga waye ba ya san Arshaad ne
“Welcome back bro”
yace mishi kafin ya cika shi yana murmushi yace
“I miss u, a lot.”

Kallonshi Aslam yayi, a hankali yace “mee too”.

Trolley d’in tasa Arshaad ya karb’a suka k’arasa mota
Arshaad d’in yana tambayarshi “ya uk?”.
“Alhamdulillah”
kawai Aslam d’in ya iya cewa.

A haka suka k’arasa motar suka shiga suka zauna Arshaad ne ke ta magana Aslam kuma daga ‘ummm’ sai ‘um um’ k’arshema ajiyar zuciya ya sauk’e daga haka
ya d’an jingina kanshi ya runtse idanuwanshi…
Ganin haka yasa Arshaad d’in yin shiru shima bai sake cewa komai ba har suka iso.

Gidansu Aslam suka nufa direct! Arshaad ya d’anyi horn kad’an.
Mai gadi ne ya d’an lek’o ganin motar yasa shi saurin bud’ewa ba tare da tmbayar dalilin zuwanshi da mota cikin dare ba.
A hankali ya k’arasa da motar kamar baya so yayi parking d’inta a parking space kafin yad’an kalleshi, in a calm voice yace “Mun iso.”

“Tnx”
Kawai Aslam yace bayan ya d’ago ya bud’e idanuwan nashi
sannan ya fara k’ok’arin bud’e motar…

A hankali Arshaad yace
“Are you sure a nan zaka sauk’a?!
Ka zo kawai muje chan mana, a side d’ina akwai rooms sai
ka zab’i d’aya.”

Juyowa Aslam d’in yayi ya kalleshi sannan yace “I’m good, open the door pls it’s late.”

“Well, you don’t seems good!!
Ina lura da mood d’inka tun d’azu ai, you look disturbed and scared!
Ka zo muje gobe sai a san abun yi!”
Arshaad d’in ya fad’a cikin d’an tsare gida.

Komawa kawai ya ga Aslam d’in yayi ya kwantar da kanshi a jikin seat d’in sannan ya mayar da idanuwansa ya lumshe.
Ganin haka kawai yasa Arshaad ya bud’e mishi lock d’in, dan ya san tunda Aslam d’in yayi haka to idan zasu dauwwama a nan shi fa ya gama magana kenan!.

Yana bud’e mishi kuwa ya sa k’afa ya fice…

fitowa Arshaad d’in yayi shima ya zagaya ya d’auko mishi trolley d’inshi.
Har bakin main door na parlour d’in ya rakoshi tukunna yace
“Zan juya daga nan”

Hannu kawai ya saka ya karb’i trolley d’in sannan yace ,
“Thankyou Arshaad.”

Har Arshaad ya juya zai tafi sai kuma ya juyo yace
“You sure about this??”

“Yeah”
kawai Aslam yace mishi sannan ya k’arasa ya danna door bell.

Ya jima a wajen sosai tukunna wata y’ar dattijuwa mara jiki sosai tazo ta bud’e k’ofar.

Tana ganin shi tace “ai kuwa kai d’inne, tun d’azu nake ta lek’owa ta ramin nan inaso in tabbatar! D’an albarka….”
Sai kuma kawai ta fad’a jikin shi ta fashe da kuka.

Murmushi yayi sannan ya d’an yi tapping bayan ta alamun rarrashi kafin yace
“Kin tare ni a k’ofa ko dai in koma ne? Daman Arshaad sai tallar ‘inje In kwana a gidansu’ yake ta yi min.”

Da sauri ta cika shi tana d’an murmushi, sannan ta bashi hanya ya wuce….

“Home sweet home” shine abinda ya furta kafin a hankali ya sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya, sannan ya d’an lumshe idanuwanshi da suka fara chanja launi a hankali ya bud’e su.

Murmushi ‘Gwaggo Asabe’ tayi tana k’ara girmama k’ok’ari da k’arfin hali irin na Aslam!
Sarai take hango abubuwa barkatai a idanunshi amman shi k’ok’ari ma yake ya b’oye har da janta da wasa duk dan kar ta gane kuma ta damu.

“Dad, yana Abuja ko?”
Taji muryar shi.

“Eh” tace, sannan tace zauna in kawo maka wani abun ka d’an sakawa cikin naka, ko?”.
Har tayi hanyar kitchen yayi saurin dakatar da ita ta hanyar cewa “No, I’m full fa.
Naci abinci sosai a jirgi, sai dai gobe da safe pls ayi min d’an wake, i miss it.”

Murmushi tayi bayan ta juyo sannan tace “Tam shikenan Aslam, sannu ko”
Har yayi hanyar side d’inshi dake a nan k’asan, sai kuma ya juyo yace
“Ta fara baccin dare kenan!
Na ji shiru”

Ajiyar zuciya Gwaggo Asabe ta sauk’e kafin tace
“Bata dad’e da yi ba, dan ko minti ashirin bana jin anyi, shiyasa ma ka tarar dani idanuna biyu. Amman dai gaskiya yau kusan shekara biyar ai na fada maka tun a waya, wannan koke koken duk babu, har takan zauna ayi hira da ita fa wasu lokutan, matsalar sai an sauk’k’o k’asa! Tana yin ido biyu da b’angaren ka zata fara!”.

Da sauri Aslam yace
“Bara inje in yi wanka.”
Bai jira jin me zata ce ba ya tura sliding glass door d’in side d’in nashi ya shige sannan ya mayar ya rufe……


Bayan yayi wanka ya sha tea.
Kwata kwata sai ya kasa bacci, hakan yaasa kawai ya mik’e ya fito daga side d’in nashi, parlourn ba kowa
hakan na nufin Gwaggo Asabe har tayi bacci kenan dan duk bulbs d’in ma an kashe su.

K’arasawa yayi Inda staircase na hannun dama yake sannan ya kama ya fara hawa…

A hankali yake kallon parlourn yana nan yadda ya sanshi!
Da sauri ya runtse idonuwanshi ya tsaya cak! Sakamokon wasu memories da suka fara flashin…..
Sai da yayi y’an addu’o’i sannan nutsawarshi ta dawo, ya samu ya ci gaba da tafiya.

A hankali ya k’arasa inda bedroom d’inta yake!
Sai da ya sauk’e tagwayen ajjiyar zuciya kafin yasa hannu a kan handle d’in ya d’an murd’a a ransa yana adduar ‘Allah yasa a bud’e ne’
Aikuwa yana murd’awa k’ofar ta bud’u!.

Ajiyar zuciya ya sauk’e sannan ya kutsa kai ya shige d’akin tare da mayar da k’ofar ya rufeta....

BULAMA ✍️.



So da Buri
Free Book
30


D’akin da d’an duhu amman ba chan sosai ba sakamokon side lamps d’in da suke a kunne wanda hakan ya bashi daman hango ta kwance a kan gadon.
A hankali ya k’arasa ya zauna a gefen gadon.

A kwance take, rigingine..
pillows wajen uku aka d’aura kanta a kai hannayenta duka biyu tayi folding d’insu a kan cikinta!
Kalar fata ta iri d’ayane da ta Aslam, sai dai shi ya d’an fi ta haske kad’an.
Babu d’ankwali a kanta, wanda hakan ya bawa gashin kanta damar baiyyana wanda yake nan rabinsa bak’i rabi furfura!
Mai santsi da shek’i had’e da tsaho sosai.

Shekarunta ba zasu wuce hamsin ba…kallo d’aya tak! Zakayi mata ka gano kyakkyawa ce ajin farko.
Yanayin hancinta ne Aslam d’in ya d’auko sai dai nata har ya d’an so yafi nashi tsayi da tsaruwa amma saboda yanayin na Yarinta yasa za’a iya cewa ya fita kyau.....

Hannunshi ya saka ya kamo nata sannan ya d’aura d’ayan hannun nasa a kai ya dunk’ule a hankali ya saka guiwowin hannayenshi a kan gadon for sopport kafin ya d’aura fuskarshi a kan hannayen nasu !

Tunani ya fara ‘rabonshi da ita yau shekaru bakwai! Kenan....

........Tun lokacin da psychiatric Doctor d’inta yace musu “the last option d’in da suke dashi shine a kulle su a d’aki d’aya, daga ita sai shi sannan a d’aure hannayenta da k’afafuwanta gudun kar ta cutar da shi ko ita kanta.
Hatta abinci ana so ya zamana shi ne zai dinga bata a baki, yayi mata alwala yayi mata komai for 24 hours!
May be daga hakan tayi snapping out, ta dawo cikin hankalinta.”

Tun a 12 hours Aslam ya ga ba zai iya ba domin kuwa tak’i chin abinci kuma daga ya matso kusa da ita sai ihu! K’arshe ma suma ta fara yi…
Gaba d’aya duk ta firgice.
Ganin haka yasa ya d’auki waya ya kira Dad wanda shima d’in jin da yayi tanata suma yasa yace “bara ya zo ya gani.”
Sannan ya kira Doctor,
shima Doctor d’in yace gashi nan zuwa.

Dad d’in yana zuwa yayi knocking k’ofa Aslam ya bud’e, basu ankara ba kafin ya shigo ta taho da gudu ta hankad’o Aslam d’in waje ashe ta kunce hannayenta ba tare da ta bari ya lura ba!
A take ta saka key…

Ba suyi wata wata ba Aslam ya fara k’ok’arin b’alla k’ofar Dad kuma ya tafi ya d’auko spare key!…Amman ko da ya zo ya saka k’ofar k’in bud’uwa tayi sakamokon barin key d’in da tayi a jiki ta ciki..
Suna cikin kiciniyar bud’ewa suka ji k’arar fad’uwar abu kamar kujera, a rikice Aslam yayi kan 3 seater d’in da take a parlourn ya cewa Dad “ya zo ya kama mishi”.
Haka suka kinkimi kujerar da kyar, suka yi kan k’ofar da gudu da k’arfi suka buga!
Allah ya taimake su kuwa ta bud’u….

Aslam kasa motsi yayi sakamokon ganin k’afafuwanta a sama suna lilo kanta kuma tayi hanging a jikin chandelier d’in d’akin, sai dai k’afafuwan nata still suna d’an motsi!!.

Dad ne yayi k’arfin halin shiga da gudu ya d’auki kujerar data taka ta sak’ale kan nata ta yar! Ya saita mata ya d’aura kafafun nata a kai sannan ya hau ya kunto ta, sai dai zuwa wannan lokacin bata motsi!.

Shi dai Aslam duhu kawai ya fara gani daga nan bai sake sanin inda kanshi yake ba.

Sai da ya farfad’o tukunna ya fahimci ashe suma yayi…
Yana farfad’owa Dad da Arshaad suka yo kanshi suna tambayar shi jiki…
Cikin tsananin tashin hankali , muryarshi tana rawa yace
“Dad ta mutu ko?
Shikenan nayi silar mutuwar mahaifiyata!!”

Da sauri Dad yace mishi
“Bata mutu ba Aslam, suma kawai tayi.”

A tunanin Aslam kwantar mishi da hankali kawai Dad yake k’ok’arin yi, shiyasa yak’i yarda da zancenshi har sai da Dad d’in ya kaishi ya ganta ta window tana zaune Gwaggo Asabe tana bata abinci a baki hannunta kuma ana mata k’arin ruwa!.

Ajiyar zuciya ya sauk’e sannan yace
“Alhamdulillah”

Ba a dad’e bai aka yi discharging d’inshi..
Auna komawa gida ko gama dedeta parking d’in mota bai bari Dad yayi ba, ya fito cikin hanzari ya nufi cikin gidan..

A d’akinsa Dad ya sameshi…yanata kiciniyar had’a kayayyakinsa, gaba d’aya ya sauk’o da akwatina ya hargitsa d’akin da alamun komai da komai yake son tattarawa dan hatta games d’insa suka har yayi parking nasu a daban.!

Da sauri Dad yaje ya rik’e mishi hannu..
Yana juyowa yace “Dad please! Don’t stop me i’ve to do this..”

“Shh” d’in da Dad yace mishi ne ya sanya shi yin shiru.

Ji yayi Dad d’in ya rungume shi ya fashe da kuka…..

Sai da Abba da Daddy suka shigo tukunna suka iya lallashin Dad! Dan Aslam shi kam ya ma kasa cigaba da magana in banda ajiyar zuciya babu abinda yake ta faman sauk’ewa!.


Bayan sun yi shiru ne Abba yayi suggesting “Aslam d’in ya je side d’inshi ya zauna, ba lalle su dinga had’uwa da ita ba in yana chan.”

Ajiyar zuciya Dad ya sauk’e kafin yace
“Abun nata kamar har da aljanu fa, dan indai suna a waje d’aya tou bata sakewa koda kuwa basu yi ido biyu ba!
Daman wajen da yafi dacewa yaje idan irin haka ta faru shine gidan Gwaggo Asabe tou itama yanzu mijin nata ya rasu a gidan itama take!
Sannan y’ay’anta(Gwaggo Asabe)duk ba wani girman
Aslam d’in suka yi ba ballantana a ce yaje gidansu ya zauna!
Babbar 3 years ta bashi, k’aramar kuma 2 months.

So kawai ni a nawa tunannin gara in tafi dashi Abuja…”

Aslam d’in ne yace musu “Dan Allah kawai yanason barin k’asar gaba d’aya! In komai ya lafa sai ya dawo…”

Haka nan ba yadda suka iya, ganin halin da yake ciki yasa suka amince ya tafi...............’.

…….

Kiran sallar farko ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi!
A hankali ya sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya,
idanuwan nan nasa sun kad’a sun yi jazir! Sannan jijiyoyin goshinsa duk sun yi rud’u rud’u!
A hankali yace
“Mommy, please this time around don’t push me away!
Ko menene kike ji ki yi k’ok’ari ki danne ki yi fighting…..i don’t want to run anymore! All my life tun Ina js 1 nake boarding school, hutu kuma sai dai inje inyi a wani waje!
I don’t want this life anymore, it sucks it hurts, i need you…”
A hankali yace
“I’m all alone, please get well.”

Motsi yaga ta fara alamun zata farka hakan yasa ya d’an matso da hannunta (wanda tun d’azun yake a cikin nashi) saitin lips d’inshi, a hankali yayi kissing hannun nata sannan ya mayar mata shi kan cikinta ya mik’e da sauri ya fita dan yaga motsin nata ya tsananta…..

Sai da yayi sallah yayi azkar..
Ya dad’e yana karatu tukunna bacci mai dad’i ya kwasheshi around 8:40 am.

Jin ana tab’a shi ne yasa ya fara k’ok’arin bud’e idanunsa,
dishi

Download complete TXT · Novel page