AJIYA A DUHU BOOK 1

Chapter 46 of 76

shagwaɓa ta ce, “Besty!”.
     Wata irin ajiyar zuciya Ajwaad ya sauke yana lumshe ido da ya zame masa ɗabi'a duk da ƙarancin shekarunsa. Sai kuma a cikin muryarsa mai sanyi da zurfi ya amsa da, “Oummyim!”.
      “Haushina kake ji dan na tafi na barka? Banfa da lafiya nima, yau har asibiti Babu ya kaini akamin karin ruwa”. Ta ƙare maganar muryarta na rawa alamar son yin kuka. Tashi zaune Ajwaad yayi sosai, cikin damuwa ya ce, “To kar kiyi kuka, nima banda lafiyan ai, jiya saida aka min ƙarin ruwan”.
     Kukan ta sakar masa kuwa, da faɗin, “Besty nidai kace Babu ya dawo dani wajenka. Ni bana son nan. Akwai muguwar mata a garin. Yanzu ma ka ganta sai hararata take...” kuka sosai yaci ƙarfinta
       Sosai hankalin Ajwaad ya sake tashi daga can, sai ƙoƙarin lallashinta yake yi amma tana ƙara ƙarfin kukan harda tutturza ƙafafu. Ga Gwaggo ta zuba mata wani shegen kallo. Kukanta yasa Shahidah fitowa. Sai dai suna haɗa ido da Gwaggo ta koma ciki da sauri. Dama a tunaninsu ko wani abu akama Maanal ɗin tunda sun san halin muguwar kakar tasu sai a hankali ce. Sosai Maanal take kuka har sai da Oum ta amsa wayar daga hannun Ajwaad da duk ya rikice da kukan nata itama tana lallashinta da tabbatar mata Bestien nata zaizo ya sameta. Da ƙyar tai shiru sannan Oum ta maida ma Ajwaad waya suka cigaba da hirarsu mai cike da shirme da shiririta musamman ga Maanal dan ko yaya shi Ajwaad ya ɗan tasa ya fara hankali....
    
     Sam rayuwa a Giro batama Ammie da yaranta daɗi. Maanal ce ma dai babu ruwanta, tashin hankalinta kawai ace ta yini batai waya da Ajwaad ba. Anan ne zaka ganta kamar mara lafiya. Amma da sunyi waya sai ka walwalarta ta dawo. Sai ma ta fice wasa cikin gida abinta. Maanal dai dama jaruma ce a fagen iya faɗa da tsokala, anan ɗin ma duk da matsin da suke a ciki bata canja ba. Dan kuwa jibgar ƴaƴan mutane take yi, idan kafi ƙarfinta kasha ƙasa a cikin ido. Gwaggo kuwa idan ta harareta itama ta rama. Ɗakinta kuwa kai tsaye take shiga tace tana son abu kaza. Idan Gwaggon ta korota da zagi taƙi fitowa. Kota warto abinda take so ɗin ta fito a guje. Wannan hatsabibancin nata yasa Gwaggo tafi tsanarta fiye da kowa. Kullum cikin aibantata take da zaginta. Abin na damun Babu da Ammie sai dai babu yanda zasuyi, dan Ammie tama Maanal faɗa akan shiga harkar Gwaggon amma yarinyar nan data faki idon Ammie sai tasan abinda taima Gwaggo. A haka dai sukai sati uku a Giro, duk sun fita hayyacinsu sunyi baƙi sun rame saboda rashin abinci mai inganci. Suna a kwana na ashirin da biyar Babu yazo ma Ammie da batun wai zai yi aure. Sannan suma kawunan sa sunyi magana akan Shahidah da Amaal ya kamata a musu aure dan sun isa, musamman ma Shahidah data fara zama uwar mata. Dan haka sun yanke hukuncin ita Shahidah ta auri Lado ɗan wajen Badaru. Ita kuma Maanal Ƙasimu ɗan wajen Sagiru. Wani irin tashin hankali ne ya ziyarci Ammie. Ita ba auren Babu ɗin ne damuwarta ba, batun Shahidah da Amaal.........✍️


✨ZAFAFAN DAI ✨

1 ƘALBIM (Mamu gee)
2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)


Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000

0022419171
Access bank
Maryam Sani Gumi
Shaida:- 09033181070

Kati MTN:- 09032345899

Ƴan NIGER 🇮🇷
1000CF
89825722
Nousaiba Lawali Maradi
Shaida:-09033181070




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_💞AJIYA A DUHU....💞_*




*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*


*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R


_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_


🅿️➖6️⃣2️⃣


______________

.......Kuka sosai Ammie ta sanya ma Babu da roƙo da magiya, amma sai ya nuna mata shima bada son ransa bane. Dan bazai so yaransa suyi rayuwar garin ba, ba kuma zai so a yanke musu karatunsu ba. To amma bazai iya jayayya da ƴan uwan mahaifinsa da ƴan uwansa ba. Ina sam wannan batu bai shigi Ammie ba. Dan tasan wannan ba umarnin kowa bane sai Gwaggo. Hankali tashe taje ta samu Gwaggo da kuka da roƙo, sai Gwaggon ta rufeta da zagi ta kuma juya maganar. Dan kuka ta sanya da kururuwa wai Ammie ta sameta har ɗaki tana mata gargaɗi idan bata saka Babu ya janye batun ƙara aurensa ba sai tabi dare ta kasheta. Dandanan wajen ya cika da mutanen gidan harda makwafta. Kasancewar Ammie nada tabon fitar kishiya yasa kowa ya yarda da batun Gwaggo. Nanfa akaita cancana magana da zagin Ammie har saida Baba Haruna ya shigo gidan ya tsawatar.
    Sam Ammie bata san miya rufema Babu ido ba, yana dawowa gidan Gwaggo ta faɗa masa ƙarya da gaskiya sai ya hau ya zauna. Aiko ya birkice mata yayta tujara a tsakar gida mutane naji, shi bazai yarda a raina masa mahaifiya ba. Ai ba a kanta aka fara kishiya ba. Shi ya gaji da baƙin halinta. Idan bata gode masa ba bata tsine masa ba. Shekara nawa yana zaune da ita zaman haƙuri badan ya taɓa jin sonta a zuciyarsa ba ko sau ɗaya. Sai dan kawai kar ace yama iyayenta rashin halacci ya kasa riƙeta. Shima namiji ne, yana son ya auri wacce yake so, yana son haihuwar ɗa namiji.. kai tujara dai kala-kala data sanya Shahidah da Amaal kuka sosai. Ita dai hajiya Maanal hidima bata san ma anai ba. Tana can tare da Baba Haruna daya fita da ita gaisuwa gidan wani abokinsa. Ammie tayi kuka har ta godema ALLAH, taji inama iyayenta na raye, ashe duk zaman da take da Babu ba soyayyarta a ransa har zuwa yanzu...
      Anyi haka da kwana huɗu Babu baya kulata hakama ƴan gidan kowa ya ƙara ɗauke mata wuta ita da ƴaƴanta sai ga batun yima Shahidah da Amaal wai baiko. Ranar ji Ammie tai kamar tabar duniya ta huta. Karon farko ta sami Baba Haruna da roƙo. Yayi mamakin jin bada son ranta ake shirin auren yaran ba. Dan shi Babu ya nuna masa komai da amincewarta ne. Lallashinta yayi akan hakan, yace taje zai zauna da ƴan uwansa akan al'amurin. Wannan ya sakata ɗan jin sanyi a ranta. Sai dai me, koda Baba Haruna ya zauna da ƴan uwansa duk sai suka kasa fahimtarsa, ƙarshe ma mahaifiyarsa da har yanzu tana a raye duk da ta tsufa sosai ko tafiya bata iyayi sai tace idan bai bari amma yaran nan aure ba bata yafe ba. Hauka ake yara sunyi zagada-zagada ace an barsu babu aure. Ko so yake suna a musu irin yanda Umaru yay ma ita Asiya ɗin kamar ƴar arna sai da ta shekara ashirin a gida. Wannan yasa dole Baba Haruna ya bar maganar, ya kuma dinga lallashin Ammie. Ina hankalin Ammie ya kasa kwanciya, dan ko maƙiyinta bazata so ya kasance cikin wannan zuri'ar ba balle ɗiyanta. Balle kuma yara ƙanana kamar su Shahidah. Inama ƙudan yake ballantana romonsa.
     Komai yama Ammie tsanani, dan sun tabbatar mata bazata koma da su Shahidah ba. Maanal ma za'ayi mata miji da lokaci yayi su dawo da ita gida. Ranar da aka saka ranar auren daya kasance sati huɗu kacal Ammie batai kwanan lafiya ba. Dan jininta hawa yayi ƙololuwa sai a asibiti ta kwana. Duk da wannan halin da take ciki sai zaginta mutane keyi wai kishi ne. Tana kishi dan mijinta zai ƙara aure. Babu wanda yay mata uzuri akan ƴaƴanta da ake shirin musu auren fin ƙarfi. Washe gari ta ɗan samu dai-daito, iya tunaninta ta rasa wazata tunkara ya taimaketa ya kuɓutar mata da yaranta, ƙanwar mahaifiyarta Shamsiyya kawai ta sani, itama a yanzu bata san duniyar da take ba. Dan tun bayan rasuwar iyayenta bata sake ganinta ba. Minna kuwa dama ba zuwa take ba tunda babu wanda ta sani sai kakanta ko'a lokacin, sai matarsa mara mutunci, yanzu kuma babu shi wajen wa zataje?. Wannan mutanen sune dangin mahaifinta, su kawai ta sani. Sai su Oum da suka zame musu ƴan uwa yanzu a garin Kano. A wannan karon kam sai kawai ta yanke shawarar kiran Oum ɗin, dan itace kawai mafitar data rage mata.
      Bayan ta gama zayyanema Oum komai tana kuka itama Oum ɗin kukan take. Da ƙyar suka lallashi juna Oum tace ta saurareta zatai magana da Aban Fadeel in sha ALLAHU za'a kuɓutar da su Shahidahn daga wannan auren. Wannan waya itace ta sanya Ammie jin ɗan sanyi a ranta, har jininta ya ɗan sauka aka sallameta daga asibitin a ranar....

     Washe gari kusan azhar saiga Amaal data fita sayo mata fura ta dawo cike da ɗoki. Kallonta Ammie da Shahidah keyi, sai kuma Shahidah ta ce, “Ke kuma ina furan? Kin san fa Ammie bataci komai ba ga magani zata sha”.
      Zama Amal tayi da faɗin, “Yanzu zan koma na sayo, Abah na gani a waje tare da Ajwaad”.
     Da mamaki Shahidah ta ce, “Aban Kano wai?”.
   Cike da zumuɗi Amal ta amsa mata da “Eh”.
    Ba ƙaramin waro ido Shahidah tayi ba. Yayinda Ammie ta saki murmushi mai faɗi tana rufe idonta sai ga hawaye sharrr. Da sauri tasa hannu ta goge kafin yaran su gani, wata irin ƙaunar Oum na ratsa mata zuciya da ruhi. Kallon Maanal dake barci sukai, Shahidah ta ce, “Lallai yau da bidiri a gidan nan ga Bestyn Maanal a Giro”. Dariya Amal tayi tana matsawa kusa da Maanal ɗin ta shiga tadata. Da faɗa kuwa ta tashi, dan dama faɗan sukai da wata yarinya a gidan ta fasama yarinyar baki shine Ammie ta daketa tai barcin dole. Dan uwar yarinyar har sashen tazo tana faɗin bazata yarda ba sai ta daki Maanal, yarinya duk tabi ta addabar musu yara. Haƙuri Ammie taita bata amma matar nan sai da ta gama cima Ammie mutunci da gori sannan tabar sashen. Hakkanne ma ya saka Ammie kasa cin abinci dan kanta wani irin ciwo yake mata mai zafin gaske......
        
       A cikin gidan ma tuni labari ya kai musu daga bakin yaransu. Kasancewar duk suna a ainahin babban tsakar gidan kowa na ayyukansa. Masu surfe, masu sakar mahucin kaba, bamu hira, masu sana'oinsu. Sun ɗauki ƙus-ƙus ɗin zance sai ga wani almajiri ya shigo hannunsa niƙi-niƙi da kaya wani matashin yaro biye da shi. A zahirance dai yaro ne, dan dudu bai wuce shekaru goma sha ba. Sanye yake cikin ƙananun kaya na jeans daga wandon har jacket ɗin saman duk sky blue. Sai rigar ciki data kasance red haka ma belt ɗinsa da boot ɗin takalmansa. Ƙyaƙyƙyawar fuskarsa sakaye da farin siririn gilashi mai shegen ƙyau da a kallo ɗaya zaka fahimci mai tsada ne duk da kuwa na ƙarin gani ne. Tafiya yake a nutse babu hayaniya balle garaje, kallo ɗaya kuma yayma tarin matan dake cike da tsakar gidan ya kauda nasa idon ganin yanda suka zuba masa idanunsu har yana jin tsigar jikinsa na tashi.
      Cikin muryarsa mara ƙarfi da hayaniya ya gaishesu a jimlace batare da ya damu da sunji ko basu jin ba, shi dai yana biye da almajirin nan da kai tsaye ya nufi sashen Gwaggo. Suna gab da shiga sai ga Maanal a guje ta fito har tana ture almajirin. Kanta tsaye Ajwaad tanufa, shima da ya jiyo ihunta tuni ya tsaya cak yana kallonta. Ko damuwa da yanda jikinta yay buɗu-buɗu da ƙasar danben da sukai kafin tayi barci ma baiyi ba. Tuni ya buɗe mata hannayensa tazo ta shige jikinsa. Yako ɗagata camak sama yana juyi da ita illahirin fuskarsa na washewa da wani irin sassanyar murmushi daya bama ƴan gidan mamaki. Dan daya shigo sam babu alamar fara'a a tattare da shi. Sai da yay juyi sosai da Maanal dake ƙyalƙyala dariya kafin ya sauketa, sai kuma ta sakar masa kuka. Zuru yay yana kallonta, sai kuma ya kai duƙe a gabanta dan ya fita tsoho sosai, duk da kasancewarsa yaro shi ɗin dogo ne kamar sauran yayunsa da mahaifinsu. Tuni fuskarsa ta koma ta tsuke daga murmushin da yake, idanunsa farare tas da kamar an watsa madara sun fara canja launi.
        “Is something bothering you?”. Ya tambaya kamar wani babba yana tsatstsareta da idanunsa. Ƙara ɓarkewa Maanal tayi da kukan iskanci, tare da faɗin, “Ni tare dakai zan koma. Bana son nan mugaye sunyi yawa. Kullum su Safare sai sun dakan, Ammie ma haka, su Didi ma suyita zaluntata. Wicked old woman ɗin can taita min harara da zagina tana cemin shaiɗaniya. Kowa cutata yake anan ƙauyen Baffa ne kawai ke sona da saya min kayan daɗi. Kuma dama na faɗama su Lami duk randa kazo saika rama min duk abinda suke min.”
         Sosai ɓacin rai ya bayyana a fuskar Ajwaad. Har yama ji ya kasa magana. Dan shi fa idan kana son kaga ainahin fushinsa to kuwa ka taɓa Maanal. Ko Ammie da Babu dan baida yanda zayi ne kawai....
     “Ajwaad!”.
    Sassanyar muryar Ammie ta saka shi janye idanunsa daga kallon Maanal ya maida ga Ammien. Murmushi ta sakar masa da faɗin, “Kaga tashi kaji karka biyema wannan ibilishiyar. Kadai san halin mutuniyar taka maza taso”.
        Dan Ammie ce kawai ya tashi, hannunsa riƙe dana Maanal suka shiga. Su Shahidah na masa sannu da zuwa yana faman balla musu harara. Amaal daba barin saita kwana take ba itama tai saurin faɗin oh har an kai maka munafuncinmu kenan?”.
      Caraf Maanal dake naniƙe da shi ta murguɗa mata baki da faɗin, “E ɗin an faɗa, kuma duk abinda kuka min sai ya rama min har ma Ammie ko Besty?”. Tai maganar tana kallon AA. A hankali ya jinjina mata kansa, sai kuma ya ce, “Amma banda Ammie”. Fuska ta ɓata sai kuma ta sanya kuka tana turza ƙafafu. “Ni dai harda ita Besty, kullum fa sai ta dakan, yanzu ma ta daken ta sani barcin dole.....”
        “An dake kin, oh ni Asiya nima ƙarar tawa kika kawo wajen Ajwaad ɗin?”. Ammie ce tai maganar tana ajiyewa Ajwaad ruwa a gabansa. Sai kuma ta zauna idonta na harar Maanal ta ce, “Karma ka bari ta ɓata maka rai kaji Ajwaad. Yarinyar nan tabi ta fitini ƴaƴan mutane a gidan nan, kullum babu ranar banza saita fasa kan wani ɗan kota jawo min magana. Fitinar Maanal ta isheni wlhy. Kuma ALLAH in baki min shiru ba zan miki duka agaban Ajwaad ɗin”.
      Sarai Maanal ta san halin Ammie, tanada zafi akansu, sanyinta akan Babu ne kawai da mutanen gidan nan nasu. Muƙut ta haɗiye kukan tana mai lafewa a jikin Ajwaad. Cikin maganar nan tasa sanyi-sanyi ya ce, “Ammie kiyi hakuri, amma idan bata ramawa ai sai suyita dukanta. Yanzu ma jiba duk yanda ta rame tai baƙi”.
    Baki Ammie ta saki tana kallonsa. Yayinda Shahidah da Amaal ke kwasar dariya. In dai Ajwaad ne zai yi fiye da haka akan Maanal, dan haka Ammie ta ce, “Shike nan ai dama kai ke ɗaure mata ƙugu, amma dai kubi a hankali, dan ina tsoratar muku randa hajar mai gari zata tsinke”.
    Babu dai abinda Ajwaad yace, amma Maanal sai tura baki take yi. Koda aka kawo masa abinci bai iya ya nutsu yaci ba sai da ya dinga bama Maanal a baki. Itama sai ta dinga amsar spoon ɗin tana bashi. A haka Baabu da Aba suka shigo. Suma dai tsayawa sukai kawai suna kallonsu, sai kuma suka kalli juna suna murmushi. Al'amarin yaran na ƙara tasiri a zukatansu. Cike da farin ciki Maanal ta tafi ta rungume Aba. Shima ya ɗauketa yana dariya da faɗin, “Oh oh my Baby, Autar Oum kuma Bestyn Auta”.
     Dariya Maanal ta sanya da jin wannan kirari na Aba, hakama Ammie da Baabu. Zama Aba yay da ita a jikinsa tana masa surutu, shiko yana biye mata dan harga ALLAH yana ƙaunar yarinyar, yanama ɗansa sha'awa da fatan wannan kusancin da shaƙuwar ya kasance musu har girma su kasance ma'aurata, duk da shi fa ko'a yanzu da su Baabu zasu amince wlhy baiƙi a ɗaurama yaran aure ba kawai. Yana dannewa ne kar ace ya cika azarɓaɓi, ba kuma asan mi gobe zata zo da shi ba.........✍️



✨ZAFAFAN DAI ✨

1 ƘALBIM (Mamu gee)
2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)


Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000

0022419171
Access bank
Maryam Sani Gumi
Shaida:- 09033181070

Kati MTN:- 09032345899

Ƴan NIGER 🇮🇷
1000CF
89825722
Nousaiba Lawali Maradi
Shaida:-09033181070




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_💞AJIYA A DUHU....💞_*




*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*


*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R


_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_


🅿️➖6️⃣3️⃣


______________

.........Sai da Aba yasha furar da Ammie ta kawo masa sannan suka zauna tattaunawa. Gently Ajwaad ya miƙe idonsa akan Maanal dake tama Aba surutun Giro har yanzu. Nuni ya mata data tashi, ta maƙe masa kafaɗa bakinta a sama. “A'a ni ban gama ba Aba labari ba. Ka zauna na ƙarasa masa sai muje na nuna maka su Hanne dake dukana ɗaya bayan ɗaya ka musu duka har ɗakunan uwayensu”.
      Harararta Ajwaad yayi, sai kuma ya sake tsuke fuska. “Idan baki taso ba ALLAH nan zan barki mu wuce ni da Aba”.
    Ai baima gama rufe baki ba ta miƙe zaram, sai kuma ta kalla Aba kamar zatai kuka. “Aba ai dai dani zaku tafi ko?”.
        Da ƙyar Aba ya gumtse dariyarsa da faɗin, “Sosai kuwa. Ai ƙafar bestynki ƙafarki har Kano. Oum ɗinku ma tace karna sake na baroki”. Sosai ta shiga dirga tsallen farin ciki, sai kuma ta nufi Ajwaad ta kama hannunsa. “Besty muje kafin Aba ya gama kama yaran can su Hanne jina-jina. Dan bazan tafi ban bar fuskokinsu da tabon da zasu dinga tunawa da ni ba, dole kuma asan Bestyna mai ƙarfin ILIYA ƊAN MAI

Download complete TXT · Novel page