AJIYA A DUHU BOOK 1

Chapter 61 of 76

a kansa. Ni ban san mike damun ya Fawzan ba sam, bana son wannan sanyin halin nasa. In dai zai ware rana ɗaya yaci mata uwa ai da ta dawo hankalinta. Kawai ka zauna yarinya ƙarama ƴar cikinka na raina maka wayo, da auren wuri yay daya haifeta ai”.
     Dariya RK yay da ɗan dukan kafaɗar AA ɗin, “Common Oum's boy hakan fa normal ne ga ma'aurata. Bari dai kayi auren malam zama ka ɗauki fiye da hakan. Mace kuma ko jika kayi da ita a ɗakin aure ai dai-dai kuke tunda ta gama ƙure maka girma”.
         Harrarsa AA ɗin yay. “Oh irinsa zaka zama kaima kenan?”.
    Cikin dariya RK ya ce, “Idan ta kama mizai hana. Balle ma nasan ni tawa mai hankali ce zata dinga lallaɓani bazata bari ta ganni cikin fushi ba. Kai ni yanzu ma fa zuwa nai muyi magana da Aunty da Yaya akan batun nawa wannan kuma rikicin ya shiga tsakkiya. Magana ta ALLAH aure nake so, idan har anyi azumin nan dani a tuzuru bana son nayi babbar salla a gwauro”.
     Sosai AA ya taɓe baki, sai kuma ya koma ya kwanta yana ɗaukar wayarsa, cikin halin ko in kula ya ce, “Ka samu matar kenan?”........✍️


09032345899

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_💞AJIYA A DUHU....💞_*




*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*


*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R


_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_


🅿️➖8️⃣2️⃣


______________


.......Harara shima RK ya maka masa yana miƙewa, sai da ya ɗauki hanyar closet ɗin AA ɗin sannan ya amsa masa da, “Bazaka bani auren ƙanwar taka Maanal ba kenan da kake min wannan tambayar rainin wayon?”.
      Sai da AA ya wani cije lips saboda yanda furucin na RK ya dakar masa zuciya. Amma sai ya zaɓi masa shiru bai tanka ba. Shima RK ɗin bai sake magana ba sai da ya kimtsa ya fito daga closet ɗin cikin pyjamas. Zama yay ya jawo basket ɗin kayan abincin ya shiga zubawa. Batare daya kalla AA ba ya cigaba da faɗin, “Da gaske nake Ajwaad ina son ka muje Kano wajen Abbu da a weekend ɗin nan, amma sai mun fara zuwa wajen Baba Sardauna first, dan Maanal ta bani dama bai kamata kuma nayi wasa da ita ba.”
       Shiru AA bai tanka masa ba. Dan haka RK ya ɗago yana kallonsa. Wayarsa kawai yake faman latsawa babu alamar ma yana da niyyar tanka masan. “Ikon rabbu, kaifa wani lokacin ɗan wulaƙanci ne baka jini bane wai?”.
      A ɗan tunzure AA ya ce, “Malam mind your own business kaji, ka tafi kaje ka nema aurenka ina da abunyi. Dan zan mayi tafiya ne zuwa Chaina wannan weekend ɗin”.
         “Chaina kuma? Yin uwar mi to?”.
   Nan ma banza AA ɗin ya masa. Sai kawai RK ya taɓe baki da jan abincinsa ya fara ci. “Kai dai ka sani, idan ka tashi ka ƙarasa har katangar bangon duniya ba Chaina ba ma. Kai wlhy ina matuƙar tausayin matar da zata aureka a duniyar nan Ajwaad. Shiyyasa ma kayi kwantai har yanzu babu mashinshiniya. Ya kamata Oum ɗin taka ta saka a fara maka ruƙiyya ko aljanun kanka zasu ragu mu huta muma.”
       “SHURI ne a kaina”.
   AA ya faɗa yana miƙewa, bathroom ya shiga ya bar RK da dariya. “Ai da alama har shurin ma da kukoki za'a iya samu ALLAH. Murɗaɗɗen banza”.
    AA na jiyowa amma bai sake tanka masa ba. Ya jima a bayin sannan ya fito, bai kula RK ba ya haye gadon yay kwanciyarsa. Shima RK ɗin sai bai sake kulashi ba. Sai ma ƙoƙarin neman number ɗinsa dake a hannun Maanal yake. Sai da tana gab da tsinkewa ta ɗauka, cikin yanayin mai barci tai masa sallama.
        “Oh oh har kinyi barci yau haka da wuri?”.
    Daga can Maanal ta ce, “ALLAH na gaji ne Ya Rafeeq.”
     “A niba yayanki bane. Ga dai ƴaƴan ki nan ɗan balaja'u. Dan nima yanzu Yaya zan koma kiransa ma”.
        Cikin rashin fahimta ta ce, “Ni kuma dai, a ina na samu Yaya?”.
    “AA mana, gashi nan ya tasani gaba sai masifa yake min”.
    Wani irin zuuuuu zuciyar Maanal tayi, amma sai ta dake tai ɗan murmushi mai sauti da faɗin, “Ai gara dai ka lallaɓashi dan kasan shine mai baka auren nawa.”
        “Shiyyasa ai nake haƙuri da mugun halinsa. Naji ni na ajiye kawun a gefe zan girmamashi, idan ya bani ke sai mu dawo dai-dai my queen.”
     Nan ma murmushi kawai tayi batace komai ba. Shima sai ya saki batun AA ɗin ya miƙe ya fita daga ɗakin ya koma falo suka cigaba da hirarsu. Duk da ma dai shine ke maganar ita kam sama-sama ne. Bai cika damuwa da hakan ba saboda zuwa yanzu ya gama fahimtar ta akan miskilancin ta da rashin yawan magana. Jin tanata hamma yay mata sallama. Koda ya dawo ɗakin samun AA yay har yayi barci, sai shima kawai yay shirin kwanciyar. Sai dai abinda bai sani ba duk AA na jinsa, dan idanunsa biyu kawai yayi shiru ne. Sai da ya tabbatar RK yay barci sannan ya tashi zaune. Wayar RK ɗin ya ɗauka ya fita falo, yasan password ɗonsa, dan haka ya buɗe ya shiga masa bincike dalla-dalla. Sannan yay tsiyatakun da zaiyi a ciki ya dawo ya ajiye masa wayar sannan ya kwanta. Yana hararar RK dake barcinsa hankali kwance.....

      😆😆An dai ji k...
(Na daiyi shiru😂🤪)

__________★

        “Wai shi wannan tagumin na miye Baby? Ba komai ya wuce ba”. Fawzan ya faɗa yana kallon Nibras. A hankali ta janye tagumin da tayi, tare da sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ta matsa ta kwanta a jikinsa kanta a saman ƙirjinsa. Ji take inama a jikin AA take haka.
    “Jaan”.
Ta kira Fawzan ɗin da sunan da take kiransa. Amsa mata yay idanunsa a lumshe yana shafa bayanta.
        “Dan ALLAH ka kira Yaya AA a waya mana na ƙara bashi haƙuri. Kar yay barci da fushina”.
     Ɗan jimm Fawzan yayi kafin ya buɗe idanunsa a kanta. Duk da maganar tata tayi masa wani banbarakwai sai ya daure ya ce, “Nibras na faɗa miki zai huce. Kema kin san halin Auta ai. Yana da zafi amma baida riƙo. Zuwa safe normal zaki ganshi kamar komai bai faru ba. Amma duk kinbi kin damu kanki. Please ajiye batun wani Auta a gefe zo kiga na nuna miki wani abu”. Bai bata damar magana ba ya haɗe lips ɗinsu waje guda. Kicin-kicin turesa ta shiga yi, sai dai bai mata da wasa ba. Dan in dai wannan wahalar ce ya saba sha a wajen Nibras a duk lokacin da yake buƙatar hakkinsa. Kuma a farkon aurensu ba haka take masa ba. Daga baya ne dai matsalar tasu ta fara. Sai sun sha uban daru wani lokacin ma ya nuna mata ƙarfi sannan. Amma bai taɓa faɗama kowa hakan ba saboda Fawzan akwai haƙuri. Ta ɓangaren zurfin ciki kuwa shi da AA suna kamancece niya..
      Koda suka gama dai-daita tashi tai ta bar masa ɗakin. Da kallo kawai ya bita, zuciyarsa dai sai son kawo masa wani tunani take yana turewa. Daga ƙarshe ya miƙe ya shiga bathroom domin tsarkake kansa.....

________★

      Washe gari suna breakfast a sashin Oum kowanne cikin shirin tafiya office RK ya sanar ma Oum batun zuwa Kano da yake son yi da kuma abinda zai kaisan. Har ga ALLAH sai da gaban Oum ya faɗi ta ɗan dubi sashen da AA yake har tana neman ƙwarewa da shayi. AA ɗin ne cike da dakewa ya miƙa mata ruwa yana mai tsatstsareta da idanunsa da suka ɗan juye..
      (Magana ta ALLAH Uncle RK kana saka Oum da ɗanta a cakwakiya fa🥱 ka kiyaye mu😂🤣🏃🏃.)
Murmushi Oum ta ɗan sakarma AA na yaƙe, tare da sanya masa albarka bayan tasha ruwan. Sai kuma ta maida dubanta ga RK da shima ke mata sannu. Amsa masa tayi tana jinjina kanta. Sai kuma ta maida hankalinta ga abincin tana juya abinda ta ke son faɗa a cikin ranta. Fin mintuna biyu sannan ta ce, “Ita Maanal ɗin ce ta baka dama Rafeeq?”.
       “Eh Aunty, tun kwana biyar ma daya wuce. Jiya kuma muka sake maganar da ita dan nace miki yaje kd. Sai kawai naga nima ya kamata naje su Abbu su san da zancen shi da Baba Sardauna ayi a wuce wajen ko ya kika gani”.
      “Hakan yayi, ALLAH ya zaɓa abinda tafi alkairi.”
     “Amin ya rabbi”.
RK ya faɗa fuska washe da murmushi. Miƙewa AA yay tsam, tare da ɗaukar wayoyinsa. Ɗagowa Oum da RK sukai suna kallonsa. Batare da shi ya yarda ya kallesu ba ya ce, “Oum na wuce office bye”. Sai kuma ya ɗan duƙo ya kama hannunta ya sumbata. Kafin ta samu damar yin magana har ya fice. Murmushi RK yayi da faɗin, “Uhmm Aunty wannan ɗan naki dai sai ke. Ko har yanzu fushin jiyan ne oho masa. Nace ya shirya muje Kanon wai shi Chaina zaije, haka ya balbaleni da bala'i daren jiya laifin matar Fawzan ya koma kaina”.
      Murmushi kawai Oum tayi, “Ya dai faɗa ne kawai. Duka yaushe ya dawo ƙasar ma, balle a yanzu da suke kan project babba a Company.”
        “Nima abinda na gani kenan, amma nasan sa kamar ɗan sama jannati yake ba wahala gantalin ke masa ba. Bara nima naje anata kirana daga asibiti. Komi kenan zan dawo mu sake tattaunawa dai”.
    Kai ta jinjina masa tare da addu'ar fatan alkairi. Ya amsa da jin daɗi yana mai ficewa. Dan bayan uwa da uba a duniya ƴar uwar tasa da mijinta sune na biyu da yake matuƙar so da girmamawa. Yana musu kallon iyaye na biyu a rayuwarsa ne duk da suna amsa sunan yayu ne......

      Wani irin gajiyayyen numfashi Oum ta sauke bayan fitar RK, sai kuma ta ajiye cokalin hannunta ta dafe kanta da taji yana mata nauyi. A hankali Abah dake kallonta ya kai hannu ya taɓata, firgigit ta dawo hanyyacinta, sai kuma ta zuba masa ido kamar yau ne ta fara ganinsa. Zaune ya kai a kusa da ita, tare da jimƙe hannunta cikin nashi sosai, cike da kulawa ya ce, “Fatima na mike damunki haka da irin wannan zurfin tunani? Ko akan Fawzan ɗin ne dai? Dan ALLAH ki kwantar da hankalinki,  jiya fa ina lura dake bakiyi wani barcin kirki ba sam, shin haihuwa bata ALLAH bace ba. Kuma lokaci ne”.
      A hankali hawayen da suka cika mata ido suka shiga silalowa. Sai ta kauda kanta da sauri tana ƙoƙarin sharewa. Fuskar tata ya kamo cikin duka hannayensa, idanunsa cikin nata ya ce, “Zarah na kin san fa damuwar ki na tayar min da hankali, hakama yaranki da zarar sun ganki a damuwa hankalinsu tashi yake yi. Ki duba har na fita na sake dawowa saboda ban gamsu da yanayin dana fita na barki ba”.
           “Kayi haƙuri Zaki na, in sha ALLAHU zan kiyaye. Zan kuma cigaba da musu addu'a su dukansu”.
     “Yauwa haka shine dai-dai, ALLAH yay miki albarka kinji.”.
    “Amin tare da kai kaima da yarana duka”.
    Murmushi ya saki tare da jan hancinta kaɗan ya kashe mata ido ɗaya, ta saki dariya tana mai saka kanta a ƙirjinsa. Shima dariyar yayi yana rungumota. Sun jima a haka kafin ya ɗagota ya fara bata abincin a baki cike da kulawa.
          “Gadanga!”.
      “Uhmyim Fateeman Gadanga minene?”.
     “Ajwaad da Rafeeq”.
“Miya samu Ajwaad da Rafeeq ɗin?”.
Sai da taja numfashi mai nauyi sannan ta ce, “Rafeeq ne yake cigaba da damuna akan aurensa da Maanal.”
         Ɗan tsai Abah yay yana kallonta, sai kuma ya sauke numfashi shima yana mai furzar da iska. “To ni Fateema mi kike so nayi? Yaron kin nan ya cika murɗi. Tunda shi taurin kai ne aikinsa basai a bar Rafeeq ɗin ya aureta ba. Ni zanyi farin ciki da hakan, dan har cikin raina ina ƙaunar Yarinyar nan, har gobe tana a raina wlhy, zan so ta kasance a cikin zuri'ar nan tamu”.........✍️




09032345899





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_💞AJIYA A DUHU....💞_*




*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*


*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R


_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_


🅿️➖8️⃣3️⃣


______________


........“Humm amma Gadanga kasan Auta na matuƙar son Maanal. Ka duba al'amarin nan, kada mu biye ta nashi zurfin ciki ne kawai ke damunsa. Ka duba yanda bayan samun lafiyarsa ya shiryo yazo ƙasar nan yayta wahalar nemanta, duk da bai fito ya faɗa mana ba ai munji a majiya mai ƙarfi akan ƙoƙarin sa.”
       “Amma yanzu daya gantan wane mataki ya ɗauka?. Tunda kika bani labarin komai ai na sanya ido a kansa, amma ban taɓa ganin wani yunƙurinsa ba, ko gidan Shahidah bai taɓa zuwa ba sai dai su haɗu a wajen aiki. Ni kuma ba zanje nema a bashi auren yarinyata dole ba. Itama sai ta zaɓa ta darje. Idan kuma har Rafeeq ya mata zan tsaya tsayin daga na mata auren gata, shiyyasa ma ranar juma'a ɗin nan zamuje Kaduna ɗin. Mijin Asiyan na aurar da ɗa kuma ya gayyaceni, sai muyi amfani da wannan damar muje gareta duk da ina jin matuƙar kunya wlhy”.
      Fuska sosai Oum ta ɓata tana kallon Abah. Idonta cike da ƙwalla ta ce, “Amma ya kamata ku mana uziri, ku fahimci Ajwaad, sannan ita kanta Maanal tana son shi ai, ka zauna da shi kuma zakaji ta bakinsa. Zuwa Kaduna kuma ALLAH nima kunyar sake haɗuwa da Asiya nake yi, shiyyasa naketa tufka da warwarar tunkararta. Dama Majdiya ta faɗa min zancen bikin. Amma dan ALLAH ka duba al'amarin nan na Ajwaad a sassauta masa”.
         “Ai in dai bashi ne ya kawo min zancen ba bai isa na masa ba. Kema kuma ban yarda ki saka shi ya min ba. Ki barsa ya mangantu a karan kansa ni naga ƙarshem miskilanci.”
    “Amma Gadanga.......”
  Kai ya girgiza mata tare da ɗaura yatsarsa akan lips ɗinta. Idanunsa a cikin nata ya ce, “Please Fateema ki fahimceni, in dai maganar Ajwaad ce na gama ta a gidan nan. Zuwa Kaduna kuma ku shirya ku duka zamu je”.
       “Na fahimceka, amma hukuncin ya mana nauyi a sassauta mana”.
    “Sassaucin a hannunku yake ai. Sai dai ina sake gargaɗi bana buƙatar fargarwa daga gareki a kansa.”
    Rasama abin cewa Oum tayi, sai kawai ta zubama Abah daya miƙe ido. Sallama ya mata ya fice yana sanar mata ya koma wajen aiki...

    Da sauri Saheeba tabar kitchen ɗin Oum ɗin ta baya, da alama duk tattaunawar Abah da Oum a kunnenta ne. Kai tun zaman RK da AA ma tana a sashen. Ta shigo ne wai zata amsarwa su Naufal abinci dan ita yau ta makara da girki, masu aikin sashen Mamy kuwa ba wani iya abinci sukai ba, ita ko Oum da kanta take girki bata saka masu aiki. Shine taci karo da hirar RK da Oum. Mai aikin Oum ta bama abincin su Anum tace ta kai musu, idan kuma takai kada ta dawo kitchen ɗin sai ta kirata. Shine ta laɓe tana saurare. Bayan fitar RK harta fito sai ta hangi Abah daya dawo, shine itama ta dawo da sauri ta sake laɓewa taji komai nan ma.
      Da sassarfa ta isa sashen Mamy, masu aiki ne keta faman gyara, ganin bata a ƙasa ta haye sama nemanta. Acan kuwa ta sameta zaune a dining zata karya. Zama tayi itama a saman dining ɗin ta gaisheta. Mamyn ta amsa tana kallonta, dan yanayinta ya nuna da zance tazo. Saheeba kuwa ta cigaba da faɗin, “Humm Mamy da ga sashen matar can nake. Yau dai mun sami tabbacin itace ta dawo da yarinyar nan rayuwar Ajwaad. Tana can tana tsara Abah akan Ajwaad ya auri yarinyar shi kuma yana botsare mata. Wai ashe kin san bayan samun lafiyar Ajwaad tafiyar da yace zai yi ɗin nan ya barmu a can Nigeria yazo neman yarinyar nan”.
“Nigeria?”.
“Wlhy kuwa Mamy nan yazo ya dinga nemanta lungu da saƙo. Ni wlhy yanzu ma wani tunani yazo min, wai minene ma'anar sunan kamfaninsa na agogo?”.
Tsai Mamy tai tana kallon Saheeba zuciyarta na wani kalar tsaitsinkewa. Sai kuma a hankali ta girgiza kanta. “Ban sani ba Saheeba. Ban kuma taɓa maida hankali akan na sani ba. Wani abu su Fateeman sukace akan sunan kamfanin?”.
“A'a, basu ce komai ba. Nice dai nayi tunanin yanzu.”
Ture plate ɗin abincin Mamy tai gefe, batare data sake cema Saheeba komai ba ta miƙe. Bedroom ta nufa, hakan yasa Saheeba rakata da idanu tana wani ƙyaƙyƙyafta su. Sai kuma ta miƙe tana murmushi. Sashenta ta nufa. Tana zuwa tai kiran uwarta a waya ta zayyane mata komai. Daga can mamanta tai ƴar dariya da faɗin, “Kai Saheeba ALLAH ya shirya min ke. Yanzu to mi tace?”.
“Tashi tai ta shige ɗaki Umma. Wlhy na fahimci idan ba wuta-wuta mukai mataba yanzu zata canja ra'ayinta ne akan auren Nuratu da Ajwaad maƙiya sumana dariya. Kin dai ji abinda malam ya faɗa ai yarinyar can Huznah take komi shegiya ita da uwarta ba zaune suke ba. Ga kuma wannan maƙallaiyar mayyar Maanal ɗin da danginta, munafukar can kuma ta ɗaure musu ƙugu, idan ba munafunci ba ta bari ƙanin nata ya auri yarinyar mana ba sai suje suyi zumuncin ba da ƙyau”
“Ke ko tayi haka tunda tasan burin yarinyar da iyayenta cin dukiya ne, ai gara aci wadda ba tasu ba. Ta ƙaninta kuwa aita ubansu ce akwai gadonta a ciki. Ai Yaya Kamila ta tafka babban kuskure a rayuwarta wlhy da gyarashi sai dai ALLAH kawai. Yoni ina zan iya mallakama kishiya ƴaƴana dan neman wata soyayyar mijin banza can. Gashi nan har yanzu bata sami yanda take so a mijin ba ƴaƴa kuma sun nuna basu santa ba”.
“Ai Umma sai ma kina gidan nan zakiga ikon ALLAH. Jiya dai mai aikina ke faɗa min rigima Fawzan yasha da

Download complete TXT · Novel page