Showing 54001 words to 57000 words out of 250533 words
Chapter 19 - Kurkukun Kaddara Book 2 Middle Steps By Boss Bature.
zamu ganta, in kuma ta riga mu gidan gaskiya, Allah Ya jiƙanta, yana daga cikin ƙaddarar bawa, ba dole ya rayu da abunda ya ke so ba, wata rana ma kowa zai mutu ba wanda za’a bari gadin duniyar.......” fira ta yi daɗi sai nutsawa suke Yi, cikin Dajin ba tare da sunsan inda zasu dosa ba, Ga wata iska mai daɗi da ta ke kaɗawa, wasa wasa Ƙarfin iskar sai ƙaruwa ya ke Yi, ta cika masu idanuwansu daƙyar suke buɗe su.
Yayin da su Angel suka tafi nemo masu abinci, Sun yi zazzaune zaman jiran tsammani, Har sun fara lumshe idanuwan su saboda iskar dake kaɗa masu ba ƙaramin kasala take haifar masu ba, kwatsam! Ba zato ba tsammani kunnuwansu suka soma Jiyo masu wani irin sautin gurnani mai matuƙar rikitarwa da razanarwa, A firgice suka ware idanuwansu, Yayin da zuciyarsu ke buguwa da ƙarfi da ƙarfi tamkar zata 6allo ƙirjin su, tsananin tsorone Ya kamasu sai faman wurwurga ƙwayar idanuwansu suke Yi, a ƙoƙarinsu na su gano ta inda sautin gurnani ke fitowa, sai dai sun kasa sani kuma sun kasa ta6uka komai, Azeeza tuni ta shige ma Batul kamar zata koma Cikinta, Jikin su sai faman yin kakarwa yake yi saboda gurnanin ya cika kunnuwansu, Haris dake azaune gaban shimfiɗar Danish muryar shi adabarbarce ya ke ambaton sunanshi”da..da..nish ka tashi, pls ka tashi danish, Wani abu yana tunkaro mu’ Da rarrafe su batul suka ƙarasa gaban shimfiɗar Danish, Cikin fitar hayyaci suke bugun Jikinshi don ya farka ya ceci rayuwarsu, duk sun bi sun ruɗe tsigar Jikinsu ta tashi haiƙam, Har suna haɗa baki wurin ambaton sunanshi”Danish mun shiga uku, dan Allah ka farka, Wannan wani irin sauti ne haka babu daɗin ji, ga Angel bata nan sun tafi tare da Gabriel, Ni dama nasan zai yi wuya mu bar dajin nan da ran mu’ cikin shessheƙar ku ka suke magana hawaye na bin fuskokinsu, Jemimah da azeeza tuni sun rushe da kuka mai sautin gaske, tunkafin ma suga menene ke tunkarosu, sautin kukansu Jemimah shiya ƙara Janyo hankalin Abunda ke nufo su, basu san sune suke Janyo shi ba, babu wanda yai hankalin Ya tsawatar da su akan su daina Yin kukan suyi shiru, ba su yi tunanin yin hakan ba, lokacin da sautin gurnani ya ƙarfafa hatta ganyayyakin dake a wurin Girgixa suke yi, nan take idanuwansu suka tsaya cak akan wurin da suke zargin zai 6ullo, Kamar An Jeho suka faɗo ƙasan wurin, wasu irin Mugayen Halittun namun dawa, masu gashi gashi a jikinsu babu kyan gani gwanin ban ƙyama, Suffarsu tamkar ta majici sai dai sun gurmi maciji a halitta tsaf zasu Iya haɗiye mutun su nannade shi a cikin bakunansu, Tashin hankalin da ba’a sama shi Date, Wata irin gigitacciyar ƙara suka fasa, Ganin Yadda halittun suke Kurɗaɗowa saƙo da lungu masu Yawan gaske gasu manya manya, Gadan gadan suke tunkarosu Harwani nannaɗe Jikinsu suke yi suna harɗewa, tsabar firgi da tsoro ne yasa suka Watsa da gudun gaske kamar zasu Tashi sama, Gudu su ke yi na fitar hayyaci, gudun ceton rai, su kan su basu son Inda zasu dosa ba, wani ƙarin tashin hankalin Halittun da gudu suke binsu, Ga sauri da Allah yai masu, sun fuskanci matsanancin tashin hankali mara misaltuwa, musamman ƙananun cikinsu Azeeza da jemimah duk sun tarwatse kowa Da inda nufa, dan bala’i, Halittun suna lura da kowace kusurwa suka faɗa, Yadda suka raba kawunansu haka suma halittun su ka karkasa kawunansu wurin binsu, Haris da ba ƙoshin lafiya gare shi ba, tuni Numfashin shi ya soma sarƙewa, bakinshi ya soma fitar da jini, Gashi kowa Ya watse sun barshi, Yana ji yana gani halittar nan Ta ta taɗiye ƙafarshi gaba ɗaya ya kife ƙasa, tana gurnani ta wage bakinta masu haƙora a jere babu kyan gani, ta Zurma ƙafafuwanshi.....Innalillah
A 6angaren Azeeza da ke ruƙe da jemimah suna tiƙar gudu, hada tuntu6e sun rasa ina zasu dosa, Jemimah sai kuka take yi tana ambaton sunan Genie, Cikin rashin sanya Wasu muggan ƙayoyi suka Sargaho ƙafafuwansu kusan atare suka rubza ƙasa kansu ya daku.
A 6angaren Batul da parveen da Hannah da suka nufi Hanya ɗaya, Halittun nan sai binsu suke yi, sun rasa ina zasu dosa, suna gudu Sumar kansu Na rufe Masu idanuwansu, ba zato ba tsammani ƙafafuwansu suka zurma a cikin wani rami da ca6ali ya cika shi, gaba ɗaya su ka nutse cikin shi, Ko numfashi basu Iya fitarwa.
Idan muka Koma 6angaren Angel da Gabriel, lokacin da suka ƙaraso bakin wata bishiyar Mangaro sun tsaya suna tunanin hawa saman bishiyar don su tsigo su, atare suka haye suna aikin tsinkar magaro, sai da suka gama ɗibarshi a cikin kwando, Gabriel na yunƙurin zura ƙafarshi Ya sauko ƙasa kwatsam idanuwanshi suka sauka akan kurar dake ƙasan bishiyar tana cin wani namun dawa data kamo, wahalallan yawu ya haɗiya tare da kallon Angel, ita sam bata lura da abunda ya hango ba,
“Gabriel mu sauko mana, Suna jiran mu” Muryarshi Na kakarwa yace”Angel mun shiga uku, wlh kura ce a ƙasa take cin nama,” Sai lokacin ta wurga Idanuwanta ƙasan bishiyar, Gabanta yai mugun bugu, muryarta da tashin hankali ta furta Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un! Kafin Gabriel ya furta wani abu daga can cikin Dajin ihun muryar Naufal Ta karaɗe kunnuwan su, Kallon Juna su ka yi nan ta ke su ka fahimci babu lafiya a wurin Ƴan uwan su, zufa tuni ta wanke fuskarsu, ganin tana yunƙurin sauka yasa gabriel damƙo hannunta, muryarshi a hargitse yace”Kada ki sauka angel kashe ki za ta yi” Girgiza mashi kai tayi idanuwanta sun rikiɗa jawur dasu tace”ƙwara ta cinye ni, wlh sai naje wurin ƴan uwana, Baka ji ihun naufal ba, Allah kaɗai yasan meke faruwa dasu” kokawa suka soma yi da Gabriel a saman bishiyar, ya hana ta saukowa sai kiciniyar kwace kanta ta ke yi, aiko Suna cikin Yin kokawar nan Gaba ɗayansu suka ƙundumo ƙasa agaban kurar nan, Bakin ta ca6a ca6a da jini, Kafin ta ɗago da ido ta kallesu, Da iya ƙarfinsu na ƙarshe suka yunƙura suka miƙe a guje suka watsa, da gudu itama kurar tabisu tana gurnani, babu wanda bai fita hayyacin shi ba, lokacin da suka faɗo wurin da suka bar su azeeza hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba, gabin babu kowa ga kuma Danish a kwance yana ta sharar baccin shi. Kafin Angel tayi yunƙurin zuwa wuri shi kurar nan ta dako uban tsalle ta faɗo masu, Da ƙarfi gabriel Ya fusgi hannunta tana kuka tana ambaton sunan danish Tana miƙa hannu yaja ta da gudu, wani iko na Allah kurar ta tsalle Danish tabisu da gudu, su kawai ta ke hari, kurɗaɗawa suka yi cikin dajin suna gudun famfalaki Kura ta zamar masu masifa ta hanasu sakat.........”
*Boss Bature✍️*
Tun bayan da dr shureim ya fito daga bedroom ɗinshi ya nufi Palour, A zazzaune ya samu Alhaji ubaid tare da Uncle musa zaune saman Sofa mai mazaunin mutun uku, Layla tana a zaune saman sofa mai mazaunin mutun biyu, Idon shi na akan Uncle ɗin nashi, Ya ɗauki wankan tsadaddiyar shadda mai ɗaukar ido, ƙamshin turaren shi Ya cika palourn, idanuwanshi suna a lumshe, hannun shi na dama haɗaɗɗiyar agogon diamond ce wadda a ƙalla price ɗinta ya kai 300m, mutunne mai ji da naira, hutu ya zauna mashi ko Alhaji ubaid ba zai nuna mashi tarin dukiya ba, ko a muƙami bai kai shi matsayi ba, Alhaji musa ƙanine ga Alhaji ubaid uwa ɗaya uba ɗaya, kuma shine former president, akwai tazarar shekaru a tsakaninsu, A kyawun halitta Musa ya zarce Alhaji ubaid, Yana da hasken fata yayin da Alhaji ubaid yake da duhun fata, Sannan yana da Yalwatacciyar sumar kai tasha gyara ga sajen gefe da gefen fuskarshi baƙi wulik, Kamar matashin saurayi. Ya iya ɗaukar wanka ga aji ga kuma ji da kai.
Daga ƙasan carpet dr Shureim ya zauna cikin girmamawa ya gaishe dasu, Alhaji ubaid ne kaɗai ya amsa mashi, kawun nashi kuwa ko arziƙin kallo bai samu ba, har sai da hajiya layla tace mashi”baka ji shureim yana gashe ka ba”? Ba tare daya buɗe idon shi ba yace”Naji,” sanin halin shi yasa Shureim bai damu ba, Layla dai ce ranta ya 6aci dama ita bata iya 6oye fushin ta, Alhaji ubaid ko murmushi ne akan fuskarshi, Har yau mamakin Halin Ƙanin nashi Yake yi.
“Shureim, kasan shi fa mutumin turaine ba haka yake son ka gaishe shi ba, Ka matsa kusa dashi yaji ɗumin ɗanshi a jikin shi” acewar Alhaji ubaid,
Yatsina fuska layla tayi, aranta kuma ji take kamar ta shaƙe wuyan Alhaji musa, jin kanshi na matuƙar ƙona mata rai, miƙewa shureim yai tare da nufar sofa ɗin da musa ya ke a hakimce, ya zauna daga ƙasa,
“Uncle sannu da zuwa, Ya gajiyar tafiya” sai lokacin ya ɗan ware idanuwanshi tare da kallon shureim na tsawon mintuna, sai da ya mula ya sha iska tukunna ya soma magana
“Babu gajiya atare da ni, kai zanyiwa sannu, ni banzo da niyar in ganka ba, banma yi tunanin kana a ƙasar ba, sai da Ya ya ya ke faɗamin, shureim kafi ƙarfin ka tako kazo gidana ne? Laifin hada ni ya shafa kenan”? Tun da ya soma magana, hajiya layla take jifar shi da harara a fakaice batare da ta bari Alhaji ubaid ya gani ba, ita sam baya burgeta, haushin nuna isar da yake yi take ji,
“Ay min afwa Uncle, bani da kwanciyar hankali ne shiyasa bana samun damar zuwa, amma kuna araina,”
Ta6e baki Alhaji musa yai ba tare da ya furta kalma ba
Hajiya layla tace”To ai kaima ɗin baka damu dashi ba, Ba ka neman shi taya zai yi tunanin kana buƙatar ganin shi a gidan ka......” bata ƙarasa maganar ba, da sauri ta dakata ganin irin kallon da Alhaji ubaid ya ke jefa mata, sam baya son tana shiga tsakanin shureim da ƙanin shi, saboda mugun son shi ya ke yi baya son 6acin ranshi.
“Kare shi za ki yi”? Alhaji musa ne yai maganar sautin muryar shi a kausashe, Shiru tayi bata tanka mashi ba,
“Kada ki shiga tsakanin Uba da ɗansa, Kija baki kiyi shiru” Alhaji ubaid ne yai maganar, Ta6e baki tayi tana faman hura hanci.
“Ae da kabarta yaya ta ƙarasa maganarta,” yai maganar fuskarshi ɗauke da murmushi. Kafin ya kawar da idonshi daga kallonta.
“Shureim, Idan na tashi tafiya abuja atare da kai zamu tafi, bazan barka a gidan nan ba, don Na fahimci akwai masu takura maka, Shiyasa duk ka rame kayi duhu,” Cikin kulawa yake yi mashi maganar, hannun shi ɗaya asaman kafaɗar dr shureim ɗin, Layla ta yi mamakin jin abunda yace, mutumin da ko ƴa’ƴan shi bai sakar masu fuska shine ya ke zancen zai tafi da shureim, kwa6e fuska ta yi don ta fahimci so ya ke ya ƙuntata mata.
Alhaji ubaid yana murmushi yace”naji dadin jin hakan, wata’ƙil idan kuka je can yafi sakewa, don na fahimci shureim baya son zama gida...” kafin ya ƙarasa maganar, layla ta katse shi da cewa ‘’ae sai ku tsaya kuji ra’ayin shi ko? Idan ya ce yana son zuwa can ɗin,” Tana rufe baki Alhaji musa yace”ai ba shawara nake nema dashi ba, Umarni ne” Cikin isa Ya furta hakan, Kafin ya kalli dr shureim, ka shirya komai naka idan muka tashi tafiya atare zamu tafi”
Lamarin ya ɗaure mata kai, shi dai Dr shureim yai shiru bai tanka masu ba, Girgiza kai Hajiya layla tayi’bazai yiwuwa ba, haba dan Allah duka yaushe muka samu shureim ɗin ya dawo wurin mu, Sannan kuma yanzu kace zaka tafi dashi? Aɗan bari ya huta mana, Shi kaɗai fa nake gani inji daɗi,” rai a6ace take magana, Sun natsu suna sauraronta, sai da takai ƙarshen Aya tukunna Alhaji ubaid yace da ita”meye na tada jijiyoyin wuya? Guduwa zai yi dashi ne? Bafa raba ki zaiyi dashi ba, Yana so ya zauna gidan shi na ɗan wani lokaci,” fuskar Alhaji musa aɗaure yace”idan na ga dama zaici gaba da zama awurina ne kuma ke baki isa ki hana shi ba” murmushin fuskar Alhaji ubaid bai washe ba yace”ba girmanku bane ku tsaya kuna sa’insa akan Shureim sai kace wani ƙaramin yaro, ko da ya ke laifin ka ne shureim tuntuni nake baka shawarar kayi aure ka ƙi yi, da ace kana da Iyali babu wanda ya isa yai iko da kai” da zolaya yayi maganar, Shureim dai ya natsu yana jinsu, Ya jima yana jin takaici yadda rayuwa ta canza mashi, Ya koma tamkar ƙaramin yaro a idon kowa, saboda raunin zuciyarshi.
daƙyar Alhaji ubaid ya samu Ya maida sa’in sar tasu Wasa, dama can basu jituwa tsakanin Layla da ƙanin shi tunfil azal.
“Yakamata mu tashi muje muci abinci, zainab ta shirya mana a dining” layla ce tayi maganar, Ɗaya bayan ɗaya suka miƙe tare da nufar Dining room.
*Kaɗan daga Cikin Na sati mai zuwa idan Allah ya kaimu da rai da lafiya*
*Evil forest*
Sautin Ƙarar Danƙararen Helicopter mai saukar angulu Ƙirar UH-60 Black Hawk mallakin Sojin Ƙasar america ne Ya karaɗe ko’ina Na Cikin Dajin Evil forest Hatta rassan bishiyoyin da ke a cikin dajin girgiza suke yi saboda ƙarfin iskar fankar Jirgin, Shawagi jirgin yake yi a saman Iska Yana kewaye ko’ina na tsawon mintuna talatin, Yayin da Hot soldiers din dake a tsaye saman jirgin cikin shigarsu Ta ka ki sun ɗaura ɗamarar Yaki, Sai dai ga dukkan alamu Sun kammala gudanar da abunda Ya kawo su Cikin Dajin, Ɗaya daga Cikin sojojin dake a tsaye bakin ƙofar helicopter ɗin Hannun shi ruƙe da tactic phone Wayar da sojoji suke yin amfani da ita wurin yin sadarwa ga Manyansu dake acan Headquater, Cikin Harshen turancin Yake Yin magana muryarshi na fita da amon murya saboda ƙarfin iskar Dajin
“We successfully apprehended the criminal. We are now on our way back to the U.S. with the eleven children we found in the forest.”
Da wani irin speed jirgin ya karya kwana ya miƙi hanyar komawa ƙasar da ya fito......, Nima kuma na ajiye alƙalamina.
*Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_~*BossLadiesWriters*~_
_*KURKUKUN ƘADDARA*_
_The Prisoners E11🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
~Middle step~
_A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._
Gaba ɗaya Haris ya fidda rai da rayuwa, tun da halittar nan ta zura ƙafafuwansa cikin wawakeken bakinta, tsabar tsoro da firgici sun hana shi motsawa jini duk ya wanke bakinsa har saman rigar sa, jikinsa yai wani irin mahaukacin zafi na fitar hayyaci, Bawan Allah sai sambatu ya ke yi yana ambaton Sunan Danish dana sauran ƴan uwan su don su kawo mashi agaji.
Ba zato ba tsammani ya ji Sautin dirar wani abu daram! tamkar zai fasa kunnansa, tsabar firgitar da yai ne yasa nan take ya sume saman koraren ciyayin.
Wani Gabjejen Bature ne A tsaye cika shigar Kaya na tatattun Ƴan ta’adda babu ɗigon Imani akan fuskarsa, Hannunsa ɗaya ya ruƙe da Bindigar da yai amfani da ita wurin harbin Halittar da ta nannaɗe Jikin Haris, yayin da ɗayan hannun ya ke ruƙe da cigarette.
Hankalin shi a kwance ya ke zuƙar Tabar Cikin ƙwarewa Har ta hanci Hayaƙin Ya ke fita, kwarkwararrun idanuwanshi na akan Haris dake kwance Ya sume, Tuntsirewa Baturen Ya yi da dariya hada ɗan girgiza kanshi, da ƙarƙarfan muryar sa ta Mashaya giya cikin harshen turanci ya ke faɗin
“wani irin ganganci ne ya kawo ka ƙurmin daji da ƙananun shekarun ka, ba ka da hankali ne? Matashi da kai kake son ƙare rayuwarka abanza? Ina iyayen ka su ke”?
kamar zautacce Shi kaɗai ya ke yin maganar shi, sam bai fahimci Yaron Ya sume ba, Sai da Ya gama Magana kafin ya matsa inda Haris yake a kwance, Ya zuƙunna Bayan Ya soke pistol ɗin a qugunsa, Ya sanya hannayensa Biyu Da ƙarfi Yake jan jikin halittar, Har sai da yai nasarar zaro ƙafafuwan Haris daga bakinta, Allah yaso ba ta kai ga Gatsa haƙoranta akan legs ɗinsa ba, da ko ta yi mashi babbar illa, Bayan Ya zame jikin Halittar da karfi Ya jefar da ita gefe ɗaya, yunƙurawa yai ya miƙe tsaye yana kakka6e tafin Hannayensa, Zuƙar Tabar sa Ya ƙara Yi”Bani da zuciyar Imanin da zan Iya taimakon ka, ka gode wa Allah da na raba ka da dabbar nan, da ko yau Ka rasa ƙafar zuwa gidan Iyayen ka” Yana magana yana sakin dariya idanuwansa akan fuskar Haris.
Sautin kururuwar neman a gajin da ya Ji ce Tasa shi Kan ga kunnansa ga iska Don Ya ji da kyau, Muryar Naufal ce Ya ke faman Fasa Ihu, Da gudu Baturen Ya kutsa Cikin Dajin Yana Tunkarar inda sautin Ƙarar ke fitowa, ta wutsiyar idon shi ya hango gifcin mutune sanye da Jajayen kaya, Ta tsakantsakin jibga jibgan Bishiyoyin dake a kewaye da wurin da yake, Cikin Zafin Nama Ya daka uban tsalle ta tsakiyar wasu bishiyoyi, Kamar an jeho shi Ya faɗo Tsakar wurin da Su Naufal su ke, Gaba ɗaya sun fita hayyacin su, Halittun sun kewaye su sai gurnani su ke yi, Naufal da javed sun ƙanƙame Juna, Kuka hada majina fuskokin su jaga jaga da hawaye, wandunansu a jiƙe sharkaf da ruwan fitsarin da suka saki, Ɗan iskan murmushi dangerous terrorist Ya saki kafin Ya zaro bingidar da ke soke a qugunshi, Ya saita Jikin Halittun ɗaya bayan ɗaya yake sakar masu alburushi, duk wadda ya harba nan take Tsakiyar Cikinta yake tarwatsewa Ƴan hanji su fito waje, Sautin harbin bindigar da basu ta6a ji bane Yasa