So Da Buri Book 1

Chapter 25 of 43

goshina a k’asa sai na yiwa Huda adduar miji da dangin miji na gari sannan da karatu! Ina so Huda tayi karatu amman yanzu bani da wani burin daya wuce in raba ta da Yaron nan.
Yadda yake zak’ewa d’innan yake yin abubuwa kina ganin bashi da wani mugun agender??”

Murmushi Ummu tayi kafin tace “nima nayi tunanin haka da farko amma ntic na Kano da muka bincika basu cika d’aukar y’an scholarship ba
sai wannan karon kuma suna ta sanarwa for good 3 months sannan ranar monday d’innan shine date d’in basu chanja ba!
Abinda nakeso ki gane shine komai yazo ne a k’urarren lokacine kuma right time, shiyasa muke ganin gaggawarshi.
In sha Allah ba komai.
Ke da kanki kina cewa Hudan bata da foundation na boko da waye da waye idan har ba irin waennan makarantun muka samu taje ba, ba lalle kwakwalwar tata ta taso ba!
Ni dai har ga Allah Mama Ina hango alkhairi a tattare da bawan Allah n nan, in dai muka bincika security na school d’in mukaga is good kawai suje idan har sun ci, mu bisu da addu’a. Ballantana ma na san cewa makaranta mai kud’i irin haka ba abunda zai hana ta samu kwakkwaran security.
Kar ki duba Yaron ki duba karatun Huda da future d’inta kuma kiyi addua, ba ko wanne mai kud’i bane aka taru aka zama d’aya ba!
Wasu zakiga ba ruwan su…
Sannan Baban Sakina ce mini yayi ‘in sha Allah, yana hango silver lining a rayuwarki ata dalilin relationship d’in Huda da Arshaad!
Addua kawai shine namu…..”

Ummu bata bar Mama ba sai da ta tabbatar ta yi convincing d’inta. Sannan suka tsayar akan Ummu zata je ta gayawa Madu Mama kuma ita zata sanar wa Kaka......

Su Sakina suna fita suka nemi waje gefe kad’an dasu Umma mai d’an Inuwa suka zauna suka fara hira, Sakina tanata tsokanar Hudan wadda ta turb’ine fuska kamar zatayi kuka ita ala dole a daina cewa Arshaad saurayin ta ne!
Su Sakina sunata yi mata dariya…..
Umma kuwa suna gefe, ta tak’ark’are sai zabga musu uwar harara take yi, su kam bama su san tana yi ba!
A zuciyarta kuwa cewa take yi “ai dole kuyi farin ciki daku da iyayenku, tunda ga mai kud’i nan yazo yana son d’aya daga cikin ku!!”
Ita babban tashin hankalinta shine d’akin da taga Ummu da Mama sun shige, gashi sun turo Yara waje da alama magana mai mugun mahimmanci suke yi!
Tanaso taji me suke cewa amman ba dama tunda ga Yaran a waje. Gabanta ne yayi mugun fad’uwa a lokacin da zuciyarta ta raya mata ‘to ko dai Arshaad d’inne yace zai turo!! Shiyasa suke ta k’us k’us’. Bata san lokacin da tace
“Kaii!! inaaaa, ai Allah ma ba zai yi haka ba!” A fili sannan da k’arfi!!.
Hakan yasa su Jalila da Anty Zainab juyowa suka kalleta,
suma su Hudan zuba mata idanuwa suka yi suna binta da kallon mamaki.
Sakina ce ta matso kusa da kunnen Hudan tace “Da alama fa matar nan ta fara haukacewa.”
A d’an zabure Hudan tayi saurin juyowa ta rufe mata baki! Ita tsoranta kar su Umman suji shiyasa tashi d’aya duk ta bi ta rikice.
Su kuma su Sakina yadda Hudan ta rikice d’inne ya basu dariya nan kuwa suka hau kyakyatawa Sumayya har da rik’e ciki.

Ai kuwa Umma kamar jira take ta hau zagin su tana “Shegu y’ay’an y’an iska kawai! Uwar ku kuke yiwa dariya ba dai mu ba wallahi.”
Da sauri Sakina tace
“shegu y’ay’an y’an iska suna layin baya! Idan kikaje layin su Kaka ki tambaya kice a nuna miki ‘gidan marasa tarbiyya’ za a nuna miki gidan yana nan kusa da gidan dillaliya!”.

Ba umma ba hatta Jalila mik’ewa tayi za suyi kan Sakina, itama Sakinan ganin haka yasa ta mik’e, jira kawai takeyi su k’araso dan ta lura tabon goshin Jalila ya warke da alamun tana buk’atar wani kuma daman tun ranar da Ya Jaafar ya sumar da Hudan take adduar Allah ya kawo abinda zai had’ata fad’a da su!.

Ita kuwa Jalila ko da ace taje ma ba ta kan Sakina take shirin zata bi ba, tun ranar da taga Hudan da Arshaad take ji kamar ta mak’ureta, Yarinyar da bata yi makaranta ba wata kuchaka da ita amma wai itace har zata yi saurayin da ya fi nata?!
Shiyasa so take kawai ta isa wajen ta samu ko da marin Hudan ne tayi atleast ta san hakan zai rage mata rad’ad’in da take ji a ranta….
Gashi su Umma suma sun gama tunzurata! Ji take kamar ta fashe….

Ganin dai da gaske Umma fad’a zata yi da Sakina ne ya sanya Anty Zainab ta sha gabanta ta rik’e hannayen Jalila sannan ta cewa Umma “haba! haba dan Allah, abun har ya kai haka? Y’ar cikin ki fa! ai girma sai ya fad’i.
Ku zo muje d’aki kuji, dan Allah.”
Shiru Umman ta d’anyi tana kallon su Sakina tana huci sai kuma kawai ta juya a fusace ta shige d’aki.

Sai da Anty Zainab ta dakawa Jalila tsawa tukunna ta wuce tayi d’aki tana mai dannawa Sakina zagi!.

A d’akin su Mama kuwa! Mama har zata fito amma sai Ummu tace mata “ta rabu dasu kawai! In dai Sakina ce daidai take dasu.”
Dan haka suka zauna suka ci gaba da tattaunawa….

Sai da Anty Zainab tayi da gaske tukunna ta iya lallab’a Umma da Jalila suka hak’ura Danna k’ad’an ba sun d’au zafi!k’arshe ma Umma cewa tayi “in taci gaba da zama a cikin gidan, zuciyar ta zata iya bugawa, dan haka suka fita tare da Anty Zainab, aka bar Jalila.
Ko kallon inda suka bi Sakina bata yi ba, dan ita har mamakin Anty Zainab d’in take idan taga tana biyewa su Umma. So take yi ta fita a gidan shiyasa ta cewa Hudan tazo ta rakata ta karb’i kud’i a wajen Ummu suje gidan kitso, dan su Umma suna fita Jalila ta sake fitowa ta zauna a tsakar gidan tana wani ciccin magani kana gani ka san neman bala’i take yi.
Har Sakina ta mik’e zata je d’akin Maman sai Hudan tace “dan Allah su zo su tayata tsefe kanta sai su tafi tare, ba zata iya tsefewa ita kad’ai ba.”
Sakina ce ta dawo tana cewa “Huda Allah ya nunamin ranar da zaki koyi tsefe gashinki da kanki”
Da d’an k’arfi Sakinan ta kuma cewa “Dan ma dai Arshaad d’in naki mai kud’i ne, nasan y’an aiki a ciki harda mai yi miki tsifa zai nemo, idan bayanan ta dinga tayaki, In kuwa yana nan na san shi zai dinga yi miki dan yadda yake nacin son nan naki ba zai bari ki sha wahalar komai ba.”
Ta fad’i hakan tana mai kunce d’ankwalin dake a kan Huda wadda take cewa
“Allah Sakina za muyi fad’a dake ni daina ki daina, banaso.”

Ai kuwa kamar yadda Sakina taso haka maganarta tayi tasiri a kan Jalila, dan har wani huci taga tanayi daga nan inda take a zaune.
Haka nan Sakina tana dariyar mugunta ta hau tsefewa Huda kalbar kanta da suka sauk’a har chan gadon bayanta.

Jalila tana zaune tana kallon su…tabbas ta san tanada kyau dan ana yawan gaya mata
sannan tafi Hudan manyan idanuwa amman idanun huda sunfi nata kyau nesa ba kusa ba dan ita nata idon ba cycle baneba irin dogayen nan ne sannan farare tas kuma kamar tana jin bacci, gata da dogon hanci ga bakinta mai kyau d’an k’arami. Ta san a iya fuska ma Hudan ta fita…maganar kalar fata kam ba’a magana, ta san ita ba bak’a baceba amman ba zata tab’a had’a farinta dana Hudan dayake da sirkin yellow yellow, kuma mai d’aukar ido, ba.

A kyauwun sura kuwa, Hudan a iya yanzu ta kusan kamo ta tsayi duk da ta grime ta, dukda cewa k’irjinta yafi na Huda cika a yanzu amma ta san ko tak’i Allah ba zata had’a hips d’inta dana Huda ba dan Hudan ta fita nesa ba kusa ba dan idan ta juya tana tafiya zaka d’auka wata shahararriyar budurwa ce.
Jalila bata gama sarewa ba sai da ta kalli gashin Hudan da Sakina ke tsefe mata y’ar kalbarta guda biyar har ta kusan gamawa, Gashin bak’i k’irin, gashi har gaban gashinta ga wani saje da takeda shi mai mugun kyau..
Tsayawa Jalila tayi tana kallon gashin dukda ba yau ta fara ganin gashin Hudan ba amman tabbas ta san ya Kara tsayi kwana biyun nan, tana zaune amman kamar zai tab’o k’asa! Bata san lokacin data sa hannu ta shafa nata ba, wanda ya wuce kafad’arta da kyar, d’aurin ta na ture kaga tsiya ta gyara dan ji tayi gaba d’aya ranta ya dagule!
Tabbas a yanzu idan taje wa Arshaad d’inma ba kula ta zai yi ba, ahaka ma bai ga gashin Hudan ba, gaskiya tun kafin ya gani ko ruwan batir ne sai ta kwara mata a gashin wallahi…..
Da sauri ta muk’e ta shige d’aki jin Sakina na cewa “bara inje In d’akko mike ribbon da comb sai in gayawa Ummu In taho mana da kud’in kitson.”
Jalila tana shiga batayi wata wata ba ta d’aga k’asan kayan ta inda take da wani ajiyeyyen almakashi, ai kuwa ta d’auko tayi waje da sauri, ta b’oye a k’asan zaninta.
ji tayi Hudan na cewa Sumayya “dan Allah ta d’auko mata hijabin ta a cikin kayanta”.

Cike da murmushin mugunta tayo inda take zaune kamar zata wuce, tana ganin d’aga labule da shigar Sumayya d’akin Mama ta k’araso inda Hudan take da sauri ta kama gashin kamar zata ribbon!!
Ita Huda da farko dake bata ga tahowarta ba ta d’auka Sakina ce, sai da taji an damk’i gashin da k’arfin sannan ta juyo zata cewa Sakinan baki taje mini ba zaki sa ribbon d’in? Kawai suka had’a ido da Jalila…..
Ai kuwa a take ta fara k’ok’atin kwace kanta, amma kafin ta kufce tuni Jalila ta zaro almakashinta ta daidaita gashin Hudan da iya k’arfinta ta yanke shi kitt!!!!!
Iyakar wanda ta bar mata wanda za a iya had’awa ayi parkin ne kawai, shima kuma jelar sai dai yayi kamar bindin kaza!
Hakan yayi daidai da fitowar Sakina da comb da ribbon a hannunta dan Ummu cewa tayi “su bar kitson sai gobe suje da wuri yanzu yamma tayi”
Huda da sauri ta juyo tana kallon k’asa jin abu ya fad’i, wani razanannen ihu tayi sakamokon ganin gashinta wanwar a k’asa! ita abun ma mugun tsoro ya bata shiyasa
ta shiga shafa kan tana wani irin kuka….
Jalila bata ga k’arasowar Sakina ba sai wani mugun mari n da taji ya sauk’a a kan kumatunta, kafin ta yunk’ura Sakina ta rufeta da duka ta koina….dukda tazarar shekarun dake a tsakaninsu yau kam Jalila ta daku a hannun Sakina dan k’arshe ma ihu Jalilan ta fara tana neman taimako.
Su Mama jin abun yayi yawa dan su duk a tunani su su Umma sunan nan, sanin halinsu yasa suka k’i fita kar su fita su Umman su had’a dasu a fad’an Yara
Shiyasa har Sumayya data shigo d’aukar hijabi suka hanata fita. Amman ihun Jalila daya k’arashe ko Ina lungu da sak’o na gidan ne ya sanya sanya suka fito.
Turus!!! Haka suka ka suka tsaya sakamokon ganin gashin Huda a tsattsaye, ga uban tulin gashi a k’asa tanata k’ok’arin tattarewa tana d’aurawa a kan cinyarta tana kuka, gefe guda kuma ga Sakina a gefe sai jibgar Jalila take yi da iya k’arfinta.
Kafin su k’arasa tuni Ya Junaidu wanda shigowarshi kenan yayi saurin yin kansu Jalilan. Da kyar ya iya kwatar ta a hannun Sakina amman fa ta fasa mata hanci har da baki, ta yi mata jina jina!
Su Mama ne suka hau tambayar ba’asi, nan Sakina ta hau kwararo musu jawabi iya abinda ta gani…
Junaidu ji yayi da ma bai kwaci Jalila ba ji yake kamar ya juya yaci gaba da dukanta tun bama da yaga yadda Hudan take kuka ba abun tausayi,
juyawa yayi kan Jalilan a fad’ace har zai fara magana
kamar kuma wanda ya tuna wani abun sai kawai yace mata “wuce ki shige d’aki”
Tana tafiya ya juyo ya kalli Hudan, wadda take mishi kallon ‘ya yau bai shigar mata ba!’ Gashi kuma abunda aka yi mata yau d’in ma yama fi na kullum…
Da sauri ya d’auke kanshi ya juya ya nufi hanyar d’akin shi ba tare da yace musu komai ba.
Sakina ce tace “Kinga irinta ko!! Saboda Allah ai atlest ya kamata ko fad’a ne yayi mata.”
Mama da Ummu kuwa sarai sun san dalilin da yasa Junaidu yayi hakan, dan labarin abinda ya faru shekaran jiya Mama take bawa Ummu sukaji ihun Jalila!
Shiyasa ba tare da sunce komai ba, suka tattare gashin kawai, suka d’aga Huda suka yi d’aki da ita tanata faman kuka.
Sai da suka rarrasheta da kyar! Aka samu bacci ya kwasheta tukunnan suka tafi bayan Ummu ta tabbatarwa da Mama kafin ta tafi gida sai taje ta samu su Baaba Talatu
kuma daga nan zata fad’a musu zancen makarantar da su Hudan zasu tafi, ta san ko su zasu yarda dan yanzu kam abun na su Umma ya zama hauka k’arara!! Dole a d’auki mataki sannan kuma Hudan tayi nesa da su……
Tanata fad’a baki da kumfa haka ta tusa k’eyar su Sakina suka tafi.
Ita dai Mama tayi shiruu! Dan tama rasa bakin yin magana.


BULAMA ✍️



So da Buri
Free Book
24


Successfully, Kaka da Baba Talatu suka amince da batun makarantar Huda, Kaka shi ya sanar wa Madu wanda shima bai hana ba bai kuma ce taje ba kawai dai ya jinjina kai alamar ya ji kuma ya fahimta.
Kaka ne ya yanke shawarar Hudan ta tafi gidan su Ummu tayi koda sati ne, bayan ya kira Baba da Umma da Jalila yayi musu fad’a sosai!! Sannan ya cewa Jalila “tunda y’ar daba take son ta zama kuma iyayenta sun kasa tsawatar mata to ta tabbata tana gama ssce d’inta ta fito da Miji idan ba hakaba to zai bada hotonta a masallaci duk wanda ya zo kuma shi zata aura koda kuwa gurgu ne!.”
Jalila kuka wiwi haka suka baro gidan Kaka, Umma sai mita take yi wai ‘anyi son kai!’ Idan ba haka ba dan maiyasa ba a yiwa Sakina fad’an dukan da ta yiwa Jalila ba?!.

A Daren ranar da su Ummu suka koma gida suka samu takardun Sakina itama har sun zama ready..
Duk wani preparation na exams d’in yi suke dan Arshaad har wata lesson teacher ya d’auko tayi musu isashshen lesson ranar asabar da lahadi wanda da farko shi yaso yi musu lesson d’in amman sai aka tura shi wani aiki Abuja sai monday da yamma tukunna zai dawo.
Sakina tana fahimtar lesson d’in sosai amman Hudan kam sai dai godiyar Allah,
matsalar da aka samu shine ita lesson teacher bata jin Hausa ita kuma Huda turancin sai a hankali.
Sai da ya zamana
duk abinda lesson teacher ta fad’a sai an mata translating da Hausa! Duk k’ok’ari da hak’uri irin na matar sai da ta k’ule a cikin kwana biyun.
Da kyar Hudan ta tsinci iya abubuwan da zata iya tsinta ranar Litinin kamar yadda aka fad’a Baban Sakina da Ummu suka kaisu makarantar domin su zana jarabawar.


Hudan har kusan kukan murna tayi da taga jarabar tasu zab’i ka tik’a ce! Saboda daman adduar da take ta yi kenan.
Sai dai kuma duk da hakan
da kyar da sid’in goshi ta iya amsa question biyar a cikin guda d’ari biyun da take tunanin ta gane wanda hakan ya d’auketa sama da awa d’aya.
Tayi kokari wajen ganin ta amsa ragowan dan bata so ace ta fad’i jarabawar nan tana mugun son tayi karatu a rayuwarta amman kwata kwata sai ta kasa.
Har kuka tayi a exams hall d’in, bata ankara ba taji ana cewa “20 minutes remaining!!” idan ta fahimta sauran minti ashirin kenan a tashi! Hakan ya sanya
kawai ta rufe idanunta ta karanto sunayen Allah ta nemi nasara da sa’a sannan ta d’aga pencil d’inta ta fara sheding, duk shed d’in da zata yi sai ta kira sunan Allah tukunna ta tik’a…
Haka tayi daga Ar Rahman zuwa As Sabboor, ta sake dawowa Ar Rahman a haka har ta gama wanda yayi dai dai da fara amsar takardun nasu.
Sai da ta tofe takardarta da addua tukunna ta bayar invigilator d’in yana ta tsokanarta.

Kasancewar y’an hall d’in su Sakina sun rigasu shiga yasa tana fitowa suka had’u da Sakina a k’ofa tana jiranta.
Sakina na ganinta ta k’araso da murnarta tana cewa
“Hudan jarabawar tayi sauk’i ko? kinga duk abinda malamarnan ta koya mana kusan duk sun fito, kamar ta sani.”
Da mamaki Hudan ta kalleta kafin tace “Tab! Ni fa biyar kawai na gani irin wanda tayi mana, a maths d’in kuma naga irin wannan mai kamar triangle d’in wanda kika sake koya min da daddare dayawa amman duk sun chanja nambobin.”
Lumshe ido Sakina tayi a hankali sannan ta bud’e, kafin tace mata
“Ai numbers d’in kawai suka chanja, kin dai yi ko?”.
Hudan bata b’oyewa Sakina ba ta gaya mata yadda tayi..
Jikin Sakina duk sai yayi sanyi amman gudun kar ta sace mata guiwa ya sa kawai tayi ta bata kwarin gwiwa.
Suna shirin wucewa aka ce “kowa ya tsaya akwai d’an guntun orientation da za ayi musu, babu isheshshen lokacine amman da it’s sopposed to be for weeks..”
Haka nan suka d’unguma aka fara orientation d’in. Ita kam Huda zuciyarta duk a dagule, bare ma da aka fara orientation d’in nan ta sake ji makarantar ta shiga ranta, duba kuma da abunda ta rafka a exams d’in duk sai hankalinta ya sake tashi.

Sai da aka yi rounding up sannan suka kama hanyar inda su Ummu suka yi parking, Hudan har da y’ar kwallarta,
da kyar Sakina ta d’an lallasheta ta bata kwarin guiwa tukunna aka samu hankalinta ya d’an kwanta.

Suna zuwa nan ma Ummu da Baban Sakina suka shiga tambayarsu, ita dai Hudan k’arshe ma kuka ta

Download complete TXT · Novel page