So Da Buri Book 1
Chapter 26 of 43
saka, dan gani take yi kamar har ta fad’i ne, sai da su Ummu suka yi ta bata baki tukunna ta hak’ura tayi shiru.
A haka dai duk jikinsu yayi sanyi jin Hudan bata yi wani abun kirki ba, suka k’araso gida.
D’aki suka wuce ita da Sakina sai da suka yi wanka suka shirya suka yi waya da Mama sannan suka fito suka ci abinci suka d’an yi hira da kallo sama sama isha nayi kowa ya nufi gado.
Ranar Hudan bata yi bacci ba kwana tayi tsayuwar dare tana rok’on Allah yasa suci jarabawar nan…
Washegari ma da safe haka ta tashi duk jiki ba kwari har dare, kamar jiya yau ma bata yi bacci ba, kwana tayi tana sallah..
Haka ta kasance kullum, itama Sakina daga baya tayi joining d’inta a sallar daren, a haka aka yi sati.
Ranar litinin da yamma sai ga Arshaad ya zo.
Su bama su san yazo ba, suna falo suna kallo, sun gama waya da Mama kenan! Wayar Baban Sakina ta shigo layin Ummu, d’auka tayi suka yi magana bayan ta ajjiye ta kalli Sakina da Huda tace “kuje Babanku yana son ganinku, Arshaad yazo da result d’in jarabawar da kuka yi.”
Da kyar gabansu yanata fad’uwa suka iya mik’ewa suka nufi d’aki, bayan sun d’auko hijabansu suka tafi parlourn Baban Sakinan.
Sakina ce tayi sallama aka basu izinin shiga, ita ta fara shiga sai Hudan a bayanta kansu a k’asa suka gaida Arshaad.
Cikin kulawa ya amsa yanata satar kallon Huda wadda ta kusan yin fitsari a wando tsabar fargaba! So take kawai taji me za a ce.
Baban Sakina ne ya mik’a musu takardun yace “ga results d’inku”
Da kyar Sakina ta iya mik’ewa taje ta amso sannan ta dawo kusa da Huda ta mik’a mata d’aya… har rige rigen bud’ewa suka hau yi.
Hudan tana bud’ewa taga 149/200 sai kuma daga chan k’asa anyi stamping ‘PASS’ da green rubutu!
Sai da ta kalli sama sai taga sunan ba nata bane ashe takardar Sakina ce. Murna ta hau yi dan taji dad’i duk da fargaban rashin ganin nata amman atleast Sakina ta wuce.
Ita kuma Sakina tana bud’ewa taga sunan Huda, da sauri Hudan ta lek’o, bata san lokacin data ce
“Kaiii!! nawa ne kuwa?”
Da taga 185/200 itama an mata stamping ‘PASS’.
Ai kuwa da sauri suka rungume juna a wajen suna dariya suna maimaita kalmar “Alhamdulillah” Hudan har da kwallarta a ranta tana aiyyana
“Yanzu kenan itama zata yi karatu kuma a wannan makarantar y’an gayun data gani zata je tayi karatunta.”
Wani irin farin ciki ne ya lullub’e Arshaad a ransa yace
“So she’s this happy and it’s all because of him? Ai kuwa
In shaa Allah he will make it his life’s mission to keep her happy.”
Ya ji dad’i sosai dan bai san lokacin da shima ya fara murmushin ba. Tabbas Yarinyar tana son karatu, he wonders why iyayenta basu barta tayi ba, ko saboda halin babu ne maybe shiyasa….
Maganar Baban Sakina ce ta katse mishi tunani…
Godiya ya sake yi mishi kafin ya juya ya cewa su Hudan
“murnar ai ta isa haka ko? Ko godiya fa baku yi mishi ba.”
Nan suka had’a baki suka ce
“Mun gode, Allah ya saka da alkhairi.”
“Ameen, ba komai.”
Kawai yace dasu daga nan
Baban Sakina yace su tashi su tafi.
Sai da suka fita Arshaad yace “akwai interview d’in da ake zuwa ayi kuma du, amman dai shi ba wani issue bane tunda sun riga sun yi passing wannan.”
Godiya Baban Sakinan ya k’ara yi mishi.
Bayan Arshaad d’in ya
sanar dashi date na interview d’in ya wuce.
Successfully, suka je suka yi interview d’insu daga nan kuma aka fara preparation d’in tafiya.
Baban su Sakina ne yayi yayi musu provision da komai da komai har books, da farko Asrshaad yaso yi amman ya hanashi kwata kwata.
Sai a lokacin kuma Shuwa taji labarin tafiyar Huda da Sakina makaranta. Ita dai bata cewa Mama komai ba tunda daman ai ta dad’e da cire harkar ta a ranta amma Ummu kam ta sha fad’a! Wai “taje ta had’e kai da y’ar uwar ta sun b’oye mata abu, kuma Baban Sakinan da Mijin mama yayiwa rashin mutunci shine yanzu ta tura shi yake yiwa Maman abu salon wani abun ya sake faruwa ta jawowa kanta matsala a
Auranta!” harda cewa “ta raba Huda da Sakina dan ita tana da nata asalin.” Haka nan dai tayi ta mita.
Ita dai Ummu hak’uri tayi ta bata, sannan tace “Kaka ne yace Hudan taje gidanta ta d’an zauna”
Tukunna Shuwa ta d’an sauk’o.
Sai ranar lahadi tukunna Ummu ta bar Huda tazo gidansu..
Washegari da safe ta saka sabon uniform d’inta ta shirya tsaf sai a lokacin Mama taji kuka ya zo mata, itama Hudan kuka tayita yi ahaka Ummu da Sakina itama data shirya suka zo suka samesu.
Da kyar suka lallashi kansu sannan Ummu ta kai Huda da Sakina d’akin Umma dan su yi mata sallama.
Kasa b’oye bak’in cikin su suka yi, tun ba ma da sukaji sunan makarantar ba!
Ita dai Ummu bata bi ta kansu ba ta sanya suka yi musu sallama suka fito suka tafi.
A gate d’in makarantar suka had’u da Arshaad da k’anwarsa Aaima wadda tana ganinsu Huda ta dinga jansu a jiki kamat sun shekara da sanin juna.
Duk wasu formalities aka yi aka gama sannan Aaima ta sanya aka taya su kai kayansu hostel, sunata kuka ita tayi ta lallashinsu ta jasu suka tafi.
Su Ummu da Arshaad ma suna ganin shigewarsu suka juya suka wuce bayan doguwar godiyar da suka yi ta jera mishi, shi kam abun ma sai ya fara bashi kunya..............
Bayan shekara uku!
After 3 years (present day).
Yau Monday kuma yau su Hudan za suyi graduating.
Arshaad tare da Aaima suka zo, su suka fara zuwan ma su Huda dan sun riga su Ummu ma zuwa.................
Bayan an kai su Sakina makarantar shekaru uku da suka wuce Aaima ce ta tsaya a kansu especially Huda har
personal lesson take yi musu.
Tana son Yaran ba kad’an ba, ranar graduation d’inta kam sunci kuka, da kyar suka warware daga baya suka yi friends.
Daga nesa ta hango su cikin graduation gown d’insu sun yi kyau sosai sun zama y’an
mata sun yi fresh hasken
fatar su ya k’ara fitowa.
Basu lura da ita ba saboda duba wayar da suka ara domin kiran su Ummu da suke ta k’ok’arin yi, dan sunga har an kusan farawa amman shiru basu k’araso ba.
Sai da Aaima ta k’araso ta dafa kafad’ar Huda, tukunna
suka lura da ita.
Ai kuwa da sauri suka yi hugging d’inta suka hau murna, nan shima Arshaad ya k’araso, da murmushi a kan fuskarsa yake bin Hudan da kallo… Dukda cewa duk visiting yakan zo ya ganta amman yau d’in sai yaga gaba d’aya ta chanza, tayi wani kyau kamar yayi irin shekaru d’innan bai ganta ba.
Sakina ce ta fara gaidashi sannan itama Hudan ta sunkuyar da kanta ta gaidashi
dan ita har ga Allah yanzu wata kunyar shi take ji saboda tun lokacin da zasu fara zaman extension da yazo kawo musu books da abubuwan buk’ata yake gaya ‘yana sonta’ shikenan har yau bata iya ko had’a ido da shi.
Murmushi yayi ya amsa gaisuwar yana mamakin kunya irin ta Huda.
Sallamar da su Ummu suka yi ne ya juyo da hankalinsu..
Tun da suke zo makarantar sau biyu taje gida hutu a lokacin tana ss1, bayan nan a gidansu Sakina take hutunta kuma Mama bai fi taje sau d’aya ba dan ko visiting Baba hanata zuwa yake yi.
Shiyasa yau take ta adduar Allah yasa azo da ita, ranar farin ciki ya kamata ace tana kusa da ita.
Ai kuwa tana d’agowa da Maman suka fara had’a ido, ba tayi wata wata ba ta tafi da gudu ta fad’a jikinta, ji tayi kawai kuka ya sub’uce mata
Itama Maman harda y’ar kwallarta amman sai tayi saurin sharewa….
Sai da ta cewa Hudan “zata koma idan bata yi shiru ba”tukunna tayi shiru ta goge hawayen ta tana mai sauk’e tagwayen ajiyar zuciya.
Aaima ce ta fara matsowa ta gaida Mama dan ko ba’a fad’a mata ba ta san itace mahaifiyar Huda, daga nan
ta gaida Baban su Sakina da Ummu sannan ta hau tsokanar Sumayya tana cewa “ta zama y’a mata” ita kuma Sumayyan tana murmushi tana cewa “bata so” daman sun saba.
Sai da Sakina ta k’arasa dai dai gaban Arshaad ta tsaya tayi snapping fingers d’inta tukunna yayi firgigit! Ya kawar da idanunsa daga kan Mama da ya kafe da idanu, sannan yayi saurin juyo da hankalinshi kan Sakina yana murmushi.
Kallon da yaga Sakina tana yi mishi tana kuma waiwayawa tana kallon inda taga yana kallo ne yasa shi cewa
“Itane Maman Huda??”
Murmushi Sakina tayi sannan tace “Ai ni na d’auka wata kake kallo, baka ga har na had’e rai ba? Ashe Mama kake kallo.”
Ta k’arashe maganar tata tana murmushi.
Shima murmushin yayi sannan yace “kina tayata kishi bayan ita ko kishin nawa batayi, I don’t even think ma tana sona!”
Yayi maganar yana langab’ar da kai yanayin kalar tausayi.
Dariya Sakina tayi sannan ta d’an matso ta sa hannunta ta kare bakinta ta gefe kamar zatayi rad’a, tace “Kar ka damu zan yi maka campaign mai zafi!”
Dariya yayi yace
“Woow!! really? tnx sis, you are the best!”
Yayi maganar yana yi mata tumbs up.
Dariya tayi tana d’aga kanta alamar ‘eh’ sannan at the same time tana d’aga girar ta,
hakan yasa gaba d’aya suka kwashe da dariya, sannan
tace mishi zo muje ka gaisa da surukarka, yau ne had’uwar ku ta farko so you better act decent!”
Dariya kawai yayi, sannan ya bi bayan ta suka k’arasa inda su Maman suke tsaye.
Sai da ya d’an russuna sannan ya gaida Mama.
Cike da kunya ta amsa dan tunda ya nufo su Ummu tace mata “ga Arshaad”
Su ummu ma cikin ladabi ya gaida su suka amsa mishi da kulawa.
Daga nan suka d’unguma gaba d’ayan su suka yi hall d’in da ake taron bayan sun gaggaisa cikin mutunta juna…
Suna zuwa kamar su kad’ai ake jira nan aka fara gudanar da programs of event, Hudan aka kira ta bada speech wadda in mutun yaji kalar turanci da accent dining Hudan sai yace ba ita bace ba.
Bayan ta gama aka fara raba gifts sai da ta karb’i hud’u!!Best in English
Physics
Most decent da
most beautiful.
Sakina kuma ta karb’i
Best in maths
Most popular da
Da gift d’inta na social prefect da aka had’a mata.
Mama dai sai share kwalla take yi sunata murna.
Bayan nan akayi pictures da ragowan abubuwa daga nan kowa ya watse.
A waje ma sai da Aaima ta sake yi musu kowa
da kowa
Sannan tace sai Huda ta tsaya anyi mata da Arshaad, da kyar
ta tsaya kuwa dan sai da ma ta fakaici idon su Mama taga sun d’an juyo sun basu baya.
Haka nan cikin farin ciki suka nufi gida.
A gidan su Sakina suka yada zango.
Arshaad a falon Baban su Sakina suka tsaya, a nan aka kai musu ruwa da abinci suka ci.
Su Hudan suna cikin cin abincin suma Baban Sakina ya shigo ya cewa Hudan “taje falonshi” sannan ya nufi hanyar d’akin shi. Sai da Ummu ta sake maimaita mata tukunna ta mik’e kamar munafuka tana jan Sakina tana kallon Mama wadda ta d’auke kai tayi kamar bata ji su ba.
Sai da suka je d’aki suka chanzo hijabai sannan suka nufi falon….
Babu yadda Sakina bata yi da ita akan ta fesa turare ta shafa powder ba amman fur tak’i! Haka suka fito Sakina tana ta faman b’alla mata harara ita kuwa Hudan sai dariya take yi. Suna zuwa dai dai k’ofar falon kuwa bayan sun bud’e Sakina
tasa duka k’arfinta ta turata ciki sannan ta juya da gudu tana yi mata dariya itama…
Cike da kunya ta d’an juyo tana kallon Arshaad wanda shima dariyar yake yi mata dan ya san wannan aikin Sakina ne.
Turo baki tayi kafin tace
“Ya arshaad kana gani ta turoni kuma baka ce min sannu ba kake min dariya?”
Murmushi yayi kafin yace
“Nasani ko tirjiya kika yi? Kika ce ba zaki zo wajena ba shiyasa ta turoki?”.
Sake turo bakin tayi.
Ganin haka yasa yayi saurin kama bakin nashi da y’an yatsun shi yana dariya k’asa k’asa, kafin yace “Afuwan wifey! Zo ki zauna tou nayi
shiru ba zan sake cewa komai ba.”
Yayi maganar yana mata nuni da gaban kujerar da take facing d’inshi.
Da sauri taja gaban hijabinta ta rufe idanunta sannan tazo ta zauna a wajen da ya nuna mata ta sake sunnar da kanta k’asa.
Tafi minti uku a haka jin shiru yasa ta d’ago kanta a hankali a tunaninta ko wani abun yake yi a waya amman tana d’agowa sukai ido biyu dashi da sauri ta kuma sunkuyar da kanta.
Murmushi gefen baki yayi kafin yace “Hudan”.
“Um”
Tace.
“Hudan”
Ya sake kiranta.
A hankali tace
“Na’am”
Sai da ya d’an yi jim!
Tukunna yace
“Pls ki cire wannan hijabin daga idonki, I want to talk to you about something that is very important, kinji”.
A hankali ta d’an jashi sama, face d’inta ya fito.
Ajiyan zuciya ya sauk’e kafin yace “Last time da naje wajen ki a school!
I told u what i feel towards you amman baki ce komai ba har yanzu.
Inaso in san matsayina
dan i think is about time da ya kamata in san where i stand ko?”
Yayi maganar yana d’an lek’o fuskarta.
Shirun da tayi ne yasa yace
“Um? Please don’t say you need more time Hudan, Allah kad’ai ya san what I’m going through!
Ko menene just say it, in ma bakya sona ne ki fad’a min zan d’auki k’addara.”
A hankali yaji tace
“Ya Arshaad nifa ban ce bana sonka ba.”
Zuciyan shi har wani bugawa take yi, cikin k’aguwa da son jin amsar ta yace “Does this means kina sona?”
Murmushi tayi sannan ta d’aga kanta alamar ‘eh’
“Alhamdulillah”
Taji ya furta tare da sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya
kafin ya sake cewa “zaki aureni right?”
Murmushi tayi sannan ta d’aga kanta still alamar ‘yes’
Kunyace taji tana shirin nutsar da ita shiyasa ta tashi da sauri ta fice a falon, tana jinsa yana cewa “No pls wait bamu k’arasa ba”
amman ta fice cikin sauri….
Arshaad ya kusan 1 hour a parlourn shi kad’ai a zaune yanata murmushi da day dreaming na yadda rayuwanshi zai kasance tare da Huda.
Yanata plans shi kad’ai
kala kala, bai san lokaci ya ja har haka ba!
Kiran sallar la’asar ne ya fargar dashi, gashi yanada meeting d’in gaggawa a company wanda Granpa ya turo mishi d’azu akan za suyi su biyu @5pm! Bai san akan menene ba.
Da sauri ya d’au wayar shi ya buga kiran Aaima yace “ta sameshi a mota yanzu yanzu.”
A gurguje Aaima ta yiwa su Mama sallama, dan taji kamar Yayan nata yana cikin sauri ne.
Tana zuwa kuwa ta fad’a motar yaja suka fita daga gidan…
Gudun da taga yana yi ne ya sanya ta tambayeshi
Nan yake ce mata “Granpa ne yace mishi ya sameshi a office bai san mai ya fari ba.”
“Allah yasa lafiya.”
shine abinda Aaima ta fad’a sannan ta jingina da jikin kujera ta lumshe idanunta ta fara tunanin Auwal…
Yau kwana biyar kenan bata gansa ba kuka ko ta kirashi baya d’auka! Daman kwana biyun nan rashin mutunci yake ji dashi, dan kawai yace tayi mishi abu tak’i yi! Ita wani abun na Auwal sai take ganin kamar iskancine amman friends d’inta na nile su ce mata suke yi ‘hakan wai wayewa ce, its a normal thing and dan yana sonta ne shiyasa yake demanding, inda iskanci ya so yi to da ba zai na demanding peck da kisses ba, he would have ask for something different!’.
To ko dai tayi mishi kawai tunda ba wani abun bane ba, dan ita dai har ga Allah
Allah ya d’aura mata son Auwal, bama ta san wanne irin so take yi mishi ba! She don’t ever want to see him angry,
besides she is in level 2, tana ganin yadda mates d’inta suke kula da samarin su......
Maganar Arshaad ce ta katse mata tunani jin yana cewa
“Wai tunanin me kike yi ne haka?”
Cikin fad’a.
Firgigit!! Ta bud’e idanunta.
K’ura mata ido yayi sannan a hankali yace “anjima around 9, ki sameni a parlourna.”
“To”
kawai tace, sannan ta bud’e k’ofar ta fita, binta yayi da kallo har ta shige sannan ya nufi mosque d’in jikin estate d’in yayi sallah, yana idarwa ya d’anyi addua, sannan ya fito ya shiga mota ya nufi office....
Yana zuwa bai tsaya b’ata lokaci ba ya nufi hanyar office d’in da yake mallakinsa a cikin building d’in dan Granpa yace mishi “a nan zasu had’u”
kuma kamar yaga d’aya daga cikin motocin da Granpa d’in yake hawa a parking lot shiyasa a
gaggauce ya dinga amsa gaisuwar securities da wasu ma’aikatan da suke ta gaidashi yana mai k’arsawa office d’in nasa.
Key ya zaro zai bud’e k’ofar amman yana d’aurawa yaga ashema k’ofar a bud’e ne hakan ya bashi tabbacin Granpa ya rigashi k’arasowa kenan!! Agogon hannunshi ya kalla yaga ya k’ara 5 minutes akan time d’in da yace masa ya sameshi.
Ajiyar zuciya ya sauk’e kawai yayi ‘bismillah’ ya tura kai ya shiga.
Yana shiga ya hango Granpa a kan kujerar shi ya juya baya.
Sai da yayi addua sannan ya k’arasa inda yake…
D’an gyaran murya yayi sannan cikin girmamawa ya gaidashi.
Ba tare da ya amsa gaisuwar tashi ba yace “I’ve waited for you, for six minutes!”
Arshaad zai yi magana Granpa ya katseshi ta hanyar mik’o mishi wasu takardun. Karb’a
yayi ya fara dubawa……
Cikin no nonsense voice d’inshi yaji Granpa d’in yana cewa “3 days ago mun samu embezzlement, ko kuma in ce theft from an insider, munyi ta bincike da ni da Auwal at long
A haka dai duk jikinsu yayi sanyi jin Hudan bata yi wani abun kirki ba, suka k’araso gida.
D’aki suka wuce ita da Sakina sai da suka yi wanka suka shirya suka yi waya da Mama sannan suka fito suka ci abinci suka d’an yi hira da kallo sama sama isha nayi kowa ya nufi gado.
Ranar Hudan bata yi bacci ba kwana tayi tsayuwar dare tana rok’on Allah yasa suci jarabawar nan…
Washegari ma da safe haka ta tashi duk jiki ba kwari har dare, kamar jiya yau ma bata yi bacci ba, kwana tayi tana sallah..
Haka ta kasance kullum, itama Sakina daga baya tayi joining d’inta a sallar daren, a haka aka yi sati.
Ranar litinin da yamma sai ga Arshaad ya zo.
Su bama su san yazo ba, suna falo suna kallo, sun gama waya da Mama kenan! Wayar Baban Sakina ta shigo layin Ummu, d’auka tayi suka yi magana bayan ta ajjiye ta kalli Sakina da Huda tace “kuje Babanku yana son ganinku, Arshaad yazo da result d’in jarabawar da kuka yi.”
Da kyar gabansu yanata fad’uwa suka iya mik’ewa suka nufi d’aki, bayan sun d’auko hijabansu suka tafi parlourn Baban Sakinan.
Sakina ce tayi sallama aka basu izinin shiga, ita ta fara shiga sai Hudan a bayanta kansu a k’asa suka gaida Arshaad.
Cikin kulawa ya amsa yanata satar kallon Huda wadda ta kusan yin fitsari a wando tsabar fargaba! So take kawai taji me za a ce.
Baban Sakina ne ya mik’a musu takardun yace “ga results d’inku”
Da kyar Sakina ta iya mik’ewa taje ta amso sannan ta dawo kusa da Huda ta mik’a mata d’aya… har rige rigen bud’ewa suka hau yi.
Hudan tana bud’ewa taga 149/200 sai kuma daga chan k’asa anyi stamping ‘PASS’ da green rubutu!
Sai da ta kalli sama sai taga sunan ba nata bane ashe takardar Sakina ce. Murna ta hau yi dan taji dad’i duk da fargaban rashin ganin nata amman atleast Sakina ta wuce.
Ita kuma Sakina tana bud’ewa taga sunan Huda, da sauri Hudan ta lek’o, bata san lokacin data ce
“Kaiii!! nawa ne kuwa?”
Da taga 185/200 itama an mata stamping ‘PASS’.
Ai kuwa da sauri suka rungume juna a wajen suna dariya suna maimaita kalmar “Alhamdulillah” Hudan har da kwallarta a ranta tana aiyyana
“Yanzu kenan itama zata yi karatu kuma a wannan makarantar y’an gayun data gani zata je tayi karatunta.”
Wani irin farin ciki ne ya lullub’e Arshaad a ransa yace
“So she’s this happy and it’s all because of him? Ai kuwa
In shaa Allah he will make it his life’s mission to keep her happy.”
Ya ji dad’i sosai dan bai san lokacin da shima ya fara murmushin ba. Tabbas Yarinyar tana son karatu, he wonders why iyayenta basu barta tayi ba, ko saboda halin babu ne maybe shiyasa….
Maganar Baban Sakina ce ta katse mishi tunani…
Godiya ya sake yi mishi kafin ya juya ya cewa su Hudan
“murnar ai ta isa haka ko? Ko godiya fa baku yi mishi ba.”
Nan suka had’a baki suka ce
“Mun gode, Allah ya saka da alkhairi.”
“Ameen, ba komai.”
Kawai yace dasu daga nan
Baban Sakina yace su tashi su tafi.
Sai da suka fita Arshaad yace “akwai interview d’in da ake zuwa ayi kuma du, amman dai shi ba wani issue bane tunda sun riga sun yi passing wannan.”
Godiya Baban Sakinan ya k’ara yi mishi.
Bayan Arshaad d’in ya
sanar dashi date na interview d’in ya wuce.
Successfully, suka je suka yi interview d’insu daga nan kuma aka fara preparation d’in tafiya.
Baban su Sakina ne yayi yayi musu provision da komai da komai har books, da farko Asrshaad yaso yi amman ya hanashi kwata kwata.
Sai a lokacin kuma Shuwa taji labarin tafiyar Huda da Sakina makaranta. Ita dai bata cewa Mama komai ba tunda daman ai ta dad’e da cire harkar ta a ranta amma Ummu kam ta sha fad’a! Wai “taje ta had’e kai da y’ar uwar ta sun b’oye mata abu, kuma Baban Sakinan da Mijin mama yayiwa rashin mutunci shine yanzu ta tura shi yake yiwa Maman abu salon wani abun ya sake faruwa ta jawowa kanta matsala a
Auranta!” harda cewa “ta raba Huda da Sakina dan ita tana da nata asalin.” Haka nan dai tayi ta mita.
Ita dai Ummu hak’uri tayi ta bata, sannan tace “Kaka ne yace Hudan taje gidanta ta d’an zauna”
Tukunna Shuwa ta d’an sauk’o.
Sai ranar lahadi tukunna Ummu ta bar Huda tazo gidansu..
Washegari da safe ta saka sabon uniform d’inta ta shirya tsaf sai a lokacin Mama taji kuka ya zo mata, itama Hudan kuka tayita yi ahaka Ummu da Sakina itama data shirya suka zo suka samesu.
Da kyar suka lallashi kansu sannan Ummu ta kai Huda da Sakina d’akin Umma dan su yi mata sallama.
Kasa b’oye bak’in cikin su suka yi, tun ba ma da sukaji sunan makarantar ba!
Ita dai Ummu bata bi ta kansu ba ta sanya suka yi musu sallama suka fito suka tafi.
A gate d’in makarantar suka had’u da Arshaad da k’anwarsa Aaima wadda tana ganinsu Huda ta dinga jansu a jiki kamat sun shekara da sanin juna.
Duk wasu formalities aka yi aka gama sannan Aaima ta sanya aka taya su kai kayansu hostel, sunata kuka ita tayi ta lallashinsu ta jasu suka tafi.
Su Ummu da Arshaad ma suna ganin shigewarsu suka juya suka wuce bayan doguwar godiyar da suka yi ta jera mishi, shi kam abun ma sai ya fara bashi kunya..............
Bayan shekara uku!
After 3 years (present day).
Yau Monday kuma yau su Hudan za suyi graduating.
Arshaad tare da Aaima suka zo, su suka fara zuwan ma su Huda dan sun riga su Ummu ma zuwa.................
Bayan an kai su Sakina makarantar shekaru uku da suka wuce Aaima ce ta tsaya a kansu especially Huda har
personal lesson take yi musu.
Tana son Yaran ba kad’an ba, ranar graduation d’inta kam sunci kuka, da kyar suka warware daga baya suka yi friends.
Daga nesa ta hango su cikin graduation gown d’insu sun yi kyau sosai sun zama y’an
mata sun yi fresh hasken
fatar su ya k’ara fitowa.
Basu lura da ita ba saboda duba wayar da suka ara domin kiran su Ummu da suke ta k’ok’arin yi, dan sunga har an kusan farawa amman shiru basu k’araso ba.
Sai da Aaima ta k’araso ta dafa kafad’ar Huda, tukunna
suka lura da ita.
Ai kuwa da sauri suka yi hugging d’inta suka hau murna, nan shima Arshaad ya k’araso, da murmushi a kan fuskarsa yake bin Hudan da kallo… Dukda cewa duk visiting yakan zo ya ganta amman yau d’in sai yaga gaba d’aya ta chanza, tayi wani kyau kamar yayi irin shekaru d’innan bai ganta ba.
Sakina ce ta fara gaidashi sannan itama Hudan ta sunkuyar da kanta ta gaidashi
dan ita har ga Allah yanzu wata kunyar shi take ji saboda tun lokacin da zasu fara zaman extension da yazo kawo musu books da abubuwan buk’ata yake gaya ‘yana sonta’ shikenan har yau bata iya ko had’a ido da shi.
Murmushi yayi ya amsa gaisuwar yana mamakin kunya irin ta Huda.
Sallamar da su Ummu suka yi ne ya juyo da hankalinsu..
Tun da suke zo makarantar sau biyu taje gida hutu a lokacin tana ss1, bayan nan a gidansu Sakina take hutunta kuma Mama bai fi taje sau d’aya ba dan ko visiting Baba hanata zuwa yake yi.
Shiyasa yau take ta adduar Allah yasa azo da ita, ranar farin ciki ya kamata ace tana kusa da ita.
Ai kuwa tana d’agowa da Maman suka fara had’a ido, ba tayi wata wata ba ta tafi da gudu ta fad’a jikinta, ji tayi kawai kuka ya sub’uce mata
Itama Maman harda y’ar kwallarta amman sai tayi saurin sharewa….
Sai da ta cewa Hudan “zata koma idan bata yi shiru ba”tukunna tayi shiru ta goge hawayen ta tana mai sauk’e tagwayen ajiyar zuciya.
Aaima ce ta fara matsowa ta gaida Mama dan ko ba’a fad’a mata ba ta san itace mahaifiyar Huda, daga nan
ta gaida Baban su Sakina da Ummu sannan ta hau tsokanar Sumayya tana cewa “ta zama y’a mata” ita kuma Sumayyan tana murmushi tana cewa “bata so” daman sun saba.
Sai da Sakina ta k’arasa dai dai gaban Arshaad ta tsaya tayi snapping fingers d’inta tukunna yayi firgigit! Ya kawar da idanunsa daga kan Mama da ya kafe da idanu, sannan yayi saurin juyo da hankalinshi kan Sakina yana murmushi.
Kallon da yaga Sakina tana yi mishi tana kuma waiwayawa tana kallon inda taga yana kallo ne yasa shi cewa
“Itane Maman Huda??”
Murmushi Sakina tayi sannan tace “Ai ni na d’auka wata kake kallo, baka ga har na had’e rai ba? Ashe Mama kake kallo.”
Ta k’arashe maganar tata tana murmushi.
Shima murmushin yayi sannan yace “kina tayata kishi bayan ita ko kishin nawa batayi, I don’t even think ma tana sona!”
Yayi maganar yana langab’ar da kai yanayin kalar tausayi.
Dariya Sakina tayi sannan ta d’an matso ta sa hannunta ta kare bakinta ta gefe kamar zatayi rad’a, tace “Kar ka damu zan yi maka campaign mai zafi!”
Dariya yayi yace
“Woow!! really? tnx sis, you are the best!”
Yayi maganar yana yi mata tumbs up.
Dariya tayi tana d’aga kanta alamar ‘eh’ sannan at the same time tana d’aga girar ta,
hakan yasa gaba d’aya suka kwashe da dariya, sannan
tace mishi zo muje ka gaisa da surukarka, yau ne had’uwar ku ta farko so you better act decent!”
Dariya kawai yayi, sannan ya bi bayan ta suka k’arasa inda su Maman suke tsaye.
Sai da ya d’an russuna sannan ya gaida Mama.
Cike da kunya ta amsa dan tunda ya nufo su Ummu tace mata “ga Arshaad”
Su ummu ma cikin ladabi ya gaida su suka amsa mishi da kulawa.
Daga nan suka d’unguma gaba d’ayan su suka yi hall d’in da ake taron bayan sun gaggaisa cikin mutunta juna…
Suna zuwa kamar su kad’ai ake jira nan aka fara gudanar da programs of event, Hudan aka kira ta bada speech wadda in mutun yaji kalar turanci da accent dining Hudan sai yace ba ita bace ba.
Bayan ta gama aka fara raba gifts sai da ta karb’i hud’u!!Best in English
Physics
Most decent da
most beautiful.
Sakina kuma ta karb’i
Best in maths
Most popular da
Da gift d’inta na social prefect da aka had’a mata.
Mama dai sai share kwalla take yi sunata murna.
Bayan nan akayi pictures da ragowan abubuwa daga nan kowa ya watse.
A waje ma sai da Aaima ta sake yi musu kowa
da kowa
Sannan tace sai Huda ta tsaya anyi mata da Arshaad, da kyar
ta tsaya kuwa dan sai da ma ta fakaici idon su Mama taga sun d’an juyo sun basu baya.
Haka nan cikin farin ciki suka nufi gida.
A gidan su Sakina suka yada zango.
Arshaad a falon Baban su Sakina suka tsaya, a nan aka kai musu ruwa da abinci suka ci.
Su Hudan suna cikin cin abincin suma Baban Sakina ya shigo ya cewa Hudan “taje falonshi” sannan ya nufi hanyar d’akin shi. Sai da Ummu ta sake maimaita mata tukunna ta mik’e kamar munafuka tana jan Sakina tana kallon Mama wadda ta d’auke kai tayi kamar bata ji su ba.
Sai da suka je d’aki suka chanzo hijabai sannan suka nufi falon….
Babu yadda Sakina bata yi da ita akan ta fesa turare ta shafa powder ba amman fur tak’i! Haka suka fito Sakina tana ta faman b’alla mata harara ita kuwa Hudan sai dariya take yi. Suna zuwa dai dai k’ofar falon kuwa bayan sun bud’e Sakina
tasa duka k’arfinta ta turata ciki sannan ta juya da gudu tana yi mata dariya itama…
Cike da kunya ta d’an juyo tana kallon Arshaad wanda shima dariyar yake yi mata dan ya san wannan aikin Sakina ne.
Turo baki tayi kafin tace
“Ya arshaad kana gani ta turoni kuma baka ce min sannu ba kake min dariya?”
Murmushi yayi kafin yace
“Nasani ko tirjiya kika yi? Kika ce ba zaki zo wajena ba shiyasa ta turoki?”.
Sake turo bakin tayi.
Ganin haka yasa yayi saurin kama bakin nashi da y’an yatsun shi yana dariya k’asa k’asa, kafin yace “Afuwan wifey! Zo ki zauna tou nayi
shiru ba zan sake cewa komai ba.”
Yayi maganar yana mata nuni da gaban kujerar da take facing d’inshi.
Da sauri taja gaban hijabinta ta rufe idanunta sannan tazo ta zauna a wajen da ya nuna mata ta sake sunnar da kanta k’asa.
Tafi minti uku a haka jin shiru yasa ta d’ago kanta a hankali a tunaninta ko wani abun yake yi a waya amman tana d’agowa sukai ido biyu dashi da sauri ta kuma sunkuyar da kanta.
Murmushi gefen baki yayi kafin yace “Hudan”.
“Um”
Tace.
“Hudan”
Ya sake kiranta.
A hankali tace
“Na’am”
Sai da ya d’an yi jim!
Tukunna yace
“Pls ki cire wannan hijabin daga idonki, I want to talk to you about something that is very important, kinji”.
A hankali ta d’an jashi sama, face d’inta ya fito.
Ajiyan zuciya ya sauk’e kafin yace “Last time da naje wajen ki a school!
I told u what i feel towards you amman baki ce komai ba har yanzu.
Inaso in san matsayina
dan i think is about time da ya kamata in san where i stand ko?”
Yayi maganar yana d’an lek’o fuskarta.
Shirun da tayi ne yasa yace
“Um? Please don’t say you need more time Hudan, Allah kad’ai ya san what I’m going through!
Ko menene just say it, in ma bakya sona ne ki fad’a min zan d’auki k’addara.”
A hankali yaji tace
“Ya Arshaad nifa ban ce bana sonka ba.”
Zuciyan shi har wani bugawa take yi, cikin k’aguwa da son jin amsar ta yace “Does this means kina sona?”
Murmushi tayi sannan ta d’aga kanta alamar ‘eh’
“Alhamdulillah”
Taji ya furta tare da sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya
kafin ya sake cewa “zaki aureni right?”
Murmushi tayi sannan ta d’aga kanta still alamar ‘yes’
Kunyace taji tana shirin nutsar da ita shiyasa ta tashi da sauri ta fice a falon, tana jinsa yana cewa “No pls wait bamu k’arasa ba”
amman ta fice cikin sauri….
Arshaad ya kusan 1 hour a parlourn shi kad’ai a zaune yanata murmushi da day dreaming na yadda rayuwanshi zai kasance tare da Huda.
Yanata plans shi kad’ai
kala kala, bai san lokaci ya ja har haka ba!
Kiran sallar la’asar ne ya fargar dashi, gashi yanada meeting d’in gaggawa a company wanda Granpa ya turo mishi d’azu akan za suyi su biyu @5pm! Bai san akan menene ba.
Da sauri ya d’au wayar shi ya buga kiran Aaima yace “ta sameshi a mota yanzu yanzu.”
A gurguje Aaima ta yiwa su Mama sallama, dan taji kamar Yayan nata yana cikin sauri ne.
Tana zuwa kuwa ta fad’a motar yaja suka fita daga gidan…
Gudun da taga yana yi ne ya sanya ta tambayeshi
Nan yake ce mata “Granpa ne yace mishi ya sameshi a office bai san mai ya fari ba.”
“Allah yasa lafiya.”
shine abinda Aaima ta fad’a sannan ta jingina da jikin kujera ta lumshe idanunta ta fara tunanin Auwal…
Yau kwana biyar kenan bata gansa ba kuka ko ta kirashi baya d’auka! Daman kwana biyun nan rashin mutunci yake ji dashi, dan kawai yace tayi mishi abu tak’i yi! Ita wani abun na Auwal sai take ganin kamar iskancine amman friends d’inta na nile su ce mata suke yi ‘hakan wai wayewa ce, its a normal thing and dan yana sonta ne shiyasa yake demanding, inda iskanci ya so yi to da ba zai na demanding peck da kisses ba, he would have ask for something different!’.
To ko dai tayi mishi kawai tunda ba wani abun bane ba, dan ita dai har ga Allah
Allah ya d’aura mata son Auwal, bama ta san wanne irin so take yi mishi ba! She don’t ever want to see him angry,
besides she is in level 2, tana ganin yadda mates d’inta suke kula da samarin su......
Maganar Arshaad ce ta katse mata tunani jin yana cewa
“Wai tunanin me kike yi ne haka?”
Cikin fad’a.
Firgigit!! Ta bud’e idanunta.
K’ura mata ido yayi sannan a hankali yace “anjima around 9, ki sameni a parlourna.”
“To”
kawai tace, sannan ta bud’e k’ofar ta fita, binta yayi da kallo har ta shige sannan ya nufi mosque d’in jikin estate d’in yayi sallah, yana idarwa ya d’anyi addua, sannan ya fito ya shiga mota ya nufi office....
Yana zuwa bai tsaya b’ata lokaci ba ya nufi hanyar office d’in da yake mallakinsa a cikin building d’in dan Granpa yace mishi “a nan zasu had’u”
kuma kamar yaga d’aya daga cikin motocin da Granpa d’in yake hawa a parking lot shiyasa a
gaggauce ya dinga amsa gaisuwar securities da wasu ma’aikatan da suke ta gaidashi yana mai k’arsawa office d’in nasa.
Key ya zaro zai bud’e k’ofar amman yana d’aurawa yaga ashema k’ofar a bud’e ne hakan ya bashi tabbacin Granpa ya rigashi k’arasowa kenan!! Agogon hannunshi ya kalla yaga ya k’ara 5 minutes akan time d’in da yace masa ya sameshi.
Ajiyar zuciya ya sauk’e kawai yayi ‘bismillah’ ya tura kai ya shiga.
Yana shiga ya hango Granpa a kan kujerar shi ya juya baya.
Sai da yayi addua sannan ya k’arasa inda yake…
D’an gyaran murya yayi sannan cikin girmamawa ya gaidashi.
Ba tare da ya amsa gaisuwar tashi ba yace “I’ve waited for you, for six minutes!”
Arshaad zai yi magana Granpa ya katseshi ta hanyar mik’o mishi wasu takardun. Karb’a
yayi ya fara dubawa……
Cikin no nonsense voice d’inshi yaji Granpa d’in yana cewa “3 days ago mun samu embezzlement, ko kuma in ce theft from an insider, munyi ta bincike da ni da Auwal at long