So Da Buri Book 1
Chapter 27 of 43
last mun gano waye!”
Dai dai nan idanun Arshaad suka kai kan abunda takardar ta k’unsa!
Gabanshi ne ya hau fad’uwa babu k’akk’autawa!
Naira miliyan dubu d’ari tara ne suka b’ata! Kuma shine yayi signing, gashi kuma a d’ayan takardan an nuna ya shiga personnel account d’inshi!.
Da sauri ya d’ago ya kalli Granpa a mugun firgice yace
Grandpa, i don’t know anything about this! Maybe mistake ne ko kuma someone is trying to frame me, amman wallahi i have no clue......”
Kura mishi idon da yaga Granpa yayi ne ya sanya shi yin shiru.
Cikin kakkausar murya Granpa yace “Who’s trying to frame you?
Um?
Ni ko Auwal?
Use your words!
Dan mune muka yi binciken, just the two of us!.”
Shiruuu, Arshaad yayi ya sunkuyar da kanshi k’asa.
Granpa yaci gaba da cewa
“For your information nayi suspending Auwal d’in kanshi for a week!
Did you know wat he did??
I ask him to investigate, and after he finds out kai ne b’arawon he hid it from me! Bawan Allah n nan was even trying to pay back the money from his own pocket duk dan kar in gane kaine mu samu matsala da kai….”
Da k’arfi Arshaad ya runtse idanunshi, har ga Allah Auwal fa ya fara kaishi mai’ura da makirce makircensa!
Shi da yake a matsayin MD amma wai yana yi mishi bak’in cikin treasurer d’in da aka bashi! For wat!??
Sai kace ba y’an uwa suke ba?
Maganar Granpa ne ya dawo dashi daga tunanin daya fad’a
jin yana ce mishi “take this!”
Hannu Arshaad yasa ya karb’a jikinshi duk yayi sanyi.
Mik’ewa Granpa yayi ya gyara suit d’in jikinshi, sannan ya fara tafiya yana dogara sandarshi, sai da ya kai bak’in k’ofa ya juyo ya kalli Arshaad
Sai a lokacin yaga bai ma duba takardarba, yana nan tsaye yadda ya barshi ya lumshe idanuwanshi…
Bud’e k’ofar Granpa yayi sannan yace mishi “the door is open and ranar Monday zamu fara zaman kotu da kai!”
Da sauri Arshaad ya kalleshi sai kuma ya hau duba takardun hannunshi, ta farkon takardar kora ce ta biyun kuma takardar sammaci ce!.
Da sauri ya k’araso gaban Granpa yace “Granpa pls i ....”
“OUT!!”
D’in da Granpa yace mishi da k’arfi ne ya sakashi saurin yin shiru dan yaga alamar kamar ran Granpa ya soma b’aci dan haka kawai sai ya yanke shawarar tafiya….
Jiki a mugun sanyaye ya sa kai ya fice daga office d’in!
Yana fita yaga Granpa ya d’aga sandarsa ya buga a jikin k’ofar dai dai inda glass d’in da aka rubuta sunanshi yake ‘Muhammad Arshaad Yahaya MT’
Nan take sunan ya tarwatse ya zube a k’asa.
Da sauri Arshaad ya juya ya fara tafiya da sauri….
Bai tsaya a ko ina ba sai a bakin motarshi, yana zuwa ya
bud’e ya shige ya kunna ya bata wuta…
Ikon Allah ne kawai ya kaisa gida, saboda uban gudun da yake zubawa.
Yana yin parking ya fito ya nufi gidansu Auwal..
A parlourn farko yana shiga ya hango shi a bakin kitchen da cup yana kurb’a da waya a hannunshi!
Gadan gadan yayi kanshi yana zuwa ya zuba mishi naushi!
Auwal bai ga shigowar mutum bama, kawai naushin da aka yi mishi yaji wanda yayi sandiyyar fad’uwar waya da cup d’in dake hannunshi da kuma fashewar hancinshi.
Jikin bango ya kama dan sauran kad’an ya shima d’in ya zube k’asa! Sannan da sauri ya d’ago dan ganin waye…
Suna had’a ido da Arshaad kawai ya kwashe da wata mahaukaciyar dariya har da rik’e ciki!
Arshaad bai kula shi ba sai da ya barshi ya d’an tsagaita
tukunna yace masa “why? And how do you do it??”
Murmushin gefen baki Auwal yayi sannan ya lakato jinin da yake bin hancinshi wanda ya sauko har kan k’irjin shi, kallon jinin yayi kafin ya gogawa Arshaad d’in a daidai kan kirjinshi wajen heart d’inshi, sannan yace
“Na tabbatar zafin da nake ji a face d’ina da jinin dana zubar bai kai wanda kake ji anan ba”
Buge mishi hannu Arshaad yayi kafin yace “ I don’t have time for this, just tell me, me nayi maka haka? What do you want from me?”.
Murmushi Auwal ya sake yi kafin yace “Yanzu kam i want nothing from you, a time d’in da nake neman abu a wajenka ai k’in yi mini kayi.
Kai ka san waye ni bana mantuwa kuma bana yafiya!
Zaka iya tuna ranar da Khadija tazo wajenka akan kayi mata signing ka k’i yi!?
A time d’in I called you Arshaad a whole me ina a matsayin MD nace maka kayi signing d’innan, I’ll explain later amman saboda taurin kai irin naka da kuma son kayi proving wasu silly principles d’inka ka k’i yi! A whole me ace wai in saka ka kayi abu amma ka
k’i yi! Who do you think you are??”
Da mamaki Arshaad yake kallon Auwal, kafin yace
“Yanzu saboda wannan ne kake son lalata mini image da carrier da future d’ina gaba d’aya?
Auwal Granpa ya kai ni court!! I’ve been sued by my own family for theft!! wanne company ne kake tunanin zasu bani aiki da wannan pent d’in da kayi mini??”.
Gyara tsayuwanshi Auwal d’in yayi kafin yace
“Actually Arshaad maganan court was my idea, although ban fad’awa Grandpa direct ba
kawai dai na bashi labarin wani Abokina da yayiwa mahaifinshi haka shikuma Mahaifin nasa ya kaishi court! That’s all i said i was hoping yayi same thing to you, and look! He did!!”
Ya fad’a yana murmushi kafin ya ci gaba da cewa “Arshaad!!you should have known me by now, bana son shishshigi…actually akwai abubuwan da kayi mini dayawa a company d’innan, tun dawowarka da aka baka position d’inka shikenan ka saka mini ido dayawa, I’m the MD bai kamata ka dinga bin al’a’mura na ba amman kwanaki har investigation ta k’ark’ashin k’asa kayi mini.
Duk wasu abubuwan da kake yi ina sane da kai.
I warned you twice amma baka ji ba!
A tsarina bana maimaita magana sau uku…
Da Khadija ta zo, na kiraka nace kai signing mata, ko nawa ne zasu fita ta acc d’in company Ina ruwanka??
amma still u refuse.
On a serious note Arshaad nayi tolerating Dinka more than yadda nake tunanin zan iya ma.
And you should stop saying wai nayi tarnishing image naka akan small thing cos this is not a small thing to me, remember i hate nonsense, and small thing su suke komawa manya shiyasa nayi deciding in yi dealing with you now!.”
Yana gama fad’in haka ya juya har ya d’an yi gaba sai kuma ya sake juyowa yace “sai mun had’u a court, i‘ll make sure na kawo wasu takardun da zasu sake girgiza ka!!
Don’t underestimate the power of your MD, wannan ma ina baka san ya aka yi suka fito ba ko?”
Bai jira jin me Arshaad d’in zai ce ba ya ci gaba
“A daa abokin fad’a ne da kai! Yanzu kam you’ve made an enemy that too a powerful one so be afraid!!”
Yana gama fad’in haka yayi hanyar sama ya kyale shi a wajen….
A hanyar main k’ofa na shigowa ya hango Mom da alamun yanzu ta shigo amman tabbas taji komai dan da mugun mamaki take kallon shi, d’an takowa tayi tana lek’a inda Arshaad d’in yake taga bai juyo ba har yanzu,
Yana ganin ta matso kusa dashi da alamun tausar shi zata yi a take ya b’ata rai yaja d’an gajeren tsaki kafin k’asa kasa ciki b’acin rai yace
“What a terrible timing u have! duk inda ake abunda bai kamata ki sani ba sai an ganki a wajen!!
Anyways it’s on u, cos I’m not gonna change or do anything for you. Kece kika ce inyi k’ok’ari nayi winning MT and that’s wat i’ve been trying to do.”
Yana gama fad’an haka ya wuce yayi hanyar stairs d’in side d’inshi.
Mom bata so Arshaad ya ganta a wajen, amman shock d’in da Auwal ya bata ya sa ta daskare a wajen ta kasa matsawa…
Gaba d’aya kullum Auwal sake rainata yake yi kamar kashin gindinshi, why?.
Tana a haka har bata san Arshaad d’in ya k’araso ba, sai muryarshi taji yana gaisheta.
Da kyar ta iya amsawa tana tunanin yadda zasuyi da Mammy idan case ya fito…ta san Mammy k’awar ta ce amma yadda take son Arshaad ko uwarta fad’a suke yi da ita akansa…
Amsawa tayi cikin basarwa da nuna kamar bata ji conversation d’inshi da Auwal ba.
Arshaad kam bai ma wani lura ba ya wuce dan duk jikinshi a mace yake, sannan har ga Allah bai san ta ina zai fara zaman court da Granpa da Auwal ba!!…
Mom kuwa ta dad’e a wajen tana lissafin nemo yadda zata b’ullo wa alamarin, ganin bata da wata mafita ya sanya kawai ta hak’ura ta wuce d’akinta tana mai jiran k’arasowar Mammy dan ta san tana hanya muddin zancen yaje kunnenta.......
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
25
Jiki a mace haka Arshaad ya shiga gida, bai tarar da kowa a parlour ba, dama kuma hakan yake hoping dan ya san in dai Mammy ta ganshi a wannan situation d’in to sai ta fahimci yana cikin matsala, kuma ta dinga tambayar shi kenan, shi kuma a halin yanzu baya buk’atar yin magana ma, he just need rest, peace and quite!.
A haka ya k’arasa side d’inshi ya wuce bedroom, yana shiga ya fad’a kan gado rigingine yayi pillow da hannayenshi ya lumshe ido ko takalmin k’afarsa bai cire ba.
Ya dad’e a haka, tukunna ya zaro wayarsa daga aljihu ya shiga contacts ya fara scrolling, yana zuwa kan ‘bff’ yayi dialing da alamun daman number yake nema…
Bugu uku a na hud’u aka d’auka!
Wata murya very calm cike da jarumta da dad’in sauraro mamallakinta yayi amfani da ita wajen cewa
“Assalam alaika!”
Nannauyar ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin yace
“Ameen, wa alaika assalam. Ya aiki?”
“Alhamdulillah, wats up!?”
Aka ce daga d’ayan b’angaren.
“A lot!”
Shine abinda Arshaad yace, sannan cikin nutsuwa ya hau kwararo mishi bayanin yadda suka yi da Granpa da Auwal d’azun, da kuma zancen shiga kotu!…
Shiruuu, kowannen su yayi bayan Arshaad ya gama bayani. Chaan!! daga d’ayan b’angaren akace ,
“I’m coming home this Sunday, in sha Allah.”
Da k’arfi Arshaad wanda a take yaji kusan 70% na damuwarshi ya kau, yace
“Really?? Woow!”
Sai a lokacin ’ASLAM’ yayi murmushi, sannan yace
“Yeah really, Bro. I was planning nayi surprising naku gaba d’aya, but naga u need something to brighten up your mood, so i have no choice but to tell u.”
“U really did brighten up my mood kam.
Allah ya kawoka lafiya and i also have a surprise for you.“
Cewar Arshaad.
“Ok, sai na zo d’in in sha Allah.”
Cewar Aslam, har zai kashe wayar sai kuma yace “karfa ka gayawa kowa, remember it’s a surprise.”
“Yeah i won’t, i promise.”
Shine abunda Arshaad yace yana murmushi.
D’an tattaunawa suka yi akan case d’in da Auwal ya had’a, bayan sun gama
Arshaad yayi mishi godiya sannan yace “bara ya barshi ya ci gaba da aiki.” Dan ya san maybe abunda yake yi kenan ya tsayar da shi.
Shiruuu, Aslam yayi bai kashe ba kuma bai yi magana ba….chaan! Ya sauk’e ajiyar zuciya sannan yace “how is she??”
Lumshe ido Arshaad yayi a hankali, sannan ya bud’e su kafin yace
“She’s fine, sai ka dawo.”
Fahimtar da Aslam yayi k’ok’arin hanging up Arshaad yake son yi yasa da sauri yace
“No, pls wait!”.
Shiruu, ne ya sake biyo baya chan Aslam d’in yace
“Tayi maganata? Did she ask about me?
Dan Allah ka gaya min gaskiya.”
Gaba d’aya zuwa yanzu Arshaad ya fara regretting kiran sa d’in da yayi!
Wani yawu mai mugun d’aci ya had’iye da kyar kafin yace
“A’a!
Amman tana.....”
‘Kit!!’ yaji an yanke kiran…
Da k’arfi Arshaad ya runtse idanunshi tare da damk’e hannunshi kamar zai yi boxing!
Ya fi minti biyar a haka tukunna a hankali ya fara bud’e idanuwan nashi da suka sauya kala tukunna ya samu ya iya janye wayan daga kunnenshi…
Yana mugun jin tausayin Yayan nasa, da ace yana da yadda zai yi to da ko nawa ne zai biya in iyakar kud’in shi kenan to zai biya ya yaye mishi wannan damuwar!.
Duk fad’in duniyar nan ko wajen Mammy yaje bata samo mishi solution d’in problems d’inshi amma minti goma yayi yawa Aslam zai nema mishi solution d’in matsalar shi ko wacce iri ce.
But shi gashi matsala guda d’aya tak! Wadda ya taso ya ganshi a cikinta sam ya kasa taimaka mishi…
Gaba d’aya Arshaad sai ya fara jin haushin kanshi…
Haka nan ranshi babu dad’i yana zaune har aka yi kiran sallar Magrib!
Toilet ya wuce yayi alwala, ya fice zuwa masallaci..
Bai dawo d’akin ba sai da yayi Sallar isha.
Yana shiga ya fad’a toilet bai dad’e ba ya fito d’aure da bathrub kanshi yana digar ruwa da alamun wankeshi yayi…
Tsadaddun mayuka da turarrurruka yayi amfani dasu wajen shafe jikinshi, sannan ya nufi wajen kayayyakin shi ya d’auko wani three quarter wando cream colour, da wata armless riga itama cream mai ratsi ratsin red a jiki ya saka, kayan ya mugun karb’ar shi,
yayi kyau sosai.
Bai damu ya tsaya taje sumar tasa ba, ya d’auko wayar shi.
Kunyar kiran Ummu yake yi amman ba yadda zai yi, tun d’azu yaketa daurewa akan ya bari sai gobe su had’u amman ya kasa.
Dialing number Ummu yayi yana adduar Allah yasa Sakina ce zata d’auka ta yadda cikin sauk’i zata had’ashi da Huda.
Adduar shi kam bata amsuba dan ana d’aukar wayar ya gane Ummu ce
“Assalama alaikom, Arshaad ya gida.”
Ummun tace
“Lafiya Alhamdulillah Ummu ina wuni.”
“Lafiya k’alau ya su Maman ka?”
“suna lafiya kowa lafiya.”
Sai kuma yayi shiru, kafin yace “ya su Sumayya?”
Nan take Ummu ta gano shi, hakan yasa tayi murmushi kafin tace “Sumayya lafiya k’alau, su Huda kam da Sakina d’azu sun bi Mama datazo tafiya sai jibi zasu dawo.
Kana da number Maman ko?”.
Kamar yana gabanta haka ya hau sosa kai, yana sunkuyar da kai sannan yace
“Eh, ina da shi.”
Murmushi ta sakeyi sannan tace “to a gaida mutan gidan Arshaad, mun gode sosai.”
“Tam zasu ji, in sha Allah sai da safe.”
“Mu kwana lafiya.”
Ummu tace, sannan ta kashe wayar, tana murmushi da mamakin kunya irin ta Arshaad !
Shi kam wannan shi ya cika cikakken bafulatani, ta san sarai ba zai tab’a kiran Mama a yau ba, tunda ya lura ta gano shi, talkless of ya nemi magana da Huda.
Mikewa tayi ta nufi kitchen ta d’auko tray ta isa dining….
Tun d’azu take jiran Baban Sakina ya fito suci abinci, amma yana dawowa a sallah ya shige ciki har yanzu shiru. Dan haka ta d’aba musu abincin ta d’aura a tray ta wuce d’akin shi.
Sai da tayi knocking ya bata izinin shiga tukunna ta shiga da sallama.
A kan gado ta hangoshi ya kwanta rigingine, yayi
pillow da hannunshi d’aya d’ayan hannun kuma ya dafe goshinsa da shi.
Kan tebur d’in d’akin mai d’auke da kujeru biyu da suke d’an gefen gadon kad’an taje ta ijjeye sannan ta dawo bakin gadon kusa dashi ta zauna.
A hankali ya juyo ya kalleta kafin ya k’ak’alo murmushi sannan ya mik’e ya zauna ya kamo hannunta duka biyu a nashi hannayen bayan ya gyara zama ya fuskanceta.
Itama murmushin ta mayar masa sannan tace “kazo muje kaci abinci.”
Bai musa mata ba ya mik’e suka nufi inda ta ajjiye abincin…
Sai da suka gama ci sannan tace “Me yake damunka? Naga kamar kana cikin damuwa.”
B’oyayyiyar ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace “ba komai, aiki ne kawai, an ma yi settling. Kawai dai ina wasu y’an lissafe lissafe ne.”
Ummu kwata kwata bata gamsu da amsar daya bata ba, amman gudun ja inja da zargi a tsakaninta da Mijin nata yasa kawai ta kawar da zancen ta kawo wata hirar..
Sun d’an jima suna hira kafin yace mata “D’azu Arshaad ya same ni akan yana son ganin Mahaifin Huda.!”
Da sauri Ummu ta d’ago tana kallonshi.
Ganin hakan yasa yaci gaba da cewa “Ban b’oye mishi ba, na fito na fad’a mishi cewa ‘an samu matsala tsakanin kakanninta na wajen uwa da mahaifinshi dashi kanshi Mahaifin nata, yanzu dai Huda a hannunmu take.
Nayi matuk’ar mamaki da Arshaad ya gaya mini cewa ‘iyayensa zasu amince da auren ko da babu Mahaifinta!’.”
Murmushi Ummu tayi kafin tace “Ai fa Baban Sakina ba koina ne aka taru aka zama d’aya ba! Inaga shi nasa dangin in dai suka bincika suka ga tarbiyyar Yarinya kuma suka tabbatar babu wani mugun abu a kanta ai dan dai fad’an iyaye ba sai sunbi diddigi ba, shiyasa yace maka ba matsala, danginshi basu da zafi kenan tunda kaji ya fad’a maka hakan!”
Jin yayi shiru yasa Ummu ta sake cewa “Ko?”
“Um, yes! maybe.”
Shine abunda Baban Sakina yace da alamun hankalinshi baya gareta…
A hankali ta d’an matso ta sake cewa “Kayi bincike sosai ko, i mean a kan shi Arshaad d’in.”
“Eh, nayi sosai, ba wata matsala fa.”
“Alhamdulillah” shine abunda Ummu tace sannan ta cigaba da cewa “ina so ma inje wajen Maman shi, inyi mata godiya akan yadda Aaima da Arshaad suka yi ta d’awainiya da Yaran nan.”
K’ura mata ido Baban Sakina yayi har sai da ta d’an sunkuyar da kanta, kafin ahankali yace “Ki bari ba yanzu ba tukunna ko?”
Sannan ya d’aura da cewa
“Yanzu dai a halin da ake ciki yana buk’atar zuwa wajen su Madu ne, dan yace mini in dai suka gama daidaitawa da ita Hudan to baya so auren ya d’auki lokaci mai tsayi.”
Murmushi Ummu tayi sannan tace “Allah ya tabbatar mana da alkhairi, abun nan yayi min dad’i Baban Sakina, ko ba komai hankalin Mama da ita kanta Hudan zai kwanta zata rabu da masifar su Sadiya, ita kanta Mama kullum fargabarta kar a aurawa Huda Junaidu, to dai yanzu babu wannan zancen, tunda gashi
Dai dai nan idanun Arshaad suka kai kan abunda takardar ta k’unsa!
Gabanshi ne ya hau fad’uwa babu k’akk’autawa!
Naira miliyan dubu d’ari tara ne suka b’ata! Kuma shine yayi signing, gashi kuma a d’ayan takardan an nuna ya shiga personnel account d’inshi!.
Da sauri ya d’ago ya kalli Granpa a mugun firgice yace
Grandpa, i don’t know anything about this! Maybe mistake ne ko kuma someone is trying to frame me, amman wallahi i have no clue......”
Kura mishi idon da yaga Granpa yayi ne ya sanya shi yin shiru.
Cikin kakkausar murya Granpa yace “Who’s trying to frame you?
Um?
Ni ko Auwal?
Use your words!
Dan mune muka yi binciken, just the two of us!.”
Shiruuu, Arshaad yayi ya sunkuyar da kanshi k’asa.
Granpa yaci gaba da cewa
“For your information nayi suspending Auwal d’in kanshi for a week!
Did you know wat he did??
I ask him to investigate, and after he finds out kai ne b’arawon he hid it from me! Bawan Allah n nan was even trying to pay back the money from his own pocket duk dan kar in gane kaine mu samu matsala da kai….”
Da k’arfi Arshaad ya runtse idanunshi, har ga Allah Auwal fa ya fara kaishi mai’ura da makirce makircensa!
Shi da yake a matsayin MD amma wai yana yi mishi bak’in cikin treasurer d’in da aka bashi! For wat!??
Sai kace ba y’an uwa suke ba?
Maganar Granpa ne ya dawo dashi daga tunanin daya fad’a
jin yana ce mishi “take this!”
Hannu Arshaad yasa ya karb’a jikinshi duk yayi sanyi.
Mik’ewa Granpa yayi ya gyara suit d’in jikinshi, sannan ya fara tafiya yana dogara sandarshi, sai da ya kai bak’in k’ofa ya juyo ya kalli Arshaad
Sai a lokacin yaga bai ma duba takardarba, yana nan tsaye yadda ya barshi ya lumshe idanuwanshi…
Bud’e k’ofar Granpa yayi sannan yace mishi “the door is open and ranar Monday zamu fara zaman kotu da kai!”
Da sauri Arshaad ya kalleshi sai kuma ya hau duba takardun hannunshi, ta farkon takardar kora ce ta biyun kuma takardar sammaci ce!.
Da sauri ya k’araso gaban Granpa yace “Granpa pls i ....”
“OUT!!”
D’in da Granpa yace mishi da k’arfi ne ya sakashi saurin yin shiru dan yaga alamar kamar ran Granpa ya soma b’aci dan haka kawai sai ya yanke shawarar tafiya….
Jiki a mugun sanyaye ya sa kai ya fice daga office d’in!
Yana fita yaga Granpa ya d’aga sandarsa ya buga a jikin k’ofar dai dai inda glass d’in da aka rubuta sunanshi yake ‘Muhammad Arshaad Yahaya MT’
Nan take sunan ya tarwatse ya zube a k’asa.
Da sauri Arshaad ya juya ya fara tafiya da sauri….
Bai tsaya a ko ina ba sai a bakin motarshi, yana zuwa ya
bud’e ya shige ya kunna ya bata wuta…
Ikon Allah ne kawai ya kaisa gida, saboda uban gudun da yake zubawa.
Yana yin parking ya fito ya nufi gidansu Auwal..
A parlourn farko yana shiga ya hango shi a bakin kitchen da cup yana kurb’a da waya a hannunshi!
Gadan gadan yayi kanshi yana zuwa ya zuba mishi naushi!
Auwal bai ga shigowar mutum bama, kawai naushin da aka yi mishi yaji wanda yayi sandiyyar fad’uwar waya da cup d’in dake hannunshi da kuma fashewar hancinshi.
Jikin bango ya kama dan sauran kad’an ya shima d’in ya zube k’asa! Sannan da sauri ya d’ago dan ganin waye…
Suna had’a ido da Arshaad kawai ya kwashe da wata mahaukaciyar dariya har da rik’e ciki!
Arshaad bai kula shi ba sai da ya barshi ya d’an tsagaita
tukunna yace masa “why? And how do you do it??”
Murmushin gefen baki Auwal yayi sannan ya lakato jinin da yake bin hancinshi wanda ya sauko har kan k’irjin shi, kallon jinin yayi kafin ya gogawa Arshaad d’in a daidai kan kirjinshi wajen heart d’inshi, sannan yace
“Na tabbatar zafin da nake ji a face d’ina da jinin dana zubar bai kai wanda kake ji anan ba”
Buge mishi hannu Arshaad yayi kafin yace “ I don’t have time for this, just tell me, me nayi maka haka? What do you want from me?”.
Murmushi Auwal ya sake yi kafin yace “Yanzu kam i want nothing from you, a time d’in da nake neman abu a wajenka ai k’in yi mini kayi.
Kai ka san waye ni bana mantuwa kuma bana yafiya!
Zaka iya tuna ranar da Khadija tazo wajenka akan kayi mata signing ka k’i yi!?
A time d’in I called you Arshaad a whole me ina a matsayin MD nace maka kayi signing d’innan, I’ll explain later amman saboda taurin kai irin naka da kuma son kayi proving wasu silly principles d’inka ka k’i yi! A whole me ace wai in saka ka kayi abu amma ka
k’i yi! Who do you think you are??”
Da mamaki Arshaad yake kallon Auwal, kafin yace
“Yanzu saboda wannan ne kake son lalata mini image da carrier da future d’ina gaba d’aya?
Auwal Granpa ya kai ni court!! I’ve been sued by my own family for theft!! wanne company ne kake tunanin zasu bani aiki da wannan pent d’in da kayi mini??”.
Gyara tsayuwanshi Auwal d’in yayi kafin yace
“Actually Arshaad maganan court was my idea, although ban fad’awa Grandpa direct ba
kawai dai na bashi labarin wani Abokina da yayiwa mahaifinshi haka shikuma Mahaifin nasa ya kaishi court! That’s all i said i was hoping yayi same thing to you, and look! He did!!”
Ya fad’a yana murmushi kafin ya ci gaba da cewa “Arshaad!!you should have known me by now, bana son shishshigi…actually akwai abubuwan da kayi mini dayawa a company d’innan, tun dawowarka da aka baka position d’inka shikenan ka saka mini ido dayawa, I’m the MD bai kamata ka dinga bin al’a’mura na ba amman kwanaki har investigation ta k’ark’ashin k’asa kayi mini.
Duk wasu abubuwan da kake yi ina sane da kai.
I warned you twice amma baka ji ba!
A tsarina bana maimaita magana sau uku…
Da Khadija ta zo, na kiraka nace kai signing mata, ko nawa ne zasu fita ta acc d’in company Ina ruwanka??
amma still u refuse.
On a serious note Arshaad nayi tolerating Dinka more than yadda nake tunanin zan iya ma.
And you should stop saying wai nayi tarnishing image naka akan small thing cos this is not a small thing to me, remember i hate nonsense, and small thing su suke komawa manya shiyasa nayi deciding in yi dealing with you now!.”
Yana gama fad’in haka ya juya har ya d’an yi gaba sai kuma ya sake juyowa yace “sai mun had’u a court, i‘ll make sure na kawo wasu takardun da zasu sake girgiza ka!!
Don’t underestimate the power of your MD, wannan ma ina baka san ya aka yi suka fito ba ko?”
Bai jira jin me Arshaad d’in zai ce ba ya ci gaba
“A daa abokin fad’a ne da kai! Yanzu kam you’ve made an enemy that too a powerful one so be afraid!!”
Yana gama fad’in haka yayi hanyar sama ya kyale shi a wajen….
A hanyar main k’ofa na shigowa ya hango Mom da alamun yanzu ta shigo amman tabbas taji komai dan da mugun mamaki take kallon shi, d’an takowa tayi tana lek’a inda Arshaad d’in yake taga bai juyo ba har yanzu,
Yana ganin ta matso kusa dashi da alamun tausar shi zata yi a take ya b’ata rai yaja d’an gajeren tsaki kafin k’asa kasa ciki b’acin rai yace
“What a terrible timing u have! duk inda ake abunda bai kamata ki sani ba sai an ganki a wajen!!
Anyways it’s on u, cos I’m not gonna change or do anything for you. Kece kika ce inyi k’ok’ari nayi winning MT and that’s wat i’ve been trying to do.”
Yana gama fad’an haka ya wuce yayi hanyar stairs d’in side d’inshi.
Mom bata so Arshaad ya ganta a wajen, amman shock d’in da Auwal ya bata ya sa ta daskare a wajen ta kasa matsawa…
Gaba d’aya kullum Auwal sake rainata yake yi kamar kashin gindinshi, why?.
Tana a haka har bata san Arshaad d’in ya k’araso ba, sai muryarshi taji yana gaisheta.
Da kyar ta iya amsawa tana tunanin yadda zasuyi da Mammy idan case ya fito…ta san Mammy k’awar ta ce amma yadda take son Arshaad ko uwarta fad’a suke yi da ita akansa…
Amsawa tayi cikin basarwa da nuna kamar bata ji conversation d’inshi da Auwal ba.
Arshaad kam bai ma wani lura ba ya wuce dan duk jikinshi a mace yake, sannan har ga Allah bai san ta ina zai fara zaman court da Granpa da Auwal ba!!…
Mom kuwa ta dad’e a wajen tana lissafin nemo yadda zata b’ullo wa alamarin, ganin bata da wata mafita ya sanya kawai ta hak’ura ta wuce d’akinta tana mai jiran k’arasowar Mammy dan ta san tana hanya muddin zancen yaje kunnenta.......
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
25
Jiki a mace haka Arshaad ya shiga gida, bai tarar da kowa a parlour ba, dama kuma hakan yake hoping dan ya san in dai Mammy ta ganshi a wannan situation d’in to sai ta fahimci yana cikin matsala, kuma ta dinga tambayar shi kenan, shi kuma a halin yanzu baya buk’atar yin magana ma, he just need rest, peace and quite!.
A haka ya k’arasa side d’inshi ya wuce bedroom, yana shiga ya fad’a kan gado rigingine yayi pillow da hannayenshi ya lumshe ido ko takalmin k’afarsa bai cire ba.
Ya dad’e a haka, tukunna ya zaro wayarsa daga aljihu ya shiga contacts ya fara scrolling, yana zuwa kan ‘bff’ yayi dialing da alamun daman number yake nema…
Bugu uku a na hud’u aka d’auka!
Wata murya very calm cike da jarumta da dad’in sauraro mamallakinta yayi amfani da ita wajen cewa
“Assalam alaika!”
Nannauyar ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin yace
“Ameen, wa alaika assalam. Ya aiki?”
“Alhamdulillah, wats up!?”
Aka ce daga d’ayan b’angaren.
“A lot!”
Shine abinda Arshaad yace, sannan cikin nutsuwa ya hau kwararo mishi bayanin yadda suka yi da Granpa da Auwal d’azun, da kuma zancen shiga kotu!…
Shiruuu, kowannen su yayi bayan Arshaad ya gama bayani. Chaan!! daga d’ayan b’angaren akace ,
“I’m coming home this Sunday, in sha Allah.”
Da k’arfi Arshaad wanda a take yaji kusan 70% na damuwarshi ya kau, yace
“Really?? Woow!”
Sai a lokacin ’ASLAM’ yayi murmushi, sannan yace
“Yeah really, Bro. I was planning nayi surprising naku gaba d’aya, but naga u need something to brighten up your mood, so i have no choice but to tell u.”
“U really did brighten up my mood kam.
Allah ya kawoka lafiya and i also have a surprise for you.“
Cewar Arshaad.
“Ok, sai na zo d’in in sha Allah.”
Cewar Aslam, har zai kashe wayar sai kuma yace “karfa ka gayawa kowa, remember it’s a surprise.”
“Yeah i won’t, i promise.”
Shine abunda Arshaad yace yana murmushi.
D’an tattaunawa suka yi akan case d’in da Auwal ya had’a, bayan sun gama
Arshaad yayi mishi godiya sannan yace “bara ya barshi ya ci gaba da aiki.” Dan ya san maybe abunda yake yi kenan ya tsayar da shi.
Shiruuu, Aslam yayi bai kashe ba kuma bai yi magana ba….chaan! Ya sauk’e ajiyar zuciya sannan yace “how is she??”
Lumshe ido Arshaad yayi a hankali, sannan ya bud’e su kafin yace
“She’s fine, sai ka dawo.”
Fahimtar da Aslam yayi k’ok’arin hanging up Arshaad yake son yi yasa da sauri yace
“No, pls wait!”.
Shiruu, ne ya sake biyo baya chan Aslam d’in yace
“Tayi maganata? Did she ask about me?
Dan Allah ka gaya min gaskiya.”
Gaba d’aya zuwa yanzu Arshaad ya fara regretting kiran sa d’in da yayi!
Wani yawu mai mugun d’aci ya had’iye da kyar kafin yace
“A’a!
Amman tana.....”
‘Kit!!’ yaji an yanke kiran…
Da k’arfi Arshaad ya runtse idanunshi tare da damk’e hannunshi kamar zai yi boxing!
Ya fi minti biyar a haka tukunna a hankali ya fara bud’e idanuwan nashi da suka sauya kala tukunna ya samu ya iya janye wayan daga kunnenshi…
Yana mugun jin tausayin Yayan nasa, da ace yana da yadda zai yi to da ko nawa ne zai biya in iyakar kud’in shi kenan to zai biya ya yaye mishi wannan damuwar!.
Duk fad’in duniyar nan ko wajen Mammy yaje bata samo mishi solution d’in problems d’inshi amma minti goma yayi yawa Aslam zai nema mishi solution d’in matsalar shi ko wacce iri ce.
But shi gashi matsala guda d’aya tak! Wadda ya taso ya ganshi a cikinta sam ya kasa taimaka mishi…
Gaba d’aya Arshaad sai ya fara jin haushin kanshi…
Haka nan ranshi babu dad’i yana zaune har aka yi kiran sallar Magrib!
Toilet ya wuce yayi alwala, ya fice zuwa masallaci..
Bai dawo d’akin ba sai da yayi Sallar isha.
Yana shiga ya fad’a toilet bai dad’e ba ya fito d’aure da bathrub kanshi yana digar ruwa da alamun wankeshi yayi…
Tsadaddun mayuka da turarrurruka yayi amfani dasu wajen shafe jikinshi, sannan ya nufi wajen kayayyakin shi ya d’auko wani three quarter wando cream colour, da wata armless riga itama cream mai ratsi ratsin red a jiki ya saka, kayan ya mugun karb’ar shi,
yayi kyau sosai.
Bai damu ya tsaya taje sumar tasa ba, ya d’auko wayar shi.
Kunyar kiran Ummu yake yi amman ba yadda zai yi, tun d’azu yaketa daurewa akan ya bari sai gobe su had’u amman ya kasa.
Dialing number Ummu yayi yana adduar Allah yasa Sakina ce zata d’auka ta yadda cikin sauk’i zata had’ashi da Huda.
Adduar shi kam bata amsuba dan ana d’aukar wayar ya gane Ummu ce
“Assalama alaikom, Arshaad ya gida.”
Ummun tace
“Lafiya Alhamdulillah Ummu ina wuni.”
“Lafiya k’alau ya su Maman ka?”
“suna lafiya kowa lafiya.”
Sai kuma yayi shiru, kafin yace “ya su Sumayya?”
Nan take Ummu ta gano shi, hakan yasa tayi murmushi kafin tace “Sumayya lafiya k’alau, su Huda kam da Sakina d’azu sun bi Mama datazo tafiya sai jibi zasu dawo.
Kana da number Maman ko?”.
Kamar yana gabanta haka ya hau sosa kai, yana sunkuyar da kai sannan yace
“Eh, ina da shi.”
Murmushi ta sakeyi sannan tace “to a gaida mutan gidan Arshaad, mun gode sosai.”
“Tam zasu ji, in sha Allah sai da safe.”
“Mu kwana lafiya.”
Ummu tace, sannan ta kashe wayar, tana murmushi da mamakin kunya irin ta Arshaad !
Shi kam wannan shi ya cika cikakken bafulatani, ta san sarai ba zai tab’a kiran Mama a yau ba, tunda ya lura ta gano shi, talkless of ya nemi magana da Huda.
Mikewa tayi ta nufi kitchen ta d’auko tray ta isa dining….
Tun d’azu take jiran Baban Sakina ya fito suci abinci, amma yana dawowa a sallah ya shige ciki har yanzu shiru. Dan haka ta d’aba musu abincin ta d’aura a tray ta wuce d’akin shi.
Sai da tayi knocking ya bata izinin shiga tukunna ta shiga da sallama.
A kan gado ta hangoshi ya kwanta rigingine, yayi
pillow da hannunshi d’aya d’ayan hannun kuma ya dafe goshinsa da shi.
Kan tebur d’in d’akin mai d’auke da kujeru biyu da suke d’an gefen gadon kad’an taje ta ijjeye sannan ta dawo bakin gadon kusa dashi ta zauna.
A hankali ya juyo ya kalleta kafin ya k’ak’alo murmushi sannan ya mik’e ya zauna ya kamo hannunta duka biyu a nashi hannayen bayan ya gyara zama ya fuskanceta.
Itama murmushin ta mayar masa sannan tace “kazo muje kaci abinci.”
Bai musa mata ba ya mik’e suka nufi inda ta ajjiye abincin…
Sai da suka gama ci sannan tace “Me yake damunka? Naga kamar kana cikin damuwa.”
B’oyayyiyar ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace “ba komai, aiki ne kawai, an ma yi settling. Kawai dai ina wasu y’an lissafe lissafe ne.”
Ummu kwata kwata bata gamsu da amsar daya bata ba, amman gudun ja inja da zargi a tsakaninta da Mijin nata yasa kawai ta kawar da zancen ta kawo wata hirar..
Sun d’an jima suna hira kafin yace mata “D’azu Arshaad ya same ni akan yana son ganin Mahaifin Huda.!”
Da sauri Ummu ta d’ago tana kallonshi.
Ganin hakan yasa yaci gaba da cewa “Ban b’oye mishi ba, na fito na fad’a mishi cewa ‘an samu matsala tsakanin kakanninta na wajen uwa da mahaifinshi dashi kanshi Mahaifin nata, yanzu dai Huda a hannunmu take.
Nayi matuk’ar mamaki da Arshaad ya gaya mini cewa ‘iyayensa zasu amince da auren ko da babu Mahaifinta!’.”
Murmushi Ummu tayi kafin tace “Ai fa Baban Sakina ba koina ne aka taru aka zama d’aya ba! Inaga shi nasa dangin in dai suka bincika suka ga tarbiyyar Yarinya kuma suka tabbatar babu wani mugun abu a kanta ai dan dai fad’an iyaye ba sai sunbi diddigi ba, shiyasa yace maka ba matsala, danginshi basu da zafi kenan tunda kaji ya fad’a maka hakan!”
Jin yayi shiru yasa Ummu ta sake cewa “Ko?”
“Um, yes! maybe.”
Shine abunda Baban Sakina yace da alamun hankalinshi baya gareta…
A hankali ta d’an matso ta sake cewa “Kayi bincike sosai ko, i mean a kan shi Arshaad d’in.”
“Eh, nayi sosai, ba wata matsala fa.”
“Alhamdulillah” shine abunda Ummu tace sannan ta cigaba da cewa “ina so ma inje wajen Maman shi, inyi mata godiya akan yadda Aaima da Arshaad suka yi ta d’awainiya da Yaran nan.”
K’ura mata ido Baban Sakina yayi har sai da ta d’an sunkuyar da kanta, kafin ahankali yace “Ki bari ba yanzu ba tukunna ko?”
Sannan ya d’aura da cewa
“Yanzu dai a halin da ake ciki yana buk’atar zuwa wajen su Madu ne, dan yace mini in dai suka gama daidaitawa da ita Hudan to baya so auren ya d’auki lokaci mai tsayi.”
Murmushi Ummu tayi sannan tace “Allah ya tabbatar mana da alkhairi, abun nan yayi min dad’i Baban Sakina, ko ba komai hankalin Mama da ita kanta Hudan zai kwanta zata rabu da masifar su Sadiya, ita kanta Mama kullum fargabarta kar a aurawa Huda Junaidu, to dai yanzu babu wannan zancen, tunda gashi