So Da Buri Book 1

Chapter 31 of 43

kayayyaki har da waya ya kawo musu ita da Sakina..
Har cikin gidan nan ma ya shigo muka gaisa.”

Shiruu, Baba yayi bai ce da ita komai ba. Sai da ya gama shirinshi tsaf ita har ta ma manta tayi maganar, dan har ta fad’a wata duniyar tunanin…
Yana dedeta zaman Hular kanshi ya kalleta yace
“Ko da wasa!! Idan kika sake bari Yaron nan ya shigo mini cikin gida to duk abinda nayi miki kar ki ji haushi na ki kuka da kanki!
Tunda ke abinda kwad’ayi ya ja miki bai kai ga zama izina a gareki ba, k’iri k’iri gashi zaki tura y’arki itama ta bi sahunki!!!
To duk iskancinsu da za suyi su tsaya iyaka k’ofar gida kuma shima ki gayawa Hudan nace tace mishi ya daina yi min parking daf k’ofar Gidana!
Tunda na san yanzu ina yin magana Kaka bayan ki zai bi!.

K’iri k’iri bani da yadda na iya an d’aura mini ruk’on shegiya tun tana jinjira!
Amman ku tsabar baku san kara ba! Jalila na cikin gidan nan aka yo siyayya dan cin fuska babu ita kuma har kike iya gaya min ya kawowa Hudan da wata Sakina wadda itama bani da ikon hanata zuwa gidan, abubuwa.
Sannan na tabbatar ko tsinke baku bawa Jalilan ba!!
Ba wai Ina gaya miki bane saboda kwad’ayi ko kiyi tunanin ina son abunku, ni abunku bai dameni ba, kawai dai inaso ki gane ta wajaje da yawa da na fiki!!”
Yana gama fad’an haka ya juya ya sa takalmanshi ya fice, ko ‘a dawo lafiyan’ ta bai amsa ba.

Girgiza kai kawai tayi tace
“Allah ya kyauta!” Sannan ta k’arasa aikinta ta wuce d’akinta.
Kamar yadda tayi zato su Huda har sun gama abun karyawan gida, daman ita da safe ta yiwa Baba nashi tace musu ‘in sun shirya su d’aura na mutan gida’.

Tana shiga d’aki ta tadda su suna ninke kaya.
Waje ta samu ta zauna a kan cafet d’in da yake malale a tsakiyar d’akin d’an gefe kad’an dasu sannan tace
“Sakina kwaso min kayan da Arshaad ya kawo jiya, duka”
“To” Sakina tace sannan ta nufi wardrobe ta bud’e
locker d’in chan k’asa ta d’auko kayan gaba d’aya waenda har yanzu suke cikin leda.
Juyesu suka yi a k’asa gabaki d’aya, sannan Mama ta hau rabawa gida biyu, abaya sunfi kala ashirin haka ta rabasu dai dai, hatta da rings dede ta raba su da su bracelet, bayan ta gama rabawa ta ware kashi d’aya a gefe sannan ta sake raba d’aya kashi Dayan gida biyu ta cewa “Huda da Sakina su d’auki kashi d’ai d’ai.
D’aya mai yawan kuma ta ce “su kwasa su zuba a leda su kaiwa Jalila.”
Har Sakina ta yunk’uro zata yi magana Hudan tayi saurin rik’e mata hannun alamun tayi shiru sannan tace “to Mama”
Ba yadda Sakina ta iya haka tana ji tana gani suka juye a leda suka fito..

Suna fitowa tace “yanzu dan Allah an.....”
Da sauri Huda tace
“Dan Allah Sakina ki yi shiru mana meye a ciki idan mun bata?
Ni daman ko Mama bata yi hakan ba ma dama inada shirin kai mata.”

Da sauri Sakina tace
“Ai ni ba wai batan da akayi bane ya b’ata min rai ba, fin namu yawa da nata rabon yayi shi yafi yi min ciwo.”

Ita dai Huda shiru tayi mata dan har sun k’araso k’ofar d’akin Umma hakan yasa ta fara sallama..
Ta yi kusan minti biyu tana sallama tukunna aka ce “shigo”
Tsaki Sakina taja sannan tace
“Zan jiraki a nan dan ba zan iya kwasar takaici ba!”
Haka Hudan ta shiga ta same su, da kyar Umma ta amsa gaisuwarta
Ita kam Jalila iskar da ta kwasota ma bata kalla ba.
Hakanan jiki ba kwari ta ajjiye k’atuwar ledar da wata y’ar k’arama tace “gashi na Ya Jalila ne” sannan ta mik’e ta fito..
Kamar ta biya su bashi ko godiya babu wadda tayi mata a cikinsu..

Suna fitowa kitchen suka nufa suka hau zuzzuba abinci.
Sun zubawa Ya Ja’afar da su da su Umma nasu suka ajjiye, dan tun dawowarsu ba su ga Junaidu a gidan ba
Hudan tana son tambaya amma tana jin tsoron Mama.

Nasu suka d’iba suma ita da Sakina da Mama a kwano d’aya, daga nan suka fara k’ok’arin barin kitchen d’in….

Hudan ce ta d’auko kwanon ita kuma Sakina tana biye da ita a baya suna magana…saura k’iris ta juyewa Ya Junaidu abincin a gaban rigarsa sakamokon gwaren da suka yi da shi.

Kwata kwata bata san yana bakin kitchen d’inba, gashi tana tafe tana kallon baya ne…
Da sauri ta ja baya ta rik’e kwanon da kyau, sannan ta hau sosa gurin da suka yi gwaren dan mugun zafi yake yi mata har idanuwanta sun kawo kwalla….

Hannunsa ya d’aura a kan goshin nata saman hannunta, da sauri ta janye hannun nata ta d’an ja baya kad’an…

Ganin da yayi wajen ya d’an yi jaaa kad’an yasa ya kalleta a hankali kamar wanda baya son yin maganar yace
“Sorry”
Jijjiga kai tayi alamun ‘ok’ sannnan tace
“ina kwana”
Yanzun ma kamar ba zai amsa ba a hankali yace “lafiya” sannan ya kalli Sakina itama da tace mishi “In kwanan” ya amsa.
Hannunshi yasa ya karb’i kwanon hannunta ya mik’awa Sakina sannan ya cewa Hudan
“Zo, ina son ganin ki.”
Yana gama fad’an haka ya juya ya wuce ya nufi hanyar d’akinsa.

Hudan, yi tayi kamar ba zata je ba, sai da Sakina tace “kije mana, baki san me zai gaya miki ba, kuma ko ba komai dai ai he’s your brother ko? kuma shi ai da hankalinshi a cikin y’an d’akin nasu.”

Shiru tayi hakan yasa Sakina kawai itama bata sake magana ba ta wuce tayi d’akin Maama.

Ta kusan minti uku a tsaye tukunna kamar mara gaskiya ta nufi hanyar d’akin bayan ta ware d’an kwalin doguwar rigar atamfar jikinta ta yafe shi daga kanta zuwa k’irjinta.

Tana isa tayi sallama a bakin k’ofar d’akin, ko k’arasa rufe bakinta bata yi ba akace
“Come in”.

A hankali ta tura k’ofar ta shiga.
Yana tsaye a tsakiyar d’akin,
kallon d’akin take yi tana sakewa dan ya koma kamar ba shi ba, yadda ya gyara gidan gaba d’aya, haka ya yiwa d’akin nasa nutsetsen gyara! Ya sha penti mai mugun kyau har da pop, ga tv k’atuwa!
Dayake d’akunan gidan suna da girma sosai har yanka yayi aka yi mishi bayi a d’akin dan ga k’ofa nan.

“How have you been??”
D’in da yace mata ne ya dawo da hankalinta gareshi.
A hankali tace “Alhamdulillah”.
Kujera ya nuna mata yace
“Zauna mana.”
A hankali ta girgiza kai
“Ok” yace, ya jinjina kai kafin yace
“Baki nemi ni ba, kin kyauta kenan??”.
Sunkuyar da kanta tayi tace “kayi hak’uri, ai babu wanda zan tambaya kai, Ya Jalila ka san ba wani shiri take yi da ni ba.”
A hankali ta sunkuyar da kai tana tunanin rabon ta dashi tun farkon shiganta ss2, haka kurum ya daina zuwa mata amman da farko farkon zuwanta makarantar kafin lokacin visiting ma yayi ya kan zo sau biyu sometimes har uku, sannan kuma duk visiting sai su Ummu sun zo da shi, dan har sak’o Mama take bashi ya kai mata kuma in yaje suyi waya da Maman!
A ranta taji ya kamata ta tambayeshi, ko ba komai Ya Junaidu yana da kirki, dan haka tace
“Meyasa ka daina zuwa min visiting?”

Murmushin yayi, kafin
a hankali yace “ashe dai an damu dani, ko?”
Bai jira jin amsarta ba yaci gaba
“Visiting da zuwa da nake yi akai akai Arshaad ne ya hana!
Dan akwai time d’in da naje gate man d’in yace min ‘wanda ya kawoku yace kar a k’ara barina ina shiga!’
Wai yazo akace mishi anyi exceeding zuwar miki sai dai ya jira next month..
Shine yayi ta fad’a yace ‘kar a sake barina In shiga’.”

Murmushi Hudan tayi kafin tace “Ya junaidu baka san halin mai gadin mu bane ba
wajen iya had’a mutane..
Ni na san ba wani Ya Arshaad da ya hana kawai dai baiga daman barin ka ka shiga bane!
Amman shi Ya Arshaad ina ma ya iya fad’a,
ba ruwanshi…
Sannnan in da ace yayi hakan to da zai fad’a min…
To gidansu Sakina fa? Me yasa baka je ba chan ba?”

Shiruuu, yayi dan ji yake kamar zuciyarshi zata fashe!!
Yadda ta tak’ark’are take yabon Arshaad a gaban shi abun yayi mugun b’ata mishi rai! Inama laifin tace zata tambaye Arshaad d’in amman ji yadda directly ta fito tayi backing d’in shi….

“Ya Junaidu!”
Yaji muryar ta, da kyar ya iya controlling kanshi, ya d’an seseta kanshi kad’an amman still idanuwanshi har sun sauya kala!
Danne abunda yake ji yayi kafin yace mata “Bayan naje school d’inku an hanani shiga, i think after a month aka yi muku hutu, and wallahi Huda that’s the longest month dana tab’a gani a rayuwana..
Kullum Ina cikin duba date,
ranar ana yi muku hutu daman na san ba nan zaki zo ba dan naji Baba yana yiwa Mama kashedi a tsakar gida ‘kar kizo mishi kuma itama idan taje a bakin aurenta!’
Yana fita na shirya zan je wajenki…
A tsakar gida Mama take bani sak’o in kai miki ke da Sakina ashe Umma tana d’aki bamu sani ba, sai kawai gani muka yi ta fito mana..
A take tace mini ‘in dai na taka k’afata naje gidansu Sakina to bata yafe min ba....’.

D’azu na dawo daga Abuja,
flight d’in asuba na biyo,
kawai cikin bacci na ke jiyo muryar ki sama sama
I tot qizo voice d’in naki ke yimini saboda yadda nake tunaninki day and night, sai da naji muryan Sakina tukunna na tabbatar ku d’in ne..
Ya aka yi Baba ya barki kika zo?
Yaushe kuka dawo?
Kun gama ko?”
Ya jero mata tambayoyi yana kafeta da manyan idanuwanshi.

Cikin nutsuwarta tace
“Wajen Kaka Mama taje, as usual….shine ya yiwa Baba magana.
Jiya muka yi graduating
a jiya muka zo nan ni da Sakina.
Na ma yi jamb, kuma duk mun ci.”

“Alhamdulillah!” yace, sannan yace “Huda i think Mama itama is against our relationship, tunda tana ganin fa yadda naketa son ganin ki but kin dawo ko a waya bata gaya min ba, kumafa jiya ma na kirata na gaisheta.”

Shiru tayi sannan tace
“Kawai dai bata son fad’a da Umma ne”

Bai ce mata komai ba, ya matso kusa da ita sannan yace
“Forget all that.
Yanzu let’s talk about us, ko?”

Kallonshi tayi sai kuma ta d’anyi k’asa da kanta ganin yadda ya tsareta da idanuwa.

“Um?”
Ya sake cewa, sannan ya d’aura da “Ina jinki, let’s talk tunda kin k’i yarda ki zauna a d’akin nawa, sai muyi a tsaya.”

Cikin rashin fahimtar shi take, “kamar akan me kenan za muyi maganan?”

Kamar an fisgi maganan a bakinshi taji yace
“Yaushe kike planning yin aure?”

Da sauri ta d’ago ta kalleshi
“Sai kuma ta maida kanta k’asa tace “duk sanda Allah yayi” sannan ta juya zata fita tana cewa “Mama zata nemi ni”

“Hudan!!”
taji ya kira sunanta.
Tsayawa tayi ita bata juyo ba kuma bata tafi ba…
Takowa ya sake yi ya zo inda take tsaye sannan yace
“I know what you are afraid of!
Umma da jalila ko?
I promise you har k’arshen rayuwan mu zan kareki daga garesu…
I won’t let them harm you in any way..
Jalila sister nace, i have full control over her
Umma kuma Mahaifiyata ce
amman na yi miki alk’awarin sai kina so ma tukunna zaki zauna a garin da take.
Hudan ko k’asar nan ne in kikace bakya son zama to zan yi k’ok’ari inga na fitar dake!
Duk inda business yake k’ok’ari nake yi inyi duk saboda ke, sannan ina aiki
I promise you i‘ll give you all the happiness and luxury’s that you deserve!.”

D’agowa tayi ta kalleshi sannan tace
“Ya junaidu gani kake yi kaiima kamar kwad’ayi ne da ni?”

Ganin da yayi kamar ranta yad’an b’aci ne yasa yayi saurin girgiza kai sannan yace
“Sorry Hudan not at all, akwai abunda nake tunani ne wanda in ma hakan ya faru to ba za a iya yi min shige ba, kar kiyi misunderstanding d’ina, please.”
Ya k’arashe in a low tone.

“To” kawai tace
Ganin yadda ya marairaice duk sai taji wani iri…
Tunanin ‘kar su tsaya b’atawa juna lokaci’ ne yazo mata dan haka kawai ta dake ta fara magana ba tare da ta yarda sun had’a ido ba…...
…”Ya Junaidu kai Yaya nane, ba zan so In yaudareka ba, kuma ya kamata in fad’a maka gaskiya tun yanzu..
Babu amfani muyi aure iyayenmu basa farin ciki da auren, kai ka sani a duk duniyar nan babu wadda Baba baya so kamar ni, a ta dalilin Kaka kawai nake zaune a cikin gidan nan!
Sannan Umma ita ma bata sona!
Ga Ya Jalila itama
sannan Ya Ja’afar!
Duk fa kowa naka kai kad’ai ne kawai kake sona
And ba zan b’oye maka ba
Mama itama bata son auren mu, duk a ta dalilin su Umma.”

Da sauri ya katseta ta hanyar cewa “Huda na fad’a miki i’ll take care of them, all of them i promise, ba wanda za a cuta in sha Allah.”

Shiruuu, tayi
chaaan kuma, kamar an fisgi maganar daga bakinta tace
“Na yiwa Ya Arshaad alk’awarin aure.”

Junaidu, da kyar ya iya had’a 1+1 d’in maganar a cikin kwakwalwarsa…
Ji yayi jiri yana neman zubar da shi dan haka ya nemi waje ya zauna, a hankali yace
“Says the person that just finish saying ‘bata da kwad’ayi!’.”

Hawayene ya gangaro daga idanunta, a hankali tace
“Bafa ka tab’a cewa kana sona ba tun farko and kuma kaga......”

K’arar fashewar center table din dake a tsakiyan d’akin ne yasa tayi saurin yin shiru sannan ta sanya tafukan hannayenta ta rufe kunnuwanta, tare da rumtse idanuwanta duk a lokaci daya!.

A zuciye ya taso yazo ya kama k’afafunta da k’arfi kamar zai karyata har sai da tayi k’ara!
Bai damu ba ya fara magana cikin tsananin b’acin rai da d’aci!!
“Ni kike cewa ban tab’a cewa ina sonki ba??
Makauniyace ke ko sokuwa?
Ko kuwa dai renin hankali ko kuma Yarinya ce ke da zaki ce baki fahimceni ba tuntuni?
Hudan tun kina baby, y’ar baby!”
Yayi maganar yana kwatanta d’aukar baby da hannunshi,
sannan ya ci gaba da cewa “nake gwada miki so! I don’t think akwai need na inyi amfani da fatar baki in fad’a miki domin kuwa na san ko wanda bai tab’a sanin me kalmar so take nufi ba, abunda nake nuna miki, ya ci a ce ya bada full definition na wat luv is!!!
Kin san irin bak’ar wahalar da na sha first zuwana Abuja da Lagos kafin in samu inyi settling kuwa??? All because of you!!!”
Ya k’arashe maganar cikin d’aga murya sannan ya girgiza ta da k’arfi!.

Fashewa tayi da kuka….
Tunda Mama ta kawota duniya bata tab’a ganin b’acin ran Ya Junaidu irin haka ba, gabaki d’aya ya birkice kamar ba shi ba, sannan idanuwanshi sunyi jazur! Sun cika da kwalla kamar zai fashe da kuka…

Kukan da yaga tana yi ne ya sanyashi yin shiru sannan ya runtse idanuwanshi!…… Ya fi 3 minutes a haka kafin ya bud’e idanunsa, ya kalleta tayi k’asa da fuskarta still kukan take yi…
A hankali ya cika mata kafad’a sannan ya juya ya fara tafiya yayi hanyar gado kafin yace
“Get out!”

Har ta juya zata fita sai kuma ta juyo tace “Ya Junaidu dan Allah ka fahimce.......”

Da sauri ya juyo ya had’e hannuwanshi guri guda alamun rok’o, sannan yace
“Huda dan girman Allah ki fita, please!!”.

Hawayenta ta share sannan ta juya a hankali ta fice a d’akin.......


BULAMA ✍️


So da Buri
Free Book
28.


Babu yadda Mama da Sakina basu yi da ita akan ‘ta fad’a musu abunda yake damunta’ ba amman tak’i!
Mama data gaji mik’ewa tayi ta nufi hanyar k’ofa tana cewa
“Ai daman tunda aka ce ya kirawo ki na san a rina!
In banda rashin hankali ma me ya kaiki shiga har d’akin shi?
Ai kad’an kenan daga aikin ‘d’an da Sadiya da Usman suka haifa’, tunda ke dai ban isa in fad’a miki ki ji ba!”
Tana gama fad’in haka ta sa kai ta fice tana cewa “Sakina su yi sauri Kaka na jiransu.”

Sakina bata ci gaba da takura mata da tambaya ba. Da ta k’i cin abincin ma kyale ta tayi ta kwashe ta kai waje dan tana so ta d’an huce tukunna sai ta sake tambayar ta.

Haka nan suka shirya suka nufi gidan Kaka..
A hanya ma Sakina labarin Yayan wata k’awar su wanda tun suna ss2 yake sonta ta dinga bata, nan take ce mata “ai jiya tana yiwa k’awar tasu magana a watsapp ta turawa Yayan nata numberta, daman duk lokacin da suka had’u idan anje visiting sai ya tambayeta bata da waya, ita kuma tsoron bashi na Ummu take yi
sai gashi kawai yau ya kirata.”

Murmushi kawai Hudan tayi….
Tun lokacin da ta fito daga d’akin Ya Junaidu take ta tunani kuma a kaff lissafinta duk in da taje ta dawo to
lissafin nata nuna mata yake
yi ‘bata kyautawa Ya Junaidun ba!’.

Sai da suka jira Kaka, dan suna zuwa suka tarar ya fita sadaka shi da Madu a masallaci kuma sai sun yi azahar tukunna za su dawo.. A nan Sakina ta samu damar sake tambayar Hudan
Nan Hudan ta kwashe duk yadda suka yi da Ya Junaidu ta fad’a mata sannan ta k’ara da cewa “ban yiwa Ya Junaidu halacci ba, duk tsahon zamana a gidan nan shi kad’ai ne in yana nan yake k’ok’arin kareni a ko da yaushe baya bari a cutar dani, ni yanzu ban san ya zan yi ba!”

Da mamaki Sakina take kallonta kafin tace
“Ban gane maganar ‘ba ki san ya za ki yi ba!? Hudan kina buk’atar peace a rayuwarki kuwa? Ya Junaidu fa d’an Umma ne Yayan Jalila k’anin Jaafar sannan d’an Baba!!
Kin san me kike

Download complete TXT · Novel page