SO DA BURI BOOK 2

Chapter 33 of 39

wajen ingije Arshaad d’in sannan kafin yayi nasarar tsaidata ta tafi gaban Dad ta tsaya! Tana mai jin wani tuk’uk’in bak’in ciki yana taso mata,
babu abunda idan ta tuna yake k’ona mata rai irin yanda taga Daddy yana ziryar zuwa wajen Adama last zuwanshi da yayi har kusan kuka taga yayi daga nan ma yace ‘ba zai iya sake ganinta a haka ba’
Tun daga ranar kuwa idan bai kirata sau d’aya ba tou zai kira sau biyu!
Amman ita ko lek’enta ko waya Dad bai tab’a yi yace a bata ba, ita tana chan tana tunanin sa ashe shi yana nan Aisha ta d’auke masa hankali!
Kalli fa sarai ya san ta dawo amman ko lek’enta bai yi ba kuma suna cikin gida d’aya, sai yanzu dan rashin kunya da tsaurin ido ya buk’aci ganinta
kuma ko alamar tambayarta ya take bai yi ba instead
ya hau wani tsattsare ido yana hucin banza..
Waennan takaicin ne suka sanya ta kasa cewa komai kawai ta zube a wajen ta fashe da wani mugun kukan bak’in ciki.

Cikin son kawar da lamarin Arshaad yace “Dad, dan Allah ka bar maganar nan, na fad’a maka ba komai fa”.

Banza Dad yayi da shi kawai ya juya ya fice! Yaso ace Mammy tayi mishi wani shirmen yau wallahi da sai ya yi mata abunda bata tab’a tsammani ba! Ya san at least zai samu peace of mind at last.

Yana fita Mammy ta mik’e!
Tunda take a rayuwar ta bata tab’a jin kishi da takaici da tashin hankali da bak’in ciki irin na yau ba!
Ta rasa dalili amma ko y’ar kissar da ta saba yiwa y’ay’an nata da Dad d’in ta kasa kuma bata jin zata iya, babu abunda take so kuma take buri irin taga ta b’atawa Dad rai ko ta samu zuciyarta ta d’anyi sanyi.
Tayi imani yanzu haka wajen Aisha zai tafi yaje ya ganta yad’an samu nutsuwa hankalinshi ya d’an kwanta alhalin ita kuma gashi ya k’unsa mata bak’in cikin da bata jin zata iya mantawa da shi har abada!
Taya zai yi mata haka?
Taya zai banzantar da ita har haka saboda Allah kamar
wata dabba?
‘Inaaa!! Ba zai yiu ba Wallahi’
Shine abunda ta fad’a ta gyara tsayuwarta tana k’ok’arin yin hanyar waje…..

Da sauri Hajiya Binta ta tareta tace
“Meye haka ne wai Mammy?
Ba a isa a fad’a miki kiji bane?
Ina za ki ji yanzun?”

Cikin kukan Mammy tace
“Kina ganin fa abubuwan da Yahaya yake yi mini
Ya gama b’ata min rai ya fice ya tafi wajen uwar gidan shi ya bar ni ni anan zuciyata ta kama da wuta kenan ko me?
Ki cikani kawai, wallahi bai isa yayi farin ciki ba, ba inda zai je yau, kullle k’ofar gidan nan zan yi sai dai mu kashe juna ni da shi a cikin gidan nan!”

Da sauri Arshaad ya matso kusa da su ya rik’eta, wani
tsananin takaicin sa take ji hakan yasa ta juyo da sauri ta kifa masa Mari! Sai kuma ta fashe da kuka, cikin kukan
tace
“Ai kaima baka kishina
Arshaad, a tunanina ko Hudan y’ar gwal ce wallahi ba za ka so auren ta b.
Taya za ka had’ani da ita mu zama surukai!?
Ko kasan cin mutuncin nan da aka yi min shine abu mafi muni a rayuwata?.
Na fad’a na k’ara fad’a yanzu ma zan maimaita maka
‘Wallahi idan ka aureta sai na tsine maka!’.”

Arshaad bai san lokacin da ya tsugunna a wajen ba ya fashe da wani mugun kuka.

Cikin b’acin rai da kafiya Mammy tace
“Kuma ko event d’in yau da suka gaiyyaceka ban yarda ka je ba!
In kaje kuma wallahi Allah ya isa ban yafe ba!
Zan ga wa zaka zab’a tsakanin ni da ita.”

Da sauri ya mik’e yace
“Haba Mammy ya kike so inyi ne?
Ki tsaya ki saurareni kuma kin k’i..
Dad ne ya nema min aurenta Abba kuma ya bani,
idan nayi miki biyayya
su kuma bijire musu kike so in yi?”

Da sauri cikin katsesu Hajiya Binta tace
“Rukayya ban tab’a tunanin baki da hankali ba sai yau wallahi!
Ni, na fad’a miki!
Mahaifiyarmu, itama ta fad’a miki! Amma ba za ki ji ba?
Waye a cikinmu zai fad’a miki abunda zai cutar da ke?
Munce kiyi hak’uri ko?
Waennan irin y’an iskan aljanu masu shegan taurin kai kika kwaso a cell d’in ne wai?”

In banda gunjin kuka babu abunda Mammy take yi.

Cikin son su kad’aita iyaka su biyu dan ta samu damar lallashinta da fahimtar da ita Hajiya Binta ta cewa Arshaad “wuce ka tafi ka shirya ku je ku yi event d’in, idan ka dawo sai mu k’arasa”

Ai kuwa Mammy na jin haka ta tafi da gudu hanyar k’ofar fita ta tsaya tayi stretching hannunwanta sideways ta kare k’ofar tace “wallahi idan ka fita sai na tsine maka!!”

Da sauri Hajiya Binta tazo ta kama hannun tana k’ok’arin janyeta tana cewa “Arshaad zo ka wuce” a ranta tana aiyyanawa
‘Tabbas akwai abu a kan Mammy’
“Zo ka wuce nace kar ka bari tayi maka spoiling day d’inka!”
Hajiya Binta ta sake maimaitawa ganin Arshaad d’in ya k’ame a waje d’aya abun tausayi.

A hankali ya k’araso ya shiga lallab’ata, Hajiya Binta itama tana yi, amman fur!! Mammy ta yi kane kane a hanyar tana ta faman maimaita kalma d’aya
‘Idan ka fita sai na tsine maka!!’

Basu ji lokacin da akai sliding k’ofar aka shigowa ba sai dai
kawai suka ga an juyo da Mammy an wanke ta da mari!
Diff!! haka parlourn yayi tsit!
Cikin b’acin rai Maman Mammyn tace
“Yi maza kaje ga Aaima chan driver ya bata kayan da zaka saka ta kawo.
Jeka ka shirya yanzun nan za muzo mu rakaka.”

Har ya d’anyi gaba sai kuma ya juyo yace
“Tace fa In na fita sai ta tsi..”
Cikin katseshi Maman Mammyn tace
“Nace ka fita ko!
Ta tsine makan in gani.”
A hankali yad’an kalli Mammyn yaga ta d’auke kai daga kallonshi, cikin nutsuwa yayi sliding door d’in ya bud’e ya fice, yana mai share ragowar kwallar dake kwance akan fuskarshi.

Yana fita ta fashe da kuka, cikin kukan tace
“Da wanne kuke so inji ne wai?
Ya kuke son inyi?
Wallahi ko sunan Yarinyar bana so a kira!
Ji nake yi kamar zan mutu, ku
duba fa kuga yanda yake kuka shab’e shab’e dan kawai nace ba zai aureta ba!
Idan ya aureta kuma ya kuke tunani??”

Hugging d’inta Mahaifiyar tata tayi tana d’an bubbuga bayanta…
Sai da ta tabbatar tayi shiru tukun cikin sigar lallashi tace
“Kiyi hak’uri Rukayya,
ke fa da kanki kikace Mijinki yana share ki! Ki duba fa ko wajen ki baya zuwa kuma da kika dawo bai nemeki ba, ko ya yi miki magana bayaga yanzun?”

Cikin sheshshekar kuka Mammy ta hau girgiza kai alamun ‘a’a’.
Ajiyar zuciya Maman nata ta sauk’e kafin tace
“Kinga ko!
Wannan ma kad’ai abu ne wanda ya kamata a tsaya a duba da kyau.
Yanda kikace Matar nan tasa ta warke, da kuma dalilin da ya sanya yake ta faman jin haushin ki wanda bamu san daliliba
yanzu shine abun a tsaya a duba a gyara bawai wannan k’aramin alhakin ba.”

Da sauri Mammy tace
“Wallahi Hajiya Hudan ba k’aramin alhaki bace ba!
Ki dubafa ki ga tun daga ranar data shigo estate d’innan nake cikin tashin hankali..”

Cikin d’an b’acin rai Maman nata tace
“To yanzu ya za ki yi?
Kinga fa wannan abun da muka san za kiyi wallahi shiyasa muka k’i mu fad’a miki maganar auren tun kina cell!
Ki tsaya ki danne zuciyarki yanda kika saba, ki fara gano matsalar da ta shiga tsakaninki da Mijinki a samu a gyara a shawo kanshi in yaso daga baya sai kiyi yadda kikeso
Amman yanzu idan kikayi yunk’urin hana auren nan, wallahi kowa bak’in ki zai gani, kuma hatta Arshaad d’in dakike ta haukar ‘kar Hudan ta janye miki shi’
Ke ce da kanki gashi kike k’ok’arin kawo matsala a tsakaninku da kanki gashi kina turashi away from you
dan
Wallahi kinji na rantse miki yadda Arshaad ya kwallafa rai akan Yarinyar nan muddin kika sake kika zama silar da ya rasata to kuwa ba zai tab’a yafe miki ba!
Kuma sai kin yi dana sani.
Ki bari ayi auren sai mu san abunyi. Yanzu kar ki fito b’aro b’aro a matsayin wadda ta hanashi aurent....”

Cikin katseta Mammy tace
“Ki kwantar da hankalinki ni na san ta inda zan b’ullo mishi yana jin maganata ai yana yi min biyayya.
Matsalar da za a samu shine
In har na bari ya aureta!
D’azu fa muka gama waya da Adama wai ashe ma k’asar za su bari gaba d’aya!
Haba dan Allah taya ba zan yi kuka ba? D’ana kwalli d’aya a duniya zata d’auke shi su tafi sai ta gama mallakeshi tukun a dawo min da fanko? Dama yanzun ma ya aka k’are?? Ballantana kuma yaje yayi spending years da ita!
Ni kawai ku kyaleni dan girman Allah, dan na tabbatar ranar da Arshaad ya aureta to ni kuma zan iya barin duniyar nan a ranar.”
Ta k’arashe tana sake fashewa da wani sabon kuka.

Cikin fad’a Maman nata tace
“Baki rabu da su Adaman nan ba har yanzu ko? Na ce miki ki tsaya ku fara shiryawa da Mijinki ki fara gano matsalar da ta shig..........”

Da sauri Mammy tace
“Matsalata da Dad, Aisha ce!
Na rigada na sani.
Ki bari kawai in fara kashe wannan boss d’in after that idan na tashi bi ta kan Aisha wallahi duk wanda ya ce zai shiga tsakani sai na had’a da shi”.

BULAMA ✍️


So da Buri
Free Book
52


Cikin fad’a Maman nata tace
“Baki rabu da su Adaman nan ba har yanzu ko? Na ce miki ki tsaya ku fara shiryawa da Mijinki ki fara gano matsalar da ta shig..........”

Da sauri Mammy tace
“Matsalata da Dad, Aisha ce!
Na rigada na sani.
Ki bari kawai in fara kashe wannan boss d’in after that idan na tashi bi ta kan Aisha wallahi duk wanda ya ce zai shiga tsakani sai na had’a da shi”.
Tana gama fad’in haka ta juya ta fice da sauri tana share hawayenta.
Ko bi ta kan y’an parlourn bata yi ba, ta wuce sama abunta tana huci.

Tana fita Maman nata ta sauk’e ajiyar zuciya!
A hankali ta kalli Hajiya Binta tace
“Allah ya rufa asiri..tunda tak’i jin maganata ni uwarta!
Ni zan tafi yanzu, idan ta yarda aje wajen event d’in su Amaryar to ku rakashi
Idan kuma ta hana sai ku zuba mata ido.
Sannan ki samu y’an uwanki ki jasu gefe kice nace ‘ko me zata yi kar wanda yayi yunk’urin hanata’
Ita ta sani.
Taje tayi yadda taga ya dace.”
Tana gama fad’in haka itama tayi hanyar waje cikin y’ar tafiyar su ta tsoffi...

Sallama ta yiwa matan dake babban parlourn daga nan ta wuce abunta.
Har k’ofar mota ragowar sister’s d’in Mammy guda biyu k’annenta suka rakata, suka
bud’e mata gidan baya
ta shiga suka rufe driver yaja suka tafi.
Su duk basu san wainar da ake toyawa ba Hajiya Binta wadda ta kasa fitowa parlourn tun tafiyar Mahaifiyar tasu ce kawai ta sani dan haka suna komawa aka shiga bidiri ana ciye ciye ana ta hotuna!
Fitowar Ango da Aaima ne ya k’arawa abun armashi, ba a dad’e ba Mom da Ummi wadda ta d’an ji sauk’i suka shigo, nan
suka had’u aka yi ta hotuna….

After kamar 30 minutes haka, aka fara shirye shiryen tafiya gidan su Amarya, anata had’a gifts..
Dai dai nan Mammy ta sauk’o.

Sai da gaban Arshaad ya yanke ya fad’i amman ya dake ya k’arasa inda take ya fara k’ok’arin jan hannunta yana cewa “ta zo su yi hoto”

Ko alamar zata motsa bata yi ba dan haka ya tsaya ya d’an kalleta yace
“Mammy dan Allah mana,
mutane suna kallo fa, ki zo
muje”
Ya fad’a yana sake k’ok’arin janta.
Suna a haka sisters d’inta da Aaima suka iso wajen.
Fisgewa tayi da mugun k’arfi, kafin tace masa
“Idan baka je ka cire wannan wata kalar shigar ba
wallahi Arshaad sai na ci ubanka!!
Sannan
ni za ka mayar y’ar iska mai magana biyu?
Mu gama magana da kai amma ka je ka wani shirya tsaf sannan dan tsabar raini kazo kana ce min wani muje muyi hoto?
Da kai da hoton kun ci kutumar ubanku!”

Runtse idanunsa yayi da mugun k’arfi!
Dai dai nan Mommy da Aslam waenda suka shigo yanzun
suka nufo su, suka k’araso!
Kusan duk sun ji furucinta.

Da mamaki suke kallonta,
a hankali Aslam yad’an dafa kafad’ar Arshaad d’in, dukda bai gama sanin wainar da ake toyawa ba amman yad’an fahimci wani abun, hakan
ya sanya shi jin mugun tausayinsa ya rufeshi....

Da mamaki Mommy take kallon Mammy
kafin tace
“Lafiya kuwa?
Me naji kamar kin ce?”

“Amin, wa alaiki Assalam Aisha!”
Mammy ta fad’a cikin tsareta da ido tana jin wani mugun tsanarta na taso mata…

Murmushi Mommy tayi
kafin tace “Assalam alaikom,
me yake faruwa ne Arshaad?”
Ta yi maganar tana me mayar da akalar tambayar tata kan Arshaad
saboda tsananin mamakin Mammy da ya rufeta..
Tunda suke tare ko da wasa Mammy bata tab’a yi mata kwatankwacin irin haka ba.

Arshaad Yana shirin yin magana Mom ta k’araso
tace
“Ya dai? Kukayi cirko cirko duk anan?”
Kafin ta kalli Mommy tace
“Ina ta yi miki magana Mommy, kika k’i kulani kika wuce.
Ina wuni.”
Dai dai nan Ummi itama ta k’araso wajen nasu.
Cikin kulawa Mommy tace
“Yi hak’uri Adama,
hankalina ya yo kansu ne dan naga kamar ba k’alau ba.”

Da sauri Mammy tace
“K’alau d’in....”

Cikin katseta da d’an k’arfi Mom tace
“Haba k’alau ne mana,
komai normal Ina?”
Ta fad’i hakan tana kallon Mammy da d’an sign d’in tayi calming down mana…

Tsaf Mammy ta fahimceta..
Itafa ta rasa gane dalilin da yasa su Adama da y’an uwanta suke tunanin zata iya yin wata kissa a wannan stage d’in!
Taya ma zata iya danne wannan duka dubu d’in da akai mata?
Ya an dake ta kuma suna so su hana ta kuka??…

Mom na shirin yin magana taji Ummi tace
“Arshaad akwai matsala ne?
Yi magana mana, kar
lokaci ya k’ure!
Kaga yanzu tafiya za mu yi.”

Da sauri Mommy tace
“Dankuwa har na cewa Maryam d’in ma mun kusan fitowa, na san mu suke jira yanzu haka.”

Ajiyar zuciya Mom ta sauk’e
tana ji kamar ta shak’e Mommy !
‘Wato irin ita har ta jone da Maryam d’innan’.

Mammy na shirin yin magana

Arshaad wanda ya ga b’oye b’oye shi ba inda zai kaisa dan kwata kwata ya kasa shawo kan Mammy kuma yana ganin in dai ya gayawa Mommy maybe a samu sauk’i ta hanyar Dad da Gramma
ne, yace
“Mommy cewa tayi ko a fasa auren ko ta tsine min”

Da sauri Mommy tace
“Whatt!!”
Cikin firgici kafin ta juya kan Mammy tace
“Rukayya wanne aure kike so a fasa?”

Ba tare da b’ata lokaci ba
cikin b’acin rai da tarar numfashin ta tace
“Auren Huda da Arshaad, Aisha!
Shi nake so a fasa
Idan kuma kina da ja to sai in ji...”

Sai a sannan Aslam ya d’ago ya kalleta, bata san mai ya faru ba amman sai Yaron yayi mata kwarjini ta kasa ci gaba da magana.

Mommy ta yunk’uro za tayi magana kenan taji Aslam d’in ya rik’e hannunta, ba tare
da yace mata uffan ba kawai ya juya da ita suka fara tafiya.

Har suka fice a parlourn bai ce uffan ba ita kuma bata yi mishi tirjiya ba, sai da suka isa tsakiyar compound d’in tukunna ya zaro waya
ya danna kiran Dad!
Ba tare da b’ata lokaci na ya gaya mishi halin da ake ciki…

Suna gama wayar, ya ga
tana k’ok’arin komawa
A hankali yace
“Mommy please kar ki koma ciki, kina jin fa yanda take yi miki magana ba respect.
Please dan Allah kar ki je.”

Za tayi magana yace
“Please Mommy, i can’t take it”

Ajiyar zuciya ta sauk’e
kafin a hankali tace
“To kaini gidansu Huda.
I have to be there,
suna ta expecting d’inmu.”

Da k’arfi yaji zuciyarshi ta buga !
Sai kuma yaji zafi kamar
an soka mishi wuk’a…

Sai da ta sake maimaita maganar tata tukun yace
“Tam”
Daga nan suka fara tafiya suka wuce inda motarsa take a chan wajen gidan, suka shiga suka wuce.


A chan parlourn kuwa
Zuwa wannan lokacin gaba d’aya hankalin matan parlourn ya koma kan su Mammy.
Su Mommy suna fita Ummi ta hau lallab’a Mammy
tana bata baki, basu kulata ba sam daga ita har Mom dan
tun a cell daman sun fita harkarta saboda ta zama
wata salaha doluwa wawiya! kamar ba ita ba.

Arshaad kuwa ji yake kamar ya chaka wa kanshi wuk’a!
Babu abunda yafi d’aga mishi hankali kamar kalmar ‘sai ta tsine mishi’ da taketa faman ambata, hakan yasa kawai ya juya zai bar wajen
suka yi karo da Dad! Fuskarshi sam babu alamun annuri dan hatta Arshaad d’in sai da ya d’an tsorata da yanayin shi.

Ganin yana shirin fara zuba musu tujara a gaban jama’a ne
ya sanya Mom tace
“Dad da mun d’an shiga daga ciki ko mu hau sama
Kalla kowa ya zubo ido mu yake kallo”
Juyowa yayi yana kallonta
wanda hakan yasanya ta sha jinin jikinta.
Da kakkausar murya yace
“Granpa ya san kina nan?”

A hankali jikin a mace ta girgiza kai,
Snapping fingers d’inshi yayi
kafin ya nuna mata hanyar main door straight!

Ba k’aramin sanyi jikin Mom yayi ba! Kunya da takaici kuwa kamar su kashe ta,
a hankali tace
“Sai anjiman ku”
daga nan ta fara k’ok’arin wucewa taji Ummi tace
“Adama d’an jirani in je in d’auko wayata a side d’in Granpa In zo mu wuce.
Ya sallameni tun jiya.”

Ba tare da Dad ya kalleta ba yace
“Ki jirani zan maidake anjima, ina son ganinku tare, ke da Abba.”

“Ok” kawai tace
Mom kuma ta wuce ta fita.

Sai a

Download complete TXT · Novel page