SO DA BURI BOOK 2
Chapter 35 of 39
Sakina suka take musu baya.
Hudan, so take ta yakice tunanin Arshaad a kanta amman ta kasa!
K’arshema bigewa tayi da adduar Allah yasa tana fita ta ganshi amman yanayin yanda taji an zaunar da ita a doguwar kujerar da aka k’awata domin ita da shi ne yasanya ta fahimci bai zo d’inba.
Ummu ce ta fito ta bud’e taro da addua sannan ta fara gabatar da al’ada a Huda,
A matsayin uwa.
Mama suna parlourn Madu, tun lokacin da Mommy da Aslam suka zo suka buk’aci ganinta har yanzu bata samu damar fitowa ba.
Wata distant relative d’in Shuwa wadda zata d’an girmi Shuwan kad’an ce
ta k’arasa wajen sannan
cewa Ummu “Ina uwar Angon?
Ta zo ta zauna a kusa da ke
yadda kina gamawa zata karb’a.
Sannan ba ayi welcomin Ango ba kuma ba aga shigowarsu ba besides ai dole sai yananan ma tukunna za ayi komai.
Na ga bai riga yazo ba
amman kin yi wuff kin fara abu haka bayan kuma akwai abubuwa da yawa before wannan.”
Karaf! A kunnen umma. Daman neman abun yi suke yi ita da Anty Zainab shiyasa
suka zo suka zauna a k’asa gefen kujerar Amarya. Da sauri sannan da d’an k’arfi yadda ta tabbatar kowa zai ji
Umman tace
“Eh kam tabbas!”
Sannan ta mik’e tsaye
kafin tace
“Uwar Ango! Tana Ina?
Ana buk’atar Uwar Ango a nan yanzu yanzu”
Da k’arfi ta yadda kowa ya iya jiyota tunda daman wak’ar da aka kunna a low tune yake
kuma iya murya ne kawai babu kid’a.
Da sauri Ummu tace
“Umma meye haka?
Idan kin yi min magana ba zan je In kirata baneba?
Ko hakan da kika yi kina tunanin shi zai sa ta fito?”
Still da k’arfi Umma ta sake cewa
“A’a, ai ji nayi kamar kince bata zo ba!
Gashi shima Angon shiru.
Duk da dai ni ba Shuwa bace ba amman Tabbas na asan cewa Ango da Amarya a tare ake shafa musu lalle, manshanu, da ragowan abubuwa! Dan har yau ina tuno naki, a tare aka shafa muku ke da Muhammadu wanda ya zo wurwuri
bai tsaya b’ata lokaciba,
Ita kuwa yayarki daman ba a yi mata ba
shiyasa gaba d’aya auren nata duk biyun suka tab’arb’are!
To kuwa kinga ai ba zan so auren Huda itama ya samu matsala ba ko?
Dan haka gara mu jira Angon ya zo ko nan da k’arfe taran dare ne mu masu iya jiransu ne
har sai shi da uwarshi sun zo an yi alada yadda ya kamata!”.
Ta k’arashe maganar har wani karkarwa jikinta yake yi, wanda kana gani ka san bala’ine kawai yake cinta.
Ummu bata ga k’arasowar Sakina ba sai tayi tana cewa
“Eh tabbas kam Hajiya Umma kya zauna ai kiyi ta jira tunda daman kallon kwaf da munafurci ne ya kawo ki!
Mu nan dukkannin mu munada aikin yi kuma ba mu da lokacin zaman jira har k’arfe taran dare!
In dai Ango kike son gani to ki bada nan da awa biyu zaki ganshi sun iso tare shi da iyayenshi maza da za su kawo lefe wanda na tabbatar abunda ya tsaidasu kenan
ba wai abunda makirar zuciyarki ta shirya miki ba!”
Umma na shirin k’arasowa inda Sakinar take taga Ummu ta d’auke ta da mari!
Cikin yaren Shuwa Ummu ta hau yiwa Sakinar fad’a k’asa k’asa yanda ta tabbar ba kowa ne zai ji su, tace
“Baki da hankali ashe?
A cikin dangi da y’an uwa za ki bud’e baki kina yiwa babbar mata rashin kunya haka?
So kike a tafi dake a baki?
Wuce!
Wuce ki tafi chaan sama d’akin Shuwa ki rufe!
Idan ba ni na neme ki ba wallahi kika fito sai ranki yayi mugun b’aci!”.
Juyawa kawai Sakina tayi ta wuce tana ji kamar ta had’iye zuciyarta!
A kan Umma aka mareta a gaban mutane haka!?
Kuma ta tabbatar tunda Umma ta fara wannan maganganun to fa idan taka mata burki aka yi ba ko kuma Arshaad d’in ta gani ba tabbas ba zata
tab’a barin mutane su sha ruwa ba.
Ita daman tun d’azu da ta ganta tazo da sassafe ta san ba alkhairi ne ya kawota ba.
Ita da take da abun fad’a a gindi amma shine har take da audacity d’in yin magana!
Wallahi yau da Ummu ta barta da sai ta yiwa Umma zazzagar kwanyo....
Da wannan tunanin ta k’arasa d’akin Shuwa, sai a lokacin hawayen bak’in ciki suka samu nasarar zubo mata…
Daga Shuwa sai Baabaa Talatu ne a d’akin suna
shirya tukuicin da za a bayar in an kawo lefe.
Baaba Talatu tana ganin ta shigo tana kuka ta mik’e tana
“Subahanallah, mai ya
faru?
Ke da waye?”
Da sauri ta k’arasa ta hau shafa fuskarta inda hannun Ummu ya fito tarr!! Ya kwanta akan farar fuskarta
Cikin fad’a Baaba Talatun tace
“Wanne d’an iskan ne ya mare ki??”
Fashewa tayi da kuka
cikin kukan tace
“Umma ce take ta abubuwa a waje, shine Ummu ta mareni
wai dan....”
Ai bata tsaya jin k’arshen ba,
tayi waje.
Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar
tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina .
Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba...........”
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
53
Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar,
tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina.
Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba.”
“To”
Kawai Sakina tace,
tana mai sake goge fuskarta
sannan ta koma gefe ta fara warware laffayar jikinta da d’aurin d’ankwalin dake kanta..
Sai da ya rage daga ita sai long camisole d’inta wadda ta saka a ciki mai dogon hannu yayinda dogon gashinta ya kwanta a gadon bayanta sannan ta fara k’ok’arin kiran Arshaad...
Tayi mishi misscalls sun fi ashirin amman shiru. Dan haka
nan da nan hankalinta ya sake tashi…. Tun jiya take danne zuciyarta take k’ok’arin kawar da maganar da Aaima ta gaya mata a cikin kwakwalwarta
amman kuma attitude d’in Arshaad da k’in zuwanshi a yanzu ya yi matuk’ar bata tsoro.
Ba wadda take jin fargabar taji wannan batu irin Hudan
shiyasa jiya ta kwana Sallah akan Allah yasa maganar Aaima ta zama k’arya
idan kuma gaskiyace Allah yasa su Abba su gyara lamarin cikin sauk’i…
Gaba d’aya hankalinta a tashe yake dauriya ce kawai take yi, tana kuma k’ok’arin taga ba wanda ta bari ya ma ji zancen har a samu a gyara lamarin in sha Allah.
Ganin arshaad d’in bashi da niyyar amsa ta ne
yasa kawai ta kira Auwal
dan taji me ke faruwa
a ina aka tsaya..
Shi sai a bakinta ma yake jin wai ‘Arshaad d’in bai je ba’
Saboda shi suna asibiti.
Ganin kamar bai san me yake faruwa ba ya sanya taja bakinta tayi shiru
saboda ance yawan yayata magana kan iya tabbatar da gasgatuwar ta. Dan haka kawai sai tace mishi
“ya duba musu Arshaad din pls”
Daga haka suka yi sallama.
Daman shima yana da shirinshi zai je wajen
So yanzu zai duba Arshaad d’in sai su wuce tare kawai
dan haka ya cewa Dad
“Bara yaje gida,
Sakina ta kirashi wai har yanzu Arshaad be k’arasa ba.”
“to” kawai Dad d’in yace masa.
Yana fita shima Dad din ya d’au waya ya kira Gwaggo Asabe yace
“Dan Allah tazo ta ji da Ummi.
Zai yiwa drivern da zai kawota kwatancen asibitin da suke....”
Drivern da ya kawota (Gwaggwo Asabe) shi ya maidashi mansion d’in.
Yana zuwa ya tarar da Daddy
ya shirya chap yana jiranshi
da akwatuna dozen biyu sun sha decoration
sai kuma basket na gift guda biyar, da akwatunan uwa uba gwaggwo da kawu..
Duk sun had’a. Tun sassafe Mommy ta aiko da kayan
shi kuma ya duba ya tabbatar komai dai dai.
Sai da aka gama loda kayayyakin a motoci wajen goma tukunna Abba ya fito da shirin shi shima da alama rakasu zai yi!
Dad, yana shirin shiga mota har driver ya bud’e mishi k’ofar motar ya hango tahowar Abba!
Wani takaici ne ya d’ebesa
bai san lokacin da ya daka masa tsawa ba! Yace
“Idan ka k’araso nan wallahi sai mun kwashi y’an kallo ni da kai!
Kaji dai na rantse
wallahi!!”
Ya k’arashe maganar yana mishi nuni da yatsar shi manuniya yana nuna sama.
Ajiyar zuciya Abban ya sauk’e kafin yace
“Dad nimafa rakaku zan y....”
Cikin fushi Dad d’in yace
“Kaga mota nan, zo ka shiga!
Amman direct
Asibitin da aka kwantar da Ummi zaka je
Idan kuma ba haka ba to ka koma ka zauna a ciki.
Zab’i d’aya!”
idanuwa direbobin da masu aikin suka tsura musu..Ganin da Abba yayi har sun fara kwasar y’an kallon kamar yadda Dad d’in ya ambata ne yasa kawai ya juya ya koma ciki ranshi a mugun b’ace!.
Tsaki Dad yayi ya shige motar
yana mai cewa
“Ba za ku haukata ni ba,
wallahi!”.
Shi dai Daddy
shiga yayi ya zauna a kusa da shi, yana son tambayarshi
wata zuciyar kuma sai ta bashi shawarar ya bari ya Dad d’in ya d’an sauk’o tukunna sai suyi magana…
A haka drivern ya ja su suka nufi Gandun Albasa
Daddy yana mamakin meye haka yake damun Dad??
Dan tabbas ya san akwai abunda aka yi mishi......
GANDUN ALBASA.
Baaba Talatu tana fita harabar gidan ta tarar gurin har ya fara kachamewa!
Dan bayan Sakina ta bar wajen Umma da Anty Zainab kan Ummu suka dawo
wai “ai itace bata yi mata tarbiyya mai kyau ba shiyasa ta raina manya har haka...”
Ga kuma wannan tsohuwa ita ma ta kafa ta tsare tace
“Sai Ango ya fito tukunna za a fara gabatar da komai!”
Yayinda Ummu da wasu cousins d’inta suke ta k’ok’arin ganin sun yayyafa wa lamarin ruwa amman abun ya faskara!.
Baaba Talatu ce ta k’arasa ta ja wannan tsohuwar gefe suka had’u ita da Shuwa suna mata magana k’asa k’asa…
Ganin kamar ana shirin fara traditional event d’in
cikin kwanciyar hankali ne yasanya Umma ta sake cewa
“Nima fa kamar uwa nake a wajen Hudan!
Dan haka ba zan bari kowa ya tab’a ta ba har sai Angon nata ya k’araso..
idam kuma fasawa yayi ne to kawai a fito a fad’a wa mutane sai a fasa sakata a lallen,
dan ba girman mu bane mu tsaya muna yiwa mutane wasa da hankali!
Ko ya kuka gani?”
Ta k’arashe maganar tana kallon cousins d’in Ummu waenda suke gefen ta! Ba su kad’ai ba kusan kaff wajen babu wanda bai ji abinda tace ba hatta su Shuwa.
“Ga Angon nan”
Muryar Mommy wadda suka fito su uku yanzu ta daki dodon kunnuwansu!
Da sauri Mama da Aslam suka kalleta!
Ba tare da ta kallesu ba ta
kama hannun Aslam ta fara janshi
Mama na binsu a baya kamar rak’umi da akala shi kuma yana binta!..
Bata cikashi ba sai da ta kaishi gefen Hudan sannan ta zaunar da shi.
Da sauri Ummu ta matso k’asa k’asa tace
“Mommy a Al’ada fa dole sai Angon zai....
Cikin katseta Mommy tace
“A addini fa?”
Bata jira Ummu ta bata amsa ba ta sake ce mata
“Kalla nan kinga”
Tayi maganar tana
nuna mata Huda wadda sai a lokacin Ummu ta lura da yanda mayafinta ya jik’e sharkaf!
Wanda kana gani ka san ruwan hawaye ne…
Mommy bata jira jin me zata ce ba ta ci gaba da yi mata magana k’asa k’asa irin na masu hankali,
tace
“Saboda ita kawai ki bari ayi a gama!
Na tabbatar ba wai rashin zuwan Arshaad kad’ai bane ya saka ta kuka ba! Har da maganganun matar nan! Tun muna parlourn bayankun nan muke juyo komai.
Dan Allah kar kice a’a!
Kalla kiga mutane kowa ya zuba ido an fara k’ananun maganganu, na tabbatar in dai ba Angon suka gani ba to haka za a tashi ana gulmace gulmace shima kuma sai idan an samu waenchan matan sun bari anyi d’in kenan.
Na tabbatar mutane k’alilan ne kuma na jikinku sosai suka san ba Arshaad bane wannan, ba kowa ne zai gane ba
so dan Allah ki kwantar da hankalinki ayi abun nan a gama without any more dramas.
Saka lalle ai ba d’aurin aure bane ba, ba komai kawai bidi’a ce so mu bisu kawai ayi a gama.”
Tana gama fad’an haka ta juya ga jamaar wajen tace
“Kuyi hak’uri mun yi latti wani d’an uzuri ne ya tsaida mu!
Sunana Hajiya Aisha
Maman Ango, mun gode kwarai da zuwanku dan taya mu farin ciki.”
Daga nan ta juya ta cewa
Ummu
“Ni zan fara ko ke?”
Da murmushi kwance akan fuskarta.
Kallonta kawai suke yi
daga Ummu har Mama.....……
Mama da Ummu sun so hana mai video coverage da pics d’auka amman ganin yanda hankalin kowa yake a kansu
da kuma Mommy wadda tace ‘su bari kawai tunda ga wasu ma a gefe suna ta d’auka da waya’ ne ya sanya
kawai suka hak’ura.
K’awayen su Huda kuwa abun ba k’aramin d’aure musu kai yayi ba dan tabbas sun san wannan ba da shi akayi cocktail jiya ba, kuma ba shine a pre wedding ba!
A haka dai suka bar maganar akan in an tashi za suni komai a bakin Sakina....
Aslam kuwa so yake ya mik’e amman sam ya kasa!
Ya rasa dalili..tun da yake bai tab’a jin fargaba irin wadda yake ciki a halin yanzu ba!
Ana cewa k’afafuwa da gangar jikin mutun suna sagewa ya koma kamar gunki bai tab’a yarda da hakan ba sai yau da ya faru a kansa dan hatta kwayar idanunsa ya kasa juyawa, so yake ya runtse idanuwanshi ya samu ya dedeta zuciyar shi amman sam ya kasa!
Yana nan a haka yaji Ummu na rufa mishi wata jibgegiyar alkyabba akan jamfar jikinshi
Akan hular kanshi
Ummu ta d’aura mishi wani jan kyalle mai tambarin moon a gaba golden colour
(Allah yaso suna da extra)
Daga nan ta mik’a mishi wata sanda wadda ta ci ado! Tace masa “ungo, rik’e”
Mommy ce ta kama hannunshi ta sanya mishi
sandar sannan ta had’a da nata hannun ta maste!
Sai a lokacin ya samu nasarar lumshe idanuwanshi
sannan ya d’an bud’e su kad’an yana kallon k’asa....
Ba tare da b’ata lokaci ba aka fara gudanar da alada……..
Bayan uwar Amarya da uwar Ango sun yi, ragowar jama a suma suka zo suka sanya musu suka basu gift
daga nan aka fara serving abinci.
Sai a lokacin Anty Zainab da Umma suka samu suka iya zama…Umma so take yi ta sake mik’ewa tsaye tace
“To Ina y’an unwan Ango!?” ta sake creating scene amman sam ta kaasa dan in banda
dishi dishi babu abunda take gani! A ranta ta shiga aiyyana
…..Tabbas sai taci uwar malan ado! Wallahi sai ta saka an yi mishi yasin mai walk’iya!
Ba Malami ba ko uban waye shi. Kuma sai ya bata kud’inta.
Jiya jiyan nan fa ta sake komawa wajenshi dan ta sake nanata mishi, shi kuma ya
tabbatar mata da “babu aure tsakanin Hudan da Arshaad
ya riga ya gama aiki
kuma ya buga k’asa ya tabbatar ba Mijin ta bane ba
sannan
ya ingiza zuciyar iyayen shi (Arshaad) ya rura wutar k’iyayyar Hudan a cikinta
ta yanda ba zasu tab’a bari ayi auren ba musamman ma Mahaifiyarshi (Arshaad)…”
Amman kalli yadda Maman nasa taketa jan Hudan a jiki,
anyi musu hoto yafi kala nawa tare sai faman fara’a take yi tana washe baki kana ganinta ka san tana cikin tsantsar farin ciki….Inaaaaa!!!!!
Taya ma zata tsaya ta yarda Hudan ta auri wannan
No1 kyakkyawan da ita tunda take a rayuwarta ko a telebijin bata tab’a ganin mai kyawunsa ba! Ga uban kud’i ga kyau kamar aljani
Allah sarki Jalilan ta
dole ta mutu akan soyayyar Arshaad, ai kuwa idan zata yi yawo tsirara wallahi sai ta raba auren Huda da Arshaad ko sama da k’asa zasu had’e
Wallahi sai dai in rabo ya kasheta akan dai ta zauna ta nad’i wannan abun takaicin da ta san k’arshe in dai bata d’auki mataki ba to shine ajalinta!
Kuma ko yana so ko baya so sai ya auri Jalila!
Wannan alkawari ne ta d’aukarwa Jalila da ita kanta!
D’an halal ka fasa……..
Anty Zainab ce ta tab’o ta
wanda hakan ne ya katse mata tunani.
Da kyar ta iya motsa wuyanta dan ji take kamar ba jini da rai a dukkannin ilahirin jikinta
Suna had’a ido taga itama Anty Zainab d’in idanuwanta sun kad’a sun yi jazir!
Kafin Umman tace wani abu
taji tace
“Sadiya taso mu tafi,
kai na ciwo yake yi min”
Suna shirin mik’ewa
suka fara jiyo gud’a daga parlourn Madu sai a sannan ma suka lura Shuwa da Baaba Talatu da wasu y’an tsirrun mutane basa wajen
A bakin matan wajen sukaji an fara k’us k’us d’in
“Ashe tun d’azu mazan gidan Ango suka zo sun kawo lefe yanzu suka wuce
da yake falon Madu yana da k’ofar shiga da fita ta waje, shiyasa har suka zo suka tafi ba wanda ya sani
Sai da suka tafi yanzu akace aje a fito da shi” Sunaji anata k’usk’us d’in “ai motocin da suka zo da su ma kansu abun kallo ne!
Gasu kana ganinsu kaga manyan mutanen da kud’i ya zaunamawa”
Da kyar Umma take iya jan numfashi, dan ji take yi gaba d’aya iskar wajen bata isarta!.
Ummu ce ta d’an matsosu kafin tace
“Umma kuzo muje a fito da lefen nan kowa ya gani ko?”
Anty Zainab ce ta iya ce mata “eh”
Itanma da kyar,
daga haka ta mik’e ta d’an dafa Umma kana tace
“Muje Sadiya”
Da kyar ta iya mik’ewa k’afafun ta suna rawa suka jera ita da Anty Zainab suka bi bayan Ummu suka yi parlourn b’aki.
Mutane kam wasu basu ma samu damar shiga ba
dan akwatunan sun cike parlourn tap!
Ganin kowa cirko cirko a tsaye iya y’an k’alilan kuma na a ciki suna mik’owa ana fitowa da shi ne yasa suma suka ja suka tsaya a gefe
kai kana ganinsu ka san basa cikin hayyacin su..
Ta gabansu
Hudan, so take ta yakice tunanin Arshaad a kanta amman ta kasa!
K’arshema bigewa tayi da adduar Allah yasa tana fita ta ganshi amman yanayin yanda taji an zaunar da ita a doguwar kujerar da aka k’awata domin ita da shi ne yasanya ta fahimci bai zo d’inba.
Ummu ce ta fito ta bud’e taro da addua sannan ta fara gabatar da al’ada a Huda,
A matsayin uwa.
Mama suna parlourn Madu, tun lokacin da Mommy da Aslam suka zo suka buk’aci ganinta har yanzu bata samu damar fitowa ba.
Wata distant relative d’in Shuwa wadda zata d’an girmi Shuwan kad’an ce
ta k’arasa wajen sannan
cewa Ummu “Ina uwar Angon?
Ta zo ta zauna a kusa da ke
yadda kina gamawa zata karb’a.
Sannan ba ayi welcomin Ango ba kuma ba aga shigowarsu ba besides ai dole sai yananan ma tukunna za ayi komai.
Na ga bai riga yazo ba
amman kin yi wuff kin fara abu haka bayan kuma akwai abubuwa da yawa before wannan.”
Karaf! A kunnen umma. Daman neman abun yi suke yi ita da Anty Zainab shiyasa
suka zo suka zauna a k’asa gefen kujerar Amarya. Da sauri sannan da d’an k’arfi yadda ta tabbatar kowa zai ji
Umman tace
“Eh kam tabbas!”
Sannan ta mik’e tsaye
kafin tace
“Uwar Ango! Tana Ina?
Ana buk’atar Uwar Ango a nan yanzu yanzu”
Da k’arfi ta yadda kowa ya iya jiyota tunda daman wak’ar da aka kunna a low tune yake
kuma iya murya ne kawai babu kid’a.
Da sauri Ummu tace
“Umma meye haka?
Idan kin yi min magana ba zan je In kirata baneba?
Ko hakan da kika yi kina tunanin shi zai sa ta fito?”
Still da k’arfi Umma ta sake cewa
“A’a, ai ji nayi kamar kince bata zo ba!
Gashi shima Angon shiru.
Duk da dai ni ba Shuwa bace ba amman Tabbas na asan cewa Ango da Amarya a tare ake shafa musu lalle, manshanu, da ragowan abubuwa! Dan har yau ina tuno naki, a tare aka shafa muku ke da Muhammadu wanda ya zo wurwuri
bai tsaya b’ata lokaciba,
Ita kuwa yayarki daman ba a yi mata ba
shiyasa gaba d’aya auren nata duk biyun suka tab’arb’are!
To kuwa kinga ai ba zan so auren Huda itama ya samu matsala ba ko?
Dan haka gara mu jira Angon ya zo ko nan da k’arfe taran dare ne mu masu iya jiransu ne
har sai shi da uwarshi sun zo an yi alada yadda ya kamata!”.
Ta k’arashe maganar har wani karkarwa jikinta yake yi, wanda kana gani ka san bala’ine kawai yake cinta.
Ummu bata ga k’arasowar Sakina ba sai tayi tana cewa
“Eh tabbas kam Hajiya Umma kya zauna ai kiyi ta jira tunda daman kallon kwaf da munafurci ne ya kawo ki!
Mu nan dukkannin mu munada aikin yi kuma ba mu da lokacin zaman jira har k’arfe taran dare!
In dai Ango kike son gani to ki bada nan da awa biyu zaki ganshi sun iso tare shi da iyayenshi maza da za su kawo lefe wanda na tabbatar abunda ya tsaidasu kenan
ba wai abunda makirar zuciyarki ta shirya miki ba!”
Umma na shirin k’arasowa inda Sakinar take taga Ummu ta d’auke ta da mari!
Cikin yaren Shuwa Ummu ta hau yiwa Sakinar fad’a k’asa k’asa yanda ta tabbar ba kowa ne zai ji su, tace
“Baki da hankali ashe?
A cikin dangi da y’an uwa za ki bud’e baki kina yiwa babbar mata rashin kunya haka?
So kike a tafi dake a baki?
Wuce!
Wuce ki tafi chaan sama d’akin Shuwa ki rufe!
Idan ba ni na neme ki ba wallahi kika fito sai ranki yayi mugun b’aci!”.
Juyawa kawai Sakina tayi ta wuce tana ji kamar ta had’iye zuciyarta!
A kan Umma aka mareta a gaban mutane haka!?
Kuma ta tabbatar tunda Umma ta fara wannan maganganun to fa idan taka mata burki aka yi ba ko kuma Arshaad d’in ta gani ba tabbas ba zata
tab’a barin mutane su sha ruwa ba.
Ita daman tun d’azu da ta ganta tazo da sassafe ta san ba alkhairi ne ya kawota ba.
Ita da take da abun fad’a a gindi amma shine har take da audacity d’in yin magana!
Wallahi yau da Ummu ta barta da sai ta yiwa Umma zazzagar kwanyo....
Da wannan tunanin ta k’arasa d’akin Shuwa, sai a lokacin hawayen bak’in ciki suka samu nasarar zubo mata…
Daga Shuwa sai Baabaa Talatu ne a d’akin suna
shirya tukuicin da za a bayar in an kawo lefe.
Baaba Talatu tana ganin ta shigo tana kuka ta mik’e tana
“Subahanallah, mai ya
faru?
Ke da waye?”
Da sauri ta k’arasa ta hau shafa fuskarta inda hannun Ummu ya fito tarr!! Ya kwanta akan farar fuskarta
Cikin fad’a Baaba Talatun tace
“Wanne d’an iskan ne ya mare ki??”
Fashewa tayi da kuka
cikin kukan tace
“Umma ce take ta abubuwa a waje, shine Ummu ta mareni
wai dan....”
Ai bata tsaya jin k’arshen ba,
tayi waje.
Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar
tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina .
Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba...........”
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
53
Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar,
tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina.
Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba.”
“To”
Kawai Sakina tace,
tana mai sake goge fuskarta
sannan ta koma gefe ta fara warware laffayar jikinta da d’aurin d’ankwalin dake kanta..
Sai da ya rage daga ita sai long camisole d’inta wadda ta saka a ciki mai dogon hannu yayinda dogon gashinta ya kwanta a gadon bayanta sannan ta fara k’ok’arin kiran Arshaad...
Tayi mishi misscalls sun fi ashirin amman shiru. Dan haka
nan da nan hankalinta ya sake tashi…. Tun jiya take danne zuciyarta take k’ok’arin kawar da maganar da Aaima ta gaya mata a cikin kwakwalwarta
amman kuma attitude d’in Arshaad da k’in zuwanshi a yanzu ya yi matuk’ar bata tsoro.
Ba wadda take jin fargabar taji wannan batu irin Hudan
shiyasa jiya ta kwana Sallah akan Allah yasa maganar Aaima ta zama k’arya
idan kuma gaskiyace Allah yasa su Abba su gyara lamarin cikin sauk’i…
Gaba d’aya hankalinta a tashe yake dauriya ce kawai take yi, tana kuma k’ok’arin taga ba wanda ta bari ya ma ji zancen har a samu a gyara lamarin in sha Allah.
Ganin arshaad d’in bashi da niyyar amsa ta ne
yasa kawai ta kira Auwal
dan taji me ke faruwa
a ina aka tsaya..
Shi sai a bakinta ma yake jin wai ‘Arshaad d’in bai je ba’
Saboda shi suna asibiti.
Ganin kamar bai san me yake faruwa ba ya sanya taja bakinta tayi shiru
saboda ance yawan yayata magana kan iya tabbatar da gasgatuwar ta. Dan haka kawai sai tace mishi
“ya duba musu Arshaad din pls”
Daga haka suka yi sallama.
Daman shima yana da shirinshi zai je wajen
So yanzu zai duba Arshaad d’in sai su wuce tare kawai
dan haka ya cewa Dad
“Bara yaje gida,
Sakina ta kirashi wai har yanzu Arshaad be k’arasa ba.”
“to” kawai Dad d’in yace masa.
Yana fita shima Dad din ya d’au waya ya kira Gwaggo Asabe yace
“Dan Allah tazo ta ji da Ummi.
Zai yiwa drivern da zai kawota kwatancen asibitin da suke....”
Drivern da ya kawota (Gwaggwo Asabe) shi ya maidashi mansion d’in.
Yana zuwa ya tarar da Daddy
ya shirya chap yana jiranshi
da akwatuna dozen biyu sun sha decoration
sai kuma basket na gift guda biyar, da akwatunan uwa uba gwaggwo da kawu..
Duk sun had’a. Tun sassafe Mommy ta aiko da kayan
shi kuma ya duba ya tabbatar komai dai dai.
Sai da aka gama loda kayayyakin a motoci wajen goma tukunna Abba ya fito da shirin shi shima da alama rakasu zai yi!
Dad, yana shirin shiga mota har driver ya bud’e mishi k’ofar motar ya hango tahowar Abba!
Wani takaici ne ya d’ebesa
bai san lokacin da ya daka masa tsawa ba! Yace
“Idan ka k’araso nan wallahi sai mun kwashi y’an kallo ni da kai!
Kaji dai na rantse
wallahi!!”
Ya k’arashe maganar yana mishi nuni da yatsar shi manuniya yana nuna sama.
Ajiyar zuciya Abban ya sauk’e kafin yace
“Dad nimafa rakaku zan y....”
Cikin fushi Dad d’in yace
“Kaga mota nan, zo ka shiga!
Amman direct
Asibitin da aka kwantar da Ummi zaka je
Idan kuma ba haka ba to ka koma ka zauna a ciki.
Zab’i d’aya!”
idanuwa direbobin da masu aikin suka tsura musu..Ganin da Abba yayi har sun fara kwasar y’an kallon kamar yadda Dad d’in ya ambata ne yasa kawai ya juya ya koma ciki ranshi a mugun b’ace!.
Tsaki Dad yayi ya shige motar
yana mai cewa
“Ba za ku haukata ni ba,
wallahi!”.
Shi dai Daddy
shiga yayi ya zauna a kusa da shi, yana son tambayarshi
wata zuciyar kuma sai ta bashi shawarar ya bari ya Dad d’in ya d’an sauk’o tukunna sai suyi magana…
A haka drivern ya ja su suka nufi Gandun Albasa
Daddy yana mamakin meye haka yake damun Dad??
Dan tabbas ya san akwai abunda aka yi mishi......
GANDUN ALBASA.
Baaba Talatu tana fita harabar gidan ta tarar gurin har ya fara kachamewa!
Dan bayan Sakina ta bar wajen Umma da Anty Zainab kan Ummu suka dawo
wai “ai itace bata yi mata tarbiyya mai kyau ba shiyasa ta raina manya har haka...”
Ga kuma wannan tsohuwa ita ma ta kafa ta tsare tace
“Sai Ango ya fito tukunna za a fara gabatar da komai!”
Yayinda Ummu da wasu cousins d’inta suke ta k’ok’arin ganin sun yayyafa wa lamarin ruwa amman abun ya faskara!.
Baaba Talatu ce ta k’arasa ta ja wannan tsohuwar gefe suka had’u ita da Shuwa suna mata magana k’asa k’asa…
Ganin kamar ana shirin fara traditional event d’in
cikin kwanciyar hankali ne yasanya Umma ta sake cewa
“Nima fa kamar uwa nake a wajen Hudan!
Dan haka ba zan bari kowa ya tab’a ta ba har sai Angon nata ya k’araso..
idam kuma fasawa yayi ne to kawai a fito a fad’a wa mutane sai a fasa sakata a lallen,
dan ba girman mu bane mu tsaya muna yiwa mutane wasa da hankali!
Ko ya kuka gani?”
Ta k’arashe maganar tana kallon cousins d’in Ummu waenda suke gefen ta! Ba su kad’ai ba kusan kaff wajen babu wanda bai ji abinda tace ba hatta su Shuwa.
“Ga Angon nan”
Muryar Mommy wadda suka fito su uku yanzu ta daki dodon kunnuwansu!
Da sauri Mama da Aslam suka kalleta!
Ba tare da ta kallesu ba ta
kama hannun Aslam ta fara janshi
Mama na binsu a baya kamar rak’umi da akala shi kuma yana binta!..
Bata cikashi ba sai da ta kaishi gefen Hudan sannan ta zaunar da shi.
Da sauri Ummu ta matso k’asa k’asa tace
“Mommy a Al’ada fa dole sai Angon zai....
Cikin katseta Mommy tace
“A addini fa?”
Bata jira Ummu ta bata amsa ba ta sake ce mata
“Kalla nan kinga”
Tayi maganar tana
nuna mata Huda wadda sai a lokacin Ummu ta lura da yanda mayafinta ya jik’e sharkaf!
Wanda kana gani ka san ruwan hawaye ne…
Mommy bata jira jin me zata ce ba ta ci gaba da yi mata magana k’asa k’asa irin na masu hankali,
tace
“Saboda ita kawai ki bari ayi a gama!
Na tabbatar ba wai rashin zuwan Arshaad kad’ai bane ya saka ta kuka ba! Har da maganganun matar nan! Tun muna parlourn bayankun nan muke juyo komai.
Dan Allah kar kice a’a!
Kalla kiga mutane kowa ya zuba ido an fara k’ananun maganganu, na tabbatar in dai ba Angon suka gani ba to haka za a tashi ana gulmace gulmace shima kuma sai idan an samu waenchan matan sun bari anyi d’in kenan.
Na tabbatar mutane k’alilan ne kuma na jikinku sosai suka san ba Arshaad bane wannan, ba kowa ne zai gane ba
so dan Allah ki kwantar da hankalinki ayi abun nan a gama without any more dramas.
Saka lalle ai ba d’aurin aure bane ba, ba komai kawai bidi’a ce so mu bisu kawai ayi a gama.”
Tana gama fad’an haka ta juya ga jamaar wajen tace
“Kuyi hak’uri mun yi latti wani d’an uzuri ne ya tsaida mu!
Sunana Hajiya Aisha
Maman Ango, mun gode kwarai da zuwanku dan taya mu farin ciki.”
Daga nan ta juya ta cewa
Ummu
“Ni zan fara ko ke?”
Da murmushi kwance akan fuskarta.
Kallonta kawai suke yi
daga Ummu har Mama.....……
Mama da Ummu sun so hana mai video coverage da pics d’auka amman ganin yanda hankalin kowa yake a kansu
da kuma Mommy wadda tace ‘su bari kawai tunda ga wasu ma a gefe suna ta d’auka da waya’ ne ya sanya
kawai suka hak’ura.
K’awayen su Huda kuwa abun ba k’aramin d’aure musu kai yayi ba dan tabbas sun san wannan ba da shi akayi cocktail jiya ba, kuma ba shine a pre wedding ba!
A haka dai suka bar maganar akan in an tashi za suni komai a bakin Sakina....
Aslam kuwa so yake ya mik’e amman sam ya kasa!
Ya rasa dalili..tun da yake bai tab’a jin fargaba irin wadda yake ciki a halin yanzu ba!
Ana cewa k’afafuwa da gangar jikin mutun suna sagewa ya koma kamar gunki bai tab’a yarda da hakan ba sai yau da ya faru a kansa dan hatta kwayar idanunsa ya kasa juyawa, so yake ya runtse idanuwanshi ya samu ya dedeta zuciyar shi amman sam ya kasa!
Yana nan a haka yaji Ummu na rufa mishi wata jibgegiyar alkyabba akan jamfar jikinshi
Akan hular kanshi
Ummu ta d’aura mishi wani jan kyalle mai tambarin moon a gaba golden colour
(Allah yaso suna da extra)
Daga nan ta mik’a mishi wata sanda wadda ta ci ado! Tace masa “ungo, rik’e”
Mommy ce ta kama hannunshi ta sanya mishi
sandar sannan ta had’a da nata hannun ta maste!
Sai a lokacin ya samu nasarar lumshe idanuwanshi
sannan ya d’an bud’e su kad’an yana kallon k’asa....
Ba tare da b’ata lokaci ba aka fara gudanar da alada……..
Bayan uwar Amarya da uwar Ango sun yi, ragowar jama a suma suka zo suka sanya musu suka basu gift
daga nan aka fara serving abinci.
Sai a lokacin Anty Zainab da Umma suka samu suka iya zama…Umma so take yi ta sake mik’ewa tsaye tace
“To Ina y’an unwan Ango!?” ta sake creating scene amman sam ta kaasa dan in banda
dishi dishi babu abunda take gani! A ranta ta shiga aiyyana
…..Tabbas sai taci uwar malan ado! Wallahi sai ta saka an yi mishi yasin mai walk’iya!
Ba Malami ba ko uban waye shi. Kuma sai ya bata kud’inta.
Jiya jiyan nan fa ta sake komawa wajenshi dan ta sake nanata mishi, shi kuma ya
tabbatar mata da “babu aure tsakanin Hudan da Arshaad
ya riga ya gama aiki
kuma ya buga k’asa ya tabbatar ba Mijin ta bane ba
sannan
ya ingiza zuciyar iyayen shi (Arshaad) ya rura wutar k’iyayyar Hudan a cikinta
ta yanda ba zasu tab’a bari ayi auren ba musamman ma Mahaifiyarshi (Arshaad)…”
Amman kalli yadda Maman nasa taketa jan Hudan a jiki,
anyi musu hoto yafi kala nawa tare sai faman fara’a take yi tana washe baki kana ganinta ka san tana cikin tsantsar farin ciki….Inaaaaa!!!!!
Taya ma zata tsaya ta yarda Hudan ta auri wannan
No1 kyakkyawan da ita tunda take a rayuwarta ko a telebijin bata tab’a ganin mai kyawunsa ba! Ga uban kud’i ga kyau kamar aljani
Allah sarki Jalilan ta
dole ta mutu akan soyayyar Arshaad, ai kuwa idan zata yi yawo tsirara wallahi sai ta raba auren Huda da Arshaad ko sama da k’asa zasu had’e
Wallahi sai dai in rabo ya kasheta akan dai ta zauna ta nad’i wannan abun takaicin da ta san k’arshe in dai bata d’auki mataki ba to shine ajalinta!
Kuma ko yana so ko baya so sai ya auri Jalila!
Wannan alkawari ne ta d’aukarwa Jalila da ita kanta!
D’an halal ka fasa……..
Anty Zainab ce ta tab’o ta
wanda hakan ne ya katse mata tunani.
Da kyar ta iya motsa wuyanta dan ji take kamar ba jini da rai a dukkannin ilahirin jikinta
Suna had’a ido taga itama Anty Zainab d’in idanuwanta sun kad’a sun yi jazir!
Kafin Umman tace wani abu
taji tace
“Sadiya taso mu tafi,
kai na ciwo yake yi min”
Suna shirin mik’ewa
suka fara jiyo gud’a daga parlourn Madu sai a sannan ma suka lura Shuwa da Baaba Talatu da wasu y’an tsirrun mutane basa wajen
A bakin matan wajen sukaji an fara k’us k’us d’in
“Ashe tun d’azu mazan gidan Ango suka zo sun kawo lefe yanzu suka wuce
da yake falon Madu yana da k’ofar shiga da fita ta waje, shiyasa har suka zo suka tafi ba wanda ya sani
Sai da suka tafi yanzu akace aje a fito da shi” Sunaji anata k’usk’us d’in “ai motocin da suka zo da su ma kansu abun kallo ne!
Gasu kana ganinsu kaga manyan mutanen da kud’i ya zaunamawa”
Da kyar Umma take iya jan numfashi, dan ji take yi gaba d’aya iskar wajen bata isarta!.
Ummu ce ta d’an matsosu kafin tace
“Umma kuzo muje a fito da lefen nan kowa ya gani ko?”
Anty Zainab ce ta iya ce mata “eh”
Itanma da kyar,
daga haka ta mik’e ta d’an dafa Umma kana tace
“Muje Sadiya”
Da kyar ta iya mik’ewa k’afafun ta suna rawa suka jera ita da Anty Zainab suka bi bayan Ummu suka yi parlourn b’aki.
Mutane kam wasu basu ma samu damar shiga ba
dan akwatunan sun cike parlourn tap!
Ganin kowa cirko cirko a tsaye iya y’an k’alilan kuma na a ciki suna mik’owa ana fitowa da shi ne yasa suma suka ja suka tsaya a gefe
kai kana ganinsu ka san basa cikin hayyacin su..
Ta gabansu