Murucin Kan Dutse

Chapter 71 of 146

ake lectures akan likitoci na roke shi da ya bari na dan jona su kafin mu bar kasan bai ki ba don dama zaman da nake na kadaici ya na damun shi sosai.
Don bai san aikin zaiyi zafi hakan ba akansu sosai sai da mukaje ne ta fahinci abin ba haka bane.
Ranan da na fara zuwa daukan darasin sai da na raina kaina a gurin sosai don sai naga kamar mu ba karatu muke ba acan.
Haka na daure na kuke na mayar da hankalina nakuma samu karuwa sosai ga abinda naje nema a gurin.
Sai idan na dawo da yamma nakan kira gida mu gaisa dasu anty wani lokaci na samu yaran wani lokaci kuma ace sunyi barci ko sun fita.
Daddy wani lokkaci har yakan yi kwana biyu baya tare dani idan sun je wasu garuruwa na kasan dole sai sunyi kwanaki zasu dawo.
Na kwantar da hankalina ina samun karuwa a gun karatun da nake zuwa dauka can.

********* ********* *********
Barina garin ya ba matan daddy damar aiwatar da shirin su sosai akaina dukkan su biyun ba wacce ta zauna kowa da irin nata aike da take tura min.
Inda Anty kuma rashina kusa da ita yasa tasan muhinmancina a gareta sosai don ba karamin kewa na tayi ba a lokacin.
Ga yan rainin wayon matan gidan bata da shakat a kan su sun saka mata yara a gaba da kiyayyan da suke masu.
Bata son fitina dole take kyalesu don ruwan ciki irin nata tana ji tana gani yara da gidan uban su amma an hasu shakat a gidan.
Wani lokaci sai Gajiye ta rufe iddo tayi magana da kanta akan abinda ake a gidan haka yasa anty ta takura kan ta sai kafa kafa take da yaran ta da ita kanta don yaran sun riga sun saba da irin abubuwan da nake masu yanzu gashi kuma an hanasu sakewa su da gidan uban su.
Ranan a gajiye na dawo ban ko hutaba na kira wayan su yadda naji muryan ta sai banji dadi ba take nagane bata cikin daddin rasi.
Walau ciwonta ko akwai abindake damun rayuwan ta haka dai muke magana sama sama da ita.
Gashi kuma bawai fushi take ba balle nace ko dani take fushin don harda tambayana tayi Rama kina dai maida hankali ga karatunki ko ki samu ki dan diba kafin ku dawo nace da ita eh anty .
Tace don Allah ki ta hakkuri da mijin ki maza sai hakkuri balle maa yanzu da kike can ke kadai dole sai kin hada da hakkurin wani abin.
Bayan mun gama wayane na zauna ina tunanen may ke damun anty ne wai nidai in ba ciwon tane ya taso ba take boyewa ?
Fatima na kira nake tambayan ta tace lafiyan ta kalau kila dai rigimar da akayi akan yara ne nace shine har zai damay ta haka take cewa .
Mama ihisan ce ta daki Nasir wai don suyi fada da ihisan a school da suka dawo shine takama yaron ta mamare shi kuma tasa ihisan tai ta dukan shi nan dai ta labarta min irin halin da ake ciki a gidan.
Raina ya baci har nai sallah na idar raina bai daina baci ba ina zaune na kunna tv wanda kusan kallon dai kawai nake bani fahintar abinda ake a tv .
Har ya shigo banji zuwan shi yazo ta bayana tare da dan rufo min idanuwa a hankali na sauke ajiyan zuciya tare da kamo hannayen nashi ina mashi sannu da dawowa.
Nan ya zube saman kujera yana fadin wassh Allah nagaji wallahi mikewa nayi na dauko mai goran ruwa da cup na kawo mashi tare da balle marfin goran na zuba mai namika mashi ya shanye na kara mai wani ya sake shanyewa again.
Bayan naje cup din daya sha ruwan , ya mayar da kanshi bayan kujera tare da mike kafafuwan shi na duka a hankali nafara cire mai takalman kafan shi tare da cire mai safan dake saye a kafan nashi
Yace Rama idanun shi still a rufe na amsa da na,am daddy, yacce may kike tunane haka har nashigo da sallama bakijini ba ?
Kamar nace dashi gida sai dai na dake a fili nace naga yau tun safe daka fita ko waya bamuyi bane dakai.
Yace nasan zaki damu da hakan amma ba wanan bane tunanen ki fada min may kike tunane ne wai ?
Daddy babu komai na bashi amsa tare da mikewa na kwashe takalman da nufin mayarwa inda yake aje takalman shi a falon.
Ban yi aune ba naji ya jawo hannuna na fada a jikin shi ya mayar da hannayen ya rufe dani yai min zobe da hannuwan nashi.
Ya kura min ido na dan wani lokaci yace dani Rama ki fada min may ke damun ki nace ?
Maimakon nayi magana sai idona ya kawo kwalla kawai gida kike son komawa ?.
Kai na girgiza mai ban dai yi magana ba dashi yace kin gaji da nine ko nai saurin dago kai tare da kallon shi na girgiza mai kai kawai.
Yace idan ba kin gaji da zama nan dani ba akan may zaki sawa ranki damu ki shirya sai na sakaki jirgi kii koma gida .
Don ni ban gama abinda ya kawoni ba nan din, cikin daurewa nace dashi ba hakana bane wallahi wai hindatu ce ta mari Nasir akan ihisan har sai da ya kwanta ciwo.
Yace a zafafe what ?
Mari fa kika ce Rahama marin karamin yaro may ye mata haka har haka ya faru.
Nace cikin kuka wai sunyi fada da Ihisan a mota ta yaga mai note book din shi shine uwar ta mare shi har uku takuma rike shi ihisan din ta rama bugun ta son ranta.
Ita uwarshi fa tana may hakan ya faru dabata dauki mataki ba kuma bata fada min ba.
Nace daddy may kake tunanen anty zata iya yi akan hakan koda lafiya gareta balle halin da take ciki na rashin lafiya.
Nan dai na fada mai komai ranshi yai balain baci sai maimaitawa yake yana fadin mari fa abin da mamaki gaskiya.
Amma kyale su dukkan su zan dauki mataki ne a kan su ya daga waya ya kira waya bayan sun gaisa ne yake cewa da anty din yace ta bashi Amira aka mika mata wayan ta karba suka gaisa da uban yace abawa Nasir din.
Amira tace daddy Nasir baida lafiya yau two days ke nan sai aka karbe wayan a hannun ta yace da uwar mika mata waya muna magana zaki karbe wayan a hannunta?
Yaro baida lafiya baki fada min ba ta na fada min kuma ki karbe wayan gurin ta mika mata muyi magana da ita.
Zatai magana yace ba Amira wayan yanaji ana cewa yarinyar kada ki fadi wa daddy abinda ya samay shi.
Yarinyar ta karba tace daddy yace Amira na may ya samu Nasir ne baida lafiya tace maman Ihisan ce ta do sai kuma tai shiru.
Yace maman ihisan tayi mai may Amira tace daddy baida lafiya ne yace Amira bakya son na sayo maki katon teddy dakikace kina so ne tace ina so daddy.
Yace to fada min may taiwa Nasir din tace dukan shi tayi daddy ita da ihisan har bakin shi ya fashe idon shi ya kwantar da jini.
Kuma ta shure shi a ciki ya runtse idon shi yana jin zafin maganan a ran shi bai bari anty tai magana ba ya kashe wayan.
Yana mamaki ita Saade wai wani irin sanyin raine da ita haka wai da har za ai wanan aika aikan taki fada mai kuma ta hana a fada mai.
Daga haka yamike ya shige daki wanka yayi ya canza kayan jikin shi ya fito na gabatar mai da abincin shi.
Ci yake kamar bai son ci haka yasa na dan matso kusa dashi na karbi spoon din a hannun shi ina diba a hankali ina bashi har na samu ya danci sosai.
Na kwashe kayan zuwa kitchen dasu ya zauna wurin yai shiru naga ya dan shiga damu na dan daure na kawar da nawa damuwar nace dashi.
Daddy kada wanan zancen ya damay ka haka duk abinda mutum yayi don kan shi idan ta cuta mashi yau ai gobe bazata cuta mai ba.
Shi yaro an haife shi ne ba, asan mai cin amfanin shi ba watarana zata ji kunyan abinda tai mai da yardan Allah.
Ya numfasa yace ita ai bata san hakan ba da batayi ba ni bani daukan hindatu cikin masu hankali da amfani da ilimin su shi kishi haukane Rahama ?
So take tasa kiyayya a tsakanin yara na komay abinda yai Nasir shi yai ihisan ai nace hakane daddy shi zai sa ka kyale ta idan halinta ne ai zata kara.
Ya limshe idanuwan shi tare da mikewa saman kujera na karaso tare da saka kafafuwana na zauna a saman jikin shi yadda kirjina zai iya gogan jikin shi.
Ajiyan zuciya ya sauke nacs hakkuri za, ayi don kowa da halin shi ake zama dashi amma bata kyauta ba gaskiya.
Kamo hannaye na yayi yana wasa dasu guri daya yace hindatu bata san don iyayye da dubaiyya nake zaune da ita ba har yanzu.
Dadin may naji ga auren ta ba kwanciyan hankali a kaina babu ga abokan zama.
Babu gwani a gurin hindatu kanta kawai ita tasani sai yarta bata damu da damuwar kowa ba a duniya.
Ta manta da yadda aka sakani a gaba kan auren ta na daure nayi shi badon naso ba don ni a lokacin Saade ta isheni rayuwa nake gani.
Ban taba tunanen zai zo nan gaba na ci karo da wa yan nan abubuwan ba a raayuwana ya nuna kirjina da hannun shi.
Na kara manna maisu nace kafin kai gamo da wa yan nan ai kayi gamo da wasu ya jawoni jikin shi da kyau yace ummumm hakane kuma sai dai su wa yan nan na daban ne ko ?
Nan wasan ya canza sallon anan falon muka murji junan mu sai da na matar dashi komai a ranan na samu natsuwa.
Hasken safiya ya hake min idona na bude su a hankali na sauke kan daddy daya dunkule a jikina mun rufu acikin fadin zanin rufa duk jikin shi yana a kaina.
A hankali na zare jikina daga nashi na fada ban daki nai wanka saida na fito nazo na tayar dashi yai sallah ruwan dake a jikina ne.
Yasa shi bude idanuwan shi ya sauke su akaina sai kuma ya dan zabura yace what Rahama makara nayi haka yau ko nafila ban samu ba ?
Ya mike da sauri ya fada bathroom sai da ya karya ne ya shirya tsab dashi yace yau ba zan dade ba zan dawo mu shiga gari kiga gari don ki samu bakin bada labarin kasar chaina da kyau.
Yadda yace hakan yayi ya dawo muka fita tare zuwa wani unguwa mai nisa can cikin garin gidan wani abokin business din shi muka je.
Da alama su a garin ma suke zaune don har iyalinshi na garin sai dai wai mutanen kasar ghana ne su mun dan jima gidan da zamu dawo matar da mijin ta sukai min kyata na bajinta.
Ba karamin alheri na samu ba ga abokan arzikin daddy ga abinda akaje nema Allah ya bashi saa sosai an yi signing din contrac din su wanda ba karamin kudi zasu samu ba ga hakan idan sun shigo dashi Africa.
Shi da bakin shi naji suna hira da abokin shi suna cewa basu taba saan tafiya ba irin wanan karon don komai yazo masu yadda suke so don basu taba zaton hakan ba garesu.
Shirin da naga yanayi yasa nasan mun kusa dawowa gida lokacin don haka nima na dinga sayen abin bukatan da nake so acan komai zan sayo dani da anty nake sayo muna shi.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA, , ,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANCE BATA BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH DON CIN AMANAN ZAMA TARE DAKIKAYI, , , ,
51

Abubuwan sun daure mai kai tunda yake zuwa tafiya da mace bai taba irin wanan tafiyan ba da wata irin hakan .
Zai ci ya sha yadda yake so zai samu kwanciyan hankali yadda ya dace ko ranshi ya baci da ya dawo gida zan san yadda nayi na sashi ya sake.
Haka kuma yana mamaki yadda nake sayayyan kaya haka da kudaden da nake samu a gurin abokan shi da kanzo ko mu mutafi inda suke idan zasu tafi su kan min kyauta mai matukar daraja.
Ni kuma sai nake dabaran sayen kaya ina jefa a cikin kaayan shi da ake shigo masu dashi a gida Nigeria.
Babu wani wanda ke a cikin damuwa daga cikin mu munyi kyau sosai farina ya matukar karuwa don har da dan kiba nayi .
Shima mI gidan yayi haske sosai ya kara kiba jikin shi da gashin jikin shi yai mashi lub lub lub dasu gwanin ban sha, awa.
Ashe idan yai tafiya da mace ba karamin karuwa suke samu ba ga tafiyan shi yasa suke fadan zuwa tafiya idan ba da su za, ai tafiyan ba, don ba karamin alheri suke samowa ba idan antafi dasu a hakan.
Bai kara mamakina ba sai da yabani irin kudin da yake bawa mace in zasu dawo gida nata dana sauran yan uwa tai masu tsaraban irin kayan kasan da suka tafi.
Bayan na sayi wa kowa abinda ya dace na kuma yo nawa sayayyan da yaga yawan su sai da yai mamaki sosai don babu macen da yazo da ita take sayayya haka kuma kudin suna samu amma bai sanin inda suke kai kudin su agidan.
Ba karamin sayayya nayi ba da kudin daya ban don na saro bedshet na kasan chaina masu kyau pure cotton na saro takalma da bags masu kyau da sauran kayan amfanin mata nima ina son na soma yar sana,a idan na koma gida.
Kamar yadda muka bar garin da dare haka ma mukai wa garin saukan asuba da zamu dawo.
Hamza da Bashir ne suka dauko mu dare ne kowa na barci da kyat na samu layin gajiye ta fito ta bude min kofan part din mu.
Na fito saye cikin dogon riga purple, yaddin rigan mai mugun taushi da santsi, silk ne kayan sun matukar karban jikina sosai.
A hankali nake takawa na fito daga motan bashir din ina tare dashi ya riko dayan hannu na ina rataye da handbag dina mai kyau da tsada a kafada na.
Kowa yasan da dawowan mu ranan don haka suna jin motsin bude get suka fito don taron maigidan.
Idanuwan su kar a kaina babu wacce bata razana ba da gani na gaba daya na canza masu lokaci guda.
Na koma gefe daya duk da bai saki hannu na ba a lokacin yana rike da ni still ko wace tazo ta rugumay shi.
Balaifi shima yai masu murnan ganin su nan guri yadan rude da surutu duk da dare ne Bashir yai mashi sallama ya juya zuwa gidan shi bayan ya sauke kayan da muka shigo dasu wanda kusan duk nawa ne don shi bai tafiya da kaya haka masu yawa.
Yace dasu kowa yaje ya kwanta kafin gari ya karasa wayewa don karfe hudu saura a lokacin yace zamu dan kwanta mu huta don a gajiye muke.
Basu so hakan ba sai dai babu yadda zasuyi dole suka fice suka bar mu don yaki sake ni na koma part din mu don ita antyna bata fito ba.
Basu bar juna ba sai da sukai gulma na tare hindatu tace Zulfa kinga yadda wanan yar kauyen ta koma kodai ciki ne da ita ?
Zulfa tace nima mamakin da nake ke nan gaba daya ta juye wata iri kamar yar wani da wata ?
Sukace ba dole ba Allah kadai yasan abinda sukayi haka acan hindatu tace kin san namiji muna fuki ne ai.
Bamu tashi ba sai sha dayan rana daddy ya baru na fito part din ko shi sai da naita hada shi da Allah ya bari naje naga anty don yace sai two zan fito wai ina da gajiya kafana duk sunyi wani suntum don zaman jirgi da nasha.
Nashigo part din Anty dake zaune sai ganina tayi kamar a mafalki tace wai da gaske dama kun dawo ne Rama na rugumay anty da sai kallona take cikin mamaki don gaba daya na canzawa idon ta baki daya zaka rantse da Allah kace injin aka sakani na koma haka a lokaci guda yadda na goge na waye nayi kyau sosai kamar wata yar gidan wasu masu fada aji.
Nace miss you anty na ina cewa ina yaran tace sun tafi school ai tunda safe Gajiye ke fada masu dawowan ku sukai ta ihu suna neman ki.
Na zauna ina cewa kin san daddy da son rigima ko yanzu sai da nayi da kyat yabari nazo na ganki tace shi wanan yanzu wake batun shi ai duk ya burge ne gaba daya baijin has.
Nai murmushi don na gane nufinta Fatima tazo da murnan ta muka rugumay juna cikin farin ciki.
Itama ta yi kyau da ita fes kauyancin ta duk ya goge ta zama wata babba a idona.
Na tambaye ta lafiyan jikin ta take cewa dani da sauki nan muka zauna mukai hira sosai da ita tace bari taje dakin maigida su gaisa nima na mike zuwa nawa part din don na huta.
Tana shiga falon shi taci karo da kayyan dana muka dawo dasu a falon tabi kayan da kallon mamaki haka don tasan shi ba gwanin tafiya da kaya bane amma yau gashi yazo da kayya haka duniya juyin juyi ke nan.
Yana kwance barci yake ya dunkule a guri daya kamar maijin sanyi ta dan dade tsaye a kan shi tana kallon shi ta juya zata bar dakin tunda barci yakeyi.
Taji yace Saade karaso mana na gaji da yawa ne wallahi, tai murmushi

Download complete TXT · Novel page