Kanin Ajali

Chapter 31 of 34

mu ne baba ya nemo ni nan yake min bayanin mutanen sun kirashi akwai wasu takarda da zamu saka hannu a cikin shi kwanan nan don haka in zauna a cikin shiri ke nan .
Nafi kowa murnan zuwan wanan kudin duk da kowanan mu a matse yake kan zancen kudin nan dama a cikin mu.
Sai dai ni nawa yafi na kowa don ga Amira ta isa shiga makaranta mahaifin ta yace shi sai priravert zai sakata bai kaita na gwanati.
Har kaita babban wan mu yace zaiyi wani makaranta dake kusa damu na gwaunati amma ya hana hakan.
Wai sai lokacin da ya samu kudi zai kaita makarantar kudi irin na yayan masu shi karya da burgan aiki irin nasa.
Wai isan baka isa irin na dan tallaka daya dauki duniya da fadi kamar jamil sam shi baison yin abin kananan mutane.
Bai gida ko da baba ya kirani sai da ya dawo nake fada mai kiran da baba yai min din har ya fara fada yana huci wai na fita ban fada mai ba.
Saida nace akan kudin mu ne kuma ka bani baki ko baka nan idan an kiranika ace udn in tafi.
Sai naji yace yanzu akan kudin ne suka neme ki nace eh baba yace sun kira kudin zasu iya samuwa ko wani lokaci.
Sai naga ya kai zaune yana fadin saboda Allah yausje ke nan nace yadai ce zasu samu ko wani lokaci daga yau za a iya kiran mu.
Nan fira ya kaure a tsakani mu duk akan kudin da zasu zo muna ya fara sabon tsare tsaren shi ina kallon shi harda tsuki yana fadin.
Sai dai tsiyan kudin naku kuma sai anjawa mutane rai dashi kafin ya fito mm nace ba dai in ya fito ba za a mu samu.
Sai bude baki yayi yana fadin na matsune kudin suzo wallahi don a uzurce nake dasu dama na rasa inda zan samu kudi wallahi ina da lalura mai karfi a gabana.
Nace idan ma kasarai ga kudin nan gara ka fitar don wallahi dakina zan gyara da sana, a wanan karo ba zan bawa kowa ba gaskiya.
Fadin hakan danayi ya kalle ni da mamaki tare da fadi haka kikace nace haka din ne ma wallahi don ni zaman nan haka ya ishe ni.
Wasa wasa daga fadin haka ya fara daure mun fuska yana wani sham kanshi dani tun ma kudin basu iso ba gare mu ke nan.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Wanda baba ya kira a waya ne yake ta faman magana a cikin wayan sai da baba ya tsnkayi muryan kamar daga sama mutumin na fadin hello hello ya karba shi da sauri tare da fadin.
Hello mr Josua mun tashi lafiya ya iyalinka mutumin ya karba wa baba don wayan a handfree take a lokacin kowa najin mutumin a lokacin.
Baba yace mr Josua dama akan maganan kudin yaran nan ne don Allah nawa ne kudin karshe da aka turo masu nan mutumin ya shiga yin bayani dala dala a waya yadda kudin suke a yadda zamu fahinta.
Yana gama bayani yace ihope ba wani matsala aka samu ba dai ko baba yace yarinya tace abinda ta gani matar nan ta nuna mata miliyan goma sha shidda ne .
Jesus mutumin ya furta da karfi lokaci guda tare da fafin ai duka kudin ma idan an hada bai kai haka ba sai kace kudin wani IG ko commitioner.
Nan dai ya kara bayani baba yai mai godiya ya kashe wayan tare da fadin idan ma baku yarda ba ga nomban mutumin zaku iya kiranshi kuji karin bayani a gurin shi.
Sai baffa yace ta yaya zataga abu a rubuce yanzu kuma ace ba hakana bane ?
Innalillahi inji baba kabir Baffa nine kuma zan cuta maku yau kan kudin ku yace baba ba hakana bane don za a iya canza digit din kudin su rage babu abin da ba a iyawa gaskiya.
Hawaye ke zuba daga idon baba kabiru na bacin rai kan maganan da mukayi yanzu a gaban kowa yace cikin wani murya mai ban tausayi ga mai saurare.
Josua ko zaka iya hada ni da wanan matar da ta bamu takardu muka cika ranan Josua yace kwarai kuwa tana nan office din ta ai bara nakai mata wayan.
Dan shiru ya biyo baya kafin ya kai ma matar wayan ta dauka muna ji ta dauka baba ya fara tambayan ta da fadin ko zaki duba muna takardan mu ji nawa muka saka hannu a kai.
Ta duba tace miliyan shidda ne kamar yadda baba ya fada muna din nayi caraf nace ba naka sha shidda a waje farin rubutun kudin ba ?
Dariya mai ban haushi sosai matar ta kwashe dashi sosai muna jin ta a waya tare da fadin amma ke kina da abin dariya fa.
Luckly muna da komai anan a cikin computer mu muna reconding idan zaku iya zuwa kuzo ku duba da kan ku wanan lamban da kike magana.
Shine serial nomba na kudin ku nan ta kara karanto min shi wanda shi din ne na gani a can sai nace bashine kika ce min kudin namu ba.
Tace ke mahaukaciyar ina ne da za a baku wanan kudi haka mai uban yawa kiyi abu na masu hankali mana.
Zaku iya zuwa ku duba komai na nan wurin mu a rubuce cikin computer mu kuzo ku duba shaaa ta katse wayan.
Muryan baba musa ne ke fadin assha wanan hali a ina kuka samay shi ne haka kan kudi ku rufe ido kuciwa kowa mutunci wanan bawan Allah idan baku gode mashi ba bai kamata ku nuna mashi haka a fili ba.
Baffa yace baba ba hakana bane shi sharian kudi idan yazo ds kowa kana iya yin sa ai mu abinda ta fada muna ne ta gani muka sa rai.
Baba kabiru dai bai iya fadin komai ba lokacin sai hawayen da yake sharewa baba yushau yana bashi hakkuri kan maganan.
Nan dai baba musa ya zage mu tas yasa mu bawa baba kabir di hakkuri wanda har muka gama ya kasa furta komai gare mu.
Haka muka fito rai a bace don kudin ba suyi muna dadi ba kamar wa yanda suka sai da wani abu a kasuwa ba mahaifan su ne suka rasu ba.
Gidana muka nufa da kudin kai tsaye inda muka samu Jamil yana jiran mu a kage dashi kamar yai tsuntsuwa ya bimu gidan baba din inda ake rabon kudin.
Muna shiga yana ganin mi rai a bace yake fadin yaya akayi baffa ya ce kai rabu da mashiririciya kawai taje ta sa mutane a ciki kawai ashe ba haka na bane abin.
Nan ya tare shi da fadin kai abi abin nan a hankali zaku gane gaskiya fa ba abinda ba a iyawa yanzu wallahi.
Kana ganin ba hadin baki akayi a rage kudin ba a baku abinda bashi bane wai ma nawa ne suka baku wai ?
Baffa yaja tsuki ya mike ba tare da ya fada mai komai ba ya fice daga gidan .
Kallon mamaki Jamil ya bishi dashi har ya fice nan dai ya sakani gaba na fara mai bayanin shiririta cikin rashin fahinta.
Yace kai ina ba za a yarda ba wallahi zanbi in gani har sai na gano gaskiyar wanan maganan sai kudin nan sun fito wallahi.
Yace bari in nemi layin baba hamza wani dan uwan mahaifin mu dake aikin yan sanda shima a sokoto ne ya mike ya fita.
Don zuwa nema layin baba namu dake sokoto ya fita bai dade ba ya dawo yana fadin na samo layin baba hamza barj in kira baffa yazo muji yadda za a yi.
Ya zauna yana kiran layin baffa din har ya katse bai dauka ba ya ha tsuki ya kasa hakkuri ya kira layi wanan baban namu na sokoto can ya dauka.
Kun san mutanen yanzu sai a hankali maimakon ya gyara zancen sai cewa yayi da Jamil tunda ta fadi haka ta ganine.
Ni yanzu abinda zanyi shine zan nemo maku wayan wanan da aka saka gaba wurin fitowan kudin ku don muji gaskiyan maganan.
Idan ya kama kuzo ne sai ku shirya kuzo ku samay ni nan sokoto muje office din da ake abin muji komai.
Basu kashe waya ba suka shiga zagin su baba ina jin ban iya daukan matakain komai ba akai don nima a lokacin na hau sosai dasu a raina.
Nan dai muka bar zancen iba batun tashi in fita naji yace to yaya ake ciki ne wai banji kince dani komai ba har yanzu mana ?
Dakatawa nayi nace kamar na may fa yace a dake ba a baki kudin bane ko may nace ambani mana amma duka suna gurin baffa ai bai ba kowa nasa ba tukun.
Kamar ya suna gurin Baffa kudin ke baki da laluran yi da kudine da zai rike maki kudi ko rainin wayau ne kuma yin hakan ?
Nace suna dai guri shi ya rike baice dani komai ba har yanzu gaskiya yaja wani guntun tsuki ya mike yana fadin an sa muna da lalurar kudi zai wani rike kudi a hannun shi.
Ko ya fiki sanin duniya ne da zai wani rike kudi a hannun shi yana karami gare ku kuma nidai tunda na fadi hakan ban kara mai magana ba.
Sai dai nasan da wuya kudin nan su shiga hannun shi yadda aka saba don Baffa yasha alwashin shi zai rike namu din gaba daya dani da kanwata .
Washe gari da muka tashi da wuri ranan Jamil din ya tashi yana tambayana ko baffa yazo a daren jiya wuri na ?.
Nace tun fitan nan da yayi ba sake shigowa ba har yanzu ya ja tsukin da ya saba ja din kamar ko yaushe.
Kafin karfe biya ya tambaye ni sau ba adadi ko Baffa din ya shigo nace bai shigo sai ya ja tsuki ya fita.
Yinin ranan nan ya zauna a kofan gidan yana hira a camban yan unguwar wanda nasan zaman jiran Baffa yake ya bullo.
Sai yamma lis Baffa din yazo gidan yana hango shi da kyat ya daure ya jira karasowan shi inda inda ya dan tsaya na wani lokaci har ya dan bada time kada aga gazawan shi.
Tunda baffa din ya shigo muka gaisa nake tambayan shi ko yaga Jamil din a waje yake tambayan may zan mai idan na ganshi.
Nake fadin kai yake jiran zuwan ka tundazun ai yaja tsuki yaci gaba da min bayanin abinda suka tsara da sauran yan uwana.
Kan mu mata zamu bada dubu ashiri su maza dubu hamsin a rabawa yan uwa na birni dana kauye mazajen mu kuma dubu hamsim daga cikin kudaden mu .
Sauran zai aje muna a gurin shi ya duba abinda ya dace asai muna dashi don gudun tabarbarewan kidin a hannun mu.
Ban kai ga magana ba Jamil din ya shigo gidan yana fadin Baffa ka shigo ai dazun na kira layin ka bai shiga ba tunda safe nake gwada layin naka.
Yace eh barci nake da safe na kashe wayana ne Jamil yace dama akan maganan kiran baba hamza ne don na samu layin nasa har na kirashi nayi mai bayani .
Amma yace hakan ba gaskiya bane don hakama ba zai yuyuba tunda tagani a rubuce lalai an rage kudin nan ne anbi wani hanya dasu.
Tsuki Baffa yaja tare da fadin kai wanan maganan a barshi kawai, don Allah, ba kamshin gaskiya ga maganan ta ko kadan .
Jamil yace a, ba hakana bane kada kayi mamakin sai azo abincika kaga kudin sun fito daga baya don sun mayar da ita mace ce kawai wallahi ya kawo haka.
Ni tun farko ban so aje da ita wanan tafiyan ba ita kadai haka, na riga da munyi magana da mutanen sun ce muna iya bi hakkin mu.
Wani kallon kai din Baffa yaiwa Jamil tare da fadin da kudin wa zakuyi wanan hidiman haka yana fadin haka ya fice yana dariya.
Ina zaune ina sauraren su, nan dai ya bi Baffa din zuwa waje sin dade suna magana dashi koda ya dawo naga fuskanshi a daure .
Sai dai yana ga bakan shi na son abi kidinkidin din kudin da yake tunanen an lake muna a sokoto.
Yana wanan maganan sai dai hankalin shi yana gun kaso na da baiji labarin shi ba har lokacin don haka a cikin dare ina barci ya tutseni ta hanyar tayar dani daga barci.
Sai na fada mai ina kudina suke akan may ba a bani ba yadda aka saba bani nawa a hannu na da farko wanan karon aka hana min.
Nace suna gun baffa duk kudin namu yana gurin shi ga baki daya ya rike ranan dai munyi fada sosai dashi kan kudin.
Da safe kamar baffa ya san munyi wanan fitinar sai gashi ya sallama min da kudi daya lissafa min din zai bawa kowa ya fara fitar wa sai ga Jamil ya fito daga daki fuska a daure yana shan kanshi kamar wani Alhaji dashi.
Sun gaisa da baffa a tsatsaye baffa ya kirgo kudin daya ware mai daga cikin kaso na dubu hamsin ya miko mai kallon kudin yayi shekeke tare da fadin wanan fa kudin may ye ?
Shima cikin daure fuska ya bashi amsa da fadin kason kane daga cikin kudin matan ku dana cire makowanin ku.
Kallon kudin yayi kamar ba zai karba sai kuma ya karba yana juya su a wullakance tare da fadin wanan ne kason nawa wanan karon?
Eh su muka cire maku inji baffa shima ya kara bashi amsa a wullakance kamar yadda yai mashi magana shima.
Yace kasan yadda mukai tsamanin kudin ba haka suka zo muna ba don haka ayi hakkuri da abinda aka gani kamar kowa.
Ya juya inda nake yaci gaba da fadin sai kudin da za a rabawa mutane gasu nan naso nakai masu amma ina ganin banda lokacin yin hakan don zan koma wurin services dina wanan satin.
Fita jamil yayi a dakin rai bace bai kara bi ta kan mu ba kuma ya fice gidan ga baki daya har muka gama maganan mu da baffa din.
Ashe komawa yayi kofan gida wurin wani icce ya zauna yana hadiyan rai don bakin ciki da takaicin da ke diban shi a lokacin.
Shi a ganin shi an mashi rainin wayau don may za a yanka mai abinda za a bashi daga cikin kaso na kuma don wullakanci.
Ya dade gurin zaune yana sake sake a zuciyar shi har ya gaji ya mike ya shiga gari don kudin basu usan shi ko biyan bashin gari balle na can inda yake zuwa din.
Cikin dare ya dawo har lokacin fuskan shi ba wani walwala a tare dashi sai bacin rai zalla da yake tare dashi.
Muna zaune da yarana muna hira ya shigo falon ya samay mu a zaune muka gaida shi da dawowa gida.
Ya amsa muna wani iri dashi ni dai ina zaune ina jiran jin abinda zai ce min din wuri ya samu ya zauna tare da bude abincin dake rufe nasa.
Ya juyo yana kallo na da tambayan yaya naga miyar ba komai a cikin sa kuma ?
Nace ba komai da zan saka ka fita baka dawo ba tu dazun kuma naga yamma bayi na dora hakana.
Na bashi amsa ina kawar da kaina gefe daya yace naga alaman kun shiry yi min cin mutunci ke da yan uwanki a gidan nan .
Kuna son mayar dani wanda bai san ciwon kanshi ba ko wani gara can dai kuke kokarin mayar dani ?
Wanan ai wullakanci ne da rainin wayau ni ake gudu da kudin ki ko may yanzu don ban gane may kuke nufi dani ba haka ?
Shiru nayi ina kallon shi yaci gaba da fadin don kun raina ni za a dauki wani dubu hamsin a bani anga mabukaci ko may ?
Na kasa hakkuri da maganan da yake fadi din nace ni may ye nawa a cikin maganan nan tunda bani na tsara hakan ba.
Idan bake kika tsara ba waya tsara hakan kudin su ne ko naki idan ba da yardan ki aikai hakan ba yaya zasuyi hakan da kudin ki ?
To bari kiji ni ba zan yarda da wanan tsarin da aka fito dashi ba yanzu dole ne ki karbi kudin ki hannun baffa ki bani in juya su yadda muka saba.
Nace ni wanan ba magana na bane ka samu baffa din kuyi magana dashi zaifi amma kazo ka samay ni kana fadin kai baka yarda va nima naga kudin nawa ne.
Yace sai sun cire kudin su da kaci na haya aciki saura kuma kadan kadan zai dinga bani ina sayen abu dashi idan bukatan hakan ya taso min.
Bai bari nakai aya ba yace a harzuke ida baki karbo kudin na ba wallahi sai rayuka su baci a gidan nan ni za a kawo wa raini hankalin banza ko wa ?
Ya kare da fadin don rashin tausayi zakiyi wa yara abinci haka babu komai a ciki may ye amfanin kudin da kika samu yanzu yana fadin haka ya shige daki ya bar ni a gurin zaune.
Wasa wasa ya tayar min da hankali sosai kan kudin ya hana mu zaman lafiya shi kuma ya kasa yiwa baffa maganan kufin da bakin sa sai ni yake turawa in mashi.
Tun ina boyo har yakai na kira baffa din na fada mai halin da ake ciki akan kudin baffa yace idan yana son kudin ya nemay shi mana ai bani zaiwa magana ba.
Kudin da baffa ya bani in kai wa yan uwana a kauye yasa ni gaba a kansu su da yake gani a kusa sai da ya kwaci dubu talatin a cikin su da fada da komai kuwa.
Sai lissafin ya bace min yadda zan raba kudin wa mutane tu ina boyo har dai najewa anty da naganan bata so saka muna baki ha amma haka ta hakkura ta yi min bayani.
Ta gane cewa Jamil

Download complete TXT · Novel page