Showing 324001 words to 327000 words out of 452169 words
Chapter 109 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar
din Mayraah?" Mayraah tace "Na yi" Zaunawa tayi tana kallon Mami a hankali tace "Mami da safen nan za a kai ni can gidan?" Mami ta ɗan buda ido tace "Har kin gaji da nan din Mayraah?" Mayraah sai taji kunya, sai a sannan taga kamar fa bai kamata tayi maganar ba ma, da kyar ta girgiza kai lkci daya ta wayance tace "A'a Mami, dama Yaya zai kai ni gidansu wata kawata ne..." Da mamaki Mami tace "kawarki kuma?" Wani yayan? Ko Aliyu?" Mayraah ta gyada mata kai da sauri, Mami ta ɗan yi murmushi tace "Nan din ma don ya zama dole ne aka kawo ki Mayraah, da aure a kanki fa yanzu, auren da ko tarewa baki yi ba, so it's not possible to go out anyhow now, ita kawar ta zo nan din mana ta sameki" Dai dai nan MD ya shigo parlon, Mami dake kallonsa tace "Sai yanzu ka tashi Daddy" Yace "Yanzu kuma, no... karatu nake" Mami tace "Kai kace zaka kai ta gidan kawarta? Ko dai baka da kai ne?" Ya buda ido yana kallon Mayraah, da sauri ta girgiza kai tace "Aa Mami dama yace min sai dai ta zo nan...." Zai yi magana Musharraf ya shigo parlon, Mami na kallonsa har ya shigo ya zauna, shi dai MD kallon gefen ido yayi masa ya dauke kai, Calmly Musharraf ya kalli Mayraah yace "Good morning Mayraah" Ba tare da ta kallesa ba a takaice tace "Ina kwana" Yace "Lafiya lau" Mikewa tayi ta nufi kofa, kafin ta fita taji Mami dake kallon Musharraf tace "Lafiya son? What happened?" Sounding pissed off Musharraf yace "My expensive white Duvet da shekaranjiya na fara amfani da shi Daddy ya sa min a washing machine" Mami ta kalli MD da damuwa tace "Me ya kai ka dakinsa Aliyu?" MD yace "Ni bana repeating duvet sau biyu, kuma ina son kwanciya ne a dakin, me yasa bazan sa a washing machine ba? He should do better in his sanitary practices, why use duvet for 2 days" Daga haka ya fice ya bar masu parlon, Mami tayi shiru wato shi yasa jiya wajen karfe biyun dare ya shigo mata daki ya dau duvet, har cikin ranta take tausaya ma macen da zata auri Aliyu. Bayan azahar MD da Mayraah suka bar gidan zai maidata gidan grandparent dinta, she was so palliate leaving the house at that moment, duk da tun safen nan bata sake haduwa da Musharraf ba, sannan sun yi waya da Maleeha tace mata zata zo da yamma, amma da ta zauna gidan nan har zuwa yamma to gwara kawai kar ta hadu da Maleehan, bayan sun yi nisa Mayraah ta kalli MD a hankali tace "Yanzu baza ka iya kai ni in ga kawar tawa ba, even if it's just for 5 mins, tace min da yamma zata zo kuma kaga ni gida zan koma yanzu" Ya kalleta yace "Toh sai mu koma ki jirata zuwa yamman" Da sauri Mayraah ta girgiza kai tace "Aa pls" Shi dai driving kawai yake, can tace "Amma da ka amshi numberta jiya ai ce min kayi zaka kirata, shi ne ashe baka kirata ba har yanzu...." Yace "Ohh na manta fa, but why not give her my number sai ita ta kirani, don ni mantawa zan dinga yi" Mayraah ta sake baki tana kallonsa, bata sake ce masa komai ba har dai suka isa Malali, bata san jiya kawai don ya kwantar mata da hankali ba ya biye ta da number Maleeha. Ammi na zaune parlon Abba tana ta kallonsa bayan ya gama magana, jin bata ce komai ba ya daga kai ya kalleta yace "Bai maki dadi ba ko Hajiya?" Ajiyar zuciya ta sauke ta girgiza kai tace "Not at all...." Yace "Mayraah is an only child and an only grandchild, it's nothing don an yi bikin a can Hajiya, sai su kawo mana ita Abuja" Ammi ta sunkuyar da kai tace "To gyaran jikin fa? ni nan jira nake ta dawo ai a fara" Abba yace "Sai aka ce maki su din ma can baza su mata abinda ya kamata ba? Hear what u are saying fa" Abba yayi murmushi yace "We can't just hijack both the Bride and Groom a wajenmu Hajiyata, ku nan kuyi naku taron kawai, su ma can su yi, kinga bayan biki sai su kawo mana amarya, in ma dakinta za su kai ta su kai ta, we can't ignore the fact that su ma suna da hakki a kanta" Ammi tace "To wai a ina ku ka zauna ku ka shirya wannan abu ban sani ba?" Abba yace "Alhaji Saminu yaje Kano wani taro dazu, so mun hadu, sai yake tambayata ya mu ka tsara bikin, a Abujan za ayi komai da komai, ni kuma kawai sai naga we are not being fair, wannan ne dalilin da yasa na gaya masa wannan tsarin don mu fita hakkinsu, and he was very happy about it" Ammi tace "Amma baka yi shawara da ni ba Yallabai, kasan irin burin da na ci na bikin Mayraah kuwa? Yanzu shkkn sai dai kawai a kawo min ita?" Abba yace "Gaskiya hakan shine adalci, su yi bikinsu a can su kawo mana amarya, ku ma kuyi naku a nan" Ammi bata sake cewa komai ba tana ta tunanin irin burin da ta ci na bikin Mayraah tun ma ba a fasa aurenta da Musharraf ba, shkkn duk burin nata ya tashi a banza kenan, Abba ya katse mata tunani yace "So now, shi Maheer din me yace maki yake shiryawa, i mean events or anything of such, ko baku yi magana ba" Ammi ta kalli Abba tace "Yace ba abinda za ayi fa, babu yanda ban yi da shi ba wllhi yaki, ko zaka masa magana kai, kaga tunda Kaduna za ayi taron bikin ae za su dinga expecting Dinner ko kuma dai wani program da mu za mu yi daga nan" Abba yace "Tunda yace baya so kawai a kyalesa, ai dama ba wai wani amfani ke gare taron ba, albarkan auren kawai ake nema, so i am in support of him" Ammi dake kallon Abba a hankali tace "A aurensa na farko ma fa babu abinda aka yi lokacin duk muna cikin tashin hankali yallabai, wannan ma sai ayi sa haka fisabilillahi?" Mikewa Abba yayi yace "Za ku iya hada naku program din mana ku yi da yan uwanki da abokan arziki ba lallai sai da shi ba, can din ma za su yi duk abubuwan da suke so ko bai je ba" Ammi bata sake cewa Abba komai ba, kawai ta bar parlon, can bangaren da Hajja da su Yahanasu da Mama Ladi suka sauka ta tafi, don gobe ake son kai lefen Mayraah kaduna, zaunawa tayi cikin sanyin murya ta masu bayanin da Abba yayi mata, Mama Ladi da ta saki baki tace "Naga abinda ya isheni, to mu meye amfanin kwaso jiki da muka yi muka yo nan din? Fisabilillahi me yasa tun wuri ba a sanar min ba inyi zamana a kadunan a amshi lefen da ni a can, to Al-qur'an komawa zanyi, dama babu yanda Hajiya Ramatun bata yi kan cewar in ɗan kara kwanaki ba nace aa bari dai mu koma Abujan mu fara shirye shiryenmu mu ma, ashe ba uwar da za ayi a nan, ranan fa da na bar gidan ranan Mayraah ta sauka gidan ita kuma, to a gaskiya Mamuda ya bamu kudin mota kawai mu koma kadunan tunda can za ayi biki, mu zauna nan mu ci me, ga can inda ake biki" Yahanasu tace "Mu fa nan dangin ango ne Ladi, kuma mu za a kawo ma amarya a damka mana a hannu mu amsheta, idan muka ce za mu je biki kaduna su wa za su tarbi Meran idan sun kawo ta??" Mama Ladi ta mike tana hada akwatinta tace "Sai ku tarbeta in mun kawota...." Hajja dai sai kallon Mama Ladi take cike da takaici, Yahanasu tace "Ke dai Ladi baki son gaskiya, ki koma kiyi masu uban me a kadunan" Mama Ladi ta juya ta kalleta tace "Kar fa ki sa ince inyi ubanki a kaduna Yahanasu, ki fita idona in rufe, a ina aka taɓa ganin biki gidansu amarya babu dangin ango ko daya? In sunce can za ayi biki mu ma nan dangin ango ai sai a cire mutum biyu ace mu je can" Hajja tace "Mariya bata iso ba, don haka sai ita ta xauna kadunan..." Mama Ladi tace "Aa wallahi, sanda ke da 'ya yanki da jikokinki ku ka guje Meran kuka mata koran kare ina ce ni da Mamuda ne kawai muka tsaya mata cikin tsanani cikin wuya? Ai ita Meran ba dabba bace tasan komai duk kallonku take, iyaka ta raga ma Ammi da ta ci kashinta ta ci fitsarinta, to kuma wani burga za a min kan Mera" Ammi ta mike kawai ta fita daga dakin, Hajja dai bata sake cewa komai ba. Washegari Surkar Dr Khalil da wata aminiyarta, sai kawayen Ammi biyu da wata matar abokin Abba, da matar ɗan uwansa na kano sai Yahanasu suka tafi kai lefen Mayraah kaduna inda Aunty Mariya zata hadu da su a tafi gidan Alhaji Saminu, kaya ne na gani na fada da suka dame na Musharraf suka shanye, ashe Musharraf bai hada mata komai ba wancan lokacin, set din gold dinta ma kadai ya ci millions, Mama Ladi suna daga cikin masu amsan lefe a parlon sai washe baki take tayi tsumu tsumu cikin dangin Alhaji Saminu ke kya ce er uwarsa ce, Kunya yasa Aunty Halima da yan uwanta da suka yi zugan kwaso lefen Musharraf a gidansu Ammi suka kasa dago kai a babban parlon, Ai ko su Mami da familyn gaba daya suka rasa inda za su sa su Aunty Mariya don tarba, a haka yan kai lefen suka bar gidan da abubuwan arziki da aka basu su ma. Tuni aka fara yi ma Mayraah gyaran jiki a gidan kakanninta, ita dai ta dawo ga ta nan gata nan ne kawai, irin kamar kaga abinda kake dauka wasa ya fara zama gaske gashi har da lefe, har a sannan she is still finding it hard to believe and assimilate da gasken fa Maheer ne mijinta kuma gidansa za ace za a kai ta, Ya Maheer fa? She just wish duk wannan abun kawai mafarki take zata farka soon, wa ennan tunanin ke kara karyar mata da zuciya ya kara jefata cikin damuwa sosai, ta dawo ko abinci bata iya ci ganin kwanakin na ta tahowa a hankali, lkci daya ta rame bata da aiki sai kuka da tunani, babu ranan da zai wuce da bazata tuna irin yanda suka taso a gida daya da Ya Maheer ba da irin relationship dinsu na Yaya with his favorite Lil sis, kawai kuma yanzu ace mijinta, it's so disturbing, daga karshe Mayraah kashe wayarta ma tayi gaba daya don kullum sai Ammi ta kirata Usman ma ya kan kirata to yanzu taji ko magana ma bata so, kakarta duk ta zata normal damuwa ne da ko wace amarya ke shiga idan aka kusa bikinta bata san wannan yafi karfin wannan damuwar ba, a ko da yaushe Hajiya Ramatu cikin kwantar mata da hankali take tana lallabata, Mayraah taji ita dama gun uwarta kawai aka kai ta kilan ta dinga jin saukin abinda take ji a ranta amma ko uwar ta zo gidan bata shigowa Bedroom din Hajiya Ramatu balle ta ganta, kuma da sun zo da sun tafi... Babban gidan ya dawo bai rabo da yan uwa da abokan arziki tunda bikin na ta karatowa, gashi tare za ayi taron bikin da na Musharraf wanda shi a Adamawa za a daura aurensa da Jiddah, duk wani event dinsu ma a can za ayi, kawai iyayensa maza ne za su je daurin aure Adamawa, a mata kuma Hajiya Halima da wasu matan Kannen Alhaji Saminu ne za su je Adamawan biki, Mami kuma will remain in kaduna don su za su kai Mayraah Abuja, duk da Abba ya sanar masu Maheer is not interested in any event sun shirya nasu events din da za ayi ranan bikin... Ana saura kwana uku biki gaba daya familyn suka tare a gidan Alhaji Saminu da Mama Ladi dake cikinsu tsumu tsumu, yan mata kaman Mayraah wa enda duk yan uwanta ne sun kusa goma and they were all by her side kamar da can sun saba da ita, and finally the D day arrived.
I dedicate the whole of this page to *Meenah Parrot, Ummi and Ma'ani.....* Ba sai nace maku komai ba but just know that i have got brand new sisters added to my fanmily list, i love and appreciate you so much sisters 🥰💖
101
Duk wani shagali da ake ta yi tun wayewar garin wannan rana Mayraah na kwance dakin kakarta zazzabi ya rufeta, har sai da aka kira mata wani likita ya zo ya dubata sannan ya aika aka siyo mata magunguna, tunda tasha drugs din ta samu bacci me nauyi, duk bayan ɗan lokaci Hajiya Ramatu ke shigowa dakin dubata don abun ya fara damunta ganin yanda Mayraah ta dau lamarin auren nan, sai a sannan zuciyarta ta fara tunanin to ko dai bata son auren nan ne, don in dai ba auren dole ba babu ta yanda mace zata shiga irin wannan damuwa haka for almost 10 days now, duk da wannan tunanin nata bata dai ce ma kowa komai ba a gidan amma abun ya tsaya mata a rai sosai. Wajen karfe biyu da rabi Mayraah ta bude ido a hankali jin hannu a forehead dinta, MD dake kallonta ya cire hannunsa yace "Ya jikin?" Juyawa tayi taga Kakarta tsaye kanta, daga gefenta kuma Musharraf ne tsaye yana sanye da fararen kaya kal just like MD, kana ganinsu kasan daga daurin aure suke, suna hada ido shi ya fara sauke idonsa kasa, ta gyara Duvet din jikinta a hankali ita ma ta sunkuyar da kai, MD na kallon Hajiya Ramatu yace "Wani magungunan likitan ya bata?" Hajiya Ramatu ta dauko masa magungunan ta mika masa cike da damuwa tace "Har yanzu babu abinda ta ci fa Daddy, shayin ma da kyar ta sha ɗan kadan dazu, jiya ma haka ta wuni ba cin abinci, ga zafin da jikinta yake" MD yace "Ai jikin ba zafi yanzu" Musharraf na kallon Mayraah cikin sanyin murya yace "Allah ya sauke Mayraah" Ita dai bata daga kai ba tana kallon lafiyayyen lallen da aka zanzara mata a hannunta tace "Ameen" juyawa yayi ya fita daga dakin, MD yace "A kawo mata abincin zata ci yanzu" Hajiya Ramatu tace "To Allah ya sa, mu je sai ka taho mata da shi" Tare suka fita daga dakin nata, bayan ta kulle kofar suna tafiya tayi kasa da murya cike da damuwa tace "Anya Aliyu yarinyar nan na son auren nan kuwa? Sai kace warce aka yi ma auren dole? Tun fa da ta zo garin nan a haka take cikin damuwa da ƙunci, ko fa bacci bata yi da daddare, anya lamarin nan ba abun dubawa bane Daddy??" Da mamaki MD yace "Me zai hana ta so auren Umma? Yayanta ne fa, gida daya suka tashi da shi, kuma baki ga shakuwar da suka yi ba wllh, kawai dai kinsan kowa da yanda fargaban aure ke zuwa masa, barin ita da nake ganin kamar a sangarce take she look so pampered, don Allah kar ma ki kara wannan magana wani yaji Umma, beside ta yaya ma za su mata abinda zai cutar da ita, for 22 years basu cuceta ba sai yanzu? Don Allah kar ki bari wani yaji maganar nan" Hajiya Ramatu tace "To in sha Allah, hankalina ne kawai ya tashi wllh, amma ni dama wa zan je in gaya ma, da kai kawai nayi magana" MD yace "Yaushe ne za a kai ta Abujan?" Hajiya Ramatu tace "Gobe da yamma in sha Allah aka tsara" MD yace "Toh Allah ya kai mu, zata warware in sha Allah kar ki ji komai, sangarci ne yayi mata yawa" Hajiya Ramatu bata sake cewa komai ba, shi ya amshi abincin da ta dauko ya tafi yaje kai ma Mayraah, ya ajiye mata saman carpet yana kallonta yace "Sauko ki ci abinci" Ta mike zaune da kyar ta girgiza masa tace "Ni bazan iya ci ba, amai zan yi" Zaunawa yayi saman kujera yana kallonta yace "Mimi kike ko wa? me yasa kike da taurin kai ne, Why are you acting like u are not civilize kamar wata er kauye, Duk maganar da na maki last week ya tashi a banza kenan i just wasted my effort, kin zata ina bada shawara ne nan da kika gan ni? Now tell me what exactly is ur problem da kike sa ma kan ki damuwa haka?" Mayraah dai tayi shiru tana kallonsa babu ko kiftawa, whereas tunanin da take daban a ranta wato imagining Maheer a matsayin mijinta, ya ɗan mata tsawa yace "Malama ba shiru zaki yi ba kina kallona haka, answer my question now" Hawaye cike idonta muryarta na rawa tace "Yaya Maheer fa" Yace "So? Haramun ne aure tsakaninku? Tun watanni nawa baya kika san ba jininki bane shi din? Is it going to take u forever to assimilate that?" Ta fashe da kuka har da daura hannu a kai tace "Na shiga uku, wllhi bazan iya ba, baza ka gane ba" Yace "Ba a kai ki gidan nasa bane.... sanda zaki iya mu muna ina? Kilan ni ina Canada" Ta kara rushe masa da kuka tace "Yayana ne fa, wllh yayana ne, he is my brother...." Dariya ta ba MD ganin she is so serious tsakaninta da Allah take maganar, Yana zare mata ido yace "To yanzu get this stuck to ur head ba brother dinki bane shi, he is ur Husband, Maheer mijinki ne yanzu, ke duk wannan kinibibin da kike kar fa nan da wata hudu mu ganki da cikin Maheer a jikinki" Ai bata san sanda ta sauka daga kan gadon ba