Showing 327001 words to 330000 words out of 452169 words
Chapter 110 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar
ta dawo kasa a rikice tace "Na shiga uku na lalace don Allah ka dena wannan magana, don girman Allah ka rufa min asiri ka daina" Gaba daya ta rikice sai gwale ido take irin ya fadi wani mugun abu din nan, dariya kawai yake yace "Za ki sani, don wallahi sai na tuna maki wannan ranan in dai na ganki da cikin Maheer" Ta hade kanta da gado da sauri tana kara rusa kukan wnn abu da yake gaya mata a kunnenta, MD ya kwantar da murya yace "Mayraah" Ta dago da sauri tana kallonsa hawaye na zuba idonta duk tayi mugun tsurewa da batun da yake mata, nan ya hau kwantar mata da hankali kamar yanda yayi wancan ranan a gidan Mami, for almost an hour he was trying to talk sense into her head, ita dai tana jingine da gado tana kallonsa kai kace she is paying attention, sai dai duk wannan abun da yake bai san her mind is absent ba, ta lula duniyar wani tunanin daban, a haka Babanta da wasu cousins dinsa da suka dawo daga Adamawa daurin aure suka shigo dubata a dakin su ma. Taro sosai aka yi a gidan Alhaji Saminu, don gidan ya dawo ba masaka tsinke saboda jama'a, kudi kam ba na wasa aka kashe ba a wannan biki, matan prominent people daga garurruwa daban daban suka halarci bikin da aka hada har da na Musharraf, komai baja baja, kaji har sai mutum ya ture, duk da babu amarya balle ango amma duk wani events da suka shirya sai da suka yi since Musharraf is also involved, ita Amarya Mayraah anyi considering bata da lafiya... Bayan magrib MD ya shigo babban parlon Alhaji Saminu tare da Maheer dake biye da shi a baya, duk yawan mazan parlon daga kannen Alhaji Saminu sai cousins da kuma abokansa ne, nan MD yayi introducing Maheer da ya zauna saman carpet bayan duk ya gaishesu da ladabi, yawanci duk basu san angon ba sai a lokacin, nan suka masa fatan alkhairi da zuri'a dayyaba, wasu suka masa nasiha akan zamantakewar aure aka dinga basa shawarwari, daga karshe Maheer suka bar parlon da MD, can gun relatives dinsu mata MD ya tafi da shi don ya gaida su, tunda Maheer ya zauna yan matan dake parlon ke kallonsa attentively, wanda yawancinsu sa'annin Mayraah ne, sai wa enda suka girmeta, Maheer dai ya gaida elders din parlon with respect, nan MD yayi introducing dinsa as Mayraah's Husband, duk sai da yan matan parlon suka kalli juna, shi dai Maheer kansa na kasa yana sauraron duk nasihar da tsofaffin parlon ke masa da fatan zaman lafiya, after like 15 mins suka bar Parlon, haka nan MD ya dinga kai sa gun dangi dake gidan yana gaishesu, daga karshe ya kai sa parlon Hajiya Ramatu da yan uwanta, second parlor dinta ta samesu don can suka zauna, da fara'a take welcoming din Maheer ta sa aka kawo masa ruwa har da abinci, Hajiya Ramatu na kallonsa tace "Yaushe ka shigo ne?" Maheer ya daga kai a hankali yace "Daxu da yamma" Hajiya Ramatu tace "Allah sarki, to ya su Amminku suka ji da taro" Yace "Alhamdulillah" Tace "Toh maa sha Allah, Allah Ubangiji ya baku zaman lafiya, ya kauda duk wata fitina tsakanin ku" Sunkuyar da kansa yayi, Hajiya Ramatu ta bar masu parlon, MD na kallonsa yace "Ka ci abincin mana" Maheer ya ɗan yi murmushi yace "I am okay, mun ci abinci da frnds dina" MD yace "Oh ok, suna ina frnds din?" Maheer yace "Hotel mu ka yi lodging" MD ya mike yace "Ka shiga ciki ka duba amaryar taka, ba ma ta jin dadi" Da sauri Maheer ya girgiza kai yace "No, ai ina ga ba sai na shiga ba, since, erm i know an dubata ai, ba sai na shiga ba" MD yace "Aa mu shiga ka dubata, kasan tun yaushe ne bata da lafiyan?" Zai yi magana sai ga Hajiya Ramatu da wani warmer cike da kaji, MD na kallonta yace "Umma wai bazai iya shiga dakin ki ya dubata ba" Hajiya Ramatu ta buda baki tace "Ni fa kakarku ce, ka manta kuma ni ce Uwargidan taka" Maheer dai yayi murmushi kawai kansa a kasa, MD yace "To kai ka ji, sai mu je dakin uwargida a duba amarya" Maheer ya ɗan kalli Hajiya Ramatu dake kallonsa tana murmushi don kawai nutsuwarsa ne ya burgeta, kana ganinsa kaga bafillatanin yaro, mikewa yayi ba don ya so har cikin ransa ba ya bi bayan MD zuwa Bedroom din Hajiya Ramatu, Mayraah har ta fara bacci kan darduma daga yin sallan magariba, MD ya tsaya yana kallon Maheer da ya kasa karasawa cikin dakin, Maheer ya kallesa calmly yace "Kaga bacci take MD, pls ba sai mun tasheta ba..." Bai jira me MD zai ce ba ya fita daga dakin, dariya abun ya ba MD yaga kamar shi ma bai son haduwa da ita ne, Maheer's reaction was so funny to him, ya ɗan yi murmushi ya juya ya fita daga dakin shi ma, Maheer bai kara minti ashirin a gidan ba ya koma hotel din da suka sauka da abokansa bayan Hajiya Ramatu tayi masa takeaway din kaji da drinks. Washegari da safe aka ci gaba da shagulgula a gidan Alhaji Saminu, ba laifi yau Mayraah ta fito cikin mutane duk da ba wani dadewa tayi ba kakar ta mayar da ita daki, tsadaddun kayan da aka mata na fitar biki kusan kala 15 uku kawai ta saka a ciki.... Bayan azahar aka fara shirye shiryen tafiya da amarya Abuja nan hankalin Mayraah ya kara mugun tashi ta dinga kuka gabanta na faduwa, tsadadden alkyabba fari da Gold Mayraah ta saka kan kayan jikinta, tayi kyau har ta gaji, kana ganinta ka ga amarya, haka aka bi da ita duk gun tsofaffin dake gidan wa enda duk yawancinsu kakanni suke a gareta suka dinga mata nasiha da yi mata fatan zaman lafiya da mijinta, daga nan aka kai ta gun kakanta shi ma yayi masa nata tare da kannesa dake parlon, shi dai Babanta na zaune a Parlon sai kallonta yake, daga haka aka maido hankali kansa shi ma yayi mata nasa nasihan, bai iya yace komai ba, kawai ya sa mata albarka aka fita da ita, dakin da Aaria take a gidan aka kai Mayraah, Aaria ma dai ta kasa cewa komai sai hawaye. Karfe hudu da rabi yan kai amarya suka sauka a cikin garin Abuja, ciki har da Mama Ladi da sae ka rantse er pamilyn Alhaji Saminu ce, Mayraah dai na jikin Mamin Musharraf ta kasa daina kuka, sai yanzu ta yarda all this while ashe ba mafarki take ba, biyar da yan mintuna convey din yan kai amarya suka iso gidan Abba, duk yawan motocin da suka kawota sai da compound din gidan ya dauke su tas, niyyar su Mami dama bayan an kai Mayraah gidan Ammi in ta mata nata nasihan Abba ma yayi mata sai su kai ta dakinta daga can su kuma su tafi masaukinsu washegari su koma Kaduna, amma sai Hajiya Safiyya da Surkan Dr Khalil ke sanar masu ai za ayi Mothers eve gobe, su yi hakuri goben sai su kai amarya in an gama, haka nan aka bar ma su Mami wani bangare na cikin gidan. Mayraah na kwance dakin da aka sauketa wajen karfe tara na dare, Badiyyah ce zaune kasan carpet din dakin duk ta dawo so calm kamar ba Badiyyah ba, ko maganar kirki yanzu bata cika yi ba sai dai ta bi ka da ido, daga daya side din kuma Farrah ce er wajen Aunty Halima sai cousins dinta uku, Farida da Maimoon sai Rabi'a wanda tare da su aka taho kawo Mayraah kusan sun zama kamar su ne kawayen amarya hiransu suke kasa kasa a dakin, duk yawan mutanen dake gidan sannan ga kuma family din Alhaji Saminu da suka kawo Mayraah kusan su Talatin hakan bai sa Ammi ta ki dinga shigowa gun Mayraah ba, don bi ni bini zata shigo dakin to check on her barin da taji jikinta da zafi tun da aka kawota gashi taki cin abinci, Mayraah dai bacci take restlessly a dakin, Ammi ta shigo rike da cup din shayi da ta hado mata ganin bata ci abinci ba, ajiye shayin tayi saman beside drawer ta cire duvet din jikinta a hankali tace "Mimi" Mayraah ta bude idonta da yayi ja tana kallonta, kasa cewa komai Ammi tayi jin jikinta yayi zafi sosai gashi sai rawan sanyi take, dama kuma Mami tace mata bata da lafiya, Ammi ta mayar mata da duvet din ta fita daga dakin ta tafi bangarenta ta dauko wayar ta, number Maheer tayi dialing, bayan ya daga da damuwa tace "Maheer baza ka shigo ka duba Mimi ba kuwa, zazzabi ne sosai fa jikinta, ga shi sai rawan sanyi take, dama sun ce tun a Kaduna bata da lafiya" Maheer dake sauraronta yayi kasa da murya yace "Amma.... ammi ko dai in kira abokina, yana nan area din yanxun nan zan...." Ammi ta katse sa tace "Har sai yaushe muka san zai karaso Maheer? pls kar ka bata min rai ka zo ka duba min yarinyata in magani zaka siyo kaje ka siyo mata sai kuma ka tsaya kana min maganar banza, in baza ka iya ba yanzu in yi ma Abbanku magana ya kai mu asibiti tunda ba kai kadai bane likita...." Kasa ce mata komai Maheer yayi, ta katse wayarta...... Ɗaga kai su Farrah suka yi suna kallon sa bayan ya shigo dakin da sallama murya can kasa, a tare suka gaishesa still looking at him, amsawa yayi sannan ya nufi inda Mayraah ke kwance, duk su Farrah suka zuba masa na mujiya, mikewa Badiyyah tayi tana kallonsu cikin sanyin murya tace "Ko za mu ɗan je wancan dakin tunda dubata zai yi" Duk suka wani juya suka kalleta, da daddaya da daddaya suka mike suka fita daga dakin sannan ita ma ta fita ta kullo kofar, shi dai Maheer na tsaye gaban gadon yana kallon Mayraah dake baccin wahala tana sauke numfashi da kyar, ya duka gaban gadon ya cire duvet din jikinta a hankali yana feeling temperature dinta, buda idanuwanta tayi lokaci daya suka hada ido da shi, hannunsa ta riko ta marairaice masa kamar zata fashe da kuka ta kai hannun nasa wuyanta tace "Yaya kaina ciwo yake min sosai, my temperature is so high, ko zaka min allura" Shi dai kallonta kawai yake, kamar dai yanda take langwabe masa a baya in bata da lafiya, a hankali ta cire hannunsa daga wuyanta ta fara komawa baya slowly kamar warce ta tuna wani abu, lkci daya zuciyarta ya tsananta bugawa, zata koma daya side din gadon da sauri kamar warce aka tsikara yayi saurin fizgota ya dawo da ita, gigicewa tayi tana zare ido, ya hade rai cikin muryar da bata san sa da shi ba yace "Ni dodonki??" Jikinta na rawa taki yarda ta kallesa tace "Wayyoo Ammi, ni dai ka kyaleni kar in gaya ka da Ammi" ƙin saketa yayi ta dinga mutsu mutsun kwace kanta da duk karfinta amma ta kasa, shi dai kallonta kawai yake, da ta ga ba sarki sai Allah ta gatsa masa cizo da karfi, hakan yasa ya cikata ta samu ta sauka daga kan gadon da gudu ta shige bandaki ta kulle kofar da makulli tana zare ido, tunda take da shi bata taɓa jin tsoronsa a zuciyarta ba sai yau.... Barin dakin Maheer yayi ya tafi pharmacy ya siyo mata magunguna, bayan ya dawo ko shiga gidan bai yi ba ya kira Badiyyah ya bata maganin ta kai mata sannan yayi wucewarsa.....
102
Washegari duk da garau Mayraah ta tashi amma sai kara dukunkunewa take cikin duvet tana sauke numfashi a hankali, nan kuma mothers eve din da za ayi ne bata son fita shine take kara narkewa cikin bargo kamar bata da lafiya, haka Ammi tayi ta lallabata bini bini ta shigo dakin dubata hatta shayi da kanta ta bata, wajen karfe goma aka bude kofar dakin, rufe ido tayi duk tunaninta Ammi ce ta kara shigowa dakin, muryar Usman taji yana amsa gaisuwan su Farrah, sai a sannan ta bude ido, ya karasa kusa da gadon ya xaga ta inda take yana kallonta yace "Ya jikin Mimi?" A hankali tace "Alhamdulillah" muryar Hajiya Amina ta ji ita ma tana amsa gaisuwan su Farrah da Badiyyah, Mayraah ta juya, Hajiya Amina ta karasa kusa da ita tana mata murmushi tace "Mimi Amarya, sannu, ya jikin?" Mayraah ta sauke idonta ta mike zaune da kyar, cikin sanyin murya tace "Ina kwana Aunty" Hajiya Amina na murmushi tace "Lafiya lau Mimi, jiya ina barin gidan ku ka iso...." Zaunawa tayi gefen gadon ta dafa goshinta tace "Allah Ubangiji ya sanya alkhairi my dear, Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a dayyaba, Allah ya kauda duk wata fitina tsakanin ku" Mayraah ta dinga kallonta ta kasa cewa komai nan kuwa wani iri take ji a ranta idan ana cewa Allah ya basu zuri'a, Ammi ce ta shigo dakin da lafiyayyen farfesun da ta sa Aunty Mariya tayi ma Mayraah, tana ganin Hajiya Amina ta juya ta fita daga dakin tun kan Hajiya Aminan ta juyo, Hajiya Amina dai ta ci gaba da kallon Mayraah tace "Tare muke da masu maki kwalliya yanzu..." Sosai gaban Mayraah ya fadi, ta marairaice tace "Aunty jikina babu kwari, sai dinga jin kamar zan fadi saboda jiri" Hajiya Amina tayi murmushi don ita bata ga alamar rashin lafiya a tare da ita ba, ta dai ga ta rame sosai, zata yi magana sai ga Ceo ta shigo dakin, ita ma ta karasa har gun gadon bayan sun gaisa da Hajiya Amina, ta amsa gaisuwan Usman sannan ta kalli Mayraah tace "How are you dear?" Mayraah ta sunkuyar da kai ta gaisheta, Ceo ta kai hannu jikinta tace "Amminki tace min baki da lafiya" Mayraah ta kasa cewa komai, Ceo tace "You look very much okay now" Hajiya Amina tace "Kin yi wanka ma kuwa?" Mayraah ta gyada mata kai, Hajiya Amina tace "Bari in ce masu kwalliyan su shigo" Tare suka fita dakin da Ceo da zuwanta gidan kenan ita ma, Usman dake kallon Mayraah ganin yanda ta rame yace "Baki cin abinci da kika je kadunan ko?" Sauke idonta tayi bata ce komai ba don kwalliyan da aka ce za ayi mata yayi mugun damunta, so tayi yau ta yini a daki ko parlor kar ta leka, Usman ya juya ya fita daga dakin. Su farrah suka dinga kallon Mayraah bayan an gama yi mata make up don wani bala'in kyau tayi, tsadadden kayan da Hajiya Amina ta kawo mata shi zata sa for the mother's eve, kayan was so unique and attractive kana gani kasan da kudi ba na wasa ba aka yi kayan, Mayraah tayi kyau har ta gaji, duk wanda ya kalleta sau daya sai ya sake kallonta, bayan azahar aka fara mother's eve a gidan, Gayya na musamman surkar Dr Khalil tayi na jama'anta ita ma, kai kace sun yi mugun dadewa da Ammi, Duk da Zainab ta zo Mother's day din amma taki sakin jiki don ko ido hudu bata son yi da Mayraah, Ga kuma matan manya manyan abokan Abba wa enda duk suka sha gwala-gwalai da nasu ankon, danginsu Alhaji Saminu ma ba a bar su a baya ba, ko wannensu yayi shiga ta kece raini, yan uwa da abokan arziki ne kaca kaca a gidan ana ta shagali, abinci ma yafi kala goma kuma duk serve ur self, kamar ance in juya daga special seat din da aka bani nake zaune na hango yan Ahalin Arewa books da yan Mayraah conversation a tsatstsaye bakin gate suna kokarin yi ma manyan securites dake bakin gate din bayanin su suwaye amma an hanasu shigowa gidan, Meenah Parrot da ta ƙwama wani arnen glasses ta mika ma Ummu Abdurrahaman er ta, rai bace take kokarin masu bayanin yanda take da Maheer da irin jajircewar da tayi na ganin an bar masa Mimin sa, Ma'ani don takaici gefe ta koma ta rataye jakarta irin na Mama Ladi tana cewa "Maheer din ne fa ya gayyace mu ba wai haka kawai muka zo ba, ni fa daga Maiduguri nake, haba don Allah ni wallahi duk an ban haushi" Fatima shanono ta zuge zip din jakarta fuska a murtuke ta ciro ID card dinta na lauya tana nuna masu, Security din ya taɓe baki yace "Madam ba ID card zaki nuna mana ba, ina invitation card dinku?" Ummi dake ta hada zufa sai fifita take da gyalenta ganin da gaske securites din suke tace "Naga abinda ya isheni, wallahi Maheer din fa yasan da zuwan mu, kawai mun kasa samunsa a waya ne, don Allah ku rufa mana asiri" Su Suwaiba Sunusi, Nana Aflam, Bint Hayat, Namafs sai yan idanuwa suke zarewa a bakin gate din ko wanne ta cakare cikin ankon da Meenah Parrot ta fiddo masu, wasu ma bashi suka ci, Aysha Bee ta nemi dakali ta zauna ta rafka uban tagumi tana tunanin uban kudin motar da ta kashe gashi ko na komawa bata da shi, Aisha Yuguda tace "To ko dai kun ga mun maku kama da matsiyata ne, kun dai san babu yanda za ayi mu shigo irin wannan anguwa ba tare da an gayyace mu ba, ku ji tsoron Allah fa" Boss Lady ta cire glass dinta ganin zufa ya fara ɓata mata make up, ita babban takaicinta dubu dari biyu da ta canza ta mayar sabbin naira dari dari zata yi liki, ga su Mom twins da Ummu Nabila da Ice da suka ki zuwa sai kiranta suke a waya wai ta turo masu hotuna da video na biki, basu san har yanzu tana bakin gate ba, Aysha S Bayero ta kalli Damsel da takaici yasa ta kasa magana tace "Tirrr dama sai da nace ma Parrot anya kuwa za a bar mu mu shiga taki saurarata, sai fafa take mana da sunan Maheer yau ga irinta nan, da