Showing 342001 words to 345000 words out of 452169 words

Chapter 115 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

ziyara gida taki barinka ka koma da matarka, don ina guje maka yanda uwar ka da makirar yarinyar nan za su hade maka kai a kwanan nan, zugata kawai zata dinga yi wllh, sai ma kaga gaisuwan walakancin da ta min da muka dawo tana zaune kasan kafet wai ina yini Mama, duk uban wahala da sintirin da na dinga yi daga Kaduna zuwa Abuja akan bikinta matar nan bata ce min ya gajiyan biki ba ga tsohuwar banza, ko da yake taga yanxu ta shigo layin manya dole ta billo da sabon fitsara.... Ahaf Mera kuma" Shi dai Maheer kallonta kawai yake bai ce komai ba, Mama Ladi ta juya ta nufi kitchen tana cewa "In kana son tsira da ɗan guntun mutuncin ka kayi abinda kawai nace maka, uwarka dai bata da kai, banda ma abun ka yaushe har ku ka tare da zaka wani kinkimota ku zo gida banda dai yaran yanzu jun zama fitsararru" Daga haka ta shige kitchen. Ammi na parlonta tare da Aunty Mariya, Mayraah kuma na Bedroom a kwance, Ammi bata boye ma Aunty Mariya duk abinda Mayraah ta gaya mata ba, Aunty Mariya dai tayi shiru tana kallonta ta kasa cewa komai, Ammi tace "Ina ga saboda ya sameta a banza bai wahala ba shi yasa har zai fara tsiro da wannan hali da ba tasa ba, duk wannan abubuwan nan da tace yake alamomi ne na cewa bai son auren, tsabar rashin mutunci a gabanta ma yake waya fa, sannan bi yake yana ce ma jama'a ba matarsa bace kanwarsa ce ita, ni dama tun ranan da suka shigo nan da Usman da yake cewa zai saketa tunda bata son auren na sha jinin jikina da shi, alamu sun nuna biyayya kawai yayi ya amshi auren, gani zai dinga yi an makala masa ita ne, don haka bazata taɓa mutunci a idonsa ba, to tun ba aje ko ina ba gwara a san me yiwuwa" Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya tace "To amma Ammi shi kin basa listening ears kin ji me zai ce?" Ammi tace "Babu abinda zai ce min, Mayraah bazata masa sharri ba kuma ni nasan bazata min karya ba" Aunty Mariya tace "To Allah ya sauwake" Ammi tace "Ameen amma don Allah ko Mama Ladi kar ki fada ma wannan magana, kin dai san halinta" Ko rufe baki Ammi bata yi ba sai ga Mama Ladi ta shigo, tana nuna Ammi da yatsa tace "Ke dai kar ki zama uwar banza uwar hofi Ammi, yanzun nan na samu yaron nan yace min ba da niyyar kwana suka zo ba kika rike masa matarsa wai bazai koma da ita ba, gashi can zaune parlor cikin sauro kamar maraya, me yasa ke duk wani abun ƙaranta daga wajenki yake fitowa? Ji irin sallaman da kika ma kishiyarki me kirki jiya kawai don za su koma Kano tare da mijinta Mamuda...." Mikewa Aunty Mariya tayi ta fita daga parlon, tana sauka downstairs ta tarda Maheer zaune a inda yake har sannan, ta zauna tana kallonsa, tayi kasa da murya saboda Bilkisu dake gyara dinning area, tace "Maheer me ke faruwa?" Ajiyar zuciya ya sauke yana kallonta, ta mike tace "Mu je daki mu yi magana" Babu musu ya mike ya bi bayanta, Maheer bai boye ma Aunty Mariya duk yanda suka yi da Mayraah ba tun daga sanda aka kawota gidansa, Aunty Mariya tace "Ya kamata kasan yarinta ne da wauta kawai ke damun Mayraah, kuma tun farko bai kamata ace ka biyeta ba Maheer, sannan babban mistake dinka wayar da ka zauna kayi a gabanta, that is not proper" Maheer dai bai sake cewa komai ba, Aunty Mariya ta mike tace "Bari in samu Ammi" Daga haka ta nufi kofa ta fita. Ko da Aunty Mariya ta samu Ammi tayi mata bayanin da Maheer yayi mata, Ammi da kusan rabin attention dinta na kan abinda take yi tace "Kin ga Mariya ni babu ruwana da duk wannan bayanin naki, banda yana ganin kamar sadaka aka basa ita har zai zauna yana waya a gabanta? Ke fa mace ce in ke aka ma haka ya za ki ji? Bana son goyan bayan rashin gaskiya, dama ni ban ma so ta tare yanzu ba, don haka duk sanda yasan mutuncinta sai ya dauketa su tafi gida amma ba yanzu ba, ko Mahmud ne ya zo zai daga min hankali wllhi sae in fitar da ita daga gidan in kai ta ajiya" Duk da takaicin da ya ishi Aunty Mariya she couldn't help it but laugh, Ammi ta mike ta bar ta wajen, Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya, Mama Ladi dai dakinta ta wuce da shayinta da bread bayan da ta gano kess din bai shafeta ba take tsoma kanta ciki. Karfe goma saura Maheer ya shigo part din Ammi zai mata sallama ya wuce gida, bai ganta a parlor ba hakan yasa ya karasa Bedroom dinta, yana bude kofa yaga Mayraah zaune gaban mirror dinta tana daure gashinta bayan tayi wanka tayi shirin bacci, tana ganinsa ta dauke kai tana ci gaba da abinda take, ya karasa cikin dakin ya kulle kofar, ta dakatar da abinda take tana kallonsa ta madubi ganin yana sa ma kofar key, dai dai nan Ammi ta fito daga bandaki, jingina yayi da kofa yana kallonta don bai san tana ciki ba, tuni Ammi ta murtuke fuska, yayi kasa da kai yace "Ammi sai da safe" a takaice Ammi tace "Allah ya tashemu lafiya" Ta gefen ido ya kalli Mayraah sannan ya juya kamar munafuki ya bude kofar da ya sa ma key ya fita. Washegari throughout haka Mayraah ta yini a gidan daga dakin Ammi zuwa parlonta ko downstairs bata sauka, abinci ma sai dai a kawo mata bangaren Ammi, Ammi na dakin da su Mama Ladi suke bayan magrib tana harhada souvenirs da za su tafi da shi kaduna don Aunty Mariya tace gobe zata tafi tunda Mayraan ma da za su je wajenta tana gida yanzu, dakinta kuma tun kan ta tare sun riga sun je sun gani, Mama Ladi ta kalli Aunty Mariya tace "To wai Mariya yaushe za mu je kwaso kaya ne? Gashi har za mu tafi kaduna gobe" Ammi da Aunty Mariya duk suka juya suna kallonta, can Aunty Mariya tace "Wani kayan kuma Mama?" Mama Ladi ta gyara zama tace "Na Mera mana, kayan dakinta, ai kamata yayi mu je mu kwaso kayan kar suje su lalace a banza gashi masu tsada dangin ubanta suka mata, kinga ga daki kaca kaca a gidan nan duk sai a zuba su a jera tunda kashe auren ake son yi, ko ke ya kika ga? Shawara ce dama na kawo ba wani abu ba" Ammi ta dauke kai ta ci gaba da harhada abinda take, Ita dai Aunty Mariya bata ce komai ba, Mama Ladi tace "Ko wani taɓara dai daga pamilyn mu yake samo asali, kafin ya isa pamilyn wasu, tirrrrr" mikewa tayi ta shige bandaki, Aunty Mariya tayi kasa da murya tana kallon Ammi tace "Don Allah Ammi ki bari ya zo su tafi da ita, ran monday fa zai koma aiki" Ammi tace "Mariya ki fita idona in rufe, yaje can ya auri warce zai aura nan da wata dayan da yace, kinga can ai zai fi sanin darajan auren tunda ba sadaka za a basa ba, Mayraah kuwa kinga ai a kyauta ya sameta" Aunty Mariya tace "Amma Ammi kin fi kowa sanin halin Maheer fa, me yasa baza ki masa uzuri ki sauraresa ba...." Ammi ta katse ta tace "Na sani ko canzawa yayi? Ke dai kiyi ta kanki ki rabu da ni da zancen nan" Aunty Mariya ta ja bakinta tayi shiru bata sake cewa komai ba... Mayraah ta shigo dakin Ammi wajen karfe takwas da rabi bayan ta tafi can dakinta ta duba press ta dauko kayan baccinta, yawanci duk kayanta na gidan ba a kai mata gidan Maheer ba, ta ajiye kayan baccin gefen gado sannan ta cire hijab din jikinta ta linke ta ajiye ta karasa gaban madubin Ammi tana daure da towel don ta riga tayi wanka, Humran Ammi ta bude tana shafawa taji an bude kofar dakin, duk tunaninta Ammi ce kamar ance ta daga kai ta gansa ta madubi a bakin kofa, da sauri ta juya tana kallonsa har ya shigo ciki ya kulle kofar, ta kulle Humran da ta bude ta nufi gadon dakin zata dauko Hijab dinta, zaro ido tayi ganin ya rigata isa wajen fizge hijab din, ta wani hade rai ta koma baya tace "Yaya baka yi sallama ba fa, kuma gashi ban saka...." Bata rufe baki ba taga ya fizgota nan da nan ta rikice tana rike da towel dinta gam tace "Wallahi zan gaya ka da Ammi, meye haka kake yi, zan maka ihu fa...." lkci daya ya fara kokarin fizge towel din jikinta, sosai ta tsorata ta kankamesa tace "Na shiga uku, Yaya wllhi ban fa sa komai ba, don girman Allah kayi hakuri wallahi zan ce ma Ammi karya nayi maka jiya, don Allah kayi hakuri" Maheer yaki ce mata komai har sai da ya fincike towel din gaba daya daga jikinta ya jefar kasa, ta madubin dakin da tayi backing yake kallonta from head to toes baya ko kiftawa, nan da nan zuciyarsa ya fara bugawa da sauri, within seconds yaji kamar ana zuke masa strength dinsa, ya kasa ci gaba da tsayuwa at the same time yana kokarin juyowa da ita tayi facing madubin amma ta wani kankamesa jikinta na rawa tana kiran Ammi. Shi kuma kafafuwansa ne suka masa nauyi sosai, bai san sanda ya fada saman gadon ba still tightly holding on to her, Bude kofar dakin aka yi, Maheer yayi saurin canza position dinsu ya maida ta kasa cikin hanzari ya dawo shine a sama ta yanda zai bata shield, ko shigowa cikin dakin Ammi bata karasa yi ba ta juya da sauri ta fita within few seconds....

107
Tun da Mayraah ta samu ta sauka daga saman gadon bayan Maheer ya koma daya side din gadon ta takure waje daya jikinta na rawa ta jawo hijab dinta dake ƙasan dakin ta rufe jikinta da sauri, hawaye ne kawai ke sauka idonta kana ganinta kasan tayi mugun tsorata, ko da wasa taki dago kanta balle ma tasan inda yake a dakin, ko ya fita ko bai fita ba oho ita dai kanta na sunkuye sai bari jikinta yake, can kasan zuciyarta kuwa ta kasa yarda Maheer ne yayi mata haka, she still can't believe it is him, wasu sabbin hawaye suka dinga kwaranya a idonta, the worst of all bude kofar dakin da Ammi tayi ta gansu, bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba tana jin kamar kasa ya bude mata ta shige kawai ta huta, Maheer dai na zaune can edge din gadon shi ma kansa a sunkuye ya rike kansa ko kwakkwaran motsi ya kasa, yana son tashi ya fita daga dakin amma ya kasa don ji yayi kamar anyi glue dinsa a wajen, everything just happened within a minute, ko da wasa bai yarda ya kalli inda Mayraah take a durkushe ba tana kuka, sun fi minti uku a haka babu wanda ya kalli inda ɗan uwansa yake, can dai daga karshe Maheer yayi karfin halin mikewa da kyar, ya nufi kofa yana tafiya a hankali har ya fita daga dakin bai juyo ba balle ya kalleta, still bayan ya shigo Parlon Ammi ya kasa fita waje, anya ma ya taɓa jin irin kunyan da yaji yau a rayuwarsa kuwa, don shi gaba daya kunyan yanayin da Ammi ta bude kofar dakinta ta gansu ne ya karasa kashe masa jiki gaba daya, he wish kawai zai gansa a compound yanzu, cike da karfin hali ya fita daga parlon kansa a kasa, ko da wasa bai yarda ya dago kansa ba yana tafiya, har zai sauka downstairs yaji muryar Mama Ladi tana kiransa, tsayawa yayi bai juya ba, ta karaso da sauri tana kallonsa tayi kasa da murya tace "Ammin na bangarenta ne ko bata nan?" Maheer ya girgiza mata kai yace "Bata can" Mama Ladi tace "To yanzu ina za ka? Na gan ka duk a sanyaye, kar fa rashin hankalin uwarka ya dame ka har kaje ka sa ma kanka wata cutar mu shiga uku, sam bata da lissafi matar, yanzu dai ka sauka kasa ka jirani a parlor gani nan zuwa" Ya sauke idonsa yace "Gida zan tafi ai Mama" Mama Ladi tace "Kaji jaraba, cewa nayi ka jirani a parlor ko" Daga haka ta bar wajen da sauri, Maheer ya bi ta da kallo yaga ta bude kofar dakin Mayraah ta shiga, ba a dau lokaci ba sai gata ta fito, Maheer ya fara sauka downstairs, ita kuma ta nufi bangaren Ammi, Mama Ladi na shiga parlon Ammi ganin babu kowa ta karasa cikin daki, tana hango Mayraah dake durkushe har sannan tace "Munafuka maza tashi ki bi mijinki, algunguma kawai, uwar me za mu ci da ke a nan idan kin kwana? Wallahi in baki yi wasa ba kashe maki aure kawai matar nan zata yi kamar yanda uwarta ta sa ta kusa kashe nata auren, auren da duk gajiyarsa bai gama bin lafiyarmu ba za a fara kokarin kashesa, salon wani ya zo gidan ya ganki yayi zaton matsala aka samu a tafi da mu a baki..." Mayraah dai kuka kawai take tana kallon Mama Ladi, Mama Ladi ta mata tsawa tace "Baza ki tashi ina maki magana ba ko sai na karaso nan" Da kyar Mayraah ta fara kokarin saka Hijab dinta sannan ta mike tsaye da sauri, Mama Ladi tace "Ehh ba shakka, wato Kinyi wanka kina jiran Ammi ta zo ta shafa maki mai ta saka maki kaya gaki er auta ko? To zo ki fita kar in kwade ki" Mayraah dai ta sunkuyar da kai ta dau kayanta ta shiga bandaki ta saka sannan ta fito tana sinne kai, Mama Ladi tace "Fita mu je...." Mayraah na tafiya a hankali ta nufi kofa ta fita gabanta na faduwan kar ta hadu da Ammi don bata san da wani ido zata kalleta ba, haka nan Mama Ladi ta tisa keyarta har suka sauka downstairs Mayraah na biye da ita kamar munafuka, Maheer na hada ido da Mayraah ya dauke kai da sauri, ita ma suna hada ido ta sunkuyar da kai gabanta na faduwa, Mama Ladi tace "Maza kama hannunta ku tafi Mashir, sannan in ba wata uku tayi ba kar ka kuskura ka sake kawo mana ita gidan nan, sam bata da wani amfanin da zata yi mana kawai ta zauna gidan mijinta tayi ibada ta samu lada, ita Ammi bata ki a kwaso tsadaddun kayan dakin da dangin ubanta suka mata a jera mata su a gidan nan ba" Shi dai Maheer bai ce komai ba kuma bai dago kansa ba, Mama Ladi tace "Bari in debo maku abinci ku tafi da shi ko da zaku tashi yunwan dare.... Ai da yake tasan bata da gaskiya tana can makale wani dakin taki fitowa" Sai a sannan Maheer ya daga kai yayi kasa da murya yace "A'a Mama, bayan kwana biyu zan zo in dauketa...." Ko rufa baki bai yi ba suka ga Mayraah ta nufi kofar fita daga parlon da sauri, Mama Ladi tace "Ahaf, ka dai ga alamar ita ma tana son tafiya gidan amma ake neman a kashe mata aure a cuceta ko, maza tashi ku tafi, in sha Allahu ran Talata in dai bamu tafi ba muna nan zuwa da Mariya, don akwai inda zan je ran Manday" Sai kuma da sauri tace "Auu, ku jira in dauko maku turaren da matar ubanka ta bada a bata, da kyar in turarrukan nan ba na daruruwan kudi bane, kaji kamshin su kuwa, nayi nayi da Ammi ko biyu ne ta dauka a ciki taki sbda baƙin kishi, to ni dai in muka zo ran talatan sai Mera ta dibar min a er kwalba...." Daga haka ta wuce sama, Maheer ya ɗan yi murmushi ya koma ya zauna, sosai reaction din Mayraah ya basa dariya, wato bazata iya zaman gidan ba, ba a dau lokaci ba sai ga Mama Ladi ta dawo parlon da ledan turarrukan, Mama Ladi tace "Wallahi in gaya maka ina shiga parlon sai gashi matar ta miko min turarrukan kamar tasan abinda ya kai ni kenan, halan ka kira Mamuda ne ka gaya masa don shi kadai ke iya mata.... Sam Ammi ba kyau" Maheer ya mike ya amshi ledan, Mama Ladi ta rakasa har parking space, tsaye suka ga Mayraah kamar munafuka a wajen, yana bude motar ta shige back seat hawaye na sauka idonta, Maheer yayi ma Mama Ladi sai da safe sannan suka bar gidan, har suka kusa gida Mayraah da ta rufe fuskarta da hijab bata daina kukan da take ba a hankali, she is just confuse at this point, idan tace bazata bi sa ba zata zauna gidan bata san da idon da zata dinga kallon Ammi ba, yanxu kuma in sun koma gidan shi ma bata abinda zai faru ba, ji take kamar ta gudu ta tafi kaduna, yana parking a space din da aka tanadar domin parking ta bude mota fuskarta a murtuke ta sauka ta nufi entrance din shiga gidan kamar zata tashi sama, shi dai ya bi ta da kallo, jingina tayi da pillar ta rungume hannu tana kallon wani direction din daban har ya iso entrance din parlon ya bude da makulli ya shiga, sai da ya shiga parlon da kusan minti biyu sannan ta shigo kamar zata tashi sama ta nufi hanyar daki, ya dake yace "Ke..." Ko juyowa bata yi ba tana ci gaba da tafiyarta, ya mike ya hade rai yace "Ba magana nake maki ba" Tsayawa tayi ba tare da ta juyo ba duk da yanda gabanta ke bugawa ta dake tace "Plss daga yau kar ka sake min magana a gidan nan, let continue with how we started i prefer that, don naga u can't keep to promise, bana son

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login