Showing 375001 words to 378000 words out of 452169 words
Chapter 126 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar
ne ta turo baki amma taki yarda su hada ido, kulle kofar dakin taji yayi da makulli sannan ya nufeta, ta marairaice masa tace "Kaga fa yaya this wasn't our agreement" Ya zauna gefenta yayi kasa da murya yace "I know, but ko na tafi Billah bazan iya bacci ba Mimi..." Kamo hannunta yayi trying to explain to her the reason why he won't sleep ko ya koma gida without saying a word, Mayraah tayi maza ta bar wajen ta hade rai kamar zata yi kuka ta koma can karshen gadon ta zauna tace "Ni dai ba haka agreement din yake ba, why not keep to the agreement" Kallonta Maheer ya dinga yi, can ya mike yace "Shikenan, sai da safe, ayi rainon babies lafiya" Mikewa yayi tun kan ya isa kofa yaji ta a bayansa ta rikesa, leaning her body against his, a hankali tace "To kayi hakuri pls, bari in ma Ammi sallama mu tafi gida" Ya juya yana kallonta ya rungumeta, ta kwanta jikinsa ta lumshe ido. Karfe dayan dare Maheer ya farka daga baccin da ya daukesa, kallon Mayraah dake bacci jikinsa yayi, a hankali ya daura kanta saman pillow being careful not to wake her, har sannan yana jin ciwon da cikinsa ke masa, ya daure ya sauka daga saman gadon ya shiga bandakinta, wanka yayi ya dauro alwala ya fito, sai da yayi sallah raka'a biyu, bayan ya idar ya juya yana kallon Mayraah, mikewa yayi ya koma kusa da ita ya zauna yana shafata a hankali yace "Meemee" Bude ido tayi a hankali, suna hada ido ta turo masa baki ta ja duvet ta rufe jikinta zata juya masa baya yace "Oh don ma na kyaleki kike turo min baki?" Kamar zata yi kuka tace "Yaya bacci fa nake ji" Yayi murmushi yana kallonta, a ransa kuwa mamakinta yake, ashe rakinta ya wuce yanda yake tunani, assuming he didn't use force on her sanda ya fara saninta da har yau suna nan jiya e yau kenan, yau din ma dai kawai hakura yayi da feelings dinsa ya kyaleta after making sure yayi satisfying dinta, ya cire duvet din da ta rufe jikinta yace "Ta shi kiyi wanka before going back to sleep Mimi" Taki juyowa tace "Zan yi anjima" Yace "No Mimi, ki daure kiyi..." shiru Mayraah tayi sanin bazai barta ta ci gaba da baccin ba without cleansing her self, mikewa tayi ba tare da ta bari sun hada ido ba tace "Pls ka dauko min towel dina a bandaki" Yace "Bazan iya tashi ba" Kamar zata yi kuka tace "Plss yaya" Tuni ta kashe masa jiki saboda salon da tayi amfani da shi wajen cewa pls din, tashi yayi ya tafi bandakinta ya dauko mata towel din ya mika mata yana kallonta, ta amsa tace "To meye kake kallona?" Murmushi yayi ya juya kansa, da sauri ta sauka daga kan gadon zata daura tawul din, ta zaro ido ganin ya sake juyowa tun kan ta daura, dukawa kasa tayi kamar zata yi kuka, yana murmushi a hankali yace "Baki san i have the screenshot of all what u are hiding a idona ba ko?" Ko kallonsa Mayraah bata yi ba ta samu ta daura tawul din hannunta ta wuce bathroom, Maheer ya sauke ajiyar zuciya ya mike ya nufi kofar dakin ya bude ya fita da nufin zuwa kitchen yayi making coffee, kukan da ya ji twins ke yi yasa ya tsaya yana kallon bangaren Ammi, after some seconds ya karasa can, sallama yayi kofar parlon Ammi ta amsa sannan ya shiga, Abba ya gani tsaye parlon sai Usman dake zaune kan kujera rike da Aryaan yana kokarin lallashinsa, duk sun cika parlon da kukan su, Ammi na kallon Maheer tace "Jikin nasu yayi zafi sosai Maheer, sun ki amsan abincin balle ruwa, ko asibitin za mu koma" Abba yace "Ku dai ku ka jiyo, banda ma tunani irin na mata, ta yaya za ku ce a lallai a dole za ku raba yara da uwarsu ta karfi da yaji ba mutuwa uwar tayi ba kuma ba ciwon hauka take ba, duk kun rufe ido kun mance Allah kan fitar da rayayye daga jikin matacce, sam babu tunani a wannan abun da ku ka yi, yanzu ku dubi condition din da ku ka jefa yaran nan tun daga shekaranjiya, da uwarsu a raye ku je kanti ku siyo madaran gwangwani kuna dura masu saboda wani dalili naku, in kun kashesu sai hankalinku ya kwanta ai" Ammi dai ko kallonsa bata yi ba, Abba ya juya ya fice daga parlon, yaran kamar sun san fadan da Abba yake sai kara buda murya suke suna tsala ihu a parlon, Usman na kallon Ammi yace "Ammi i think the best solution shine a kai yaran nan kano gun mahaifiyarsu, no mother will want to hurt her child intentionally, in ma ta cucesu ita da Allah, balle bana sa ran zata yi harming yaranta in any way, we should consider how the absence of their mother will harm dem before any other thing, ko a asibiti likitoci na jadadda muhimmancin breastfeeding ga sabon jariri...." Dakatar da shi Ammi tayi a fusace tace "To baza a kai su ba, kuma ban ga wanda ya isa yasa a kai su ba, in ma sun mutu lokacinsu ne yayi, kar ka kuskura ka bata min rai" Mikewa Usman yayi ya kwantar da Aaryan ya fita daga parlon, Shi dai Maheer na tsaye bai ce komai ba, tun a farko shi ma yasan rabasu da nonon mahaifiyarsu might affect them in one way or the other, but baya son ya bata ma kowa rai shi sa ya ja bakinsa yayi shiru ko me aka ce sai yace to, at least da sun samu breastfeeding ko na wata biyu ne, before giving them formula, Maheer ya dau Aryaan ya zauna yana kallon Ammi a hankali yace "Da safe sai a koma asibitin" Ammi tace "Allah ya kai mu" Har kusan karfe uku Ammi da Maheer na fama da babies din, sun ki bacci, sun ki shan madaran sai dai ruwa, ga jikinsu yayi zafi duk da magungunan da Maheer ya sake basu, ko gajiya da kukan ma basa yi, karfe hudu na asuba Mayraah ta shigo parlon saboda kukan babies din da taji, kanta a kasa ta karasa kusa da Ammi ta zauna tace "Ammi tashi suka yi?" Ammi tace "Ai tun karfe sha biyu idon mu biyu Mimi" Mayraah ta zaro ido tace "Sha biyu?" Amsan Ayman tayi hannun Ammi, jin temperature dinsa is high ta kalli Maheer tace "Yaya an basu magani?" Ya gyada mata kai yace "An basu" Tace "Ammi ko in goyo sa?" Ammi tace "Za ki iya" Mayraah tace "Zan iya, sai ki sa min shi a bayana" Ammi tace "To kawosa kije daki ki dauko zani" Mayraah ta ba Ammi Aymaan, sannan ta mike ta tafi dakin Ammi ta dauko zani, tsaf ta goya ɗan jaririn a bayanta bayan Ammi ta dora mata shi a bayan, Maheer dai kallonta kawai yake, ko minti goma ba ayi ba Aymaan yayi bacci a bayan nata, Ammi ta amshi Aryaan hannun Maheer tace "Kaje ka kwanta kafin lokacin sallah Maheer" Maheer ya sauke boyayyen ajiyar zuciya ya mike ya fita daga parlon bai san wa zai ba Ammi shawaran a kai yaran nan gun uwarsu ta ji ba.... Da safe karfe bakwai da rabi Maheer ya kai su asibitin don har a sannan sun ki shan madara, ga jikinsu yaki rabo da zazzabi.
Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788
119
Mayraah na zaune parlon Ammi tana rike da baby tana bashi madara a feeder, second baby din kuma na kwance kan gadonsa yana bacci, tun da Ammi tayi masu wanka wajen karfe biyar na yamma suke bacci, sai yanzu da other twin din ya tashi yana kuka Ammi ta hada masa madara ta ba Mayraah dake basa, throughout ranan yini Mayraah tayi tana renon twin din a parlon Ammi, bayan ta gama basa madaran ta rungumesa tana kallon Ammi tace "Ammi ba a yi naming dinsu ba har yanzu?" Ammi tace "Bai gaya maki sunan nasu ba" Mayraah ta girgiza mata kai, Ammi tace "Abbanku ne da Usman" Mayraah ta bude ido sosai, sai kuma tayi murmushi tace "Allah ya raya su, za mu dinga kiransu Aryan da Ayman" Ammi tayi murmushi tace "To waye Aryan din, waye kuma Ayman?" Mayraah na kallon abinda ke hannun babyn sbda ayi differentiating dinsu tace "Wannan ne Hassan ko?" Ammi tace "Eh shi ne" Mayraah tace "Toh shine Ayman, Hussaini kuma Aryan" Murmushi kawai Ammi tayi tace "Lallai kam, to a ina kika samo masu sunan?" Bude kofar parlon aka yi Maheer ya shigo, hakan yasa Mayraah tayi shiru bata ba Ammi amsa ba, Ammi tace "Miko min shi ki tashi ki shirya ku wuce gida Mimi dare na yi" fara'ar da ke fuskar Mayraah ya bace, sai kuma ta kalli Maheer dake tsaye tace "Yaya ba cewa kayi nan za mu kwana ba yau ma" Shi dai Maheer ta gefen ido ya kalleta bai ce komai ba, Ammi tace "Mi ko min shi ki je ki shirya nace" Mayraah ta tashi da kyar ta tafi ta mika ma Ammi babyn hannunta fuskarta babu walwala, dai dai nan wayar Ammi ya fara ringing, Mayraah ta dauko mata wayar dake kan kujera ta kai mata, juyawa Maheer yayi ya fita daga parlon, Ammi na amsan wayar ta ga Mama Ladi ce ke kiranta, dagawa tayi ta sa handsfree, Mama Ladi ta rafka mata sallama cikin nutsuwa, Ammi ta amsa tace "Ina ta kiranki bakya dagawa Mama, Mariya kuma tace min a tasha ku ka rabu, na kira Baaba Yahanasu tace baki je can ba" Daga daya bangaren Mama Ladi tace "Wacece kuma Baaba Yahanasu?" Ammi tace "A'a ai na zata can kika sauka ne Mama" Mama Ladi tace "Mun yi dake zan je gidan wata yahanasu ne ko dai kawai neman magana, meye kuma Yahanasu" Ammi tace "To ya gajiya Mama?" Mama Ladi tace "Aa ba gajiya wallahi, ina yan jikokin naki, inji suna ta shan madaran?" Ammi tace "Eh suna sha" Mama Ladi tace "To dai shi ya fi masu, sai sun girma za su san gata Ladi ta masu da rabasu da nonon er iskar uwarsu, in gaya maki Hasinu dai mun maida ta gida lafiya, ashe uwarta mutuniyar kirki ce ga dattako, kuma tasan abinda ya kamata, shegiyar sai kinga yanda take tsoron uwar, jikinta sai rawa yake, uwar ta mana godiya kwarai ta kuma goyi bayan amshe jariran mu da mu ka yi, in takaice maki dakin mai aikin gidan ta sa Hasinu ta kai akwatinta taje can ta gwamutsu da mai aikin" Ammi tace "To Allah ya kyauta" Mama Ladi tace "Atoh dai, ta tashi a tutar babu, ita ba ga auren ba, ita ba ga yan biyunta ba, sai taje kuma ta ci kanta, da ban fitar da ita daga gidan nan ba Allah kadai yasan wani mugun abun zata sake tafkawa, ke dai yanzu kyau ace ki sallami Mamuda ya koma kano gun amaryarsa don ki samu isasshen lokacin kula da wannan jariran, renon yan biyu da mugun wahala bari ki ji in gaya maki, barin ma ke da kika yi shekara ashirin da uku rabon ki da reno..." a takaice Ammi tace "Sai anjima" Daga haka ta katse wayarta ta ajiye, Ammi ta kalli Mayraah da ta koma kan kujera ta zauna tace "Hajiya cewa nayi ki shirya ku tafi gida ko" A hankali Mayraah ta mike, ganin duk mood dinta ya canza Ammi ta kwantar da murya tace "In dai yan biyu ne duk bayan kwana biyu sai ya dinga kawo ki kina ganinsu Mayraah" Mayraah ta kirkiri murmushi ta nufi kofa ta fita, mayafinta ta dauko da handbag dinta, bayan ta saka wayarta a handbag din ta fito ta nufi bangaren Ammi, zaune taga Maheer a parlon yana rike da Ayman, Ammi kuma ta shiga daki zata dauko maganinsu bayan Maheer yace mata jikinsa da zafi, Mayraah na kallon Maheer ta ɗan hade rai tayi kasa da murya tace "Yaya ni dai kace mata a nan za mu kwana" Sai a sannan ya daga kai ya kalleta shi ma din yayi kasa da murya yace "Sai in kin yarda a dakin ki zan kwana" Dai dai nan Ammi ta fito daga Bedroom dinta, maganin ta ba Maheer ya ba Babyn sannan ta amshesa ta kwantar da shi ta dauko masa dayan don shi ma ya tashi, Ammi taji jikin Aryan din ma yafi zafi, Maheer ya bashi maganin shi ma ta kwantar da shi, mikewa Maheer yayi ya maida magungunan dakin Ammi sannan ya fito yana kallon Ammi yace "Sai da safe Ammi" Ammi tace "Allah ya tashe mu lafiya" Da kyar Mayraah tayi ma Ammi sai da safe sannan ta nufi kofa ta fita daga parlon tana cika tana batsewa, duk Ammi na kula da cewar bata son tafiyar, a haka suka bar gidan Mayraah taki ce ma Maheer komai.. A hanya Maheer ya tsaya ya siya masu gasassun kaji, ita dai Mayraah ko kallonsa ta ki tayi, a haka har suka isa gida yayi parking, sai a sannan taji gabanta ya fara faduwa, a hankali ta bude motar ta sauka ta nufi entrance din shiga parlor tana tafiya a hankali har ta isa, gefe ta koma ta jingina da bango tana jiran sa ya bude kofar, ya karaso yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi, ya mika mata ledan hannunsa ta amsa ya bude kofar, shi ya fara shiga parlon ya kunna wuta sannan Mayraah ta shiga, ta ajiye ledan kajin hannunta zata wuce dakinta yace "It's for you Mimi" Ta ɗan yatsine fuska tace "Ni na ci abinci a gida, sai dai gobe" Yace "To ni ai baki ban abincin a gida ba" Ta ɗan yi jim, sai kuma ta dawo parlon ta nufi kitchen, plate ta dauko zata dibar masa kazar yace "Nahhh, wanka zan yi tukunna inyi sallan isha..." Tace "Toh" Tana tafiya a hankali ta nufi dakinta. Karfe tara saura Mayraah ta gama shirin kwanciya ta dau hijab dinta har kasa ta saka kan kayan baccin jikinta sannan ta nufi kofa ta fita, tana shigowa parlor taga baya nan, ta kalli ledan kajin dake parlon har lokacin, tana tafiya a hankali ta karasa can ta duka ta debar masa kazar a plate, mikewa tayi ta nufi dakinsa, tana bude kofar taga baya ciki, juyawa tayi ta dawo parlor ta ajiye kazar ta zauna, tana ta zaune tana jiran fitowarsa don tasan probably yana Masters Bedroom amma shiru bai fito ba har karfe tara da yan mintuna, tashi tayi daga karshe ta dau plate din kazar ta tafi can, baya cikin parlon hakan yasa ta karasa ta bude kofar dakin a hankali tana kallon ciki, zaune ta gansa ya jingina da pillow waya na kare kunnensa alamar he is making call, mikewa yayi yana kallonta bayan yayi ending conversation din ta hanyar cewa sai da safe, Mayraah dai kallonsa kawai take ya ajiye wayar hannunsa ya nufeta tun kan yace komai tace "Da wa kake waya?" Ita kanta bata san sanda tambayar ya fito bakinta ba, Maheer ya ɗan buda ido, sai kuma ya dauko wayar da sauri ya nuna mata call log dinsa taga da Ammi yake wayar, murmushi yayi ya kamo hannunta zuwa cikin dakin ya lumshe ido ya bude, kamshin da yaji take har ya fara saukar masa da kasala, amsar plate din kazar yayi ya ajiye yana kallonta daga sama har kasa ya fara kokarin cire mata hijab din jikinta a hankali yace "Wannan Hijab din kuma na menene?" Ta turo baki tana kara rike hijab din gam don kar ya cire tace "Ni dai ka bari sanyi nake ji" ko rufe baki bata yi ba taga ya fige hijab din daga jikinta ya jefar kan gado, tuni kamshinta ya cika hancinsa, ta zauna kasan carpet da sauri kamar zata yi kuka tana kallonsa tace "Yaya meye haka?" Yana kallonta da lumsassun idonsa yace "Tambayata ma kike" Ta marairaice masa tace "Ni dai ka bani zan je in kwanta bacci nake ji" Yayi kasa da murya yace "Meye kike boyewa a jikin naki da ban gani ba yanzu Mimi? Har can gun fa na gani" Da sauri ta hade kanta da gwiwanta tana jin kamar ta nutse don kunya, ya dinga kallon fresh lap dinta, kawai jin sa tayi a gefenta, ta dago kai da sauri tana zaro ido tace "Yaya naman kazan ka fa zai huce" yayi kasa da murya yace "Ga abinda yafi kaza a kusa da ni" Kokarin tashi ta fara yi daga wajen ya jawota jikinsa da sauri, daga nan kuma labari ya canza, a wannan moment din Maheer wasn't even after his own urge, kawai so yake ta saki jiki sannan memory din moment din ya makale a brain dinta, tuni kam ta sakar masa jiki tsoron da ya cikata da farko ma nemansa tayi ta rasa, sai da Maheer ya tabbatar ya kai ta cloud 9 sannan ya kyaleta ba tare da ya biya nasa bukatar ba, tuni bacci ya dauketa a jikinsa.... Da asuba Mayraah ta kasa hada ido da Maheer, don a dakin suka yi sallah saboda ruwan sama da ake, shi dai kallonta kawai yake, dariya ma take basa, sai wani sinne kai take, ya dawo kusa da ita as if whispering yace "Good morning Wifey" Rufe fuskarta tayi a shoulder dinsa a hankali tace "Ina kwana" yayi mata side hug yace "How was ur night" ta gyada masa kai kawai, they where like that for almost 10mins, Taga ya kai bakinsa kunnenta murya can kasa yace "I love you" Mayraah ta kasa cewa komai har sannan fuskarta na shoulder dinsa, dagota yayi suka koma saman gado ya rufesu da duvet, Mayraah ta shige jikinsa idonta a lumshe, tuni bacci ya dauketa... Karfe goma da rabi na safe Mayraah na kitchen tana wanke utensils da suka yi amfani da shi for breakfast, har ta gama wanke wanken bata