Showing 378001 words to 381000 words out of 452169 words
Chapter 127 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar
san ta gama ba sai ganin sink din tayi wayam, moment dinsu da Maheer jiya da daddare kawai take tunawa ya kasa fita a ranta, juyawa tayi ta jingina da cabinet din kitchen din ta lumshe ido ta bude, gradually tana ji a ranta tana developing soft spot for him as her husband a zuciyarta unlike before da take jinsa as yayanta, walking slowly ta fito daga kitchen din duk jikinta ba kwari kawai daga tuna daren jiya, Maheer dake zaune parlor ya daga kai yana kallonta har ta karaso cikin parlon ta zauna kasan carpet without looking at him, har sannan ta kasa hada ido da shi kamar wani surkinta, wani kunyarsa na musamman take ji, yayi kasa da murya yace "Mimi" Daga kai tayi suka hada ido, da sauri ta rufe fuskarta da kujera tana murmushi, er dariya yayi ya dawo kasa kusa da ita ya zauna ya kai bakinsa kunnenta yayi mata rada, Mayraah ji tayi kamar ta nutse don kunya, da sauri ta rufe fuskarta jikinsa kamar zata yi kuka cike da shagwaba tace "Bana so yaya" daya daga kalmomin da ta dinga masa daren jiya wanda ita kanta bata san ta ya ya ma suka fito bakinta ba ya rada mata a kunne, yana kallonta yana murmushi yace "To na bari Baby gal" Kwantar da kanta tayi jikinsa a hankali tace "Yaya ka kira Ammi mu tambayeta babies...." Maheer da dama tun da gari ya waye twins din suke ransa amma kawai ya daure bai kira Ammi ba saboda yana tare da Mayraah baya son duk abinda zai bata mata rai, ya dauko wayarsa dake kan kujera ya mika mata yace "Kirata da kanki" Mayraah ta amshi wayar har sannan kanta na kwance jikinsa tayi dialing number Ammi, yana fara ring Mayraah tayi kasa da murya tace "Kai zaka fara gaisawa da ita sai ka bani wayar" Dai dai nan Ammi tayi picking call din, wayar na hannun Mayraah Maheer yayi mata sallama, Ammi ta amsa sannan suka gaisa tace "Ya Mimi fa" a hankali yace "Tana lafiya Ammi" Still ya kasa tambayarta yan biyun, Ammi tace "To Madallah, a hospital fa muka kwana jiya Maheer" Maheer yace "Asibiti kuma? Waye ba lafiya" a sanyaye Ammi tace "The twins, naga dare yayi ne shi sa ban kira ka ba, wajen karfe daya Usman ya kai mu hospital, they are all very sick, yanzu haka ma wani test aka rubuta mana za ayi masu, ban dai san wanne bane"
Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788
120
Ammi na zaune office din likitan yara tana sauraron duk bayanin da yake mata akan muhimmanci breakfeeding ga jariri, ita da Mayraah ne zaune office din, Mayraah dake rungume da Aryaan ita ma duk tana sauraron bayanin pediatrician din, likitan yayi concluding bayaninsa da cewa "Amma in har baza su samu breastfeeding din ba saboda wata damuwa ko matsala that is best known to you people, zan iya canza masu wani formula din ku jaraba masu, but i recommend su samu breast milk ko da na yan watanni ne tunda kince uwarsu na da rai" Ammi tace "Toh ba damuwa mun gode Dr, a rubuta mana wani madaran mu jaraba kawai" Likitan yace "Alright" Yana rubuta masu madaran ya mika ma Ammi, ta amsa tayi masa godiya tace "Toh rashes din jikin nasu fa? Da bloat din da cikinsu yayi" Yace "Ba wani abu bane allergy ne from the previous milk da ku ka basu, shi ma wannan da na rubuta kamar yanda nace maki jarabasa za ku yi mu ga ko zai yi suiting dinsu, don shi ma idan bai amshe su ba at the end akwai probability din sake canza masu wani" Ammi ta mike tana rungume da Aymaan tace "Toh shikenan mun gode Dr" Mikewa Mayraah tayi ita ma ta ma likitan sallama sannan suka fita, Usman na reception yana jiransu don ya ki shiga gun likitan ma, yana ganinsu ya mike, Ammi ta mika masa takardan da likitan ya bata tace "Ga madaran da yace za a canza masu" Amsa Usman yayi, suka fita asibitin zuwa inda yayi parking motarsa, har suka bar asibitin Usman bai tambayi Ammi yanda suka yi da likitan ba ita ma bata ce masa komai ba, ya samu babban shopping mall yayi parking yana kallon Ammi ta madubi yace "Bari in siyo madaran in dawo" Ammi tace "Ohk" Bude motar yayi ya sauka, Mayraah dai kallon Ammi kawai take, bayan few seconds a hankali tace "Ammi kilan babies din sun fi gane ma Breast milk" Ammi tace "Ai tunda kika sha madara kika rayu babu abinda ya same ki, to su ma haka za su sha su rayu lafiya lau, da madara na da wani illa da tun a kanki zan san hakan" Mayraah bata sake cewa komai ba har Usman ya fito rike da ledan madaran da ya siyo guda biyu, suna isa gida Ammi ta hada masu madaran ta basu, yanda suka dinga walakanta na farkon suna maido mata wannan ma haka suka dingo maido shi, Ammi ta dirka masu ruwan glucose ta basu magani ta sa Mayraah ta goya daya ita ma ta goya daya... Bayan La'asar Maheer ya dawo daga aiki, Ammi bata ce masa ga abinda likita yace masu a asibiti ba shi ma bai tambayeta ba, daga karshe ya mike ya fita daga parlon, bayan fitarsa da kusan 15 mins Ammi na ta jiran taga Mayraah ta fita zuwa gun sa amma bata ga alamar zata tashi ba, nan kuwa Mayraah duk hankalinta na gunsa amma kunyan Ammi yasa ta kasa tashi ta bi sa, daga karshe Ammi ta amshi Aryaan dake hannunta tace "Ki je ki kai masa abinci in zai ci Mimi" Mayraah bata ce komai ba, bayan few seconds ta mike ta fita daga parlon, downstairs ta sauko ta shiga dakinsa, ya fito daga wanka kenan ta shigo dakin, Sunkuyar da kai tayi ta zauna gefen gado tace "Sannu da dawowa" zaunawa yayi gefenta yace "What did the Dr said?" Mayraah tace "He just layed emphasis on the reasons why they should be breastfed..." Maheer yace "Me Ammi tace akan hakan?" Mayraah tace "Cewa tayi ya rubuta masu wani madaran, har ma an siyo sabon da ya rubuta" Maheer yace "Ohk, shirya mu tafi gida" Ta daga kai ta kallesa, yace "Ko yau din ma rainon babies za ki yi?" Ta marairaice tana kallonsa, yace "Shikenan, ni sai inyi wucewa na gida" Shiru tayi bata ce komai ba, bayan ya gama sa kayansa ta juya ta kallesa tace "In kawo maka abinci?" Yace "Am okay" Makullin motarsa taga ya dauka, ta marairaice tace "Ina zaka?" Yace "Gida, i need to go and rest" A hankali tace "To nan ba gida bane?" Fita yayi daga dakin bai ce mata komai ba ta bi sa da kallo, a hankali ta mike ta bi bayansa, sama ta tafi zuwa bangaren Ammi, ta zauna kan kujera ta kasa ce ma Ammi za su tafi gida, Ammi ta kalleta tace "Kin kai masa abincin?" Mayraah ta girgiza kai tace "Yace ya ci abinci" Ammi tace "Ko gida za ku tafi?" Mayraah ta sauke kanta kasa tace "Haka yace" Ammi tace "Toh ki tashi ki shirya ku tafi" Mayraah bata ce komai ba, bayan wasu yan mintuna ta mike ta fita, dakinta ta tafi ta shirya ta dau handbag dinta sannan ta dawo parlon Ammi, tsaye taga Maheer a parlon ya shigo yi ma Ammi sallama, Ammi tace "Kaga maganin ya sa suna ta bacci, dama kuma jariri ai da bacci aka san sa" Maheer ya ɗan yi murmushi bai ce komai ba, Ammi tace "In sha Allah ma sabon madaran zai amshe su" Maheer ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yayi ma Ammi sallama sannan ya fita, A hankali Mayraah ma tayi ma Ammi sallama, Ammi tace "Ko za ku tafi da abinci?" Mayraah ta girgiza kai tace "Zan dafa Ammi" Ammi tace "Toh shikenan" A haka Mayraah ta fita daga parlon ta sauka downstairs taga Maheer tsaye parlon yana jiran yaga ko zata sakko, turo masa baki tayi ya nufi kofar fita daga parlon.... Bayan isha Mayraah ta gama hada fruits salad a kitchen ta fito parlor da shi, ganin bata ga Maheer a parlon ba ta ajiye bowl din kan center table, wayarsa dake kan kujera take kallo jin yana vibrate, kan ta karasa gun wayar har ya katse, tayi unlocking phone din taga number ne da bai yi saving ba, tana ajiye wayar zata bar wajen taga text ya shigo, ta sake daukar wayar ta bude ta shiga text din, nan taga text sun kusa ashirin from the number, sosai gabanta ya fadi duk da bata kai ga karanta content din text din ba, tayi scrolling zuwa can sama zata fara da message din farko, a hankali ta zauna kan kujera tana fara karanta first message din ta gane Haseenah ce don rokansa take yayi mata rai kar shi da familynsa su rabata da yaranta, su yi hakuri su bar ta ta shayar da su idan yaso daga baya sai su amshe su, yawanci duk ire iren message din da take masa kenan na ban hakuri da magiyan kar ya rabata da yan biyunta she want to breastfeed them, upon yawan messages din Maheer bai taɓa mata reply ba, kuma da alama wani layin ta samu take ta kiransa take masa message da shi, Mayraah ta shiga call log taga bai taɓa daga kiranta ba duk miss calls ne kusan 50, duk da haka sai da Mayraah taji wani kishi a ranta, ta tabe baki ta ajiye wayar, can master bedroom ta tafi ta gansa zaune gefen gado yana duba abu a laptop dinsa, ta jingina kusa da kofa tana kallonsa a hankali tace "Fruit salad din yana can parlor" Ya daga kai ya kalleta, sai kuma ya ajiye laptop din yace "Wani laifin nayi kuma?" Turo baki tayi ta dauke kai taki ce masa komai, yana jin yanda tayi maganar kawai yasan da wani abu, ya mike ya karasa kusa da ita ya kamo hannunta a hankali yace "Tell me what is it" Ta ɗan yi yake tace "Kawai na gama yin fruits salad din yana can parlor na ajiye maka" Yana rike da hannunta ya kai ta edge din gadon dakin ya zaunar da ita ya zauna kusa da ita yana kallonta yace "Then why the change of mood all of a sudden?" Ta dan yatsina fuska tace "Bacci nake ji" Shiru yayi bai ce komai ba, can yace "Toh kwanta kiyi baccin ki" Tace "Zan je dakina in kwanta" Yace "Aa ki kwanta a nan don in tabbatar baccin za kiyi" Tace "Fruits salad din fa?" Yace "Zan je in dauko" a hankali ta daura fararen kafafuwanta kan gadon ta koma tsakiyan gadon ta kwanta ta juya masa baya, riga da wando na mutunci yau ta saka na bacci, ya ɗan yi murmushi sannan ya ci gaba da abinda yake yi a laptop dinsa, after a while ya kashe laptop din ya ajiye sannan ya fita daga dakin, zaunawa yayi a parlon yana shan fruit salad din, wayarsa da yayi vibrate alamar shigowar message ya juya ya kalla ganin number da ya turo message din ya ci gaba da shan fruits dinsa, sai wajen karfe tara Maheer ya koma master bedroom, har a sannan Mayraah bata yi bacci ba, sosai messages din da taga Haseenah ke turo masa ya tsaya mata a rai, tasan kawai as far as this babies are between she and Maheer babu ta yanda za su yi cutting communication na har abada, no matter what she remains the mother of his boys kuma dole akwai lokacin da zai zama wajibi su yi communicating for one reason or the other akan yan biyun, Mayraah na jin shigowarsa ta rufe ido da sauri kamar me bacci duk da tana backing dinsa, bandaki ya shiga yayi wanka ya fito, tana jin ya fita dakin ta mike ta zauna, haka nan taji zuciyarta ya kasa nutsuwa ta sauka daga kan gadon tana tafiya a hankali ta fita daga bangaren gaba daya ta karasa can main parlor ta makale tana lekansa, wayarsa ta gani kare kunnensa, after some seconds taji yace "Look Haseenah, in kika ci gaba da damuna da kira da text messages i will block this line too, ni na raba ki da yaranki da zaki dinga damuna haka?" Shiru Mayraah taji yayi alamar yana sauraron Haseenah, sai kuma taji yace "Kina da number Ammi, kina da number Abba so why disturb me bayan bani nace a amshe yara a hannunki ba, plss bana son ki ja min issues da matana idan taga kina kirana da turo min text messages, kindly avoid calling me pls, ni bani na raba ki da yaranki ba, in kika ci gaba da damuna i will block you i promise" Daga haka ya katse wayar, mikewa yayi Mayraah na ganin haka ta juya da sauri ta koma can masters bedroom ta hau kan gado ta kwanta, a parlorn dake bangaren ya jona wayarsa a caji sannan ya shiga bedroom din, karasawa yayi kan gadon ya zauna kusa da Mayraah ya duka yana kallon fuskarta murya can kasa yace "Nasan ba bacci kike ba" Ko da wasa Mayraah bata yarda ta bude idonta ba, tickling dinta ya fara yi, ta matsa da sauri daga kusa da shi kamar zata yi kuka tace "Yaya bacci fa nake" Ya kwanta bayanta ya jawota kusa da shi yace "To yi hakuri" lamo tayi taki ce masa komai, ya kashe wutan dakin, they were like that for 5 mins yana shaƙan kamshinta, hade rai tayi jin abinda yake mata, tana cire hannunsa a jikinta a hankali tace "Yaya bacci fa nake ji" Yace "To sai da safe" Juya mata baya taji yayi ya matsa daga kusa da ita, ita dai bata ce komai ba ta rufe idonta, bayan kusan minti goma ta juya a hankali ta matsa kusa da shi, murya can kasa tace "To yi hakuri Yaya" ya juyo yana kallonta yace "Really?" Ta gyada masa kai, kwantar da ita yayi jikinsa tayi lamo, daga karshe dai Mayraah tayi mugun da ta sanin komawa kusa da shi har ta basa hakuri, don da tasan wahalan da zata sha kenan da bazata fara ba, duk tunaninta iya abinda ya saba mata this pass days ne zai mata ya kyaleta in ta marairaice masa tace zafi, he made sure ya sauke duk urge dinsa daren nan, ko tunawa da batun wani lubricant bai yi ba, ba irin lallashin da bai mata ba bayan ya dawo hankalinsa amma taki sauraransa sai kuka take sosai, wajen karfe daya saura ya kyaleta ya shiga bandaki zai yi wanka, ko da ya fito bai ganta a dakin ba, yayi murmushi ya saka Pajamas dinsa sannan ya fita daga bangaren, ya tafi dakinta ya murda kofar dakin a hankali yaji ta sa makulli, komawa daki yayi ya kwanta feeling so refresh, nan da nan bacci ya daukesa.... Maheer na tashi sallan Asuba bayan yayi alwala ya fito parlor ya cire wayarsa a caji yaga miss calls din Ammi har hudu, sosai gabansa ya fadi ya dinga kallon wayar sai kuma ya duba time din da ta kira yaga tun karfe hudu ta kirasa, kasa kiranta yayi, jin za a tada sallah yayi karfin halin ajiye wayar ya tafi masallaci...
Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788
121
Maheer na dawowa masallaci ya dau wayarsa ya kira Ammi, har kiran ya katse bata daga ba, ya sake kiranta nan ma no response, ajiye wayar yayi ya fita daga bangaren ya nufi dakin Mayraah, murda kofar dakin nata yayi yaji still bata bude ba, ya juya kawai ya koma dakinsa. Gari na wayewa Maheer ya fito bayan yayi wanka ya shirya, har a sannan Ammi bata biyo kiransa ba shi ma bai sake kiranta ba, tun da ya ga miss calls dinta da asuba ya rasa nutsuwarsa gaba daya, gashi ya kasa sake kiranta, kawai yayi deciding ya shirya ya tafi can gidan, knocking kofar dakin Mayraah yayi don har a sannan bata bude ba, a hankali yace "Mimi..." Bai wani tsaya bata lokaci a bakin kofar ba sanin baza ta bude ba, ya karasa parlor ya dau makullin motarsa ya fita zuwa parking space, Mayraah na jin ya tada motarsa ta mike zaune daga kwancen da take, a hankali ta tashi ta nufi kofa ta bude ta fita zuwa parlor, tsaye tayi tana kallonsa ta windan parlor bayan ta ɗan bude labulen kadan, yana gama warming motarsa mai gadi ya bude masa gate ya fita, komawa tayi ta zauna kan kujera tana kallon agogo dake nuni da karfe bakwai da rabi, ta san karfe takwas da rabi yake fita gun aiki in dai yana da morning shift, she don't know why he is leaving early today, har ranta bata ji dadin da ya fita bai yi breakfast ba, a hankali ta tashi ta koma dakinta. Maheer na isa gida bai ma shiga da motarsa compound din ba yayi parking a waje, sai da ya shiga compound bayan sun gaisa da securities din bakin gate ya ɗan ji hankalinsa ya kwanta, babu kowa parlon gidan ya haura sama zuwa bangaren Ammi, da sallama ya shiga cikin parlon, zaune ya tadda Ammi tana zipping din babban akwati ga Aymaan goye a bayanta, Bilkisu dake goye da Aryaan ita ma tana kokarin rufe wani akwatin, Zaunawa yayi yace "Ina kwana Ammi?" Ammi na ci gaba da abinda take tace "Lafiya lau" Maheer ya amsa gaisuwan da Bilkisu take masa sannan a hankali yace "Ammi wannan akwatunan fa?" Ammi tace "Ka ga tun kan Abbanka da ɗan uwanka su sa ni a bakin duniya ga kayan yaran nan na hada masu tas, a samu warce zata kai su kano gun uwarsu su huta nima in huta, yanda muka ga rana haka muka ga dare, har yanzu kuma sun ki shan sabon madaran, ruwan ma da suke ɗan sha sun ki amsa yanzu, ga zazzabin jikinsu yaki