Showing 381001 words to 384000 words out of 452169 words

Chapter 128 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

sauka, to shine yasa na kira ka tun da asuba in ce maka in za a samu jirgin karfe shidda ka siyi ticket kawai a samu wanda zai kai su kano, Allah Ubangiji ya raya su..." Shiru Maheer yayi, Ammi ta karasa rufe zip ɗin akwatin dake dauke da kayan jariran tace "Toh ga kayansu, in ma ba a samu ticket din ba sai a zuba fetur a mota a tafi a kai su" Maheer ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "To wa zai kai su Ammi?" Ammi tace "Oho, ni dai ba na hada masu kayansu ba, sai kaje bangaren Abban naka ku yi shawaran wanda zai kai su, kar a sa ni a bakin duniya" Maheer bai sake cewa komai ba, Ammi ta kalli Bilkisu tace "Ki shiga daki ki dauko sabon pampers din da aka bude" Bilkisu ta shiga dakin, Maheer dai kallon Ammi kawai yake, Ammi tace "Ai na samu labarin matarsa ta shigo Abujan jiya, sai kaje ka samesa a bangarensa in ita zai ba yaran ta koma kano da su sai ku bata, ko kuma a ba Usman ya kai su tunda shi da Abban naka sun fi kowa damuwan a kai su kano gun uwarsu" Bayan few seconds Maheer ya mike ya nufi kofa ya fita, bangaren Abbansa ya tafi yayi sallama, Abba na zaune parlor yana waya, Maheer ya zauna ya jira har Abba ya gama wayar da yake sannan ya gaishesa, Abba ya amsa yace "Ya gida?" Maheer yace "Alhamdulillah" Abba yace "Wato kai a matsayinka na babba baza ka bude baki ka dinga gaya ma uwarka gaskiya ba ko? You act like duk abinda tayi dai dai ne, sai kayi shiru ka koma gefe kana kallonta, wani irin wawan biyayya ne wannan Maheer, ko attempting na saka ta a hanya kai baka yi, her yes is always ur yes, to in baka sani ba you are doing her harm than good, in the case of this little babies kai likita ne kasan consequences din rabasu da baabarsu amma kayi shiru ka koma gefe acting like it's normal, they are so many ways u can talk to ur mother without being rude, beside kai da ita akwai mutual understanding tsakanin ku, in kayi mata magana zata fi fahimtarka akan ɗan uwanka ko ni, amma you prefer to keep mute a cutar da yaran, to alhaki a kanku kai da ita" Maheer ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Abba ai ta shirya kayansu yanzu za a kai su kanon, ban dai san yanda za ayi arranging tafiyar ba" Abba yace "Arranging wani tafiya? Ita da mai aikinta baza su iya kai su Kanon ba?" Maheer ya sauke kansa yace "She said she is not too fine, shine tace in sameka mu yi magana a samu wanda zai kai su can Kanon" Abba yace "Amina is around, yau kuma zata koma Kano, so she can go with the babies" Maheer yace "To shikenan" Bayan few minutes Maheer ya mike ya fita daga parlon, shi kansa ya samu relieve bayan Ammi ta amince a kai twins din gun uwarsu, Maheer na fita Abba ya kira Hajiya Amina don ya sanar mata tunda karfe goma dama tace masa zata bi Flight ta koma Kano tare da yan biyunta da suka shigo Abujan tare, bayan Abba ya sanar mata zata kai su Aymaan kano tace "To dai yafi kam, don za a shiga hakkinsu da yawa, idan ya so tana yayesu sai a amshesu idan hakan mai yiwuwa ne" Maheer na zaune parlon Ammi bayan ya sanar mata yanda suka yi da Abba, Ammi da ko kallonsa bata yi ba tace "Sai a kai yaran airport ta amshesu a can" Kallonta kawai Maheer yake ya ma rasa abun cewa, Ammi tace "Amma zan fi so ayi tafiyar tare da Mimi" Maheer yace "Sai ta dawo ita kadai?" Ammi tace "Aa sai kaje ka daukota tunda yarinya ce ita" Maheer ya lura Ammi a fusace take, hakan yasa kawai ya mike ya fita daga parlon, flight din karfe goma da rabi yayi booking ma Hajiya Amina da Twins dinta mata sai Mayraah da little babies din, karfe tara saura ya bar gidan zai je ya taho da Mayraah a gida, Mayraah na jin shigowar motarsa gidan ta dai ci gaba da wanke wanken da take, kitchen din ya nufa yana kallonta, taki yarda su hada ido ya karasa kusa da ita yace "Mimi" dauraye hanunta tayi don ta gama, yana murmushi yace "Are you still angry at me?" Wani kallo ta masa, ya danne dariyar da ta basa, yace "You know what?" Ta daga manyan idonta ta kallesa, yace "Finally Ammi ta yarda a kai babies din kano" Kallonsa Mayraah ta dinga yi babu ko kiftawa, lokaci daya jikinta yayi sanyi, returning the twins to kano yana nufin Haseenah is still partially part of the family, communication bazai taɓa seizing tsakaninta da either Maheer or his family ba, then why is he even telling her, har ma taga kamar murna yake, Maheer sai kallonta yake ganin yanda gaba daya yanayinta ya canza, ya kamo hannunta a hankali yace "Ko hakan bai yi ba Mimi?" Mayraah ta kirki murmushi ta girgiza masa kai tace "A'a yayi mana, ya kamata dama ayi considering little babies din, Allah yasa hakan yafi alkhairi, Allah kuma ya raya mana su cikin aminci" a hankali Maheer yace "Ameen wife, and you know what?" Ta girgiza masa kai, yace "Har da ke za aje kai babies din kano" Mayraah tace "Ni a wa kuma?" Shiru Maheer yayi yana kallonta, sam bata ji tana sha'awar aje kai yaran kano da ita ba, ita da ko son ganin uwarsu bata yi har cikin ranta, a takaice tace "I don't think zan iya zuwa, don bana ma wani jin dadi" Maheer ya kwantar da murya yace "Nima ba ni na tsara hakan ba Mimi, instruction din Ammi ne, shine ma yasa na dawo in dauke ki in kai ki can gidan" Mayraah ta sake ji mood dinta ya baci sosai, bata dai ce komai ba yace "Mu je ki shirya Flight din karfe goma da rabi ne" Daga haka ya kama hannunta zuwa dakinta, ta zame hannunta daga nasa a hankali tace "To ina son zan je kaduna daga kano" Maheer yace "Kaduna? Me zaki je kiyi a kaduna?" Daga kai Mayraah tayi ta kallesa, he just realized what he just said, yayi murmushi yace "Ohhh, ok, zaki je gun grannies dinki?" Ta gyada masa kai, tana son ce masa har Mom dinta amma ta kasa ce masa haka, don a duniya kam Ammi ya kamata kawai ta bar ma wannan kalmar, a hankali Maheer yace "Har da gun Momy da Dady ko?" Ta gyada masa kai, yace "Toh shkkn, kwana nawa za ki yi?" Tace "Ko 4 days" Yace "Toh Allah ya kai mu" Ki hada kayanki kar kuyi missing flight din yana fadin haka ya kalli wayarsa dake vibrate a hannunsa, Mayraah ta kallesa yace "Ina jiranki Baby Gal, ki hada kayan" Daga haka ya juya ya fita ta bi sa da kallo with different thought running her mind, bayan few minutes kawai taji zuciyarta ya kasa hakuri ta bi bayansa, bata karasa shiga parlon ba ta tsaya jikin bango jin kamar waya yake a parlon in a low tone, sosai ta kasa kunne don jin me yake cewa, ji tayi yace "Idan ma kin cucesu Allahn da ya halicceki na kallonki kuma ki sani bazai bar ki ba, and lastly kar ki kuma kiran line dina ko ki turo min text since they are taking the twins back to you, duk wani abu na bukatarsu idan ya taso you have Ammi's number, ki kirata ki gaya mata ita zata gaya min zan kuma tura koma menene ta wajenta ta tura maki, that is all i have to say" Mayraah taji hawaye ya cika idonta, ita kawai tasan all this he is saying won't work, dole akwai lkcn da dalili zai kawo su yi waya kamar yanzu da yake waya da ita, bata tsaya ta karasa jin wayar tasa ba ta juya ta koma dakinta hawaye na zuba idonta ta hada kayanta kala biyar a akwati, muryarsa taji a bayanta yace "Har yanzu baki gama ba Mimi" Kin ce masa komai tayi, ya zagayo gabanta yana kallonta ganin danshin hawaye a idonta da mamaki yace "What happened Mimi?" Banza tayi masa, bai sake ce mata komai ba alamar ya sha jinin jikinsa, ta gama rufe akwatinta ta dau mayafinta da handbag without looking at him zata fita dakin ya Jawota jikinsa a hankali yace "Common Mimi, in dai conversation din da nayi a waya kika ji bai kamata kiyi judging dina ba if you listen to the conversation well" Ta fashe da kuka tace "Conversation da za a kebe a gefe ayi ai ya zama na munafurci, why didn't u pick her call in my presence idan baka son inyi judging dinka?" Sosai jikinsa yayi sanyi ganin hawayen dake zuba idonta, ya rungumeta ya lumshe ido cikin sanyin murya yace "Kiyi hakuri wife, i accept nayi kuskure, kuma hakan bazai sake faruwa ba in sha Allah, i promise you yau shine last day da zan sake magana da ita ta waya in sha Allah" Lallashinta ya dinga yi hawaye na zuba idonta tana jin zuciyarta na mata zafi, har cikin ranta bata son komai ya sake hada shi da Haseenah, amma taga kamar hakan ba me yiwuwa bane dole yan biyunsu za su hada su in ma komai bai hadasu ba, a haka Maheer ya lallasheta har ta hakura ta daina kukan bayan sun bar gidan yana driving ya kamo hannunta a hankali yace "Na tura maki kati a wayarki, if there is anything ki kirani" A hankali tace "Nagode" Suna isa gida suka tadda Hajiya Amina da kyawawan twins dinta mata a parlon Ammi, Maheer ya gaisheta ta amsa da fara'a, Mayraah ma ta gaisheta, Maheer ya amsa gaisuwar yan biyun, Hajiya Amina ta kalli Ammi tace "Toh Hajiya tunda sun karaso bari mu tafi kar muyi missing Flight din" Ammi tace "Toh Allah Ubangiji ya tsare, Allah ya kai ku lafiya" Dubu ashirin da turamen atamfa biyu Ammi ta ba Ihsaan da Eeman, Hajiya Amina tayi mata godiya sosai, har downstairs Ammi ta rakosu, Hajiya Amina na rungume da Aymaan, Aryaan kuma na hannun Eeman, tuni dama Bilkisu ta kai akwatunan kayan jariran Booth din motar Usman don shi zai kai su Airport din, Maheer ya fiddo box din Mayraah dake booth dinsa ya sa a na Usman, Mayraah ta shiga front seat ta zauna, Hajiya Amina da yan biyunta suka zauna a baya, Abba dai na bangarensa bai fito ba, Ammi ta kalli Bilkisu tace "Ina pampers da nace ki dauko dazu?" Da sauri Bilkisu ta juya ta koma cikin gidan don dauko pack din Pampers din, Maheer sai kallon Mayraah yake ganin she is moody, kana ganinta kasan tana da damuwa, ya ciro wayarsa ya tura mata text kamar haka "Will miss you soo much my one and only wife, Yesternight was sweet...." Mayraah ta kalli wayarta jin message ya shigo tana karanta abinda ya turo mata ta juya ta kallesa, kashe mata ido yayi, bata san sanda tayi murmushi ba ta dauke kanta kawai ta kife wayar a cinyarta, sosai yaji dadin ganin murmushinta me kyau, Bilkisu na kawo pampers din, Usman na kallon Eeman ta madubi yace "My phone?" Ta ɗan buda manyan idanuwanta tace "I left it upstairs together with mine...." Shi dai Usman kallonta kawai yake ta madubi, Mika ma Ihsaan Aryaan tayi sannan ta sauka a motar ta koma cikin gidan da sauri, Hajiya Amina tace "Da baka tuna ba sai mun je Airport ka tambayeta tayi ta zare maka idanuwa tana maka turanci..." Murmushi kawai Usman yayi, ita dai Ammi na tsaye gefe tana kallon different direction, ba a dau lokaci ba sai ga Eeman da wayarta da na Usman ta bude back seat ta shiga, hararanta yake ta madubi, ita dai tayi murmushi ta amshi Aryaan a hannun twin sis dinta, sai da suka bar compound din sannan Ammi ta juya ita da Bilkisu suka koma ciki, Maheer dama daga nan yayi ma Ammi sallama yace zai tafi Hospital. Karfe sha daya da rabi su Hajiya Amina suka sauka Kano, Driver din gidanta dama na airport yana jiransu, ya daukesu gaba daya sai gidansu Haseenah, tunda suka baro Abuja ko tari yaran basu yi ba har suka iso kano, Sosai Mahaifiyar Haseenah da kawarta suka yi welcoming dinsu bayan sun iso gidan da twins din, Mayraah dai na zaune parlon babu yabo babu fallasa, ko hada ido da Haseenah taki yarda tayi sai danna wayarta kawai take, Haseenah kuwa sai satan kallonta take ta kasa daina satan kallonta, Hajiya Amina na kallon mahaifiyar Haseenah daga karshe tace "In dai wani abu ya taso na bukatar yaran za a iya kiran mahaifiyar Maheer din, ko kuma ni a kirani tunda mun ma fi kusa, zan baki lambata yanzu duk me zai taso kawai ayi min waya in sha Allahu i will deliver tunda ina kanon" Mom din Haseenah tace "Toh in sha Allahu Hajiya, Allah Ubangiji ya saka da alkhairi, Allah ya bar zumunci, mun gode kwarai da gaske" Hajiya Amina tace "Ameen, ragon suna kuma in sha Allahu zuwa anjima za a aiko kamar yanda Abbansu yace, nasan dai an sanar daku sunan yaran" Mom din Haseenah tace "Kwarai kam, ance an samu Alhaji Mamudan da Usman, Allah dai ya masu albarka, Allah ya raya mana su cikin aminci" Hajiya Amina tace "Ameen Ya Allah" Basu wani dade ba a gidan kasancewar driver na waje yana jiran su, Hajiya Amina ta yi ma su Mom din Haseenah da ita kanta Haseenar Sallama sannan suka bar gidan tare da yan biyunta da Mayraah, Hajiya Amina na kallon Mayraah tace "Gobe da safe sai driver ya kai ki har kadunan Mayraah" Murmushi kawai Mayraah tayi, Eeman tace "Momy pls nima zan je kadunan wajen Aunty Khadijah sai in mata kwana daya, dama Ya Usman yace min zai je kaduna gobe daga nan zai zo kano sai kawai mu dawo da shi"

Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

122
Mayraah ta dau handbag dinta tana kallon Ihsaan tace "Ke me yasa baza ki bi mu kadunan ba?" Ihsaan dake danna wayarta ta ɗan yi murmushi tace "Kawai haka nan Aunty" Eeman ta ajiye turaren da take fesawa gaban mirror tace "Tana da phobia din shiga mutane" Hajiya Amina ta bude kofar dakin tana kallonsu tace "Baku gama bane har yanzu ga driver can na ta jira?" Mayraah ta nufi kofar tace "Mun gama" Eeman ta dau handbag dinta tana kallon twin sis dinta tace "Baza ki raka mu downstairs ba" Ihsaan ta ajiye wayarta ta sauka daga kan gadon suka fita daga dakin gaba daya.... Sai kusan la'asar Mayraah suka iso garin Kaduna, Mayraah ta kalli Eeman da ta kwantar da kanta jikin kujeran motar tana bacci ga wayarta dake gefenta yana vibrate, Mayraah ta dinga kallon number da tayi saving da Bro Usman, can ta taɓa ta a hankali tace "Eeman" Bude ido tayi, Mayraah ta dau wayar ta mika mata tace "Ana kiranki" Eeman ta amshi wayar tana kallon screen din sai kuma ta koma ta kwanta sannan tayi picking call din, Mayraah dai ta dauke kanta, har ta gama wayar ta ajiye Mayraah bata ji me suke cewa ba, Drivern ya fara dropping Eeman a gidan aunt dinta, Eeman ta sauka motar bayan driver ya dauko mata karamin box dinta a booth din motar, tana murmushi ta daga ma Mayraah hannu tace "Sai anjima Aunty Mimi" Mayraah ma murmushin tayi mata ta daga mata hannu, a haka driver ya ja motar suka bar unguwan. Sosai Hajiya Ramatu da su Aunty Halima suka yi farin ciki da ganin Mayraah, bayan Aunty Halima ta fita Hajiya Ramatu na kallon Mayraah tace "Sallama kika zo yi ma su Maryam hala? Ai sun tafi tun da safe, basu ce maki flight din na safe bane?" Mayraah ta daga kai tana kallonta, can tace "Aa ni daga kano nake" Hajiya Ramatu tace "Ayyo, ai na zata kin san da tafiyar tasu ne kika zo kuyi sallama da su, dazu da safe jirginsu ya tashi zuwa US" A hankali Mayraah tace "Ban sani ba" har cikin ranta taji babu dadi don saboda taga Mahaifiyarta yasa tace zata zo kaduna, Hajiya Ramatu tace "Toh kece baki son kiran mutane Mayraah" Mayraah ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, Hajiya Ramatu tace "Ina jin yau kwana uku kenan da na kira Amminki nayi mata albarka, Hajiya Ladi tace mana an samu karuwan yan biyu" Bude kofar aka yi Aunty Halima ta shigo tana kallon Hajiya Ramatu tace "Umma bakuwarki zata tafi wai" Hajiya Ramatu tace "Toh gani nan zuwa" Aunty Halima ta juya ta fita, Hajiya Ramatu na kallon Mayraah tace "Ki kai akwatin naki daki" Mayraah ta daga kai tana kallonta tace "Umma yaushe za su dawo?" Hajiya Ramatu tayi murmushi tace "Ai can Baban naki ke aiki Mayraah, sai mu yi wata hudu ma bai zo mana nan ba, kuma kinga tun bayan bikinki tafiya yake yana dawowa, sai yanzu ne zai koma da Maryam din can gaba daya" Sosai jikin Mayraah yayi sanyi ta kasa cewa komai, Hajiya Ramatu tace "Kin yi sallah kuwa?" Mayraah ta girgiza mata kai tace "Ban yi ba" Hajiya Ramatu tace "Toh ki shiga ciki kiyi, za a kawo maki abinci yanzu" Mikewa Mayraah tayi ta dau akwatinta ta shiga dakin kakarta da shi, Mayraah na idar da sallah ta dau handbag dinta jin wayarta na vibrate, tana ciro wayar taga miss calls din Maheer biyu, kiransa ta shiga yi, yana fara ring ya katse ya kirata, ta daga ta kai kunne yace "Baby Gal" A hankali tace "Ina yini yaya" Yace "Waye yaya? ai na bar ma Usman wannan sunan tun tuni" Ita dai bata ce komai ba sai ɗan murmushi da tayi, yace "Ya hanya Dear?" Tace "Alhmdlh"

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login