Showing 384001 words to 387000 words out of 452169 words
Chapter 129 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar
Yace "Ya su grandma da mutanen gidan?" Tace "Duk suna lafiya" Yayi kasa da murya yace "I miss you so much Mimi" Ta kwantar da kanta jikin gado a hankali tace "Uhm" Yace "Uhm ko?" Murmushi tayi, Yace "Saboda kinsan baza kiyi missing dina ba shi yasa kika tafi kiyi kwana uku ko" Tace "To in dawo gobe ne" Yace "I will gladly come and pick you" tace "Kaga fa zan je har gidan Aunty Mariya, sannan inje in gaida Hajja gidan Baaba Yahanasu" Maheer yace "Duk za ki iya yi a goben sai mu biyo train na yamma" Mayraah tace "Aa ka dai bari jibi pls" Yace "Alright dear, yau din zaki je wajen su Momy?" Ta girgiza masa kai a hankali tace "Basa kasar" Maheer yace "Yaushe rabon kiyi communicating da su?" Mayraah tayi shiru, Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace "Ya kamata ku dinga communicating a kai a kai don ku saba sosai Mimi" Ita dai bata ce komai ba, yace "Kin ci abinci?" Tace "Yanxu zan ci" Yace "Alright, i will call u back later, nima zan shiga theatre ne yanzu" Sallama suka yi ta ajiye wayar, she is soo sad bata hadu da Mom dinta ba, Shigowar Hajiya Ramatu dakin ya dawo da ita daga tunanin da ta tafi, Hajiya Ramatu ta ajiye mata abincin da ta kawo mata.... Da daddare bayan isha Mayraah na zaune parlon grandma dinta dake sanar mata an sa bikin Farrah er gidan Aunty Halima nan da wata biyu, Mayraah tace "Toh Allah ya kai mu lafiya" Hajiya Ramatu tace "Ameen, akwai wani kawun ki ma da baki sani ba shi ma zai yi auren, duk rana daya aka sa da na Farrahn" Mayraah tace "Allah ya sanya alkhairi" Hajiya Ramatu tace "Ameen" Mayraah na kallonta tace "Umma, Yaya Aliyu yana nan?" Hajiya Ramatu tace "Aliyu yana Canada, kilan mu ga ya zo bikin" Mayraah ta dau wayar ta dake ringing ganin Maheer ne tayi silencing ta ajiye, Hajiya Ramatu tace "Ba mijinki ke kira ba, tafi daki kiyi wayarki mana" Mikewa Mayraah tayi ta wuce dakin tayi picking call din, bayan sun gaisa a hankali tace "Yaya na mance ban taho da Charger na ba, na bar shi a kano" Yace "How manage? ke da baki da mantuwa, yanzu wayar ba caji kenan?" Tace "Aa nayi using na Aunt dina, but i don't want to be inconveniencing her" Maheer yace "Ohk, Usman zai shigo kadunan gobe zan gaya masa ya siya ya kai maki" Mayraah tace "Toh Allah ya kai mu" Yace "Ameen Baby gal" Tace "Have u eaten?" yace "Wa zai girka min bayan baki nan?" Mayraah tace "Me yasa baka je gida wajen Ammi ka ci ba?" Yace "Let video call" A hankali tace "Ohk" Washegari wajen karfe daya na rana Mayraah ta fito compound ta dalilin kiranta da Usman yayi, ta ɗan buda ido ganin Eeman a motarsa, amsa gaisuwarta tayi tana murmushi, Usman ya dau charger da ya siyo mata ya bata ta amsa tace "Nagode, yaya amma dai ba kanon za ku tafi yanzu da ranan nan ba?" Yace "Kina da sakon da za a kai maki can ne?" Tayi murmushi tace "Aa, am just asking" yace "ke yaushe zaki koma Abuja?" Tace "Tomorrow in sha Allah, yau zan je gidan Aunty Mariya daga can inje wajen Hajja" Usman yace "Ohk" A hankali tace "Yaya ko zaka yi dropping dina gidan Aunty Mariyan kafin ku tafi" Yace "Aa, Driver yayi dropping dinki mu da za mu tafi kano" Tace "Toh shikenan, Allah ya tsare hanya" Sallama tayi ma Eeman sannan ta juya ta koma ciki, tana shiga gidan Usman ya kirata a waya, tana dagawa yace "Did you inform ur husband that u will be going out?" Ta ɗan turo baki tace "Ya sani ae" Yace "Toh fito mu tafi" Sosai Mayraah tayi mamaki, shi da ta riga tasan No dinsa is always No, tasan definitely Eeman ce zata masa magana shine ya canza mind zai kai ta, murmushi kawai tayi, ta tafi bangaren grandma dinta ta sanar mata zata je gidan kanwar Ammi, mayafinta kawai ta yafa ta dau jakarta ta fita, back seat ta bude ta shiga, Usman ya ja motar suka bar layin... Mayraah na shiga compound din gidan Aunty Mariya ta gaida duk mutanen da ta hadu dasu a tsakar gidan, Eeman na biye da ita har suka karasa part din Aunty Mariya, bata yi tunanin Usman zai ce su shiga gidan da Eeman ba, don duk zaton ta suna ajiyeta za su wuce, amma sai yace mata idan yayi sallah zai shigo shi ma, Mama Ladi dake zaune parlon ta tsuke fuska tana fiffita da maficin hannunta duk da fan din dake aiki a sama ta dinga kallon Mayraah bayan sun shigo parlon, can tace "Ikon Allah, ke kuma daga ina haka?" Mayraah na murmushi ta zauna kan carpet tace "Ina yini Mama" Eemaan ta zauna gefen Mayraah ita ma ta gaida Mama Ladi, Mama Ladi na kallon Eeman tace "Wacece wannan kuma, amma ba daga gidan Saminu take ba don duk nasan yan matan gidan" Dai dai nan Aunty Mariya ta fito daga daki, da fara'a tayi welcoming din su Mayraah, tace "Dazu kuwa muka yi waya da Maheer yake ce min kina nan kaduna ai, ya kika baro su Ammi da Bilkisu?" Mayraah tace "Lafiya qlau" Aunty Mariya ta amsa gaisuwar Eeman tana murmushi tace "Sannu yan mata" Duk tunanin Aunty Mariya daga can gidan Alhaji Saminu Mayraah ta taho da Eeman, bude kofar parlon aka yi wata budurwa ta shigo da cooler din shinkafa da miya ta ajiye a parlon, Mama Ladi dai ta kyabe baki ta kauda kai, Aunty Mariya na kallon budurwar tace "An gama rabon abincin ne Hussaina?" Yarinyar tace "Ehh an gama" Aunty Mariya na kallon Mayraah tace "Ku je can ku ci abinci Mimi" Mayraah na murmushi tace "Aa Aunty ni dai na koshi sai dai ko Eeman" Eeman ta girgiza kai da sauri tace "Nima na ci abinci" Aunty Mariya tace "Toh ku je ku dau drink a fridge, kina yin abu sai kace gidan bakon ki ne Mayraah" Mayraah ta ɗan yi murmushi ta mike Eeman na ganin haka ita ma ta mike ta bi bayan Mayraah, suna fita Mama Ladi tace "Wannan dai tsari na gidan ku tirr da shi Mariya, ace sai yunwa ya ci ya cinye mutum, duk mutum sai ya galabaita sannan a basa abinci a er tsohuwar cooler? Su fa yan kauye in suka yi kudi sama taka za'a ga fi'ili da sanabe iri iri malam, banda haka ta yaya wannan babban gida haka da mutane kaca kaca a cikinsa kamar yan gudun hijira ace lallai sai a tukunya daya za ayi duk girkin gidan, lemon nan dan banza ma sai anje can za a bude katon firiji a dauka, gaskiya kina kokari Mariya, wannan ai rayuwar wahala ce kawai, ga uwar miji da kishiyoyinta uku, ga facalolinki biyar, ga gandara gandaran samari da yan mata a gida sun kusa 30, ga jikoki yarkacee sun kusa arba'in, inaaa.... sam bazan iya ba wallahi, yanzu gashi kinyi baki ace ko lemon da zaki basu a nan babu sai sunje can cikin gida an bude katuwar firiji sun dauka" Aunty Mariya dai danna wayarta kawai take, sai ga Mayraah ta shigo parlon, Mama Ladi tace "Kin samo lemun ko sun wawashe?" Mayraah tace "Aa cokali aka ce in amso sai mun ci abinci a can" Mama Ladi ta kyalkyale da dariya har da kyakyatawa tace "A katon faranti suka zuba abincin ko?" Tuni Mayraah ta tafi ta dauko cokali biyu a kitchen din Aunty Mariya ta fito, Mama Ladi tace "To har ita sadaka yallar da kuka je amso lemon tare suka tilasta ta zauna taci abincin a cikinsu?" Sai kuma ta kara kwashewa da dariya har da kwanciya, Mayraah zata fita Aunty Mariya tace "Daga can gidan ki ka taho tare da ita Mimi?" Da sauri Mama Ladi ta dago tace "Sam, wnn dai ba daga gidan Saminu take ba, abinda duk nasan yaran gidan" Mayraah na kallon Aunty Mariya tace "Aa, kano za su tafi da Ya Usman" Aunty Mariya tace "Wacece ita?" Mayraah tace "Yarinyar Aunty ce" Aunty Mariya tace "Wacece Aunty kuma?" Mayraah tace "Aunty Amina" Mama Ladi ta gwalo ido tace "Ko dai amaryar Mamuda?" Mayraah dai bata ce komai ba, Mama Ladi tace "Habaa, ni dai ina ta kallon yarinyar naga sak kamar Amina tayi kaki, har dirin irin na uwar ne, a ina ku ka samo ta ke da Usuman din??" Mayraah tace "Kano za su koma ne tare" Mama Ladi tace "Toh me ya hadasa da ita har za su koma kano tare? Kun ji neman bala'i ko" Bude kofar parlon aka yi Usman ya shigo, Mayraah ta juya ta fita daga parlon, Usman ya zauna kan kujera ya gaishesu gaba daya, Aunty Mariya ta amsa tace "Ashe kana Kadunan Ussy" Yace "Dazu da safe na shigo" Mama Ladi tace "Yanzu Mera ke bamu labari wai zaka koma kano da er wajen Hajiya Amina" Usman bai tanka ta ba ya ciro wayarsa, Aunty Mariya tace "A zuba maka abinci Usman?" Usman yace "Na ci abinci" Mama Ladi tace "Ai ko yarinyar kyakyawa da ita ga fara'a" Shi dai Usman idonsa na kan wayarsa, Text din Aunty Mariya ne ya shigo wayar tasa ya daga kai ya kalleta, sai kuma ya bude text din, bayan ya karanta content din, after some minutes ya mike ya tafi dakin baƙi, Mama Ladi ta bi sa da kallo, Aunty Mariya ta tafi kitchen ta dauko mata plate da spoon ta kawo ta ajiye mata, Mama Ladi tace "Ko er lemon ma yau basu hado min da shi ba kilan bai isa bane" Aunty Mariya ta nufi dakin da Usman ya shiga, tana shiga dakin ta kulle kofa tana kallon Usman tace "Kai kuma Usman a ina ka dauko yarinyar nan za ku tafi kano?" Usman yace "Tare suka zo da Mimi from kano yesterday" Aunty Mariya tace "Toh tun wuri ka san yanda zaka canza zancen nan a kunnen Mama Ladi kar ta kai ka gaba" Usman yace "Kamar ya kenan?" Aunty Mariya tace "Tsaf zata iya kiran Ammi tace mata gashi gashi ko baka san halinta bane" Usman yace "To ai ba komai ko ta kira Ammin" Aunty Mariya tace "Ko dai baka da kai ne??" Usman yace "No, but like seriously is there anything wrong don mun tafi kano tare da ita Aunty?" Bude kofar dakin aka yi duk suka juya, Mama Ladi na tsaye bakin kofar tace "Wannan ai walakanci ne a kawo min abinci babu ruwa kamar wata doki, saura kadan in kware, kin wani shigo daki da shi kuna zantawa ga Ladi bare na zaune a parlor" Mikewa Usman yayi ya fita daga dakin ya koma parlor, Mama Ladi ta bi bayansa, zaunawa tayi gaban abincin nata tana kallon Usman tace "In ba lalura ba me zai kawo ni gidanta da har zata dinga walakanta ni haka Usuman, ai kamata yayi ni ta dinga min nawa girkin daban a kitchen dinta tunda ba zaman dindindin na zo yi gidan ba, kaga fa ranan kawai wani ikon Allah naje gaida Ramatu kakar Mera sai muka hadu da Alhaji Saminu muka gaisa a mutunce shine yake tambayata ko in da passpo don yaga ya dace ya biya min Umrah, to ina na ga passpo, ai ko nace masa akwai 'ya ta a garin nan zan je ta rakani mu je inyi, shine ya hadani da uban kudade na taho Mariya ta rakani muje ayi min, kaji dalilin zuwana gidanta har na kwana biyu" Usman ya ɗan yi murmushi yace "Toh Allah ya sanya alkhairi" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Amma fa na kwabeta nace kar ta gaya ma Ammi, kai ma ka ja bakinka kayi shiru sai komai ya kankama" Usman yace "Toh shikenan" Mama Ladi tace "To ita er wajen Hajiya Aminar da za ku kano tare ya sunanta?" Usman yace "Sunan Ammi gareta" Mama Ladi ta toshe bakinta da hannunta, can tace "Wallahi yarinyar kyakkyawa ce ga nutsuwa, ko kan kujera taki zama tsabar kunya, gata er yarinya karama, zata yi shekara nawa yanzu?" Usman yace "Ina jin 18" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Wallahi da ma kawai ka nemeta, don ni shaida ce uwarta mutuniyar kirki ce wayayyiya, ga haɓa haɓa da mutane, tasan kan zaman duniya matar" Usman dai murmushi kawai yayi yana danna wayarsa, Mama Ladi tace "Allah kuwa, ko ni da kaina sai in ma Mamuda magana, matsalar dai uwarka, tunda kasan wani lokacin ba nutsuwa gareta ba, ta dau azababben kishi ta kuntsa a ranta ya hanata sukuni" Shigowar Aunty Mariya parlon yasa Mama Ladi tayi shiru ta ci gaba da cin abincinta, Mayraah ce ta fara shigowa parlon Eeman na biye da ita, Mama Ladi na washe baki tana kallon Eeman tace "Kun ci abincin Yan mata?" Eeman ta gyada mata kai tace "Mun ci" Mama Ladi tace "Ko zaki kara da nawa?" Eeman na murmushi ta girgiza kai tace "Aa na koshi Mama" Mikewa Usman yayi ya bi Aunty Mariya kitchen yayi mata sallama ya fito, sannan yana kallon Mama Ladi yace "Za mu tafi Mama" Mama Ladi tace "Kanon za ku tafi yanzu?" Yace "Ehh" Mama Ladi ta jawo jakarta ta bude, yan dari biyar biyar sababbi ƙal sai kamshi suke ta ciro har guda goma ta mika ma Eeman tana murmushi tace "Amma ya sunanki" Eeman ta sunkuyar da kanta tace "Eeman" Mama Ladi tace "Toh gashi Eeman ki saka kati ba yawa kin ji" Eeman bata amshi kudin ba, Usman ya amsa ya mika mata, bayan few seconds ta amsa tayi ma Mama Ladi godiya, Mama Ladi ta kwalo ma Aunty Mariya kira tace "Ki fito Eeman za su tafi kano" Aunty Mariya ta fito tace "Har za ku tafi Usman" Daki ta tafi ta dauko sabon turare a kwali ta saka a leda sannan ta hada da 2k, ta ba Eeman, wnn din ma Usman ne ya amsar mata, Mayraah ta dau handbag dinta tace "Aunty za su ajiye ni a gida ne su wuce" Aunty Mariya tace "Ke da na zata zaki kai yamma, ki bari kawai da yamma mai napep dina ya maida ke gidan" Mayraah tace "To" Har mota ta rakasu sannan ta dawo cikin gidan, Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Don Allah Mera basu dace ba? Ni dai wallahi ta kwanta min a rai, da zai ji shawarata kawai ya neme ta ya aureta" Ita dai Mayraah Murmushi kawai take, Mama Ladi tace "Allah kuwa" Mayraah na kallonta tace "Mama Hajja tana nan Kaduna ne?" Mama Ladi tace "Wacce Hajja, Hajja ai tana Adamawa" Mayraah tace "Aunty Badiyyah fa?" Mama Ladi tace "Badiyyah tana can wajen dangin ubanta a Bichi, nima jiya Mariya ke gaya min wai za a kai kudin aurenta ranan juma'a, ta samu wani dattijo a wani kauye kafin a karasa Bichi, matansa biyu zai rufa mata asiri ya aureta, taɓon cikin shege dai bazai taɓa goguwa a rayuwarta ba har duniya ta nade" Mayraah dai tayi shiru, duk jikinta a sanyaye tana kallon Mama Ladi. Mayraah na dakin Aunty Mariya dake kallonta tace "Kinyi amfani da kayan nan da na tura maki kuwa Mimi?" Mayraah ta sunkuyar da kanta tace "Aa" Aunty Mariya tace "Toh saboda me?" Shiru Mayraah tayi, Aunty Mariya tace "Yanzu yaushe za ki koma Abuja?" Mayraah tace "Gobe in sha Allah" Aunty Mariya tace "To goben da safe ki dawo nan, ki gaya ma Grandma din taki ko driver sai ya kawo ki" Mayraah tace "Toh" Da yamma me napep din Aunty Mariya ya maida Mayraah can gidan Grandparent dinta. Mayraah na zaune part din Aunty Halima tana danna wayarta bayan Isha, Aunty Halima ta shigo parlon tana kallon cup din gabanta tace "Baki shanye ba Mayraah? Shi kenan fa" Mayraah ta ajiye wayar hannunta ta dau cup din, da kyar ta tilasta kanta ta shanye content din cikin cup din, magungunan gyara masu inganci Aunty Halima ta siya ma Mayraah kafin ta dawo daga gidan Aunty Mariya, shine ta kirata parlonta duk ta bata su ta sha.... Washegari da sassafe warce zata yi ma Mayraah kitso ta zo gidan, Mayraah ba ta kitso saboda tsayin gashinta amma ta kasa gaya ma Grandma dinta, haka nan ta hakura aka fara mata kitson, kafin karfe goma aka gama zanzara mata kitso da yayi mugun mata kyau, sai kallon kitson take ta madubi, ita kanta tayi mamakin yanda kitson yayi mata kyau sosai, still haka nan ta sake zama don me lalle na jiranta, sai kusan azahar aka gama lallin, sosai lallin ya haskata ta dawo kamar wata sabuwar amarya, wanka tayi ta dauro alwala, bayan tayi sallah ta ci abinci sannan ta shirya don driver zai kai ta gidan Aunty Mariya....
Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788
123
Har karfe biyar na yamma Mayraah na gidan Aunty Mariya don ko da ta kira Maheer bata samesa a waya ba ta cire ran tafiya ranan, tana zaune parlon surkar Aunty Mariya bayan ta kai mata pack din sabulu da Omo da Aunty Mariya tace ta kai mata inji Ammi, sosai surkarta da suke ce ma Hajiya Mama tayi farin ciki da sabulun da Omon da Mayraah ta kawo mata, Hajiya Mama na kallonta tace "Yanzu yashe za ki koma Abujan?" Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Gobe in sha Allah" Hajiya Mama tace "Amma nan zaki kwana de ko" Mayraah ta girgiza kai tace "Aa anjima zan tafi" Hajiya Mama tace "Toh Allah ya kai mu" Tashi Hajiya Mama tayi ta tafi daki sai ga ta ta fito da turmin atamfa a leda ta ba Mayraah, Mayraah ta kasa amsan atamfar, sai da Hajiya Mama tayi da gaske da ita tace "Ke fa na ba ki dinka, dama Allah bai bani ikon zuwa bikinki ba, amma wasu daga matan gidan duk sun je, ke dai ki zauna lafiya da mijinki kiyi masa biyayya, kuma ayi ta hakuri"