Showing 387001 words to 390000 words out of 452169 words

Chapter 130 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

Godiya Mayraah tayi mata kanta a kasa bayan ta amshi atamfar, daga karshe ta mike ta mata sallama ta bar parlon, tana isa part din Aunty Mariya ta cire takalminta tana kallon takalmin dake bakin kofar parlon sannan ta shiga ciki ta kulle kofar, ɗaga kai yayi ya kalleta, ta dinga kallonsa babu ko kiftawa, kawai gani tayi ya mike ya nufota ya rungumeta jikinsa, ta lumshe ido tana shakar kamshin turarensa da ya cikata, ya zame mayafin kanta yana kallon kitsonta, underneath his breathe yace "Waow it's so beautiful" Ta daga kai ta ɗan kallesa tana murmushi, a hankali yace "I missed you so much Baby" Kawai ji tayi ya fara kissing lips dinta, Dai dai nan Aunty Mariya ta fito parlorn, saketa yayi da sauri, Mayraah da duk ta daburce ta bar wajen, Aunty Mariya tayi kamar bata gansu ba, ta kullo kofar dakin baƙi dake a bude, sannan ta karasa cikin parlon tana kallon Maheer da mamaki tace "Aa, dama kana anguwan ka kirani?" Bai yarda sun hada ido ba ya zauna kan kujera yace "Ina wuni Aunty" Tace "Lallai Maheer ce min fa kayi ka kusa baka shigo kadunan ba" Murmushi yayi kansa a kasa, tace "To ya hanya?" Yace "Alhamdulillah" Tace "Ya ka baro su Ammi" Yace "Duk lafiya lau" Ta kalli Mayraah da ta kasa dago kai kamar munafuka, tace "Mimi duba fridge a kitchen akwai table water ki dauko masa" Mayraah ta ajiye ledan hannunta ba tare da ta yarda sun hada ido da Aunty Mariya ba ta wuce kitchen, Shi ma dai har a lkcn ya kasa kallon idon Aunty Mariya, definitely yasan ta gansu, Mayraah ta fito rike da ruwan gora a tray da cup ta ajiye masa, sannan ta tafi ta dau ledan atamfar da Hajiya Mama ta bata tace "Aunty, Mama ta ban wannan" Aunty Mariya ta buda baki tana kallon atamfar dake cikin ledan tace "Ni fa ba don ta baki komai na bada sabulu da Omo ki kai mata ba, gani nayi Mama Ladi ta zo bata yi dubaran kawo mata komai ba, kema kin zo kuma nace daga Abuja kike shi sa na baki nace kawai ki kai mata in ji Ammi" Mayraah dai bata ce komai ba, Aunty Mariya tace "Toh ai shikenan, Allah ya saka da alkhairi, mun gode kwarai" Kallon Mayraah kawai Maheer yake as if ranan ya fara ganinta, sosai yaga kitson da aka mata yayi ya mata kyau da lallin hannunta da kafarta, Aunty Mariya ta dawo da shi daga shagalan da yayi yana kallon Mayraah, tace "Amma sai gobe za ku koma Abujan ko?" Yace "Aunty kawai zan bar motar gidan Usman sai mu bi train" Aunty Mariya tace "Toh ai naga lokaci na wucewa, gashi har after 5" Yace "Eh yanzu za mu tafi in sha Allah" Aunty Mariya ta kalli Mayraah tace "Mu je in baki sakon Ammi Mimi" Mikewa Mayraah tayi ta bi baya Aunty Mariya zuwa Bedroom dinta Maheer ya bi ta da kallo, Aunty Mariya na kallonta bayan sun shiga dakin tace "Ai dai kinga duk yanda kika yi amfani da abubuwan da na baki ko?" Mayraah dai ta gyada mata kai avoiding eye contact with her, Aunty Mariya tace "To wanda ke can gidanki ma duk haka zaki yi using dinsu bayan 2 weeks kin ji?" A hankali Mayraah tace "Toh" Aunty Mariya tace "Kar fa ki ki amfani da su Mimi" Mayraah bata dago kanta ba tace "Zan yi Aunty" Aunty Mariya ta bata Humra da ta saka mata a leda, Mayraah ta risina ta amsa tace "Nagode Aunty" Tare suka fito parlon, tana kallon Maheer tace "To in dai kun isa Abujan za mu yi magana Maheer" Maheer yace "Toh Aunty" Aunty Mariya tace "Yanzu fa sai kun je Malali kun dau box din kayanta sannan tayi masu sallama kafin kuje train station din" Maheer yace "Eh can za mu je" Aunty Mariya tace "Toh Allah ya tsare hanya, a gaida min da Ammi" Har bakin gate ta rakasu, sai bayan da taga tafiyarsu ta juya ta koma cikin gida.... Maheer sai da ya shiga har cikin gidan Alhaji Saminu don gaida Grandma din Mayraah bayan sun isa gidan, da fara'a Hajiya Ramatu ta tarbesa tana tambayarsa su Ammi, har yan biyu sai da ta tambayesa yace "Suna lafiya Umma" Mayraah ta bar su nan parlon ta tafi sama zuwa daki ta ajiye mayafin jikinta gefen gado tana tunanin ko period dinta ne ya zo don last period dinta ko kadan bata yi cramps ba kawai ganinsa tayi, fitowa tayi daga bathroom din ganin she is not seeing her period, jin ana knocking ta karasa ta bude kofar dakin, Daya daga masu aikin gidan ce tace mata Aunty Halima na kiranta a dakinta, Mayraah na isa dakin Aunty Halima ta dauko mata sauran magungun da suka rage ta bata tana kallonta tace "Kar dai kije ki ajiyesu kina kallo a gida Mayraah" Mayraah ta ɗan yi murmushi kanta a kasa tace "Zan sha Aunty" Aunty Halima tace "Yauwa to, ki gaida su Amminki da kyau, Allah ya tsare" Mai aiki ce ta kai box din kayan Mayraah zuwa motar Maheer, bayan sun bar layin Maheer yayi wrapping hannun Mayraah a nasa a hankali yace "I miss you soo much Baby gal" Mayraah ta kasa ce masa komai tana jin wani iri with just him holding her hands, yace "There is no train going to Abuja this evening fa" Mayraah ta kallesa a hankali tace "Yaya driving din dare zaka yi kenan?" Calmly yace "No, za mu yi lodging hotel gobe sai mu tafi Abujan da safe" Ta ɗan buda ido tace "Hotel kuma Yaya?" Ya kalleta ya kashe mata ido yace "Allah na kallonmu ko?" Ta wani kallesa sai kuma ta turo baki ta kauda kai tana murmushi, ya matsa hannunta, ta zaro ido tayi er kara... Hotel me tsada Maheer ya biya masu, yana gaba tana biye da shi har zuwa dakin hotel din da aka basu makulli, bayan ya ajiye wayoyinsa yace "Zan je sallah, close the door" Yana fita ta kulle kofar dakin. Mayraah ta dau sabulunta ta shiga bandaki, sai da tayi wanka ta dauro alwala ta fito dakin, bayan ta idar da sallah ta gama addu'o'inta ta mike ta linke hijab dinta ta ajiye, ta bude box dinta ta fiddo kayan baccinta riga da wando, sai da ta gama shafa turarrukanta ta saka kayan baccin, tana zaune gefen gado tana chatting ta WhatsApp da Mom dinta Maheer yayi knocking, ajiye wayar tayi ta mike ta bude kofar, ya shigo ciki yana kallonta yace "I met with an old time frnd, after many years, shine muke ta labari" Mayraah dake kallonsa tace "Mace ko namiji?" Murmushi yayi ya ajiye abincin hannunsa yace "Kinsan dai bazan maki karya ba, Namiji ne...." Zaunawa Mayraah tayi gefen gado, shi kuma ya bude abincin da aka basu na hotel din, a hankali tace "I am not hungry, kawai drink din zan sha" Ko don abubuwan da Aunty Mariya ta dinga bata ne yasa taji bata jin yunwa ita kanta bata sani ba, Maheer na kallonta yace "Me kika ci?" Tace "Da gaske bana jin yunwa" Yace "Ohk, let me take my bath" Yana shiga bandaki Mayraah ta bude abincin tana kallo, naman ciki ta dauka ta fara ci tana sha da drink din... Bayan ya fito daga wanka yace "Kiyi alwala mu yi isha" Ta tashi ta shiga bandaki, wani alwalan tayi ta fito, suna idar da sallah Maheer ya cire jallabiyarsa ya dawo kusa da ita yana kallonta a hankali yace "Did you miss me Baby gal?" Ita dai bata ce komai ba ta daura kanta jikin gado tana kallonsa bata ko kiftawa, hijab din jikinta ya cire yana kallon riga da wandon jikinta yace "Bana son wannan kayan baccin gaskiya" Ta ɗan buda ido ta kallesa, duk da dariyan da ya bata kawai tayi murmushi tace "Ban gane ba?" Ya matso kusa da ita kamar zai shige jikinta underneath his breathe yace "Change it pls Baby, change it to a more sexy one" Mayraah ta kasa ce masa komai, lkci daya taji duk jikinta was very weak, ya kafeta da ido as if waiting for an answer to his request, da kyar ta iya bude baki tace "Irinsu kadai na taho da fa" Ya kai bakinsa kunnenta yace "Ohk just take 'em off" Mayraah ta zaro ido, sai kuma murya can kasa tace "Sai in sa me?" a hankali yace "U are refusing me my Halal Mimi, whereas kinga yanda ake turo min wanda ba halal ba without me requesting for it... " Mayraah ji tayi wani abu ya tsaya mata a chest bayan Zeenat ta fado mata, ta wani turo baki ta langwabar da kai tace "To ni ya kamata in cire... tunda bai maka ba ai sai ka cire da kanka" Mikewa yayi ya dagota yana kallonta kasa kasa, bata yarda ta hada ido da shi ba saboda she is so ashame dakewa kawai take yi, yayi unbotton din silky rigan baccin dake jikinta, ji tayi kamar ta nutse kasa, barin yanda taga yake kallon bare chest dinta, shi kam kasa daina kallon chest din yayi baya ko kiftawa, taji bazata iya ba ta rufe fuskarta a jikinsa a hankali, ta lumshe ido zuciyarta na bugawa, he made sure he took everything off her body, ya fara exploring din jikinta slowly, he was so surprise after noticing how ready her body was, after a while ya dago kanta as if whispering yace "Look at me pls Mimi" Da kyar ta iya bude idanuwanta kamar me jin bacci tana kallon nasa idon, as if counting his words yace "You are beautiful wife" Ta shige jikinsa tana murmushi, this night would also be a one to remember in their memories, he genuinely cried for her out of pleasance, gashi ta basa co-operation dari bisa dari, ba wanda zai ce ba karatun lamarin aka mata zuwanta kaduna ba, ita kanta bata san ma inda ta ajiye kunyan nata ba a daren nan, haukatar da shi ne kawai bata yi ba, da asuba bayan sun idar da sallah ta kasa hada ido da shi tsabar kunya, sai yanxu take jin kamar ta ɓace kawai don kunyarsa, ya jinginar da kansa a shoulders dinta bayan ya dawo kusa da ita cikin sanyin murya yace "Good morning Wifee" A hankali tace "Ina kwana Yaya" Ya dago kansa yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi da sauri, yayi kasa da murya yace "Plss Baby change that name" Tana murmushi tace "Toh me zance?" Shi dai kallonta kawai yake, ta kwantar da kanta kirjinsa ta lumshe ido, rubbing the chest with her other hand murya can kasa tace "Good morning My Man" Tuni ta kara rikita ma Ammi bawan Allahn ta, yanzun ma dai sai da ta kai sa gaba da cloud 9, whatt... Maheer couldn't believe it is his Lil sis giving him this full co-operation, he genuinely appreciate the reason that lead to Mimi being his wife, ya gode ma dalilin da yasa har ya samu Mimi as wife, he realize she is soo good and perfect in bed, gashi yanzu ta saki jiki gaba daya kunyan ma ajiyesa take aside, sai after everything take sinne kai tana makale masa kar su hada ido, sai kusan karfe tara Maheer ya farka daga baccin da ya daukesu, kallon Mayraah dake jikinsa tana bacci yayi, ya kwantar da ita a hankali yayi kissing forehead dinta sannan ya sauka daga kan gadon ya shiga bandaki, wanka yayi ya fito ya shirya sannan ya masu order din breakfast a hotel din. Karfe sha daya suka bar hotel din suka kama hanyar Abuja, ko barin Kaduna basu yi ba Mayraah ta fara bacci don duk a gajiye take, ya gyara mata kujeran motar yanda zata zama comfortable, duk bayan ɗan lokaci Maheer ke juyawa ya kalleta, shi dai yasan har karshen rayuwarsa bazai gaji da yi ma Allah godiyan mallaka masa Mimi as wife ba, in this life dama there is reason for everything be it good or bad, banda abubuwan nan da suka faru ta yaya har zai mallaki Mayraah a matsayin mata, ashe duk qualities din da yake ganin tana da shi as his lil sis back then tun daga iya girkinta, kokarinta a boko da islamiyya, biyayyanta da kamun kanta, sanyin halinta ashe duk ba komai bane akan quality dinta in bed, infact she is a type of woman every man will be proud to have as wife, ta riga ta gama goge masa hadda tass a bangaren other room, ji yayi a yanzu dai bazai ma iya rayuwa babu ita ba, sai yanzu yake jin yayi aure ashe Haseenah rako mata kawai tayi, baya kwakkwaran 10 mins bai juya ya kalli Mayraah ba, ita kuwa baccinta kawai take, ya ma san dole tayi wnn baccin gajiyan, karfe biyu da yan mintuna suka isa garin Abuja, zuwa sannan Mayraah ta tashi daga baccin da take, da ta hada ido da shi sai ta wani turo masa baki cike da shagwaba, kawai ya rabu da ita ya ma daina kallonta ganin zata kwance masa not din kansa ya sake Steering a kan titi, kawai yayi concentrate a tukin da yake, gidan Abba Maheer ya nufa da su, yana kallon Mayraah bayan yayi parking ya kamo hannunta a hankali yace "Pls wife muna gaida Ammi za mu wuce gida, girkin ki nake son ci yau, i miss it so much" Mayraah ta langwabar da kai tana kallonsa, yace "Ko kin gaji?" A hankali tace "Aa zan yi mana" Ya lumshe ido yayi pecking hannunta yace "Yauwa my baby gal" Maheer na gaida Ammi a bangarenta ya sauko downstairs ya zauna, Mayraah ta nuna ma Ammi atamfar da surkar Aunty Mariya ta bata, Ammi tace "Maa sha Allah, zan ko kirata in mata godiya" Ammi na kallonta tace "Kin dai ga yanda kitson nan ya maki kyau Mimi, dama ki daure ki ci gaba da kitson ko bai kai haka yawa ba" Er dariya Mayraah tayi tace "Ammi kinsan awa nawa aka yi use aka yi kitson?" Ammi tace "Koma awa nawa ne" Murmushi Mayraah tayi, can ta kalli kayan gugan Ammi da Bilkisu ta shigo da shi ba dadewa ta ajiye kan kujera tace "Ammi in gyara maki kayan a press?" Ammi tace "Na ko gode Mimi" Tashi Mayraah tayi ta dau kayan ta shiga daki da shi, saboda kar ma su dade gidan shi sa Maheer yaki zama parlon Ammi ya sauka downstairs amma shiru shiru bai ga Mayraah ta sauko ba, Ita kanta Mayraah hankalinta na kansa kawai dai ta saba in har aka ma Ammi Laundary ita ke gyara mata kayan a press dinta, sharp sharp ta gama jera kayan ta fito parlor, Ammi na kallonta tace "Anya Mimi gyaran arziki kika min kuwa?" Mayraah tayi dariya tace "Allah shigo ki gani Ammi, na gyara kayan fa da kyau" Ammi tayi murmushi tace "To ai shikenan, gida za ku tafi yanzu ko" Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Eh ina son zan yi girki" Ammi tace "Toh shikenan, kun hadu da Usman a kadunan ne?" Mayraah ta daga kai ta kalli Ammi tace "Ehh, amma ya tafi kano" Ammi tace "Kano kuma? Me yaje yi kano?" Shiru Mayraah tayi, can ta ɗan yi yake tace "Toh ban dai san ko wasa yake min ba" Ammi dai tayi shiru bata sake cewa komai ba, Mayraah ta karaso cikin parlon ta dau gyalenta da handbag tace "Ammi sai anjima" Ammi tace "Toh ku gaida gida Mimi" Mayraah ta nufi kofa Ammi ta bi ta da kallo har ta fita, ai daga yanda tayi mata gyaran kaya sharp sharp tasan gida za su tafi, shi ma Maheer din tasan dalilin da yasa yaki zaman parlon nata, don da banza ne da har yanzu yana parlon a zaune, Ammi ta ɗan yi murmushi ta mike ta shiga dakin, tsabar sauri Mayraah ko ledan laundary din da ta ciro kayan a ciki a kan gadon ta bar mata, Ammi ta girgiza kai ta dau ledan ta fita da shi. Bayan isha Mayraah ta gama wanke plate din da suka ci abinci da Maheer, ko da ta fito parlor bata gansa ba, ta dauke sauran drink din da suka rage ta kai fridge, dakinta ta tafi duk da tayi wanka ta sake yi, bayan ta gama shafa turarrukanta ta dinga kallon kayan baccin da ta dauko, zaunawa gefen gado tayi tana jin kamar bazata iya sa shi ba, amma da ta tuna irin yan iskan hotunan da Zeenat ta turo masa kwanaki kawai ta dake ta danne abinda take ji a zuciyarta ta dau kayan baccin ta saka, ta fi minti daya tana kallon kanta ta madubi, can ta yakice kunyar zuciyata ta juya ta nufi kofa ta fita, can bangaren da tasan yake ta tafi, tana shiga parlon taga baya ciki taji alamar he is making call don bai kulle kofar dakin gaba daya ba, tana tafiya a hankali ta karasa kofar ta makale jiki trying to listen to his conversation on the phone, taji yace "But Aunty ina ga kece kawai kika yi wannnan tunanin, kilan ba komai tsakaninsa da ita, probably aiki ma zai je yi kanon shi yasa zai yi dropping dinta" Nan da nan Mayraah ta gane da wa yake wayar kuma akan me suke maganar, juyawa tayi ta bar bakin kofar ta koma cikin parlor ta zauna, sai da taji alamar he is done with the phone call sannan ta mike tana tafiya a hankali ta karasa bakin kofar dakin, calmly tayi knocking kofar ta ɗan koma baya, bude kofar Maheer yayi yana kallonta daga sama har kasa, ta ɗan langwabar da kai cikin sirriyar murya tace "You need coffee or Milk?" Kasa ce mata komai yayi, nan da nan yaji his legs ain't doing him justice don sun kasa ci gaba da daukarsa, ganin ya kasa bata amsa, as if counting her words tana juya masa manyan idanuwanta tace "I said Coffee or Milk?" Stammering

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login