Showing 396001 words to 399000 words out of 452169 words

Chapter 133 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

murya yace "Don girman Allah Ammi kiyi hakuri ki daina irin wannan maganar, duk bai kai haka ba plss, ni nasan barrister in dai kika ce baki son abu to ya bar shi har abada komin son da yake ma abun nan, kema kuma kinsan da haka so bai kamata kina wannan maganar ba, kiyi hakuri don Allah" Hakuri Maheer ya dinga ba Ammi yana kokarin calming dinta down amma taki sauraronsa, daga karshe ta kashe wayar, ya fi minti uku zaune a Parlon ya ma rasa tunanin da zai yi don Ammi ta dau lamarin da zafi, after a while ya mike ya nufi dakin Mayraah, yana bude kofar dakin tana fitowa daga bandaki daure da towel tayi wanka, sau daya ta kallesa ta nufi gaban mirror dinta, ya kulle kofar ya karasa ciki yayi kasa da murya leaning against her body yace "Good morning Better halve" Tana goge jikinta without looking at him tace "Good morning My man" Yana tsaye a bayanta yace "Are you just waking up Baby gal?" Tace "Yeah" Yace "Kin yi breakfast?" Ta girgiza masa kai tace "Zan dai yi yanzu" Duk a takaice take basa amsan tana shafa lotion dinta, a hankali yace "Ohk, bari in je inyi wanka, yau dama bazan je aiki ba, we have all day to cuddle baby gal" Ya kai bakinsa wuyanta yace "Don ma akwai interruption..." Hada ido suka yi ta madubi ta sakar masa murmushin da bai kai zuciyarta ba tana ci gaba da shafa cream dinta, yace "Ko ya dauke ne?" Er dariya tayi tace "Yana nan tukunna" Yace "Ohk let me take my bath" Yana fadin haka ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo ta madubin gabanta har ya fita ya kullo mata kofa, sosai take jin zuciyarta na mata zafi, ita kanta tayi mamakin ta yanda aka yi ta iya dakewa haka take basa amsa, tayi karfin halin yakice kukan da taji na kokarin zuwa mata ta gama shafe shafen da zata yi ta dau kayanta ta saka, gefen gado ta zauna, ta dade zaune kan gadon tayi nisa tunanin da take, kawai saukan ruwan sama ta ji, a hankali ta mike ta tafi ta kulle window din dakinta da ta bude sannan ta fita daga dakin ta tafi parlor, kitchen ta tafi ta dauko breakfast din da tayi ma kanta, tana fitowa parlor sai gashi shi ma ya fito, kallo daya tayi masa ta karaso parlon ta zauna kan carpet da breakfast dinta, ya nufeta ya zauna gabanta yana kallonta yace "Nawa fa?" Ta ɗan buda ido tana kallonsa tace "Ai na zata za kayi kafin ka dawo, i wasn't even expecting you, all my thought daga can zaka tafi Hospital sai yamma kuma" A hankali yace "Shiyasa baki yi breakfast da ni ba?" Ta gyada masa kai, yace "Toh yanzu da na dawo ya za kiyi da ni?" Ta langwabar da kai tace "Sai ka jira idan anyi na rana, kaga wannan dai bai da yawa" Kallonta kawai Maheer yake ganin she is so serious, ita dai ta sauke kanta ta fara cin abincinta, daga kai tayi taga har sannan kallonta yake tace "Ko kuma ka hada shayi ka sha kafin inyi girkin rana" Ya ɗan yi murmushi yace "Zan jira na ranan kawai" Yana fadin haka ya mike ya koma kan kujera yayi powering Tv, tsaf Mayraah ta cinye ɗan dankali da kwan da ta soya ta tafi ta kai plate din kitchen ya bi ta da kallo, tana fitowa daga kitchen din ta karaso ta zauna gefensa tana kallonsa tace "Zan yi bacci idan karfe biyu yayi ka tasheni zan girka lunch" Yace "Ohk dear" Mikewa tayi ta nufi dakinta, tana shiga ta kulle kofarta, wani mugun haushinsa take ji har cikin ranta, ta kwanta ta rufe har kanta da duvet jin hawaye na sauka idonta. Ammi ta fito daga dakinta wajen karfe hudu jin kamar Mama Ladi ce ke rafka sallama a parlonta, ai ko ta ganta tsaye duk ta jike da ruwan sama, Ammi tace "Mama kece cikin ruwan nan?" Mama Ladi tace "To ba kya gan ni cikin ruwa ba, daga kaduna fa nake, wllhi idan nace ban gaji da froblem din pamilyn nan namu ba nayi ma Allahn da ya halicce ni karya, Allah ma ya gani na gaji, ace daga wannan sai wannan kamar mun tafka babban sabo a duniya, Al-qur'an a pamilyn Alhaji Saminu ban ga suna haka ba, in kin gaji da zama da Mamudan ne ba sai ki kama kanki ba cikin mutunci da mutuntawa, wallahi shayi me ƙauri na hada zan sha da burodi da kwai Mamuda ya kirani a fusace wai babu abinda kika mance baki gaya masa ba har kina kiransa da butulu me manta alkhairi, yace min gori sai wanda kika mance ne baki masa ba, shayin da ban sha ba kenan na kamo hanya kamar tababbiya ko rigar mama ban sa ba, ai ko rabin tafiya bamu yi ba ashe rubabbiyar mota na shiga motar ta lalace mana a tsakiyar daji, an fi awa uku ana kokarin dawo da ran motar duk muka zazzauna a gefen titi da ma Allah ya rufa mana asiri ba a kwashe mu anyi cikin daji da mu ba, yanzu haka duk hanjin cikina sun galabaita da yunwa, ga dukan ruwan sama, wannan wani irin jaraba ne ni Ladi, yaushe kika lalace kika tambade haka Hajaru?" Ammi tace "Sai kuma bai gaya maki nace ya tattara ya bar min gidan ya koma gun amaryarsa ba?" Mama Ladi tace "Au, wato kin yanke shawaran zaki sallama ma mai mazaunan mijinki tun auren saurayi da budurwa? Ashe baki da seti ban sani ba, a kanki aka fara kishiya ne wai? To bari dai in canza kayan nan in dawo kada mura ya kamani a banza a hofi ku bar ni da jinya ni ba tsinana ni ku ke da komai ba, shi ma Mamudan yace min yana gida tsabar bacin rai ko fita bai yi ba yau, bari dai in sauya kaya in dawo...." Mama Ladi na tafiya dakin da ta saba sauka ta canza kayanta sannan ta nufi bangaren Abba, tare suka dawo parlon Ammi da Abba, Mama Ladi ta shiga daki ta kira Ammi, Ammi ta zauna kan one seater fuskarta a daure bayan ta fito, Mama Ladi ta zauna tana kallonta tayi kasa da murya tace "Yanzu fisabilillahi Hajara gaki da yara gandara gandara har kin aurar da biyu ana harin na uku amma ace abinda baki yi da kuruciyarki ba shi zaki fara yanzu na rashin yi ma miji biyayya? Duk kin bi kin maida kanki fitinanniyar bafillatana?" Ammi tace "Mama ba fa sai an kai zancen nan da nisa ba, kawai Mamuda ya sauwake min ya tattara ya koma gun matarsa ya bar min gida, bana auren kuma, idan na masa rana zai sani wataran, in ma ban masa ba duk zai sani, haka kawai a dakeni a hanani kuka, akan me? to wallahi na gaji kawai ya sauwake min... naga dai duk maganar da yayi ban tanka sa a parlon ba da ɗana nayi magana na tashi na fita, still ya biyoni bangarena zai min tijara akan nace ɗa na bazai auri er matarsa ba, to na gama aurensa yaje can ya zauna da warce ta fi masa alkhairi" Mama Ladi ta saki salati ta dafe kanta tace "Huhuhu, yau ga abinda ya isheni ni Ladi" Abba dai kallon Ammi kawai yake, Mama Ladi ta sake kanta tace "To ai in ke mahaukaciya ce shi Mamudan ba mahaukaci bane Hajara, kuna zaune lafiya na kusan shekara arba'in babu wanda ya taɓa jin kanku sai da ku ka manyanta za ku fara abubuwa irin na yara, yanzu haka ku ke so Mera da Maheer su kwaikwaya?" Ammi ta katse Mama Ladi tace "Ai wallahi da raina dai Maheer bai isa yace zai ma Mayraah kishiya ba sai in bana numfashi, ba ma Maheer ba duk 'ya yana basu isa su ce za suyi ma matansu kishiya ba, don ina tsoron kada suyi gadon rashin adalci irin na ubansu Allah ya tambayesu, kinga kuwa ai na taimake su" Abba har sannan bai daina kallon Ammi ba, Mama Ladi na kallon Ammi tace "Mamuda bai hanaki ci ba, bai hanaki sha ba, bai hanaki sutura ba, bai kai ma amaryarsa kwananki ba, ga ki a muhalli me kyau na nuna ma sa'a gida duu Ac, to wani rashin adalci kike fadi in za ayi batu na tsakani da Allah? Sannan ke dai naga ba gida daya kike da Aminar nan ba balle ki ga ana fifitata a kanki" Ammi dai bata ce komai ba tana share hawayen da ya kawo idonta, Mama Ladi ta juya tana kallon Abba tace "kai kuma Mamuda banda neman magana da rashin son zaman lafiya irin naka ban ga dalilin da zaka ce lallai lallai sai Usman ya auri er Amina ba, kishiyar da kai kanka kasan har yanzu matar ka bata yi na'am da ita ba saboda kishi irin namu mata, amma duk da haka tana dannewa a ranta..." Abba yace "Ta fadi takamaiman abinda Aminar ta mata da taki na'am da ita har yanzu" Mama Ladi tayi karaf tace "Ta aure mata miji mana, akwai laifin da ya wuce wannan..." Mikewa Ammi tayi tana share idonta tace "Mama kawai ya sallameni ya bar min gidan kawai, aure ne nace na gama, kawai ya kama gabansa bana yi kuma" Tana fadin haka ta shige daki, Mama Ladi tayi kasa da murya tana kallon Abba tace "Kayi hakuri Mamuda, da bata sonka ma bazata fara wannan azababben kishin a kanka ba wallahi, kasan mu mata bamu da control wajen kishin abinda muke so, kishiyar ce ka mata ita a bazata shi sa da duk ta zama haka..." Abba yace "Amma ni abinda nake son in fahimta shine menene aibun auren Usman da er wajen Amina?" Mama Ladi tace "Ai duk aibun da take hangowa kai ba lallai ka hango ba, er kishiyar ta fa aka ce, kawai don a zauna lafiya kayi hakuri ka janye batun nan Mamuda, babu inda aka ce sai lallai ka hada ɗan ka aure da er kishiyar uwarsa, Ammi ba abar walakantawa bace a gareka ina me tunasar da kai, duk sanda ta kwafsa maka kayi kokarin dinga yi mata uzuri kana tuna halaccin da tayi maka a baya sai kaji zuciyarka ta wanke" Abba yace "Sannan ni rabuwan da take fadi kanta tsaye ne ke daure min kai, daga anyi magana daya biyu sai tace a sallameta, a sallameta akan me?" Mama Ladi tace "Duk kishi ne ya rufe mata ido, ka yi mata kishiya a sanda bata yi zato ba bata yi tsammani ba, hakan kuma ya doketa sosai, don haka sai kana lallabata kana kauda kai a wasu abubuwan, nan da shekara daya zuwa biyu sai kaga ta hakura gaba daya ta dawo dai dai, shekara da shekaru kana tare da ita da dadi ba dadi sannan kun san halin juna bai kamata kana yin amarya ka dena mata uzuri ba ka dinga nuna gazawarka na yi mata uzuri, ina lura da yanda kake gasa mata duk maganar da ta zo bakin ka yanzu a gaban kowa, kuma sam da ba haka kake ba wllhi Mamuda, wannan auren da kayi ne ya lalata mana kai ya sauya maka tunani akan komai na gidan ka, shi yasa yanzu idan na zo gidan nan bana wuce kwana biyu don duk ka canza kamar ba kai ba, kaga kuwa Ammi dole ta ga kamar baka bukatarta ne yanzu a rayuwarka, gani zata yi a dole kake tare da ita saboda yara don kafi karkata hankalinka kan amaryarka Amina" Abba dai bai ce komai ba duk yana sauraron Mama Ladi, Mama Ladi ta mike tace "Bari in je kuma in sallami yan hanjina, anjima za mu yi magana ta fahimta da kai" Tana fadin haka ta fice daga parlon, Abba ya fi minti uku zaune parlon bayan fitan Mama Ladi, can ya tashi ya nufi dakin Ammi..... Wajen karfe shidda na yamma Mayraah ta fito daga kitchen bayan ta gama girkin da take, har a sannan ruwa ake duk da bai kai na daxu karfi ba, sosai garin yayi sanyi don rigar sanyi ne ma jikinta, ji take kamar zazzabi ne zai rufeta tun dazu bata jin dadin jikinta, bata tadda Maheer a parlon ba, zata wuce dakinta taji anyi knocking kofar parlor, juyawa tayi tana kallon kofar sai kuma ta karasa bakin kofar don tana ji daxu Maheer na aiken mai gadi amma dai bata san me yace ya siyo masa ba, bude kofar parlon tayi lkci daya tayi turus tana kallonta daga sama har kasa babu ko kiftawa, tana goye da yaro daya a bayanta tana jijjigasa saboda kukan da yake, dayan kuma ta daurasa kan kafadarta shi din ma dai jijjigasan take yana kuka, they were all drenched in rain water, Haseenah na kallon Mayraah cike da gadara tace "A bamu hanya" Mayraah da taki barin bakin kofar tace "Ai ba gidan ubanki bane da za a baki hanya...." Er dariya Haseenah tayi tana kallonta da kyau tace "Eh ba gidan ubana bane, kamar yanda kema ba gidan ubanki bane, amma su kuma twins kinga ai gidan ubansu ne don haka babu karamar shegiyar da ta isa ta hanasu shiga gidan ubansu" Mayraah tace "Zan ko nuna maki na wuce karamar shegiya don wallahi wallahi baki isa ki shigo gidan nan ba daga ke har su" Dariya sosai Haseenah tayi tana jijjiga Aryaan dake kuka sosai yana tari, Aymaan dake bayanta ma tarin yake, tana kallon Mayraah da kyau tace "Ni fa na zata da muka hadu a kaduna zan ganki da cikin naki yan biyun haihuwa ko yau ko gobe sai naga ba haka ba, ke baki yi cikin haifa masa yara ba kuma kice zaki nisanta sa da wa enda Allah ya basa? Ke har kin isa ki raba shi da yaransa in ba dodewar kwakwalwa irin taki ba?" Mayraah tace "Kin baro masu dodadden ƙwaƙwalwa a kano, don in ba dodewar kwakwalwa ba baza su bari ki biyo hanya da kananun yara haka ba, sannan tsabar dodewar kwakwalwarsu basu tunatar maki babu aure tsakaninki da shi wanda kika zo garin nan dominsa ba, banza kawai gantalalliya er wahala" Wani dariya Haseenah tayi har da shewa tace "I am promising you this, in kika ga Maheer bai maida ni gidansa a matsayin matarsa ba sannan uwar tagwayensa to mutuwa yayi, ko kuma ke ce kika mutu bakiyi witnessing ya maida aurenmu ba, yan biyu fa na haifa masa ke kuma ko cikin dayan ma kin kasa dauka har yanzu" Da sauri Maheer ya karaso cikin parlor bayan ya fito daga dakinsa jin kamar hayaniya, buda baki yayi yana kallon Haseenah da yaran a jike jagab, fita balcony yayi da sauri yana kokarin amsan Aryaan a hannunta yace "What's wrong with you Haseenah? Are you mad? menene yasa za ki fito min da yarana cikin ruwa?" Haseenah dai bata tankasa ba, yana amsan Aryaan ta sakko da Aymaan dake bayanta ta daurasa saman kafadarta, juyawa Maheer yayi da sauri zai shiga parlor da yaron hannunsa don cire masa jikakkun kayan jikinsa, Haseenah ta ɗan yi murmushi tana ma Mayraah wani kallo tana biye da Maheer ita ma zata shiga parlon, Mayraah ta tare hanya tana kallon Maheer da kyau tace "Ka daukesu kaje duk inda za ku amma baza a shigo min gida ba" Kallonta Maheer ya dinga yi baya ko kiftawa, can yace "Are you kidding me?" Mayraah tace "Abinda ya fi kidding... In kuma kace lallai sai kun shiga to wallahi tallahi sai dai ka ci gaba da zama da ita da yaran a gidan nan" Maheer that was stunned yace "Mayraah"
Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788

127
Mayraah bata ko kallesa ba zata kulle kofar parlon fuskarta a murtuke ya dakatar da ita yace "Let me get my car key" Yana fadin haka ya ajiye yaron hannunsa dake kuka a nan kasan balcony din ya bi ta gefenta ya shiga cikin parlon, Haseenah tayi wani murmushi tana kallon Mayraah da kyau, cike da gadara tace "Ai in kin san wata baki san wata ba, kuma a banza don kin hanasa shiga gidan da yaransa tunda gashi a kan idonki dai zai kai mu inda ya dace ya kai mu saboda muna da muhimmanci a garesa, ko banza dai ya gwada maki mun fi ki value da matsayi a gunsa, we are far ahead of you...." Fitowar Maheer yasa Haseenah tayi shiru tana jijjiga yaron bayanta dake kuka, ya dau Aryaan dake ta kukan shi ma a kasan tiles din Balcony ya nufi parking space da shi har a sannan ruwan da ake bai tsaya ba, Haseenah na murmushi idonta a kan Mayraah da ta bi Maheer da kallo tace "Sai kuma ayi hakuri sai sanda kika gansa, in kina da hankali da tunani yanzu sai ki gane yaransa sun fi ki value, don kin hanasa shiga ciki da mu to baki isa ki hanasa ya kai mu wani wajen ba, sai a koma ciki ayi zaman jiransa in ma kin gansa kenan yau, banza kawai" Tuni Mayraah ta kulle kofar parlon, ta jingina da kofar lkci daya taji hawaye na zuba idonta numfashinta na yin sama sama, Haseenah ta bi bayan Maheer zuwa parking space, back seat ya bude ya kwantar da Aryaan, ya mika mata hannu yace "Sauko min da shi" Haseenah ta kwance Aymaan dake bayanta Maheer ya amshesa ya bude bayan motar shi ma ya kwantar da shi kusa da ɗan uwansa, Haseenah na kokarin shiga motar strictly yace "Kar ki kuskura ki shigar min mota" Da mamaki take kallonsa baki bude, she wasn't expecting this from him, kawai ji tayi yana kiran security din bakin gate, security din ya taho da sauri, Maheer yace "Bude min gate, ina fita kuma ka tabbatar ka fitar min da wannan matar daga cikin gidan nan, sannan yau ya zama rana ta karshe da ka bude mata

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login