Showing 402001 words to 405000 words out of 452169 words
Chapter 135 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar
komai don ganin Mayraah ta dawo mara amfani a doron kasa, she can go to any extent into making Mayraah useless in life, ita yanzu ko tsoron a maida ta prison din ma bata yi, kawai Allah Allah take gari ya fara haske ta bar unguwan, jakarta ta bude ta ciro wayarta ta tafi contact ta lalubo wani number ta kira, har ya katse ba a daga ba, ta maida wayar jakarta, tana jin an kira sallah ta fito daga shukokin tana rike da jakarta ta bar gun. Karfe goma saura na safe Maheer ya shigo parlor bayan sun dawo daga makabarta, tunda ya shigo parlon Ammi ke kallonsa, daga kusa da ita Aunty Mariya ce da jama'an da suka shigo yi masu gaisuwa, Daga gefen Ammi Mama Ladi ce sanye da zumbulelen hijab da carbi a hannunta tana ja, mikewa Ammi tayi ta bi sa zuwa dakinsa tace "Wai ka sanar ma Mayraah kuwa, nayi ta kiran wayarta bata dagawa" Yace "Eh makullin mota na shigo in dauka zan tafi can gida" Ammi tace "Ko zaka fara yin breakfast?" Yace "Aa idan naje gida zan yi" Ammi ta bi sa da kallo har ya dau car key din sa, sai da ya fita sannan ta dawo ta zauna cikin jama'an dake parlor... Maheer na isa gida bayan yayi parking mai gadi ya rufe gate sannan ya nufosa da sauri yana kara gaishesa, Amsawa Maheer yayi ya kulle motarsa, Mai gadin yace "Yallabai wannan matar ta jiya fa ta sake zuwa nan" Maheer ya juya yana kallonsa yace "Yaushe kenan?" Mai gadin yace "Wajen karfe bakwai na safe" Maheer yace "Sai aka yi yaya?" Mai gadin yace "Aa ban bari ta shigo ba kamar yanda kace Yallabai, don har sai da muka yi hayaniya da ita, mai gadin wancan gidan ya fito da shi muka hadu muka korata" Maheer yace "Shikenan...." Entrance din shiga parlor ya nufa yana tunanin zuwa police station ayi setting masa boundary between Haseenah and his family in all. Yana shiga parlon ya dinga bin ko ina da kallo ganin everything was the way it was yesterday evening, walking slowly ya nufi dakinta ya bude kofar ya shiga ciki, karasawa yayi kan gadonta ya zauna yana kallonta, after few seconds ya yaye duvet da ta rufe har kanta dashi a hankali, ta bude idanuwanta da suka yi ja tana ganinsa zata juya ya rikota da sauri yayi kasa da murya yace "I am sorry Mimi" Da kyar tace "I don't understand, you are sorry for what?" Ya sauke idonsa kasa, after few seconds yace "For what happened yesterday" Ta girgiza kai tace "They are ur family also so there is nothing to be sorry about, just create time for them too" Tana fadin haka ta juya masa baya lkci daya hawaye ya cika idonta yana gangaro mata, Maheer dai ya kasa ce mata komai kansa a kasa, he wasn't expecting this reaction from her, he was expecting her to be mad at him, tun da ya baro can gida yake zullumin yanda za su kwashe da ita in ya iso, but her reaction now made him so weak, sai yaji gwara ma ta zama mad at him da wannan reaction din nata, a hankali yace "We lost the kids Mimi...." Mikewa zaune Mayraah tayi ba tare da ta shirya hakan ba ta juya tana kallonsa bata ko kiftawa, shi dai bai bari sun hada ido da ita ba, da alama she was shock and speechless, after few seconds Maheer ya daga kai ya kalleta yace "Ki shirya za mu tafi can gidan...." Her voice was trembling ta matso kusa da shi da sauri ta kamo hannunsa tace "Ban gane ba Yaya" Yana gyada mata kai cikin karfin hali yace "Yea, Allah ya masu rasuwa gaba daya tun jiya..." Mikewa yayi ya nufi kofa ya fita daga dakin Mayraah ta bi sa da kallo zuciyarta na wani irin bugawa ta koma ta jingina da gado, bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba ta sauka daga kan gadon da sauri. Maheer na komawa parlor da few seconds sai gata ta fito parlon, ya daga kai daga inda yake zaune yana kallonta, kanta a kasa ta nufo inda yake zaune tana tafiya a hankali hawaye na zuba idonta, dukawa tayi kan kneels dinta a gabansa tana girgiza kai cikin rawan murya tace "I don't mean to be mean to dem, just that the mother...." Kasa ci gaba tayi ta hade kanta da kujeran da yake zaune tana kuka sosai, dagota yayi yace "It's not and will never be ur fault Mimi, mahaifiyarsu ce tayi ajalinsu because of her evil mind and selfish interest, she caused their death, dama kuma Allah ya kaddara ba masu tsawon rai bane, don haka kar ki zargi kanki, the least i will do is to blame you wife, i know you have a heart of gold, u have ur reasons which are on point, Alhamdulillah abinda ya hadamu da ita ya raba, and i will now have peace of mind, i know u will bore me many many beautiful kids just like you in sha Allah" Mayraah dai ta kasa daina kukan da take, sosai tayi regretting act dinta, gani take kamar kawai yana kokarin kwantar mata da hankali ne amma ba haka bane a ransa, ta dade bata ji ta shiga wannan tashin hankalin da ta shiga ba, kawai ganin kyawawan yaran take suna mata gizo a vision dinta, Maheer ya dagota ya rungumeta jikinsa trying to calm her down ya kwantar da kanta saman kirjinsa, har a sannan ta kasa daina kuka, abinda ya faru jiya ne kawai ya dinga dawo mata, ita kanta in ance zata yi acting yanda tayi jiya bazata taɓa yarda ba, but maganganun Haseenah was so harsh ba kowa ne zai iya kai zuciyarsa nesa ba, muryarta na rawa ta daga kai tana kallonsa tace "I hate my self for this, i was mean" Maheer yayi murmushi yana girgiza mata kai yace "Noo Baby gal, ke kika shiga cikin ruwa da su? Kinsan tun daga ina ta taho da su a cikin ruwa?" Mayraah dai bata ce komai ba hawaye na sauka idonta, Yayi kasa da murya yana goge mata fuskarta yace "Ki tafi ki shirya mu je can gidan, Ammi is asking of you, blame ur self not wife, it's already written that baza su yi tsawon rai ba, and we all should accept that with good faith" Da kyar Mayraah ta iya mikewa duk jikinta a sanyaye ta nufi dakin ta. Da yammacin ranan wajen karfe bakwai Mayraah ta shigo parlon Ammi rike da plate din abinci da ta zubo ma Mama Ladi, har a sannan bata da kuzari ga wani zazzabi da take ji, Aunty Mariya na kallonta bayan ta ajiye ma Mama Ladi abincin tace "Kin kai ma Maheer ne" Mayraah ta girgiza kai tace "Ya fita zai siyo magani ne" Mama Ladi ta hadiye abincin bakinta tace "Ji jaraba, waye kuma bai da lafiya?" Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Kaina ke ciwo" Mama Ladi tace "Yo ba dole ba wannan uban kuka da kika ci yau ko kece uwar yan biyun nan sai haka, duk mun hakura muna ta cin abinci amma ke ko ruwa kin ki kai wa baki, in an bibiya ma uwar tasu tana can ko dar, dama don ta muzanta mu ta kashe yaran da ruwan sama, da kyar in Hasinu zata ga annabi S.A.W, mu dai Alhamdulillahi tunda Allah ya dubi Maheer ba shi da rabon wahala a duniya, don hada iri da Hasinu ai bala'i ne, Allah mun gode maka da wannan ni'imar da ka mana na daukan ran yaran nan tun ba aje ko ina ba" Daga Ammi har Aunty Mariya wani kallo suke ma Mama Ladi, Yahanasu ta rike haɓa tace "Ke dai Ladi baki da kai sai na daukan kaya, mutuwar ce ni'ima ko kuwa dai baki da hankali ne?" Mama Ladi ta juya ta kalli su Ammi tace "Ku fa yi min iyaka da tsohuwar can, ku min iyaka da ita fa, tun dazu take shigar min hanci da kundundune, wallahi kar mu raba hali a gidan mutuwa a tafi da mu a baki, haka dazu na zubo abinci ta dinga yi da ni, uwar me na tsare mata, to a gaskiya na gaji kada in mata rashin kirki a gidan Mamuda a sa ni a bakin duniya" Shigowar Usman parlon ne yasa Mama Ladi tayi shiru, ya karasa cikin parlon ya nufi Ammi da wayarsa ya mika mata yace "Ammi duba ki ga wacece wannan?" Ammi ta amshi wayar tana duba abinda yake nuna mata, kallonsa tayi da sauri tace "Ba Haseenah bace wannan?" Usman dai was speechless yana kallon Ammi da ita ma ta bude baki, Aunty Mariya ta amshi wayar hannun Ammi tana kallon screen din tace "Me ya faru" Lkci daya Aunty Mariya ta ajiye wayar tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mama Ladi ta maida kwanon abincinta gefe ta tashi da sauri ta nufesu tace "Wani lafin ta kuma tafkawa?" Bata jira a bata amsa ba ta dau wayar tayi mici mici da ido tana kallo.
Gaba daya kowa na parlon yayi shiru ko wanne da tunanin da yake a ransa, Mama Ladi dai shinkafar gabanta take ci tana korawa da lemon fanta me sanyi, Ammi ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Maheer tace "Amma tun yaushe aka kira ka Maheer?" Maheer dake zaune parlon ya daga kai yana kallon Ammi, a hankali yace "Tun kafin magrib, but before then anyi ta kirana da rana i wasn't responding, da naga kiran yayi yawa ne na daga dazu da na fita" Mayraah dai kallon Maheer kawai take, he look so stressed and tired, Ammi tace "To su a ina suka samu Number ka?" Mama Ladi ta dago kai da sauri tace "Wallahi abinda ya fi ƙona min rai kenan, duk lambobin danginta a rasa wanda za a kira sai nasa, meye gamin sa da ita da za a kirasa in ba neman magana ba?" Maheer yace "Tun wajen karfe sha daya na safe tayi accident din, ba a samu wayarta a scene din accident din ba shi yasa har aka dorata yanan gizo ana neman yan uwanta dazu wajen karfe shidda, ina jin daga baya ne ta farfoda sai ta bada lambata...." Mama Ladi tace "Kaji er iska, toh me zaka mata da ta bada lambarka? Ai tunda aka dorata a yanar gizo har mu nan mun gani to danginta ma duk sun gani wllh, don haka kar shegen da ya sake kiranka a bar mu muyi zaman makokin mu a nutse cikin kwanciyar hankali, har yanzu babu ɗan iskan da ya kira mu daga pamilynta yayi mana gaisuwa ko ta'aziyya ba, ko basu san ta kashe yaran bane ohon masu" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Allah ya kyauta, amma da ka kira ko mahaifiyarta don ba lallai sun kai ga gani a social media din ba tunda ba a dade da dorawa ba...." Mama Ladi ta daga kai tana kallon Ammi tace "Yau ni nake ganin jaraba, to ko dai shiryawa za kiyi ki je Zari'an nan ne naga duk kin bi kin damu? haba duk kin bi kin ishe yaro da tambaya a kunnensa baza ki bar sa yaji da mutuwar yaransa har biyu ba, meye hadinsa da Hasinu kuma yanzu da har za a damu don tayi hatsari a hanyar Zari'a, wa gareta a Zaria da ta kama hanyar can din ayi magana ta domin Allah, banda ma dai ma'aikatan asibitin en sharri ne akan wani dalili za su kira Mashir? Meye hadin Maheer da ita yanzu? Dama can wannan yaran ne kuma Allah ya kashesu ba shikenan ba, kilan ma wani mugun abun ta je zata yi a Zari'a Allah ya nuna mata iyakarta, Al-qur'an ban gane ta ba da farko da Usuman ya mika min wayar, kai kace daga bakin ƙura aka kwato ta, da kyar in bata rasa ido daya ba a yanda na ga hoton nan, Usuman da yaga abun bai shafesa ba ai kinga yayi wucewarsa bayan ya nuna mana ita a hoto ya tafi ya ci gaba da harkokin gabansa, ni ma dai wllh bai shafeni ba haka Mashir da Mera, ban dai san ko ke da Mariya ya shafeku ba irin wannan sanyi da jikin ku yayi sai ku shirya ku tafi Zari'a" Ammi ta dau wayarta ta hau kiran Mahaifiyar Haseenah, mikewa Maheer yayi ya ajiye ma Mayraah ledan maganin da ya siyo mata, ita dai kallonsa kawai take har ya fita daga parlon, Mama Ladi tace "Atoh dai ya fi maka gwara kaje kayi abinda zai fissheka, tunda uwar taka ita ta kawo tausayi duniya ba sai ta tashi ta tafi asibitin da aka kwantar da Hasinun ba, mu dai Allah ya isa yan biyun mu da tayi mana sanadin mutuwarsu, gashi tun a duniya ta fara ganin karshenta, Shari'ar mu da ita kuwa sai mun hadu a lahira" Aunty Mariya dai ta ma rasa abun cewa a parlon, sosai jikinta yayi sanyi ganin critical situation din da Haseenah take a hoto, abun ba kyan gani, after a while Mayraah ta mike ganin Mama Ladi ta gama cinye abincin gabanta ta tafi ta dau plate din, Mama Ladi tace "Atoh dai, maza fita ki je kiji da mijinki kiyi ta kwantar masa da hankali kina basa baki Allahn da ya basa su shi zai kara basa wasu nan ba da dadewa ba in sha Allah" Mayraah ta kasa daga kanta, tun da Maheer ya fita take son ta bi sa amma ta kasa tashi a parlon sai yanzu da ta samu opportunity sai gashi Mama Ladi ta mata handsfree, tana rike da plate din ta fita daga parlon, bayan ta kai plate din kitchen ta nufi dakin Maheer, zaune ta samesa a dakin yana deleting pictures din su Aryaan da Aymaan wanda Aunty Mariya ta turo masa few days back a wayarsa, daga kai yayi yana kallonta, ta sunkuyar da kai har ta isa kusa da shi har a lkcn idonsa na kanta yace "Have you eaten dear?" Mayraah ta duka gabansa a hankali tace "What should i make for you?" Yace "I just took tea now" Ta daga kai tana kallonsa, murmushi ya sakar mata ya dagota ta zauna gefensa yayi kasa da murya yace "Ko mu tafi gida, naji ma jikinki da zafi, ina maganin da na siyo maki" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Talk to me baby gal" Ta daga kai tana kallonsa yace "Kin sha maganin?" Ta girgiza masa kai, yace "Yana parlorn Ammi har yanzu? Let me get it for you" Saketa yayi ya mike ta bi sa da kallo har ya fita, ta goge hawayen da ya cika idonta, tun safe har zuwa yanzu bata samu sukuni a ranta ba, gani take kamar ta bada nata contribution din wajen rasuwan yaran, sosai ta shiga damuwa wanda ko abinci ta kasa ci, ta rufe fuskarta da pillow hawaye na sauka idonta, she wish zata iya maida hannun agogo baya da bata yi abinda tayi ba, a haka Maheer ya dawo dakin ya sameta, ya ajiye ledan maganin hannunsa da ruwan goran da ya dauko, ya zauna gefenta ya dago ta yace "Mimi" Ta daga kai hawaye na sauka idonta, rungumeta yayi a hankali yace "Kina son ki gan ni cikin damuwa ne Mimi? Bana son wannan kukan da kike yi, erase every thinking that is making you to cry off ur mind, i believe and have faith that hakan da ya faru shine mafi Alkhairi garemu baki daya, so plss let move on, su kuma Allah ya sa masu ceto ne"
Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788
129
Mayraah dai tayi shiru tana jin duk abinda yake fada, dago kanta yayi yace "Me za ki ci let me get it for you?" Ta girgiza masa kai a hankali tace "I am not hungry" Yace "No dear, you are" Ta girgiza masa kai tace "Da gaske, i am okay" Shiru yayi yana kallonta can ya cire mata hijab dinta yace "To kiyi wanka sai ki sha maganin ki kwanta" Ita dai bata ce komai ba, yace "Let me get u your sleeping dress a dakin ki" Daga haka ya mike ta bi sa da kallo har ya fita daga dakin, ba a wani dau lokaci ba ya dawo dakin, har a sannan tana zaune yanda ya bar ta, ya ajiye rigar baccin gefen gado ya zauna kusa da ita yana kallonta yayi kasa da murya yace "Ko mu yi tare Baby?" Ta daga manyan idanuwanta tana kallonsa, ɗan murmushi tayi ta rufe fuskarta a chest dinsa ta lumshe idonta, duk sakewar da tayi da shi this pass month bata yarda su yi wanka tare ba saboda kunya, zata iya komai da daddare cikin duhu amma da zaran da haske to bata iya yin komai sbda kunya, but if that will please him today zata cire duk kunyarta ta yarda da request dinsa, ya kai bakinsa kunnenta a hankali yace "Kin yi shiru Baby" kai ta gyada masa ba tare da ta bude idonta ba, tana ji ya fara taking off every single cloth that is on her, ita ko tayi nisa tunanin da take na yanda suka taso gida daya seeing their selves as siblings from the same parent, those beautiful memories of them as siblings keep on coming to her mind and how things later turn out, and now the Maheer she sees as her favorite elder brother, the Maheer she cherish soo much as an understanding and lovely elder brother is now a husband to her, they made love... katse tunanin tayi da sauri daga ranta tana girgiza kai a hankali, who could have ever imagine this between the two of them, bata ankara ba kawai sai jin bakinsa tayi a neck dinta ta bude ido da sauri tana kallonsa, shi ma kallonta yake da lumsassun idanuwansa ya dagata heading straight to the large bathroom with her.... Ba su suka fito daga