Showing 405001 words to 408000 words out of 452169 words
Chapter 136 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar
bathroom din ba sai after an hour, ko kayan baccin bata sa ba bacci ya dauketa sai shi ne ya sa mata kayan baccin covering her with duvet, wajen karfe dayan dare taji yana tashinta, ta bude ido da kyar tana kallonsa, kunna wutan dakin yayi mara haske yayi kasa da murya yace "I am hungry wife" Mikewa zaune tayi tace "Toh me zaka ci?" Yace "Ba akwai abinci da aka dafa ba a gidan" Ta sauka daga kan gadon ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta fita daga dakin ta nufi kitchen, ganin da akwai abincin tayi microwaving din masa, ita kanta sai da ya tasheta taji tana jin yuwan don tun safe ta kasa cin abincin kirki, ta daura ruwan da zata hada masa shayi, bayan ta gama ta tafi masu daki da abincin da tea. Washegari da safe wajen karfe tara da rabi bayan Mayraah tayi wanka ta fita daga dakin Maheer ta tafi sama dakinta ta shirya sannan ta nufi bangaren Ammi tana tafiya a hankali, kunya ma take ji ace sai yanzu zata je gaishesu, kuma duk shi yasa suka makara, tana shiga parlon ta zauna kan carpet ta gaishesu, Ammi da Aunty Mariya suka amsa, Mama Ladi ta rike haɓa tace "Ke kuma daga fita da plate din da na ci abinci kitchen shiru bamu sake jin duriyarki ba, ni na zata ma tafiyar ku kuka yi gida kuka bar mu da zaman makoki" Mayraah dai bata ce komai ba, bude kofar parlon aka yi Maheer ya shigo da sallama, Ita dai Mayraah bata dago kanta ba ya zauna kan carpet ya gaishesu, tunda yake bai taɓa kai wa har wannan lokacin in dai yana gida bai shigo gaida Ammi ba, infact da asuba ma yake shigowa gaisheta idan ya dawo masallaci, Mama Ladi tace "Kai dai in gaya maka Mashir Ammi dai tayi waya da mahaifiyar Hasinu, ashe iyayen basu ma san ta kamo hanyar Habuja ba tun daga kano, karya ta lafta ma kanwar uwar cewar zata gidansu tayi kwana biyu don gidan kanwar uwar ta dawo da zama da yan biyun, kaga ai ita ba yarinya bace da kanwar uwar zata hanata zuwa gida kamar yanda ta ce mata, to fa tana lafta wannan karya shine ta nufi tasha ta hau mota ta kamo hanyar Habuja da yara biye raɓe raɓe, sam iyayen basu san abinda ke faruwa ba sai ganin hotonta suka yi yana yawo a yanar gizo ana neman yan uwanta tayi mummunan hatsarin mota a hanyar Zari'a, uwar tace abun sam ba kyau, ta samu lafiyayyun karaya a duk kafafuwanta biyu, hannunta daya ma ya karye sosai, tun daga hancinta zuwa haɓarta kuwa dama sai dai a yanki wani sashi na jikinta ayi mata joni idan zai yiwu kenan, idonta daya ma ana zargin ya tsiyaye abun sai dai iyayenta su ce Innalillahi wa inna ilaihi raji'una don mu kam bai shafemu ba muji da zaman makokin da ta ja mana muke yi ma, amma dai hatsarin na ya sauya mata halitta" Daga Ammi har Aunty Mariya kallon Mama Ladi suke, kai kace taga Haseenah da idonta irin wannan bayanin da take badawa in details, Mama Ladi ta gyara zama tace "Uwar na ta kuka tana Allah wadai da er da Allah ya bata, nace ba kuka zata yi ba tayi ta nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, haba jama'a da wannan wahalan da ta jajibo masu na kashe kudi ai gwara ace mutuwa tayi a hatsarin bakinta alekum, ni dai wallahi ko digon tausayinta ban ji ba a raina, karshenta ne Allah ya kawo, don Hasinu kam ba er arziki bace, kawai mata sbda kin ga yara sun shiga ran mu sai ki kashe mana su da ruwan sama duk da mutuwar tasu tafi alkhairi gare mu, kaga da bata nufi Mera da sharri ba ko Alhaji Saminu sai inyi ma magana a fitar da ita kasar waje ayi mata aiki cikin gaggawa, ban taɓa neman wani abu gun Alhaji Saminu na rasa ba, yanzu ma ba sai na tambayesa ba yake min wllh, sai dai kawai in ga ya min, gida kuwa dama har an siya...." Sai kuma tayi shiru tana gwale ido kamar warce tayi ma sarki karya, Aunty Mariya tace "Wani gidan Mama?" Sallaman da aka yi bakin kofar parlon yasa Mama Ladi ta amsa da sauri duk don ta kawar da tambayar da Aunty Mariya ke mata tace "Bismillah shigo muna nan gaba daya a zaune" Hajiya Amina ce ta shigo parlon, Mama Ladi na murmushi tace "Aa Amina ce ashe, sannu da zuwa Amina" Hajiya Amina ta karaso cikin parlon Aunty Mariya na mata sannu da zuwa, Ta zauna kan carpet ta fara gaida Mama Ladi, Mama Ladi tace "Hau kujera abun ki Amina" Hajiya Amina ta maida dubanta kan su Ammi su ma ta gaishesu, Ammi ta amsa tace "Ya hanya" Maheer ya gaida ta haka ma Mayraah, Hajiya Amina tace "Ya mu ka ji da karin hakuri?" Mama Ladi tayi karaf cikin sanyin murya tace "Hakuri ai sai ma'aiki, mu kam mun dau dangana ma, Allah ya sa hakan shine mafi Alkhairi gare mu baki daya" Hajiya Amina tace "Ameen ya Allah" Ammi tace "Ya su Ihsaan?" Hajiya Amina tace "Suna nan lafiya" Mama Ladi tace "Ya aka yi baki zo da su ba, tun da gaisuwa ce ai da sai ki taho da su mu ma za mu ji dadi" Aunty Mariya dai sai kallon Mama Ladi take, Hajiya Amina tana murmushi tace "Sun je gidan kanwar babansu ne a Katsina" Mama Ladi tace "Maa sha Allah, dama tun da na gansu kyawawa nasan marigayin ubansu bakatsine ne, Allah dai ya ji kansa yayi masa Rahama" Murmushi kawai Hajiya Amina take a hankali tace "Ameen ya Allah" Maheer ya mike ya fita daga parlon. Bayan wani lokaci Hajiya Amina ta mike tace "Bari mu je can parlon, naga da mutane" Mama Ladi tace "Ehh gaskiya can ma yafi iska, tashi mu je can kawai" Mama Ladi ta dau carbinta ta mike ta bi bayan Hajiya Amina suka fita daga parlon, Ammi na kallon Mayraah tace "Kin yi breakfast Mimi?" Mayraah ta girgiza kai sannan ta mike ta fita daga parlon, Aunty Mariya na kallon Ammi tace "Amma dai Ammi ya kamata a samu me ƙwabar Mama Ladi akan shisshige ma kakannin Mayraah da take, haba abun ai yayi yawa sam ba tsari" Ammi tace "Wa kika ga ya isa ya kwabeta Mariya? Nima abun na damu na wallahi, a ina aka taɓa yin haka? Allah ne kadai yasan irin abubuwan da take masu a can, wannan ai sai mutunci ya zube" Aunty Mariya tace "Ai ko zan kira Hajja in gaya mata tayi mata magana gaskiya, zagi dai ne na san za mu sha shi kwando kwando amma aje a haka, haba tun ana mata abu na marmari har sai ta tsire ma mutane" Ammi dai tayi tagumi bata ce komai ba, Aunty Mariya tace "Amma Ammi don Allah ki saki ranki ki tashi mu sauka downstairs mu zauna, wannan baiwar Allahn da ta zo yanzu naga alamar er siyasa ce sannan ta san kan zama da mutane, yanzu fa a rayuwar nan komai siyasa ne wallahi Ammi" Ammi tace "Siyasa ko munafurci? Ke kanki kin san ban iya munafurci ba kuma bazan fara ba da sunan siyasa, don yanzu munafurci ake dangantawa da siyasa, though ni bani da wani issue da ita right from beginning, sannan ni babu abinda ya taɓa hada ni da ita, the issue i am having is with my husband, ya kuma gano laifinsa and he promise to amend his ways that is if he can keep to that promise, amma ban taɓa ce maku ina da matsala da matarsa ba kuma bana fatan in samu matsala da ita after all a ina zan ganta ko kuma ita a ina zata gan ni in ba da kwakkwaran dalili ba kamar irin wannan wato zuwa taya farin ciki or otherwise which we don't pray for" Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya tace "Haka ne kam" Ammi tace "Sai kuma da yake kokarin hada ɗan sa da er ta ta karfi da yaji, that i will never approve and i told him bluntly..." Aunty Mariya tace "Allah ya sa mu dace" Ammi tace "Ameen" Throughout ranan Ammi da Aunty Mariya suna downstairs tare da Hajiya Amina warce zata kwana a gidan saboda sadakan uku da za ayi na yan biyu gobe, yanda Mama Ladi ke jan ta a jiki kai kace wajenta ta zo, hatta abinci ita ta debo mata da manyan kaji sannan ga lemo kala uku... Wajen karfe biyar na yamma Mayraah ta kawo ma Hajiya Amina wayarta da ta jona mata a caji ganin Abba ne ke kiranta, Hajiya Amina ta amshi wayar sai bata daga ba har ya katse, miss calls dinta ta hau dubawa bayan kiran Abba ya katse, Mama Ladi tace "Ba kiranki ake ba Amina?" Hajiya Amina ta kalleta tace "Ai kam har ma ya katse" Ita dai Ammi na zaune suna hira da surkar Dr Khalil da ta zo yi masu gaisuwa tare da er ta Zainab, Ita Mayraah dariya ma Zainab din ke bata don abu kusan wata nawa amma bata wani son hada ido da Mayraah sai tayi ta kame kame, ita kam Mayraah har cikin ranta taji ta yafe mata abinda tayi mata amma Zainab still taki sakin jiki, wayar Hajiya Amina ne ya fara ring, Mama Ladi tayi karaf ta ce "To gashi an maido da kiran" Hajiya Amina ta daga kiran ta kai kunne hade da sallama, lkci daya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mama Ladi ta mike tsaye da sauri tace "Lafiya??" Su Ammi duk suka juya suna kallonta su ma, Aunty Mariya ta mike ta dawo kusa da ita tace "Hajiya Lafiya?" Sai da Hajiya Amina ta gama wayar da take sannan ta ajiye wayar a gefenta, Mama Ladi tace "Lafiya? Me ke faruwa?" Aunty Mariya ta wani kalli Mama Ladi, tare fa duk suka ji communication din da take a waya kuma still Mama Ladi na tambayar me ke faruwa, Hajiya Amina tana kallon Mama Ladi tace "Gwaggon su Ihsaan ce ta kira ni wai basu da lafiya tun da safe" Mama Ladi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, naji kamar tace maki har da suma ko?" Hajiya Amina tace "Eh wallahi" Mama Ladi ta zauna gefen kujera cike da alhini tace "Dama basu da lafiya ne?" Hajiya Amina ta girgiza kai tace "Lafiyarsu kalau suka bar kano wllhi" Aunty Mariya tace "Allah Ubangiji ya basu lafiya" Ammi da Mom din Zainab su ma duk suka masu fatan samun lafiya Hajiya Amina tace "Ameen" Mama Ladi tace "To amma banda abun gwaggwan tasu meye sai ta kiraki ta gaya maki ko er yarinya ce dai, banda haka sai ta masu abinda ya kamata tunda ita ma uwa take garesu" Hajiya Amina tace "Tun safe ne ai abun ya faru kuma kinga sai yanzu take gaya min" Mama Ladi tace "To an kai su asibiti dai ko?" Hajiya Amina tace "Eh suna asibitin ma yanzu haka" Mama Ladi tace "Amma dai magana ta domin Allah bai kamata ta kira ki ta daga maki hankali ba kina gidan mutuwa, kuma duk su biyun ne ba lafiya?" Hajiya Amina tace "Eh wai Eeman ce ta fara, to dama su haka suke daya baya rashin lafiya daya bai yi ba" Mama Ladi tace "Amma dai dama can sun saba suma ko?" Ammi dai ta dauke kai, Aunty Mariya tayi tagumi cike da takaici, yanda Mama Ladi ke jero tambayar one by one zaka zata retired er jarida ce, Hajiya Amina tace "Aa basu taɓa ba gaskiya, shine ma yasa har ta kirani yanzu" Mama Ladi tace "To ki kwantar da hankalinki babu abinda zai faru sai alkhairi, kawai ina jin canjin ruwa ne kilan ruwan pampo suke sha a gidan, nima nan da girmana farko farko kafin in saba da zaman Kaduna haka na dinga zazzabi sama sama sbda rashin sabo, to gashi yanzu zaman garin ya zame min jiki ina zaune lafiyan Allah, ba ko ciwon kai, kwana nawa za su yi a Katsinan ne?" Hajiya Amina dai duk bata san abinda Mama Ladi ke cewa ba don gaba daya tunaninta yayi wani wajen daban, sosai taji hankalinta ya koma kan yan biyunta, it's very rare su yi rashin lafiya kuma wai har da suma, abinda basu taɓa yi ba, muryar Mama Ladi da taji a tsakiyar kanta ne yasa ta daga kai da sauri tana kallonta, Mama Ladi tace "Kwanan su nawa a katsinan?" Hajiya Amina tace "Kwanan su biyu kenan" Mama Ladi tace "Ahaf zuwa anjima duk za su warware canjin ruwa ne" Hajiya Amina ta ɗan yi murmushi tace "Allah ya sa" Mama Ladi tace "Haba ai jini ba wasa ba, dama tun da kika shigo na lura baki da kuzari karfin hali kawai kike, ashe tagwayenki ne kwance ba lafiya kike ji a jikin ki, Allah Ubangiji dai ya basu lafiya, mu dai gashi an kashe mana namu tagwayen har lahira don mugunta, Allah dai ya ji kansu kawai yasa masu ceto ne" Mama Ladi na kai wa nan ta fara matsar kwalla, a hankali Hajiya Amina tace "Ameen ya Allah" Nan Mama Ladi ta dinga bata labarin ta yanda su Aymaan suka rasu, shidda saura Ammi ta fita raka Ummi, Aunty Mariya kuma ta mike ta tafi kitchen don ita ke assisting Bilkisu suna girka Dinner, Mama Ladi na kallon Hajiya Amina tace "Bari dai in je in ga yau kuma me ake dafa mana ga magariba ya gabato har yanzu ban ga an sauke tukunya ba..." Tashi tayi ta nufi kitchen, tana shiga ta tsallake Aunty Mariya ta tafi inda Mayraah ke yi ma Maheer girki tana murmushi tace "Ikon Allah, abincin kala biyu za a mana kenan yau" Aunty Mariya tace "Aa ga nan namu ina yi, wancan kuma mijinta take ma girki" Mama Ladi ta kalli abinda su Aunty Mariya ke dafawa sannan ta sake kallon wanda Mayraah ke dafawa tace "Ikon Allah, wato ke me miji bazai ci wanda aka dafa ma yaku bayin dake gidan ba, to ni dai bari in taya ki yanka koren tattasan" Aunty Mariya dai ta girgiza kai tana ci gaba da juya stew din dake kan wuta... Bayan barin Mama Ladi parlon Ammi ta dawo daga rakiyar da tayi ma baƙinta zuwa compound, tana kallon Hajiya Amina tace mata ta taho sama tayi alwala lkcn sallah yayi sannan ta tafi sama, Hajiya Amina ta sake kiran Aunt dinsu Eeman, tana dagawa tace "Aisha can i speak to them?" Aunt dinsu Eeman ta sanar mata sun samu bacci, Hajiya Amina tace "Ki tada Eeman ki bata waya let her talk to me" Hakan Aunt din nasu tayi, Hankalin Hajiya Amina ya kara tashi sosai hearing Eeman's voice, kawai ji tayi she just have to go to her girls, this is so unusual of them tunda ta haifesu basu taba wani abu wai shi suma ba, shi yasa duk take jin ta wani iri tun da ta fito gida a kano har ta iso Abuja, katse wayar tayi tana kokarin dialing number Abba Usman ya shigo parlon, ya karaso ya zauna yana kallonta ya gaisheta, ta amsa da murmushi tace "Ai na zata ma kana Kaduna" Yace "Aa ina nan..." Tace "Ya karin hakuri?" Yace "Alhamdulillah" After few seconds ta daga kai ta kallesa tace "Usman za a samu flight going to Kano da daddaren nan kuwa?" Yace "Komawa kanon za ku yi Aunty?" A hankali tace "Wallahi kirana aka yi su Ihsaan basu da lafiya suna asibiti, it's so unusual of them..." Usman yace "Subhanallah, me ya same su?" Hajiya Amina tace "Wai sun ma fita ne da safe za su je kitso and Eeman pass out on their way, kafin ma a isa hospital da ita Ihsaan did same too, not long ago aka kirani ake gaya min" Usman ya ɗan yi shiru, can yace "Allah ya basu lafiya, amma da ki bari sai ki bi Flight din safe Aunty" Tace "Duba min dai ko za a samu" Usman bai sake cewa komai ba ya ciro wayarsa zai duba mata if their is any available flight to kano that evening, ta mike tace "Before then bari in ɗan yi magana da Abbanku" Yace "Ohk" wayarta ta dauka ta fita compound, tayi dialing number Abba hoping bai shiga Masallaci ba don lkcn sallahn magrib yayi, Abba na dagawa bayan ta gaishesa ta sanar masa zata koma kano da dalilin komawar nata, Abba da yayi shiru yana sauraronta yace "To su kuma da suke katsina ko kin koma kano a daren nan ba wani difference da zai yi making ba ai, ki bari kawai sai Allah ya kai mu gobe sai ki bi morning flight" Shirun da tayi ne yasa Abba yace "But if kinga hankalinki zai fi kwanciya idan kin koma kanon yau it's fine, in an samu Flight din sai ki sanar min" Hajiya Amina tace "Alright thank you ranka shi dade" Komawa cikin parlor tayi tana kallon Usman tace "Ka samu Flight din" yace "Ehh na samu but nan da 30mins jirgin zai tashi, bai ma cika ba za su tashi" Hajiya Amina tace "Toh bari in sanar ma Ammin ku" Sama ta tafi zuwa parlon Ammi, bayan ta sanar ma Ammi, Ammi tace "Toh Allah Ubangiji ya basu lafiya cikin gaggawa" Hajiya Amina tana kallon Ammi tace "Ameen ya Allah" Ammi tace "An samu jirgin ne yanzu?" Tace "Ehh Usman yace min an samu, ya ma kusa tashi" Ammi tace "Toh Alhamdulillah, sai ya kai ki airport din da wurwuri, amma dai ba a yau din zaki karasa katsinan ba in kin sauka kano saboda dare ga hanya sai addu'a" Hajiya Amina tace "Zan bari da safe in sha Allah" Ammi tace "Toh Allah ya kai mu" Hajiya Amina tace "In ji dai baki yi fushi ba, ba za ayi sadakan uku da ni ba" Ammi tace "Haba dai, ba komai wallahi