Showing 408001 words to 411000 words out of 452169 words

Chapter 137 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

ai lalura ce ta taso, Allah dai ya basu lafiya" Hajiya Amina tace "Ameen" Sai da Hajiya Amina tayi sallahn magrib sannan ta sauko downstairs tare da Ammi, Mama Ladi da ta fito daga kitchen kenan ta saki baki ganin Hajiya Amina da karamin jakarta a hannu, tace "Ina kuma za ki Amina? Kaddai kano za ki koma da daddaren nan?" Hajiya Amina tayi murmushi tace "Mama ai jirgi ne" Mama Ladi tace "Ikon Allah yanzu dai in ba dora ido kika yi kan yaran nan ba kika ganki kusa da su baza ki taɓa samun sukuni da nutsuwa ba, ko da yake da gaskiyarki mu da muka yi sakwa sakwa da namu yan biyun ba gashi an kashe mana su har lahira ba, gwara ki je gun kayanki bakinki alekum, Allah dai ya basu lafiya cikin gaggawa, kuma duk kice muna masu sannu, in na samu sarari har kanon zan zo dubasu idan Allah ya yarda" Ita da Hajiya Amina murmushi kawai take, Mayraah ta karasa ta amshi jakar hannunta, nan duk suka rakata compound, don Usman na can parking space ya tada mota yana jiranta, Hajiya Amina na kallon Mama Ladi tace "To mama ayi min hakuri ban zauna ayi sadakan uku da ni ba" Da sauri Mama Ladi tace "Haba dai ai duk mun san lalura, ke dai Allah ya kai ki kanon lafiya ya ba yan biyun ki lafiya" Hajiya Amina tayi ma Ammi da Aunty Mariya sallama sannan ta juya tana kallon Mayraah ta amshi jakarta a hannunta, Mayraah tace "Allah ya tsare Aunty" Hajiya Amina tace "Ameen Mayraah, ai ta hakuri a zauna lafiya kin ji, duk da nasan Maheer ba shi da matsala be a good wife to him, Allah ya baku zuri'a dayyaba" Mayraah dai ta sauke idonta kasa, Hajiya Amina ta shiga motar, suka dau hanyar airport da Usman. Suna isa airport Hajiya Amina tace ma Usman ba sai ya shiga ba don har ciki ya so rakata, tana rike da karamin jakar hannunta tace "Ka tura min ticket din ai ta WhatsApp ko?" Yace "Eh na tura" Tace "Nawa ne kudin ticket din?" Yace "Kawai ganin alert nayi Abba ya turo 150k, but the ticket is 110k" Hajiya Amina tace "Ohk to, sai mun yi magana" Yace "Allah ya tsare" Tace "Ameen" Sai da ya ga shigarta airport sannan ya juya motarsa, Hajiya Amina na shiga airport din aka sanar mata ko minti uku ba ayi da tashin jirgin ba, zaunawa tayi tana tunanin yanda zata yi, hankalinta bazai taɓa kwanciya ba in ba ganinta tayi gun yan biyunta ba don so tayi jirgin na sauka kano ta dau hanyar kt, tana ta zaune airport din tuna nazarin yanda zata yi, tasan tana ce ma Abba babu jirgi zai ce ta dawo, ta ciro wayarta ta saka Flight mode ta mayar cikin handbag dinta. Karfe takwas da yan mintuna Maheer ya shigo parlor bayan ya raka colleagues dinsa da suka zo yi ma Ammi gaisuwa, bai tadda Ammi a parlon ba, hakan yasa ya tafi sama don tunda ya dawo bai ga Mayraah ba, bude kofar dakinta yayi ya ganta kwance kan darduman da tayi sallah har ta fara bacci, ya karasa kusa da ita ya duka yana kallonta yace "Mimi" a hankali ta bude ido, sai kuma ta mike zaune da sauri tace "Yaya ka dawo?" Yace "Kin gaji ko?" Ta marairaice masa tace "Kaina ke min ciwo, amma na sha magani naji ma yayi sauki" Ya dafa goshinta yace "Allah ya sauwake Baby Gal, gobe za mu tafi gida in sha Allah" Tace "In kawo maka abincin yanzu?" Yace "Wanka zan fara yi tukun" Tace "Ohk" Mikewa tsaye tayi ta dauke darduman tace "Ko zaka shiga bathroom dina kayi wankan?" A hankali yace "Sai mu yi tare?" Turo baki tayi ta masa wani kallo, yace "Toh shikenan an fasa wankan ma, abincin ma an koshi" Ta marairaice masa tace "Wallahi ka fiye wayo yaya" Yace "I will take off ur clothe, and then you retaliate" Ta masa wani kallo ta fara unbotton din masa shirt din jikinsa a hankali yana kallonta..... Abba na zaune parlonsa wajen karfe goma na dare, Ammi ta shigo masa da black tea da ta dafa masa, ajiye masa tayi ta nemi waje ta zauna tana kallonsa tace "Nayi ta kiran layin Maman su Ihsaan ban samu ba har yanzu, fatan dai ta isa gida lafiya, sannan ya jikin su Ihsaan din?" Abba yace "Nayi trying line din nata nima ban samu ba probably network...." Ammi tace "To ka kira mai gadin gidan mana" Mikewa Ammi tayi ta fita daga parlon zata dauko masa water melon da ta saka masa a fridge yayi sanyi, Ammi na fita ba dadewa wayan Abba ya fara ring, ya duba ganin Hajiya Amina ya daga kiran ya kai kunne.....

Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788

130
Yanda Haseenah taga rana haka ta ga dare a cikin flowers din kofar gidan Abba da ta rakube, tayi kuka har ta gode Allah, ga insect dake ta cizon ta a jiki, har a sannan ta kasa yarda wai yaronta daya ya mutu, ta yaya ma zai mutu yaran da ta taho Abuja da su hale and hearty, so full of life, bazai taɓa yiwuwa ba ace daya ya mutu, gani take kamar mafarki take kuma zata farka daga mugun mafarkin, a haka aka fara yayyafi wajen karfe hudun asuba, kawai abubuwan da suka faru a gidan Maheer ne ya dinga dawo mata daya bayan daya, har da yanda Mayraah ta hanasa shiga da su cikin gidan, ta fashe da matsanancin kuka zuciyarta na tafarfasa tace "Wallahi ita ta kashe min yarona, ita ce sanadi, ita ce silar mutuwarsa, don da mun shiga gidan duk haka bazai faru ba, dole in dau revenge din kashe min yaro da kika yi" Har aka kira sallan asuba tunaninta na kan abinda zata ma Mayraah as revenge, ta zo Abuja da mission iri iri amma ko daya bata yi achieving ba sai ma mutuwa da ɗan ta daya yayi, ji tayi gaba daya zuciyarta ya kekashe, har ranta taji zata iya yin komai don ganin Mayraah ta dawo mara amfani a doron kasa, she can go to any extent into making Mayraah useless in life, ita yanzu ko tsoron a maida ta prison din ma bata yi, kawai Allah Allah take gari ya fara haske ta bar unguwan, jakarta ta bude ta ciro wayarta ta tafi contact ta lalubo wani number ta kira, har ya katse ba a daga ba, ta maida wayar jakarta, tana jin an kira sallah ta fito daga shukokin tana rike da jakarta ta bar gun. Karfe goma saura na safe Maheer ya shigo parlor bayan sun dawo daga makabarta, tunda ya shigo parlon Ammi ke kallonsa, daga kusa da ita Aunty Mariya ce da jama'an da suka shigo yi masu gaisuwa, Daga gefen Ammi Mama Ladi ce sanye da zumbulelen hijab da carbi a hannunta tana ja, mikewa Ammi tayi ta bi sa zuwa dakinsa tace "Wai ka sanar ma Mayraah kuwa, nayi ta kiran wayarta bata dagawa" Yace "Eh makullin mota na shigo in dauka zan tafi can gida" Ammi tace "Ko zaka fara yin breakfast?" Yace "Aa idan naje gida zan yi" Ammi ta bi sa da kallo har ya dau car key din sa, sai da ya fita sannan ta dawo ta zauna cikin jama'an dake parlor... Maheer na isa gida bayan yayi parking mai gadi ya rufe gate sannan ya nufosa da sauri yana kara gaishesa, Amsawa Maheer yayi ya kulle motarsa, Mai gadin yace "Yallabai wannan matar ta jiya fa ta sake zuwa nan" Maheer ya juya yana kallonsa yace "Yaushe kenan?" Mai gadin yace "Wajen karfe bakwai na safe" Maheer yace "Sai aka yi yaya?" Mai gadin yace "Aa ban bari ta shigo ba kamar yanda kace Yallabai, don har sai da muka yi hayaniya da ita, mai gadin wancan gidan ya fito da shi muka hadu muka korata" Maheer yace "Shikenan...." Entrance din shiga parlor ya nufa yana tunanin zuwa police station ayi setting masa boundary between Haseenah and his family in all. Yana shiga parlon ya dinga bin ko ina da kallo ganin everything was the way it was yesterday evening, walking slowly ya nufi dakinta ya bude kofar ya shiga ciki, karasawa yayi kan gadonta ya zauna yana kallonta, after few seconds ya yaye duvet da ta rufe har kanta dashi a hankali, ta bude idanuwanta da suka yi ja tana ganinsa zata juya ya rikota da sauri yayi kasa da murya yace "I am sorry Mimi" Da kyar tace "I don't understand, you are sorry for what?" Ya sauke idonsa kasa, after few seconds yace "For what happened yesterday" Ta girgiza kai tace "They are ur family also so there is nothing to be sorry about, just create time for them too" Tana fadin haka ta juya masa baya lkci daya hawaye ya cika idonta yana gangaro mata, Maheer dai ya kasa ce mata komai kansa a kasa, he wasn't expecting this reaction from her, he was expecting her to be mad at him, tun da ya baro can gida yake zullumin yanda za su kwashe da ita in ya iso, but her reaction now made him so weak, sai yaji gwara ma ta zama mad at him da wannan reaction din nata, a hankali yace "We lost the kids Mimi...." Mikewa zaune Mayraah tayi ba tare da ta shirya hakan ba ta juya tana kallonsa bata ko kiftawa, shi dai bai bari sun hada ido da ita ba, da alama she was shock and speechless, after few seconds Maheer ya daga kai ya kalleta yace "Ki shirya za mu tafi can gidan...." Her voice was trembling ta matso kusa da shi da sauri ta kamo hannunsa tace "Ban gane ba Yaya" Yana gyada mata kai cikin karfin hali yace "Yea, Allah ya masu rasuwa gaba daya tun jiya..." Mikewa yayi ya nufi kofa ya fita daga dakin Mayraah ta bi sa da kallo zuciyarta na wani irin bugawa ta koma ta jingina da gado, bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba ta sauka daga kan gadon da sauri. Maheer na komawa parlor da few seconds sai gata ta fito parlon, ya daga kai daga inda yake zaune yana kallonta, kanta a kasa ta nufo inda yake zaune tana tafiya a hankali hawaye na zuba idonta, dukawa tayi kan kneels dinta a gabansa tana girgiza kai cikin rawan murya tace "I don't mean to be mean to dem, just that the mother...." Kasa ci gaba tayi ta hade kanta da kujeran da yake zaune tana kuka sosai, dagota yayi yace "It's not and will never be ur fault Mimi, mahaifiyarsu ce tayi ajalinsu because of her evil mind and selfish interest, she caused their death, dama kuma Allah ya kaddara ba masu tsawon rai bane, don haka kar ki zargi kanki, the least i will do is to blame you wife, i know you have a heart of gold, u have ur reasons which are on point, Alhamdulillah abinda ya hadamu da ita ya raba, and i will now have peace of mind, i know u will bore me many many beautiful kids just like you in sha Allah" Mayraah dai ta kasa daina kukan da take, sosai tayi regretting act dinta, gani take kamar kawai yana kokarin kwantar mata da hankali ne amma ba haka bane a ransa, ta dade bata ji ta shiga wannan tashin hankalin da ta shiga ba, kawai ganin kyawawan yaran take suna mata gizo a vision dinta, Maheer ya dagota ya rungumeta jikinsa trying to calm her down ya kwantar da kanta saman kirjinsa, har a sannan ta kasa daina kuka, abinda ya faru jiya ne kawai ya dinga dawo mata, ita kanta in ance zata yi acting yanda tayi jiya bazata taɓa yarda ba, but maganganun Haseenah was so harsh ba kowa ne zai iya kai zuciyarsa nesa ba, muryarta na rawa ta daga kai tana kallonsa tace "I hate my self for this, i was mean" Maheer yayi murmushi yana girgiza mata kai yace "Noo Baby gal, ke kika shiga cikin ruwa da su? Kinsan tun daga ina ta taho da su a cikin ruwa?" Mayraah dai bata ce komai ba hawaye na sauka idonta, Yayi kasa da murya yana goge mata fuskarta yace "Ki tafi ki shirya mu je can gidan, Ammi is asking of you, blame ur self not wife, it's already written that baza su yi tsawon rai ba, and we all should accept that with good faith" Da kyar Mayraah ta iya mikewa duk jikinta a sanyaye ta nufi dakin ta. Da yammacin ranan wajen karfe bakwai Mayraah ta shigo parlon Ammi rike da plate din abinci da ta zubo ma Mama Ladi, har a sannan bata da kuzari ga wani zazzabi da take ji, Aunty Mariya na kallonta bayan ta ajiye ma Mama Ladi abincin tace "Kin kai ma Maheer ne" Mayraah ta girgiza kai tace "Ya fita zai siyo magani ne" Mama Ladi ta hadiye abincin bakinta tace "Ji jaraba, waye kuma bai da lafiya?" Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Kaina ke ciwo" Mama Ladi tace "Yo ba dole ba wannan uban kuka da kika ci yau ko kece uwar yan biyun nan sai haka, duk mun hakura muna ta cin abinci amma ke ko ruwa kin ki kai wa baki, in an bibiya ma uwar tasu tana can ko dar, dama don ta muzanta mu ta kashe yaran da ruwan sama, da kyar in Hasinu zata ga annabi S.A.W, mu dai Alhamdulillahi tunda Allah ya dubi Maheer ba shi da rabon wahala a duniya, don hada iri da Hasinu ai bala'i ne, Allah mun gode maka da wannan ni'imar da ka mana na daukan ran yaran nan tun ba aje ko ina ba" Daga Ammi har Aunty Mariya wani kallo suke ma Mama Ladi, Yahanasu ta rike haɓa tace "Ke dai Ladi baki da kai sai na daukan kaya, mutuwar ce ni'ima ko kuwa dai baki da hankali ne?" Mama Ladi ta juya ta kalli su Ammi tace "Ku fa yi min iyaka da tsohuwar can, ku min iyaka da ita fa, tun dazu take shigar min hanci da kundundune, wallahi kar mu raba hali a gidan mutuwa a tafi da mu a baki, haka dazu na zubo abinci ta dinga yi da ni, uwar me na tsare mata, to a gaskiya na gaji kada in mata rashin kirki a gidan Mamuda a sa ni a bakin duniya" Shigowar Usman parlon ne yasa Mama Ladi tayi shiru, ya karasa cikin parlon ya nufi Ammi da wayarsa ya mika mata yace "Ammi duba ki ga wacece wannan?" Ammi ta amshi wayar tana duba abinda yake nuna mata, kallonsa tayi da sauri tace "Ba Haseenah bace wannan?" Usman dai was speechless yana kallon Ammi da ita ma ta bude baki, Aunty Mariya ta amshi wayar hannun Ammi tana kallon screen din tace "Me ya faru" Lkci daya Aunty Mariya ta ajiye wayar tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mama Ladi ta maida kwanon abincinta gefe ta tashi da sauri ta nufesu tace "Wani lafin ta kuma tafkawa?" Bata jira a bata amsa ba ta dau wayar tayi mici mici da ido tana kallo.

Gaba daya kowa na parlon yayi shiru ko wanne da tunanin da yake a ransa, Mama Ladi dai shinkafar gabanta take ci tana korawa da lemon fanta me sanyi, Ammi ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Maheer tace "Amma tun yaushe aka kira ka Maheer?" Maheer dake zaune parlon ya daga kai yana kallon Ammi, a hankali yace "Tun kafin magrib, but before then anyi ta kirana da rana i wasn't responding, da naga kiran yayi yawa ne na daga dazu da na fita" Mayraah dai kallon Maheer kawai take, he look so stressed and tired, Ammi tace "To su a ina suka samu Number ka?" Mama Ladi ta dago kai da sauri tace "Wallahi abinda ya fi ƙona min rai kenan, duk lambobin danginta a rasa wanda za a kira sai nasa, meye gamin sa da ita da za a kirasa in ba neman magana ba?" Maheer yace "Tun wajen karfe sha daya na safe tayi accident din, ba a samu wayarta a scene din accident din ba shi yasa har aka dorata yanan gizo ana neman yan uwanta dazu wajen karfe shidda, ina jin daga baya ne ta farfoda sai ta bada lambata...." Mama Ladi tace "Kaji er iska, toh me zaka mata da ta bada lambarka? Ai tunda aka dorata a yanar gizo har mu nan mun gani to danginta ma duk sun gani wllh, don haka kar shegen da ya sake kiranka a bar mu muyi zaman makokin mu a nutse cikin kwanciyar hankali, har yanzu babu ɗan iskan da ya kira mu daga pamilynta yayi mana gaisuwa ko ta'aziyya ba, ko basu san ta kashe yaran bane ohon masu" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Allah ya kyauta, amma da ka kira ko mahaifiyarta don ba lallai sun kai ga gani a social media din ba tunda ba a dade da dorawa ba...." Mama Ladi ta daga kai tana kallon Ammi tace "Yau ni nake ganin jaraba, to ko dai shiryawa za kiyi ki je Zari'an nan ne naga duk kin bi kin damu? haba duk kin bi kin ishe yaro da tambaya a kunnensa baza ki bar sa yaji da mutuwar yaransa har biyu ba, meye hadinsa da Hasinu kuma yanzu da har za a damu don tayi hatsari a hanyar Zari'a, wa gareta a Zaria da ta kama hanyar can din ayi magana ta domin Allah, banda ma dai ma'aikatan asibitin en sharri ne akan wani dalili za su kira Mashir? Meye hadin Maheer da ita yanzu? Dama can wannan yaran ne kuma Allah ya kashesu ba shikenan ba, kilan ma wani mugun abun ta je zata yi a Zari'a Allah ya nuna mata iyakarta, Al-qur'an ban gane ta ba da farko da Usuman ya mika min wayar, kai

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login