Showing 411001 words to 414000 words out of 452169 words

Chapter 138 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

kace daga bakin ƙura aka kwato ta, da kyar in bata rasa ido daya ba a yanda na ga hoton nan, Usuman da yaga abun bai shafesa ba ai kinga yayi wucewarsa bayan ya nuna mana ita a hoto ya tafi ya ci gaba da harkokin gabansa, ni ma dai wllh bai shafeni ba haka Mashir da Mera, ban dai san ko ke da Mariya ya shafeku ba irin wannan sanyi da jikin ku yayi sai ku shirya ku tafi Zari'a" Ammi ta dau wayarta ta hau kiran Mahaifiyar Haseenah, mikewa Maheer yayi ya ajiye ma Mayraah ledan maganin da ya siyo mata, ita dai kallonsa kawai take har ya fita daga parlon, Mama Ladi tace "Atoh dai ya fi maka gwara kaje kayi abinda zai fissheka, tunda uwar taka ita ta kawo tausayi duniya ba sai ta tashi ta tafi asibitin da aka kwantar da Hasinun ba, mu dai Allah ya isa yan biyun mu da tayi mana sanadin mutuwarsu, gashi tun a duniya ta fara ganin karshenta, Shari'ar mu da ita kuwa sai mun hadu a lahira" Aunty Mariya dai ta ma rasa abun cewa a parlon, sosai jikinta yayi sanyi ganin critical situation din da Haseenah take a hoto, abun ba kyan gani, after a while Mayraah ta mike ganin Mama Ladi ta gama cinye abincin gabanta ta tafi ta dau plate din, Mama Ladi tace "Atoh dai, maza fita ki je kiji da mijinki kiyi ta kwantar masa da hankali kina basa baki Allahn da ya basa su shi zai kara basa wasu nan ba da dadewa ba in sha Allah" Mayraah ta kasa daga kanta, tun da Maheer ya fita take son ta bi sa amma ta kasa tashi a parlon sai yanzu da ta samu opportunity sai gashi Mama Ladi ta mata handsfree, tana rike da plate din ta fita daga parlon, bayan ta kai plate din kitchen ta nufi dakin Maheer, zaune ta samesa a dakin yana deleting pictures din su Aryaan da Aymaan wanda Aunty Mariya ta turo masa few days back a wayarsa, daga kai yayi yana kallonta, ta sunkuyar da kai har ta isa kusa da shi har a lkcn idonsa na kanta yace "Have you eaten dear?" Mayraah ta duka gabansa a hankali tace "What should i make for you?" Yace "I just took tea now" Ta daga kai tana kallonsa, murmushi ya sakar mata ya dagota ta zauna gefensa yayi kasa da murya yace "Ko mu tafi gida, naji ma jikinki da zafi, ina maganin da na siyo maki" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Talk to me baby gal" Ta daga kai tana kallonsa yace "Kin sha maganin?" Ta girgiza masa kai, yace "Yana parlorn Ammi har yanzu? Let me get it for you" Saketa yayi ya mike ta bi sa da kallo har ya fita, ta goge hawayen da ya cika idonta, tun safe har zuwa yanzu bata samu sukuni a ranta ba, gani take kamar ta bada nata contribution din wajen rasuwan yaran, sosai ta shiga damuwa wanda ko abinci ta kasa ci, ta rufe fuskarta da pillow hawaye na sauka idonta, she wish zata iya maida hannun agogo baya da bata yi abinda tayi ba, a haka Maheer ya dawo dakin ya sameta, ya ajiye ledan maganin hannunsa da ruwan goran da ya dauko, ya zauna gefenta ya dago ta yace "Mimi" Ta daga kai hawaye na sauka idonta, rungumeta yayi a hankali yace "Kina son ki gan ni cikin damuwa ne Mimi? Bana son wannan kukan da kike yi, erase every thinking that is making you to cry off ur mind, i believe and have faith that hakan da ya faru shine mafi Alkhairi garemu baki daya, so plss let move on, su kuma Allah ya sa masu ceto ne"

Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

131
Abba ya ajiye mug din black tea din hannunsa a hankali ya mike tsaye har a sannan wayarsa na kare a kunnensa, jin the person on the other line na ta cewa "Hello, Hello..." Abba ya koma a hankali ya zauna saman kujera still not responding kuma har a sannan bai cire wayar a kunnensa ba, ji yayi an katse call din ya dinga kallon screen din wayar, a haka Ammi ta dawo parlon ta samesa, ta ajiye watermelon din hannunta ta zauna gefensa tana kallonsa sai kuma ta kalli wayar hannunsa tace "Is anything the matter?" Abba ya juya ya kalleta amma ya kasa cewa komai, Ammi sai da taji gabanta ya fadi, ta dake tace "Wai lafiya Yallabai?? Me ya faru?" Abba ya dauke kansa, after few seconds wayar hannunsa ya fara ringing again, Ammi ta kalli wayar ganin Hajiya Amina, ta daga kai ta kalli Abba, mika mata wayar yayi, da mamaki Ammi dake kallonsa taki amsan wayar tace "I don't understand? for what reason?" Hakan yasa Abba ya daga kiran ya sa handsfree ya ajiye wayar a hankali kan kujera, muryar namiji Ammi taji yayi sallama, sosai taji faduwar gabanta yafi na da, ta daga kai da sauri tana kallon Abba, can tayi karfin halin amsa sallaman da mutumin ke yi, a takaice mutumin yayi introducing kansa sannan ya fara sanar mata me wayar sun samu accident a public transport that was heading to kano from Abuja, and the accident occurred a kusa da Kaduna, Ammi bata san sanda ta mike tsaye da sauri ba cikin kidimewa ta dinga nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, mutumin ya ci gaba da sanar mata an kawota hospital din 44 dake garin kaduna with 2 other passengers that survive the accident for intervention, Ammi bata fasa nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un ba cikin tashin hankali, Shi dai Abba was just short of words, mutumin na katse wayar Ammi ta koma ta zauna tana facing Abba a rikice tace "Yanzu kadunan za mu tafi?" Abba ya sauke ajiyar zuciya, calmly yace "Sai dai gobe, it's already late now" Ammi na girgiza masa kai tace "Har sai gari ya waye yallabai? tunda Usman kan yi driving din dare ba sai ku je kadunan da shi ba yanzu, in yaso sai mu mu taho gobe" Abba dai bai ce komai ba, Ammi tace "Incase ko da bukatar wani abu shi yasa ya dace ku tafi yanzu ba har sai gobe ba" Bata jira cewar Abba ba ta fita daga parlon da sauri, ta tafi dakin Usman, bata samesa ba a dakin nasa ta sauka downstairs, Maheer ya fito daga dakinsa kenan rike da magungunan da ya siyo ma Mayraah jiya zai kai mata ta tasha don she is running temperature, Tsayawa yayi yana kallon Ammi da ta nufosa cikin tashin hankali, sosai ya ji gabansa ya fadi tun bata karosa ba, tana isowa inda yake ta sanar masa abinda ke faruwa, Maheer yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wani asibitin a kaduna?" Ammi tace "Wai forty four mutumin yace, ina Usman?" Dai dai nan Usman ya fito daga kitchen rike da cup din lipton, Ammi ta nufesa shi ma tana gaya masa, he was soo shock and speechless yana kallon Ammi, da kyar yace "Accident kuma?" Ammi tace "Yanzu aka kira Abban ku, shine nace ku tafi Kadunan tunda naga wani lkcn kana tukin dare" Usman sai da ya nemi waje ya zauna tsabar yanda batun ya dakesa, sai ga Abba ya sauko downstairs din, makullin mota kawai Usman ya dauko a dakinsa da Atm card, Maheer da shi ma duk jikinsa yayi sanyi ya mika ma Ammi ledan maganin Mayraah yace "Ammi na Mimi ne, she is running temperature, let me go with them..." Ammi ta amshi maganin tace "Toh Allah ya tsare, da asuba in sha Allah zan taho nima" Maheer bai ce komai ba ya bi bayan Abba da Usman suka fita daga parlon, da ya tuna Ta'aziyyar yan biyu ya kawota Abujan sai yaji hankalinsa ya kara tashi, Ammi ma ta bi su har compound, tana tsaye compound din har suka fita gidan a motar Usman, sai a sannan ta juya ta koma cikin gidan, ta dade zaune parlor duk jikinta yayi la'asar, daga karshe ta mike ta wuce sama har sannan ledan maganin Mayraah na hannunta, dakinta ta nufa ta bude kofar a hankali ta shiga, kwance ta ganta ta rufe har kanta da duvet, Ammi ta zauna gefenta ta sauke duvet din daga fuskarta tana kallonta, a hankali Mayraah ta bude ido tana ganin Ammi ta rike duvet din don ba kaya jikinta, Da kyar ta mike zaune har sannan taki sakin Duvet din a hankali tace "Ammi" Ammi tace "Ga maganinki ki sha Mimi" Ammi na fadin haka ta fiddo magungunan a leda ta balla mata each and every one sannan ta mike mata a hannu, ta mike ta dauko ruwan goran da ta gani gaban mirror ta mika mata Mayraah ta amsa ruwan ta sha maganin gaba daya, Ammi na kallonta tace "Sannu" Komawa Mayraah tayi ta kwanta ta lumshe idonta, Ammi na ta zaune a dakin har ta lura ta koma bacci sannan ta mike ta kashe mata wutan dakin ta koma bangaren ta, har sha biyu Ammi ta kasa bacci, she was soo disturb, har a lkcn kuma bata gaya ma su Mama Ladi abinda ke faruwa ba suna can suna bacci da Aunty Mariya, lokaci lokaci Ammi ke kiran Maheer taji ko sun kusa, har daga karshe wajen karfe dayan dare yace mata sun isa kadunan amma basu karasa hospital din ba. ko da su Abba suka isa asibitin ba a bari sun shiga gun Hajiya Amina dake Emergency har a sannan ba saboda she was in a state of coma, haka suka yi ta zama a hospital din har asuba, karfe bakwai saura wani likita ya taho inda su Abba suke zaune yana kallon Abba yace "Kai ne mai gidan nata ko?" Abba yace "Haka ne" Likitan yace "Ohk ka sameni office" Abba ya bi sa har zuwa office dinsa, likitan na kallon Abba yace "The accident left her with a critical traumatic brain injury, no doubt a bugu sosai a kanta, apart from that ko kwarzane bata yi ba, so sai tayi regaining consciousness fully za mu ji ko da wani waje dake mata ciwo, wa enda aka kawosu tare ma duk sun rasu tun a daren jiya, hopefully za ayi mata CT scan yanzu don ganin state din da brain dinta ke ciki domin mu san next move da za mu dauka" Abba da duk jikinsa yayi sanyi yace "Amma ta farfado yanzu?" Likitan yace "Yeah, but not fully gaskiya, tana da yara ne?" Abba yace "Tana da" Likitan na gyada kai yace "Eeman??" Abba yace "Eh, she is our daughter" Likitan yace "Yauwa sunan yan mata biyu dai ta kira sai namiji, so na rike Eeman saboda sunan daughter na kenan, if possible a taho mata da yaran nata ko zuwa anjima, that might help too" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Amma zan iya shiga wajenta yanzu Doctor?" Likitan ya mike yace "Mu je, duk da dai yanzu za a shiga da ita inda za ayi mata CT scan din" Mikewa Abba yayi ya bi bayan likitan suka fita har zuwa inda aka kwantar da Hajiya Amina, har a sannan akwai likitoci biyu a ciki doing one or two things, Abba ya karasa kan gadon yana kallonta, kamar yanda likitan ya fada babu ko kwarzane a jikinta da zai baka tabbacin tayi accident, ya duka ya kira sunanta cikin calmness, tana son bude ido amma da alama it's so difficult for her to do so, kana ganinta kasan she is in so much pain, ta rike hannun Abba gam, da kyar ta iya bude baki tace "Mahmud, my daughters... they lost der father at a very young age, they have no one apart from me, i am all they have..." Abba yayi karfin halin cewa "Be strong Amina, in sha Allah zaki samu lafiya, kiyi ta addu'a" Muryarta na rawa tace "Sure, i will be strong for them, i will act strong for the girls" Likitan yayi kasa da murya yana kallon Abba yace "She is stressing her self, ka ɗan je waje Alhaji" Ba musu Abba ya juya ya fita daga ward din, Abba na fita ya zauna nan walkway din ya tallabi chin dinsa, sosai ya shiga damuwa da halin da ya ganta a ciki, yan biyunta da take ta nanatawa ne suka kara tsaya masa a rai, tun bayan rasuwan mahaifin yan biyun a yanda ta basa labari yan uwansa suka amshe duk dukiyarsa bayan sun cire mata nata tumunin takaban wai za su rike gadon yan biyun har sai sun mallaki hankalinsu, duk wani fadi tashi ita ke yi ma yaran nata biyu da taimakon kanwar mahaifiyarta don duk iyayenta sun rasu kuma ita kadai ta rayu cikin 'ya ya hudu da iyayenta suka haifa a duniya don duk sauran SS ne da girmansu kuma suke rasuwa, ita ce aka haifa a AS, ana haka ita ma kanwar mahaifiyar nata ta rasu few years ago, shkkn ta dawo babu me taimakonta amma da yake tana da zuciyar nema tayi ta fadi tashi domin yan biyunta su samu ingantaccen rayuwa, duk da rashin adalcin dangin marigayin mijinta bata hana yaranta zuwa inda suke ba, dadewa ne dai baza su yi ba don tasan baza a kulan mata da su yanda ya kamata ba tunda ba wani sonta suke ba hakan kuma ya shafi yaran, ko sun je bai fi suyi kwana uku zuwa hudu su dawo ba, in suka tashi dawowa kuma ko tsinke basa hado su da shi amma duk hakan bai dameta ba bata kuma fasa turasu katsina su kai masu ziyara ba don su din ne dai dolensu saboda halin rayuwa, sam bata nisanta su da dangin ubansu ba.... Abba ya dafe kansa yana tunanin ta yanda har ya hadu da Hajiya Amina ya aureta, basu taɓa sanin juna in person ba, wani abokinsa ne yayi connecting dinsa da ita, a lkcn tana yawan kai masu kayan siyarwa a organization din da abokin nasa yake aiki, saboda kamewarta yasa abokin nasa har ya hada sa da ita, at first Hajiya Amina tayi declining ta nuna masa aure baya gabanta yanzu sbda tana son kula da yan biyunta dake boarding school, da yake Allah ya kaddara za su yi auren sai gashi sun yi just a week da aka hadasa da ita, ire iren tunanin nan ne suka yi occupying mind din Abba, a watannin da yayi tare da Hajiya Amina bazai taɓa cewa ga wani laifi da tayi masa ba, Hajiya Amina mace ce da ko wani namiji zai yi fatan mallaka a matsayin matarsa, ta ko ina ta hadu, kuma har yau bai ga flaws dinta ba, ko da kayi mata abinda bata ji dadi ba baza ka taɓa gani a fuskarta ba, a ko da yaushe zaka ganta da fara'a, har mamakinta yake, hakan kuma na tuna masa irin zaman da yayi da Ammi na shekara da shekaru kafin kwatsam abubuwa su sauya lkci daya, kawai banbancin Ammi da Hajiya Amina shine in kayi mata abinda bai mata ba zata nuna kayi mata, Abba na ta zaune a kujeran dake walkway din tunani iri iri na yawo a ransa at the same time yana ma Hajiya Amina addu'an Allah ya tashi kafadunta cikin gaggawa, gani yake kamar likitocin are too slow akan aikinsu, yaji gwara kawai ya fita da ita kasar waje ko da da last penny dinsa ne in dai Hajiya Amina zata samu lafiya he won't mind, yana cikin wannan tunanin likitan da ya kai sa office dinsa ya fito, Abba ya mike da sauri yana kallonsa kamar yanda likitan ke kallonsa shi ma, karasawa gun likitan yayi kafin yace komai likitan yace "We tried our best Sir, but we lost her, Allah ya mata rasuwa...." Yana fadin haka ya bar Abba tsaye a wajen ya wuce, it seems Abba ya kasa assimilating abinda likitan yace masa at once, yana ta tsaye inda likitan ya bar sa ko kiftawa baya yi at the same time he was trying to digest what the Dr just said to him, sai ga sauran likitocin sun fito su ma, Abba ya bi su da ido, daya a cikinsu ya tsaya yana kallon Abba cikin kwantar da murya yace "Kayi hakuri Alhaji, Allah ya gafarta mata, Allah ya baku hakurin rashi" Yana fadin haka ya juya ya bi bayan sauran Drs din da suka yi gaba, sai a sannan Abba ya daga kafa yana tafiya a hankali ya shiga cikin Emergency ward din, ya dinga kallon gadon da take kwance sun rufa mata zanin gado, cike da karfin hali Abba ya karasa don har wani dishi dishi yake gani, a haka dai ya isa gadon, ya bude zanin gadon da aka rufeta da shi yana kallon fuskar ta, Abba ya duka kusa da ita da kyar yayi gathering duk sauran courage dinsa with shaky voice yace "Allah ya ji ƙan ki Amina, Allah ya maki rahama, Allah ya gafarta maki, Annabi ya san da zuwan ki, Allah....." Kasa ci gaba Abba yayi bayan ya ji hawaye na sauka idonsa... Mutuwar Hajiya Amina, mutuwa ce da ta girgiza duk wanda yasan ta ya kuma yi mu'amala da ita, it was soo hard to believe she was gone for ever, A nan Kaduna aka yi jana'izarta aka kai ta makwancinta, duk dauriya da dakiya irin ta Abba ya kasa dena xubda hawaye, Daga Maheer har Usman duk babu wanda ke da kuzari da nutsuwar driving most especially Usman wanda ba karamin abu bane zai sa shi zubda hawaye, da ya tuna su Eeman da yanda za su dauki mutuwar uwarsu wanda duk duniya basu da sama da ita sai yaji hawaye na bin idonsa ashe sign din mutuwar uwarsu suka ji duk suke rashin lafiya, dole sai train suka bi gaba daya zuwa Abuja... Kaf dangin marigayin mijin Hajiya Amina sun yi matukar girgiza da mutuwar ta don baza su ce ga abinda ta taba masu ba, sun santa a mace me hakuri da

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login