Showing 417001 words to 420000 words out of 452169 words
Chapter 140 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar
auren bane ba fa, from the look of things so suke in cire hannu a lamarin yaran gaba daya, they were emphasizing on abinda ya hada ya raba, ko makarantar da yake cewa zai nema masu ba haka bane, from my observation gadon da uwarsu ta bari suke hari, they were even asking me of her Atm cards" Ammi ta kasa rufe baki don mamaki tana kallon Abba, can tace "To yan uwanta fa?" Abba yace "Ita kadai ce ai, duk siblings dinta died of sickle cell, her parent are late, sai distance relatives" Ammi ta kasa cewa komai, after few seconds Abba yace "Yara dai nasu ne, we have no say akan su, kawai iyaka namu mu bi su da addu'a" Abba na kaiwa nan ya mike ya shiga bedroom dinsa. Ammi na zaune parlonta tare da Bilkisu dake ta mata hira Usman ya shigo parlon da sallama, mikewa Bilkisu tayi ta fita daga parlon, Usman ya zauna yana kallon Ammi, sai kuma yayi kasa da kai yace "Ammi dama za a zo gaishe ki ne gobe" Ammi dake kallonsa tace "Wa zai zo gaisheni kuma?" Usman ya daga kai yace "Sunan ta Maryam" Ammi ta kasa daina kallonsa, a hankali tace "Toh Allah ya kai mu" Yace "Ameen" Mikewa yayi, Ammi tace "Amma..." Usman ya tsaya yana kallonta, a hankali tace "Eeman din kuma fa Usman?" Usman ya ɗan yi murmushi yace "Aa, ai ba wannan zancen kuma Ammi, tunda kika nuna a'a tun a lkcn na bar maganar" Ammi ta girgiza kai tace "Aa Usman, baza ka bar maganar ba yanzu...." Zaunawa Usman yayi yace "Kiyi hakuri Ammi, na bar maganar nan tuntuni, Eeman da Ihsaan a matsayin wa nake garesu yanzu" Ammi was speechless, after a while Usman ya mike yace "Zan je in ci abinci" Da ido Ammi ta bi sa har ya fita daga parlon, Yana dakinsa Ammi ta bi sa, tana daga tsaye bakin kofa tace "Amma zan fita gobe Usman, sai dai wani lkcn ka kawota" Usman dake kallonta yace "To Allah ya kai mu"
Wajen karfe biyun dare Maheer ya farka bai ga Mayraah kusa da shi ba, mikewa zaune yayi after a while don at first yayi tunanin tana bandaki ne, ya sauka daga kan gadon ya fita, dakinta ya nufa yana bude kofar ya ganta zaune kan darduma ta hade kanta da gwiwa tana jin an bude kofa ta daga kai da sauri tana goge idonta, ya karasa kusa da ita yana mata kallon mamaki ya duka gabanta yace "Mimi" Bata yarda sun hada ido ba tace "Sallah nake ne" Cike da damuwa yace "Why are you crying Mimi? Did i offend you in anyway?" Daga kai tayi ta kallesa nan da nan hawaye ya cika idonta, sosai hankalinsa ya tashi ya dagota ya zaunar da ita gefen gado ya zauna gefenta cike da damuwa yace "Don Allah ki gaya min me ya faru wife?" Ta rufe fuskarta a shoulder dinsa tana shesshekan kuka, sosai ta rikita sa ya dinga lallashinta, da kyar ya samu ta daina kukan yana rungume da ita, bayan wani lkci yayi kasa da murya yace "Tell me what the problem is Mimi?" Ta lumshe idonta tana jin wani sabon kukan na taho mata, a hankali yace "Wife" Muryarta na rawa tace "I will write it down tomorrow" Shiru Maheer yayi, yana patting bayanta a hankali yace "Why not now wife?" Ta girgiza masa kai tace "I will tomorrow" Ɗagata yayi suka fita daga dakin nata ya koma nasa da ita, tana rungume jikinsa bacci ya ɗauketa, ya dinga shafa bayanta yana shakan daddadan kamshin da gashinta ke yi ya lumshe ido, a haka shima bacci ya daukesa.... Da asuba Maheer na dawowa masallaci yaga Mayraah bata dakinsa, ya dinga kallon takardan da ta ajiye masa kan gado, ya karasa ya dau takardan ya warware yana karanta content din, zaunawa yayi gefen gado bayan ya gama karanta abinda takardan ya kunsa, after few minutes ya sauke ajiyar zuciya ya mike ya linke takardan ya ajiye, yana tafiya slowly ya fita daga dakin nasa ya tafi nata, yana bude kofar ya ganta zaune kan darduma, ita dai bata daga kai ba har ya karasa inda take ya duka gabanta yana kallonta.
Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788
133
Mayraah ta bude mota ta sauka bayan Maheer yayi parking, ta juya tana kallonsa tace "Ko dai kawai ka bar shi Dear" Yace "No, let me get it in dawo yanzu, Flight din ai na karfe shidda ne so there is still time" Mayraah tace "Just an hour and a half fa" Yace "Don't worry, am not taking long wife" a hankali tace "Ohk dear, Allah ya tsare" Yace "Ameen my love" Gate ta nufa ta shiga gidan shi kuma yayi reverse, tun da ta bude kofar parlor ta shiga take kallon sa, yana daga kai tayi masa murmushi ta karasa cikin parlon ta zauna tace "Ina yini yaya?" Yace "Lafiya lau, how are you doing?" Tace "Alhamdulillah, ya su Mami?" Yace "They are fine, ina Maheer din?" Tace "Yaje ya dawo yanzu, yaushe ku ka zo yaya?" Yace "Not too long, ke mu ke jira ai" Mama Ladi ce ta sauko parlon daga sama, ta karaso tsakiyar parlon tana washe baki hannunta rike da ledan gyada me gishiri tace "Sannu da zuwa Mendi, yanzu Hajiya Ramatu ke ce min ai tare ku ka zo" ɗaga kai MD yayi yana kallonta, Mayraah dai ta sunkuyar da kanta tana murmushi, Mama Ladi ta zauna kujeran dake kallon wanda yake zaune tace "Ashe wai kai zaka raka su kasar wajen" MD yace "Ina wuni Mama" Mama Ladi tace "Lafiya lau Mendi, ya aiki?" Ya ɗan yi murmushi yace "Alhamdulillah" Mama Ladi tace "To madallah" Mayraah ta gaida Mama Ladi, Mama Ladi tace "Lafiya lau, ina mijin naki?" Mama Ladi bata jira cewar Mayraah ba tana kallon sama ta kwalo ma Ihsaan kira, ba a dau lokaci ba sai ga Eemaan ta sauko downstairs ta karaso kusa da Mama Ladi tace "Gani Mama" Mayraah dai kallon Eeman kawai take ganin yanda ainahin haskenta ya dawo, skin dinta sai glowing yake, kwanansu goma kenan da barin katsina amma har sun dawo hayyacin su, Mama Ladi ta daga kai tana kallon Eemaan tace "Kece Ihsaan ko neman magana..." Eeman na murmushi tace "Aa Mama tana can parlon Ammi ne shi sa na zo" Mama Ladi ta dauke kai tana cin gyadar hannunta tace "To ba ke na kira ba, ki tafi kice mata Mama Ladi na kiranta" Eemaan da har sannan fara'a ke kwance fuskarta ta kalli MD dake kallonta ta dan risina tace "Ina yini?" Ya gyada mata kai yace "Lafiya lau" Kallon Mayraah tayi ita ma ta gaishe ta, Mayraah ta amsa mata da murmushi fuskarta, Eemaan ta juya ta koma sama, Mama Ladi na kallon MD tace "Bari yanzu za a zo a kawo maka ruwa Mendi" MD ya daga kai yana kallonta yace "Mama sunana fa Aliyu" Mayraah ta kyalkyale da dariyar da bata yi niyya ba, Mama Ladi tace "Ai nasan sunan ka Aliyu, ba su Hajiya Ramatu naji suna kiran ka Mendi ba, sun ma fi kiran ka Mendin ai akan Aliyu" MD ya jinginar da kansa da kujera after letting out a sigh, bai sake ce mata komai ba, Mama Ladi na mika masa ledar gyadar hannunta tace "Ko zaka ci gyada me gishiri, Halima ce ta bani nima" MD ya girgiza mata kai yace "Alhmdlh" Mayraah dai ta kasa daina dariya, tana son tafiya sama ta gaida Ammi da kakarta da Aunty Halima da ke can bangaren Ammi amma saboda tana son ta ga yanda za a kwashe idan Ihsaan ta sakko ya sa taki tashi daga parlon, Ba a wani dau lokaci ba sai ga Ihsaan ta sauko downstairs ta karaso kusa da Mama Ladi, Kallon Mayraah dake kallonta tayi tace "Ina yini Aunty" Mayraah ta amsa mata tana murmushi, Ihsaan ta juya ta kalli MD that was looking at her a bit confused, a takaice tace masa "Ina yini" Mama Ladi dai sai washe baki take tana kallon MD kasa kasa tace "Naga kamar ka rude ko Mendi, to yan biyu ne ai" MD yayi murmushi yace "Ai nayi tunanin haka..." Mama Ladi ta kalli Ihsaan tana washe baki ba tace "Tafi ki dauko masa lemo da ruwa a kitchen Ihsani, kanin uban Mera ne" Juyawa Ihsaan tayi ta nufi kitchen, MD da ya bi ta da ido sai kuma ya maido da dubansa kan Mama Ladi yace "Aa Mama, na sha ruwa kafin in shigo, dama Mayraah mu ke jira yanzu za mu tafi airport" Ihsaan ta tsaya jin abinda yace amma bata juyo ba, Mayraah dai sai murmushi take tana kallon ikon Allah, Mama Ladi tace "Banda abun ka ko kadan ne ka sha mana Mendi, maza tafi ki dauko ruwan Ihsani" MD ya kalli Ihsaan sai kuma ya kalli Mama Ladi yace "Ai da ta farkon ma kika ce ta kawo min ruwan, naga tafi fara'a" Ihsaan ta juya ta kalli MD dake kallonta, Mama Ladi ta kyalkyale da dariya har da kyakyatawa tace "Toh banda abun ka kai din ma ai ba fara'ar bace da kai Mendi, shi sa nace a kira min ita ta baka ruwan..." MD ya ɗan buda ido jin abinda Mama Ladi tace, Ihsaan dai tuni ta tafi ta dauko ruwan da drink, sai gata ta dawo parlon ta durkusa gabansa ta ajiye, shi dai kallonta kawai yake ganin ko alamar fara'a babu a fuskarta har a lkcn, Mama Ladi dake kallonsu kasa kasa ta gefen ido sai wani murmushi take tana cin gyadar hannunta, ita kuwa Mayraah Mama Ladi ce ke bata dariya ganin yanda take wani kallonsu kasa kasa tana murmushi tana taunar gyada kamar wata boss, Tsabar dariya sai da Mayraah ta sauko daga kan kujera ta zauna a carpet, Mama Ladi ta kalleta ta wani hade rai tace "Ji mahaukaciyar banza" Mikewa Ihsaan tayi zata bar wajen shi dai MD bin ta kawai yake da ido, da sauri Mama Ladi tace "Ke dawo ki zuba masa a kopi, haka ake yi a Katsinan naku zaki wani dungurar masa da lemo a gabansa ki tafi" Mikewa Mayraah tayi tana dariya har sannan tayi hanyar stairs da sauri ta bar masu parlon ganin wani shegen kallo da Mama Ladi ta bi ta da shi, Ihsaan ta koma ta duka gabansa ta zuba masa drink a glass cup sannan ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake, mikewa tayi ta bar parlon tayi hanyar stairs, Mama Ladi kuwa kamar bakinta zai yage tsabar murmushi, sai da taga Ihsaan ta haura sama ta maido da dubanta kan MD tace "Sam bata shiga sabgar da ba tata ba, ba kuma ruwanta da hayagaga kamar er uwarta da kaga tana ta fara'a ba kwantral, sannan ka ga girman gidan nan wallahi kafin mu tashi bacci duk ta gyara ko ina, azababben tsafta gareta har ya wuce misali wllh, yanzu mai aikin gidan nan ma bata da wani amfani don duk wani aikin gidan Ihsani ce ke yi, er uwarta da kaga tana ta fara'a kamar wawiya ba abinda ta iya sai bacci da son jiki, sai ta kai karfe goma sha daya na safe bata tashi ba Al-qur'an, don ma Ammi na taka mata birki, kaga yanda ta wanke kofin nan kafin ta kawo maka to da Imani ce haka zata dauko kopin tana fara'a ta kawo maka" MD dake ta sauraronta murmushi kawai yake bai ce komai ba, har sai da tayi shiru sannan ya daga kai yace "Hutu suka zo kenan" Shiru Mama Ladi tayi, sai kuma ta fara matsar kwalla a hankali tace "Wani hutu Mendi? 'ya yan Marigayiyar matar Mamuda ne fa, marayu ne ba uwa ba uba a duniya sai tsinannun dangin ubansu yan katsina da suka handame duk gadon su, a takaice dai yanzu gatansu a duniya Ammi da Mamuda sai ni Ladi, don uwarsu mutuniyar kirki ce wllhi, duk in zamu hadu da ita sai ta ban dubu ashirin, ko a ranan da zata rasu dubu ashirin ta bani muna zaune da ita a parlor kafin a kirata ace yaran ba lafiya ta kama hanya ashe ajali ke kiranta..." Shiru Mama Ladi tayi tana matsar kwalla, kasa cewa komai MD yayi da farko don sosai jikinsa yayi sanyi, bayan few seconds a hankali yace "Allah Ubangiji ya gafarta ma iyayen su" Cikin rawan murya Mama Ladi tace "Ameen ya Allah, kuma a haka tsinannun dangin uban suka maka Mamuda a kotu wai sai ya fita sabgar yaran, duk hankalinsu ya tashi sun zata Mamuda zai kai su kotu a kan gadon yaran da suka handame shine suka riga makasa kotu, ai ko na ba Mamuda shawara bayan Usman yayi hayan tijararrun lauyoyi a tozarta yan iskan a idon duniya sannan su fito da gadon marayun duk inda ma suka kai" MD dake ta sauraron Mama Ladi yace "Ikon Allah" Mama Ladi tace "Wallahi kuwa, shekaranjiya aka kawo ma Mamuda sammaci, ni dai na kara tsorata da lamarin katsinawa wllh, ni ban ma taɓa bin hanyar garin ba ko da wasa" After few seconds MD yace "Ina da aboki lauya, a kasar waje yake aiki amma yana Nigeria yanzu haka, zan masa magana akan case din in sha Allah" Mama Ladi ta saki kabbara tace "Allah yayi maka albarka Mendi, kuma ana gana Shari'a kyau dama a aurar da marayun kawai su je su karasa karatu a gidan mazajensu" MD dake kallonta yace "Ohk, dama da maganar auren nasu kenan a kasa?" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Aa ba haka zaka ce ba, ni ce dai nake ga hakan kadai ne rufin asirinsu tunda mata ne, sannan aure ne kadai zai kubutar da su daga tuggun dangin uban nasu, kaga ita wannan me washe baki kullum cikin fara'a dama Usuman ya kyasa ta tun da dadewa, yanzu ma bini bini zaka gan su tare a parlo tana zuba masa turanci, ita kuwa wannan kamilar da ake kira Ihsani so nake ace ita ma ta samu me tsafta da kamun kai irinta, to kaga ba ko ina suke zuwa ba tunda ance makarantar har an gama daukan dalibai sai wani shekara kuma, amma dai akwai wani ɗan aminiyar Ammi naga in dai ya zo sai yayi ta kallonta kuma shi ma yana da hankali da nutsuwa gaskiya..." Duk da karya kawai Mama Ladi ta lafta haka tayi keeping serious face kamar gaske, MD yayi shiru bai ce komai ba, Mama Ladi dai sai kallonsa take ta gefen ido.
Washegari karfe tara na safe jirgin su Mayraah yayi landing a Us after almost 14 hours of leaving Nigeria, Dad dinta har ya iso airport yana jiran saukan jirginsu, bayan ya ba MD hannu sun gaisa yayi ma Umman sa Side Hug yana murmushi yana kallonta a hankali yace "I miss you so much Mom" Hajiya Ramatu ta hade rai tace "Meye haka kai?" Aunty Halima dake dariya tace "Za ka fara ma Umma shagwaba ga dai Daughter dinka tana kallon ka" Sai a sannan Abdallah ya juya ya kalli Mayraah, ɗan murmushi Mayraah tayi ta gaishesa, ya sake Umman sa ya dawo gun Mayraah, giving her a side hug too yana kallonta da murmushi fuskarsa yace "How are you daughter?" A hankali tace "I am fine" A haka duk suka shiga motar sa yayi driving dinsu zuwa gidansa dake Los Angeles yana hira da MD dake front seat a zaune, Mayraah ta dinga kallon Mansion din Dad din nata, yayi leading din su har ciki, Mayraah was soo happy to see her Mom, ko lura da Ceo dake dakin bata yi ba ta tafi da sauri ta rungume Mom dinta dake zaune, Aaria was so surprise and at the same time very happy to see her daughter, don ba ace mata har da ita za a zo Us ba, Mayraah ta ɗan buda ido ganin Ceo dake zaune a dakin tana kallonta, a hankali ta zamo kasa ta gaisheta tana murmushi, Ceo tace "Sannu Mary Ann..." Mayraah taji kunya sosai don har ta mance rabon ta gaisheta ko ta WhatsApp ko ta phone call, sunkuyar da kanta tayi, Aaria dai sai kallonta take tana murmushi, ta dauko one of the twin dake kwance kan gado ta mika mata, Mayraah ta amshesa tana kallon babyn da yau suka cika wata daya a duniya, sosai taga yaran ke kama da ita, dai dai nan Aunty Halima ta shigo dakin cike da murna tana congratulating din Aaria, Aaria ta mike ta rungumeta da fara'a tana welcoming dinta at the same time tana tambayarta ina Umma, Aunty Halima tace "Umma sallah zata yi tukunna tana downstairs..." Aunty Halima ta gaida Ceo da fara'a sannan ta karasa ta dau other twin din dake kwance. Kwana biyu kacal Hajiya Ramatu tayi a gidan only son din nata a Us, babu yanda Aaria bata yi da ita ta kara ko da wani kwana biyun ne ba amma taki, haka nan ita da MD suka koma Nigeria leaving Aunty Halima and Mayraah behind, 24/7 zaka tarar da Mayraah makale da yan kannen nata guda biyu tana renon su, sosai take jin yaran har cikin ranta, gashi sam basu da rigima, Daya anyi naming dinsa After Abba (Mahmud) Dayan kuma (Alhaji Kabir Saminu) ana kiransu da Shuraim da Sudais, akwati biyu Abba yayi ma babies din na kaya, Ammi ma tayi masu siyayya sosai, bayan tafiyar Hajiya Ramatu da MD da kwana biyu Ceo ta shirya ita ma zata tafi Canada, Gaba daya Aaria ta dawo bata da walwala ganin yayarta zata tafi duk da watan ta daya har da kwana biyar kenan a Us, Mayraah ta bude kofar dakin da Ceo take ciki a hankali ta shiga, Ceo tayi hanging call da take yi ta ajiye wayar tana kallon Mayraah tace "Come in Mary Ann" Mayraah ta karasa cikin dakin ta zauna kan kujera, Ceo na kallonta tace "Ya mai gidan naki?" Mayraah na wasa da fingers dinta tace "Yana nan lafiya" After few seconds silence Ceo