Showing 423001 words to 426000 words out of 452169 words

Chapter 142 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

ruwanki" Dariya Zainab tayi tana kallon Eeman.... Har Mayraah ta fara bacci Zainab ta tasheta jin wayarta na ta vibrating a jaka, Mayraah ta mike zaune da kyar ta bude jakar ta ciro wayar tana kallon Screen din, ganin Maheer ne ta daga ta kai kunne daga daya bangaren yace "Baki kusa da wayar ne baby gal?" Mayraah tace "Are you back?" Yace "Yeah ina kofar gida ku fito mu tafi" Mayraah tayi kasa da murya tace "Ka shigo kaga baby mana" Yace "Ai na ma Dr Khalil barka ta waya Mimi, kawai ku fito mu tafi it's late" Tace "Ohk" Katse wayar tayi ta mayar jikin jaka, Zainab tace "Kar dai tafiya za ku yi?" Mayraah ta kalli agogon dake dakin tana ɗan murmushi tace "Ai mun dade Mom twins" Har parlor Zainab ta rako Mayraah da Eeman, da kyar Mayraah ke tafi don duk jikinta is so weak, ganin babu kowa a parlon sai cousin sis din Zainab ta ji dadin hakan a ranta, a haka suka yi sallama Hafsat nayi mata fatan samun lafiya, Mayraah tace "Ina Ihsaan din?" Hafsat tace "Ina jin tana waje" Mayraah tace "Dr ya fita ne" Hafsat tace "Yes, he left with the other Dr not too long" Mayraah ta gyada mata kai tayi mata sai da safe ta fita daga parlon, Eeman dake rike da handbag dinta tana biye da ita a baya. A bayan motar Maheer suka tadda Ihsaan, Eeman ta shiga bayan motar, Mayraah dai bata ce mata komai ba duk da tayi mamakin ganinta amma maganar taji wahala yake mata, ta shiga front seat tana kallon Maheer yayi reverse suka bar layin. Har suka isa gida Mayraah bacci take, tun a hanya Maheer ke juyawa ya kalleta lkci lkci don it's so unusual of her, har dai suka iso gida, Su Eeman suka sauka bude motar suka sauka bayan Maheer ya mika ma Ihsaan makullin kofar parlor, suna kulle motar suka nufi entrance din gidan a tare, Maheer ya sauko daga driver seat ya zagayo ya bude door din inda Mayraah take ya dafa Forehead dinta a hankali yace "Wife..." Ta bude ido da sauri, sai kuma ta gyara zama tana kalle kalle tace "Yaushe muka iso gida" Yace "Kina ta bacci a hanya" Tayi murmushi, a hankali tace "I am so exhausted dear" Yace "Wani aiki kika yi yau har kika zama exhausted Baby?" Bata ce masa komai ba ta sauko daga cikin motar, ji tayi wani jiri ya debeta, Maheer yayi saurin rikota yana kallonta yace "Are you okay?" Kasa cewa komai tayi, ya rungumota jikinsa yace "Your body is warm" Da kyar tace "Na gaji ne, i need to rest" Maheer wish su kadai ne a gidan da kawai daukar abarsa zai yi ya tafi cikin gida da ita, ya dafa shoulder dinta making her rest on him suka nufi entrance din gidan yana kallonta har suka isa parlor, basu tadda su Ihsaan a parlon ba haka ya sa ta dauketa ta zaro ido murya can kasa tace "Meye haka yaya, we are not alone fa" Bai saurareta ba ya nufi Masters Bedroom da ita, ya direta saman gado ta mike ya kara hasken dakin sannan ya dawo kan gadon ya zauna yana kallonta, lumshe ido tayi tace "Bacci zan yi" Shi dai bai ce komai ba, after some minutes ya kai hannunsa goshinta, firgit ta bude ido wai har ta fara bacci, ya sakar mata murmushi kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "Me za ki ci?" Ta girgiza masa kai da sauri tace "I am full" Yana shafa cikinta yace "No dear, ko in kawo maki apple din ki?" Ta gyada masa kai, yace "Right away baby gal" Hijab dinta ya fara kokarin cire mata yana cewa "Cire hijab din so that you will be comfortable" Da sauri ta rike tace "Noo, ina jin sanyi" Yace "Ga duvet baby" Ta girgiza masa kai tace "Na fi son hijab din ni dai" Yace "Ohk my love" Mikewa yayi ya nufi kofa ya fita daga dakin ya tafi kitchen, Bayan ya gama wanke mata apples din ya ajiye bowl din kan center table, ya tafi dakin da su Eeman suke yayi knocking, Eeman ce ta bude kofar yace "Kun ci abinci kuwa?" Eeman tace "Eh mun ci yaya" Maheer yace "Ohk then, sai da safe" Juyawa yayi ya bar wajen Eeman ta kulle kofar, bangaren da Mayraah take ya tafi bayan ya dau mata apples din, ajiye bowl din yayi kan beside drawer yana kallonta ganin yanda ta takure waje daya alamar tana jin sanyi amma taki lulluba da duvet din, jawo duvet din yayi trying to cover her with it ta bude ido da sauri yace "You are shivering baby" Bata ce komai ba ya lullubeta da duvet din yace "Ga apple din na kawo maki" Ta girgiza masa kai tace "Sai gobe zan ci" Bai ce mata komai ba ta lumshe ido, ya fi minti goma zaune gefen gadon yana kallonta, daga karshe ya mike ya maida apples din kitchen ya dawo shiga wanka, bayan ya fito ya saka Pajamas dinsa ya kashe wutan dakin ya kwanta a gefenta, har ya fara bacci wajen karfe daya yaji tana tashinsa, mikewa zaune yayi ya kunna wuta yana kallonta yace "You need something dear?" A hankali tace "Ina son zan ci apple din" Yace "Ohk My love" Sauka yayi daga kan gadon ya fita daga dakin, ba a dau lokaci ba sai gashi ya dawo da bowl din apples da ya wanke, ya karaso kusa da ita ya zauna ta dau apple daya ya ajiye sauran kan beside drawer, ta jinginar da kanta kan shoulders dinsa ta fara cin apple din a hankali, shi dai kallonta kawai yake ko kiftawan kirki bai yi, ko rabin apple din bata ci ba ta mika masa, ya karba yace "Ya isheki ne?" Kasa ce masa komai tayi, ya dinga kallonta yace "You want to throw up?" Da sauri ta gyada masa kai, ya dagata suka tafi bandaki, sosai Maheer ya tausaya mata bayan tayi aman, ya wanke mata fuska ya dawo dakin da ita yana kallonta, she was so weak and worn out, kuka take yi a hankali ya rungumeta jikinsa yana patting bayanta slowly, after a while ya kai bakinsa kunnenta a hankali yace "Shi ne kika ki jira mu je Honeymoon din da nace za mu je wife?" Mayraah ta daga idanunta ta kallesa, murmushi ya sakar mata, ta sauke idonta bata ce masa komai ba, a haka bacci ya dauke. Washegari tun da sassafe Ammi ta dinga kiran Maheer a maido mata da su Eeman gida, yana son ce mata Mayraah bata da lafiya ko za ta barsu su ɗan kwana biyu amma ya kasa ce mata hakan, daga karshe babu yanda ya iya haka ya sa yan biyun su shirya Mayraah na bacci ya tafi dropping dinsu a gida, tun daga wannan rana Mayraah tayi sallama da lafiya, she gradually became so sick, babu abinda take iya ci, ko ruwa ne ta sha sai amai, gaba daya taji duniyar ta mata zafi tsabar yanda take jin jiki, hatta Maheer din bata son gani a kusa da ita, lkci daya duk ta rame ta fita hayyacinta, gashi shi dai Maheer har sannan bai fada ma su Ammi bata da lafiya ba, duk sanda suka yi waya in ta tambayi Mayraah sai yace tana nan lafiya, 3 hours kawai yake yi a hospital ya dawo gida saboda ita, ranan wani friday yana zaune parlor kiran Mama Ladi ya shigo wayar sa, ya daga ya gaisheta, ko amsawa bata yi ba tace "Yanzu dai abinda kai da matarka Mera ke nufi da mu na kira in ji, Yau sati nawa rabonku da gidan nan, ko dai kun bar garin ne bamu sani ba, sannan ga bikin marayun yaran nan ana ta shirye shirye ku ko a jikinku, ko don kaga uwarka na kawaici ka zata hakan na mata dadi ne, in ita Meran bata da hankali kai ma hankalin ka rasa ne? yara biyu duk ku fita harkar uwarku ko ɗar baku ji a ranku ba, to wallahi ku ji tsoron Allah, yau sati nawa rabon ita Meran ta kirata ta gaisheta sai dai kai ka kira, ni dai nace wllhi bazan yi shiru ba sai na amayar da abinda ke rai na, wannan ai walakanci ne, ko dai barin Habujan ku ka yi bamu sani ba" Maheer dake ta sauraron Mama Ladi, ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace "Mama Mayraah bata da lafiya ne fa" Mama Ladi tace "Innalillahi, Bata da lafiya kuma? Tun yaushe?" A hankali yace "Tun su Eeman na nan" Mama Ladi ta rafka salati ta katse wayar ta tafi dakin Ammi tace "Kin ji wai Mera bata da lafiya yau kusan sati hudu, da ban kira na masa soso da sabulu ba dama bazai gaya mana" Ammi da ta juya tana kallon Mama Ladi tace "Bata da lafiya? me ya sameta" Mama Ladi ta zauna kan kujera cikin jimami tace "Ni dai fargabana Allah ya sa ba guban da taci bane ya fara mata illa tunda har anyi shekara daya yanzu, to in ba guban ba wani rashin lafiyar arziki ne yau har sati hudu gantalallen yayi shiru yaki gaya mana?" Ammi ta dau wayarta ta zauna gefen gado ta kira Maheer, yana fara ring ya daga, Ammi tace "Maheer me ya samu Mayraah?" Maheer yayi kasa da murya yace "She is sick for almost a month today" Ammi tace "Why didn't you tell us?" Yayi shiru bai ce komai ba, Ammi ta katse wayarta, Mama Ladi tace "Sam Maheer bai da wayo wallahi, yarinya na jinya yau wata daya yaki gaya mana? So yayi sai ta mutu sannan ya sanar mana mu tafi gidan muna koke koke da iface iface? To kuwa zama bai gan ki ba ki tashi ki sa shijabin ki mu tafi gidan, dama ko hanyar gidan baki sani ba, yau ga dama ta zo" Ko musu Ammi bata yi ma Mama Ladi ba ta shirya, don sosai taji hankalinta ya tashi.... Maheer ya fito daga daki jin ana knocking kofar parlor, yana isa bakin kofar ya bude, ya ɗan buda ido yana kallonsu da mamaki, sai kuma ya fara kame kame, Mama Ladi tace "Dalla gafara ka bamu waje" Yana ɗan murmushi ya shafa kansa ya koma gefe, tuni Mama Ladi ta shige parlon Ammi na biye da ita, ya kulle kofar ya dawo Mama Ladi dake tsaye tsakar parlor tace "Ina Meran?" Yace "Bari in mata magana" Mama Ladi ta rike haɓa ta bi sa da kallo, can ta girgiza kai tace "Da Mashir bai yi boko ba da mun shiga uku mun lalace don sam lamarinsa bazai yi kyau ba Wllhi" Ammi ta nemi kujera ta zauna, tun da Maheer suka fito daga daki tare da Mayraah Ammi ke kallonta ganin yanda tayi mugun rama sai wani haske da tayi pauu, kamar yanda Ammi ke kallonta haka Mama Ladi ke kallonta baki bude, ita dai ta kasa dago kanta ta kallesu ta zauna kasan carpet, ɗan tafiyar da tayi ji take kamar gudu tayi, da kyar ta iya bude baki ta gaishe su, Mama Ladi tace "Toh Allah ubangiji ya raba lafiya" Shi dai Maheer na tsaye bayan kujera yaki kallon direction din su Mama Ladi, Mama Ladi ta nufi Mayraah tace "Tashi mu tafi gida, in ya ga dama ya biyo mu da kayanki" Dagota Mama Ladi tayi Ammi ta mike, Mama Ladi ta nufi kofa tana rike da Mayraah tace "Waiii, sai yanzu na kara tsorata da lamarin Mashir, da Usuman ne tuni zai dawo maki da ita gida ya ajiye maki, amma ki ga Mashir ya ajiye yarinya ciwon laulayi har ya kusa cinyeta ace Allah bazai kama sa ba, to dai Allah ya so mu mun taho da dreba" Ammi dai na biye da Mama Ladi a baya bata cewa komai, Maheer dake tsaye parlon ya kasa bin su har suka fita Ammi ta kullo kofar parlon, tun basu isa gida ba Ammi ta kira Bilkisu tace ta dama mata kunu. Wajen karfe biyar na yamma Mayraah na parlon Ammi a kwance kan bargon da Ammi ta shimfida mata a kasan carpet don tace bata son saman gado, bama ta son dakin gaba daya wai, tun da suka dawo ta samu ta ɗan sha kunu tayi bacci sai yanzu ta tashi, she felt a bit relieve coming back home, Ammi ce ta shigo parlon tace "Sa hijab dinki Mimi" ta mike zaune da kyar ta jawo hijab dinta tana kallon kofar parlon ta ga wanda zai shigo, MD ne ya shigo parlon da sallama tun da suka hada ido sau daya Mayraah tayi saurin sunkuyar da kanta, da tasan shi ne pretending zata yi ma tana bacci, Ammi ta shiga bedroom dinta ta bar masu parlon, ya zauna kan kujera yana kallonta yace "Sannu Mimi" Ita dai bata dago kanta ba kamar munafuka, a hankali tace "Ina yini" Yana murmushi yace "Lafiya lau, Malaria da typhoid ne ko Mimi?" Still bata dago ba ta gyada masa kai alamar eh, jin yayi shiru ta ɗan daga kai ta saci kallonsa taga wani kallo yake mata, turo baki tayi ta koma ta kwanta tana jin kamar ta nutse wajen.

Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

136
MD yace "Ina drugs din Malaria din da kike sha? Ko yayan bai siyo maki ba?" Mayraah da ke kwance ta ki juyowa tace "Ya kare" Murmushi yayi bai sake ce mata komai ba, ita dai ko da wasa taki juyowa balle ta hada ido da shi, Allah Allah take ya fita ya bar mata parlon, bude kofar parlon aka yi ya juya, Mayraah bata juyo ba balle tasan wanda ya shigo, Ihsaan ce ta shigo parlon, tun da ya shigo gidan sai a sannan ya gan ta, ta ɗan kallesa suka hada ido bata ce komai ba ta tafi inda laptop dinta yake, ya bi ta da kallon gefen ido har ta dau laptop din sannan ta fita daga parlon ta kullo kofa, mikewa yayi yana kallon Mayraah yace "Allah ya sauwake Mimin Yaya me Malaria and typhoid" Ita dai Mayraah bata juyo ba kuma taki ce masa komai sai ma kara runtse idonta da take, yayi murmushi ya juya zai fita sai ga Mama Ladi ta shigo da cup din Custard tana cewa "So fa yayi ki mutu sannan ya bugo ya gaya mana, sai mu kwasa muna kuka mu tafi gidan nasa, tirrr da Mashir...." Mayraah na jin muryan Mama Ladi taji kamar tayi tsuntsu ta ganta a dakin Ammi, Mama Ladi na ganin MD tayi tsit tana ɗan murmushi tace "Lahh, Mendi ashe ka shigo" MD ya gaisheta, tace "Lafiya lau Mendi ya aiki, dazun nan in gaya maka muka yi mota guda muka je kwaso wannan mata a gidan mijin rai a hannun Allah, ashe watan ta kusan biyu kenan tana kwance tana laulayin ciki amma sbda gaɓonci irin na Mashir yaki sanar mana, to kunyar me zai ji oho, ai da ko ni sai ya kira a waya ya gaya min, ga cikin ya zo mata da azababben laulayi in gaya maka ta kirba mana amai yayi sau uku yau, yau duk mun tsorata da halin da muka sameta duk ta fita hayyacinta sai kace cikin jaraba astagfirullah" MD dai sai murmushi yake yana kallon Mama Ladi, Mayraah taji hawaye na zubo mata bata taɓa jin haushin Mama Ladi irin na yau ba, Mama Ladi tace "Atoh, ga dai kwasta nan na dama mata ko zata iya sha, shi dai ba ya cuceta ya hadata da wahala ba, irin wnn laulayin har sai tayi wata hudu kafin ta samu kanta, nayi matukar tausaya mata" Mikewa Mayraah tayi duk da rashin kwarin jikinta bata ko kallesu ba ta shige dakin Ammi hawaye na sauka idonta, Mama Ladi tace "Auu, to ai naga dai kawun ki ne Mendin ba wani bare ba ko" MD dai sai dariya yake yace "Bari in sauka kasa Mama" Mama Ladi tace "Toh maza jeka, Ihisanin ma a kasa na bar ta, yau ita ce zata yi mana girki nace kar a kuskura a ba Eeman in ba so ake mu yi ta gudawa a gidan ba, don ni wllh in ita ce ma tayi bazan ci ba, shekaranjiya fa da ta mana jalop haka muka yi ta tsamo jalop din cikin man gyada, sam tsoron Eemani nake" Shi dae MD ya nufi kofa yana murmushi bai ce mata komai ba ya fita, Mama Ladi ta karasa daki gun Mayraah da Custard din hannunta cikin lallami tace "Naga dai kanin ubanki ne Mendi din ba bare ba balle kice na tona maki asiri" Ko kallonta Mayraah bata yi ba hawaye na sauka idonta. Tun da Mama Ladi da Ammi suka tafi gidan Maheer suka taho da Mayraah kusan sati daya kenan Maheer bai zo gidan ba sai dai ya kira Ammi a waya, shi kansa ya rasa me yasa ya kasa zuwa gidan, ga dai kullum hankalinsa da tunaninsa na kan Mayraah but kawai yana ji bazai iya zuwa gidan ba, he just wish and hope she is getting better now... Mayraah kam ko don shiga da ficen da ake yi parlon Ammi with the numbers of mutanen dake gidan ga draman Mama Ladi na yau da kullum da baya karewa yasa ta ke jin dama dama a jikinta unlike sanda take gidan Maheer, duk da yanzun ma dai sai dai tayi ta bin kowa da ido ko tayi murmushi don ko magana bata son yi, amma she is feeling much better akan gidan Maheer, kusan every evening Usman ke siyo mata Garden egg da Avocado don su kadai take iya tolerating, Mama Ladi kuma ta dama mata kunun masara ta sha babu sugar, duk dare idan Abba ya dawo shi ma ya kan shigo part din Ammi ya duba jikinta... Yau bayan Isha Mama Ladi ta shigo parlon Ammi da sallama ta nemi waje ta zauna tana kallon Ammi tace "Wai

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login