Showing 444001 words to 447000 words out of 452169 words

Chapter 149 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

fito daga bandaki, bayan ta shirya ta zagayo ta daukesa sannan Maheer ya ajiye makullin hannunsa ya shiga banɗaki.

Thanks for ur prayers.

Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

142
Babin wata sabuwar rayuwa me cike da so da kaunar juna Mayraah da Maheer suka bude with their handsome son a gidan, babu ranan da Maheer zai fita aiki da safe da bazai dawo da rana to check on them ba, every weekend da baya zuwa aiki kuwa yana tare da su a gidan, sannan duk aikin da ya san zai yi stressing Mayraah bai bari tayi sai dai shi yayi har hakan yayi ta bata mamaki, she was thinking kawai zai yi na kwana biyu ne ya dena but sai taga he is doing it continuously, kusan shi ke masu laundering ita da Aryaan, hatta girki at times sai dai taga ya masu order, kawai gani yake rainon Aryaan ma kadai ya isheta, duk da yaron bai da rigima ko kadan amma sai yaki bacci cikin daddare sai dai ayi ta masa wasa, in kuwa kace zaka kyalesa ko ka kashe wutan dakin to nan zai fara kuka, hakan yasa Mayraah bata samun baccin kirki da daddare sai kusan asuba in Aryaan yayi bacci, wani lkcn sai dai Maheer ya tasheta da safe in zai fita aiki... Yau Mayraah ta cika sati shidda da yan kwanaki da dawowarta daga Kaduna wanda a kwanakin nan sau uku suka je gidan Ammi gaisheta, kamar ko wani rana Maheer ya dawo gidan at noon after juma'at prayer to check on them don for 5 days now Aryaan ba shi da lafiya sosai, Kwance ya tarda Mayraah tana bacci a kasan carpet, Aryaan dake cikin kekensa na yara sai rigima yake har da hawayensa, amma Mayraah tayi nisa a baccin da take, Maheer ya ajiye ledan takeaway din abincin da yayi mata kan center table sannan ya karasa ya dauki Aryaan yaji jikinsa yayi zafi sosai, kallon Mayraah yayi sanin she is very tired, har ta rame unlike sanda ta dawo daga kaduna, cikin 5 days din nan duk bata wani baccin kirki saboda Aryaan that is sick, even before he became sick haka nan bai bari tayi bacci me yawa cikin dare dama, ya daura Aryaan kan kafadarsa yana patting dinsa a hankali, tunani ya fara yi ko mai aiki za a samo mata da zata dinga taimaka mata ita ma ta dinga samun lokacin hutu stress din ya ragu, firgit Mayraah ta mike zaune tana kallon keken Aryaan, sai kuma ta daga kai sama, ganin Maheer tsaye a parlon ta murza ido a hankali tace "Honey ka dawo?" Ya karaso kusa da ita ya zauna kan kujera yace "Yeah na dawo Baby gal, Aryaan is stressing you much ko?" Ta ɗan yi murmushi tace "Aa don bashi da lafiya ne ai" Yace "Kin basa magani?" Ta kalli agogon sannan tace "Eh na basa an hour ago, yaya ko allura za ayi masa ne?" Maheer yace "Ai bai gama shan magungunan ba Nurse Mimi, he is teething, he will be better soon in sha Allah" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Allah ya sa" Yace "Ga abinci na kawo maki" Ta kalli ledan a hankali tace "Ohk, ban ma dade da yin breakfast ba, i am not hungry, sai anjima zan ci" Sai da Aryaan ya koma bacci Maheer ya kwantar da shi a hankali don kar ya tashi ,sannan ya dau car key dinsa yana kallon Mayraah yace "Zan koma aiki Baby gal" Tace "Toh Allah ya tsare dear, what should i cook for dinner?" Yace "No dear, don't worry kiyi baccin ki kawai kafin ya tashi, i will get us something light for dinner" Har bakin kofa Mayraah ta rakasa ta jingina da side din kofar tana kallonsa, ko kadan bata gajiya da kallon gentle mijin nata, he is so unique in so many ways, his caring is topnotch, everything about him is close to perfection, yayi kissing cheek dinta a hankali yace "Sai na dawo wife" Rungumesa tayi ta kwantar da kanta saman kirjinsa murya can kasa tace "Take care of ur self hubby" Yana murmushi ya duka yana kallon fuskarta ya ja hancinta yace "Sure Baby gal" Da ido ta bi sa har ya fita daga compound din sannan ta juya a hankali ta koma parlon ta kulle kofar, tana karasawa cikin parlon taga idon Aryaan biyu yana kallonta, ta marairaice tana kallonsa kamar zata yi kuka. Washegari Saturday Maheer yasa Mayraah ta shirya za su je gidan Ammi, kafin karfe sha daya na safe Mayraah ta gama shirya Aryaan ita ma ta shirya, wajen sha daya da rabi Maheer ya shigo dakin nata da sallama jin shiru basu fito ba, kwance ya ganta gefen Aryaan a saman gado bacci ya dauketa, Aryaan kuwa na ta wasa da baby bag dinsa da ta saka duk wani abun da zai bukata idan sun je gidan Ammi, Maheer ya isa inda suke ya duka yana kallonta baya ko kiftawa, ya fi minti biyu duke gabanta, daga karshe dai ya mike a hankali yana kallon Aryaan, daukansa yayi hakan ya tada Mayraah ta mike zaune da sauri tace "Yaya mun gama fa" Yayi kasa da murya yace "Kawai kiyi baccin ki Wife, i will take care of Aryaan..." Mayraah ta girgiza kai da sauri tace "Aa Honey ni dai mu je kawai, yaushe rabon mu je gidan Ammi" Shiru Maheer yayi, sai kuma yace "Da dai kiyi baccin ki Mimi, i promise baza mu dameki ni da Aryaan ba" Mayraah ta tashi tsaye ta dau veil dinta tace "Ni dai na riga na shirya mu tafi kawai pls" Bata jira cewarsa ba ta ta fita daga dakin ya bi ta da kallo, sai kuma ya bi bayanta, ita Mayraah so take kawai su je gidan Ammi yanda zata yi baccinta har ya isheta without Aryaan's interruption, a parlor Maheer ya sameta zaune tana jiran sa, yace "Toh baki yi breakfast ba ai Mimi" Tace "I took pineapple dazu ai" Yace "Ohk then" Yana rike da Aryaan da Baby bag dinsa suka fita daga parlon, sai da suka yi nisa Maheer ya ɗan kallil Mayraah da ta jinginar da kanta da kujera tana rungume da Aryaan a jikinta yace "I think za mu fara ba Aryaan formula since he is 5 months old now wife" Mayraah ta juya ta kallesa tace "Aa yaya mu bari dai yayi like 7 month" Bai ce mata komai ba har suka isa gida. A kofar gidan Maheer yayi parking Mayraah ta bude motar zata sauka taji she is so weak and tired to do so, ga wani juyawa da idonta yake mata, ta juya ta kalli Maheer dake kallonta, da kyar tace "Yaya ko zaka shiga ciki da motar kayi parking, naji kaman kaina na ciwo kuma yanzu" A hankali Maheer yace "Ohk" Tada motar yayi mai gadi ya bude masa gate, ya shiga cikin compound din bayan yayi parking a parking lot ya juya ya kalli Mayraah, jinginar da kanta tayi da kujeran motar idonta a lumshe, ya sauka ya zagayo ta inda take ya bude motar ta bude ido a hankali tana kallonsa, ya amshi Aryaan daga hannunta ya rungumesa a shoulder dinsa sannan ya kamo hannunta ta sauka daga motar, jingina tayi jikin motar ta dafe kanta tace "Yaya kamar bana jin dadi...." Maheer yayi kasa da murya yace "I know Mimi, let go in sai ki kwanta" Yana rike da ita suka nufi entrance din parlon, suna shiga ta tafi ta kwanta kan kujera da sauri tana sauke numfashi don da kyar da karfin hali ta dinga tafiya har suka iso parlon, Maheer ya kwantar da Aryaan dake hannunsa ya tafi ya zauna kusa da ita yana kallonta yace "Sannu Wife" Ita dai bata ce komai ba ta rufe ido tana sauke numfashi a hankali, Bilkisu ce ta sauko parlon, ganinsu ta karaso inda suke da fara'a bayan ta ajiye kayan hannunta ta gaishesu sannan ta dau Aryaan tana kallonsa da murmushi fuskarta ta tafi da shi sama tana masa wasa, Mayraah ta bude ido a hankali kamar zata yi kuka tace "Yaya i feel like throwing up" Dagota yayi ta zauna yace "Mu je toilet ne?" Ta fashe masa da kuka tana kallonsa, ya tashi tsaye ya dagota suka nufi bandakin dake parlon, duk yunkurin ta bata samu tayi aman ba sai ma galabaita da tayi, a haka suka fito daga bandakin Maheer na rike da ita. Da ido Mama Ladi ke bin Ammi dake kokarin sauke Aryaan dake bayanta a hankali ta yanda bazai farka ba in ta kwantar da shi kan shimfidar da tayi masa a parlonta, bayan Ammi ta tabbatar ya koma baccin ta mike ta rage Ac dake aiki a parlon, Mama Ladi ta kyabe baki tace "Ai shikenan kuma, amma duka duka watan jaririn nan nawa da har ta yarda tayi wani cikin daga komawarta ni Ladi? Yaushe muka gama yi mata bautan laulayi da zata amince ta sake wani cikin, su sai kace ba wayayyu yan boko ba, shi yana likita ita tana Nas amma su tafka wannan kuskure, jariri ko wata shidda bai karasa ba ta sake kunso wani cikin ko tausayinsa basu ji ba, yanzu fa shikenan ta masa haramiyar nono, don in har ta ci gaba da shayar da shi to lalacewa zai yi ya dawo kamar ɗan kyanwa, gaskiya daga ita har Mashir din basu duba ma yaron nan ba, dama a samar mata mai aiki ta koma dakinta tayi laulayi duk abinda take so mai aikin ta mata, ke kuma a barki kiji da jaririn nan" Ammi harkan gabanta kawai take ko kallon Mama Ladi bata yi ba balle ta tanka ta, bude kofar parlon aka yi Maheer ya shigo da sallama, Mama Ladi ta bi sa da wani kallo, ya ajiye ledan formula da ya siyo ma Aryaan har ma da feeding bottles dinsa da ya dauko daga can gida, Ammi ta dau feeding bottles din ta fita don zuwa ta tafasa su cikin ruwan zafi a kitchen, Maheer ya karasa cikin dakin Ammi inda Mayraah ke kwance, bacci ya sameta tana yi ya duka gabanta yana kallonta ya kai hannunsa forehead dinta a hankali yaji jikinta yayi zafi sosai, all this while bai lura she is pregnant ba sai daxu kafin su fito daga gida, wannan ne ma yasa yayi insisting su fasa zuwa gidan Ammin amma taki, tun bayan da suka yi aure wani lkcn sai tayi har wata biyu wata uku bata ga al'adarta ba, wnn ne ma yasa take ta damuwa sanda bata yi ciki ba, since da ta dawo daga kaduna bata yi period ba amma shi bai kawo ciki a rai ba sai dazu da ya kare mata kallo a dakinta, mikewa yayi ya fita daga dakin ya koma parlor, Mama Ladi na kallonsa tayi kasa da murya tace "Yanzu dai ga bikin Usuman saura sati biyar, a haka matar nan na azababben laulayin nan za ayi bikin da ita? Sannan ga ɗan karamin yaron nan da za a yaye lokacinsa bai yi ba, ai an shiga hakkinsa wallahi, yanzun nan za mu ga ya lalace duk yayi wujiga wujiga" shi dai Maheer bai ce ma Mama Ladi komai ba ya fita daga parlon, har cikin ransa yake tausayin Mayraah in ya tuno irin rashin lafiyar da tayi na cikin Aryaan, to yanzu kuma ga wnn.... Tun daga wannan rana Mayraah tayi bankwana kuma da good health, wannan laulayin har ya fi na Aryaan wahalar da ita, sosai take jin jiki taji babu abinda ke mata dadi kuma a rayuwar, bata iya cin komai kafin sati daya duk ta rame ta fara fita hayyacinta duk da drips da ake kara mata, shi kansa Aryaan kamar bakin Mama Ladi ya bi sa don duk shima ya rame, sau uku ana canza masa formula har dai ya yarda yake shan na ukun da aka siyo masa, a ranan da ta cika kwana goma a gidan tana kwance bayan magrib a kasan dakinta don hatta bangaren Ammin taji bata so gaba daya sai dakinta, komai sai dai Ammi da Eeman su kawo mata dakin nata, Mama Ladi dama tace ita bazata yi reno biyu ba, gwara a bar ta da Aryaan tayi ta renonsa Ammi kuma taji da Mayraah da sabon cikinta, Maheer ne ya shigo dakin da sallama ya kulle kofar ya isa kusa da ita ya duka yana kallonta cike da tausayinta, duk da idonta biyu bata ce komai ba, har cikin ranta take jin haushinsa kuma bata son ganinsa, ya kamo hannunta cikin sanyin murya yace "Ya jikin Mimi?" Hawaye ya cika idonta bata ce masa komai ba, ya sauke idonsa daga kallonta, cikin rawan murya tace "Ni dai don girman Allah ka cire min cikin nan bana so" Maheer ya kwantar da murya yace "Kiyi hakuri Mimi, in sha Allah u will get better very soon" Ta fashe masa da kuka sosai tace "Saboda ba kai kake wahala ba ko?" bude kofar dakin aka yi ya juya da sauri, Ammi ce ta shigo dakin da cup din kunu, every few minutes take shiga dakin to check on Mayraah, Maheer ya mike tsaye Ammi tace "Idonta biyu ne?" Ba tare da ya kalli Ammi ba yace "Eh" Ammi ta karasa kusa da ita, shi kuma ya juya ya fita daga dakin. Wajen karfe goma na dare Mama Ladi ta lallaba ta sauka downstairs zata je kitchen ta hado shayi ta tafi dakinta ta sha, tana bude kofar kitchen din ta ga Usman tsaye at the far end of the kitchen kusa da store yana facing din Eeman da ta makale jikin bango taki hada ido da shi tana wasa da yatsunta kana ganinta kasan she is uncomfortable a wajen, Usman ya juya ya kalli Mama Ladi sai kuma ya dauke kansa yana kallon Eeman da kanta ke kasa, Mama Ladi dai tace "Dama ni ruwa na sauko dauka kada in je cikin dare kishin ruwa ya hanani sukuni, ita kuma Ammi na can yaro ya hanata zaman lafiya, duk wani wahala in aka tarkato ita ake dora ma, ga renon me laulayi ga renon jariri" Tana fadin haka ta dau ruwanta ta fita daga kitchen din, direct bangaren Ammi ta nufa, Ammi na goye da Aryaan dake kuka, duk kwanan nan ya koyi kuka abinda bai da shi, Mama Ladi ta ajiye goran ruwan hannunta tace "Yanzu dai yaushe naji ance za a kai Eemani katsina?" Ammi ta zauna kan kujera bayan ta sauke Aryaan zata kara basa abinci tace "Zuwa gobe in sha Allah" Mama Ladi tace "Wa zai kai ta katsinan?" Ammi tace "Maheer ne zai kai ta, amma za su tsaya kano don tare da Mariya za su tafi katsinan" Mama Ladi tace "To gwara dai haka, kar aje ayi aika aika a gidan nan mu shiga uku mu lalace" Ammi ta dinga kallon Mama Ladi alamar bata gane abinda take nufi ba, Mama Ladi tace "Atoh, tunda ni dai nasan me na gani" Mikewa tayi ta dau goran ruwan da ta dauko tace "Yau wai saura kwana nawa ne bikin ma?" Ammi tace "Wata daya in Allah ya yarda" Mama Ladi tace "Toh Allah dai ya kai mu da lafiya, shegu ba dai sun ga yaran sun samu daukaka ba tun ba aje ko ina ba, shi yasa suke son su lallaba su jawo su jikinsu ta yanda su ma za su dinga cin arziki, har da wani cewa a katsina za ayi biki a kai masu yarinyar, basu son duk mazajen yaran ba kanwan lasa bane, shi Mendi dama ba da uban kowa yake dariya ba, ba kuma ko wani shege yake sakar ma fuska ba, sabgar gabansa kawai yake, ni da farko ma na zata soja ne sai kuma daga baya naji ana kiransa likita, wani sa'in kuma ace masa Daddy, shi kuma mijin dayar dama suna kawo masa wargi zai lafta masu sammaci ba mutunci garesa ba, sam bai daukar nansense, mu kan mu ya muka kare da shi balle ace su kawo masa iskanci a gidansa, ai tijara ma zai masu, ba gwara Mendi ba ma a kansa, Mendi sai yayi dariya sau uku shi wnn bai yi sau daya ba, ai Usuman ba kyau, shi sa na kama kaina bana barin komai ya hadamu tunda ya zageni haihuwar wannan yaro a asibiti, ita kanta Eemanin naga a tsorace take da shi yanzu ta dena shige masa kamar da, mu dai Allah ya nuna mana ranan auren lafiya kawai" Ammi tace "Ameen" Mama Ladi tace "Sai kuma magana ta karshe, tun kan a fara biki a gidan nan saboda bakin mutane gwara a nemar ma Mera er dattijuwa su koma can gidanta dattijuwar ta dinga yi mata komai, bakin jama'a masu zuwa biki nake gudu, wani sam bakinsa bai da kyau, kowa ya ganta kwance shame shame yasan laulayin ciki take kuma an san ko wata shidda yaronta bai karasa ba, don haka gwara ta tattara su koma gidanta sai a bar mana ɗan kawai, bayan biki in ma za a dawo da ita nan din ne sai a dawo da ita, Mama Ladi na kai wa nan ta fita daga parlon. Washegari da safe Ammi ta shigo dakin Mama Ladi dake linke kayanta da Bilkisu ta wanke mata da hannu don tace bata son washing machine kar kayanta su kode, a nutse take linkin kayan sai ka rantse iron din su tayi, bata barin kowa ya mata linkin kayanta, daga kasa kuma ga tray din breakfast din da ta gama, don sai da taci tayi nak ta fara linkin, Ammi ta zauna tana kallonta tace "Sannu da aiki Mama" Mama Ladi tace "Yauwa, ina jikan naki?" Ammi tace "Yana kasa gun Bilkisu" Mama Ladi tace "Dama ita za a bar ma renonsa ranan bikin Usuman ta yanda zaki tarbi baƙin ki cikin nutsuwa ki basu kulawan da ya kamata, baza mu bi ta tasa ba ranan don naga wani sabon rigima ya koya yanzu, da har ina cewa yaro shiru shiru

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login