Showing 447001 words to 450000 words out of 452169 words

Chapter 150 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

kamar ubansa sbda hakuri ga kuma fara'a, ko da yake cutarsa aka yi aka rabasa da Mama ko wata shidda bai yi ba kinga baza mu ga lefinsa ba gaskiya" Ammi dai murmushi kawai take, bayan few seconds tace "Mama Alhaji Saminu ne ya kira Abba jiya ya bada sako wai a sanar maki" Mama Ladi ta ajiye zanin hannunta tace "Sakon me kuma?" Ita dai Ammi bata dena murmushin da take ba, Mama Ladi ta nemi waje ta zauna tace "To ina ji sakon menene? Kudi ya bada a bani?" Ammi ta girgiza kai tace "Aa ba kudi bane Mama" Mama Ladi tace "Toh menene?"

Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788

143
Shirye shiryen bikin Usman da Eeman kawai ake a gidan Abba, duk da tun bikin na sauran wata daya Eeman ta koma katsina, kamar yanda Mama Ladi ta ba Ammi shawara haka nan aka yi Mayraah ta koma gidanta tare da sabuwar mai aikinta da aka daukar mata don kula da ita, ita kanta Mayraah taji ta ma fi son ta koma gidanta don sam bata son hayaniya, shima Maheer hakan ya masa saboda lkcn cikin Aryaan duk bata wani samu kulawarsa ba don kasa zuwa gidan yake, yanzu kam he will take good care of his wife fully, Ammi kuma ta ci gaba da kula da Aryaan da taimakon Bilkisu, tuni Aryaan ya warware ya maida jikinsa, a sati yake shanye gwangwanin madarar sa wanda Usman ke siya masa, ana saura wasu yan kwanaki bikin Mama Ladi suka tafi kai lefen Eeman can Katsina gun dangin mahaifinta, kaya na gani na fada aka yi ma Eeman kamar dai yanda aka ma Twin sister dinta, Mama Ladi suna dawowa daga kai lefen Ammi ta shigo dakinta ta sameta tana murmushi, ta ajiye mata abincin da ta kawo mata tace "Sannu Mama, ya gajiyan hanya?" Mama Ladi ta rike haɓa tace "Huhuhu, ashe dai matsiyata ne dangin uban nasu, in gaya maki wallahi wasu yaku bayi muka kai ma lefen dai, yarkace yarkace da su haka nan dai muka mika masu lefen, ke kinga ɗan kuturin gidan da muka kai lefen ma kuwa? Ni dai wallahi jikina sanyi yayi, ko ruwa na kasa sha a gidan, sai yanzu na fahimci me yasa suka danne gadon marayun bayan rasuwan ubansu suka handame, kuma dai gashi ban ga sun yi abun kirki da gadon ba tunda har yau suna nan a tsiyace kamar en iska, Allah dai yaji ƙan Amina duk da mugun halinsu da talaucin da suke fama da shi bata taɓa nisanta yaran da su ba, don kinga ai suna can katsinan ma tayi hatsari ta rasu, mata me son zumunci, Allah dai yaji ƙan ta, ya gafarta mata, in sha Allahu marayun nan da ta bari sai sun samu daukaka ta yanda duk bama zato a duniya, sam bana jin Mendi, saura mana kawai mu zaunar da Usuman mu kulle kofa mu sake jaddada masa hukuncin wanda ya cuci maraya ko ya walakanta sa, don ko Eemani marainiya ce gaba da baya, in yaci amanarta to Allah zai saka mata tun a gidan duniya ya daidai ce, kawai abinda ya rage mana kenan mu yi don ni dai a tsorace nake da Usuman" Ammi dai sai kallon Mama Ladi take, Mama Ladi tace "Allah kuma ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyaba ya dora su kan mazajen nasu, ita kuma Mera Allah Ubangiji ya sauketa lafiya" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Ameen" Har aka gama bikin Eeman aka watse Mayraah bata san me ake ciki ba tana fama da kanta, ashe laulayin Aryaan ya zo mata da sauki bata sani ba, don wannan kam ji take kamar bazata yi rai ba, ta rasa ina zata sa kanta taji dadi, roban drip kuwa ta sha yafi a kirga, ga mai aikin da aka daukar mata mai hankali da nutsuwa, don sosai take kula da ita kamar er ta, bini bini zata shigo dakin ko da wani abu da zata yi mata, wani lkcn har ta zauna dakin tana ɗan mata hira wai kar kadaici yayi mata yawa, bayan biki da kwana biyu, wajen la'asar Aisha mai aikinta ta shigo dakin ta duka gabanta tace "Hajiya kin yi baƙi suna parlor" Mayraah ta bude ido da kyar tana kallonta amma ta kasa tambayarta waye don ko magana bata so, Aisha da tasan bata fiye son magana ba tace "Wannan tsohuwar da ta zo kwanakin baya ce, ita da wata bakuwar" Mayraah ta riga ta gane Mama Ladi ce ta zo, don kafin biki ta zo gidan dubata ita da Omar har sau biyu, Mayraah ta mike zaune da kyar ta dau hijab dinta ta saka, tun da ta fito parlon Aunty Mariya ke kallonta cike da tausayinta ganin wani mugun raman da tayi, Mama Ladi tace "Ai kuma shikenan, ciki dai sai kace na jaraba Allah na tuba, kina haife masa wannan dama maza kiyi ta kanki kiyi tsarin iyali, wannan wahala har ina haka?" Mayraah ta zauna kan kujera Aunty Mariya na mata sannu, Mama Ladi tace "Ko da yake ita ma uwar taku haka tayi ta wahala duk ciki sai tayi wata biyar a kwance ni da Hajja ke mata wahala, to gashi kin biyo kafarta dai, cikin Umar ma duk mun zata mutuwa zata yi" Mayraah dai tun da ta gaishesu a parlon bata sake cewa komai ba kanta a kasa, Aunty Mariya ta kalli Mama Ladi tace "Tunda an watse biki lafiya ba gwara ta koma can gidan ba Mama?" Mama Ladi tace "Wani gida? Kema dai da taya bera bari kike Mariya, ba fa cikin farko bane wannan, kuma da Ammin bata kusa da ita fa? Iya renon ma da aka bar ta da shi na jaririn yaron nan ai ya isa haka, shikenan sai sun sa baiwar Allahn ta tsufa saboda wahala hankalinsu zai kwanta, ai kamata yayi yanzu ace Ammi ta samu hutu kuma ai, ta gama bautan yaranta ta dawo kan jikoki kuma" Aunty Mariya dai bata ce komai ba, Mama Ladi tace "Nan da yan watanni zata dawo dai dai, tunda ga mai aikinta na kula da ita kawai tayi zamanta a gidan mijinta da ya dora mata wahalan....." Ita dai Mayraah ta jinginar da kanta da kujera don har ta gaji da zaman, kwanciya kawai take son yi, ko minti talatin su Aunty Mariya basu yi da shigowa gidan ba Ihsaan ta shigo parlon da sallama, Mama Ladi ta daga kai tana kallonta tace "Ke kuma ba yau aka ce jirgin naku zai tashi ba? Ko kun fasa tafiyar ne" Ihsaan na ɗan murmushi ta ajiye ledan hannunta tace "Sai karfe takwas in sha Allah" Mama Ladi ta kalli agogo tace "Atoh da sauran lokaci" Ihsaan ta zauna kan carpet ta fara gaida su Mama Ladi sannan ta kalli Mayraah dake kallonta ta gaisheta, murmushi kawai Mayraah tayi mata ta gyada mata kai, Ihsaan tace "Ya jikin Aunty?" A hankali Mayraah tace "Alhamdulillah" Mama Ladi tace "Bikin er uwarta ta zo tun bikin bai karaso ba, kilan shi ne mijin zai ce ta zo ta duba ki kafin su koma kasar ta su" Mama Ladi ta kalli Ihsaan tace "To ina Mendin?" Ihsaan ta sauke kanta tace "Yana cikin mota" Mama Ladi tace "Toh me ya hanasa shigowa? Ba gidan er sa bace?" Ihsaan na murmushi tace "Yace in gaisheta da jiki" Mama Ladi tace "Aa, je ki ce masa Ladi tace ya shigo" Ihsaan ta mike ta fita daga parlon, Mayraah ta wani daure fuska tana kallon Mama Ladi, ba a dau lokaci ba Ihsaan ta dawo parlon ta zauna kasan carpet, bayan some minutes sai ga MD ya shigo parlon da sallama, Mayraah dai ta sunkuyar da kanta, ya zauna suka gaisa da Aunty Mariya da Mama Ladi, Mama Ladi tace "Ai in kai ma ka shigo duba jikin nata zata ji dadi tunda kai ubanta ne Mendi, kasan kowa da yanda laulayin ke zuwa masa ita kam tana jin jiki, sai dai mu ce Allah Ubangiji ya bata lafiya" Mayraah dai kanta na kasa tana wasa da hijab din jikinta, MD na kallonta yace "How are you feeling Mayraah?" Da kyar tace "Alhamdulillah, ina yini?" Yace "Lafiya lau, Allah ya sauwake, gradually u will get better in sha Allah" Kai kawai ta gyada masa, Mama Ladi tace "Ga ɗan nasu na fari ma sai yanzu yayi wata shidda, ni ko nace dama ma'aikatan lafiya na yarda su yi gwarne? naga shi likita ita Nas amma kuma ace anyi gwarne saboda Allah" Aunty Mariya ta dinga kallon Mama Ladi rai bace, MD dai murmushi kawai yayi yace "To Mama ai duk yanda Allah ya tsara hakan ne zai faru ko" Mama Ladi tace "Sai dai haka kuma, to Allah ya raba lafiya dai" Mikewa MD yayi yana masu sallama, ya ajiye ma Mama Ladi 50k yace "Naga ke da Aunty a kaduna ku ke, sai ku yi kudin mota" Mama Ladi tace "Toh Allah ya maka albarka Mendi, Allah Ubangiji yasa ka fi wan ubanka wato Alhaji Saminu, Allah ya daukaka mana kai Mendi" Yana murmushi ya kalli Mayraah yace "Allah ya kara lafiya Mayraah" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa ta ɗan yi murmushi ta gyada masa kai, MD yayi ma Aunty Mariya ma sallama sannan ya fita daga parlon, Ihsaan ta dau abun da suka siya ma Mayraah ta kai gabanta ta durkusa ta ajiye tana kallonta tace "Allah ya baki lafiya Aunty" Mayraah na mata murmushi a hankali tace "Ameen Ihsaan, Allah ya kiyaye hanya" Ihsaan tace "Ameen" Daga haka ta mike tayi ma su Mama Ladi ma sallama sannan ta fita daga parlon ta bi bayansa, Mama Ladi ta fara matsar kwalla tace "Duk sun yi dacen mazaje wallahi, yanzu ki ga yanda yake kula da yarinyar nan ta dawo kamar ba ita ba, ta zama wata er gayu, kuma sanin er yarinya ce kinga ai har yanzu bai yarda tayi ciki ba sai ya gama renonta yanda ya kamata, ita kanta Eemani muna kyautata zaton Usuman zai zame mata uwa da uba a duniya, amma fa zance na gaskiya duk Mera ta fi su dacen miji, don a nan duniya dai kafin a samu me hali sak na Mashir to sai an tona wllhi, Mashir ba sa wa, ba hanawa, ga gudun bacin rai, ga kunya, ga kawaici, ga biyayya, ita kanta Ammin ace yau ta rasa Mashir Al-qur'an sai tayi karamin hauka...." Mayraah ta dinga wa Mama Ladi wani kallo jin furucinta na karshe, ita kanta Aunty Mariya wani kallon take ma Mama Ladi, Mama Ladi ta sauke ajiyar zuciya tace "Allah dai yayi masa albarka, ya basa 'ya yan da za su masa biyayya yanda yake mana, tun yanzu Aryaan din nan na lura hakuri ke garesa kamar ubansa, da wuya kaga yayi kuka in ba ko bai da lafiya ba, shi yasa yaron ya shiga raina wallahi..." Babu dae wanda ya tanka Mama Ladi a parlon. Mama Ladi ce zaune parlon Ammi tayi kicin kicin da fuska kamar bata taɓa dariya ba, Aunty Mariya na gefenta zaune a parlon, Ammi kuma na goye da Aryaan dake bacci a bayanta, rai bace Mama Ladi tace "Tun a sannan fa nace a bar wannan batu ni babu ruwana, meye kuma yanzu za a sake tado min da wannan zance fisabilillahi idan ba neman magana ba" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Banda abun ki Mama tunda ance yau zai zo ai da kin jira ya iso in bai maki ba sai a san abun yi kuma, ai dama ba ace lallai dole ba" Aunty Mariya tace "Wallahi haka na gaya mata kafin ki shigo Ammi" Mama Ladi tace "To wai akan wani dalili ma zai zo min tukun? In fa yayi gigin zuwa inda nake zan daddana masa ashar wallahi tallahi, Da girmana a kawo min wani batu na aure banda rashin tsoron Allah, da fa na haihu da ina da jika kamar Meran ki yanzu, a bar ganina ina da kyan jiki ayi zaton shekarata hamsin a duniya, shi kuma Alhaji Saminun kaf danginsa ya rasa warce zai hada da abokin nasa sai ni Ladi? Wato ga Ladi er iska ga Ladi er kauye tunda nace masa a karaye nake, In kin bibiya fa irin abokan nan ne tun na kuruciya wa enda aka yi wasan ƙasa tare, shi Alhaji Saminu sai Allah ya daukaka sa a cikinsu yayi kudi su kuma suna nan da talauci amma suna makale da shi suna maula, to fa ina ga shine a cikinsu wani shegen zai ce ai aure yake so amma bashi da halin yi bai da ko sisi, ni kuma gani er kauye sai in fado ran Alhaji Saminu sai yaga bari kawai ya hadani da shi mu karata, banda haka ai kaf abokansa da suke harkokin arziki tare nera ta zauna masu basu ma zaman kasar nan wallahi, shi kansa Alhaji Saminun sai yayi wata biyu bai kasar ai, wani lkcn da Hajiya Ramatun yake tafiya su yi watannin da za su yi su dawo tare, dama Halima ake bari da jiran gida, in mutumin arziki ne ai da Halimar zai fara yi masa tayi tunda kanwarsa ce ba ni da ban hada komai da shi ba" Daga Ammi har Aunty Mariya dai sun kasa cewa komai, Mama Ladi tace "Shi kuma Mamuda da ya dage kan batun nan har yake ce maku mutumin zai zo yau in gajiya yayi dani ba sai ya bani kudin mota inyi komawata karaye ba, don naga kamar shi ma neman kai yake da ni yana kakkabi da ni, duk ya mance halaccin da na masa a rayuwa, ni kenan kullum ina kan titi zuwa sulhu a gidansa, amma daga karshe saboda zaman lafiya ya dawo gidansa sai ya nuna ya gaji da ni" Mama Ladi na kai wa nan ta fara matsar kwalla, Ammi dai ta kalli Aunty Mariya, Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya ta mike ta fita daga parlon. Bayan Magrib da kyar da siɗin goshi Ammi da Aunty Mariya suka lallaba Mama Ladi dake dakinta akan taje parlon downstairs mutumin ya iso gidan, zagi kam sun sha shi kwando kwando a wajenta har da ɗan hawayenta, daga karshe dai ta saka hijab dinta ko gaya masu abinda ta shirya yi ma mutumin da ya zo wajenta bata yi ba ta fice daga dakin, Aunty Mariya ta kalli Ammi dake tsaye tace "Kar kuma taje ta zage bawan Allah fa Ammi mu ji kunya" Ammi tace "Wallahi nima nazarin da nake kenan Mariya, don ba karamin aikinta bane" Aunty Mariya tace "Tun farko da ta nuna bata ra'ayi Ammi da haka kawai kika gaya ma Abban ya gaya ma Alhaji Saminun, kinga da ba a zo gabar nan ba" Ammi ta sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba. Mayraah ce kwance dakin Mama Ladi tana ta kallon Aryaan dake zaune yana wasa da toys dinsa, gaba daya yaron ya juye ya koma sak ubansa, unlike farkon haihuwar sa da yake ɗan kama da ita, duk in suka zo gidan gaida Ammi tare da Maheer sai taji kamar a bata yaron su koma gida tare da shi, gashi ko saninta yaron bai yi ba don baya ma yarda da ita ko Maheer din, Ba karamin shakuwa yayi da Ammi da Bilkisu ba sai Usman me siyo masa toys iri iri, sosai Mayraah tayi nauyi kai kace haihuwa yau ko gobe, yanzun ma Mama Ladi suka zo yi ma sallama shine dalilin zuwansu gidan, Bilkisu ta shigo dakin ta dau handbag din Mama Ladi da ya rage a dakin, Aryaan na ganinta ya fara bin ta har da kukansa, Bilkisu ta daukesa tana kallon Mayraah tace "Ke kina nan Maman Aryaan, za mu je can parlon Ammi" A hankali Mayraah tace "Ina tahowa" Bilkisu ta fita tana dauke da Aryaan, Mayraah ta bi sa da kallo, bayan few minutes ta lallaba ta mike ta dau jakarta ta fita daga dakin, har zata tafi bangaren Ammi sai kuma kawai ta tafi downstairs ta zauna, Ammi na zaune parlonta rungume da Eeman dake kwance jikinta idonta a lumshe, Mama Ladi ma na zaune parlon sanye da sabon atamfarta me tsada da sabon mayafi da takalmi, ga akwatuna uku duk na sababbin kayanta, kai baka ce Mama Ladi bace zaune parlon, Ammi kam sai kallonta take tana murmushi, gaba daya ta kasa daina kallonta, Bilkisu ta ajiye Aryaan dake hannunta ta fara fita da sabbin akwatunan Mama Ladi waje don tun daxu driver ya zo daukanta, Mama Ladi ta kalli Ammi tace "Toh ke yanzu Ammi da zaki je bikin Badiyyah nan da kwana biyu ya kenan zaki yi da wannan me shigar sabon cikin da duk ta fita hayyacinta?" Ammi tayi shiru da farko, sai kuma tace "Ai Bilkisu na nan, kuma kwana daya kawai zan yi in dawo, kin ga Aryaan ma barinsa zan yi a gida...." Mama Ladi tace "To dai gwara kwana dayan, ga su nan duk kafarki suka biyo da wannan azababben laulayin, Mera ta gama farfadowa, yanzu kuma ga wannan da tafi Mera son jiki" Bude kofar parlon aka yi Usman ya shigo yana kallon Mama Ladi yace "Lokaci fa na wucewa Mama, ga driver na ta jira a waje tun daxu" Mama Ladi tace "To shi direban nan aljanna zai tuka ni ya kai ni ne da bazai iya hakuri ba, tun dazu an isheni dreba na jira, ai dai zai bari inyi sallama a tsanake cikin nutsuwa ko" Ammi ta kwantar da Eeman dake jikinta tace "Ae ba daga shi bane Mama, kar jirgin ya tashi shi yasa ya damu...." Mama Ladi tace "To ina ruwansa, in ma jirgin ya tashi sai a daga tafiyar ai" Ammi ta saka Hijab dinta ta dau handbag din Mama Ladi zata rike mata, sai ga Bilkisu ta shigo ta dau Aryaan ta fita, Ammi ta tafi gun Eeman ta duka tana kallonta tace "Za mu je raka Mama Ladi Airport, ko za ki je?" Eeman ta girgiza mata kai da sauri, Ammi tace "Toh sai

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login