Showing 183001 words to 186000 words out of 452169 words

Chapter 62 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

abinda bai shafeni ba, yanzu haka ina komawa sama shimfida zan yi in kwanta ince mata Mamudan bai dawo daga caji opis din ba" Daga haka tayi wucewarta kitchen zata kai cup din shayi.... Still wajen karfe sha daya Maheer na parlor Ammi ta sauko downstairs zata shiga kitchen ta hado ma Abba shayi, Ammi na kallonsa a hankali tace "Ita waccen dake asibitin an sallameta ne da na ganka a nan" Maheer ya girgiza kai yace "Sai gobe za a sallameta yan uwanta na asibitin, amma Ammi na so kawai taje gidansu daga asibitin don ina bukatar space, but Abba ya hana hakan ni kuma gaskiya i can't stand the sight of her a yanzu" Ammi dai tayi shiru bata ce komai ba, can ta wuce kitchen kawai. Kamar kullum yau ma karfe bakwai na safe Mayraah ta fito daga daki bayan tayi shirin tafiya aiki, kitchen ta tafi ta dafo ma inna ruwan zafi don for 5 days now ita ke kai mata ruwan zafi da breakfast kafin ta fita aiki, Mayraah na shiga dakin ta ajiye mata ta gaisheta, Inna da bakinta ya bude ras tace "Lafiya lau, kin ga yau fes na tashi bana jin ciwo a ko ina alamar guban ya sakeni" Mayraah tayi murmushi tace "Haka ake so dama inna Allah ya kara maki lafiya" Inna tace "Ameen, ai da so suka yi ace na mutu su hade har gadona, ni da nasan komai" Mayraah dai murmushi kawai take tana hada mata shayin, Inna tace "Allah maki albarka ke dai, naji wai aiki kema kike a asibitin su Halilu ko?" Mayraah tace "Eh" Inna tace "Toh Allah ya baki sa'a, kuma Kinga yaran gidan nan ki bar sake masu fuska kar su raina ki yanda suka raina ni basu da mutunci kwata kwata ya yan jaraba ne ga uwar bata kwabarsu" Mayraah dai sai murmushi take tace "Bari inje kar inyi latti Inna" Inna tace "Toh maza ki tafi Allah ya tsare" Mikewa tayi ta fita, bata tsaya tayi wani breakfast din kirki ba don ka'idar asibitin karfe takwas ne, sallama tayi ma Ummi ta fita gidan, kwana biyar yau basu hadu da Dr Khalil ba sun je wani workshop Lagos, Ta fito daga wani ward downstairs wajen karfe sha daya Dr Balogun ya shigo Reception, tare da shi aka tafi workshop din, nurses dake reception suka hau gaishesa suna masa sannu da zuwa yace "The MD is around, so u have to compose ur selves...." Daga haka ya wuce sama, Smartly dressed in black suit with white shirt ya shigo Reception din hannunsa rike da laptop dinsa, Mayraah ta bi sa da ido, gaba daya nurses din suka dinga gaishesa da ladabi kamar sun ga wani prominent person, yayi wucewarsa sama bayan ya amsa a takaice without looking at any of them, Dr Khalil dai na biye da shi a baya holding on to his laptop too ya daga ma nurses din hannu, Hafsat ta kalli Mayraah dake kokarin ajiye file din hannunta ta dawo ta zauna tayi kasa da murya tace "Wai shi ne me asibitin?" Hafsat ta buda ido sosai tace "He is the managing director" Mayraah bata sake cewa komai ba, bayan few seconds ta sake kallon Hafsat tace "But he is a foreigner?" Hafsat tace "Wallahi ban dai sani ba, amma ya cika jaraba mutumin, and he is a no nonsense, kowa shakkarsa yake" Da sauri Mayraah ta mike bayan ta tuna akwai wata patient da Dr Hamid yayi assigning dinta ta sa ma ido, ward din ta nufa to check on the patient, bayan azahar Mayraah ta tafi office din Dr Khalil zata kai masa wani file, gaishesa tayi ya amsa yace "Ya kwana biyu, ya aiki?" Tace "Alhamdulillah, how was the trip?" Yace "So stressful, nan da wata daya za mu koma in sha Allah" Mayraah tace "To Allah ya kai mu" Yace "Ameen, just that you have to be very careful cause or Director will be around har zuwa next workshop kafin ya koma, don haka ki zama diligence kan aikinki kar ki bari encounter mara dadi ya hada ku it wont be funny, though bana wani jin ki tunda har Balogun yayi commending dinki" Mayraah ta zauna bata dai ce komai ba, yace "Ya su Ummi?" Tace "Suna lafiya lau" Yace "Ummi ta ban labari kun kulla kawance da Inna yanzu" Dariya Mayraah tayi, yace "To ki dai dinga bin a hankali kar ya kwabe maku" Murmushi kawai Mayraah tayi tana gyada masa kai, yace "Kin je weekend gida kuwa?" Tace "Na je" wayar kan desk dinsa ne ya fara ring, ya kalleta yace "MD na kirana, make sure kar ki tafi gida ki jirani i will drop you don nima zan je gidan" Tace "Toh" Mikewa yayi ita ma ta tashi suka fita office din tare, shi ya tafi last flour zuwa office din MD din, ita kuma ta sauka downstairs ta dau allurai a tray zuwa wani ward zata yi ma wata yarinya da aka yi admitting da safe, tana shiga ward din ta tarar Maman yarinyar na bata abincin da aka kawo masu na asibitin, sai da ta zauna ta jira ta gama bata abinci sannan ta mike ta fara hada alluran, bude kofar ward din aka yi Mayraah ta juya, sai kuma ta koma gefe tana kallonsu, MD din ne da Dr Khalil dake biye da shi a baya, Matar ta gaishesu MD din na kallonta yace "Hello Ma, is there any improvement?" Da turanci Matar tace har yanzu jikin yarinyar na zafi, sai zazzabin ya sauka sai ya sake dawowa, sannan yarinyar na zabura, MD ya kalli Mayraah dake tsaye gefe yace "Diagnostic procedure?" Haka kawai taji gabanta ya fadi ta dau file din yarinyar da ta shigo da shi ta fara budewa da sauri, lkci daya duk sai ta daburce, Dr Khalil ya amsa file din a hannunta yana dubawa ya sanar masa diagnosis din, Gyara tsayuwa yayi yace "Ita bazata iya dubawa ba sai kai" Dr Khalil yace "We have 19 more wards ahead Doctor" MD din yace "Therapeutic procedure?" Nan ma Dr khalil ya karanto masa within few seconds, MD din yace "Any medical History?" khalil ya sanar masa yana duban file din still, karasawa MD din yayi feeling the girls temperature ya duba ta da stethoscope din wuyansa, bayan few seconds ya kalli Mayraah a takaice yace "Give her the injections" Daukan alluran tayi ta nufi kusa da yarinyar zata yi mata amma sai abun yayi mata kamar bata taɓa yi ma kowa allura ba kamar ranan zata fara ga kuma kukan da yarinyar take ya gigitata, MD din ya kalli Dr Khalil a bit pissed off yace "Why is she so sluggish? Wannan ta san aikinta kuwa?" Dr Khalil zai amshi alluran ya dakatar da shi furiously yace "What for?" Mayraah ta masa wani kallon gefen ido bayan ta ɗan daure fuska, nan dai ta tsaida hankalinta waje daya tayi ma yarinyar alluran, ficewa yayi daga ward din Dr Khalil ya bi bayansa. Karfe biyar wata senior nurse ta sanar ma nurses dake reception da za su yi ma yan evening handing over cewar su jira akwai meeting, yan evening na zuwa to su yan morning za su shiga meeting din da director a meeting room dake cikin asibitin, the next day kuma kafin yan evening su tafi za su yi nasu meeting din. Mayraah ta fito daga wani ward Dr Khalil ya nufota yana kallonta yace "Kiyi tafiyarki gida kawai ba sai kin yi attending meeting din ba Ilham, beside he doesn't even have ur data for now sai na basa, after the meeting i will be coming back home too" Mayraah taji hankalinta ya kwanta don dama tun da Matron ta sanar masu da batun meeting ta rasa sukuni, ita in son samu ne ma bata son ko wani irin encounter ya hadata da wnn MD din har sanda zai koma, kawai taji kwata kwata bai mata ba she don't like him, he is rude and arrogant sannan ta ga alamar ya iya disgi, Ta langwabar da kai tana kallon Dr Khalil tace "Toh shikenan, sai ka dawo" Yace "Hope kina da cash dai?" Tace "Ehh ina da, thank you" Ko minti goma bata kara a asibitin ba ta dau jakarta ta tafi bayan taje tayi ma Nurse Hafsat sallama a injection room, tana fita nurses din reception suka fara kus kus a tsakaninsu ganin ta tafi bayan ance akwai all staff meeting, dama tun da aka lura da yanda wasu daga likitocin asibitin ke yaba mata shkkn aka fara mata hassada kiri kiri don wasu ko magana basa mata a asibitin ita kuwa ko sanin suna yi ma bata yi ba tunda ba wani surutu take ba ko hira, tsakaninta da su gaisuwa shi ma wasun su sai suyi kamar basu ji ba, asibitin da ko kwana goma bata yi cikakke da fara zuwa ba, hatta yanda Dr Khalil ke kiranta office da kuma yanda Dr Balogun ke interacting da ita ya tsaya ma da yawansu a wuya, wata nurse fa'iza tana kallon colleague dinta murya can kasa tace "Wato ita shafaffiya da mai bazata tsaya meeting din ba kin ga ta dau jakarta ta tafi, tabdi bata san MD bane, ta zata irinsu Dr Khalil da Dr Balogun ne ko Dr Hamid dake shining mata hakora, muna nan dake wallahi sai MD ya gane bata shiga meeting din ba, sai in dai basu hadu a asibitin ba wannan mayen, zan ga ko shi ma kwarkwasan zata dinga masa yanda take ma sauran likitocin, Allah Ubangiji ya sa ya disgata gaban kowa da kowa mu ga iskanci, ko su Dr Khalil din da Dr Balogun babu abinda za su iya yi in ba haka ba ya hada da su" Nurse Victoria tace "The thing tire me my sister, ke daga zuwanki sai wani feeling kanki kike kin zo kin samu mutane a waje ki dinga wani ciccin magani kina daga masu kai wai ke me kokari, who does that?" Nurse Bola dake jin su tace "Fatana kawai yana ganinta after all the meetings ya gane bata shiga ba, a nan zata ga ikon Allah" Suna hango Nurse Hafsat duk suka yi shiru. Mayraah na isa gida ta tadda Ummi zaune parlor tare da Zainab matar Khalil da kanwar Ummi warce ake ce ma Aunty Rabi'ah, tun zuwan ta gidan sai ranan taga Zainab ta zo, ta karaso ta zauna ta gaida Ummi da Aunty Rabi'ah sannan ta gaida Zainab din ma, kallo daya Zainab tayi mata ta kauda kai ta amsa, Mayraah ta mike ta shiga dakin da take, Sai da Ummi ta ji ta kulle kofa sannan ta kalli Zainab tace "Wannan wani irin amsawar walakanci ne Zainab?" Zainab tace "Walakanci kuma Ummi, ta gaisheni kuma ai na amsa" Aunty Rabi'ah tace "Wai Ummi har yanzu bata samu gidan bane, last week da na zo ce min kika yi gida take nema fa, wannan ko sabon gidan da aka gama ginawa take so ya ci ace ta samu yanzu dai" Ummi tace "Bata samu ba, kuma baza a samun ba ma" Aunty Rabi'ah ta kyabe baki tace "To Allah ya kyauta" Har bayan magrib Mayraah bata fito daga daki ba, cause impression din Zainab duk sai yayi weaken dinta gaba daya, Mimi ce ta shigo dakin tana kallon Mayraah tace "Aunty Ummi tace in kira ki" Mayraah tace "Toh" Mikewa tayi daga kan darduma ta fita zuwa parlor, Ummi kadai ce zaune parlon, Mayraah tace "Ga ni Ummi" Ummi tace "Naga baki debi abinci ba" Mayraah tace "Ina jiran ayi isha ne" Ummi tace "To ai lokacin ma ya gabato, Inna na tambayarki nace kin dawo kina hutawa ne a daki" Mayraah tayi murmushi dai dai nan aka yi sallama kofar parlon, Ummi ta daga kai tana kallonsa da mamaki tace "Aa... kai kuma daga ina haka? 5 weeks din kenan?" Juyawa Mayraah tayi gabanta ya fadi lokaci daya ta dauke kanta da sauri.

Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa bello jidda

Ur evidence via 07087865788

INA MATA MASU AJI, BA ‘YAN RAKIYAR MATA NAKE NEMA BA. SHIN KINA DA LABARIN COMPANY DINNAN NA APHRODISIAC MA’ANA KAYAN MATA WATO *HONEYDROPS* DA KE GARIN *SOKOTO* SUNA DA INGANTATTUN KAYA DA BA SU DA NA BIYU WANDA SUKE DAWO MIKI DA MARTABARKI TA MACE KI DAWO TAMKAR BUDURWA ‘YAR SWEET 16, SUNA DA ZAFAFAN KAYA DA SUKA HA’DA DA *INFECTION FLUSHERS, BREAST FIRMING AND ENLARGEMENT PRODUCTS, HIPS AND BUTTS PRODUCTS, DIFFERENT TYPES OF WETNERS, VARIETIES OF SWEETENERS, VIRGINITY BACK PRODUCTS WATO TIGHTENERS *(MA’ANA AKWAI KALOLIN KAYAN QARIN NI’IMA, QARIN DADI, QARIN DANDANO DA KUMA MATSI NA BAN MAMAKI), SANNAN KAYANMU NA DA HADIN SINADARAN DA KE SAKA MALLAKA DA SOYAYYA A ZUCIYAR MIJI*

KAYANMU SUN HA’DA

*INFECTION FLUSHER*
*ORIGINAL SABAYA*
*ECHOES OF FOREVER*
*MOWA’S SECRET*
*HER ROYAL HIGHNESS*
*ETERNAL FLAME*
*SUGAR QUEEN* DA SAURANSU. KI HANZARTA SAVING LAMBATA KI KUMA YI MIN MAGANA DON SIYE KO SARI KO KUMA KASANCEWA CIKIN MASU SA’AR SAMUN KAYANMU A KYAUTA YAYIN DA MUKA YI GIVEAWAY. ZA A IYA TUNTUBARMU A LAMBOBI KAMAR HAKA 08167888934 KO KUMA 07026039714. KO A SHIGA LINK DOMIN MAGANA DA MU KAI TSAYE wa.me/+23481678888934

*MUNA MARABA DA KU, MUNA GARIN SOKOTO MUNA AIKE KOWANI GARI KOWACCE QASA CIKIN AMINCI*

54
Karasowa cikin parlon yayi yace "Ina wuni Ummi" Ummi tace "Lafiya lau, ko dai dama baka tafi ba?" Ya ɗan yi murmushi yace "Ban tafi ba kuma? Bayan har vid call mun yi 2 days back Ummi" Ummi tace "To na gan ka ne kamar an jefo ka ai" Sai a sannan ya ga Mayraah da kanta ke sunkuye kamar munafuka, lkci daya murmushin dake fuskarsa yayi fading, kallon Ummi yayi ya sake kallon Mayraah, kamar tasan kallon nata yake ta daga kai da sauri tace "Ina yini" Still looking at her yace "Lafiya lau" Ummi na kallonsa tace "Bakuwa ce" Yace "Oh ohk" Barin parlon yayi zuwa dakin sa, yana shiga ya ciro waya yayi dialing number Ahmad. Gaba daya Mayraah ta kasa cin abincin da ta debo a kitchen, duk ta rasa wani tunani zata yi, shi ma wannan mutumin gidansu ne nan kenan? She still vividly remember his face, Maida abincin gefe tayi ta jinginar da kanta da gado tsabar yanda ta zama confuse. Ana idar da isha mai aikin gidan ta zo tace mata Inna na kiran ta, ta mike ta saka hijab dinta ta fita, babu kowa parlor ta shiga dakin Inna da sallama murya can kasa, sosai gabanta ya fadi ganin Zainab, Dr Khalil da shi mutumin da ko sunansa bata sani ba su ma suna dakin inna, ta karasa ta zauna kasa tana kallon Inna tace "Inna ina yini?" Inna tace "Lafiya lau, naji shiru shiru baki shigo kin zubo min sabon ruwa a flask ba shine nace ko kema kin fara canza hali ne, ko kuma yan gidan sun fara canza maki ra'ayi" mikewa mutumin yayi ya fita daga dakin, Mayraah tayi murmushin karfin hali tana kallon Inna tace "Bari in kawo maki" Zainab dai sai danna wayarta take, Mayraah ta dau flask din ta fita daga dakin, Dr Khalil ya mike ya fita Zainab ta bi sa da kallon gefen ido. Mayraah na kitchen bayan ta kunna gas zata daura ruwan flask din aka bude kofa, ta juya da sauri ya shigo yana kallonta yace "U told me admission kika samu a Abuja? Aikin me kuma kike yi a asibiti yanzu?" Kallo daya tayi masa ta dauke kai ta ci gaba da abinda take tace "Admission din bai yiwu ba" yace "Why did u change ur name from the Mayraah u said at the hospital to Ilham?" Ta kallesa tace "Kaga kai ma ba dai dai ka fada sunan ba yanzu haka, so sbda irin wannan issues din yasa ake kirana Ilham most of the time" Yace "Really?" Tace "Yeah" Yace "Ohk, welcome to our home Ilham" yana fadin haka ya juya ya fita ta bi sa da kallo, wani boyayyen ajiyar zuciya ta sauke ta ci gaba da abinda take, ko da ta je kai ma Inna ruwan zafin ta tarar har Zainab da Dr Khalil sun tafi gida, ita ta ga kamar ma shakkar matar tasa yake wai ko magana bai mata ba saboda Zainab din na wajen, Inna na kallonta bayan ta ajiye flask din tace "Kin ga jikana Ahmad ya dawo daga kasar turawa ko, to shi ne babba a gidan kuma sa'annin juna ne da Halilu, shima kuma Halilun ɗan gida ne duk da ba jininmu bane shi amma ya zama ɗan gida, sai wannan mata da ta bari tayi kiba dazu da kika shigo tana zaune can tana latse latsan waya sunanta Zainab yanzu haka tana da yan biyu mata, saboda yabawa da kyawawan dabi'un Halilu, marigayi ubanta ya ba Halilun auren Zainab, kinsan ni na haifi uban nata, Allah dai ya ji kansa, Bayan Zainab sai yan biyu maza Hassan da Hussaini kullum sai su zagaya bayan windan nan su isheni da buga kwallo wai kar in huta, sai figgiyar yarinyar nan Fatima bata da aiki sai raye raye, duk Zuwaira ce ta haifesu, in ma kika ce ba ita ta haifi Halilu ba to ranta baci yake" Mayraah dai sai kirkiran murmushi take don ta kagu ta bar dakin, daga karshe ta samu ta sulale tace mata zata je tayi wanka.
Musharraf na kwance dakinsa da safe Mami ta shigo, yayi mata kallo daya ya kauda kai, mancewa ma yayi bai kulle kofar ba bayan ya dawo masallaci, ta karaso cikin dakin ta zauna gefen gado tana kallonsa tace "Musharraf" Ya kalleta bai dai ce komai ba, ta kai hannu forehead dinsa tayi kasa da murya tace "Yanzu baza ka cire ma kanka damuwar nan ba Musharraf kayi facing reality" Ya ki kallonta balle yace komai, ta sauke ajiyar zuciya tace "Ta shi mu je kayi breakfast" Mikewa zaune yayi ya matsa daga kusa da ita yace "Mami duk ke kika ja wannan abun, u caused everything, da kin bari mun yi aure tun wancan lokacin she wouldn't have gone missing now, yanzu wa

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login