Showing 234001 words to 237000 words out of 452169 words
Chapter 79 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar
hands, yana ganinta ya ajiye jakar keeping a straight face, ya kwashi wasu files kan table din Khalil, Mayraah ta kasa cewa komai don tsabar mamaki, to me yake nema a jakanta? Kofa taga ya nufo ta koma gefe tana kallonsa da mamaki tace "Meye kake nema a jakana?" Yace "Ohh jakarki ne ashe, ai na zata na Khalil din ne" Daga haka ya fice daga office din ta bi sa da ido, da sauri ta tafi gun jakar nata ta bude tana duba ciki, wayarta ne a ciki sai Atm card da glasses dinta, with oil perfumes, to me yake nema, is he even okay? Zaunawa tayi still tana searching jakan har sannan mamaki ya kasa barin ta, kenan a office dinsa ta bar key din. Sai kusan karfe daya Dr Khalil ya shigo office dinsa, Mayraah ta mike tana kallonsa tace "Uhnn I've waited all day" Dr Khalil yace "Wallahi muna fitowa kuma MD ya kirani office dinsa, kin samu kin ci abinci ma kuwa?" Mayraah ta dau jakarta tace "Dama kai kawai nake jira driver har ya zo yana jirana a waje, idan naje gida zan ci" Yace "Ohk, ina jin yayi imputing data dinki, so u are going to write me down ur account details, ur shift is from 8am to 6pm For now, resume work next week Monday" Mayraah na kallonsa tace "Ohk, thank you" Yace "Scrubs dinki kamar suna can gidan Ummi, so zan dauko maki a office din MD yanzu tunda kin ce driver yana jiranki...." Daga haka ya fita daga office din zuwa na MD, yana shiga MD dake tattara laptop dinsa da wasu textbooks yace "We are leaving together with Ceo now, idan an ajiyeta bazan dawo nan ba, sai after the workshop, na kai mata list din da muka yi creating na Dr's da 3 nurses da za aje Lagos din gobe, pls ka taho min da motata gida anjima...." Dr Khalil yace "Kana gida ai da daddare?" MD ya kallesa yace "Ka manta za mu fita tare da daddaren zuwa hotel din da frnds dina turawa suka sauka, kasan ban cika son driving at night ba, sorry for always inconveniencing you pls" Dr Khalil yayi murmushi yace "Su abokan naka turawa me yasa basu sauka gidanka ba?" MD zai yi magana Ceo ta shigo da list din da ya kai mata tana mika masa ya taho ya amsa da ladabi, tace "I saw just 3 nurses in the list, why is that?" Ya sunkuyar da kai yace "We chose just them Ma'am" Tace "Why not make them 4, include Mary Ann to the list pls" Ya daga kai yana kallonta da sauri, sai kuma ya ɗan shafa kai yace "But Ma'am, babu ticket for that same flight... Sai dai wani jirgin, wannan da muka yi booking jirgin ya cika, sai ma da muka yi contacting dinsu suka soke wasu ticket din aka samar mana 10 din da muke bukata...." Dr Khalil ya saki baki yana kallon MD don ko booking ticket din basu kai ga yi ba tukunna, Ceo tace "Ohk, that's fine" Daga haka ta juya ta fita daga office din, Dr Khalil na girgiza kai yace "Ka ji tsoron Allah Dr Aliyu, what's there idan anje workshop din da ita, ai ire irensu ma ya kamata...." Dakatar da shi MD yayi yace "Baza ta je ba, yaushe ma aka bata cikakken aiki a nan din da zata je workshop din manyan likitoci a Lagos, wa enda suka yi shekara da shekaru a nan ma basu je ba sai ita mara kunya da ko fara aikin bata yi ba" Dr Khalil yace "Toh dai Ceo da kanta ai tace aje da ita kuma ta san sabuwa ce" MD yace "To ni kuma as the MD of this hospital nace banda ita, baxata je ba, kuma abinda baka sani ba ni ba full employment na bata a asibitin nan ba, she will just work as an Intern in here, not a staff, beside ko service fa bata yi ba daga amsan statement of result kawai sai aiki?" Dr Khalil yace "Thank God dai ba government hospital bane nan din balle kace, kuma wannan kamar bakin ciki kake mata...." MD yace "Shi din ne ma" Juyawa Dr Khalil yayi zai fita, MD yace "Book the flight immediately pls... 10 seats" Dr Khalil yace "Ohk" Daga haka ya fita ya kulle masa kofa. Yana komawa office dinsa yace "Mayraah if it's okay anjima idan na amso su daga gida Ummi ko da daddare ne sai in kai maki gida, cause kamar babu scrubs din available yanzu" Mayraah ta mike tace "Ohk nagode" Yace "You are welcome, ki gaida su Ammi" Tace "Za su ji" Daga haka ta fita daga office din don tun dazu Drivernta ke waje. Wajen karfe biyu Mayraah ta isa gida, tana bude kofar parlon ta ga Usman a zaune shi kadai, sau biyu yana daga kai yana kallonta wanting to be sure ita din ce, ta karaso parlon ta ɗan yi murmushi tace "Yaya yaushe ka zo?" Ya hade rai yace "Yaushe kika fara wannan dressing din in zaki fita?" Tayi kasake tana kallonsa, can ta zagaya inda yake zaune, ya dinga kallonta daga sama har kasa, tace "Yaya me ya faru da dressing din?" Yace "Tambayata kike? Ok barin hijabs din naki kika yi a kano kenan?" Ta ɗan turo baki tace "Yaya Abaya ce fa ba wani abu ba, beside....." Calmly yayi shutting dinta yace "Keep quiet" Ammi ce ta fito daga kitchen ta tsaya tana kallonsu, A nutse yace "Kar ki sake wannan dressing din a gidan nan, were you trying to get someone impressed a hospital din?" Ammi tace "Ban gane kar ta sake wannan dressing din ba, meye da shigar tata da bazata sake ba?" Ya ɗan daga kai ya kalli Ammi don bai ma san ta fito daga kitchen din ba, Mayraah dai sai turo baki take, can dai yace "To gidan biki za ta Ammi, haka ake zuwa interview dama?" Ammi tace "Aa ba ruwanka, let her dress the way she wants as far as ba wando ta saka ta fita ba, meye laifin Abaya?" Mikewa yayi ya bar parlon ya shige daki, Mayraah ta bi sa da kallo, Ammi tace "Rabu da shi ki tafi kije ki yi wanka ki sauko ga abinci na gama" Mayraah ta gaisheta a hankali sannan ta wuce sama, wajen karfe uku ta sake saukowa downstairs bayan tayi wanka tayi sallah sannan ta canza kayanta, dinning area ta tafi ta debi abincin da Ammi ta ajiye a nan, spoon daya ta ci, sai kuma kawai ta mike ta nufi dakin da taga Usman ya shiga dazu, a hankali tayi knocking kofar dakin, tana ta tsaye taji ya bude kofar ta daga kai tana kallonsa, sai kuma ta bi ta gefensa ta shiga cikin dakin ta juya tana kallonsa ta marairaice tace "Yaya did i dress indecent?" Kulle kofar yayi ya koma ya zauna, ta bi bayansa tana kallonsa, yace "Amminki ta ce ba indecent bane... She gat your back" Murmushi tayi ta durkusa gabansa tace "Toh kayi hakuri yaya bazan sake ba, kuma ma ai uniform zan dinga sa wa ba kayan gida ba daga yau" shi dai kallonta kawai yake, ta mike tace "Have you eaten?" yace "Yeah" Tace "Toh zan je in ci abinci" Daga haka ta juya zata fita yace "Mayraah" Juyawa tayi ta kallesa, ba haka nan duk brothers dinta ke kiran sunanta kai tsaye ba, yace "In kin gama abinda kike yi da daddare ki shigo za mu yi magana" Da mamaki take kallonsa wondering maganar me za su yi, sai kawai tace "Toh in sha Allah" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita. Bayan magrib Mayraah na zaune kan darduma wayarta ya fara vibrate ta dauko a zaton ta Maheer ne don tayi masa kira har biyu bai yi responding ba, Dr Khalil ne ke kiranta, ta daga kiran bayan sun gaisa yace "Na dauko maki Scrubs din a gidan Ummi, can i come over yanzu in kawo maki, kin san za mu je lagos gobe da safe and probably monday za mu dawo" Mayraah tace "Ohk to Nagode" Yace "Address din fa?" Tace "Bari in tura maka" Katse wayar tayi ta tura masa address din, bayan minti sha biyar ya sake kiranta yace gashi a kofar gida, mikewa tayi sai da ta fara zuwa ta gaya ma Ammi sannan ta fito daga gidan sanye da hijab dinta har kasa, tana ta kallon motar wondering ko ya canza mota ne, ta dai karasa ya sauke glass din yana kallonta da murmushi yace "Good evening" MD ta gani zaune front seat ya wani hakikance, Dr Khalil ya sauko daga motar ya zagayo back seat ya dauko mata uniform din ya mika mata yace "Sai fa da yan sanda suka tsayar da mu kafin mu shigo nan, wai wajen wa za mu" Mayraah tayi murmushi tace "Sai kace masu wajena mana" Dariya yayi yace "Eh lallai kam wajenki" can yayi kasa da murya yace "Baki gaida boss dinki ba Hajiya" Mayraah ta sake kallon MD da yayi kasa da kai yana kallonta ta Mirror, don unguwan haske tarrr kamar da rana ko ina fitilu ne, yana ganin ta juyo ya dauke kai yana danna waya with a serious face, a takaice tace "Ina yini" jin bai amsa ba Khalil ya karasa har kusa da door din motar yayi knocking yace "Ana gaisuwa Oga" MD yace "Dalla ka zo mu tafi kana bata min lokaci kasan ana jirana" Mayraah na kallon Dr Khalil tace "Nagode Dr sai da safe" Ya mata murmushi yace "Ki gaida su Ammi" Tace "In sha Allah" Daga haka ta shige cikin gida, Dr Khalil ya zagaya ya shiga driver seat, MD ya kallesa yace "Burin ka kawai ka dinga ja mana raini wajen yarinyar nan, yanzu sai ta ga kamar biyoka nayi fa in her stupid mentality, ji wani iyayi da take, to meye da Unguwan nan?" Dr Khalil yace "Aa bawan Allah, sai da nace in ajiye ka eatry ka jirani in zo in kawo mata sakon kafin in koma in daukeka muje inda za mu kace no way sai ka biyo ni" MD yace "To ni ɗan iska ne zan yarda ka ajiyeni eatry ba abinci nake ci a eatry ba?" Dariya Dr Khalil yayi yace "To nan dai ne gidansu incase....." MD ya kallesa yace "Incase what?" Dr Khalil na murmushi yace "Incase Watarana mana" Mayraah na komawa dakinta ta dau wayarta taga miss calls din Maheer, murmushi tayi har zata kirasa sai kuma ta tuna za su yi magana da Ya Usman kamar yanda yace mata dazu, ta ajiye wayar with the intention of calling him back idan ta dawo, sannan ta sauka downstairs ko hijab dinta bata cire ba ta nufi dakin da ta gansa ciki daxu.
Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah
Ur evidence via 07087865788
71
Mayraah na isa kofar dakin tayi knocking, after a while ya bude kotar, shi in dai aka masa knocking baya bada izinin shigowa sai dai ya tafi da kansa ya bude kofar don bai fiye son ana shigo masa daki ba, she is already used to that, tana ganin ya bude kofar ta bi gefensa ta shiga ciki ya bi ta da kallo sai kuma ya kulle kofar ya karasa ciki yace "But i said later in the night" Mayraah ta zaro ido tace "To yanzu yaushe ne yaya? Everywhere is dark already" Zaunawa yayi yana ci gaba da abinda yake yi a laptop yace "Ai ba ayi isha ba" Ta turo baki tace "Yaya ni dai i am eager in ji maganar me zaka min, is it about my dressing dazu?" Ya kalleta yace "Ai Ammi tace dressing din ya maki kyau" Murmushi tayi tace "In dai shine ni dai kayi hakuri, nace maka bazan kara ba" Yace "Ba shi bane" Tayi shiru tana kallonsa, ya kashe laptop din ya ajiye yace "I just want to know what ur next plan is.... 2 years back kinyi saukan Al-qur'ani, this year kin yu graduating from university, immediately after graduation kin samu aiki, so what do u have in mind next?" Ta dan yi murmushi ta sunkuyar da kai tace
"Kamar me fa yaya?" Yace "Ko iyakar burinki kenan a rayuwa?" Ta daga kai a hankali ta kallesa, she wish zai gane yanda ta zama desperate ta hadu da nata relatives din ko da guda daya ne, bata son ta zama an ingrate shi yasa take kauda tunanin nan ko da yaushe a ranta bata basa mafaka ba balle ya dameta, amma God knows in this few months har cikin zuciyarta tana son sanin ko da mutum daya ne a jininta, sauke idonta tayi bata ce masa komai ba, a hankali yace "Kinyi shiru" Tayi gathering courage tace "Duk wani abun Alkhairi will always be among my wish everyday
Yaya, ba ni kadal ba kowa ma ina masa tatan abun alkhairi ya same sa kullum" Yace "Mayraah" Ta daga kai ta kallesa yace "So in ur wish there is nothing like marriage?" Ta dan buda ido, sai kuma tayi murmushi ta sunkuyar da kanta tace "Ai lokaci ne yaya, idan Allah ya kawo lokacin za ayi" Yace "Tell me the truth, is there anything between u and that Dr? I mean Dr Khalil" Mayraah ta zaro ido tace "Not at all wallahi, shi da yake da mata da yaransa biyu" Usman yace "Ohk ba a auren me mata?" Tayi dariya tace "Aa nima ban sani ba" Yace "Baza ki iya auren mai mata ba kenan?" Ta sunkuyar da kai tace "Ni dai ba ruwana" Yace
"Abokina me mata ya ga hotonki yace yana so yanzu baza ki iya aurensa ba kenan?" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta turo baki bata ce komai ba, yace "Am serious" Shiru tayi tana kallon sa, ya sauke idonsa yace "Wasa nake bai da mata, he is single, a Barrister too, are u interested? maganar da za mu yi kenan dama" Nan da nan jikinta yayi sanyi don Musharraf ne ya fado mata, Shi dai Usman kallonta kawai yake examining her reaction at the same time, bayan few seconds tace "Yaya i don't think i will love again...." Hawaye ya cika idonta ta fara gogewa da sauri, shi dai yayi shiru yana kallonta, can yace "Mayraah" ta daga kai ta kallesa tana share idonta, yace "Why won't u love again" Ta fashe da kuka tace "I don't want to remember the pass, ko ma waye zai aureni yanzu dole sae ya fara sanin ko ni wacece, after that no parent will want their blood to marry me" Yana kallonta a hankali yace "Har Ammi da Abba?" Daga kai tayi ta kallesa as if trying to apprehend what he meant by so saying, Bai bata wannan space din ba yayi saurin cewa "Forget that pass u are talking about and concentrate on the future Mayraah" Ita dai bata ce komai ba sae kallonsa take, yace "So i will want you to give this guy a chance" Nan ma dai bata ce komai ba, yace "Banda kula kowa kuma" Tayi murmushin karfin hali bata dai ce komai ba, yace
"Promise me that" Ta kallesa kamar yasan abinda ke running a mind dinta yace "Kin dai san bazan yi abinda zai cuceki ba ko?" Ta sauke idonta, yace "So now make that promise baza ki kula wasu ba" Ta gyada masa kai tace "In sha Allah" Yace "You can leave" Mikewa tayi ta nufi kofa ta fita wasu hawayen na taruwa idonta ta koma dakinta. Wajen karfe tara bayan tayi wanka ta kira Maheer, Haseenah dake parlon ta mike jin wayarsa dake ajiye kan kujera na ring, shi kuma yana kitchen yana hada shayi, kallon screen din wayar ta dinga yi taga an sa Mimi with love emoji, ta dinga kallon wayar babu kyaftawa har ya fito daga kitchen, ta juya ta shige daki, ko kallon inda ta bi bai yi ba ya dau wayarsa bayan yayi picking Mayraah ta gaishesa, ya zauna yace "Ina kika shiga?" Tace
"Kai dai zan tambaya, bayan tun dazu nake ta kiran wayarka" Yayi murmushi yace "Wayar na silent kika kira dazu, ya kike?" Tace "Alhamdulillah, ya aiki" Yace
"Cool, kin je interview din yau?" Tace "Na je" Yace
"No issues?" Kai ta gyada masa kamar yana ganinta, sai kuma tace "Ka fara processing transfer din naka yaya?" Yace "Not yet" ta dan hade rai tace "Do it soon pls, ko baka missing dinmu" Yace "I will try Mimi, ina missing dinku mana, ina Ammi?" Tace "She is in her room, Mama Ladi ta tafi ne?" Er dariya yayi yace "Jiya na kai ta har karayen wai bazata iya zaman motar haya ba" Mayraah tayi murmushi tace "Ayya, yanzu yaya idan ina son magana da sis Badiyyah ta ina zan sameta?" Maheer yace "I don't really know" Tace "I tried calling her lines severally amma duk a kashe" Yace "May be ta kashe wayar ne" Mayraah tayi shiru, shi ma haka, bayan few seconds tace "Pls try and request for the transfer kaji yaya" Yace "I will do so starting from tomorrow in sha Allah Mimi" Tana murmushi tace "Yauwa yayana, i want to go to bed now" a hankali yace "Alright Dear, sleep tight" Tace
"Bye" Daga haka ya katse wayar, ya ajiye ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, tun da suka koma Abuja sai dai ya sha tea ko coffee, idan ya fita kuma ya biya restaurant ya ci abinci, kana ganinsa kasan he is not himself, a da yayi niyyar ko zai nemi transfer din sai zuwa nan da wata biyu ko uku, amma yanzu kam yaji bazai iya ba, damuwa yayi masa yawa, ganin daga shi sai Haseenah na kara saka masa damuwar nan, don haka dole ma ya nemi transfer din nan ko ta yaya ne ya koma wajen family dinsa soon. Ranan Sunday da yamma Mayraah ta gama shiryawa ta fito daga dakinta zuwa parlon Ammi, Ammi dake