Showing 288001 words to 291000 words out of 452169 words

Chapter 97 - Mayrah Complete By Khaleesat Haydar

ba kamar tana kokarin processing maganganun yayar tata, Ceo ta mike ta juya tana kallon su Ammi babu ko kiftawa, karasawa tayi kusa da Ammi tana tafiya a hankali tana share idonta kafin tace komai Ammi ta janye Mayraah daga jikinta a hankali, cikin sanyin murya tana kallonta tace "Go to her daughter...." Mayraah ta gyada ma Ammi kai, trying hard not to cry, sai kuma ta kalli Ceo wasu sabbin hawayen da take ta avoiding na taruwa idonta, Ceo ta sauke idonta ta kama hannunta ta nufi kusa da gadon da ita, sai da suka isa gadon Mayraah ta iya kallon matar dake zaune tana kallonta ko kiftawa babu, Ceo tace "Aaria this is ur baby gal, this is ur Maryam" Zaunawa Mayraah tayi kusa da ita tana kallonta, bata san sanda ta fashe da kuka ba a hankali ta daura forehead dinta saman shoulders dinta hawaye na sauka idonta, Aaria ta dinga kallon ceo dake hawayen ita ma, gently Aaria ta dago kan Mayraah tana kallonta, rungumeta Mayraah tayi sai a sannan ita ma ta rungumeta gam tana kallon yayarta, as if counting her words tace "Maryam dita ce?" Ceo ta gyada mata kai tana murmushin karfin hali tace "Maryam din ki ce" Kuka ta fashe da tana kara rungume Mayraah jikinta, Ammi ta sunkuyar da kanta tana share hawayen dake sauka idonta ta juya ta fita daga dakin Abba ya bi ta da kallo, bin bayanta Usman yayi, Maheer dai ya jingina jikin bangon dakin, cikin kuka Aaria dake kallon yayarta tace "Don Allah kar ki sake rabani da ita Aunty, na ce maki ina sonta a haka, wallahi ina son ta" Ceo ta zauna kusa da su tana girgiza kai tace "Bazan sake rabaki da ita ba Aaria, amma su ma wanda suka rike maki ita ai iyayenta ne, kin ga su ma baza ki rabasu da ita ba" Aaria dai kuka kawai take tana rungume da Mayraah tana kallon yayar tata, juyawa Abba yayi ya fita daga dakin MD ya bi bayansa, Maheer kam kukan da yake jin Mayraah take ne ya sa ya kasa fita daga dakin, after a while dai kawai ya juya ya fita. Abba suna zaune parlor yana kokarin calming Ammi dake kuka duk da bai ma san takamaiman kukan abinda take, Usman da ya zauna gefenta dai kansa na kasa, Maheer na zaune tare da MD ko wannensu da tunanin dake ransa, after a While sai ga Ceo ta sauko downstairs tana rike da hannun kanwarta sai Mayraah dake tare da su, Mayraah na shigowa parlon ta nufi Ammi tana tafiya a hankali, ta zauna daya side dinta ta jinginar da kanta jikinta ta lumshe ido, Ammi ta ja ta jikinta, Ceo ta sa kanwarta ta zauna two sitter sannan ta zauna gefenta, gaba daya idanuwan Aaria da hankalinta na kan Mayraah, Ceo na kallon Aaria tace "Say hi to them, su ne iyayenta da suka rike maki ita" Aaria ta dinga bin su da kallo wasu hawayen na taruwa idonta, sai kuma ta kalli yayarta cikin rawan murya tace "Yanzun ma tafiya za su yi da ita? Amma kin ce min watarana za ki dawo min da ita gaba daya" Ceo ta kasa cewa komai, kuka sosai Aaria take tana bin su da kallo gaba daya a parlon, Ceo ta goge hawayen idonta cikin sanyin murya tace "Appreciate them Aaria, they look after ur Maryam for 22 years now, in ma sun tafi da ita ai tun da har suka kawo maki ita nasan zata dinga zuwa ganinki, kema zaki dinga zuwa ganinta ko da yaushe, kin san karatu take yanzu..." Aaria dai sai hawaye take tana kallon Mayraah da taki bude ido a jikin Ammi, Calmly Abba na kallon Ceo yace "Sai dai baki karasa mana labarin ba...." Ceo tayi murmushin karfin hali tace "Mary Ann's father ko?" Abba ya sauke ajiyar zuciya don abinda yake son ji kenan, gaba daya su Maheer kallonta suke, Ammi ma kallonta take, A hankali tace "I will prefer in dauke ku gaba daya mu je har gidansu a garin da yake, kuma har da Aaria za mu je..." Abba yace "Me yasa kika ce haka?" Ceo tace "Hakan zai fi Alhaji, zan yi booking flight for us gaba daya, gobe da safe za mu je har gidansu, i don't want to call his name" Abba ya sauke ajiyar zuciya thinking if hakan dai dai ne, Bayan few seconds yace "Amma kina tunanin hakan bazai haifar da wata matsalar ba? Do u think it's necessary sai mun je har gidansu" Girgiza kai tayi tace "Not at all, ai har bibiyata yake a Uk, he wants me to connect him to Aaria ban kuma san dalilinsa ba, sai da na kira masa police wani lokaci suka ja masa boundary da ni sannan ya hakura ya daina bi na, don can kawai muke haduwa, tun bayan Incident din bamu kara haduwa da shi ko family dinsa a nan Nigeria ba" Abba yace "To shikenan, Allah ya kai mu goben" Aaria dai sai kallon Mayraah take bata ko kiftawa, Ceo ta kamo hannunta a hankali tace "Za su tafi da Maryam don za ta je makaranta yau, amma na maki alkawari zaki kara ganinta gobe" Aaria ta fashe da kuka a hankali tace "But that wasn't what u promise Aunty" Ceo na shafa girarta murya can kasa tace "I know my love, for now allow her to go to school, za ku kara haduwa gobe"
Har suka Isa gida babu wanda ya iya cewa komai a motar, Mayraah dai na rungume jikin Ammi, bayan Abba yayi parking Ammi ta bude motar ta sauka tare da Mayraah suka nufi cikin gida, Daga Usman har Maheer dai na cikin motar basu sauka ba kowa da tunanin dake yawo a zuciyarsa, Calmly Abba yace "Ina son duk abinda muka ji yau ya zamana sirri a tsakaninmu duka, duk da nasan halin ku, nasan abinda za ku aikata da wanda baza ku aikata ba, da Umar na nan nasan shi ma bazai taɓa fitar da maganar nan ba har a tashi duniya, amma duk da haka tunda baya nan ko shi bana so ya ji, ita ma mahaifiyar ku zan mata magana idan mun shiga ciki"

Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah

Ur evidence via 07087865788

89
Ammi na komawa bangarenta ta nufi Bedroom dinta direct tare da Mayraah ta kulle dakin ta zaunar da ita gefen gado ita ma ta zauna tana kallonta a sanyaye, Mayraah ta sauke idonta hawaye masu zafi na zubo mata, Ammi ta share mata idon muryarta na rawa tace "Bana son kina kukan nan daughter, this is our destiny altogether, don ba jarabawanki bace ke kadai, har mu, kuma dole mu amshesa hannu bibbiyu" Mayraah ta dake tace "Kawai kukan farin ciki nake Ammi, na kuma amshi kaddarata hannu biyu don being a muslim is one of the greatest thing that have ever happen to me in my life regardless of ta yanda aka sameni, ni nasan bazan taɓa iya canza kaddarar yanda Allah yayi zan zo duniya ba, who am i ti change that? it's already written, kuma ina farin cikin da Allah ya kaddara min rayuwa tare da ku har na zama cikakkiyar musulma, ina alfaharin kasantuwar ku iyayena da bazan taɓa replacing ba no matter what, Alhamdulillah ala kulli haal.... Alhamdulillah ala ni'imatil Islam.... Don da ace na tashi tare da warce ta haifeni duk da ance tana musulunci probability dina na zama musulma will be very low don yayarta zata iya fin karfinta a kai na, ko wannan kadai na tuna zan ci gaba da godiya ga Allah, and now i will have rest of mind nasan wacece ni...." Rungumeta Ammi tayi tana kuka tace "That is just it daughter, Allah Ubangiji ya maki albarka, and i am proud of ur faith, In sha Allahu daga yau kin daina kuka" murmushi Mayraah tayi tana rungume jikin Ammi. Bayan azahar Mayraah na zaune kan darduma a dakinta Usman ya shigo da sallama, ta daga kai tana kallonsa bayan ta amsa, kasa kallonta yayi ya karaso cikin dakin ya zauna, ita dai kallonsa kawai take, bayan few seconds ya sauko kusa da ita ya zauna saman carpet din a hankali ya kamo hannunta murya can kasa yace "You know what Mimi?" Tace "Sai ka fada yaya" Ɗan murmushi yayi jin reply dinta, a hankali yace "I want you to know that no matter the situation, no matter the circumstances you still remain our little Mimi, we still sees you as our blood" murmushi kawai take tana kallonsa, Bude kofar dakin aka yi duk suka juya, Maheer ne ya shigo dakin da sallama, yana ganinsu ya wara ido yace "Really?? What are my siblings up to?" Yana fadin haka ya karaso kusa da su shi ma ya zauna ya tankwashe kafa yana kallonsu both yace "Me ake yi babu ni?" Usman na kallonsa yace "I am just reminding her that we still sees her as our little cute sis, we still sees her as our blood... And all in all, we still love her as our lovely intelligent Mimi" Maheer ya daura hannunsa kan nasu yana murmushi yace "Ayi reminder din da ni" Er dariya Mayraah tayi cikin sanyin murya tace "And i see u both as my shield! today, tomorrow, next tomorrow, and forever.... I am proud to have u both and Ya Umar as my big brothers, ina alfahari da ku yayyina a ko da yaushe" Duk murmushi suke suna kallonta, ita ma tayi murmushin tayi pecking din hannunsu gaba daya. Sosai Ammi tayi mamakin yanda Mayraah ke ta harkan gabanta throughout ranan a gidan kamar babu abinda ya faru, hakan ya sa hankalin Ammi ya kwanta, sai dai fa can kasan zuciyar Mayraah tana jin tausayin mahaifiyarta amma ba wai don tana son kasancewa tare da ita ba. A ranan da daddare MD ya tura ma Maheer Flight ticket na Business class da Ceo ta sa yayi har kujeru takwas na tafiyar da za su yi washegari, flight din kuma na karfe taran safe ne, Mayraah na tare da Maheer da Usman a dakinsa tana basa labarin yanda ta ji a sanda ta ci poison, Usman dai danna wayarsa kawai yake yana sauraronta, Maheer dake kallonta attentively ya dau wayarsa jin shigowar message, ganin wanda ya turo masa message din ya shiga WhatsApp dinsa, Mayraah ta hade rai tace "Yaya kai ma danna wayar zaka yi baza ka saurareni ba" Dariya ta ba Maheer bayan yaga ticket MD ya turo masa ya mayar da wayar ya ajiye gefe yanw murmushi, Usman ya daga kai yana kallonta yace "Wa yace maki bana jin abinda kike cewa" Ta turo baki tace "Toh gaya min me na fada last in ji" Yace "Oho"
Abba ya gama shan shayin cup din hannunsa ya kalli Ammi, sai kuma ya ɗan yi murmushi yana girgiza kai yace "Sai kuma nace maki zan je in gaya ma Hajiya Amina wannan magana" A takaice Ammi tace "I don't know, and I don't even care to know, kawai ni dai nace maka in ma kana da niyya kayi hakuri kar ka fara, don wannan babban sirrin daughter na ne da ma mu kan mu gaba daya, bana kuma son zancen nan yaje ko ina, ina son ya kasance mun binnesa ne a inda muka ji sa har a tashi duniya babu wanda zai kara tada sa after tomorrow, duk da nasan halin yarana maza hakan bai sa na fasa jaddada masu ba" Abba yace "To kafin ki jaddada masu ni na fara jaddada masu, kuma na fi ki sanin muhimmancin binne maganar a inda muka ji sa, fadan ta ma a wani waje bashi da amfani ba kuma shi da fa'ida" Ammi tayi murmushi tace "Toh Allah ya sa mu dace" Washegari da safe wajen karfe bakwai da rabi Ammi ta shigo dakin da Aunty Mariya da Mama Ladi suke, Ammi ta zauna ta gaida Mama Ladi, sannan suka gaisa da Aunty Mariya, Mama Ladi na kallon Ammi tace "Kin ji fa yau Mariya zata koma, nace mata ina lefin ta ɗan kara kwanaki kafin nan Mera ta ji kwarin jikinta, naga dai ko kwana biyu ba ayi da sallamanta a asibitin ba, ke ba miji ba yana can Legas sai sanda Allah ya kado sa" Aunty Mariya tace "Mama yau satina fa biyu a Abuja, banda muna asibiti ni na so ma mu koma tare da Hajja a sanda ta tafi, Mayraah kuma ai jiki sai dai mu ce Alhamdulillah" Mama Ladi ta kyabe baki ta gyara kwanciyarta, Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Nima yanzu shigowa nayi in ce maku za mu kaduna amma in sha Allahu yau za mu dawo, kin ga gidan ba kowa Mariya kiyi hakuri ki bari in mun dawo sai ki tafi" Mama Ladi ta mike zaune tace "Me za ku je yi a kaduna kuma?" Ammi tace "Alhaji ne yace za mu je kaduna, ina jin ziyara za mu" Mama Ladi ta gyara zama tace "To wa gareku a Kadunan? shi Mamuda ba mu kadai ne danginsa ba a halin yanzu? waye bai san bai da kowa ba, kullum mu ne dai ke fadi tashi akan matsala idan ta ɓullo a gidansa" Ammi ta mike tace "Bari in je in shirya Mama, jirgin namu na karfe tara ne" Mama Ladi tace "Toh Allah dai ya tsare, kilan wani sirrin za ku je kuyi a can bakin ku alekum, Allah de ya kyauta, dazu ma naga ai kun fita, dama fatanmu Mera ta samu sauki kuma ta samu, nan da kwana biyu in sha Allahu nima sai in san inda dare yayi min, na lura yanzu Mamuda kora da hali yake mana, banda haka ni dai wllhi nasan bashi da kowa a Kaduna" Ammi tace "To ziyara za mu je gidan abokinsa sun samu karuwa, yanzu dai hankalin ki ya kwanta dai ko" Mama Ladi tace "To Allah ya tsare" Ammi tace "Ameen" Kofa ta nufa Mama Ladi tace "Kin dai ji Badiyyah na can ranga ranga asibiti rai a hannun Allah wai ta zame wajen shiga bandakin Yahanasu, kinsan bandakin gidan Yahanasu ko na kasuwa albarka, ga uban gansa kuka, har wani yauki yauki bandakin yake wllh, abun dai ba arziki ko dake duk kun sani ai, ita fa Yahanasu tun muna yan mata take kazanta gashi ya bi ta har tsufa, ko ruwa baka iya sha in ka shiga gidanta sai in kai ma kazamin ne" Ammi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yaushe hakan ya faru?" Aunty Mariya ta numfasa tace "Da asuba aka kirani, ashe tun jiya da daddare abun ya faru" Ammi tace "Amma jikin da sauki dai ko?" Mama Ladi tace "Wuyarta ace mana tayi ɓari, kilan ma da gangan ta zame, ko da yake cikin shege ai kowa yasan naci ne da shi, ba wani zancen barewa" Ammi na kallon Aunty Mariya tace "Wa ke tare da ita a asibiti?" Aunty Mariya tace "Wai babbar jikar Yahanasu, sun kira Hajja tace masu ai ita bata garin ma, Yahanasun ma taki bin su asibitin, dole haka ni nayi masu transfer dazun nan wai za a kara mata jini, sannan she is unconscious, wannan ne ma yasa nake son in koma kadunan yau" Ammi tayi shiru ta ma rasa me zata ce, can ta sauke ajiyar zuciya tace "Shikenan, in sha Allahu zan karasa asibitin in mun je kadunan" Aunty Mariya tace "Toh Allah Ubangiji ya kai ku lafiya, wai har su Maheer?" Ammi tace "Eh har su" daga haka ta fita daga dakin. Ammi na kallon Abba bayan ya gama shiryawa, cikin sanyin murya tace "Yallabai ga wani suggestion da ya zo raina yanzun nan" Abba ya juya yana kallonta yace "Na me fa?" A hankali tace "Ni a nawa tunanin Yallabai why not mu bar Mayraah kawai ba sai mun je da ita kadunan nan ba, wallahi bana son abinda zai sake daga mata hankali duk da dai naga tun jiya bata saka damuwa a ranta ba, yau ma naga da walwalarta ta tashi ba wani damuwa, to kar mu je kadunan nan kuma ta samu heartbreak din da ya fi na jiya, i don't want my daughter to be hurt" Abba ya ɗan yi shiru yana kallonta, bayan wasu dakikai yace "Kar ki damu, in sha Allah abinda kike tsoro bazai faru ba, tun da kin ji me asibitin tace mutumin na ta bibiyanta a kasar waje yana tambayarta ita uwar Mayraah din, so wannan ne nima ya bani karfin gwiwan aje da ita, in sha Allah babu abinda zai faru sai alkhairi, we will go with her" Ammi sai da taji wani rass jin kalman da Abba ya fada wai Uwar Mayraah, sunan da ita ke ta bearing for 22 years now, a hankali Ammi ta sauke idonta tace "Toh shikenan" Abba yace "Hope duk sun gama shiryawa?" Kallonta Abba ya dinga yi jin bata ce komai ba, kuma bata ma san yayi mata magana ba, Abba yayi kasa da murya yace "To meye kuma damuwar? Gaya min menene kuma" Ta ɗan yi yake, sai kuma a hankali tace "And yallabai, sai jiya cikin dare abubuwan da suka faru suka dinga dawo min zuciyata, yallabai gaban wan Musharraf din nan fa aka yi duk wannan maganar? Wallahi da abun nan ya fado min cikin dare kasa bacci nayi, bai kamata ayi komai a gabansa ba, mun yi babban kuskure, kuma wannan kamar kara tona ma kanmu da ita Mayraan asiri muka yi, shi ma ai ba haka ake ba, family issue ne wannan da sai ya fita ya bamu waje, amma yana zaune duk ta bada wannan mummunan labarin shi ma yana ji" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Maheer da Usman sun min wannan maganar tun jiya, but ya muka iya? tunda kika ga tayi duk maganan nan a gabansa kinsan ta yarda da shi ne sosai and suna da kusanci da kyakkyawan alaka da shi, kin ga bayan da muka hau sama zuwa dakin ita wannan matar ai bata fara magana ba

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login