Murucin Kan Dutse
Chapter 16 of 146
tsigan lalashi ta san fitina ne ake da shi ga wayan.
Can taga yayi dan murmushi a fuskan yana cewa ke ma ai uwarsu ce zulfa don haka kiyi yadda ya kamata dasu mana.
Kofa likita bamu samu gani ba tukun ki ke wanan zance haka idan mun gama ai zamu dawo ne ko.
Bataji may tace dashi ba sai dai murmushin da taga yayi a fuskan yake cewa wata rana kema ai zaki bar naki a gurin ta ko ?
Don haka ki yi hakkuri kifitar da komai a ranki ina diyana diyan ki ne kema koda ba, a gida kike ba.
Can taji yace kwarai da gaske zulfa aiko ita kun san dalilin zuwan namu wannan lokacin ko.
Shiru ya dan ratsa falon yana sauraren mai maganan ta waya har ta taji shi yana cewa ok shike nan sai mun yi waya anjima ke nan.
Ya kashe wayan tare da dago kai yana kallon inda take zaune, ya dan yi murmushi .
Ya zauna gap da ita yana cewa yaya tafi mana ko kin kuma zauna anan ?
Ta dago idanuwan ta fuskan shi a cikin damuwa take cewa dashi akan yaran take magana ko ?
Bai bata amsa ba don yasan ranta zai kara baci ne ga banza yace tashi mu tafi ko ?
Da kyat ta mike tsaye ga dan matashin cikin dake a jikin ta ya turo a cikin rigan dake jikin ta.
Rai bace take magana tana fadin kaga abinda nake gudu ke nan tun farko nace ka bari na kai su gurin hibba su zauna har mu dawo amma kace wai a barsu su zauna agida tunda akwai mutane.
Ya jawo hannun ta yana fadin ke ma dai kin san bazan lamunci ina da gida da iyalina a ciki kuma na dauki diya na zuwa wani gurin ba.
Tace idan baka yarda an kaisu wani wurin ba ai gashi kana shan korafi akai ni dai tsorona kada a cutawa yaran da basuci ba basu sha ba kan zancen mu.
Haba Sa,ade Zulfa ce zata cutawa yarana kuma kada ki manta fa a matsayin yar uwa take a gareni fa.
Tace a da ke nan yanzu kan ai a matsayin diyan kishiya take daukan diyan ka gare ta.
Kofa ya bude masu suka fito daga gidan wani sanyi ne ya daki fuskan ta amma ba yadda ta iya dole haka zasu fita duk da tsananin sanyin da akeyi a garin
Don fitan ya zama masu dole sai sunyi shine dole zai sata fita a hakan.
Bayan sun gama da asibiti ne suka wuce zuwa wani shago nan ta dan yo sayayan abubuwan da ya dace ta tsinta har da tufafin yaran ta dana yaran abokan zaman nata.
Ko da suka dawo gida a gajiye take don bata da kuzarin da zata dinga tafiya haka mai nisa a jikin ta.
Zama yayi kasa a daidai kafan ta ya dan fara matsa mata su a hankali tana jin dadi hakan har cikin ranta ta dan fara lumahe idanuwan ta a hankali.
Haka yasa ta samu saukin yadda take ji a ran ta a lokacin sai bata samu wani matsala komai ba ga yadda take zato.
Washe gari ta riga shi sauko wa kasa don ta karya saboda yace yana son ya dan kara barci.
Har sai bayan ta gama ne sai gashi yau sauko kasan a lokacin har yai wanka yana saye a cikin kananan kaya a jikin shi.
Sau daya ta daga kai ta kalleshi taci gaba da duban wayan ta da takeyi tana murmushi a fuskan ta.
Da alama hiran da takeyi yana mata dadi a ran ta lokacin ya iso inda take yana cewa madam yaya jikin naki ?
Ta dan dago kan ta a hankali ta dube shi tana cewa Alhamdullahi ya kokari bai amsa mata ba sai da yakai zaune yace kokarin yiwa kaine ai nidai gurina naga Alllah ya rabaki da wanan cikin na jikin ki lafiya.
Sai lokacin tabar abinda take a wayan ta ta dago kan ta ta dube shi inda ya zauna sai suka hada ido dashi tayi saurin kawar da idon ta cikin nasa .
Yace No no no kada ki soma yi min wanan kukan naki dake tayar min da hankalina please ?
Yace cikin kamo hannun ta zuwa na shi cikin girgiza mata kai yake fadin ki dinga sakawa zuciyar ki dangana Allah daya baki ciki a cikin wanan halin da kike yasan dalilin yin haka a gare ki.
Don haka ki zamo cikin bayi masu rugumar kaddaran ubangijin su ako da yaushe.
Wanan tayar da hankalin da kikeyi zai iya kara jefa ki a cikin wani sabon tashin hankali kuma har mu dake tare dake abin ya shafi zukatan mu.
Ajiyan zuciya ta sauke tace dole na daga hankalina idan na tuna da lalurar dake tare dani sai ga shi kuma wanan cikin yazo ya shiga again.
Murmushi yayi tare da jawo ta ajikin shi yana dan shafa bayan ta yake cewa lafiya lau zaki haihu insha Allah ai ciwo ba mutuwa bane.
A hankali tace dashi abin ne ke bani tsoro sosai sai yake hanani sukuni a raina.
Ya girgiza mata kai yace ai abin bada ga nan bane heartbeat ke dai Allah ya kawo muna sauki ga al,amarin.
Sai da ya tabbatar ta kwantar da hankalin ta ya mike yana cewa zai dan fita amma ba zai dade ba indan ya fita.
Nan ya fice ya barta zaune zuciyan ta cike da tunanen yan diyan ta biyu dake gida Nigeria gurin kishiyan ta.
Tun ba akai ko ina ba gashi ta fara jin Zulfa din ta bugo waya tana korafi akan rikon yaran nata gashi zasu iya share wata uku basu koma gida ba.
Shine dalilin da tun farko taso zuwa da yaran ta ko tabar su gurin yar uwarta amma sai ya nuna mata rashin yardan shi ga hakan .
Don shi mutum ne mai matukar son iyalin shi a kusa dashi akoda yaushe haka ne yasa akwai shakuwa sosai tsakanin shi da italin shi don yana fitarwa kowa da hakkin shi yadda ya dace.
Wanan zuwan da sukayi dashi ba itace ya dace tabiyo shi ba amma saboda dalilin rashin lafiyan ta yazo da ita din.
Wanda kafin su zo saida akakai ruwa rana da sauran kishiyoyin nata akan basu yarda da hakan ba don acewa su yafi nuna kulawan shi akan Sa,ade da yaran ta bisa gasu.
Don har kara suka kai shi gurin iyayyen su kan abinda yake shirin yi masu.
Ita bata da ko labari sai dai ta fahinci ya dauki zafi da sauran matan nashi a lokacin.
Ita da ake abin akan ta sai daga baya ta fahinci rigiman akan tafiyan su ne akeyin sa.
Haka ne ya dan haifar mata da rashin natsuwa a tare da ita don haka ta bukaci da ajaye tafiya sai taga likitan ta na nan gida Nigeria.
Amma amma mijin tana yaki janye zancen ba irin rokon da bata mashi ba kan ya barta amma sai yaki yarda da bukatan ta.
Karshe ma cewa yayi da ita idan ke lafiyan ki bai damay ki ba ni ya damay ni tunda bake ce keda hasara ba ai .
Hakkuru ta bashi don yadda taga ya hau tasan itama zata iya samun nata rabon fitina a ciki don haka taja bakin ta ta tsuke tai shiru har lokacin tafiya yayi suka wuce.
Don makaran ta ne kawai yasa ta bar yaran ta a hannun kishiyoyin ta ba don taso ba don tana nan ma yaya aka kwashe da su balle bata kusa.
Ko ita Zulfa ba don Allah ta rike yaran ba don sai daya zube mata kudi masu yawa ta yarda zata zauna dasu din.
****** ********* ******
Na gama aikin da nake taya mama altine na kwashi kayan na aiki tare da kaisu bakin kwata na wanke komai fes na mayar na kife mama na zaune ta zuba min ido daga inda take zaune ta motsa furan data dama ta sha.
Ina yarfar da ruwan dakw hannu na bayan na dauraye kafana take cewa sannu Rahama ai kin huta ke bakajin kiyuyan aiki ko kadan.
Da ace uwarki lauratu ta gane haka ta nemi zaman lafiya dake a gidan dan wanan zaman da zakiyi a gida aida ta more maki sosai.
Na dago kai da sauri ina kallon mama nace kai mama matar da tun ina yar kankanuwa na fahinci bata kaunana yaya zan zauna da ita ta more min haka.
Ni fa yadda mama bata kaunana a sannu nima haka kiyayyan ta ya shiga har kasan raina wallahi.
Mutumin da zai iya maka sheri da kazafi aiko kasheka yana iyayi mama.
Bata kashe ki sai dai sherin ta ya koma mata baga diyan ta nan ba babu mashinshini a tare da su duk fa cikun mugun halin ta ne amma ita bata ganewa ne kawai.
Ki debi abinci kici kada yai sanyi gashi da zafin shi nace ba yanzu ba mama sai anjima kafin na kwanta don tunda na dawo gida idan Innata ce da girki a gidan mama altine nake kwanci na don nasan Mama bazata yarda da na kwana a dakin ta ba yadda muke din nan yanzu kamar annabi da kafiri ni da ita.
Muna nan muka ji sallaman dan wurin mama yana cewa Rahama wai kizo inji baba .
Nace yau baba lafiya ya dawo gida haka da wuri don nasa sai yamma lis da magariba yake dawowa gida.
Ban bata lokaci ba na figi hijjab dina zuwa kiran baban nawa da yake min ko da na shiga yana alwala zaiyi sallah na nufi inda yake zaune saman dutse na gaishe shi da dawowa.
Na samu guri daga gefen shi na tsugunna ina fadin baba gani .
Yace dan dajan ta min na rarage alwala na mike na koma gefe ina jiran idarwan shi har lokacin daya gama ya mike tsaye.
Sai naji yana kiran Lauratu lauratu, lauratu fa da dan karfi ta amsa daga daki da saurin ta tafito tana gyara daurin zanin ta.
Tana cewa lafiya dai malam wanan kira haka kamar zaka tsaga min kunne dashi.
Yace to ke ce din idan ba haka aka kiraki ba sai ki kyale mutum tsaye wani zubin.
Yace ina ita Asiya take inna dake bakin murhu tana kashe wutan da tai girki tace gani.
Yace to dama ba wani abu bane yasa nai kiran ku ku duka ukun sai akan Rahama gata nan.
Allah ya kawo mata mai nema a cikin sauki ba ko wani bane sai Malam Jatau na hayi dotse abokin maigidan ta marigayi.
Shine ya aiki min yau da safen nan akan yana son ta da aure ya hada ta cikin iyalin shi.
Don ya yaba da zaman ta gidan aminin nashi da tayi kwadayin hakan yasa yake sha, awan auren ta.
Wani irin dariya gami da guda mama ta ranga tare da cewa yarinyar tayi tagomashi ga tsofin gari.
Wani irin dam dam naji kirjina yaba da a lokaci guda cikin raina nace wani malam Jatau kuma can ai gara ma Alhaji garbati marigayi din shi a tsaye yake kyam ba irin malam Jatau ba dake tafiya a duke.
Gashi da dan banzan kazanta da rowa ko kiyashin gidan shi sun san shi da rowa da mugun halin.
Mama sai da ta gaji don kanta san nan ta tsagaita dariyan ta tana cewa injin ka bashi dai.
Yace ban amsa mai ba sai naji shawaran ku tukun akan zancen kafin na basu amsa ta.
Lalai ma malam yo may zaka tsaya jira da ita Allah ya kawo mata mai so da wuri haka ?
Yace ai komai sai a hankali akeyin sa tunda yanzu ita ba budurwa bace kin ga zama dan bata zabi ai ko?
Zabin may har nawa Rahama take da za, a tsaya neman wani zabin ta kudine dai akwaishi kaga sai taje taciwo muna nashi kasuwan kuma.
Ban san lokacin da bakina ya kufce ba nace ai kina da tan mata zuka zuka har uku a dakin ki kibashi mana.
Salati ta saka tare da saka kuka wai naci mutuncin ta a gaban uwaye na ai ba ita bace tasamin farin jinin tsofi balle naci mutuncin ta bakin halina ne dani da uwata ke bibiyan mu.
Da kyat baba ya lalashe ta ta koma dakin ta nikuma yai min fadan haka kaca kaca ya fice gidan.
Dakin Inna ta muka shiga kowan mu bakin ciki yana cin sa a rai da wanan sabon fitinan dake neman bullo muna kuma.
Nace wa Inna ta ni wallahi wanan karon ko kashe ni baba zaiyi ba zan yi auren nan ba ai bani kadai ce diya ba a gidan da zaita badani ga tsufin gari haka.
Inba tace kidai bi sannu ke ma kin san idan uwarku ta kafe sai ya bayar dake ko bakya so hakan.
Daga daki muna jin mama da yaran ta suna bidirin su cikin jin dadi har da shewan su.
Don su burin su dama shine suga bakin cikin mu nida uwata a gidan ga kuma wani dama ya sake samuwa gare su again.
Washegari koda na je gidan mama na kasa fada mata komai sai dai ta fahinci ina cikin yar damuwa a lokacin.
Ta tambaye ni nai mata yake kawai da cewa ba komai mama don ba ko wani sirin gidan mune zan dinga fada mata ba din yanzu girma yazo min na san wasu abu ba kowane zaka fadawa ba.
A kai sallama a kofan gidan mu lokacin baba ya fice zuwa kasuwa ba yara gida mama ta yafa ta fita.
Malam Jatau ne a cikin wani tsohon babban rigan shi daya takure don tsufa ga dauda taf ga kayan sai tsohon hular dake kan shi don tsufa har zaren hullan ya fara zarewa daga jikin shi sai shafin dauda daya kwanta akai.
Suka gaisa tana washe baki take cewa , a, a Alhaji Jatau ne sannu da zuwa .
Ai kuwa ba kunya mama take cewa har an fara zuwa zance ne gashi maigidan ya fita amma ba matsala bari a kira ma yarinyar ai tunda ina nan.
Ya washe bakin da duk goro ya bata shi yake cewa ikon Allah ashe kun san da zancen ke nan wallahi yabawa da halaiyar yarinyar don marigayi yana yaba hankalin ta.
Hakan yasa nai kwadayin saka ta a cikin nawa iyalin ko banza na taimakawa shi marigayin ga nauyin da ya bari ai.
Mama take cewa gaskiya ka kyauta muna sosai ga wanan jahadin don kaga dama yanzu auren ta sai mai dan hannu da shuni tunda ta saba da daula a can.
Ya kara washe bakin shi yana dariya tare da fadin kada aji komai zan rike ta amana yadda shima ya rike ta a gidan shi.
Mama ta wuce shi zuwa gidan mama Altine inda nake ina dakin mama na dan kwanta don ranan bamu aikin komai.
Sai muryan mama Lauratu muke ji yana tashi tun kafin ta kawo kwanan shigowa cikin gidan.
Rahama Rahama wai ina mara kunyar yarinyar nan ta shiga ne haka ana kira kamar bata ji.
Daga inda nake kwance ina jinta sai mama Altine ce kecewa injin dai lafiya wanan kiran irin haka ?
Cikin takaici take cewa ina wanan yarinyar take ne wai ana kira tana kyale mutane to ki fito ga bazawarin ki yazo gurin ki.
Bazawari kuma mama Altine ta tambaya cikin mamaki tana kallon mama lauratun dake wani haki.
Tace basu fada maki zancen malam Jatau na hayin dutse dake son auren ta bane ko may ?
Takara cewa ai kinga matsalan su basu bar kowa ba a gurin kilibibi har dake uwar dakin nasu sai sun gwadawa halin su.
Daidai lokacin na fito daga dakin mama ina mata kallon takaici nace.
Mama ina tun ranan na fada maki ra, ayina akai ke ma may yan mata uku a daki da basu taba aure ba ai su gwada sa, an su sugani gareshi ko don naga sunfi dacewa dashi bani Rahama ba.
Daga haka na shige daki abina na kwanta na barta nan waje tana sallami da zagina sai inda ta tsaya ta fita tana cewa Jatau din kyale jairan yarinyan nan sai an fito mata tabayan gida.
Koshi Alhaji marigayin ai ba kasafai ya samay ta hakana ba sai da muka hada kai dashi komai yazo daidai gareshi.
Kokai sai mun kai ga hakan in har kana son ta da gaskiya dole sai kayi wani abu don na shiga na fita a samo maka kan ta.
Ya gyara tsugun ni shi yace to wo hakane abin yake to yanzu kina ganin kamar nawa zamu kashe ke nan.?
Mama ta samu yadda take so takara dan matsowa kusa dashi ta kashe murya tana dan kuskus tare da shi cikin rada.
Badon abinda yake muradin samu bane da babu yadda mama zata iya cin naira guda nashi daga aljihun shi komai dabaran shi kuwa.
Nan dai sukai sallama da ita tai mashi alkawarin zata san yadda ta shiga tafita aka samu kaina a cikin sauki.
Bayan fitan ta gidan mama Altine ne ta saka ni gaba da tambaya ina kuka ina sharan hawayen bakin ciki da takaicin dake cina ne ina fada mata kan maganan.
Tace amma ko halin malam baiyi ba wallahi don dai wanan karon in har da adalci bai kamata yai maki haka ba.
Abune dai na sunw iyayyen ki ban da iko akan ki da sun ga tsiya wanan karon.
Kuma ai ba karya kika fada ma tana da yara dakin ta in har yarinya yake son aure ta bashi daya.
Mama ko tana shiga gida sai zagin Jatau takeyi tana cewa kaga matsiyaci ko kudin share kasa wanan yana isa ne balle na wani aiki can a haka dai komai rowan ka sai naci abin ka ta wannan fannin.
Baba na dawo wa gida ina jinta tana mayar mai da yadda mukayi da Jatau da ita.
Daga can naji yana kirana babu tsoro ko kadan a raina na fito amsa mai kiran.
Nan ya hauni da fada
Can taga yayi dan murmushi a fuskan yana cewa ke ma ai uwarsu ce zulfa don haka kiyi yadda ya kamata dasu mana.
Kofa likita bamu samu gani ba tukun ki ke wanan zance haka idan mun gama ai zamu dawo ne ko.
Bataji may tace dashi ba sai dai murmushin da taga yayi a fuskan yake cewa wata rana kema ai zaki bar naki a gurin ta ko ?
Don haka ki yi hakkuri kifitar da komai a ranki ina diyana diyan ki ne kema koda ba, a gida kike ba.
Can taji yace kwarai da gaske zulfa aiko ita kun san dalilin zuwan namu wannan lokacin ko.
Shiru ya dan ratsa falon yana sauraren mai maganan ta waya har ta taji shi yana cewa ok shike nan sai mun yi waya anjima ke nan.
Ya kashe wayan tare da dago kai yana kallon inda take zaune, ya dan yi murmushi .
Ya zauna gap da ita yana cewa yaya tafi mana ko kin kuma zauna anan ?
Ta dago idanuwan ta fuskan shi a cikin damuwa take cewa dashi akan yaran take magana ko ?
Bai bata amsa ba don yasan ranta zai kara baci ne ga banza yace tashi mu tafi ko ?
Da kyat ta mike tsaye ga dan matashin cikin dake a jikin ta ya turo a cikin rigan dake jikin ta.
Rai bace take magana tana fadin kaga abinda nake gudu ke nan tun farko nace ka bari na kai su gurin hibba su zauna har mu dawo amma kace wai a barsu su zauna agida tunda akwai mutane.
Ya jawo hannun ta yana fadin ke ma dai kin san bazan lamunci ina da gida da iyalina a ciki kuma na dauki diya na zuwa wani gurin ba.
Tace idan baka yarda an kaisu wani wurin ba ai gashi kana shan korafi akai ni dai tsorona kada a cutawa yaran da basuci ba basu sha ba kan zancen mu.
Haba Sa,ade Zulfa ce zata cutawa yarana kuma kada ki manta fa a matsayin yar uwa take a gareni fa.
Tace a da ke nan yanzu kan ai a matsayin diyan kishiya take daukan diyan ka gare ta.
Kofa ya bude masu suka fito daga gidan wani sanyi ne ya daki fuskan ta amma ba yadda ta iya dole haka zasu fita duk da tsananin sanyin da akeyi a garin
Don fitan ya zama masu dole sai sunyi shine dole zai sata fita a hakan.
Bayan sun gama da asibiti ne suka wuce zuwa wani shago nan ta dan yo sayayan abubuwan da ya dace ta tsinta har da tufafin yaran ta dana yaran abokan zaman nata.
Ko da suka dawo gida a gajiye take don bata da kuzarin da zata dinga tafiya haka mai nisa a jikin ta.
Zama yayi kasa a daidai kafan ta ya dan fara matsa mata su a hankali tana jin dadi hakan har cikin ranta ta dan fara lumahe idanuwan ta a hankali.
Haka yasa ta samu saukin yadda take ji a ran ta a lokacin sai bata samu wani matsala komai ba ga yadda take zato.
Washe gari ta riga shi sauko wa kasa don ta karya saboda yace yana son ya dan kara barci.
Har sai bayan ta gama ne sai gashi yau sauko kasan a lokacin har yai wanka yana saye a cikin kananan kaya a jikin shi.
Sau daya ta daga kai ta kalleshi taci gaba da duban wayan ta da takeyi tana murmushi a fuskan ta.
Da alama hiran da takeyi yana mata dadi a ran ta lokacin ya iso inda take yana cewa madam yaya jikin naki ?
Ta dan dago kan ta a hankali ta dube shi tana cewa Alhamdullahi ya kokari bai amsa mata ba sai da yakai zaune yace kokarin yiwa kaine ai nidai gurina naga Alllah ya rabaki da wanan cikin na jikin ki lafiya.
Sai lokacin tabar abinda take a wayan ta ta dago kan ta ta dube shi inda ya zauna sai suka hada ido dashi tayi saurin kawar da idon ta cikin nasa .
Yace No no no kada ki soma yi min wanan kukan naki dake tayar min da hankalina please ?
Yace cikin kamo hannun ta zuwa na shi cikin girgiza mata kai yake fadin ki dinga sakawa zuciyar ki dangana Allah daya baki ciki a cikin wanan halin da kike yasan dalilin yin haka a gare ki.
Don haka ki zamo cikin bayi masu rugumar kaddaran ubangijin su ako da yaushe.
Wanan tayar da hankalin da kikeyi zai iya kara jefa ki a cikin wani sabon tashin hankali kuma har mu dake tare dake abin ya shafi zukatan mu.
Ajiyan zuciya ta sauke tace dole na daga hankalina idan na tuna da lalurar dake tare dani sai ga shi kuma wanan cikin yazo ya shiga again.
Murmushi yayi tare da jawo ta ajikin shi yana dan shafa bayan ta yake cewa lafiya lau zaki haihu insha Allah ai ciwo ba mutuwa bane.
A hankali tace dashi abin ne ke bani tsoro sosai sai yake hanani sukuni a raina.
Ya girgiza mata kai yace ai abin bada ga nan bane heartbeat ke dai Allah ya kawo muna sauki ga al,amarin.
Sai da ya tabbatar ta kwantar da hankalin ta ya mike yana cewa zai dan fita amma ba zai dade ba indan ya fita.
Nan ya fice ya barta zaune zuciyan ta cike da tunanen yan diyan ta biyu dake gida Nigeria gurin kishiyan ta.
Tun ba akai ko ina ba gashi ta fara jin Zulfa din ta bugo waya tana korafi akan rikon yaran nata gashi zasu iya share wata uku basu koma gida ba.
Shine dalilin da tun farko taso zuwa da yaran ta ko tabar su gurin yar uwarta amma sai ya nuna mata rashin yardan shi ga hakan .
Don shi mutum ne mai matukar son iyalin shi a kusa dashi akoda yaushe haka ne yasa akwai shakuwa sosai tsakanin shi da italin shi don yana fitarwa kowa da hakkin shi yadda ya dace.
Wanan zuwan da sukayi dashi ba itace ya dace tabiyo shi ba amma saboda dalilin rashin lafiyan ta yazo da ita din.
Wanda kafin su zo saida akakai ruwa rana da sauran kishiyoyin nata akan basu yarda da hakan ba don acewa su yafi nuna kulawan shi akan Sa,ade da yaran ta bisa gasu.
Don har kara suka kai shi gurin iyayyen su kan abinda yake shirin yi masu.
Ita bata da ko labari sai dai ta fahinci ya dauki zafi da sauran matan nashi a lokacin.
Ita da ake abin akan ta sai daga baya ta fahinci rigiman akan tafiyan su ne akeyin sa.
Haka ne ya dan haifar mata da rashin natsuwa a tare da ita don haka ta bukaci da ajaye tafiya sai taga likitan ta na nan gida Nigeria.
Amma amma mijin tana yaki janye zancen ba irin rokon da bata mashi ba kan ya barta amma sai yaki yarda da bukatan ta.
Karshe ma cewa yayi da ita idan ke lafiyan ki bai damay ki ba ni ya damay ni tunda bake ce keda hasara ba ai .
Hakkuru ta bashi don yadda taga ya hau tasan itama zata iya samun nata rabon fitina a ciki don haka taja bakin ta ta tsuke tai shiru har lokacin tafiya yayi suka wuce.
Don makaran ta ne kawai yasa ta bar yaran ta a hannun kishiyoyin ta ba don taso ba don tana nan ma yaya aka kwashe da su balle bata kusa.
Ko ita Zulfa ba don Allah ta rike yaran ba don sai daya zube mata kudi masu yawa ta yarda zata zauna dasu din.
****** ********* ******
Na gama aikin da nake taya mama altine na kwashi kayan na aiki tare da kaisu bakin kwata na wanke komai fes na mayar na kife mama na zaune ta zuba min ido daga inda take zaune ta motsa furan data dama ta sha.
Ina yarfar da ruwan dakw hannu na bayan na dauraye kafana take cewa sannu Rahama ai kin huta ke bakajin kiyuyan aiki ko kadan.
Da ace uwarki lauratu ta gane haka ta nemi zaman lafiya dake a gidan dan wanan zaman da zakiyi a gida aida ta more maki sosai.
Na dago kai da sauri ina kallon mama nace kai mama matar da tun ina yar kankanuwa na fahinci bata kaunana yaya zan zauna da ita ta more min haka.
Ni fa yadda mama bata kaunana a sannu nima haka kiyayyan ta ya shiga har kasan raina wallahi.
Mutumin da zai iya maka sheri da kazafi aiko kasheka yana iyayi mama.
Bata kashe ki sai dai sherin ta ya koma mata baga diyan ta nan ba babu mashinshini a tare da su duk fa cikun mugun halin ta ne amma ita bata ganewa ne kawai.
Ki debi abinci kici kada yai sanyi gashi da zafin shi nace ba yanzu ba mama sai anjima kafin na kwanta don tunda na dawo gida idan Innata ce da girki a gidan mama altine nake kwanci na don nasan Mama bazata yarda da na kwana a dakin ta ba yadda muke din nan yanzu kamar annabi da kafiri ni da ita.
Muna nan muka ji sallaman dan wurin mama yana cewa Rahama wai kizo inji baba .
Nace yau baba lafiya ya dawo gida haka da wuri don nasa sai yamma lis da magariba yake dawowa gida.
Ban bata lokaci ba na figi hijjab dina zuwa kiran baban nawa da yake min ko da na shiga yana alwala zaiyi sallah na nufi inda yake zaune saman dutse na gaishe shi da dawowa.
Na samu guri daga gefen shi na tsugunna ina fadin baba gani .
Yace dan dajan ta min na rarage alwala na mike na koma gefe ina jiran idarwan shi har lokacin daya gama ya mike tsaye.
Sai naji yana kiran Lauratu lauratu, lauratu fa da dan karfi ta amsa daga daki da saurin ta tafito tana gyara daurin zanin ta.
Tana cewa lafiya dai malam wanan kira haka kamar zaka tsaga min kunne dashi.
Yace to ke ce din idan ba haka aka kiraki ba sai ki kyale mutum tsaye wani zubin.
Yace ina ita Asiya take inna dake bakin murhu tana kashe wutan da tai girki tace gani.
Yace to dama ba wani abu bane yasa nai kiran ku ku duka ukun sai akan Rahama gata nan.
Allah ya kawo mata mai nema a cikin sauki ba ko wani bane sai Malam Jatau na hayi dotse abokin maigidan ta marigayi.
Shine ya aiki min yau da safen nan akan yana son ta da aure ya hada ta cikin iyalin shi.
Don ya yaba da zaman ta gidan aminin nashi da tayi kwadayin hakan yasa yake sha, awan auren ta.
Wani irin dariya gami da guda mama ta ranga tare da cewa yarinyar tayi tagomashi ga tsofin gari.
Wani irin dam dam naji kirjina yaba da a lokaci guda cikin raina nace wani malam Jatau kuma can ai gara ma Alhaji garbati marigayi din shi a tsaye yake kyam ba irin malam Jatau ba dake tafiya a duke.
Gashi da dan banzan kazanta da rowa ko kiyashin gidan shi sun san shi da rowa da mugun halin.
Mama sai da ta gaji don kanta san nan ta tsagaita dariyan ta tana cewa injin ka bashi dai.
Yace ban amsa mai ba sai naji shawaran ku tukun akan zancen kafin na basu amsa ta.
Lalai ma malam yo may zaka tsaya jira da ita Allah ya kawo mata mai so da wuri haka ?
Yace ai komai sai a hankali akeyin sa tunda yanzu ita ba budurwa bace kin ga zama dan bata zabi ai ko?
Zabin may har nawa Rahama take da za, a tsaya neman wani zabin ta kudine dai akwaishi kaga sai taje taciwo muna nashi kasuwan kuma.
Ban san lokacin da bakina ya kufce ba nace ai kina da tan mata zuka zuka har uku a dakin ki kibashi mana.
Salati ta saka tare da saka kuka wai naci mutuncin ta a gaban uwaye na ai ba ita bace tasamin farin jinin tsofi balle naci mutuncin ta bakin halina ne dani da uwata ke bibiyan mu.
Da kyat baba ya lalashe ta ta koma dakin ta nikuma yai min fadan haka kaca kaca ya fice gidan.
Dakin Inna ta muka shiga kowan mu bakin ciki yana cin sa a rai da wanan sabon fitinan dake neman bullo muna kuma.
Nace wa Inna ta ni wallahi wanan karon ko kashe ni baba zaiyi ba zan yi auren nan ba ai bani kadai ce diya ba a gidan da zaita badani ga tsufin gari haka.
Inba tace kidai bi sannu ke ma kin san idan uwarku ta kafe sai ya bayar dake ko bakya so hakan.
Daga daki muna jin mama da yaran ta suna bidirin su cikin jin dadi har da shewan su.
Don su burin su dama shine suga bakin cikin mu nida uwata a gidan ga kuma wani dama ya sake samuwa gare su again.
Washegari koda na je gidan mama na kasa fada mata komai sai dai ta fahinci ina cikin yar damuwa a lokacin.
Ta tambaye ni nai mata yake kawai da cewa ba komai mama don ba ko wani sirin gidan mune zan dinga fada mata ba din yanzu girma yazo min na san wasu abu ba kowane zaka fadawa ba.
A kai sallama a kofan gidan mu lokacin baba ya fice zuwa kasuwa ba yara gida mama ta yafa ta fita.
Malam Jatau ne a cikin wani tsohon babban rigan shi daya takure don tsufa ga dauda taf ga kayan sai tsohon hular dake kan shi don tsufa har zaren hullan ya fara zarewa daga jikin shi sai shafin dauda daya kwanta akai.
Suka gaisa tana washe baki take cewa , a, a Alhaji Jatau ne sannu da zuwa .
Ai kuwa ba kunya mama take cewa har an fara zuwa zance ne gashi maigidan ya fita amma ba matsala bari a kira ma yarinyar ai tunda ina nan.
Ya washe bakin da duk goro ya bata shi yake cewa ikon Allah ashe kun san da zancen ke nan wallahi yabawa da halaiyar yarinyar don marigayi yana yaba hankalin ta.
Hakan yasa nai kwadayin saka ta a cikin nawa iyalin ko banza na taimakawa shi marigayin ga nauyin da ya bari ai.
Mama take cewa gaskiya ka kyauta muna sosai ga wanan jahadin don kaga dama yanzu auren ta sai mai dan hannu da shuni tunda ta saba da daula a can.
Ya kara washe bakin shi yana dariya tare da fadin kada aji komai zan rike ta amana yadda shima ya rike ta a gidan shi.
Mama ta wuce shi zuwa gidan mama Altine inda nake ina dakin mama na dan kwanta don ranan bamu aikin komai.
Sai muryan mama Lauratu muke ji yana tashi tun kafin ta kawo kwanan shigowa cikin gidan.
Rahama Rahama wai ina mara kunyar yarinyar nan ta shiga ne haka ana kira kamar bata ji.
Daga inda nake kwance ina jinta sai mama Altine ce kecewa injin dai lafiya wanan kiran irin haka ?
Cikin takaici take cewa ina wanan yarinyar take ne wai ana kira tana kyale mutane to ki fito ga bazawarin ki yazo gurin ki.
Bazawari kuma mama Altine ta tambaya cikin mamaki tana kallon mama lauratun dake wani haki.
Tace basu fada maki zancen malam Jatau na hayin dutse dake son auren ta bane ko may ?
Takara cewa ai kinga matsalan su basu bar kowa ba a gurin kilibibi har dake uwar dakin nasu sai sun gwadawa halin su.
Daidai lokacin na fito daga dakin mama ina mata kallon takaici nace.
Mama ina tun ranan na fada maki ra, ayina akai ke ma may yan mata uku a daki da basu taba aure ba ai su gwada sa, an su sugani gareshi ko don naga sunfi dacewa dashi bani Rahama ba.
Daga haka na shige daki abina na kwanta na barta nan waje tana sallami da zagina sai inda ta tsaya ta fita tana cewa Jatau din kyale jairan yarinyan nan sai an fito mata tabayan gida.
Koshi Alhaji marigayin ai ba kasafai ya samay ta hakana ba sai da muka hada kai dashi komai yazo daidai gareshi.
Kokai sai mun kai ga hakan in har kana son ta da gaskiya dole sai kayi wani abu don na shiga na fita a samo maka kan ta.
Ya gyara tsugun ni shi yace to wo hakane abin yake to yanzu kina ganin kamar nawa zamu kashe ke nan.?
Mama ta samu yadda take so takara dan matsowa kusa dashi ta kashe murya tana dan kuskus tare da shi cikin rada.
Badon abinda yake muradin samu bane da babu yadda mama zata iya cin naira guda nashi daga aljihun shi komai dabaran shi kuwa.
Nan dai sukai sallama da ita tai mashi alkawarin zata san yadda ta shiga tafita aka samu kaina a cikin sauki.
Bayan fitan ta gidan mama Altine ne ta saka ni gaba da tambaya ina kuka ina sharan hawayen bakin ciki da takaicin dake cina ne ina fada mata kan maganan.
Tace amma ko halin malam baiyi ba wallahi don dai wanan karon in har da adalci bai kamata yai maki haka ba.
Abune dai na sunw iyayyen ki ban da iko akan ki da sun ga tsiya wanan karon.
Kuma ai ba karya kika fada ma tana da yara dakin ta in har yarinya yake son aure ta bashi daya.
Mama ko tana shiga gida sai zagin Jatau takeyi tana cewa kaga matsiyaci ko kudin share kasa wanan yana isa ne balle na wani aiki can a haka dai komai rowan ka sai naci abin ka ta wannan fannin.
Baba na dawo wa gida ina jinta tana mayar mai da yadda mukayi da Jatau da ita.
Daga can naji yana kirana babu tsoro ko kadan a raina na fito amsa mai kiran.
Nan ya hauni da fada