Murucin Kan Dutse
Chapter 54 of 146
da zancen auren da kan ta.
A hankali ya tako zuwa inda take zaune yace ban fahince kiba don tunda na dawo naga wani canji daga gareku haka.
Wani kallo ta watso mai daidai lokacin da take gyara zaman ta da kyau sai ga hawaye shar shar suna biyo fuskan ta tana kokarin tare su.
Tsayawa yayi ya kura mata ido cikin mamaki yace Saade kinga abinda nake wa gudu ko ?
Tun farko abinda naiwa gudu kenan muna zaman lafiya kin kawo muna sabun fitina da zai tayar muna da hankali.
Dama nasan a karshe nice zaki bari a cikin zancen ina zaman zamana kika dauko minbsabun fitina a rayuwana .
Kece kika sakani yin auren banda ra, ayin karin mata a rayuwana ammakika sakani gaba da kai karana gurin magabata na har nakai ga amincewa da zancen.
Da kikasan bazaki iya hakkurin hakan ba da saiki barwa Allah al, amarin ki yai muna mafita da kan shi.
Amma yanzu gashi kin saka ayi abu kin kuma dawo kin tayar da hankalinki kin kasa samun natsuwa muma na tare da ke mun kasa samun namu.
Ya juya a fusace zai bar dakin sai ga mama tana shigowa dakin take cewa yaka mana Alhaji may kuma ke faruwa yau ina jin harshen ka har falo.
Mama may Saadatu take son mayar danine don taga ina tausaya mata shine take ganin kamar zata iya juyani yadda ran ta ke so, bafa tsoron ki nakeji ba, abubuwa da dama yasa nake matukar tausaya maki ina maki ragowa akan su.
Amma akan may kike son mayar dani wani bi can kamar mijin hajiya a gidan nan auren yarinyar nan kece fa kika tasa ni gaba zuwa gun magabata na .
Yanzu kuma Allah yayi abin kina kokarin tayar min da hankali so kike na zama mutumin banza ko may nace eh, na dawo kuma nace a, a komay ?
Wani kuka ne ya zo mata a lokaci daya tana fadin besty nayi nadama wanan hadin na cuci kaina da kaina besty.
Yanzu na fahinci nayi gangancin hada ka da Rama danayi a rayuwa na na fahinci yin hakan babban kuskure ne a rayuwana.
Kallon mamaki yake mata cikin rudewa yake cewa yanzu kina nufin dai kin jaye zancen auren ta a ranki sokike na sake ta ko ?
Da sauri mama ta cabe zancen tace shine saukin sakin wanan yarinyar don bai yuyuwa ace kamar Rama ta zaman kishi da Saade.
Wanan abin bayin kan ku bane kai da ita sihiri ne ke aiki akan ku kawai da zaka daure ka saki wanan yarinyar salin alin tun bata cinwa manufanta ba akan ku da zaifi saukin rufin asiri agare ku.
Kunga aniya makomiya ke nan amma ina Rahama ina shiga cikin ku , yar tallakawa lis da ita , ni ban taba yarda ba cewa ba sihiri suke a kan ku ba dama.
Wani irin abu yaji ya tokare mai makogwaron shi a lokaci guda ya gama fahintar mama tai amfani da lafazin tsofin mata akan Saade taji galaban ta, har kiyyayya ya tsiguru a zuciyar ta na Rama.
Take yaji idon shi ya canza launi yana jin kalamin mama kamar saukan aradu azuciyar shi da mama tasan kalaman sakin da take kira yaiwa Rahama yadda yake jin shi a ransa da bata kara furta ko a ba daga haka.
Yaya mama zata sa Saade ta mayar dashi mutumin banza mai magana biyu idan da yar tane ko jikan ta akaiwa haka zata ji dadin yin hakan da akai masu.
Lokaci daya anty ta fahinci rayuwa mijin ta yai matukar baci yadda mama ke ra fadin mugun kalami a kaina.
Ganin halin da yake ciki yasa ta fara tare mama dake ta faman zuba shar kamar ruwan sama.
Tace mama don Allah kibar zancen nan haka bai kamata kina fadin haka ba a gaban kowa.
Yace No ki barta ta fadi yanzu na fahinci komai dake gudana kuma na gane amma ki sani ke Saade idan wanan yarinyar bata da amanan ki kukai mata haka don tozarci Allah ba zai kyale ki ba.
Kin sani bani da ra, ayin karin aure a rayuwa na amma kika sakani gaba da fitina sai da na amince har Allah ya nufa aikai wanan abin.
Don haka ba asiri tai muna ba ko dauri tai muna bazan sake taba har abada gara ma ki kwantar da hankalin kafin yarinyar nan ta fahinci sauyin rayuwa a gare ki ki sha kunya ga hakan don mutuncin ki ne zai zube gareta.
Ina ilimin ki da imanin ki yau yashiga da har dan lokaci kadan shedan zaici galaba akan ki haka , ?
Kin bani kunya Saade kin kuma bani mamaki yau duk tarin sanin Allah ki harki bari shedan ya rude ki wai ke an maki asiri idan halintane yin haka ke kinfi kowa sanin hakan gareta.
Don kece ke zama da ita kin san komai na rayuwan ta ba sai wani ya fada maki.
Yadda yake magana yasa gaba daya jikin ta yai sanyi nadama abinda tayi yazo mata a lokaci guda hankalinta duk ya daga .
Ita kanta mama kunya da wani irin nauyin shi duk ya rufe ta saboda tasan ya gane itace ta zuga anty take hakan.
Yafara tafiya yana cewa yau din ba sai gobe ba zan samu su Abba na kuma basu takardan yarinyar nan basai ta tare min a gida ba.
Anty najin haka tamike da sauri ta tari gaban shi tana fadin dakata don Allah besty ka bari muyi magana ta fahinta dakai please?
Yace maganan may zanyi dake ke kika hada kin kuma ce a,a yanzu basai kowa ya kama kansa ba yafi sauki.
Kwata kwata ni dama wanan maganan baya a raina saboda kece nake komai da kikaga inayi din farin cikin ki yanzu ko ya kare ai.
Daga haka ya juya ya fice daga part din ta ranshi a bace zuwa nashi part din hasale yake don gaba daya kan shi ya daure ta ko ina ba dadi gare shi gaba daya matan sun sawa kan su bakin kishin yar karamar yarinya a duniya.
Amma kuma da yai nisan tunane sai yaga wannan abin duk jerabawan ubangiji ne hakan.
Allah kadai yasan hikima da albarkan dake cikin wannan aure da Allah ya nufe shi dayi batare da ya shiryawa hakan ba a rayuwan shi.
Ita Saade ya fahinci inda matsala ke taso akan ta zai yi kokari yaga ya magance wanan matsalan kada ta samu raunin imani a rayuwan ta abinda baida kyau zuwa gurin wanin Allah boka ko malam kan neman yayewan bukatan ta.
Don yadda ya fahinta ko wani lokaci mama na iya cin galabanta zuwa ire iren irin guraren nan na shirka.
Cikin kwanakin nan duk yadda Anty taso su shirya da shi abin yaci tura saboda ya dau zafi da ita sosai.
Ya dauki abin da zafi so sai a ranshi har takai ta fara shiga wani yanayi don gaba daya ya tsamany taga duk wanibal, amarin shi ya juya mata baya yana harka da sauran matan shi da yan uwan shi.
Ko zancen kai lefe gidan mu ga bakin mama laraba da Aisha ta samu labari hankakinta ya kara dagawa tasamay shi da zancen a falon shi.
Yace cikin murmushi eh dole ne nayi taka tsantsan dake yanzu Saade .
Don na fahinci sauyin rayuwa a gareki don ban taba tunanen zaki yi rayuwa irin na masu yarda da shirka ba.
Yanzu ke da kanki kin sani ke kika kawo zan cen yarinyar nan amna kika bari shedan da mama suka rude ki kan karya bayan kin san komai kece kika hada abinki.
Why zakibi rudin shedan ki hau ki zauna idan har wani yaji maganan nan in har yau Rahama na asiri kema tabbas kinayin asiri don kowa a tare ya san ku ai .
Nadama ne yazo wa Saade a lokaci daya tabbas ba karya ya fadi ba duk wanda taji maganan nan dole itama za, a ce tare suke wanan halin dubun su ne yacika ita da Rahama din kaikayi ya koma ga mashekiyar ta.
Tace don Allah besty kayi hakkuri wallahi mamace duk ta kaini ga haka kan dalilin ta mara tushe .
Ni dole inwa Allah godiya tunda na gane gaskiya kafin Rahama ta tare a gidan nan nazo naji kunya.
Yace dole ne na jaye don kada nima ki dulmiyar dani kamar yadda ke kika dulmiye kanki.
Idan zaki fadawa mama gaskiya don azauna lafiya ki kuma yi istigifari ga Allah ki roki yarinyar mutane gafara.
Kuka sosai Anty keyi tana mai nadama aranta tace nasan Allah naso na besty tun da har bai yarda naci galaban ka ba akan hakan.
Ka bijirewa bukata bamu taru mun cutawa yar mutane ba bayan tauye mata rayuwan da nayi na hata zabin kan ta kuma nabi bayan ta da kazafi da sheri.
Alhalin nasan haka ba halin wanan yarinyar bane da iyayyen ta don haka yau ba sai gobe ba nima zan zauna da mama idan ta gane wala ba, asa idan batagane ba ni dai babu hannuna ga duk abinda zatayi.
Tai mashi godiya ta fita zuwa nata sashen sai dare ta samu zama da mama cikin hikima da kuma kawo mata Allah ta ja hankalin mama.
Tace mama kin fini sanin halin yarinyar nan mama akan kishi zamu bari shedan ya yaudare mu mu cuci Rahama duk irin halarcin da yarinyar nan tai muna a rayuwan ta .
Mama dai ta fahinci gaskiya anty ke fadi dole taji nadama yazo mata bai kamata ba ta bi son rai ba taiwa yar mutane mugun kazafi haka ba.
Rahama mutum ce Saade gaskiya nima yanzu nayi nadaman abinda nai mata dole ne na nemi yafiyan wanan yarinyar.
Anty tace mama kina ganin yau in bani a gidan nan zaki shigo gidan nan koda da sunan ganin jikokin ne akarbe ki da mutunci ?
Amma idan Rahama na gidan nan tankar nice a gidan zaki zo kiyi yadda kika sabayi duk lokacin da kika ga dama ganin su.
Kuka mama ta fashe dashi sosai tana nadaman abinda tai min tace gobe zan koma gida ayi komai dani yadda aka saba ba zan yarda har akawo Rahama ba ina gidan nan dole ne naje ayi komai tare da ni.
********* ********* *********
Attu da nake gurin ta sai fanan shiri takeyi a kaina tana kara nusar dani yadda zama da kishiya yake tare da abinda zan wa miji na jan hankali.
Sai faman bani wasu jike jike takeyi tare da yi min wankan lalle akai akai tana kuma yi min hayaki da ban san ko na may ye ba ga ruwan rubutu da take faman kin kima min ina sha dare da rana.
Kashin rakumi naji tace a samo mata da kanunfari sai tasa na dinga tsugunawa ina hauakin jikina dashi.
Da nayi wanan hayakin za anji gaba daya alaura na ya wani ciko min yana min kamar kaikayi ko susa a lokacin.
Dutsen tama naji tace a tsinto mata naga ta jika a kwano duk zata dibi wanan ruwan da ta jika duwatsun tama a cikin shi ta hada da garin shasha tau da manta uwa da bita zaizai da shashatau tanika su guri guda tace na shanye su.
Ni kaina duk da ba abinci nake ci sosai ba nasan na samu canji sosai a jikina.
Ana gobe za, a fara shagalin buki ne naga tashigo dakin bayan magariba take cewa dani da mayafin ki kizo mu shiga nan gidan makwabtan mu.
Ban bata lokaci ba muka shiyar muka fita daga gidan gidan makwabcin su malam Musa muka shiga mun samay shi a zauren gidan shi muka gaidashi cikin mutunci.
Yace Attu kun iso tace dashi eh malam ga yarinyar nan nazo ma da ita na gaidashi a cikin mutum ci yace da Attu yaya sunan ta tace Rahama take.
Yace suna mai ma,ana ga musulunci kiyi amfani da martaban sunan nan naki a gidan mijin ki kikai mashi Rahaman dake cikin sunan ki a gidan shi.
Naga mijin naki mutum ne kamili mai addini a yadda nagan shi ga bincike na sai dai yana da murdade hali tare dashi ba matsala bane hakan idan har ka fahinci halinci halin mutum.
Babu wani dadin aure dayafi yi bari na bari kaso abinda taje so fiye dashi yan uwan shi su zamo tankar naki da zuciya daya.
Abokan zaman ki kada ki bisu da sheri bar mugu yaita mugunta shi idan baka rama ba kaine a kan sa duk abinda yayi sai ya koma mai.
Attu tace amma malam ya dace abata tsari wanda zaibi jikin ta don ni ina tsoron matan birni wallahi ba imani ne dasu ba akan kishiya.
Malam yai murmushi yace Attu ai shi wanan matsala bawai matan birni ne kawai ba har na kauyen idan Allah ya hada ka da maiyi hakane ke faruwa.
Ita hankalinta ba a kwance ba kaima naka da kake tare da ita ba akwance yake ba.
Bawani abu zan ma jikan ki ba sai tsari da zan bata tasha shi yanzu anan Allah ya tsare mu baki daya mu dasu.
Ya fara binciken wani abu a cikin kayan shi muna kallo yajawo ruwa cikin wani gora ya karkada ya mikowa Attu yace tabani na sha tamika min take na sha da bissimillah a gurin namiko mata dan roban da nasha yace Allah ya tsare ya kare.
Muka ansa da amin yace kiyi biyayya ga magabatan ki sai a zauna lafiya dakowa banga wani matsala mai yawa ba ga al, amarin ki sai yawan tarin alherin hakan idan Allah ya yarda.
Can ya dauko wani abu yace dani karbi wanan na sa hannu na karba yace murzashi da hannun ki biyu sai ki shafe fuskan ki da shi har zuwa kirjinki.
Nadaga hijjabina nayi yadda yace nayi yace Allah yabada zaman lafiya ya bada zuria masu albarka mukace amin.
Har zamu mike yace da Attu idan an kai ta kada ta shiga gidan sai ta karanta fatiha da kulhuwallahu falaki da nas kin gasu nan ba karamin abu bane faidar su yafi jin su da mukeyi amma muna sakaci gurin amfani dasu.
Mukai mai sallama na dawo gida gurin dana shafa wanan maganin ga kamshi gashi kuma inajin yana shiga jikina kamar wani abu na min yado a jikina lokacin.
Haka dai na daure har yazo na daina jin hakan da nake ji.
Nai mamaki ganin zarah tazo tare da wasu yan mata course mate din mu da muke dan shiri dasu nasan aikin anty ne hakan.
Taro sosai akai masu da yamma sai ga mama Altine tazo tana ra yan kamay kamay bata daiga canjin fuska ga kowa ba don an tare da mutunci yadda aka saba.
Can daki inda muke Zarah ce ke faman bamu dariya wai tana min lacture din yadda zan dinga yi na sace zuciyan miji ga sauran kishiyoyi na.
Dariya ma take bani take cewa oh dariya ma kike min wallahi ko kishiya daya zaki sama dole ne fa sai kin zage damtsem ki gurin zama karuwan gida karuwan dakin ki.
Don Allah ki daure ki fitae da kunya ga idon ki Rahama ki rage wanan halin rashin magana a gavan mijin ki don zai iya cutar dake yin hakan.
Samu kayan da kika san na jan ra, ayime ki dinga saka mai idan kuna ku biyu kai bama ku biyu ba nuna masu fa ke kece kawai a wuce gurin.
Nafisa tace aiko akwai wasu kaya english wear da suka fito masu kyau na mata su ya dace ki saya da mun isa sai ki basa na sayo maki su wallahi zaki shana sosai a cikin su ga jikin ki zai dauki kaya wallahi.
Ba wani buki bane akayi andai yi walima wanda yan uwana su Rukaiyya sunzo kuma sun nuna su nawa ne a gurin kuma an shirya dasu za, a tafi birni gurin kaini idan za, a tafi kaini din .
Babu abin da mama lauratu ta harta amna duk abinda akaci akasha sai da muka aika mata dashi.
Ba laifi iyayyena sun min gata duk da maigidan yace kada akawo ni da komai mata ya bukata mata kawai za, a kai mai.
Amma sai da maigari yaba da kudi akai dubula nakiya da alkaki da sauran abubuwan da ya dace aiwa amare.
Su mama laraba da ya uwata biyu sai Aisha da Fatima da wasu mata uku daga dangin su suka zo tare da kayan lefen su.
Nan guri ya cika da yan kallo ina daki na shirya cikin jan lafaya da anty taba Zarah tazo dashi cewan ta wai shi zan saka ajikina.
Kalar shi kamar ja ko purple gashi nan dai mai kyau da shi da tai makon Zarah na shirya jikina tsab.
Basu dade ba sukace a fito masu da amarya zasu tafi don kada yamma ya soma lokacin sai da akaini gidan mu nai masu sallama babana yai min nasiha sosai ma ratsa jiki tare da samin albarka ga aurena.
Muka fito muka nufi gurin maigari shida mutanen shi da matan shi suma saka saka min albarka ina kuka aka kama hanya dani zuwa sabon rayuwa agidan da na tsawon rayuwa a cikin shi.
Sai fanan tunane nakeyi yadda zamana zai kasance cikin wa yan nan mutanen masu wuyan fahinta.
Kaina naduke muna a motar dani da Attu da mama laraba dake zaune a gaba tare da driver da suka zo dashi.
Attu ta duko a hankali take ce min na fara adduan da malam ya fada min a raina hakan na soma jero adduoi a cikin zuciya na harda ma wanda malam baice ba duk na dinga yi a raina.
Nai mamakin jin cewa wai mun iso garin nan na ci gaba da jero addua gaba na sai faduwa yake faf faf faf duk na rude na rikice.
Muna shiga gidan naji daya daga cikin matan ta rangada guda irin mai sunan ruda kishiya.
Aiko haka din ne ban yi tsanmani zanga mutane ba cike a gidan sai dana gama addua na fito ne naga ko ina
A hankali ya tako zuwa inda take zaune yace ban fahince kiba don tunda na dawo naga wani canji daga gareku haka.
Wani kallo ta watso mai daidai lokacin da take gyara zaman ta da kyau sai ga hawaye shar shar suna biyo fuskan ta tana kokarin tare su.
Tsayawa yayi ya kura mata ido cikin mamaki yace Saade kinga abinda nake wa gudu ko ?
Tun farko abinda naiwa gudu kenan muna zaman lafiya kin kawo muna sabun fitina da zai tayar muna da hankali.
Dama nasan a karshe nice zaki bari a cikin zancen ina zaman zamana kika dauko minbsabun fitina a rayuwana .
Kece kika sakani yin auren banda ra, ayin karin mata a rayuwana ammakika sakani gaba da kai karana gurin magabata na har nakai ga amincewa da zancen.
Da kikasan bazaki iya hakkurin hakan ba da saiki barwa Allah al, amarin ki yai muna mafita da kan shi.
Amma yanzu gashi kin saka ayi abu kin kuma dawo kin tayar da hankalinki kin kasa samun natsuwa muma na tare da ke mun kasa samun namu.
Ya juya a fusace zai bar dakin sai ga mama tana shigowa dakin take cewa yaka mana Alhaji may kuma ke faruwa yau ina jin harshen ka har falo.
Mama may Saadatu take son mayar danine don taga ina tausaya mata shine take ganin kamar zata iya juyani yadda ran ta ke so, bafa tsoron ki nakeji ba, abubuwa da dama yasa nake matukar tausaya maki ina maki ragowa akan su.
Amma akan may kike son mayar dani wani bi can kamar mijin hajiya a gidan nan auren yarinyar nan kece fa kika tasa ni gaba zuwa gun magabata na .
Yanzu kuma Allah yayi abin kina kokarin tayar min da hankali so kike na zama mutumin banza ko may nace eh, na dawo kuma nace a, a komay ?
Wani kuka ne ya zo mata a lokaci daya tana fadin besty nayi nadama wanan hadin na cuci kaina da kaina besty.
Yanzu na fahinci nayi gangancin hada ka da Rama danayi a rayuwa na na fahinci yin hakan babban kuskure ne a rayuwana.
Kallon mamaki yake mata cikin rudewa yake cewa yanzu kina nufin dai kin jaye zancen auren ta a ranki sokike na sake ta ko ?
Da sauri mama ta cabe zancen tace shine saukin sakin wanan yarinyar don bai yuyuwa ace kamar Rama ta zaman kishi da Saade.
Wanan abin bayin kan ku bane kai da ita sihiri ne ke aiki akan ku kawai da zaka daure ka saki wanan yarinyar salin alin tun bata cinwa manufanta ba akan ku da zaifi saukin rufin asiri agare ku.
Kunga aniya makomiya ke nan amma ina Rahama ina shiga cikin ku , yar tallakawa lis da ita , ni ban taba yarda ba cewa ba sihiri suke a kan ku ba dama.
Wani irin abu yaji ya tokare mai makogwaron shi a lokaci guda ya gama fahintar mama tai amfani da lafazin tsofin mata akan Saade taji galaban ta, har kiyyayya ya tsiguru a zuciyar ta na Rama.
Take yaji idon shi ya canza launi yana jin kalamin mama kamar saukan aradu azuciyar shi da mama tasan kalaman sakin da take kira yaiwa Rahama yadda yake jin shi a ransa da bata kara furta ko a ba daga haka.
Yaya mama zata sa Saade ta mayar dashi mutumin banza mai magana biyu idan da yar tane ko jikan ta akaiwa haka zata ji dadin yin hakan da akai masu.
Lokaci daya anty ta fahinci rayuwa mijin ta yai matukar baci yadda mama ke ra fadin mugun kalami a kaina.
Ganin halin da yake ciki yasa ta fara tare mama dake ta faman zuba shar kamar ruwan sama.
Tace mama don Allah kibar zancen nan haka bai kamata kina fadin haka ba a gaban kowa.
Yace No ki barta ta fadi yanzu na fahinci komai dake gudana kuma na gane amma ki sani ke Saade idan wanan yarinyar bata da amanan ki kukai mata haka don tozarci Allah ba zai kyale ki ba.
Kin sani bani da ra, ayin karin aure a rayuwa na amma kika sakani gaba da fitina sai da na amince har Allah ya nufa aikai wanan abin.
Don haka ba asiri tai muna ba ko dauri tai muna bazan sake taba har abada gara ma ki kwantar da hankalin kafin yarinyar nan ta fahinci sauyin rayuwa a gare ki ki sha kunya ga hakan don mutuncin ki ne zai zube gareta.
Ina ilimin ki da imanin ki yau yashiga da har dan lokaci kadan shedan zaici galaba akan ki haka , ?
Kin bani kunya Saade kin kuma bani mamaki yau duk tarin sanin Allah ki harki bari shedan ya rude ki wai ke an maki asiri idan halintane yin haka ke kinfi kowa sanin hakan gareta.
Don kece ke zama da ita kin san komai na rayuwan ta ba sai wani ya fada maki.
Yadda yake magana yasa gaba daya jikin ta yai sanyi nadama abinda tayi yazo mata a lokaci guda hankalinta duk ya daga .
Ita kanta mama kunya da wani irin nauyin shi duk ya rufe ta saboda tasan ya gane itace ta zuga anty take hakan.
Yafara tafiya yana cewa yau din ba sai gobe ba zan samu su Abba na kuma basu takardan yarinyar nan basai ta tare min a gida ba.
Anty najin haka tamike da sauri ta tari gaban shi tana fadin dakata don Allah besty ka bari muyi magana ta fahinta dakai please?
Yace maganan may zanyi dake ke kika hada kin kuma ce a,a yanzu basai kowa ya kama kansa ba yafi sauki.
Kwata kwata ni dama wanan maganan baya a raina saboda kece nake komai da kikaga inayi din farin cikin ki yanzu ko ya kare ai.
Daga haka ya juya ya fice daga part din ta ranshi a bace zuwa nashi part din hasale yake don gaba daya kan shi ya daure ta ko ina ba dadi gare shi gaba daya matan sun sawa kan su bakin kishin yar karamar yarinya a duniya.
Amma kuma da yai nisan tunane sai yaga wannan abin duk jerabawan ubangiji ne hakan.
Allah kadai yasan hikima da albarkan dake cikin wannan aure da Allah ya nufe shi dayi batare da ya shiryawa hakan ba a rayuwan shi.
Ita Saade ya fahinci inda matsala ke taso akan ta zai yi kokari yaga ya magance wanan matsalan kada ta samu raunin imani a rayuwan ta abinda baida kyau zuwa gurin wanin Allah boka ko malam kan neman yayewan bukatan ta.
Don yadda ya fahinta ko wani lokaci mama na iya cin galabanta zuwa ire iren irin guraren nan na shirka.
Cikin kwanakin nan duk yadda Anty taso su shirya da shi abin yaci tura saboda ya dau zafi da ita sosai.
Ya dauki abin da zafi so sai a ranshi har takai ta fara shiga wani yanayi don gaba daya ya tsamany taga duk wanibal, amarin shi ya juya mata baya yana harka da sauran matan shi da yan uwan shi.
Ko zancen kai lefe gidan mu ga bakin mama laraba da Aisha ta samu labari hankakinta ya kara dagawa tasamay shi da zancen a falon shi.
Yace cikin murmushi eh dole ne nayi taka tsantsan dake yanzu Saade .
Don na fahinci sauyin rayuwa a gareki don ban taba tunanen zaki yi rayuwa irin na masu yarda da shirka ba.
Yanzu ke da kanki kin sani ke kika kawo zan cen yarinyar nan amna kika bari shedan da mama suka rude ki kan karya bayan kin san komai kece kika hada abinki.
Why zakibi rudin shedan ki hau ki zauna idan har wani yaji maganan nan in har yau Rahama na asiri kema tabbas kinayin asiri don kowa a tare ya san ku ai .
Nadama ne yazo wa Saade a lokaci daya tabbas ba karya ya fadi ba duk wanda taji maganan nan dole itama za, a ce tare suke wanan halin dubun su ne yacika ita da Rahama din kaikayi ya koma ga mashekiyar ta.
Tace don Allah besty kayi hakkuri wallahi mamace duk ta kaini ga haka kan dalilin ta mara tushe .
Ni dole inwa Allah godiya tunda na gane gaskiya kafin Rahama ta tare a gidan nan nazo naji kunya.
Yace dole ne na jaye don kada nima ki dulmiyar dani kamar yadda ke kika dulmiye kanki.
Idan zaki fadawa mama gaskiya don azauna lafiya ki kuma yi istigifari ga Allah ki roki yarinyar mutane gafara.
Kuka sosai Anty keyi tana mai nadama aranta tace nasan Allah naso na besty tun da har bai yarda naci galaban ka ba akan hakan.
Ka bijirewa bukata bamu taru mun cutawa yar mutane ba bayan tauye mata rayuwan da nayi na hata zabin kan ta kuma nabi bayan ta da kazafi da sheri.
Alhalin nasan haka ba halin wanan yarinyar bane da iyayyen ta don haka yau ba sai gobe ba nima zan zauna da mama idan ta gane wala ba, asa idan batagane ba ni dai babu hannuna ga duk abinda zatayi.
Tai mashi godiya ta fita zuwa nata sashen sai dare ta samu zama da mama cikin hikima da kuma kawo mata Allah ta ja hankalin mama.
Tace mama kin fini sanin halin yarinyar nan mama akan kishi zamu bari shedan ya yaudare mu mu cuci Rahama duk irin halarcin da yarinyar nan tai muna a rayuwan ta .
Mama dai ta fahinci gaskiya anty ke fadi dole taji nadama yazo mata bai kamata ba ta bi son rai ba taiwa yar mutane mugun kazafi haka ba.
Rahama mutum ce Saade gaskiya nima yanzu nayi nadaman abinda nai mata dole ne na nemi yafiyan wanan yarinyar.
Anty tace mama kina ganin yau in bani a gidan nan zaki shigo gidan nan koda da sunan ganin jikokin ne akarbe ki da mutunci ?
Amma idan Rahama na gidan nan tankar nice a gidan zaki zo kiyi yadda kika sabayi duk lokacin da kika ga dama ganin su.
Kuka mama ta fashe dashi sosai tana nadaman abinda tai min tace gobe zan koma gida ayi komai dani yadda aka saba ba zan yarda har akawo Rahama ba ina gidan nan dole ne naje ayi komai tare da ni.
********* ********* *********
Attu da nake gurin ta sai fanan shiri takeyi a kaina tana kara nusar dani yadda zama da kishiya yake tare da abinda zan wa miji na jan hankali.
Sai faman bani wasu jike jike takeyi tare da yi min wankan lalle akai akai tana kuma yi min hayaki da ban san ko na may ye ba ga ruwan rubutu da take faman kin kima min ina sha dare da rana.
Kashin rakumi naji tace a samo mata da kanunfari sai tasa na dinga tsugunawa ina hauakin jikina dashi.
Da nayi wanan hayakin za anji gaba daya alaura na ya wani ciko min yana min kamar kaikayi ko susa a lokacin.
Dutsen tama naji tace a tsinto mata naga ta jika a kwano duk zata dibi wanan ruwan da ta jika duwatsun tama a cikin shi ta hada da garin shasha tau da manta uwa da bita zaizai da shashatau tanika su guri guda tace na shanye su.
Ni kaina duk da ba abinci nake ci sosai ba nasan na samu canji sosai a jikina.
Ana gobe za, a fara shagalin buki ne naga tashigo dakin bayan magariba take cewa dani da mayafin ki kizo mu shiga nan gidan makwabtan mu.
Ban bata lokaci ba muka shiyar muka fita daga gidan gidan makwabcin su malam Musa muka shiga mun samay shi a zauren gidan shi muka gaidashi cikin mutunci.
Yace Attu kun iso tace dashi eh malam ga yarinyar nan nazo ma da ita na gaidashi a cikin mutum ci yace da Attu yaya sunan ta tace Rahama take.
Yace suna mai ma,ana ga musulunci kiyi amfani da martaban sunan nan naki a gidan mijin ki kikai mashi Rahaman dake cikin sunan ki a gidan shi.
Naga mijin naki mutum ne kamili mai addini a yadda nagan shi ga bincike na sai dai yana da murdade hali tare dashi ba matsala bane hakan idan har ka fahinci halinci halin mutum.
Babu wani dadin aure dayafi yi bari na bari kaso abinda taje so fiye dashi yan uwan shi su zamo tankar naki da zuciya daya.
Abokan zaman ki kada ki bisu da sheri bar mugu yaita mugunta shi idan baka rama ba kaine a kan sa duk abinda yayi sai ya koma mai.
Attu tace amma malam ya dace abata tsari wanda zaibi jikin ta don ni ina tsoron matan birni wallahi ba imani ne dasu ba akan kishiya.
Malam yai murmushi yace Attu ai shi wanan matsala bawai matan birni ne kawai ba har na kauyen idan Allah ya hada ka da maiyi hakane ke faruwa.
Ita hankalinta ba a kwance ba kaima naka da kake tare da ita ba akwance yake ba.
Bawani abu zan ma jikan ki ba sai tsari da zan bata tasha shi yanzu anan Allah ya tsare mu baki daya mu dasu.
Ya fara binciken wani abu a cikin kayan shi muna kallo yajawo ruwa cikin wani gora ya karkada ya mikowa Attu yace tabani na sha tamika min take na sha da bissimillah a gurin namiko mata dan roban da nasha yace Allah ya tsare ya kare.
Muka ansa da amin yace kiyi biyayya ga magabatan ki sai a zauna lafiya dakowa banga wani matsala mai yawa ba ga al, amarin ki sai yawan tarin alherin hakan idan Allah ya yarda.
Can ya dauko wani abu yace dani karbi wanan na sa hannu na karba yace murzashi da hannun ki biyu sai ki shafe fuskan ki da shi har zuwa kirjinki.
Nadaga hijjabina nayi yadda yace nayi yace Allah yabada zaman lafiya ya bada zuria masu albarka mukace amin.
Har zamu mike yace da Attu idan an kai ta kada ta shiga gidan sai ta karanta fatiha da kulhuwallahu falaki da nas kin gasu nan ba karamin abu bane faidar su yafi jin su da mukeyi amma muna sakaci gurin amfani dasu.
Mukai mai sallama na dawo gida gurin dana shafa wanan maganin ga kamshi gashi kuma inajin yana shiga jikina kamar wani abu na min yado a jikina lokacin.
Haka dai na daure har yazo na daina jin hakan da nake ji.
Nai mamaki ganin zarah tazo tare da wasu yan mata course mate din mu da muke dan shiri dasu nasan aikin anty ne hakan.
Taro sosai akai masu da yamma sai ga mama Altine tazo tana ra yan kamay kamay bata daiga canjin fuska ga kowa ba don an tare da mutunci yadda aka saba.
Can daki inda muke Zarah ce ke faman bamu dariya wai tana min lacture din yadda zan dinga yi na sace zuciyan miji ga sauran kishiyoyi na.
Dariya ma take bani take cewa oh dariya ma kike min wallahi ko kishiya daya zaki sama dole ne fa sai kin zage damtsem ki gurin zama karuwan gida karuwan dakin ki.
Don Allah ki daure ki fitae da kunya ga idon ki Rahama ki rage wanan halin rashin magana a gavan mijin ki don zai iya cutar dake yin hakan.
Samu kayan da kika san na jan ra, ayime ki dinga saka mai idan kuna ku biyu kai bama ku biyu ba nuna masu fa ke kece kawai a wuce gurin.
Nafisa tace aiko akwai wasu kaya english wear da suka fito masu kyau na mata su ya dace ki saya da mun isa sai ki basa na sayo maki su wallahi zaki shana sosai a cikin su ga jikin ki zai dauki kaya wallahi.
Ba wani buki bane akayi andai yi walima wanda yan uwana su Rukaiyya sunzo kuma sun nuna su nawa ne a gurin kuma an shirya dasu za, a tafi birni gurin kaini idan za, a tafi kaini din .
Babu abin da mama lauratu ta harta amna duk abinda akaci akasha sai da muka aika mata dashi.
Ba laifi iyayyena sun min gata duk da maigidan yace kada akawo ni da komai mata ya bukata mata kawai za, a kai mai.
Amma sai da maigari yaba da kudi akai dubula nakiya da alkaki da sauran abubuwan da ya dace aiwa amare.
Su mama laraba da ya uwata biyu sai Aisha da Fatima da wasu mata uku daga dangin su suka zo tare da kayan lefen su.
Nan guri ya cika da yan kallo ina daki na shirya cikin jan lafaya da anty taba Zarah tazo dashi cewan ta wai shi zan saka ajikina.
Kalar shi kamar ja ko purple gashi nan dai mai kyau da shi da tai makon Zarah na shirya jikina tsab.
Basu dade ba sukace a fito masu da amarya zasu tafi don kada yamma ya soma lokacin sai da akaini gidan mu nai masu sallama babana yai min nasiha sosai ma ratsa jiki tare da samin albarka ga aurena.
Muka fito muka nufi gurin maigari shida mutanen shi da matan shi suma saka saka min albarka ina kuka aka kama hanya dani zuwa sabon rayuwa agidan da na tsawon rayuwa a cikin shi.
Sai fanan tunane nakeyi yadda zamana zai kasance cikin wa yan nan mutanen masu wuyan fahinta.
Kaina naduke muna a motar dani da Attu da mama laraba dake zaune a gaba tare da driver da suka zo dashi.
Attu ta duko a hankali take ce min na fara adduan da malam ya fada min a raina hakan na soma jero adduoi a cikin zuciya na harda ma wanda malam baice ba duk na dinga yi a raina.
Nai mamakin jin cewa wai mun iso garin nan na ci gaba da jero addua gaba na sai faduwa yake faf faf faf duk na rude na rikice.
Muna shiga gidan naji daya daga cikin matan ta rangada guda irin mai sunan ruda kishiya.
Aiko haka din ne ban yi tsanmani zanga mutane ba cike a gidan sai dana gama addua na fito ne naga ko ina