Murucin Kan Dutse
Chapter 74 of 146
bai min magana ba nima hakan da safe duku duku na bar dakin ko wanka da sallah a dakina nayi na hada break fast nakai mai nabi yara muka bar gidan.
Sai yamma lis na dawo na samu gajiye har tagama abinci da nai sallah nakai na jera nafito ban zauna ba.
Yau ma haka na daure na tafi kamar jiya ba sauki ko kadan a kaina sai na Allah ya gama abinda zaiyi ya koma inda yake yake cewa yaushe zakuyi hutun?
Nace thursday din nan in Allah ya kaimu yace sai ki shirya sunday ku tafi kwana nawa zakiyi a can ?
Nace goma ko sati daya yace wai ko kina da hankali Rahama may zakije ki zauna gida kiyi har sati daya, ?
Saida na hade bakin ciki nace ganin iyayyena da yan uwana zanje nayi yace to ban yarda ba idan kwana hudu yayi maki sai ki shirya ku tafi din.
Banyi magana ba na gyara kwanciya na kawai ina adduan barci da safe na fice abina yana zaune yana lazumi.
Yabini da kallo kawai yana mamakin karfin hali haka irin nawa watau mata kowa da inda take da nata matsalan ke nan.
Wanan yarinyar karama tasan wai ta dakile namiji ita adole fushi take yi wawuyi kanki kikaiwa nina kwashi rabona ko ai.
Da kanki yarinya zaki dawo kamar yadda kika kawo kanki yanzu akai maki susa.
Tun ranan na fara shirina sai dana shirya tsab kafin ranan na danyiwa anty bayani sama sama sai dai ba komai ba.
Mun yi kitso har kumshi don tafiya kawai jiran gari ya waye mu dauki hanya ga yaran nason bina anty tace sai nice zanwa daddy magana amma na rasa yadda zan mai magana don basuyi hutu ba.
Hakana nai masu dabara nace daddy yace idan sunyi hutu zai kawo su mu dawo tare anty ma taban tsaraban da zamukai gida nai mata godiya.
Na dawo part dina ina cewa Fatima ta fito da kayan mu falo sai gashi ya shigo yabi jakar da Fatima ta dauko da kallo, fatima kan na ganin shi ta shige ciki.
Kudi ya miko min yace ga wanan ina ga zasu isheki ai har ku dawo nace akwai kudi a hannuna zasu isheni bai tsaya bin magana naba ya miko min kudin dari biyu ne zur yan dubu da kuma dari biyar.
Yacd nace Hamza ya shiya zaku samay shi a waje zaune yana jiran ku nace na gode a sanyayye.
Yace ku gaida mutanen gida kiyi min godiya wurin baba kafin mu hadu dashi.
Mun fito muka rufe kofa na nufi wurin anty nai mata sallama don naci arziki ba yaran suna makaranta.
Tace kun fito ko nace eh anty to idan kin je ina zaki sauka wurin mama laure ko kuwa nace anty wurin Inna ta dai zan sauka tace anya Rama bazaifi kyau ki sauka gida ba wanan karon ?
Nace anty kin san halin mama ba fasawa zatayi ba bari dai muyi nisa da nisa da ita a rabu cikin mutunci yafi tace shine kuma ai.
Tare muka fito da anty mun samu har an saka kayan a mota ko yana dan kakabewa ba anty ba koni nai mamaki ganin ACURA din daddy ce zamuyi tafiyan da ita ashe.
Mukai sallama da su anty Gajiye ma zata bimu taga gida su dawo da Hamza fatima ita ta shiga gaba ni da gajiye muna baya muka kama hanya.
Sha biyu daidai muna kauyen mu inda kowa yaga motar sai bin mu da kallon mamaki ake don ba, a san ko su waye ba cikin wanan tsaleliyar motar haka ?
Fadan mai gari yana makil da jama, a dagani wani sharia sukeyi a wurin zuwan mu ya dawo da hankalin su a kan mu.
Mun fito aka gane mune ga yara sun kewaye mu sai faman ihu da murnan ga Fatima ga anty sukeyi.
Ba karamin kaduwa nayi ba danaga irin tsaraban da daddy ya lodo muna a bayan motan shi don ban san da su ba saida na zo yanzu ake saukewa.
Nauyi da kunya ne ya kamani duk rashin mutuncin dana tsula masu gashi kuma ya bini da abin arziki kai gaskiya hindatu shu,umace wallahi don nasan ba banza ta barmu ba haka rashin fahinta na shiga tsakanin mu haka.
Don gaba daya gaskiya bakin daddy nake gani ina jin haushin shi haka kawai ba wai marin da yai min ba tun kan haka nake jin wanan yanayin a tare dani.
Abinda ban sani ba ashe shine aikin da akai muna ma daba duka ba so akayi gaba daya ma sakina akaso yayi ranan .
Sai abin ya tsaya iya mari kawai da nasha Allah baikai abin ga saki ba tsakanin mu don gaba daya lokacin haushina da takaicina yakeji.
Marin da yai min ne yadan ji sanyi a zuciyar shi sannu abin ya dan rage mashi yadda yake ji a kaina din.
Nima yadda yake ji haka nake ji idan na ganshi wani haushi da takaicin shi nake ji sai naji ma bani son ganin shi sam a raina.
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > aihausabooks@gmail.com
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
WhatsApp Number: 09017242889
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA, , , ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YABI MUNA HAKKIN MU A KANKI DON ONLINE NOVEL NE WANAN, , , ,
54
Mun yi saurin barin uguwar nace ma mama Altine zan dawo tana ta zabga min addua muka bar gidan.
Har mutane sun fara taruwa a kofan gidan mu amma haka muka wuce bamu tsaya jin takaici ba sai ma Rukaiyya ke fadin mama bata taba fadan gaskiya.
Yanzu tasan Lawali baida gaskiya amma ta zage tana biyewa matar nan suke tijara.
Yanzu ai ta samu daidai da ita ba kamar yadda ta samu innan ki tana gasa mata kwakwa ba a baya ita wanan sunyi daidai don makirace sosai matar .
Murmushi kawai nai mata a raina nace ai sin gamu da sun dace sai suyi tayi yanzu.
Gidan Jatau muka nufa daga gidan mu tare da karin tsaraban da nazo masu dashi.
Tun a kofan gida muka hadu da shi yana ganin mu ya fara wagale baki ya kara tsufa sosai duk furfura ne ko ina fuskan shi har kan shi.
Yana fadin hajiya Rahama ashe an shigo garin namu sannun ku da zuwa nace malam jatau ya gida ya iyali yaune rana na farko da mukai magana ta arziki dashi.
Nace na taki sa, a dana samay ka a gida dama akwai maganan da nake son muyi da kai akan anty na ne.
Ya kara washe baki yace to to Allah yasa alheri ne nace in sha Allahu alherin ne idan ka yarda.
Dama ba wani abu bane so nake a samu dan injimin nika wa anty wanda zata dan rika samun kwabon kashi kaga yanzu ga yara sunyi yawa dole a dan kama ma wani wurin kaima ka huta.
Yaji dadin yadda na fada sai washe baki yakeyi yace to hakan na da kyau idan har zata iya ai yar uwar taki ce ba haguwa ko kana son taimaka mata bata iya tattali ba a rayuwan ta.
Nace in har ka yarda ba matsala sai a gwada agani ko Allah zai karba muna ta wanan hanyan .
Nace babu damuwa za, a gwada a gani idan zai karbu gareta yai min godiya nasa hannu na ciro dubu biyar na bashi nace ga wanan ayi hakkuri dashi hakana.
Sai ga Jatau da tsufan shi har yana dan rusunnamin wurin karban kudin yana ta zabga godiya.
Dama muna tsaye yaran gidan na leko mu har sun koma sun fadawa iyayyen su ga yar uwar Suwaiba ta birni can ta tsaya da baban mu a waje suna wani magana.
Nan dai suka fara sake magana a tsakar gida mu ana gwada muna birni mu da muka ga gwauna.
Sai gamu mun shigo da sallaman mu Rukkaiyya ta kwasa zata wuce su babu ko gaisuwa nace haba dai anty na.
Direct inda suke zaune na nufa tare da masu sallama suka amsa a gyatsire fuska babu walwala nace mun samay ku lafiya yaya yara ya gida ya kuma bayan rabo suka amsa da lafiya kalau sai dayan ce tace anzo lafiya ya mutanen wurin ku nace Alhamdullahi.
Na juya nabi Rukaiyya data fara tafiya don bata daukan wanan a gareta sai ga Suwaiba zanin jikin ta ma dai bai ko kalluwa tayo kan mu da murnan ta.
Inajin suna cewa an dai yi hasara wallahi muka rugumay juna da murna ta rasa inda zata sani don dadi.
Tace Rahama kece kika koma haka kamar baturiya aiko birnin ma ashe amsa ne don naga wasu yan birni da suka zo kwana ki gidan nan ko mu mun fisu dadin gani.
Ashe wai wata yar uwar kishiyarta tazo daga can shine take wanan haibaicin muna shiga dakin ta sai da gabana ya fadi don bazakace mutum mai raine ke kwana ciki ba haka wai kuma harda miji a hakan.
Godiya naiwa Allah a raina da ya rabani da wanan rayuwan na mutanen mu mace da kurciyar ta amma don kazanta da talauci takoma kamar tsohuwa.
Hakana muka zauna takawo muna ruwa cikin wani kofin silver duk ya dafe don tsufa.
Kowa yace bai sha na karba na kafa kai na ji wani mugun karni ya doki hancina haka na daure na hade zuciyana yana tashi.
Mun gaisa muka barke da hiran yaushe rabo a tsakanin mu mun dan jima a zaune nace Fatima miko min jakar nan ta miko min.
Turmi uku na fitar da kudi dubu uku sai sweet da sabulun wanki da omo nace Fatima mikawa matan can wanan kice su raba .
Rahama don may zaki ba su wanan himilin uban kayan haka dako mijin da ta aje su bai iya basu shi.
Ai harshi sai da taba yanzu har dubu biyar kamar na taushe shi na kwace naji sai son banza amma shi bai iyayiwa mutane hakan.
Nace haba dai Anty wanan fa shine sayen girma da mutnci a gareki ba don wani na ba dashi ba sai don ke din nan.
Haka zai sa su gane kin fisu har abada tunda har kina da wanda zai basu abu su karba a bangaren ki.
Hakane kuma inji Rukkaiya dake zuga zancen ita dai Suwaiba duk bakin ciki ya kashe ta akan an ba abokan zaman ta alheri.
Abinda basu taba yi ba sai gasu tare duk kan su sun zo yin godiya sai faman farin ciki suke suna ta zabga godiya da fatan alheri gareni da maigida.
Bayan tafiyan su na fara yiwa Suwaiba da Rukkaiyya bayanin abinda nake so dasu tare da masu fada akan su canza rayuwan su don banji dadin abin da na sama ba a gidan Suwaiba din.
Nace gobe gobe ta kwashe kayan ta zan turo a gyara mata dakin ta zanyi magana da mijin ta sai Rukkaiyya tace a dai gyara muna nima dakina ai ko daben kasa babu kin san auren nawa ba shiri akayi mama kuma wai bata son auren.
To Rahama nagaji da yawo hakana gashi duk babu sa,a na a gari ita mama kin san hakan ko a jikin ta bata damu ba wallahi.
Nace Rukkaiya sai hakkuri da iyayyen mu tun da sun riga sun haife mu tace yanzu ma da zamu fito bakiji abinda take fada min ba wai kada na bada kaina gun Rahama.
Yo Allah na tuba yaya zan rabu da yar uwata ko baki haka balle irin taimakon da kike muna ko bakizo ba ko yaushe aiken ki na saman hanya ana kawo muna duk Altine zata dawo.
Nace ni dai yanzu abinda nake so daku shi ne ku kama kanku don Allah lokaci yayi da zaku dage wurin mai da kan ku abin kwarai don mahaifin mu yai alfahari da haihuwan mu.
Sai naga Suwaiba na kuka tace Rahama laila ke mutum ce dake da mahaifiyar ki duk irin abinda mukai maku a baya baku taba rike mu dashi ba.
Haka ma wanda mahaifiyar mu ke maki baku taba kallon mu dashi ba balle ku rike mu da hakan a ranku.
Don Allah Rahama ki yafe muna duk abinda mukai maki da wanda kika sani dama wanda baki sani ba.
Nace Anty don Allah kibar wanan magana don ni ban taba rike dayan ku da wani abu a raina ba ni dai fatana naga mun rike zumuncin mu da Allah ya kulla a tsakanin mu.
Nan dai mukai ta magana nai masu bayani kan gyaran gidan da maigidana yace aiwa baba idan nazo sukai murna sosai suna cewa.
Ai wanan abin Rahama ba baba akaiwa ba mu akaiwa don mu zamuyi alfahari da hakan a gari.
Ban bar gidan ba sai da na dan masu nasiha na zaman lafiya a fakaice sukai min godiya muka barta.
Gidan Rukkaiya muka tafi naga dakin ta tabani matukar tausayi nasan auren take son zama shiyasa harta daure cikin irin wanan rayuwan haka.
Bayan na dawo gida na samu mutane da dama sunzo gaida ni, wanka nayi don nagaji sosai bayan maigari ya dawo cikin gida taro ya watse a fadan shi ya zauna dani muna hira.
Har cikin raina naji dafin hakan sai nake ji dama ace shine mahaifina, ban boye mashi komai ba na halin rayuwan da muke ciki da kowa a gidan don ina jin shi tankar shi ya haife ni.
A rin yadda ya daukeni a matsayin diyarshi tankar wacce ya haifa yace dani na kara kwantar da hankalina su dai basuyi wa mutum sheri amma duk abinda mutum ya debo akan dan su zai koma a kan shi in hairan in sheran.
Nai mashi bayani kan gyaran gidan da nake so aiwa mahaifina yayi murna kwarai kamar shi akaiwa alheri haka.
Nace ina son asama min wanda zaiyi aikin muyi magana dashi inji yadda aikin zai kaya.
Ba bata lokaci ya aika akira mai Ado magini yazo yana neman shi maza maza.
Ba, a jima ba muna wurin zaune da shi sai ga Ado maginin yazo yai sallama bayan ya dan fita sun gana ya aiko a kirani nai bayanin yadda nake son ginan ya kasance.
Yace nan zuwa safe insha Allahu zaizo min da list din komai aji yadda za, ayi ginan.
Sai bayan sallah isha,i ne muka shirya Fatima ta rakani gidan mu don inga mahaifina.
Mun shiga gidan da gani ba zaman lafiya ko kadan na wuce gaida mama da kyat ta amsa min gaisuwan da nai mata.
Na wuce inda babana yake zaune saman shimfida, muka gaisa dashi yana murna da farin cikin ganina yace ai harda nace idan baki shigo ba da daren nan sai na shiga da safe na ganki can wurin uwar taki.
Nace baba ai na fadawa mama amarya cewa zan dawo da dare yaji dadin har cikin ran shi jin nakira matarshi abin son shi da mama.
Yace ai na dawo Lanto taks gwada min irin alherin da kika zo kikai masu bayan wanda kika aiko dashi jiya kuma ?
Nace ba komai baba ai uwaye na naiwa ba wasu ba, nan na fada mai yadda daddy yace ayi da gidan .
Yace anya Rahama bamu takurawa mutumin nan ba da bani bani ga irin taimakon da yai min kuma yanzu a ce yayi haka akan mu.
Nace baba ni wallahi ban taba rokon shi akan yai man wani abuba ko wani nawa ganin daman shi ne da ganin dacewan hakan dai yasa yakeyi.
Baba shifa daddy haka rayuwan shi yake don akwai shi da tausayin na kasa gareshi sosai.
Yace to Allah ya saka mai da alheri abinda yake nema na Alheri Allah ya bashi duniya da lahira mukace amin .
Sai ga amaryan baba tafito da abinci daga daki tana fafin har ina batun na aika maki dashi can su Jabir ne basu shigo ba ai.
Tuwon masara ne da miyar busassan kubewa sai kamahin kayan yaji yakeyi munaci muna hiran rayuwa da mahaifina yana fada min irin alherin da ya samu ga taimakon da daddy yai mashi.
Daga can naji mama na fadin an dai ji kunya wallahi babu kunya a fake ga maula a gurin suruki don kwadayi kawai.
Lauratu ki kama min bakin ki in ba haka ba kin san halina yanzu ranki zai baci a gidan nan.
Yo bakin ciki kikeyi don Allah ya mayar da yar da bakiso ganin da digon farin ciki ba a rayuwan ta haka ?
Kin sana rabu da iyalina masu so na da zuciya daya don mugun halinki don baki da kunya shine yanzu har zaki wagale baki kina fadin magana son ran ki idan fitsari banza ne kaza tayi mugani.
Banda marasa tarbiya da rashin mutunci da kika tara min a gida suna jawo min magana da abin kunya a gida dagari may kika tsinana min.
Sai naji amarya ta cabe da cewa ai dama duk wanda yace ruwan wani bai tafasa shiko nashi ai ko dumi baiyi haka abin yake.
Nace don Allah dai kuyi hakkuri kubar wanan zancen don Allah yanzu girma yazo ya kamata ku daina hakan.
Haka dazun kuka tara mutane a kofan gidan nan abin ba dadin gani don Allah don Allah na roke ku ku daina yin haka a rayuwan ku.
Daga kofan ta da take zaune tace ke kama kanki ke har yaushe kike
Sai yamma lis na dawo na samu gajiye har tagama abinci da nai sallah nakai na jera nafito ban zauna ba.
Yau ma haka na daure na tafi kamar jiya ba sauki ko kadan a kaina sai na Allah ya gama abinda zaiyi ya koma inda yake yake cewa yaushe zakuyi hutun?
Nace thursday din nan in Allah ya kaimu yace sai ki shirya sunday ku tafi kwana nawa zakiyi a can ?
Nace goma ko sati daya yace wai ko kina da hankali Rahama may zakije ki zauna gida kiyi har sati daya, ?
Saida na hade bakin ciki nace ganin iyayyena da yan uwana zanje nayi yace to ban yarda ba idan kwana hudu yayi maki sai ki shirya ku tafi din.
Banyi magana ba na gyara kwanciya na kawai ina adduan barci da safe na fice abina yana zaune yana lazumi.
Yabini da kallo kawai yana mamakin karfin hali haka irin nawa watau mata kowa da inda take da nata matsalan ke nan.
Wanan yarinyar karama tasan wai ta dakile namiji ita adole fushi take yi wawuyi kanki kikaiwa nina kwashi rabona ko ai.
Da kanki yarinya zaki dawo kamar yadda kika kawo kanki yanzu akai maki susa.
Tun ranan na fara shirina sai dana shirya tsab kafin ranan na danyiwa anty bayani sama sama sai dai ba komai ba.
Mun yi kitso har kumshi don tafiya kawai jiran gari ya waye mu dauki hanya ga yaran nason bina anty tace sai nice zanwa daddy magana amma na rasa yadda zan mai magana don basuyi hutu ba.
Hakana nai masu dabara nace daddy yace idan sunyi hutu zai kawo su mu dawo tare anty ma taban tsaraban da zamukai gida nai mata godiya.
Na dawo part dina ina cewa Fatima ta fito da kayan mu falo sai gashi ya shigo yabi jakar da Fatima ta dauko da kallo, fatima kan na ganin shi ta shige ciki.
Kudi ya miko min yace ga wanan ina ga zasu isheki ai har ku dawo nace akwai kudi a hannuna zasu isheni bai tsaya bin magana naba ya miko min kudin dari biyu ne zur yan dubu da kuma dari biyar.
Yacd nace Hamza ya shiya zaku samay shi a waje zaune yana jiran ku nace na gode a sanyayye.
Yace ku gaida mutanen gida kiyi min godiya wurin baba kafin mu hadu dashi.
Mun fito muka rufe kofa na nufi wurin anty nai mata sallama don naci arziki ba yaran suna makaranta.
Tace kun fito ko nace eh anty to idan kin je ina zaki sauka wurin mama laure ko kuwa nace anty wurin Inna ta dai zan sauka tace anya Rama bazaifi kyau ki sauka gida ba wanan karon ?
Nace anty kin san halin mama ba fasawa zatayi ba bari dai muyi nisa da nisa da ita a rabu cikin mutunci yafi tace shine kuma ai.
Tare muka fito da anty mun samu har an saka kayan a mota ko yana dan kakabewa ba anty ba koni nai mamaki ganin ACURA din daddy ce zamuyi tafiyan da ita ashe.
Mukai sallama da su anty Gajiye ma zata bimu taga gida su dawo da Hamza fatima ita ta shiga gaba ni da gajiye muna baya muka kama hanya.
Sha biyu daidai muna kauyen mu inda kowa yaga motar sai bin mu da kallon mamaki ake don ba, a san ko su waye ba cikin wanan tsaleliyar motar haka ?
Fadan mai gari yana makil da jama, a dagani wani sharia sukeyi a wurin zuwan mu ya dawo da hankalin su a kan mu.
Mun fito aka gane mune ga yara sun kewaye mu sai faman ihu da murnan ga Fatima ga anty sukeyi.
Ba karamin kaduwa nayi ba danaga irin tsaraban da daddy ya lodo muna a bayan motan shi don ban san da su ba saida na zo yanzu ake saukewa.
Nauyi da kunya ne ya kamani duk rashin mutuncin dana tsula masu gashi kuma ya bini da abin arziki kai gaskiya hindatu shu,umace wallahi don nasan ba banza ta barmu ba haka rashin fahinta na shiga tsakanin mu haka.
Don gaba daya gaskiya bakin daddy nake gani ina jin haushin shi haka kawai ba wai marin da yai min ba tun kan haka nake jin wanan yanayin a tare dani.
Abinda ban sani ba ashe shine aikin da akai muna ma daba duka ba so akayi gaba daya ma sakina akaso yayi ranan .
Sai abin ya tsaya iya mari kawai da nasha Allah baikai abin ga saki ba tsakanin mu don gaba daya lokacin haushina da takaicina yakeji.
Marin da yai min ne yadan ji sanyi a zuciyar shi sannu abin ya dan rage mashi yadda yake ji a kaina din.
Nima yadda yake ji haka nake ji idan na ganshi wani haushi da takaicin shi nake ji sai naji ma bani son ganin shi sam a raina.
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > aihausabooks@gmail.com
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
WhatsApp Number: 09017242889
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA, , , ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YABI MUNA HAKKIN MU A KANKI DON ONLINE NOVEL NE WANAN, , , ,
54
Mun yi saurin barin uguwar nace ma mama Altine zan dawo tana ta zabga min addua muka bar gidan.
Har mutane sun fara taruwa a kofan gidan mu amma haka muka wuce bamu tsaya jin takaici ba sai ma Rukaiyya ke fadin mama bata taba fadan gaskiya.
Yanzu tasan Lawali baida gaskiya amma ta zage tana biyewa matar nan suke tijara.
Yanzu ai ta samu daidai da ita ba kamar yadda ta samu innan ki tana gasa mata kwakwa ba a baya ita wanan sunyi daidai don makirace sosai matar .
Murmushi kawai nai mata a raina nace ai sin gamu da sun dace sai suyi tayi yanzu.
Gidan Jatau muka nufa daga gidan mu tare da karin tsaraban da nazo masu dashi.
Tun a kofan gida muka hadu da shi yana ganin mu ya fara wagale baki ya kara tsufa sosai duk furfura ne ko ina fuskan shi har kan shi.
Yana fadin hajiya Rahama ashe an shigo garin namu sannun ku da zuwa nace malam jatau ya gida ya iyali yaune rana na farko da mukai magana ta arziki dashi.
Nace na taki sa, a dana samay ka a gida dama akwai maganan da nake son muyi da kai akan anty na ne.
Ya kara washe baki yace to to Allah yasa alheri ne nace in sha Allahu alherin ne idan ka yarda.
Dama ba wani abu bane so nake a samu dan injimin nika wa anty wanda zata dan rika samun kwabon kashi kaga yanzu ga yara sunyi yawa dole a dan kama ma wani wurin kaima ka huta.
Yaji dadin yadda na fada sai washe baki yakeyi yace to hakan na da kyau idan har zata iya ai yar uwar taki ce ba haguwa ko kana son taimaka mata bata iya tattali ba a rayuwan ta.
Nace in har ka yarda ba matsala sai a gwada agani ko Allah zai karba muna ta wanan hanyan .
Nace babu damuwa za, a gwada a gani idan zai karbu gareta yai min godiya nasa hannu na ciro dubu biyar na bashi nace ga wanan ayi hakkuri dashi hakana.
Sai ga Jatau da tsufan shi har yana dan rusunnamin wurin karban kudin yana ta zabga godiya.
Dama muna tsaye yaran gidan na leko mu har sun koma sun fadawa iyayyen su ga yar uwar Suwaiba ta birni can ta tsaya da baban mu a waje suna wani magana.
Nan dai suka fara sake magana a tsakar gida mu ana gwada muna birni mu da muka ga gwauna.
Sai gamu mun shigo da sallaman mu Rukkaiyya ta kwasa zata wuce su babu ko gaisuwa nace haba dai anty na.
Direct inda suke zaune na nufa tare da masu sallama suka amsa a gyatsire fuska babu walwala nace mun samay ku lafiya yaya yara ya gida ya kuma bayan rabo suka amsa da lafiya kalau sai dayan ce tace anzo lafiya ya mutanen wurin ku nace Alhamdullahi.
Na juya nabi Rukaiyya data fara tafiya don bata daukan wanan a gareta sai ga Suwaiba zanin jikin ta ma dai bai ko kalluwa tayo kan mu da murnan ta.
Inajin suna cewa an dai yi hasara wallahi muka rugumay juna da murna ta rasa inda zata sani don dadi.
Tace Rahama kece kika koma haka kamar baturiya aiko birnin ma ashe amsa ne don naga wasu yan birni da suka zo kwana ki gidan nan ko mu mun fisu dadin gani.
Ashe wai wata yar uwar kishiyarta tazo daga can shine take wanan haibaicin muna shiga dakin ta sai da gabana ya fadi don bazakace mutum mai raine ke kwana ciki ba haka wai kuma harda miji a hakan.
Godiya naiwa Allah a raina da ya rabani da wanan rayuwan na mutanen mu mace da kurciyar ta amma don kazanta da talauci takoma kamar tsohuwa.
Hakana muka zauna takawo muna ruwa cikin wani kofin silver duk ya dafe don tsufa.
Kowa yace bai sha na karba na kafa kai na ji wani mugun karni ya doki hancina haka na daure na hade zuciyana yana tashi.
Mun gaisa muka barke da hiran yaushe rabo a tsakanin mu mun dan jima a zaune nace Fatima miko min jakar nan ta miko min.
Turmi uku na fitar da kudi dubu uku sai sweet da sabulun wanki da omo nace Fatima mikawa matan can wanan kice su raba .
Rahama don may zaki ba su wanan himilin uban kayan haka dako mijin da ta aje su bai iya basu shi.
Ai harshi sai da taba yanzu har dubu biyar kamar na taushe shi na kwace naji sai son banza amma shi bai iyayiwa mutane hakan.
Nace haba dai Anty wanan fa shine sayen girma da mutnci a gareki ba don wani na ba dashi ba sai don ke din nan.
Haka zai sa su gane kin fisu har abada tunda har kina da wanda zai basu abu su karba a bangaren ki.
Hakane kuma inji Rukkaiya dake zuga zancen ita dai Suwaiba duk bakin ciki ya kashe ta akan an ba abokan zaman ta alheri.
Abinda basu taba yi ba sai gasu tare duk kan su sun zo yin godiya sai faman farin ciki suke suna ta zabga godiya da fatan alheri gareni da maigida.
Bayan tafiyan su na fara yiwa Suwaiba da Rukkaiyya bayanin abinda nake so dasu tare da masu fada akan su canza rayuwan su don banji dadin abin da na sama ba a gidan Suwaiba din.
Nace gobe gobe ta kwashe kayan ta zan turo a gyara mata dakin ta zanyi magana da mijin ta sai Rukkaiyya tace a dai gyara muna nima dakina ai ko daben kasa babu kin san auren nawa ba shiri akayi mama kuma wai bata son auren.
To Rahama nagaji da yawo hakana gashi duk babu sa,a na a gari ita mama kin san hakan ko a jikin ta bata damu ba wallahi.
Nace Rukkaiya sai hakkuri da iyayyen mu tun da sun riga sun haife mu tace yanzu ma da zamu fito bakiji abinda take fada min ba wai kada na bada kaina gun Rahama.
Yo Allah na tuba yaya zan rabu da yar uwata ko baki haka balle irin taimakon da kike muna ko bakizo ba ko yaushe aiken ki na saman hanya ana kawo muna duk Altine zata dawo.
Nace ni dai yanzu abinda nake so daku shi ne ku kama kanku don Allah lokaci yayi da zaku dage wurin mai da kan ku abin kwarai don mahaifin mu yai alfahari da haihuwan mu.
Sai naga Suwaiba na kuka tace Rahama laila ke mutum ce dake da mahaifiyar ki duk irin abinda mukai maku a baya baku taba rike mu dashi ba.
Haka ma wanda mahaifiyar mu ke maki baku taba kallon mu dashi ba balle ku rike mu da hakan a ranku.
Don Allah Rahama ki yafe muna duk abinda mukai maki da wanda kika sani dama wanda baki sani ba.
Nace Anty don Allah kibar wanan magana don ni ban taba rike dayan ku da wani abu a raina ba ni dai fatana naga mun rike zumuncin mu da Allah ya kulla a tsakanin mu.
Nan dai mukai ta magana nai masu bayani kan gyaran gidan da maigidana yace aiwa baba idan nazo sukai murna sosai suna cewa.
Ai wanan abin Rahama ba baba akaiwa ba mu akaiwa don mu zamuyi alfahari da hakan a gari.
Ban bar gidan ba sai da na dan masu nasiha na zaman lafiya a fakaice sukai min godiya muka barta.
Gidan Rukkaiya muka tafi naga dakin ta tabani matukar tausayi nasan auren take son zama shiyasa harta daure cikin irin wanan rayuwan haka.
Bayan na dawo gida na samu mutane da dama sunzo gaida ni, wanka nayi don nagaji sosai bayan maigari ya dawo cikin gida taro ya watse a fadan shi ya zauna dani muna hira.
Har cikin raina naji dafin hakan sai nake ji dama ace shine mahaifina, ban boye mashi komai ba na halin rayuwan da muke ciki da kowa a gidan don ina jin shi tankar shi ya haife ni.
A rin yadda ya daukeni a matsayin diyarshi tankar wacce ya haifa yace dani na kara kwantar da hankalina su dai basuyi wa mutum sheri amma duk abinda mutum ya debo akan dan su zai koma a kan shi in hairan in sheran.
Nai mashi bayani kan gyaran gidan da nake so aiwa mahaifina yayi murna kwarai kamar shi akaiwa alheri haka.
Nace ina son asama min wanda zaiyi aikin muyi magana dashi inji yadda aikin zai kaya.
Ba bata lokaci ya aika akira mai Ado magini yazo yana neman shi maza maza.
Ba, a jima ba muna wurin zaune da shi sai ga Ado maginin yazo yai sallama bayan ya dan fita sun gana ya aiko a kirani nai bayanin yadda nake son ginan ya kasance.
Yace nan zuwa safe insha Allahu zaizo min da list din komai aji yadda za, ayi ginan.
Sai bayan sallah isha,i ne muka shirya Fatima ta rakani gidan mu don inga mahaifina.
Mun shiga gidan da gani ba zaman lafiya ko kadan na wuce gaida mama da kyat ta amsa min gaisuwan da nai mata.
Na wuce inda babana yake zaune saman shimfida, muka gaisa dashi yana murna da farin cikin ganina yace ai harda nace idan baki shigo ba da daren nan sai na shiga da safe na ganki can wurin uwar taki.
Nace baba ai na fadawa mama amarya cewa zan dawo da dare yaji dadin har cikin ran shi jin nakira matarshi abin son shi da mama.
Yace ai na dawo Lanto taks gwada min irin alherin da kika zo kikai masu bayan wanda kika aiko dashi jiya kuma ?
Nace ba komai baba ai uwaye na naiwa ba wasu ba, nan na fada mai yadda daddy yace ayi da gidan .
Yace anya Rahama bamu takurawa mutumin nan ba da bani bani ga irin taimakon da yai min kuma yanzu a ce yayi haka akan mu.
Nace baba ni wallahi ban taba rokon shi akan yai man wani abuba ko wani nawa ganin daman shi ne da ganin dacewan hakan dai yasa yakeyi.
Baba shifa daddy haka rayuwan shi yake don akwai shi da tausayin na kasa gareshi sosai.
Yace to Allah ya saka mai da alheri abinda yake nema na Alheri Allah ya bashi duniya da lahira mukace amin .
Sai ga amaryan baba tafito da abinci daga daki tana fafin har ina batun na aika maki dashi can su Jabir ne basu shigo ba ai.
Tuwon masara ne da miyar busassan kubewa sai kamahin kayan yaji yakeyi munaci muna hiran rayuwa da mahaifina yana fada min irin alherin da ya samu ga taimakon da daddy yai mashi.
Daga can naji mama na fadin an dai ji kunya wallahi babu kunya a fake ga maula a gurin suruki don kwadayi kawai.
Lauratu ki kama min bakin ki in ba haka ba kin san halina yanzu ranki zai baci a gidan nan.
Yo bakin ciki kikeyi don Allah ya mayar da yar da bakiso ganin da digon farin ciki ba a rayuwan ta haka ?
Kin sana rabu da iyalina masu so na da zuciya daya don mugun halinki don baki da kunya shine yanzu har zaki wagale baki kina fadin magana son ran ki idan fitsari banza ne kaza tayi mugani.
Banda marasa tarbiya da rashin mutunci da kika tara min a gida suna jawo min magana da abin kunya a gida dagari may kika tsinana min.
Sai naji amarya ta cabe da cewa ai dama duk wanda yace ruwan wani bai tafasa shiko nashi ai ko dumi baiyi haka abin yake.
Nace don Allah dai kuyi hakkuri kubar wanan zancen don Allah yanzu girma yazo ya kamata ku daina hakan.
Haka dazun kuka tara mutane a kofan gidan nan abin ba dadin gani don Allah don Allah na roke ku ku daina yin haka a rayuwan ku.
Daga kofan ta da take zaune tace ke kama kanki ke har yaushe kike