Kanin Ajali

Chapter 13 of 34

ace gara da akayi albarkan auren ake nema ba kyalekyalin auren ba.
Ga gida ya cika da yan uwa da abokan arziki ta ko ina a gidan don bukina kawai suka hallara wasu tsakani da Allah suka zo wasu kuma gulma aga karshen abin ne ya kawo su daga kauyen mu.
Shiko gogan sai waya muke a tsakanin mu inda yake kara karfafa min yadda nake a rayuwan shi da irin taimakon da nayiwa rayuwan shi din.
Anje an gyara min dakina komai tsone gwanin ban sha,awa dai kowa ya dawo yana yabawa irin kokarin da baba kabir din yayi don ba a ma maganan matan shi duk da suma sunyi iya kokarin su kan sha,anin.
Party kan har kala biyu aka sha don jin dadin buki wanda ya shirya da abokan shi yan karya anci ansha an gwangwaje a gurin an dawo ana bada labarin komai.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:55 PM - 🤔🤔🤔: 🙆🏼‍♂️ KANIN AJALI 🙆🏼‍♂️




1️⃣4️⃣




ZAINAB IDRIS MAKAWA




LITTTAFIN KUDI NE IDAN KIN SAYE KIJI TSORON UBANGIJI KADA KI FITAR MIN DASHI DON AMANA NE A TSAKANIN MU KI GUJI NAUYIN AMANA A KANKI YAR UWA IDAN KIN GA MARA TSORON ALLAH TA FITAR KI GUJI SHIGA HAKKIN WANI YAR UWA DON NA BIKI DARI UKU AKAN NOVEL, , , , , , , , , ,




Duk wani abin al,ada na buki angama lafiya sai fatan Alheri ga auren mu da yan uwa da abokan arziki ke gabatarwa a gare ni.
Abokan ango sun rako ango daki daya sha gyara sai kyali yake don katan alatun dayaji wanda a kauyen mu kaf idan da ca muke nabar tarihi a kauyen namu don haduwan dakin namu.
Sai dai may bayan tafiyan abokan ango da kamar minti goma Jamil ya dawo daga rakiyan su yace hadizatul kubura yau dai Allah ya cika muna gurin mu akan jajircewan mu da juna.
Ina dan murmushi na bude fuskana ina fadin bisa ga taimakon baba kabiru bawan Allah muka samu wanan cikan gurin namu da yake Allah yace ni matar kace jamil.
Banda abinda zance da baba kabiru sai fatan Allah ya saka mashi da alheri yadda ya rike zumuci Allah ya bashi ladan zumunci kamar haka.
Duk maganan da nakeyi jamil sai bin dakin da wani irin kallo yake wanda ba zan iya fassara shi a lokacin na burgewa ne ko na wani abu ba.
Budan bakin shi bayan na gama magana sai cewa yayi dani amma dai ke har yanzu yarinya ce khadija wani kokari sukai maki a nan daki kamar na kauyawa.
Da mamaki na juyo ina kallon shi ya ce eh duk irin dukiyan da mahaifin ku ya bari da wanda ya tara maku wanan abin zasuyi maki ga auren ki ?
Yanzu dai ai kinga abinda nake fada maki ko da ina fada baki yarda yanzu don Allah wanan kayan yan kauyen tsohon yayi ya dace ace sunyi maki ?
Tsaye nayi galala ina kallon shi don jin abinda yake fada a lokaci wanda ban san amsan da zan bashi ba kan maganan da yakeyi din.
Yace eh na fada kuma gaskiya nake fadi da ke yar su ce wallahi ba zasuyi maki wanan wullakancin ba haka da komai na zamani zasu kawo muna.
Amma da yake ke baki da wayau har wani addua kike kokarin zabga mashi irin haka ni har kunya naji da abokai na suka shigo suka samu dakin namu a haka.
Yanzu jamil duk wanan uban kayan basuyi maka ba kake nufi yace wallahi basuyi min ba hadiza duk sake su zamuyi musai na zamani da ake yayi mu saka don abin kunya ne a gurina abokai na su zo suga dakin matana haka a wullakance bayan sun san yar gidan wanda na aura.
Na fada maki ba son ku suke da zuciya daya ba kece baki yarda kin kasa fahinta na duk lokacin da nake fada maki sai ki dinga daukan magana kamar ina son hadaki dasu ne.
To ai yanzu kin gani da idanuwan ki abinda sukai maki yar bare kike a gurin su kin fi nan gare su jima wani karamin tv da wasu kujeru na raini da suka saka maki a daki don Allah.
Yar su da suka aurar haka kikaga sunyi mata ke baki tunanen haka da bakin ki ke fada min irin tsaruwan dakin hajara yadda suka gyara mata dakin.
Kasa magana nayi sai tsayjn danayi galala ina kallon shi don yau na tabbatar mutum bai da kunya shi da ko pant ya kasa saya ya kawo min a matsayina na wace zai aura da kowa nasa ya kasa yi mai wani abin azo a gani a matsayin shi na dan su.
Sannan iyayyena sunyi min abin arziki zai zo ya rena mamakon ya yaba da kokarin su a kaina da yake dan duniya ne sai yace koda yake ke har yanzun baki san komai ba ai.
Don wallahi wanda suka sayar da gidan mahaifin ki a abuja ya fadi inda ba a karya kudin da aka sai wanan gidan naku zai iya sai maku ukun wanan ma don girman gidan mahaifin naku.
Kuma kin san gida a abuja tsadane dashi nina dauka ya aje sauran kudin ne ai don laluran ku kawai wallahi nan hankalina ya daga sai dai ina tuna zancen baba kabir akan maganan baba na bashin da banki ke binshi sai nace niko ina ganin baba kabiru ba zai muna haka ba gaskiya.
Ya bata rai sosai yana fadin ke may kika sani don Allah an barku a duhu ana cutan ku ya ja tsuki yana cire tufafin dake jikin shi fuska a daure.
Idan akwai abinda naki baga jamil ya daure mun fuskan shi shima yasan da hakan yaune daren auren mu dashi duk da ba farkon kasancewar mu tare ke nan ba.
Amma sai na koma fadin sun cuci kansu wallahi don mu basu cuce mu ba don amana muke a gare su dan uwansu ya haifa ya bar masu amana duk abinda sukayi mun barsu ga Allah.
Wanan maganan da nayi yasa ya dan sassauta daure fuskan dayayi da farko don ya fara shawo kaina ke nan don duk takona ya sani kamar yunwar cikin shi.
Mun raya dare mu kamar na sauran ango da amarya sai dai da safe kuma ya tashi yana cika yana batsewa duk a kan maganan dai dakin baiyi mashi ba.
Ban fito ba sai da gari ya dan haska zuwa gaida iyayyen shi dake cikin gidan inda na zube daga kofan su ina gaida su da kwana ban san jamil yana dakin zaune ba tare da mahaifi nasa.
Jin muryana mahaifin nasa yace in shigo daga ciki yana fadin ashe kuma haka mayaudaran ubannen ki sukai maki ya tabbata ke nan sun cinye maku gadon ku ko ?
Nace baba basu cinye ba har yanzu kudin bai fito bane na baba yace sunciye mana waye bai san wanan maganan ba ya ta.
Yanzun dai kuyi hakkuri da dan abinda suka kawo maku din tunda kin shigo cikin mu komai zaizo da sauki don ba zamu saka ido muga ana cutan ku ba haka ai.
Nayi maki alkawarin zamu tsaya maki akan komai dake da yan uwan ki muddin muka samay ki a yadda muke son ki mai biyayya a gare mu.
Nace insha Allahu baba mun gode yadai dan muna fadan zama tare da nusar dani akan saurin yarda da iyayyen nawa da nakeyi.
Nayi godiya na bar sashen nasu don tsakanin mu dasu ba wani nisa bane kusan ma dakunan a hade suke sauran yan hayan da ba a tayar ba suna a dayan bangeren su uku.
Ya ganin amarya suna ta zuwa daga gidan mu wasu kuma suna zuwa yi min sallama don komawa gidajen su an bude dayan buhun shimkafan da iyayyenba suka kawo na gara a gidan suna dafa ma yan uwan su da suka zo gurin buki.
Sai dai abinda ke ban mamaki duk wanda yazo yana yaba kyawon dakin nawa in ka debe daidaikun yan uwan jamil dake tabe bakin su.
Dangin mahaifiyar shi da suka zo buki a wurin su nake jin ashe su suka zo da turamay nan da aka kai gidan mu ke nan, nan iyayyen shi su basu kashe mai komai ba kenan.
Ranan dai wuni nayi ina taron baki a gidan sai dai yakan shigo jefi jefi yana wani cika yana batsewa na rasa gane kan shi a gidan ga baki daya.
Zaman sati dayan da mukayi kullun a cikin korafi yake akan shi shirin dakin bai mai ba har dai na hakkura na tambaye shi yanzu yaya kake son ayi ke nan yace yanzun kikai magana dai.
Abinda nake so shine mu sayar da wanan kayan a sai wasu wanda ya dace damu a dakin ina ganin haka zaifi bada ma,ana sosai nace kana ganin haka zai yuyu tun ban kai wata daya da aure ba ace na sayar da kayan dakina.
Baka ganin zasu ga na rena da abinda sukai min a baya yin hakan zai kawo wani rigima a tsakanin mu nan gaba a hasale ya furta ina ruwan su dake yanzu ina sun sauke nauyin su da ke kansu suke gani da wanan abin da sukai maki suna ganin burgewa ne a gurin su.
Yanzu muke da ikon ki basu ba don nauyin ki ya dawo gare mu ke nan ba ruwan su da abinda zamuyi maki anan kuma yanzu.
Nace to shike nan yace da kaina zan kai kayan nan can kauyen mahaifiyana a sayar muna dashi muzo mu cika kudi a sai maki na zamani wanda ake yayi.
Nace idan kana ganin haka zaifi a kai a sayar din na kuma gode da kaunar da kake mun din dani da yan uwa na ya saki wani shu,umin murmushi a fuskan shi.
Bai bar dakin ba nan ya zauna muna hiran yan uwan mahaifina na zage ina fadin karya da gaskiya ga irin rikon da suke muna a gidan baba kabiru din.
Yana ta faman zugani ina hawa ina ganin gaskiya yake fada min don banda masoyi bayan shi a duniyan nan kaf baki daya.
Washe gari ya bude kofan falona ta baya ashe tare da motar daukan kaya yake ina ji ina gani Jamil da wasu mutane suka kwashe kayan falon nan kaf suka fice dashi a gidan.
Sai da yai kwana biyu bai dawo ba a cikin kwana na uku ne ya dawo garin fuska a daure ya shigo min ina jin muryan shi yana gaisawa da iyayyen shi bayan ya gama dasu ne ya shigo yana kara sha min kanshi.
Ba daman in tambaye shi zancen kayan don banga fuskan haka ba a gurin shi abinda ban sani ba ashe ya fita yaje gidan wata dillaliya ya juye mata kayan ta bashi kudin shi ya biya bashin da ake bin shi na party bikin daya hada sai sutura na alfarma da turararuka daya kara saye.
Sauran kuma ya hole da yan matan shi sai da kudin suka kare ya dawo gidan a lokacin shine yake cika yana batewa don kada inga fuska shi in tambaye shi yadda akayi da kudin kayan.
Sai da yaga ban tambaye shi zancen kayan ba wanda ni a zahiri tsoron haka nake ji yasa ban tambaye shi ba amma zancen kaya yana a raina.
Don ina jin kunyan mutane suna shigowa suna ganin dakin haka ba komai a cikin sa alhalin kowa gari yasan amin kayan daki na alfarma.
Matsalan farko dana fara fuskanta shine akan ibada sam Jamil baya sallah ko wani iri da safe sai sha dayan rana zai tashi daga barcin jiya da muka kwanta yayi wanka ya shirya ba maganan yin sallah.
Idan nayi mai magana sai ya hauni da fada yana fadin kin san ni bansan Allah ba sai kin koya min may zaki nuna min akan addini kin dai san na fiki sanin hakan.
Ni da na tashi a gida cikin hausawa yan uwana kuma musulmai na san Al,Qurani nasan hadisi don haka bake zaki nuna min yin sallah ba inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Ni dai na samu gefen gado nayi tagumi ina kallon shi sai ruwan bala,i yake min kan kawai nace dashi ya tashi rana nayi yayi sallah.
Har ta gaji ya mike ya dauki buta ya kurkure bakin sa ya dawo yana tambayana idan na gama abin karyawa in kawo mashi fita zaiyi.
Na mike jiki ba karfi na fita na dauko mai kayar karyawan shi da na aje mai ya zauna sai da yayi kat ya fice daga gidan.
Mikewa nayi na kwashe kaya raina ba dadi ina tunanen maganan umma a karo na farko a raina ashe abinda take hango min ke nan wanda na kaaa hangowa kaina shi.
Tun ba,a je ko ina ba zaman ya fara ban tsoro da Jamil don babu wani dadin auren da zance naji wanda amare suke ji idan anyi aure a farkon aure.
Ga tsoro shi da yake kokarin cusawa a zuciyana dan abu kadan zanyi yanzu ya hauni da fada na fitan arziki yana zagi iya son ranshi ni dai babu zancen wani amarci a gurina sam.
Iyayyen shi kuma da muke zama dasu da akace wai zasu zauna ne don barin iya mu yara a gidan baiyi ba shine suka ga dacewan zaman mu tare dasu din.
Ni dai banga wani amfanin su ba a gidan asalima kamar tsoron dan nasu suma suke ji don har su yakewa wanan tsare gidan nashi da yake min sai dan jefi jefi zakaji yana hira da mahaifin nasa.
Ko idan yana min fada mahaifin nasa ya karbe ya goyi bayan dan nasa kirikiri yana fadin nice banda gaskiya banda mutunci.
Sai dai idan sunga yana cikin dadin rai da nine nake samun sakewa dasu a gidan har zamu dan zauna muyi hira da matan amaryan baban nasa da muke zaune a tare.
Duk wanan baya damu na nidai buri na inga munyi zaman lafiya a tsakanin mu dashi kamar na sauran ma,aurata don sam banda wani walwala balle har in dan fara cikan daki da akeyi idan anyi aure.
Ranan da yan gidan mu suka zo gani na na rasa yadda zanyi akan rashin kayan dakin da babu dakina wanda akai min daga gida da Jamil ya sayar din.
Suna shiga dakin maganan farko da sukai min shine anty hadiza ina kayan dakin ki nace ku zauna mana in fada maku komai a tsanake.
Zama sukayi suna saurarona don jin abinda zance din bayan sun zauna ne muka gaisa nake fada masu sai da aka jera min kayan naga basu min kyau ba na bayar a hurhura min ne za a kawo min wani sati in Allah ya yarda.
Badon sun yarda da magana ta ba don yarda naga suna min wani irin kallon na tuhuma a ransu sai da mukai hirane zasu tafi nake rokon su akan don Allah su rufa min asiri kada su fada a gida sai idan an kawo min kayan zanje in fada a gida.
Sukai min alkawarin ba zasu fadi ba kuma hakan ne don naji shiru ya tabbatar min da basu fadi din ba a gida don banga kowa yazo min da maganan ba.
Jin shirun yayi yawa ne kan kayan yasa ranan na tambaye shi labarin kayan fada ya fara yi abinda yasan ban so ke nan fada yana fadin idan ta ban ai zan kawo maki tunda kin nuna min banda iko a kan abinki yanzu.
Da har zaki bude baki kina tambayana kayan ki kamar wanda baki yarda dashi ba ya fice yana fada kamar yadda ya saba yi idan zaiyi yaudaran nasa a gurina.
Tun ranan da nai maganan kayan ya shiga fushi dani sai ya shigo fuska a murtuke yayi abinda zaiyi a dakin ya fice daga gidan idan ya gama.
Da abin ya ishe gani ban iya gaba ba a rayuwana ranan dai na kudirta a raina zan mashi magana idan yashigo gidan don mu fahinci juna dashi.
Dama ni tsoro na kada yan gidan mu su sanda wanan zancen a dauki mataki a kaina shine kawai damuwa na a lokacin.
Can cikin dare ina barci ya shigo dakin ina jin motsin shi na bude idanuwa ina kallon shi filo ya dauka ba tare da yai min magana ba zai nufi falo dashi da sauran abinda yake bukata a dakin.
Sannu da dawowa nayi mai bai amsa min ba sai kokarin fita yakeyi a dakin zuwa falo na mike na bishi falon yana kokarin kwanci a saman dogon kujera don kujera kawai ya bar min a dakin sai ledan kasa a lokacin.
Zama nayi a dayan kujeran dake kusa dashi ina fadin haba my may ya faru da zafi haka kake fushi dani kan dan magana kankani.
Ya juyo a fusace yana fadin oh baki ma san abinda kikai min ba ke nan har kina daukan maganan dan kankani a gurin ki ko ?
Nace ni banga abindana fada mai zafi ba daga tambayan kaya sai ka hau fushi dani haka kawai yace eh tunda kin nuna min kayan ki kayan ki ne ni banda iko dasu ke nan.
Na marairaice murya ina fadin ni ba haka nake nufi ba my ka sani wanan ba halina bane amma idan maganan ya bata maka rai kayi hakkuri don Allah.
Sai hawaye ya zubo min wanda ban san ko na may ye ba a lokacin ya dago kai yana kallona tare da fadin mayye kuma na kuka yanzu daga magana.
Nace naga maganan ya bata maka rai ne sosai don kawai na tambayi ba,asin kayan dakina daka kwashe da sunan hurhura min su.
Yace baki yarda ba dani ke nan kika kasa hakkuri har kiga iya guduna a kan kayan na kara marairaicewa nace ni dama tsoro nake ji azo daga gida a samu babu kayan a dakin nan.
Yace idan sun zo sunyi magana ki fada masu abinda na fada maki a baya, ina kin gane yanzu na gyada mai kai a hankali wanan ne yasa muka shirya ya bar fushin da yake

Download complete TXT · Novel page