Kanin Ajali

Chapter 25 of 34

kowa yanzu ya kawo ido yasa muna aga iya gudun mu da mazajen namu da muka dauka uwa uba a gare mu.
Sai bayan wucewan su magana ya fara tashi wai da kudin ta mijin ta ya nemi aikun daya samu wai wanan kangon da muka saye babu nata a halin yanzu.
Waya na nema na kirata na fara mata korafi sai bata bari nakai ayya ba ta hau fada tana fadin wai ni a ina naji wana zancen wanan magana ba gaskiya bane duk wanda ya fada mun kuwa.
Haka dai magana ke faman yawo kan mazajen mu sun cinye muna kudaden mu duk wanan maganan da ake fada baba kabiru baice damu kala ba kan zancen mazajen namu.
Kuma ya hana iyali shi suyi muna magana don haka ne zancen bai daga sosai ba yadda wasu suka so cikin dangi a dauki mataki akan mu.
Yakan ce kubar yaran nan inda kuka gansu idan masara taji wuta da kanta zatai kara ai ba sai an tambaye su ba duniyace.
Don yanzu ana magana zasu ce kuna son ku kashe masu aure ne don baku kuka haifesu ba sai yan uwa suce kwarai kuwa Alhaji kabiru.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Na samu wannan kawana dake makwabtan mu tasa mijin ta ya dauko muna manja da garin rogo a can inda yake da zai dawo.
Ita nata zata aika dashi ne gidan su a sayar ni kuma tace in saida nawa a nan cikin unguwar mu din tabar min sai idan mun sayar zamu tura mai kudin ya kara sayo muna wani.
Alhamdullahi don sana,ar ta karbu min a cikin unguwar tamu da farko da Jamil ya gani ya fara tambaya a ina na samo kudin da na sai wanan abin ?
Ban so in fada mai ba amma danaga matsin yai yawa yana tambaya don zargina yake ko na samu wasu kudine naki fada mai don har bugun cikin baffa kanina yayi a waje bai ji komai ba.
Dole na fada mai inda na samu kayan ina sayarwa din nan ya hau fada wai yarabani da wanan matar don ta fini wayewa shi bai son rikici da dauko magana.
Na dai kyaleshi yayi fadan shi ya gaji ya sa mun ido mutane sai shigowa suke dare da rana suna fadin abasu manja ko gatin kwaki da sugar.
Dadi dadi na hada kudin farko don a cikin sati biyu komai ya kare muka tura ya sake turo min da wani don ita ma an sayar mata da nata acan gida da ta kai.
Wanan ma yayi saurin karewa da wuri don yanzu mutane sun sanda ina sayarwa kuma a cikin sauki na hada kudin mijin kawata cif da sunan washe gari in kai mata ta tura muna wurin mijin nata.
Washe gari tun da safe Jamil ya fita kan zai tafi wani kauye yace min a can zai kwana don haka sai dana gaba duk aikin gida na shirya na nufi inda na aje kudin don in shiga in mika mata.
Kudi yace dauke ni inda kika aje sai da na dafe kirji na nakai kasa don capert nake dagawa na aje ba wanda yasan inda nake aje kudi a dakin idan na hada su.
Don gudun haka tunda nasan halin shi da kudi ni kadai a daki sai zufa ke karyo min a lokacin don nasan babu wanda zai dauki kudin nan sai Jamil din don ba mai shiga dakina har kurya.
Ko baki nayi a falo nake ajesu basu shiga min daki, don kunyan dakin da nake ji ni kaina ban son wata mace yar uwana ta shiga min dakin.
Don haka ban zargi kowa ya shigo min daki ba na rasa yadda zanyi a lokacin sai daukan diyana nayi na nufi gidan da mahaifi shi yake.
Duk da nasan abu mawuci ne ya goyi bayan dan nasa a lokacin sai banda yadda zanyi dole in je gurin shi da wanan maganan.
A gigice na isa gidan muka gaisa dasu sai na fashe da kuka na fara fada masu halin da ake ciki budan bakin mahaifin nashi tun ban karasa ba shine.
Kina nufin Jamil ke nan yai maki sata ko wa da kika zo nan din ranan matar mahaifin nashi tayi min abin kwarai don kafin in magana tace .
Haba malam idan bata zo nan ba ina kake son taje da wanan abin kunyan kai kullun danka bai laifi itace mai laifi haba a rika yin abu don Allah mana.
Yarinyar ga dai tana iya kokarin ta wurin ganin ta kyautata mashi amma hakan bai isa ba sai an hada da dauke na mutane da ta dauko kuma yanzu mai kake son tace ma mai kudin do Allah.
Ai sunan danka ne zai baci a unguwar tunda kowa yasa halin shi a gareta ido kawai mutane suka sa masu hakanan.
Naji dadin wanan maganan har cikin raina don yau ta fadi alheri a gamay dani bayi son zuciyan da suka saba ba.
Fada ya hau yi da ita amma bata barshi ba dole tsohon ya sauko tare da fadin nawa ne kudin na fada mai yana gyaran zama yace sai dai ayi raba daidai kije ki nemi saura ki cika masu kudin su.
Ya kirga rabi kamar yadda yace din ya bani na fito ina share hawaye ina zan shiga cikin garin nan in samo rancen kudi in ba mutane kudin su.
Ko dana koma yan gidan mu ke fadin matar tazo nema na sai da gaba na ya fadi lokacin haka na daure na shiga gidan ban boye mata komai ba na fada mata halin da nake ciki da kudin na bata rabin da mahaifin shi din ya bani.
Na bata hakkuri kan zan nemo sauran in karkare mata in an kwana biyu hakkuri ta bani na fito ina hawaye gidan zuwa gidana.
Bai dawo ba sai bayan kwana uku ya dawo in da ya samay ni zaune a cikin tagumi ban ko iya mai sannu da dawowa ba don zakace ba kauye ya fito ba da yace yaje.
Shi sai wani fresh yake karawa ni ko ina figewa banda wani kumari a jikina ko kadan daka ganni, kasan damuwa ya samu gurin zama a zuciyana.
Ganin yadda na fuske shima ya fuske ya shiga daki ko may yayi a ciki can ya fito yana fadin ke lafiya kuwa mutum ya dawo ko sannu da zuwa ba zaki mai ba.
Wani kallo na watsa mashi tare da kawar da kaina daga kallon shi ina fadin azzalumi baiji dadi ba wallahi.
Ka rasa wanda zaka yaudara sai matar ka ta gida mai dawainiya da yayan ka duk wani nauyi da hakkin ka ka rataya a kaina .
Haka bai ishe kaba sai ka hada da kudin mutune ka kwashe ka tona min asiri a gari.
Ya zaro ido yana fadin wa kika mayar barawon ki gida nan nace kai tas ya kwashe ni da mari sai da ba dafe wurin don zafi.
Hakan bai sa na fasa magana ba nace ka kashe ni ka huta dama nasan mutuwa ta kake son ji macuci kawai azzalumi.
Ba wanda zai shigo ya daukan min kudi dakin nan sai kai ba zan zargi kowa ba wallahi don kaine ka kwashe su .
A harzuke yace an kwashe din kiyi abinda zakiyi in zaki iya wawiyar banza kawai kan wasu raggan kudin ki zaki dinga kirana da macuci can kudin da ko mota basu isheni shiga ba.
Nace baka nayi da zakace kada in kiraka da macuci ya kara daga hannun zai mare ni na sa mai ihu sai ga yan hanyan gidan a sukwane sun shigo suna tambayan ko lafiya ?
Ina kuka na fara fada masu abinda yai min don duk cin kudina da jamil keyi wanan din yafi bata min rai sosai wallahi.
Don ya nuna min bai damu ba duk halin da zan shiga da mutane ni na sani ke nan shi ba damuwan shi bane hakan.
Bayan sun gama ji ba mai shiga tsakanin miji da mata sai cewa sukayi inyi hakkuri in kyaleshi mu san yadda zamuyi kudin mutane ya fito.
Haka suka dinga fita daya bayan daya suka barmu a dakin dagani sai shi ya shiga kuryan daki ya fito yana fadin wawiya da bata san ciwon kanta ba.
Da kika fada masu kwatar maki zasuyi ko may ai na dauka zasu sa in biya ki ne dole ina kuka nace Allah dai zai kwatar min hakkina ba wani ba.
Mu kai ta yada ma juna bakaken magana har ya gajibya fita daga gidan ya barni nan ina tukukin bakin ciki da na daman auren shi.
Sai mutum daya ne cikin yan hayan mu ya iya mai magana kan abinda yakeyi din bai kyauta ba gaskiya kudi mutane ne fa ya dauka kuma ya sani yaya yake son inyi.
Don Allah Jamil idan ka samu kudi kaba wanan yarinyar kudin ta don hakan zubar mutunci ne a gurin mace wallahi .
Kaga dai duk cikin matan mu tafi kowa hakkuri yau gashi kakai har ta tona maka asiri a bainan jamma,a haka ai irin haka babu dadi.
Jamil din yace ta dai tona ma kanta tunda bata da wayau don kawai na dauki kudin ta zatai min wanan tonon asirin haka a idon jamma, a.
Mutumin ya sake fadin ai abin ne da cin rai jamil yace malam naga fa kana son shiga hurumin da ba naka ba gaskiya yace a, a niba haka na bane ina dai guje maka hakkin marainiya ne a kan ka.
Kada ka manta matar ka marainiyar Allah ce ta gaskiya kowa kuma nan yasa tare kuke cin kudin gadon ta idan ya samu aiko kaga hakan tayi kokari wallahi.
Don ba ko wace mace bace yanzu zaka samu haka nan yace kada ka fada min maganan banza Nasir ina ruwan ka ne da zancen mu wai da matana.
Basuji dadin juna ba da mutumin nan kowa ya fadawa dan uwan shi bakaken magana ya kulla da wanan mutumin da yake gani wai ya raina mashi wayau shi.
Tun wanan lokacin ya sa wana mutumin da matar shi agaba gidan da anyi abu zai fara fadin ba mutumin arziki bane dama ya kamata su tashi su bamu gida.
Sai dai wanan karon baiyi nasaran haka ba kaina don ban bashi hadin kai yadda yaso ba yake min a baya kan yan hayan mu.
Sannu a hankali na samu na biya kudin bashin da ake bina koshi da taimakon dan abin da nake samu a wurin baba kabiru aboye bai sani ba na biya.
Don daya sanin karbe kudin zaiyi ba wani wuyan aiki bane a gurin shi don haka yanzu na fara boye mashi komai nawa nima saboda yanzu na fara fanhintar shi.
Don a gaba shi maman jinior zata aiko batun kudin ko tazo da kanta yana ji bai cewa komai idan kuma na mashi magana sai yace idan ta samu zai bayar.
Ko hakan da yake fadi don mahaifin shi wanan karon ya fita bayan shi yayi mashi fada sosai har ranshi ya baci shine yake fadin wai zai biya da baki don baida niyar biya din.
Tun da yaji baba yace yana nema na yana daki kwance yaron yana fita zubur ya fito daga dakin yana tambaya ko lafiya baba ya aiko yans nema na ?
Nace ban san ko may yake nema na dashi ba in dai na gama zanje in ji dalilin kiran yace ki tafi ni zan karasa sauran akin daya rage din.
Ban ki nasa ba na gyara jikina na nufi gidan namu inda na samu baba na gida bai fita ba baya mun gaisa ne yake fada min zancen kudin mu ne ya taso bayan long proces da akayi yanzu ranan monday zamu je muyi signing din documents din a Abuja.
Wani irin farin ciki ne ya turnuke min zuciya ta idan mai karatu bata manta ba na fada maki kudin an kasa su uku ne kadan kadan suke zuwa muna ke nan.
Murna a gurina ba a cewa komai hakama dana koma gida da zumudi Jamil yake tambayana lafiya dai ko ?
Ba bata lokaci na labarta mai abindake faruwa ya wani washe baki yana murna tare da fadin wai Allah dai ya jikan baba.
Karo na farko danaji yayiwa mahaifina addu,a ke nan ita mahaifiyar mu ba a magana kanta.
Nan wuyan talaucin da muka fito ne a ciki yasa yai wanan addua,an haka da bai ma san yazo mashi a baki ba a lokacin.
Nan ya fara haba haba dani bai fita yawo sosai sai lokaci lokaci yakan dan fita ya dawo ana jiji dani da yarana lokacin har fita yake da yaran wurin fira kofan gida inda suke taruwa.
Yanzu idan mun zauna baida magana sai na tsara yadda za,ayi idan kudi sun shigo hannun mu har da fadin zai fito dani gari don zai sai min babban waya irin na kowa ni da ko nokia banda shi.
Sai yan uwa idan sunji haushi rashin wayana ya damay su zasu dan sai min yar nokia in rika bai kai wata daya a hannun na idan matsi ya kama mu in sayar in sai wani abin.
Gashi nima bakina yasaba da dadi irin na jamil yanzu ba ko wani abinci nakan iya ci ba in ba yan kayan kwalama ba da sauran su.
Ni dai ina jin shi yana ta tsara yadda yake so abin ya kasance wanan karon dariya nakan yi a raina kawai do ko da tsiya sai na gyara dakina wanan karon.
Nagaji da rufe kofa da boye boye wa kawayena idan sun zo gidana har kunyar yadda dakina yake nakeji don ko na wata tsohuwa yafi shi dadin kallo.
Ranan mondaya shi da kanshi ya rakani gidan baba kabiru tunda asuba don asubanci zamuyi mubar garin don mu isa da wurin during warking ahours.
Sai dai bai yarda mutanen gidan mu sun gashi ba yana isa kofa saida yaga na shiga ya koma shi bai shiga ba lokacin.
Nasan nasa wayau do kada aga zalaman shi a fili ne yasa ya boye hakan ya labe daga kofan gida yaki shiga daga ciki.
Mun isa lafiya mun samu wanan kudin a yadda sukai muna bayani suna da yawa sosai don haka zai fi na farko dana baya yawa ke nan .
Murna fal a zuciyana baki har kunne muka dawo gida da farin ciki zuciyar mu fara kal da jin wanan zancen.
Na samu ya gyara daki ya dafa abinci ya jera min yana jiran dawowana kamar ance mai da kudin zamu dawo dayani daga zuwan mu.
A gidana baba ya sauke ni suka tafi ina shiga na samu yana zaune yana jirana a cikin duhu duk da babu wuta a lokacin amma haka yake zaune kamar maye shi kadai a falon mu.
Nan yai muna sannu da zuwa ya karbi goyo na yana tambayan ta ya hanya kamar yarinyar ta iya magana lokacin.
Yace bari yai mata wanka don kada gajiyan hanya ya hanata barci shi yai mata wanka ya bata abinci taci ta kwanta tunda dama a gajiye muke.
Ya fara tambayana yadda akayi ina labarta mashi yayi wani irin ihun murna tare da fadin kice zamu faso gari ke nan sosai wanan karon.
Da yakw dan duniyan namiji ne bai barni na huta ba duk ko da gajiyan dana debo a hanya sai da ya kusanceni ranan .
Don kawai ya kara gyara min rai niko ina jin dadi a raina ga miji na tatali na ana sona don sai ka dauka ya daina halinshi ne yanzu na bariki.
Tun wanan ranan suka shiga yin meeting dashi da mijin kauwata wai idan kudi sun zo ga yadda zasuyi muna dashi .
Zakace abin na Allah ne ake shiryawa lokacin don sunce bazasu yarda su baba kabiru suna muna wayau ba ko wani lokaci duk da fa su baba basu karban ko kwandala daga cikin kason mu din.
Amma sun ce wai wayau suke muna kawai don sun dauke mu yara kanana suna yi muna yadda sukaga dama da hakkin mu .
Muko mun hau munga ga masoyan mu na asali masu kaunar mu da zuciya daya don Jamil yana cewa.
Da ke nan da baisan ciwon kan shi ba suke cinye kudin ba abin kwarai da mukeyi dashi yanzun kan tanadi sosai za a yi muna gaskiya.
Fadin haka da yakeyi yasa na kara yarda dashi sosai don na dauka talaucin da muke ciki yasa yanzu yayi hankali ne.
Mun dauka wani sati kudin zai fito a yadda aka nuna muna a can da mukaje abuja sai gashi shiru har mako uku ya share ba wani labari kuma na kudin .
Nan dai ya shiga kuma sake magana yana fadin kila ma su baba ne da sherin su kudin an sako basu fada muna ba kai ba dai abinda bai fadi kan kudin.
Har turani gida yayi in koma in tambayi baba cewa munji shiru baba dai yayi dariya yace hadiza banda abinki ko wancan karon ai haka akayi ko ?
Sai lokacin da muka ji su kin san gwaunati ba ayi mata dole tunda ba abin mutum daya bane abu ne na taro kowa dake cikin system din jira yake yi kamar mu.
Na dawo gida na fada mai abinda baba yace ya ja tsuki don takaicin da yake ji a lokacin yana fadin wanan shegen gwaunatin basu da tausayi wallahi.
Yakan yi maganan kudin nan kusan sau uku ko hudu a wuni shi dai ina ganin lokacin damuwan shi bai wuce yaji ance kudi sun shigo muna ba shine nasa.





ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU.
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Tun barin kanwata garin ya koma min ba dadi ni kadai nake harkokina don na dada maki tun farko jamil ya rabani da duk wata kawa da nake da ita a baya.
Haka kuma wa yanda ma a yanzu nakeyi baya bari muyi wani dogon hurda yake watse haduwan tamu a lokaci guda.
Sannu a hankali ya fara sayar da dan mashin din dana saya kudi

Download complete TXT · Novel page