Kanin Ajali
Chapter 26 of 34
suna dan shigo min ta hanyan mashi din .
Ni kadai naci kukana na share hawayena don ba wanda zan fadawa ya dube ni tunda kowa ya gama fahintar zaman mu da jamil din yanzu.
Don ko mutum ya nuna min kulawa ya shigs zancen mu daga baya zan iya ba mutum kunya in barshi a ciki da jin nauyi don zan dawo mu shirya da jamil din ne daram.
Wanan daliln yasa a yanzu ma ban san wanda zan kaiwa kuka na ya share min hawayena ba ta hanyar kiran jamil din yaji ba,asin zancen..
Har ya daukan mun mataki akan jamil din sai dai kassh babu mai iya kundun balun share min wanan hawayen nawa a lokaci daya.
Wanan dalilin yasa dole na hakkure da zancen nayi kuka na ni kadai ba tare da sanin kowa ba sai dai yan gidan mu suna dauka mashin din yana nan har yanzu.
Kanina Baffa na iya samu da maganan don yanzu ya tasa shima ranshi ya baci sosai da jin wanan maganan sai dai nasha fada a gurin shi sosai.
Na koma kamar nice kanwarc shi ba ya ba shi ya tunkari jamil da zancen mashin din kai tsaye ba tare da wani jin tsoro ba kamar yadda saura suke tsoron shiga maganan mu.
Sun buga sosai dashi don har ya kai su ga bacin rai sosai dashi inda ya fito fili ya nuna mashi yana cutawa rayuwana gaskiya.
Sai jamil din ya nuna mai ai shi ke da ikon komai nawa tunda shi yake aure na ba wani ba idan ina dashi muci in shike da ma ci zamuyi a tare.
Sai dai nayi zaton a yadda suka kwasa da Baffa din ba zai kara kallon kayana ba again sai dai ashe hali zanen dutse.
Don mai hali akace baya barin halin sa muna haka ne kamar ya lafa baya duban kayana sai harkokin shi yake yi .
Niko ina faman dan fadi tashi don kudi ya dan dinga shigo min tunda bai bani na kashi din koda ya sayar da abina kuwa.
Gidan iyayyen shi naje ranan gaida mahaifin shi ban wani dade ba na dawo gida misalin daya saura ina shiga falona a cikin sauri ban kula da cewa fridge dina bai falon ba sai bayan na dora girki na dawo don in huta.
Sai lokacin idona yakai gurin fridge din wayau na gani babu fridge babu dalilin shi a gurin .
Allah yasa a zaune nake don bansan lokacin da nayi bayan kujeran ba da yai min mazaune da wuyana na jingine dashi.
Sai dai na nemi kuka ko ihu na rasa a idona ko wani yaki zuwa a lokacin sai ajiyan zuciya nake faman saukewa don tashin hankalin da nake ciki.
Ina cikin wanan halin sai gashi ya shigo gidan niki niki da kayan abinci kala kala a hannun shi yana faman washe baki .
Ganina a wanan yanayin yasa ya sausauta fara,an da ya shigo gidan dashi yana tambayana ko lafiya ?
Da kyat na iya budan baki nace mai Jamil ina fridge dina cikin wani irin murya mai kama da ta mai kuka ko tashin hankali.
Bai bani amsa ba lokacin sai kokarin aje kayan abincin dake hannun shi da yakeyi ban damu da in san kayan ko damay damay ya sayo ba a lokacin.
Jin shiru yasa na mike tsaye daga zaunen da nake ina sake tambayan shi ina fridge dina jamil amsa ya bani a takaice da fadin na fitar.
Kakai ina na tambaye shi dagowa yayi ya juyo ya fuskance ni da kyau yace ya kike son muyi idan ban sayar ba na sayo muna abincin da zamuci .
Ko haka zamu zauna da yunwa baya Allah ya hore muna abinda zamu sayar muci abinci dashi ba sai naje wurin wani ina tona ma kan mu asiri ba.
Wani irin kallon mamaki nayi mai tare da fadin kana nufin ke nan da kayana haka zamu tabbata da cin komai nawa ko may ?
Yace ciki daure fuska ko yau ma gorin naki ya tashi ne don kawai na sama ma kan mu mafita nace da abina din yace,
Yace ke nan kina nufin abinki ba nawa bane ga yadda kikai maganan nan a yanzu.
Nace ni ba haka nake nufi ba sai dai abin yayi yawa ne yanzun zakace wanan dan abin da ka shigo dashi shine iya kudin fridge din nawa ko may ?
Ke nan kina ganin cutar ki zanyi ko may da kike fadin hakan ?
Banda abin fada sai kawai na fice daga falon na barshi a ciki girki na fita na karasa har na gama na dawo na samay shi kwance saman tree seater yayi matangali da hannayen shi.
Har na shigo na aje mai abinci bai dago kai ya kalle ni ba nima hakan dana aje fita nayi daga dakin .
Har tsowon wani lokaci abinda nake ji a zuciya bai barni na bude ledojin da yashigo dasu dakin ba ya fito zuwa wurin randar ruwan mu yana deba da kanshi don zuwa yayi wanka.
Ban tankashi ba don nasan fushi dani yake sai nima na share shi mu tafi a hakan da yake so din laifin ni akaiwa kuma yana kokarin ya juye shi a kaina.
Ashe kamar yadda ya saba kirkiro min zuwa unguwa idan yana son zai cuta min haka ma wanan karon yayi min ya turani gaida mahaifin shi din don yaji dadin fita da fridge din gidan.
Don yasa idan ina nan ba zan yarda ba don ina samun dan taro da sisi da fridge din ina rufawa kaina asiri shine yayi dabara turani in gaida mahaifin shi din.
Don ya samu ya yaudare ni din ya kuma yaudara din sai dai ta annabawa yin hakkuri dashi yanzu.
Mun kai sati biyu a hakan shi da kanshi ya gaji ya sauko daga motar fushin da ya shiga ya nemi shiri dani.
Sai dai shirin nasa na yaudara ne ya yaudare ni idan mun shirya ya samu cutar da yai min daga baya kuma.
Dadi dadi da muka shirya sai da yaja wani dan lokaci baiyi yaudaran nasa ba har ina dauka a raina don maganan da nayi mai ne yasa shi yin laushi.
Sai dai matsalan neman matan shi abin gaba gaba yake sosai don yanzu bai boye min cewa suna tare da Ruth.
Don jita jita nazo min kala kala akan alakan shi da ita wanda har na kasa danne hakurina a lokacin haka yasa na tayar mai da hankali kan zancen.
Sannun a hankali ya nuna kamar ya daina harka da ita a yanzu hakan yai min dadi sannun a hankali na dan fara sana, a don dan kudi ya dinga shigo min na kashi.
Sai dai banyi dace ba don shi muke har cefane dashi muci tare da yayana ko dashi ma din hakan yasa ina sana a kamar ba yi nake ba.
Abin nawa ba karuwa sai ma rikicin dake shirin hawa kaina a lokacin don kudin mutane da nake hadawa a cikin sana, an tawa.
Don da zaran yaga dan kudadeb sun taru zai san dabaran da yayi ya karbe su a hannu na sai yaga ba abinda ya saura zai daina tambayana kudi.
Da zaran kuma yaga Allah ya rufa min asiri ta wani fannin zai kara dawowa ya lalabe ni ya karbi kudin da haka rikici da zaman gida ya fara gagarana a gida .
Ko yaushe ina wajen neman wa kaina abin rufin asiri ga yarana sun fara tasawa yanzu ga ragga yana batun kashe mu a gida.
Abinci kan duk inda zai shiga ya fita ya samo mai dan dadi yana yin shi don muna cin abinci lafiyayye ba laifi.
Sai da ta fannin sutura ba kai muna kallo biyu ranka bai baci ba da mu don kamar wasu yan kauye muka koma dan da diyana.
Don ko dinki zai muna sai sallah kuma ba wani abin kwarai zai dinka muna ba daga wando da riga sai wani shegen yadi da ban san inda yake samo su ba.
Sai daga baya nake ji a gurin yan uwan mu wai ai Ruth ce ke zama ta dinka muna kayan mai kama da gwajo muna sakawa.
Duk yadda na iya gaye zuwa gidan mu sai inji yan kanne na suna kushe ma kwalliyan da nayi din wanan abin yana matukar bankanta raina sosai.
Har dai suka kai ga fada min gaskiya ranan naji bacin rai sosai a zuciyana jin wai farkan shi ce ke muna dinki ashe.
Don ni cewa yake min wai wani telan shi ne ke dinka muna don dinkin yaran zaka ganshi kamar yar kanti na gaskiya don ta iya dinki sosai ba laifi.
Na dawo gida na aza mashi jidali da zage zage sai da ya fice ya bar min gidan don haushi yana matukar mamakin yadda yan gidan mu ke saurin gane sirin shi a saukake.
Wanan abin ya kara jawo kiyayya a tsakanin shi dasu inda anty ke yawan shan zagi a gurin shi komai yace wanan matar ai shu,umace ta kwarai.
Bakajin kalamin dadi a bakin shi daya shafi yn gidan babana kabiru kullun sai aibanta su yake a bakin shi.
Wani lokaci nakan ji haushin hakan wani lokacin kuma idan ni aka batawa zan biye mashi mu zage su a tare.
Gashi dai ba damuwa sukayi da suzo gidan mu ba su sai can ba a rasa ba zaka ga sun zo gidan sai dan gurin anty ne karamin bai kwana uku shi bai zo gurina ba ya duba ni koda kuwa yana sauri ne.
Wanan yasa namu yazo daya da yaron sosai don har shawara nakan yi dashi sosai har shi Jamil din ma yana sakewa yaron saboda yawan kawo muna ziyaran da yake akoda yaushe.
A cikin hikima jamil yayi muna dabaran karban kudin yan hayan mu ya koma ta hannun shi.
Wanda yasan cewa bani kadai keda hakkin kudin hayan ba amma bai hana shi karbewa ba idan an bayar da kudin shekara.
Sai gashi wasa wasa Jamil sai canza yan hayan gidan ya keyi idan dan sabani ya hadasu da mutum yanzu zakaji ya fara korafin, korar mutum a gida.
Sai ya zama dani da yan uwana sai abinda yace damu duk sunayi ne akan suna bashi girman shi ne hakan da sukeyi.
Wanan dan uwan nawa shine nake dan samu yana ban shawara duk da kankantan shekarun shi kuma hakan yana mun dadi sosai.
Don ina amfani da shawaran shi kuma ina ganin fa,idan hakan sosai ina kuma samun karuwa da walwala da hakan .
Zan tura shi duk inda nake son abu zaije ya biya mun bukatana a cikin lokaci batare da bata rai ba.
Ranan ina gida nazo gaida mutanen gidan mu sai ga kanin nawa ya shigo ganin a gida mun gaisa shine yake fada min ai yaga Jamil yanzu da carpet din dakina ko wurin wanki zai kai ne yake tambayana ?
Gabana ne ya fadi don jin abinda ya fada min din ba tantama ko ba a fada ba nasan ya dauka zai sayar ke nan.
Da yake gida nake sai ban nuna wani abu ba na aje zancen da fadin eh wanki yakai muna sai kuma godiya ga Allah ba kowa a gurin da yake fada min zance.
Ban wani dade ba a gidan dole na shirya zuwa gida hankali a tashe na shiga falo na sai wayau.
Ya kwashe carpet din ya fita dashi nasan sunana sorry don nayi bye bye da shi ke nan don ba dawowa gidan zai yi ba .
Kamar yadda sauran suka fice babu dawowa gidan shima wanan din haka ya tafi har abadan ibada.
Ban wani wahal da kaina gurin tambayan shi ba don nasan ko na tambaya din ma a banza ne.
Haka ko ya shigo min gida yana wani cicika wai shi rako ke nan yake min abu daya nasan na fada shine ko mai mutum yayi shida Allah.
Bai kula ni ba duk da yasan dashi nake ya mayar dani mahaukaciya mara hankali ga wani hali daya tsiro min dashi.
Idan ya daka min tsawa sai na rude ko gabana ya dinga faduwa ba wani dadin rai a tsakani na dashi cikin wanan lokacin.
Ga fita sai lokacin da yaga dama zai dawo gida don kan shi ba ruwan kowa da dan uwa sai idan yana da bukata na zai tayar dani a cikin dare ya biya bukatan shi a kaina.
Idan ya gama kuma zai fice daga dakin yaje gurin kwanan shi ya kyale mu don kullun cikin kiran zafi yake a dakin mu shi bai iya kwana a ciki wai.
Kowa a gari yana min kallon tausayi do abin ya daina ba mutane haushi sun koma tausayina yanzu kuma.
Don sun san ba karamin cutamin yake yi ba babu dai yadda zan yi don an fahinci sona ya rinjayi nasa a raina.
Nima kaina nasan ina son jamil fiye da komai arayuwa na don shi ma din da yake kokari nuna min haka ada can baya yanzu ya bari.
Zama kawai yake dani na hakkuri da juriya a rayuwan shi don ba yadda zaiyi damu ko may oho ?
Haka dai nake dauriyan yin hakkuri muna zaune da juna ba yabo ba fallasa a tsakani mu sai mutane ke jin haushin da takaicin zaman mu.
Kuyi hakuri dani wanan labarin haka yazo min koni na matsu ya kare don takaicin dake cikin sa ga kuma matsalan da ya shigo na waya sai dai yanzu Alhamdullahi gaskiya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Yanayi ya canza muna baki daya sai zaman kunci da zaman hakkuri ya rage min a gidan Jamil.
Gashi ba wani jin dadin Jamil din nake ji ba ko kadan tsawa da hattara ne a tsakanin mu ko mai nayi banyi daidai ba a gurin shi.
Hakana nake hakkuri da shi don son shi da nake ya rinjayi nasa a yanzu tunda ni tsakani da Allah nake son shi dama.
Sabanin shi da nake ji mutane na fadin don kwadayi ya aureni ba matar sa bane ni don ko ganin mu kayi ba zaka taba dauka shine mijina ba a yarda.
Don sai kace shine ya tashi a birni nice tashin kauye din yanzu don duk yanayina ya koma na tifical bakauya a baki daya.
Tun Mutane sun jin haushi na har sun koma tausaya min na zama abin tausayi da kwatance a gari ga kowa da ya sanni a baya.
Muna cikin wanan yanayin ne labarin barin garin Ruth wace ta musulunta yanzu ta koma maryam sunan mahaifiyar Jamil yazo min.
Naji dadin samun wanan labarin sosai a raina don ko ba komai na samu salama a raina yanzu in huta da wani abun takaicin da yake min din.
Ashe zance bai kare ba kwanton bauna yayi min sai gashi bayan kamar wata biyu da barin garin ta shima ya shirya wai gari zai bari zai koma Abuja ya fita nema.
Sun shirya da wani abokin shi ya bashi labarin ana samu sosai idan mutum yana sana, a a can din.
Shiri ya fara yi sosai don tafiya da yasa a ranshi nidai nawa ido ga tafiyan nashi don ban tada wani hankali na ba ga tafiya.
Har ya gama ya sa rana ba tare da ya barmu da wani abin kirki ba da zai tafi don kukan babun da yakeyi ko yaushe yanzu tunda komai ya kare.
Muna haka ne ya tafi ina jin dadi miji na ya tafi abuja neman kudi nasan yanzu zamu samu walwala mu sake don tsananin yayi yawa sosai.
Acewan shi da yaje zai yo muna sako ya aiko muna da abinda zamu ci ni da yara ni kuma na yarda da hakan saboda yadda yake cika bakin shi da tafiya.
Sai bayan tafiyan shi da kamar wata biyu shiru ba sako babu dalili ga dan kudin hayan da nake dan dogora dashi ya karbe yayi tafiyan shi wai da shi zai ja jari a can idan ya tafi.
Haka na kama dan buga buga ina samun abinda zanci da yarana ba wanda zan nufa a cikin yan uwa don da na samu kin su nayi a baya.
Don abin duniya da ya rufe min ido koda yake ba laifina bane idan nace zan ba wani abu yanzu zai bata rai yace shi may ya taba taimaka min dashi.
Amma shi nasa suna ci har na kauye sai sunzo idan sunji na samu kudi a lokacin yanzu ko duk da baya nan sun san irin wahalan da mukeyi bai sa sun taimaka min ba.
Bama wanda ke zuwa inda muke sai nice nakai dan je in ziyarce su wani lokacin haka zan dawo ba wanda zai ban komai a cikin su.
Ranan nayi bakuwa tazo wurina dan abincin dana dafa na zubo mata tare da ruwan sha duk da ba mai sanyi bane na kawo mata.
Na zubo ni da yarana kamar yadda muka saba zubawa idan zamuci mun yi nisa dacin abincin ne take fadin ashe maryam tabar garin nan ?
Sam na mance da wata maryam nake tambaya wace maryam take magana tace Ruth mana data musulunta kan miji ki nace.
Cikin bata rai wanan yar iskan har na manta da zancen ta yanzu ai na bata amsa cikin canza yanayin fuskana.
Tace aini su matar wan mijin ki suka ban namaki don da sanin su ake komai suka munafunce ki dkn ko shirin tafiyan dasu akayi shi.
Duk wani kayan da bata tafi dashi ba kuma su tabawa kyauta su kai wa yan na mutane ai basuyi ba ta kare zancen da fadi hakan.
Raina naji ya baci sosai sai dai nayi dauriya danne zuciya muka dan zage su da mugu;hali su sai yamma ta bar gidana na rakata ta hau mashin.
Ina dawowa gida hankalina ya daga sosai haka nake kamar zawo banda hakkuri ko kadan don haka ban iya kwana ba sai da naje gidan su mukayi tsiya dasu naji dan sanyi a raina.
Sai dai sun karyata zancen wai kazafi akai masu wanan ba
Ni kadai naci kukana na share hawayena don ba wanda zan fadawa ya dube ni tunda kowa ya gama fahintar zaman mu da jamil din yanzu.
Don ko mutum ya nuna min kulawa ya shigs zancen mu daga baya zan iya ba mutum kunya in barshi a ciki da jin nauyi don zan dawo mu shirya da jamil din ne daram.
Wanan daliln yasa a yanzu ma ban san wanda zan kaiwa kuka na ya share min hawayena ba ta hanyar kiran jamil din yaji ba,asin zancen..
Har ya daukan mun mataki akan jamil din sai dai kassh babu mai iya kundun balun share min wanan hawayen nawa a lokaci daya.
Wanan dalilin yasa dole na hakkure da zancen nayi kuka na ni kadai ba tare da sanin kowa ba sai dai yan gidan mu suna dauka mashin din yana nan har yanzu.
Kanina Baffa na iya samu da maganan don yanzu ya tasa shima ranshi ya baci sosai da jin wanan maganan sai dai nasha fada a gurin shi sosai.
Na koma kamar nice kanwarc shi ba ya ba shi ya tunkari jamil da zancen mashin din kai tsaye ba tare da wani jin tsoro ba kamar yadda saura suke tsoron shiga maganan mu.
Sun buga sosai dashi don har ya kai su ga bacin rai sosai dashi inda ya fito fili ya nuna mashi yana cutawa rayuwana gaskiya.
Sai jamil din ya nuna mai ai shi ke da ikon komai nawa tunda shi yake aure na ba wani ba idan ina dashi muci in shike da ma ci zamuyi a tare.
Sai dai nayi zaton a yadda suka kwasa da Baffa din ba zai kara kallon kayana ba again sai dai ashe hali zanen dutse.
Don mai hali akace baya barin halin sa muna haka ne kamar ya lafa baya duban kayana sai harkokin shi yake yi .
Niko ina faman dan fadi tashi don kudi ya dan dinga shigo min tunda bai bani na kashi din koda ya sayar da abina kuwa.
Gidan iyayyen shi naje ranan gaida mahaifin shi ban wani dade ba na dawo gida misalin daya saura ina shiga falona a cikin sauri ban kula da cewa fridge dina bai falon ba sai bayan na dora girki na dawo don in huta.
Sai lokacin idona yakai gurin fridge din wayau na gani babu fridge babu dalilin shi a gurin .
Allah yasa a zaune nake don bansan lokacin da nayi bayan kujeran ba da yai min mazaune da wuyana na jingine dashi.
Sai dai na nemi kuka ko ihu na rasa a idona ko wani yaki zuwa a lokacin sai ajiyan zuciya nake faman saukewa don tashin hankalin da nake ciki.
Ina cikin wanan halin sai gashi ya shigo gidan niki niki da kayan abinci kala kala a hannun shi yana faman washe baki .
Ganina a wanan yanayin yasa ya sausauta fara,an da ya shigo gidan dashi yana tambayana ko lafiya ?
Da kyat na iya budan baki nace mai Jamil ina fridge dina cikin wani irin murya mai kama da ta mai kuka ko tashin hankali.
Bai bani amsa ba lokacin sai kokarin aje kayan abincin dake hannun shi da yakeyi ban damu da in san kayan ko damay damay ya sayo ba a lokacin.
Jin shiru yasa na mike tsaye daga zaunen da nake ina sake tambayan shi ina fridge dina jamil amsa ya bani a takaice da fadin na fitar.
Kakai ina na tambaye shi dagowa yayi ya juyo ya fuskance ni da kyau yace ya kike son muyi idan ban sayar ba na sayo muna abincin da zamuci .
Ko haka zamu zauna da yunwa baya Allah ya hore muna abinda zamu sayar muci abinci dashi ba sai naje wurin wani ina tona ma kan mu asiri ba.
Wani irin kallon mamaki nayi mai tare da fadin kana nufin ke nan da kayana haka zamu tabbata da cin komai nawa ko may ?
Yace ciki daure fuska ko yau ma gorin naki ya tashi ne don kawai na sama ma kan mu mafita nace da abina din yace,
Yace ke nan kina nufin abinki ba nawa bane ga yadda kikai maganan nan a yanzu.
Nace ni ba haka nake nufi ba sai dai abin yayi yawa ne yanzun zakace wanan dan abin da ka shigo dashi shine iya kudin fridge din nawa ko may ?
Ke nan kina ganin cutar ki zanyi ko may da kike fadin hakan ?
Banda abin fada sai kawai na fice daga falon na barshi a ciki girki na fita na karasa har na gama na dawo na samay shi kwance saman tree seater yayi matangali da hannayen shi.
Har na shigo na aje mai abinci bai dago kai ya kalle ni ba nima hakan dana aje fita nayi daga dakin .
Har tsowon wani lokaci abinda nake ji a zuciya bai barni na bude ledojin da yashigo dasu dakin ba ya fito zuwa wurin randar ruwan mu yana deba da kanshi don zuwa yayi wanka.
Ban tankashi ba don nasan fushi dani yake sai nima na share shi mu tafi a hakan da yake so din laifin ni akaiwa kuma yana kokarin ya juye shi a kaina.
Ashe kamar yadda ya saba kirkiro min zuwa unguwa idan yana son zai cuta min haka ma wanan karon yayi min ya turani gaida mahaifin shi din don yaji dadin fita da fridge din gidan.
Don yasa idan ina nan ba zan yarda ba don ina samun dan taro da sisi da fridge din ina rufawa kaina asiri shine yayi dabara turani in gaida mahaifin shi din.
Don ya samu ya yaudare ni din ya kuma yaudara din sai dai ta annabawa yin hakkuri dashi yanzu.
Mun kai sati biyu a hakan shi da kanshi ya gaji ya sauko daga motar fushin da ya shiga ya nemi shiri dani.
Sai dai shirin nasa na yaudara ne ya yaudare ni idan mun shirya ya samu cutar da yai min daga baya kuma.
Dadi dadi da muka shirya sai da yaja wani dan lokaci baiyi yaudaran nasa ba har ina dauka a raina don maganan da nayi mai ne yasa shi yin laushi.
Sai dai matsalan neman matan shi abin gaba gaba yake sosai don yanzu bai boye min cewa suna tare da Ruth.
Don jita jita nazo min kala kala akan alakan shi da ita wanda har na kasa danne hakurina a lokacin haka yasa na tayar mai da hankali kan zancen.
Sannun a hankali ya nuna kamar ya daina harka da ita a yanzu hakan yai min dadi sannun a hankali na dan fara sana, a don dan kudi ya dinga shigo min na kashi.
Sai dai banyi dace ba don shi muke har cefane dashi muci tare da yayana ko dashi ma din hakan yasa ina sana a kamar ba yi nake ba.
Abin nawa ba karuwa sai ma rikicin dake shirin hawa kaina a lokacin don kudin mutane da nake hadawa a cikin sana, an tawa.
Don da zaran yaga dan kudadeb sun taru zai san dabaran da yayi ya karbe su a hannu na sai yaga ba abinda ya saura zai daina tambayana kudi.
Da zaran kuma yaga Allah ya rufa min asiri ta wani fannin zai kara dawowa ya lalabe ni ya karbi kudin da haka rikici da zaman gida ya fara gagarana a gida .
Ko yaushe ina wajen neman wa kaina abin rufin asiri ga yarana sun fara tasawa yanzu ga ragga yana batun kashe mu a gida.
Abinci kan duk inda zai shiga ya fita ya samo mai dan dadi yana yin shi don muna cin abinci lafiyayye ba laifi.
Sai da ta fannin sutura ba kai muna kallo biyu ranka bai baci ba da mu don kamar wasu yan kauye muka koma dan da diyana.
Don ko dinki zai muna sai sallah kuma ba wani abin kwarai zai dinka muna ba daga wando da riga sai wani shegen yadi da ban san inda yake samo su ba.
Sai daga baya nake ji a gurin yan uwan mu wai ai Ruth ce ke zama ta dinka muna kayan mai kama da gwajo muna sakawa.
Duk yadda na iya gaye zuwa gidan mu sai inji yan kanne na suna kushe ma kwalliyan da nayi din wanan abin yana matukar bankanta raina sosai.
Har dai suka kai ga fada min gaskiya ranan naji bacin rai sosai a zuciyana jin wai farkan shi ce ke muna dinki ashe.
Don ni cewa yake min wai wani telan shi ne ke dinka muna don dinkin yaran zaka ganshi kamar yar kanti na gaskiya don ta iya dinki sosai ba laifi.
Na dawo gida na aza mashi jidali da zage zage sai da ya fice ya bar min gidan don haushi yana matukar mamakin yadda yan gidan mu ke saurin gane sirin shi a saukake.
Wanan abin ya kara jawo kiyayya a tsakanin shi dasu inda anty ke yawan shan zagi a gurin shi komai yace wanan matar ai shu,umace ta kwarai.
Bakajin kalamin dadi a bakin shi daya shafi yn gidan babana kabiru kullun sai aibanta su yake a bakin shi.
Wani lokaci nakan ji haushin hakan wani lokacin kuma idan ni aka batawa zan biye mashi mu zage su a tare.
Gashi dai ba damuwa sukayi da suzo gidan mu ba su sai can ba a rasa ba zaka ga sun zo gidan sai dan gurin anty ne karamin bai kwana uku shi bai zo gurina ba ya duba ni koda kuwa yana sauri ne.
Wanan yasa namu yazo daya da yaron sosai don har shawara nakan yi dashi sosai har shi Jamil din ma yana sakewa yaron saboda yawan kawo muna ziyaran da yake akoda yaushe.
A cikin hikima jamil yayi muna dabaran karban kudin yan hayan mu ya koma ta hannun shi.
Wanda yasan cewa bani kadai keda hakkin kudin hayan ba amma bai hana shi karbewa ba idan an bayar da kudin shekara.
Sai gashi wasa wasa Jamil sai canza yan hayan gidan ya keyi idan dan sabani ya hadasu da mutum yanzu zakaji ya fara korafin, korar mutum a gida.
Sai ya zama dani da yan uwana sai abinda yace damu duk sunayi ne akan suna bashi girman shi ne hakan da sukeyi.
Wanan dan uwan nawa shine nake dan samu yana ban shawara duk da kankantan shekarun shi kuma hakan yana mun dadi sosai.
Don ina amfani da shawaran shi kuma ina ganin fa,idan hakan sosai ina kuma samun karuwa da walwala da hakan .
Zan tura shi duk inda nake son abu zaije ya biya mun bukatana a cikin lokaci batare da bata rai ba.
Ranan ina gida nazo gaida mutanen gidan mu sai ga kanin nawa ya shigo ganin a gida mun gaisa shine yake fada min ai yaga Jamil yanzu da carpet din dakina ko wurin wanki zai kai ne yake tambayana ?
Gabana ne ya fadi don jin abinda ya fada min din ba tantama ko ba a fada ba nasan ya dauka zai sayar ke nan.
Da yake gida nake sai ban nuna wani abu ba na aje zancen da fadin eh wanki yakai muna sai kuma godiya ga Allah ba kowa a gurin da yake fada min zance.
Ban wani dade ba a gidan dole na shirya zuwa gida hankali a tashe na shiga falo na sai wayau.
Ya kwashe carpet din ya fita dashi nasan sunana sorry don nayi bye bye da shi ke nan don ba dawowa gidan zai yi ba .
Kamar yadda sauran suka fice babu dawowa gidan shima wanan din haka ya tafi har abadan ibada.
Ban wani wahal da kaina gurin tambayan shi ba don nasan ko na tambaya din ma a banza ne.
Haka ko ya shigo min gida yana wani cicika wai shi rako ke nan yake min abu daya nasan na fada shine ko mai mutum yayi shida Allah.
Bai kula ni ba duk da yasan dashi nake ya mayar dani mahaukaciya mara hankali ga wani hali daya tsiro min dashi.
Idan ya daka min tsawa sai na rude ko gabana ya dinga faduwa ba wani dadin rai a tsakani na dashi cikin wanan lokacin.
Ga fita sai lokacin da yaga dama zai dawo gida don kan shi ba ruwan kowa da dan uwa sai idan yana da bukata na zai tayar dani a cikin dare ya biya bukatan shi a kaina.
Idan ya gama kuma zai fice daga dakin yaje gurin kwanan shi ya kyale mu don kullun cikin kiran zafi yake a dakin mu shi bai iya kwana a ciki wai.
Kowa a gari yana min kallon tausayi do abin ya daina ba mutane haushi sun koma tausayina yanzu kuma.
Don sun san ba karamin cutamin yake yi ba babu dai yadda zan yi don an fahinci sona ya rinjayi nasa a raina.
Nima kaina nasan ina son jamil fiye da komai arayuwa na don shi ma din da yake kokari nuna min haka ada can baya yanzu ya bari.
Zama kawai yake dani na hakkuri da juriya a rayuwan shi don ba yadda zaiyi damu ko may oho ?
Haka dai nake dauriyan yin hakkuri muna zaune da juna ba yabo ba fallasa a tsakani mu sai mutane ke jin haushin da takaicin zaman mu.
Kuyi hakuri dani wanan labarin haka yazo min koni na matsu ya kare don takaicin dake cikin sa ga kuma matsalan da ya shigo na waya sai dai yanzu Alhamdullahi gaskiya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Yanayi ya canza muna baki daya sai zaman kunci da zaman hakkuri ya rage min a gidan Jamil.
Gashi ba wani jin dadin Jamil din nake ji ba ko kadan tsawa da hattara ne a tsakanin mu ko mai nayi banyi daidai ba a gurin shi.
Hakana nake hakkuri da shi don son shi da nake ya rinjayi nasa a yanzu tunda ni tsakani da Allah nake son shi dama.
Sabanin shi da nake ji mutane na fadin don kwadayi ya aureni ba matar sa bane ni don ko ganin mu kayi ba zaka taba dauka shine mijina ba a yarda.
Don sai kace shine ya tashi a birni nice tashin kauye din yanzu don duk yanayina ya koma na tifical bakauya a baki daya.
Tun Mutane sun jin haushi na har sun koma tausaya min na zama abin tausayi da kwatance a gari ga kowa da ya sanni a baya.
Muna cikin wanan yanayin ne labarin barin garin Ruth wace ta musulunta yanzu ta koma maryam sunan mahaifiyar Jamil yazo min.
Naji dadin samun wanan labarin sosai a raina don ko ba komai na samu salama a raina yanzu in huta da wani abun takaicin da yake min din.
Ashe zance bai kare ba kwanton bauna yayi min sai gashi bayan kamar wata biyu da barin garin ta shima ya shirya wai gari zai bari zai koma Abuja ya fita nema.
Sun shirya da wani abokin shi ya bashi labarin ana samu sosai idan mutum yana sana, a a can din.
Shiri ya fara yi sosai don tafiya da yasa a ranshi nidai nawa ido ga tafiyan nashi don ban tada wani hankali na ba ga tafiya.
Har ya gama ya sa rana ba tare da ya barmu da wani abin kirki ba da zai tafi don kukan babun da yakeyi ko yaushe yanzu tunda komai ya kare.
Muna haka ne ya tafi ina jin dadi miji na ya tafi abuja neman kudi nasan yanzu zamu samu walwala mu sake don tsananin yayi yawa sosai.
Acewan shi da yaje zai yo muna sako ya aiko muna da abinda zamu ci ni da yara ni kuma na yarda da hakan saboda yadda yake cika bakin shi da tafiya.
Sai bayan tafiyan shi da kamar wata biyu shiru ba sako babu dalili ga dan kudin hayan da nake dan dogora dashi ya karbe yayi tafiyan shi wai da shi zai ja jari a can idan ya tafi.
Haka na kama dan buga buga ina samun abinda zanci da yarana ba wanda zan nufa a cikin yan uwa don da na samu kin su nayi a baya.
Don abin duniya da ya rufe min ido koda yake ba laifina bane idan nace zan ba wani abu yanzu zai bata rai yace shi may ya taba taimaka min dashi.
Amma shi nasa suna ci har na kauye sai sunzo idan sunji na samu kudi a lokacin yanzu ko duk da baya nan sun san irin wahalan da mukeyi bai sa sun taimaka min ba.
Bama wanda ke zuwa inda muke sai nice nakai dan je in ziyarce su wani lokacin haka zan dawo ba wanda zai ban komai a cikin su.
Ranan nayi bakuwa tazo wurina dan abincin dana dafa na zubo mata tare da ruwan sha duk da ba mai sanyi bane na kawo mata.
Na zubo ni da yarana kamar yadda muka saba zubawa idan zamuci mun yi nisa dacin abincin ne take fadin ashe maryam tabar garin nan ?
Sam na mance da wata maryam nake tambaya wace maryam take magana tace Ruth mana data musulunta kan miji ki nace.
Cikin bata rai wanan yar iskan har na manta da zancen ta yanzu ai na bata amsa cikin canza yanayin fuskana.
Tace aini su matar wan mijin ki suka ban namaki don da sanin su ake komai suka munafunce ki dkn ko shirin tafiyan dasu akayi shi.
Duk wani kayan da bata tafi dashi ba kuma su tabawa kyauta su kai wa yan na mutane ai basuyi ba ta kare zancen da fadi hakan.
Raina naji ya baci sosai sai dai nayi dauriya danne zuciya muka dan zage su da mugu;hali su sai yamma ta bar gidana na rakata ta hau mashin.
Ina dawowa gida hankalina ya daga sosai haka nake kamar zawo banda hakkuri ko kadan don haka ban iya kwana ba sai da naje gidan su mukayi tsiya dasu naji dan sanyi a raina.
Sai dai sun karyata zancen wai kazafi akai masu wanan ba