Kanin Ajali

Chapter 28 of 34

kan abinda ya fada min din.
Haka muke zaman duk in yazo baifi yai wata daya ba ko sati uku ya koma inda ya fito da sunan neman kudi yake a abuja.
Ana son fada min gaskiya sai dai ana gudun surutuna wajen shi injawa mutum magana akai yasa kowa yayi shiru da bakin shi aka zuba muna ido aga iya gudun mu.
Sana,a kan ina dan yi don in samu kwabon kashi da diyana kar mu gani a gurin mutane musanman abinci do ban yarda suje daukan ido gurin yan hayan gidan mu.
Wanan zuwa ya dade bai koma ba muna zaune dashi a gida tunda yazo yayi sallah tare damu yake zaune a gida.
Bai komai sai dan buga buga a cikin gari mukeyi har ni don rufawa kan mu asiri a gari ba laifi tunda albashin shi yana zuwa duk wata.
Dashi muke samu muna karyan ci bashin da yake turani in samo muna wani abin don bukatan mu na gida damu da yarad mu.
Akwai wani lokaci da akai albashi ya nuna min ba kudi gashi yasa naciwo muna bashin shinkafa a guri makwaciyar mu har mudu goma.
Gashi dajin anyi albashi ta fara aiko min da sako in bata kudin ta shi kuma ya nuna min ba kudin sai dai tayi hakkuri har wani wata.
Cikin dare ina barci nake jin hayaniyar mace a kofan mu da sauri na mike ina saurare ashe bayeraban dake sai da kayan sanyi nasha ne a unguwar mu tazo bin bashi itama take wanan hayaniyar dashi haka.
Ni dai ban kula ba don haka ban ma fito ba tunda ba maganata bace nima tawa ta isheni dashi ai.
Sai da suka gama ya bata hakkuri bayan yayi mata alkawarin zai samu abinda ya rage mata bashin dashi.
Da ya shigo gidan ne nake mashi magana kan abinda yake baida kyau tunda anyi biya ya biya mutane kudin su kawai zaifi.
Fada ya hauni dashi waini zan koya mai abinda zaiyi ko may ko nafishi sanin duniyane inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Dole na kyaleshi na kwanta raina babu dadi ga wanan halin na Jamil ace mutum baya tsoron bashi har wurin mata yake cin bashi a waje.
Fitina bai kare ba da safe ina shirin dora wutan abin karyawa sai ga mai kudin shikafa da kanta ta wai ala dole kudi ta take so a lokacin tunda anyi biya taji.
Na rasa abinda zan ce mata ga matan gidan mu sunyi shiru da mazajen su suna sauraren mu don haka na fada daki na samay shi.
Nasan ba barci yakeyi ba yadai lafe ne kwance nake fada mai mata mai shin kafane ta shigo ya ce yaya nake son yayi da ita shi.
Daga waje kuma ina jin tana fadin ke nake jira fa don akwai inda zan tafi daga nan din ban samu kulawa daga gare shi ba dole na fito na bata hakkuri zan kawo mata zuwa anjima ta tafi.
Ina aikin da nakeyi ina tunane a raina inda zan samo kudi in biyata tunda ni ta sani , har na gama ban samo mafita a raina.
Ina gamawa nayi wanka na shirya lokacin shi har ya karya yayi sakkon fita daga gidan ya barni a zato shima neman kudin ya fita yi don mu biya bashin.
Nima dai ban zauna ba fita nayi zuwa gidan yar uwata yar gurin baba kabir don bamu da nisa nida ita can naje na fada mata halin da nake ciki da kudin mutane.
Sai da tayi min kwakwazon don may nasan halin mijina zan yarda in biye mashi inje ci mai bashi duk nassn ai ba biyana zaiyi ba .
Da kyat da lalami ta aramin dubu biyar bayan nayi mata alkawarin zan biyata a cikin sati biyu abinka da dan uwa ganin yadda nake kuka ta tausaya min ta bani aro ban ko shiga gida ba da kudin naje nakaiwa matar kudin ta saura kuma nadan sayo abin bukatan gida dashi.
Shiko bai shigo ba don yasan ba abinda zamu dafa da rana don haka bai damu ba ko yaya zanyi da yarana.
Sai dare sosai ya shigo gidan yana wani cin magani dani nima ban kula shi ba hakana na kwanta na kyale shi.
Ko tashin zancen kudin matar bai min ba ga kwanakin da na dauki alkawari wa yar uwata yana karasowa na bata kudin ta.
Hankalina ya tashi sosai don haka na yanke shawaran zuwa gidan mu wurin anty don ta rokan min kanne na su bani wani abu in samu in biyata kudin ta.
Da naje gidan kunya da nauyi ya hana in mata magana kamar yadda nayi niya sai ma itace taga damuwa a tare dani take tambayana ?
Ko lafiya ta ganni a haka nake cewa ganinan dai anty sai kuma na fashe mata da kuka don ban san ta inda zan fara mata bayanin abinda ke tafe dani.
Hakkuri ta shiga bani tana fadin hakkuri zakiyi hadiza matsalan mijin ki kin saba dashi nace cikin kuka anty bashi yasa naje naci yaki biya.
Nan dai na kwashe komai na fada mata muna cikin magana ne sai ga kanni ya shigo dakin kallo daya yai min ya kawar da kan shi gareni.
Don yanzu haushina suke ji suma ga shi sun gane Jamil yayi amfani damu mun saba da iyayyen mu masu kaunan mu tsakani da Allah.
Don yanzu shekaru sun kora sun yi wayau fahintar wani abu daga iyayyen namu don haka suke jin haushi har dani baki daya.
Anty ce ta iya mai magana akan abinda ke faruwa dani da Jamil din yace cikin tsaki anty bar wanan da kike gani ko yanzu ta samu kudi kara bashi zatayi wallahi.
Ai tasan halin mijinta take biye mashi tasan mayaudari ne macuci tunda anyi daya anyi biyu yanzu jira yake na uku yazo ya cinye shike nan ya korata.
Naji haushi maganan shi don ina neman abu a gurin su ban tsaya ya fada min maganan banza ba nan na haushi nima don ban son mutum yai min zancen mutuwan aure na ko kadan.
Tunda nasan kowa hakkuri yake da auren shi kowa kuma da irin kaddaran da yake gani ga rayuwan shi ni da wanan na dogara na bashi amsa.
Anty ce ta katse ni da fadin in bi a sannu tunda nema abu muke a hannun shi dole na sassauta harshena gareshi.
Da kyat da sudin goshi ya yarda zai bani amma da sunan aro idan na samu zan biya shi abinshi sai bayan ya yarda ne ya kawo maganan kudin hayan da Jamil din ke cunyewa yanzu.
Don lokaci ya kusa na biyan kudin yan hayan gidan mu don ba zasu yarda ina cinye kudi ko wani shekara ba da mijina mu kadai.
Yace karshen shi ma ba nike cin kudin ba shine mai cinyewa ya kyale kowa ranan dai kanina ya fada min magana iya son ran shi sai da anty ta taushe ni.
Na yace in tafi idan ya ciro kudin zai kawo min har gida da yamma ina komawa gida na samu Jamil yana cika yana batsewa wai na fita yawo na bar gida ba kowa.
Kyaleshi nayi ban fada mai abinda naje yi ba don in har ya sani sai yasan yadda yayi yaci wani abu a cikin dubu goman da za a aramin din nan.
Do haka naja bakina nayi shiru inda nayi sa, a koda kani yazo ya dan fita har ya bani kudin na boye bai gidan.
Sai dai kafin ya tafi ya shigo ya samay mu muna hira ya zauna suka gaisa a cikin hiran ne yake tambayan wai yaushe ne sauran kudin mu zai fito har yanzu shiru.
Amsan da Baffa di ya bashi ni kaina naji mamaki don cewa yayi dashi kudi tunda suna nan ko yaushe sukazo daidai ne.
Don masu kudin ma basu damu kanar masu son cin banza ba ai yana fadi haka ya tashi yace zai tafi nayi mai sallama shi bai tanka shi ba.
Yana fita Jamil din yace naga yanzu yaron nan yana son ya raina ni ko don yaga na damu da damuwan ku ne ko yana ganin yanzu ya kawo karfi ne shi ?
Ni dai ban bashi amsa ba na share shi yaci gaba da fadin ni zai cewa masu son banza ke nan mune masu jira muci banza ke nan ko ?
Ni abu ya damay ni ban tsaya bin ta nasa ba don tunanen maganan yaron kan kudin hayan da yayiwa anty ya damay ni a raina sosai .
Tunda yace basu yafe min ba tunda ba ni kadai keda gadon kudin ba balle mijina yai ta karbewa yana ci shi kadai.
Don haka wanan shekaran shi zai karbi kudin da kanshi gurin yan hayan nako san akwai tsiya da Jamil ke nan tunda ba kunya ke gare shi ba kan kudi da kowa yana ja tunda shi ya zama cima zaune.
Ina samu kudin nan washe gari naje na kaiwa yar uwata kudin ta nan ta dorani ga sana,an da zanyi da sauran canji na daya rage min cikin dubu goman da akace an ara min ne.
Na fara juyawa a hankali tunda banda komai ya karbe duk dan wanda nake juyawa a baya .
Dan zaman ma da yake yanzu a gida sai ya gundure ni na kwammace ace ya fita din da yake yi yanzu zuwa wani gari neman kudi.
Ko lalura zai rage min a gidan don na gane nisa da nisa dashi yanzu ya fiye min dadi da idan yana gari bai yi tafiya ba.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Sannu sanu zance ke zuwa min ban yarda akan jamil da dadiron shi wai basu rabu ba sun canza gari ne har yanzu ya tare da ita.
Da farko wanan zancen ya tayar min da hankali sosai don har yangida mu naji zancen a gurin su sai ban yarda da su ba.
Sai dai abinda ke daure min kai kuma shine yanzu zaman may yake a gida hakan ya kara ban kwarin gwiwan rashin yarda da zancen.
Karshe dai na kasa hakkuri na tunkare shi da maganan da nake jin din a bakuna da yawa na mutane.
Nan ya shiga fada yana zagi sai na fada mashi wanda ya fada min don kotu zai kai mai shi kara hankalina ya tashi yadda naga yana fadan nayi ta bashi hakkuri.
Yace daga karshe idan na sake kawo mai wana magana ni zaiyi karan bata mai suna inyaso zan fitar da wanda ya fada min din.
Hakan yasa na yarda dashi na basar da zancen duk wanda ya tare ni da maganan sai i nuna mai ba gaskiya bane wanan magana .
Gani ban iya boyo ba don har gidan mu naje na fada masu yadda muka kwashe dashi din kan maganan.
Nan sukai min caaa a kaina suna fadin yasan su suka fada yasa yace hakan da in kyale shi yai karan nasu daga wanan lokacin suka kara daukana shasha wace dai bata san abinda takeyi ba ma.
Kowa ya kawo ido yasa mun a kan zancen ga gaskiya ana gani aka kyale ni dashi mu tafi a hakan .
Kunci da talauci ya isheni babu sauran inda zan tafi in kai kukana kuma a tausaya min don ansa ko an bani shi zai karbe.
Yasa yanzu babu sauran dan uwa da ke tausaya ma al, amarina kuma sai dai irin su baba kabir dana zama ma kamar dolen shi.
Don abinda yake muna bai ko yiwa "ya"ya cikin shi gaskiya don yana matukar tausaya muna sosai a rayuwa .
Ba dai yadda zaiyi ne mun riga da mun zabi mazajen mu dasu yasa suka saka muna ido sai dai taimakawa idan suna da halin yin hakan.
Ga yanzu abin na baba kabir yaja baya sosai do yanayin da kowa na kasan nan ya shiga yanzu shima ba samu yake kamar can baya ba.
Babu sauran abin kwarai da yarage min a daki sai kujerun dake falona kawai kula na kwarai da idan nayi baki ko na Jamil banda na fita kunya a gidana.
Haka nake ta manejin rayuwa a wahalce don rashin da yai min katutu a gidana kamar ni kadai ce iyayyena suka fara mutuwa a duniya su barni.
Yau ma ina kwance saman dogon kujeran falona tun safe nake aikin sakawa ina warwara a zuciyana don rashin samun mafita gashi ko kudin sayen garin kwaki banda shi.
Balle shika ko wani abinci da zamu sarrafa a gidan.
Shawara na yake a karshe in sayar da da gadona daya saura min a dakin wands shi kadai na saura dashi daga cikin kayan da akai min tun gida.
Duk da ina fargaban hakan a raina amma kuma shine kawai mafita a gareni yanzu don in rufawa kaina asiri a gidana.
Tunda ba kowa ke shiga min dakina ba dama iyakar bakona falo don ko banza ina jin kunyan a shigo aga dakin hakana ba katifan kwarai a dakin.
Ya shigo nake fada mai shawaran dana yanke sai washe baki yayi yana fadin tuntuni naso in baki wanan shawaran ina gudun ki ce wani abu.
Yanzu ki samu mai sayen gadon ne nace a,a dama kai nake jira ja shigo in fada ma idan ka yarda sai In nemi mai saye din.
Yace kiyi ki shirya to ko za a samu ya shiga a lokaci nace ban samu abinda na dan dafa muna ba yau gaba daya ma ban karya ba tun safe.
A, a ina ko da dari biyar barin baki ku samu abinda kukaci tunda ga kudi zasu dan shigo ya sa hannu a aljihu yana kumbiya kumbiyan ciro kudin kada in gani na tabe bakina tare da kawar da kai gefe daya.
Ya ciro kudin yana miko min duk da lankwashe kudin da yayi alama ya nuna ba shi kadai bane a aljihun shi.
Ni dai na karba tare da daukan hijjabina zan fita don samo muna abinda zamu sarrafa muci da rana don yanzun safiya ya wuce.
Inda na barshi zaune nan na dawo na samay shi yana zaman jiran in dawo ina shigo yake ce min wai nace ai ya kamata a kwabe gadon kada tazo ta samay shi a kafe tace yana da wani bakasu kuma.
Nace hakane kuma fa yanzun dai girki zan dora idan nagama sai in kwabe kafi in tafi yace bari dai in tayaki kwabewa zaifi sauki don in rage maki aiki.
Na fita ya shiga aikin kwabe gadon kafin in gama hada abinci har ya gama ya fitar da gadkn wajen gidan ya jingine su.
Arzikina daya ta kofan baya ya aje kayan gadon ba tare da yan haya gidana sun sani ba balle abin yazama abin magana.
Bata na gama aikina muna zaune muna cin abinci yake fadin idan sauran kudin ku sunzo sai ki samu gado na zamani mai kyau na yayi ki saye.
Ina mamakin Jamil ba wanan ne karo na farko da yake cika min baki kan kudin mu idan ya fito ba sai dai idon kufin sun fito kuma sai abi wani hanya dasu da ban sani ba.
Na samu wata dillaliya mai saye tana sayarwa na kayan daki muka shirya da ita zata zo taga kayan sai tai mashi kudi idan zamu shirya.
Kamar yadda tace din tazo taga gado tace kuma yayi mata nan muka fara cinikin kayan gado da ita.
Dubu talatin ta saye da kyat ta karamin dubu uku sama nace ta kawo kudin an sayar mata take a gurin ta lale mun kudina ta bani ta fita neman wanda zai kwashe matasu
Har aka fitar ba wanda ya sani a gidan shine rufin asirina saidai mai washe gari ina karyawa da safe sai gashi ya fito falon .
Ya samu wuri ya zauna yana fuskanta na nasa yana da magana ke nan si kuwa bamu fi minti ralatin ba ya kawo zancen kudin.
Yana fadin may kika yanke zaKiyi da kudin gadon nan dago kai nayi ina kallon shi nace.
Sana,a nake son yi da wanan kudin ya gyara zama yans fadin sai nake ganin da zaki ban in fita garin nan zuwa wani gari da zaifi.
Dago kai nayi tare da dakatar da abincin da nakeci ina kallon shi ya wani gyara zama yana fadin ko baki yarda dani bane .
Abinda mutane ke fadi zaki dauka ni ba komai yasa nace hakan ba kinga ni wanan zaman da nake haka ya isheni.
Gashi na saba yanzu da sana,a kinga in na fita na juya muna su ba,a san iya albarkan da zasu koma muna ba ai .
Nan dai ya dinga kawo min dadin baki irin nasa yana tsarani har na yarda inda yace wanan karon ba Abuja zai tafi ba zai canza gurine.
Zuwa bakin boarder ance sana yana daukuwa can sosai kamar may kin ga zama haka bazai yuyuba gare mu yanzu ga yaran nan suna tasawa.
Amira na ina son idan na dawo mu sakata makarantar boko ta fara zuwa yakare tare da fadin ko may kikace ga shawarana.
Dan shiru nayi ina nazarin sa sai naga maganar shi kuma gaskiyace idan ya fita din zaifi sana,an da zanyi a nan din samu.
Sai na buda baki nace hakan za ayi sai kaje da kudin mu gani ko Allah zai sa muna albarka a cikin al,amarin.
Wani shu,umin dariya yayi yana cabe yar karamar yar mu tare da fadin mamana babakin ya samu mafita ku tayani da addua, don ance addu,an yara tana kamu sosai.
Tun ranan ya fara shiri kwana daya kawai yayi a tare dani ya kammala kudin shi ya bar garin ya barmu a cikin wani sabon wahala kuma.
Sai da ya tafi naga wautana daga baya na yarda dashi danayi na bashi kudin yanzun gashi ya tafi ya barmu a cikin wahala nida yara.
Nan sabon fadi tashi ya dawo min ina nema abinda zamu ci don ko na omo da sabulu ya ishe ni fama yanzu.
Ance anbin duniya baya boyuwa koda ko kai kadai kayi

Download complete TXT · Novel page